1 Blessed is the man
who does not walk in the advice of the wicked,
or stand in the pathway with sinners,
or sit in the assembly of mockers.
2 But his delight is in the law of Yahweh,
and on his law he meditates day and night.
3 He will be like a tree planted by the streams of water
that produces its fruit in its season,
whose leaves do not wither;
whatever he does will prosper.
4 The wicked are not so,
but are like the chaff that the wind drives away.
5 So the wicked will not stand in the judgment,
nor sinners in the assembly of the righteous.
6 For Yahweh approves of the way of the righteous,
but the way of the wicked will perish.
1 Albarka ga mutum wanda ba ya tafiya a cikin shawarar miyagu ko ya tsaya a hanyar masu zunubi ko ya zauna tare da masu ba'a. 2 Amma yana jin daɗin shari'ar Yahweh, yana nazarinta dare da rana. 3 Zai zama kamar itacen da aka dasa a gefen ƙorama wanda ya ke bada 'ya'yansa a kan kari, ganyayensa ba sa yin yaushi, ya kan yi nasara a dukkan abin da ya ke yi. 4 Mugaye ba haka suke ba, amma suna kamar yayi wanda iska ke kwashewa. 5 Saboda haka mugaye ba zasu tsaya a shari'a ba, ko masu zunubi su taru a wurin adalai ba. 6 Gama Yahweh yana lura da hanyar adalai, Amma hanyar mugaye za ta lalace.
1 Why are the nations in turmoil,
and why do the peoples devise vain plans?
2 The kings of the earth take their stand together
and the rulers take counsel together
against Yahweh and against his Messiah, saying,
3 "Let us tear off the shackles they put on us
and throw off their chains."
4 He who sits in the heavens will sneer at them;
the Lord mocks them.
5 Then he will speak to them in his anger
and terrify them in his rage, saying,
6 "I myself have set my king in place
on Zion, my holy mountain."
7 I will announce a decree of Yahweh.
He said to me, "You are my son!
This day I have become your Father.
8 Ask me, and I will give you the nations for your inheritance
and the ends of the earth for your possession.
9 You will break them with an iron rod;
like a jar of a potter, you will smash them to pieces."
10 So now, you kings, be prudent;
be corrected, you judges of the earth.
11 Worship Yahweh in fear
and rejoice with trembling.
12 Kiss the son or he will be angry with you,
and you will die in the way when his anger burns for just a moment.
How blessed are all those who seek refuge in him.
1 Meyasa al'ummai suke shirin tayarwa, kuma don me mutane ke ƙulla shawarwarin banza? 2 Sarakunan duniya ke ɗaukar matsayi tare, masu mulki kuma suna shirya maƙarƙshiya tare su yi gãba da Yahweh da kuma zaɓaɓɓensa Almasihu, cewa, 3 "Bari mu tsaga karkiyar da suka ɗora a kanmu, kuma mu jefar da sarƙoƙinsu." 4 Shi wanda ke zaune a sammai zai yi masu dariya; Ubangiji yana yi masu ba'a. 5 Ya yi masu magana cikin fushinsa da razanar dasu da kuma hasalarsa, cewa, 6 "Ni da kaina na naɗa sarkina a Sihiyona, tsattsarkan dutsena." 7 Zan yi shelar abin da Yahweh ya furta. Ya ce da ni, "Kai ɗana ne! Wannan rana na zama mahaifinka. 8 Ka roƙe ni, zan kuma ba ka al'ummai don gãdonka da yankunan duniya domin su zama mallakarka. 9 Za ka mallake su da sandar ƙarfe; za ka farfashe su kamar tukunyar yumɓu, za ka ragargaza su su farfashe." 10 To yanzu, ku sarakuna, ku ji gargaɗi; ku mai da hankali, ku sarakunan duniya. 11 Ku bauta wa Yahweh da tsoro da kuma murna tare da rawar jiki. 12 Sumbaci ɗan ko ya yi fushi da ku, zaku mutu ta hanyar fushinsa na ɗan lokaci. Albarka ta tabbata ga dukkan waɗanda ke zuwa gare shi neman mafaka.
1 Yahweh, how many are my enemies!
Many have risen against me.
2 Many say about me,
"There is no deliverance for him from God." Selah
3 But you, Yahweh, are a shield around me,
my glory, and the one who lifts up my head.
4 I lift up my voice to Yahweh,
and he answers me from his holy hill. Selah
5 I lay down and slept;
I awoke, for Yahweh protected me.
6 I will not be afraid of the multitudes of people
who have set themselves against me on every side.
7 Rise up, Yahweh! Save me, my God!
For you will hit all my enemies on the jaw;
you will break the teeth of the wicked.
8 Salvation comes from Yahweh.
May your blessings be on your people. Selah
1 Yahweh, nawa ne maƙiyana! Nawa ne suka tashi suna gãba da ni. 2 Da yawa suna magana a kaina, "Babu taimako dominsa daga Allah." Selah 3 Amma kai, Yahweh, kai ne garkuwa a gare ni, darajata, kuma wanda ke tallafar kaina. 4 Na yi kira da muryata ga Yahweh, ya kuma amsa mani daga tsattsarkan dutsensa. Selah 5 Na kwanta na kuma yi barci; na farka, gama Yahweh ya tsare ni. 6 Ba zan ji tsoron taron mutane waɗanda suka kewaye ni ta kowanne gefe. 7 Tashi, Yahweh! Ka cece ni, Allahna! Gama zaka buga dukkan abokan gãba har ƙasa; zaka kakkarye haƙuran mugaye. 8 Ceto zai zo daga wurin Yahweh. Bari ya sa wa jama'arsa albarka. Selah
1 Answer me when I call, God of my righteousness;
give me room when I am hemmed in.
Have mercy on me and listen to my prayer.
2 You people, how long will you turn my honor into shame?
How long will you love what is worthless and seek after lies? Selah
3 But know that Yahweh has set apart the faithful ones for himself.
Yahweh will hear when I call to him.
4 Tremble in fear, but do not sin!
Meditate in your heart on your bed and be silent. Selah
5 Offer the sacrifices of righteousness
and put your trust in Yahweh.
6 Many say, "Who will show us anything good?"
Yahweh, lift up the light of your face on us.
7 You have given my heart more gladness
than others have when their grain and new wine abound.
8 It is in peace that I will lie down and sleep,
for you alone, Yahweh, make me safe and secure.
1 Ka amsa mani sa'ad da cikin matsuwa nayi kira, Allahna mai adalci; ba ni hutu a lokacin da nake cikin matsuwa. Ka ji tausayina ka kuma saurari addu'ata. 2 Ku mutanen nan, sai yaushe zaku daina juya ɗaukakata zuwa kunya? Har yaushe zaku yi ta ƙaunar abubuwan banza kuna kuma cigaba da neman abin da ya ke na ƙarairayi? Selah 3 Amma kun sani Yahweh ne ya keɓe mai tsoronsa don kansa. Yahweh zai ji idan na yi kira a gare shi. 4 Ku ji tsoro, domin ku daina zunubi! Ku yi nazari a cikin zukatanku a kan gadajenku, kuma ku yi shuru. Selah 5 Ku miƙa hadayun adalci kuna kuma dogara ga Yahweh. 6 Da yawa sun ce, "Wane ne zai nuna mana wani abu mai kyau? Yahweh, ka ɗaga hasken fuskarka a kanmu. 7 Ka ba zuciyata farinciki fiye da na waɗanda ke da wadatar hatsi da sabon ruwa inabi. 8 A cikin salama zan kwanta har barci ya kwashe ni, domin kai kaɗai ne, Yahweh, ka kiyaye ni cikin lafiya sosai.
1 Give ear to my words, Yahweh;
think about my groanings.
2 Listen to the sound of my call, my King and my God,
for it is to you that I pray.
3 Yahweh, in the morning you hear my cry;
in the morning I will bring my petition to you and wait expectantly.
4 Certainly you are not a God who takes pleasure in evil;
evil people will not be your guests.
5 The arrogant will not stand in your presence;
you hate all who behave wickedly.
6 You will destroy liars;
Yahweh abhors the man of bloodshed and deceit.
7 But as for me, because of your great covenant faithfulness,
I will come into your house;
in reverence I will bow down toward your holy temple.
8 Oh Lord, lead me in your righteousness because of my enemies;
make your path straight before me.
9 For there is no truth in their mouth;
their inward being is wicked;
their throat is an open tomb;
they flatter with their tongue.
10 Declare them guilty, God;
may their schemes be their downfall!
Drive them out for their many transgressions,
for they have rebelled against you.
11 But may all those who take refuge in you rejoice;
let them always shout for joy because you defend them;
let them be joyful in you, those who love your name.
12 For you will bless the righteous, Yahweh;
you will surround them with favor as with a shield.
1 Ka saurari kira na zuwa gare ka, Yahweh; kayi tunani a kan nishe-nishena. 2 Ka saurari muryar kirana, sarkina da Allahna, gama a gare ka nake yin wannan addu'ar. 3 Yahweh, da safe kaji kukana; da safe zan kawo rokona gare ka in kuma jira ka. 4 Gaskiya ne kai ba Allahn dake yarda da mugunta ba ne; ko mugayen mutane su zama bãƙinka. 5 Masu fahariya ba zasu tsaya a gabanka ba; kana ƙin dukkan mugaye. 6 Ka kan hallakar da maƙaryata; Yahweh yakan rena masu ta da hankali da mayaudaran mutane. 7 Amma ni, saboda babban alƙawarin ƙaunarka, zan zo cikin gidanka; in kuma rusuna maka da bangirma a tsattsarkan haikalinka. 8 Ya Ubangiji, ka bida ni in aikata adalcinka domin abokan gãbana; ka kuma fayyace mani hanyarka a gabana. 9 Gama babu gaskiya a cikin bakinsu; abubuwansu mugunta ne; harshensu kamar buɗaɗɗen kabari ya ke; suna yaudara da harshensu. 10 Ka furta su masu laifi ne, Allah; bari shirye-shiryensu su zama dalilin faɗuwarsu! Ka kore su sabili da yawan zunubansu, da kuma tayarwar da suke yi maka. 11 Amma bari dukkan waɗanda suka fake gare ka su yi farinciki; bari kullum su yi ta murna don kana kiyaye waɗanda ke ƙaunar sunanka. 12 Gama ka sawa masu adalci albarka, Yahweh; zaka kewaye su da alheri kamar garkuwa.
1 Yahweh, do not rebuke me in your anger
or discipline me in your wrath.
2 Have mercy on me, Yahweh, for I am frail;
heal me, Yahweh, for my bones are shaking.
3 My soul also is very troubled.
But you, Yahweh—how long will this continue?
4 Return, Yahweh! rescue me.
Save me because of your covenant faithfulness!
5 For in death there is no remembrance of you.
In Sheol who will give you thanks?
6 I am weary with my groaning.
All night I drench my bed with tears;
I dissolve my couch with my tears.
7 My eyes grow dim from grief;
they grow weak because of all my adversaries.
8 Get away from me, all you who behave wickedly;
for Yahweh has heard the sound of my weeping.
9 Yahweh has heard my appeal for mercy;
Yahweh has accepted my prayer.
10 All my enemies will be ashamed and greatly troubled.
They will turn back and be suddenly humiliated.
1 Yahweh, kada ka tsauta mani a lokacin fushinka ko ka hukunta ni da fushinka. 2 Ka yi mani jinƙai, Yahweh, gama na tafke sarai, ka warkar da ni, Yahweh, domin ƙasusuwana na makyarkyata. 3 Raina yana damuwa ƙwarai. Amma kai, Yahweh - har sai yaushe wannan zai ci gaba? 4 Ka zo, Yahweh! ka kuɓutar da ni. Ka cece ni domin alƙawarin amincinka! 5 Gama a cikin mutuwa ba a tunawa da kai. Don wane ne zai yi maka godiya a lahira? 6 Na gaji tilis saboda baƙinciki. Dukkan dare gadona ya kan jiƙe da hawayena; Na jiƙa matashin kaina da hawayena. 7 Idanuna sun yi kumburi saboda kuka; sun zama marasa ƙarfi saboda dukkan abokan gãbana. 8 Ku tafi daga wuri na, dukkan ku masu aikin mugunta; Gama Yahweh ya ji kukana. Yahweh ya ji rokona don jinƙai; 9 Yahweh ya amsa mani addu'ata. 10 Dukkan abokan gãbana zasu sha kunya da babbar damuwa. Zasu juya baya tare da babban ƙasƙanci.
1 Yahweh my God, I take refuge in you!
Save me from all who chase me, and rescue me.
2 Otherwise, they will rip me apart like a lion,
tearing me in pieces with no one else able to bring me to safety.
3 Yahweh my God, if I have done this,
and there is injustice on my hands—
4 if I have done evil to him who was at peace with me,
or harmed my enemy for no reason—
5 then let my enemy pursue my life and overtake me;
let him trample my life to the ground
and lay my honor in the dust. Selah
6 Arise, Yahweh, in your anger;
stand up against the rage of my enemies;
wake up for my sake and carry out the righteous decrees that you have commanded for them.
7 The peoples are assembled all around you;
take once more your rightful place over them.
8 Yahweh, judge the nations;
vindicate me, Yahweh, because I am righteous and innocent, Most High.
9 May the evil deeds of the wicked come to an end, but establish the righteous people,
righteous God, you who examine hearts and minds.
10 My shield comes from God,
the one who saves the upright in heart.
11 God is a righteous judge,
a God who is indignant each day.
12 If a person does not repent,
God will sharpen his sword
and will prepare his bow for battle.
13 He prepares to use deadly weapons against him;
he makes his arrows flaming shafts.
14 Think about the one who is pregnant with wickedness,
who conceives destructive plans, who gives birth to harmful lies.
15 He digs a pit and hollows it out
and then falls into the pit he has made.
16 His own destructive plans return to his own head,
for his violence comes down on his own head.
17 I will give thanks to Yahweh for his justice;
I will sing praise to the name of Yahweh Most High.
1 Yahweh Allahna, na sami mafaka a wurinka! Ka cece ni daga dukkan masu nema na, ka ƙwace ni. 2 Idan ba haka ba kuwa zasu ɗauke ni kamar zaki, su yayyaga ni har babu wani da zai kawo mani ceto. 3 Yahweh Allahna, ban aikata abin da maƙiya suka ce nayi ba; babu rashin adalci a cikin hannuwana. 4 Ban yi wani abu da ba dai-dai ga kowa ba wanda muke zaman salama dani, ko da ga wani mai gãba da ni. 5 Idan ba gaskiya nake faɗa ba bari maƙiya su nemi raina har su kama shi; bari ya taka rayayyen jikina a ƙasa ya bar ni da kunyata a ƙura. Selah 6 Ka tashi, Yahweh, cikin fushinka; tashi kayi gãba da hasalar abokan gãbana; ka tashi domina ka aiwatar da alƙawarin amincinka da aka sanka da shi. 7 Dukkan kabilu sun taru a gabanka; ka sake ɗaukar wurinka a bisan su. 8 Yahweh, kai ne alƙalin dukkan alummai; ka 'yantar da ni, Yahweh, gama ni adali ne bani da laifi, Maɗaukaki. 9 Bari mugun abu na masu aikata mugunta ya zo ƙarshe, amma ka tabbatar da adalan mutane, Allah mai adalci, kai kake gwada zukata da tunane-tunane. 10 Kariyata tana zuwa daga Allah, wanda ya ke ceton masu yin adalci a zuciya. 11 Allah ne alƙali mai adalci, Allah wanda ya ke jin haushi a kowacce rana. 12 Idan mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa ya kuma shirya bakansa don yaƙi. 13 Zai shirya kayayyakin faɗa gãba da shi; zai auna kibansa masu wuta. 14 Ka yi tunani akan wanda ya ɗauki ciki da mugunta, wanda ya shirya aiwatar da mugunta, wanda ya haifi cutar ƙarairayi. 15 Yana haƙa rami mai zurfi har kuma ya faɗa ramin da ya gina. 16 Mugun shirin da yayi ya koma a kansa kenan, don rikicin ya sauka a kansa kenan. 17 Zan gode wa Yahweh saboda adalcinsa; zan raira yabo ga Yahweh Maɗaukaki.
1 Yahweh our Lord, how magnificent is your name in all the earth,
you who reveal your glory in the heavens above.
2 Out of the mouth of babies and infants you have established praise [1]
because of your enemies,
so that you might silence both the enemy and the avenger.
3 When I look up at your heavens, the work of your fingers,
the moon and the stars, which you have set in place,
4 Of what importance is the human race that you notice them,
or mankind that you pay attention to them?
5 Yet you have made them only a little lower than the heavenly beings
and have crowned them with glory and honor.
6 You make him to rule over the works of your hands;
you have put all things under his feet:
7 all sheep and oxen,
and even the wild animals of the field,
8 the birds of the heavens, and the fish of the sea,
everything that passes through the currents of the seas.
9 Yahweh our Lord,
how magnificent is your name in all the earth!
1 Yahweh Ubangijinmu, yaya girman sunanka ya ke a dukkan duniya, ka bayyana ɗaukakarka a cikin sammai. 2 Daga cikin bakin yara da jarirai ka shirya yabo domin maƙiyanka, domin ka tsai da abokan gãbarka da ramako. 3 Sa'ad da na duba sararin sammai, wanda yatsunka suka yi, wata da taurari, waɗanda kasa a wuraren zamansu. 4 Mene ne mahimmancin 'yan adam har da kake tunawa da su, ko mutune har da kake lura da su? 5 Duk da haka ka maida su ƙasa kaɗan da halittun dake sama ka kuma naɗa su da ɗaukaka da daraja. 6 Ka sa shi yayi mulkin dukkan abin da kayi da hannuwanka; ka ɗora dukkan abubuwa a ƙarƙashin ƙafafuwansa: 7 dukkan tumaki da shanu har ma da namomin jeji, 8 tsuntsayen sammai da kifayen teku da dukkan halittun dake cikin tekuna. 9 Yahweh Ubangijinmu yaya girman sunanka ya ke a cikin dukkan duniya!
1 I will give thanks to Yahweh with my whole heart;
I will tell about all your marvelous deeds.
2 I will be glad and rejoice in you;
I will sing praise to your name, Most High!
3 When my enemies turn back,
they stumble and perish before you.
4 For you have defended my just cause;
you sit on your throne, a righteous judge!
5 You rebuked the nations;
you have destroyed the wicked;
you have blotted out their name forever and ever.
6 The enemy crumbled like ruins
when you overthrew their cities.
All remembrance of them has perished.
7 But Yahweh remains forever;
he has established his throne for justice.
8 He will judge the world with righteousness,
and he will execute judgment for the nations with fairness.
9 Yahweh also will be a stronghold for the oppressed,
a stronghold in times of trouble.
10 Those who know your name trust in you,
for you, Yahweh, do not abandon those who seek you.
11 Sing praises to Yahweh, who rules in Zion;
tell the nations of his deeds.
12 For the God who avenges bloodshed remembers;
he does not forget the cry of the oppressed.
13 Have mercy on me, Yahweh; see my affliction by those who hate me,
you who can snatch me from the gates of death.
14 Oh, that I might proclaim all your praise.
In the gates of the daughter of Zion
I will rejoice in your salvation!
15 The nations have sunk down into the pit that they made;
their feet are caught in the net that they hid.
16 Yahweh has made himself known; he has executed judgment;
the wicked is ensnared by his own actions. Selah
17 The wicked are turned back and sent to Sheol,
all the nations that forget God.
18 For the needy will not always be forgotten,
nor will the hope of the oppressed be forever dashed.
19 Arise, Yahweh; do not let man win against you;
may the nations be judged in your sight.
20 Terrify them, Yahweh;
may the nations know that they are mere men. Selah
1 Zan yi maka goɗiya Yahweh da dukkan zuciyata; zan furta dukkan abubuwa masu ban mamaki da ka yi. 2 Zan yi murna da farinciki da kai; zan raira waƙar yabo ga sunanka Maɗaukaki! 3 Lokacin da magabtana suka ja da baya, sun faɗi sun mutu a gabanka. 4 Gama kai ka tsare ni; ka zauna a kan kursiyinka, mai shari'ar adalci! 5 Ka kwaɓi al'ummai, ka kuma hallakar da mugaye; ka kawar da sunayensu har abada abadin. 6 An rugurguje abokan gãba kamar kangaye a lokacin da aka lalata biranensu. Dukkan tunawa dasu ya ƙare. 7 Amma Yahweh ka kasance har abada; ka kafa kursiyinka domin yin shari'a. 8 Zan yi mulkin dukkan duniya da adalci, kuma zai yi wa mutane shari'a da gaskiya. 9 Yahweh kuma zai zama mafaka ga waɗanda ake zalunta, wurin ɓuya a lokatan wahala. 10 Waɗanda suka san sunanka zasu dogara gare ka, domin kai ne, Yahweh, ba za ka yi watsi da duk wanda ya neme ka ba. 11 Ku yi waƙar yabo ga Yahweh, wanda ke mulki a Sihiyona; ku faɗa wa al'ummai abin da ya yi. 12 Gama Allah wanda ke ramakon jinin da aka zubar na tunawa; baya mantawa da kukan waɗanda ake cutar su. 13 Ka yi mani jinƙai, Yahweh; dubi yadda waɗanda ke gãba da ni suka wulaƙanta ni, kaine wanda zai kuɓutar da ni daga ƙofofin mutuwa. 14 Dãma inyi shelar dukkan yabonka. A ƙofofin budurwar Sihiyona zan yi farincikin cetonka! 15 Al'ummai sun faɗa cikin ramin da suka haƙa; tarkon da suka kafa don su buya ya kama ƙafafuwansu. 16 Yahweh ya bayyana kansa; ya gudanar da shari'a; mugu ya kama kansa da abubuwan da ya aikata. Selah 17 An maida miyagu makomarsu a Lahira, rabon dukkan waɗanda suka manta da Allah. 18 Gama ba kullum ne ake mantawa da masu buƙata ba ko masu bege waɗanda ake zalunta zasu ɓace har abada. 19 Ka tashi, Yahweh; kada ka bar mutum yayi nasara da kai; bari a yiwa al'ummai hukunci a gabanka. 20 Tsoratar da su, Yahweh; bari al'ummai su sani su mutane ne kawai.
1 Why, Yahweh, do you stand far off?
Why do you hide yourself in times of trouble?
2 Because of their arrogance, wicked people chase the oppressed;
but please let the wicked be trapped by their own schemes that they have devised.
3 For the wicked person boasts of his deepest desires;
he blesses the greedy and insults Yahweh.
4 The wicked in the haughtiness of his face does not seek God.
All his thoughts are that there is no God.
5 He is secure at all times,
but your righteous decrees are too high for him;
he snorts at all his enemies.
6 He says in his heart," I will never fail;
throughout all generations I will not meet adversity."
7 His mouth is full of curses and lies and oppression;
under his tongue are mischief and evil.
8 He waits in ambush near the villages;
in the secret places he murders the innocent;
his eyes look for some helpless victim.
9 He lurks in secret like a lion in the thicket;
he lies in wait to catch the oppressed.
He catches the oppressed when he pulls in his net.
10 His victims are crushed and beaten down;
they fall into his strong nets.
11 He says in his heart, "God has forgotten;
he covers his face; he will never see it."
12 Arise, Yahweh! Lift up your hand, God!
Do not forget the oppressed.
13 Why does the wicked man reject God
and say in his heart, "You will not hold me accountable"?
14 You have taken notice, for you always see the one who inflicts the misery and sorrow.
The helpless entrusts himself to you;
you rescue the fatherless.
15 Break the arm of the wicked and evil man.
Make him account for his evil deeds,
which he thought you would not discover.
16 Yahweh is King forever and ever;
the nations are driven out of his land.
17 Yahweh, you have heard the needs of the oppressed;
you strengthen their heart, you listen to their prayer;
18 You defend the fatherless and the oppressed
so that no man on the earth will cause terror again.
1 Yahweh don me kake tsaye, a can nesa? Me ya sa ka ɓoye kanka a lokatan wahala? 2 Domin fahariyarsu, mugayen mutane na tsananta wa matalauta; amma bari tarkon da mugaye suka ɗana ya kama su. 3 Gama mugun mutum yana fahariya da manufofinsa; yana albarkatar haɗamarsa har yakan zagi Yahweh. 4 Mugun mutum yana ɗaga fuska; ba ya neman Allah. Ba ya tunani a kan Allah domin bai damu ya kula da dukkan al'amura a kansa ba. 5 Ya kan yi nasara a dukkan lokatai, domin adalcin dokokinka sun yi masa tsada; yana furci a kan abokan gãbansa. 6 Ya ce a cikin zuciyarsa, "Ba zan taba faɗuwa ba; a cikin dukkan tsararraki ba zan sadu da wahala ba." 7 Maganganunsa suna cike da zage-zage da yaudara, da mugayen kalmomi; harshensa kuma mai hatsari ne da hallakar wa. 8 Yana kwanto kusa da ƙauyuka; a ɓoyayyun wurare har ya kashe marasa laifi; idanuwansa kuma suna duban waɗanda baza su iya yin komai ba. 9 Yana jira a inda ya ɓuya kamar zaki a cikin kurmi; ya kan kwanta yana fakon wanda zai kama lokacin da yasa tarkonsa. 10 Kamammunsa kuma an buga su har ƙasa; suka faɗa cikin ƙaƙƙarfan ragarsa. 11 Ya ce a cikin zuciyarsa, "Allah ya manta; ya rufe fuskarsa; ba zai damu ya duba ba." 12 Tashi, Yahweh! Ɗaga hannunka, Allah! Kada ka manta da waɗanda ake tsanantawa. 13 Me yasa mugun mutum zai ƙi Allah har ya ce a cikin zuciyarsa, "Ba zai kama ni da wani alhaki ba"? 14 Kana kula da komai, don kullum kana ganin wanda ake sa masa damuwa da baƙinciki. Kana sa mai bukata yasa dogararsa a gare ka; kana kuɓutar da marasa iyaye. 15 Ka karya hannun mugu da mai aikata mugunta. Kasa ya ɗauki laifin mugun aikinsa, kada ya yi tunanin ba za a taba ganewa ba. 16 Yahweh Sarki na har abada abadin; al'ummai kuma za a kore su daga ƙasarsa. 17 Yahweh, ka ji buƙatun wanda ake tsanantawa; ka karfafa zukatansu, ka saurari addu'arsu. 18 Zaka kãre marasa iyaye da waɗanda ake ƙuntata masu saboda babu wani mutum a wannan duniya da zai sake jawo razana.
1 I take refuge in Yahweh;
how will you say to me,
"Flee like a bird to the mountain"?
2 For see! The wicked prepare their bows.
They make ready their arrows on the strings
to shoot in the darkness at the upright in heart.
3 For if the foundations are ruined,
what can the righteous do?
4 Yahweh is in his holy temple;
his eyes watch, his eyes examine the children of mankind.
5 Yahweh examines both the righteous and the wicked,
but he hates those who love to do violence.
6 He rains burning coals and sulfur upon the wicked;
a scorching wind will be their portion from his cup!
7 For Yahweh is righteous, and he loves righteousness;
the upright will see his face.
1 Na sami mafaka a wurin Yahweh; yaya zaka ce da ni, "Ka tashi kamar tsuntsu akan tsauni"? 2 Amma duba! miyagu sun shirya ƙibansu a kan tsarkiya don su harba cikin duhu a zuciyar adali. 3 Gama idan ginshiƙai suka lalace, mene ne adali zai iya yi? 4 Yahweh yana cikin tsatsarkan haikalinsa; idanuwansa suna kallo, idanuwansa suna gwada 'ya'yan 'yan adam. 5 Yahweh yana gwada masu kirki da miyagu dukka, amma yana ƙin waɗanda ke ƙaunar tashin hankali. 6 Yana ruwan garwashin wuta da ƙibiritu a kan mugaye; iska zata kone rabonsu daga finjilinsa! 7 Gama Yahweh mai adalci ne, yana kuma ƙaunar masu gaskiya; adalai kuma zasu ga fuskarsa.
1 Help, Yahweh, for the faithful ones have disappeared;
those who have integrity have vanished from the children of men.
2 Everyone says empty words to his neighbor;
everyone speaks with flattering lips and a double heart.
3 Yahweh, cut off all flattering lips,
every tongue declaring great things.
4 These are those who have said, "With our tongues we will prevail.
When our lips speak, who can be master over us?"
5 "Because of violence against the poor, because of the groans of the needy,
I will arise," says Yahweh.
"I will provide the safety for which they long."
6 The words of Yahweh are pure words,
like silver purified in a furnace on the earth,
refined seven times.
7 You are Yahweh! You keep them.
You preserve the godly people from this wicked generation and forever.
8 The wicked walk on every side
when evil is exalted among the children of mankind.
1 Ka yi taimako, Yahweh, saboda mutanen kirki sun ɓace; aminitattu ma sun ɓace. 2 Kowanne mutum yana maganar banza ga maƙwabcinsa; kowanne yana maganar yaudara da leɓuna da zuciya biyu. 3 Yahweh, ka datsa dukkan leɓunan yaudara, kowanne harshe ya riƙa faɗin manyan abubuwa. 4 Waɗannan sune waɗanda suka ce, "Ta wurin harshenmu zamu rinjaya. Sa'ad da leɓunanmu suka yi magana, wane ne zai zama gwani a bisanmu?" 5 "Saboda tashin hankali akan matalauta, domin nishin masu buƙata, zan tashi," inji Yahweh. "Zan basu tsaron da suka yi marmari." 6 Kalmomin Yahweh kalmomi ne zalla, kamar azurfar da aka narkar a tanderun wuta, aka tace har sau bakwai. 7 Kai ne Yahweh! Ka kiyaye su. Ka tsare mutanen kirki daga muguwar tsara har abada. 8 Mugaye suna tafiya ko'ina a lokacin da mugunta ke ɗaukaka a cikin 'yan adam.
1 How long, Yahweh, will you forget me? Forever?
How long will you hide your face from me?
2 How long must I worry
and have grief in my heart all day?
How long will my enemy triumph over me?
3 Look at me and answer me, Yahweh my God!
Give light to my eyes, or I will sleep in death.
4 Do not let my enemy say, "I have defeated him,"
so that my enemy may not say, "I have prevailed over my adversary";
otherwise, my enemies will rejoice when I am brought down.
5 But I have trusted in your covenant faithfulness;
my heart rejoices in your salvation.
6 I will sing to Yahweh
because he has treated me very generously.
1 Yahweh, har sai yaushe, za ka ci gaba da mantawa da ni? Har yaushe ne zaka ɓoye mani fuskarka daga gare ni? 2 Har yaushe ne zan daina damuwa da baƙinciki a zuciyata dukkan yini? Har yaushe ne maƙiyana zasu rika cin nasara a kaina? 3 Ka dube ni ka kuma amsa mani, Yahweh Allahna! Ka bani haske ga idanuwana, ko in yi barcin mutuwa. 4 Kada ka bar maƙiyina ya ce, "Na ce nasara a kansa," don kada maƙiyina ya sami abin cewa, "Na yi rinjaye akan abokin gãbana;" idan ba haka ba, maƙiyina zai yi murna saboda faɗuwata. 5 Amma na dogara ga amintaccen alƙawarinka; zuciyata zata yi murna da cetonka. 6 Zan yi waƙa ga Yahweh domin ya yi mani abin kirki ƙwarai.
1 A fool says in his heart, "There is no God."
They are corrupt and have done abominable iniquity;
there is no one who does good.
2 Yahweh looks down from heaven on the children of mankind
to see if there are any who understand,
who seek after him.
3 They have all turned away. Together they have become corrupt.
There is no one who does good, no, not one.
4 Do they not know anything, those who behave wickedly,
those who eat up my people as they eat bread,
but who do not call on Yahweh?
5 They tremble with dread,
for God is with the righteous generation!
6 You want to humiliate the poor person
even though Yahweh is his refuge.
7 Oh, that the salvation of Israel would come from Zion!
When Yahweh brings back his people from the captivity,
then Jacob will rejoice and Israel will be glad!
1 Wawa yace a cikin zuciyarsa, "Ba Allah." Sun lalace sun kuma aikata laifin ban ƙyama; babu wani wanda ya aikata nagarta. 2 Yahweh ya duba ƙasa daga sama a kan 'yan adam ya gani idan ko akwai wani mai fahimta, wanda ke neman sa. 3 Dukkansu sun koma baya. Ga baki ɗayansu sun zama marasa kirki. Ba wanda ya ke aikata abin da ya ke dai-dai, babu ko ɗaya. 4 Sun san wani abu, waɗanda suka aikata laifi, waɗanda suke cin mutanena kamar yadda suke cin gurasa, amma wane ne ba ya kiran Yahweh? 5 Sun razana tare da fargaba, gama Allah yana tare da taruwar adalai! 6 Kuna so ku ci mutuncin matalaucin mutum koda ya ke Yahweh ne mafakarsa. 7 Oh, dama ceton Isra'ila zai zo daga Sihiyona! Sa'ad da Yahweh ya dawo da mutanensa daga bauta, Yakubu zai yi murna, Isra'ila ma zata yi farinciki!
1 Yahweh, who may stay in your tabernacle?
Who may live on your holy hill?
2 Whoever walks blamelessly, does what is right
and speaks truth from his heart.
3 He does not slander with his tongue,
he does not harm others,
and he does not insult his neighbor.
4 The abhorrent is despised in his eyes,
but he honors those who fear Yahweh.
He swears to his own disadvantage
and does not take back his promises.
5 He does not charge interest when he lends money.
He does not take bribes to testify against the innocent.
He who does these things will never be shaken.
1 Yahweh, wane ne zai iya tsaya wa a rumfar sujadarka? Wa zai iya zama a tudun ka mai tsarki? 2 Duk wanda ba shi da laifi, wanda ke aikata abin dake dai-dai wanda kuma ya ke faɗar gaskiya daga zuciyarsa. 3 Wanda baya ɓatanci da harshensa, baya cin mutuncin wasu, baya ɓatanci ga maƙwabcinsa. 4 Mutumin wofi abin reni ne a idanunsa, amma yana girmama waɗanda ke tsoron Yahweh. Yana rantsuwa ba don kansa ba, kuma yana cika alƙawaran da yayi. 5 Baya karɓar ruwa a kuɗin da ya bayar bashi. Baya karɓar cin hanci don ya yi shaidar zur a kan marar laifi. Duk wanda ya ke yin waɗannan abubuwa ba zai taɓa girgiza ba.
1 Protect me, God,
for I take refuge in you.
2 I say to Yahweh, "You are my Lord;
my goodness is nothing apart from you.
3 As for the holy people who are on the earth,
they are noble people; all my delight is in them.
4 Their troubles will be increased, those who seek out other gods.
I will not pour out drink offerings of blood to their gods
or lift up their names with my lips.
5 Yahweh, you are my chosen portion and my cup.
You hold onto my lot.
6 Measuring lines have been laid for me in pleasant places;
surely a beautiful inheritance is mine.
7 I will bless Yahweh, who counsels me;
even at night my mind instructs me.
8 I set Yahweh before me at all times,
so I will not be shaken from his right hand!
9 Therefore my heart is glad; my glory is rejoicing.
Surely I will live in security.
10 For you will not abandon my soul to Sheol.
You will not let your faithful one see the pit.
11 You teach me the path of life;
abundant joy resides in your presence;
delights abide in your right hand forever!"
1 Ka tsare ni, Allah, gama na zo neman mafaka a gare ka. 2 Na ce da Yahweh, "Kai ne Ubangijina; nagarta ta a banza take idan bana tare da kai. 3 Kamar yadda tsarkakakkun mutane waɗanda ke a duniya, su mutane masu kirki; dukkan murnata a gare su take. 4 Wahalolinsu zasu ƙaru, waɗanda ke neman waɗansu gumaka. Ba zan zubo masu da baye-baye na shan jinin allolinsu ba ko in furta sunayensu da leɓuna na ba. 5 Yahweh, kaine kaɗai na zaɓa da ƙoƙona. Kai ne kake riƙe da rabona. 6 An ajiye ma'aunan layi domina a wuraren jin daɗi; babu shakka gãdon dake kawo jin daɗi nawa ne. 7 Zan albarkaci Yahweh, wanda ke bani shawara; ko da dare ma ina tunanin umarninsa. 8 Na sa kaina a wurin Yahweh a dukkan lokuta, saboda kada in girgiza daga hannun damarsa! 9 Don haka cike nake da murna; ɗaukakata na farinciki. Babu shakka zan zauna a cikin tsaro. 10 Saboda baza ka bar raina a Lahira ba. Ba zaka bar amintaccenka ya ga rami ba. 11 Ka koya mani hanyar rai; yalwataccen farinciki na kasancewarka; murna zata zauna a hannun damarka har abada!"
1 Listen to my plea for justice, Yahweh;
pay attention to my cry for help!
Give ear to my prayer from lips without deceit.
2 Let my vindication come from your presence;
let your eyes see what is right!
3 If you test my heart, if you come to me in the night,
you will purify me and will not find any evil plans;
my mouth will not transgress.
4 As for the deeds of mankind,
it is at the word of your lips
that I have kept myself from the ways of the lawless.
5 My steps have held firmly to your tracks;
my feet have not slipped.
6 I call to you, for you answer me, God;
turn your ear to me and listen when I speak.
7 Show your covenant faithfulness in a wonderful way,
you who save by your right hand
those who take refuge in you from their enemies!
8 Protect me like the apple of your eye;
hide me under the shadow of your wings
9 from the presence of the wicked ones who deal violently with me,
my enemies who surround me.
10 They have no mercy on anyone;
their mouths speak with pride.
11 They have surrounded my steps.
They set their eyes to strike me to the ground.
12 They are like a lion eager for a victim,
like a young lion crouching in hidden places.
13 Arise, Yahweh! Attack them! Throw them down on their faces!
Rescue my life from the wicked by your sword!
14 Rescue me from men by your hand, Yahweh,
from men of this world whose prosperity is in this life alone!
You will fill the bellies of your treasured ones with riches;
they will have many children
and will leave their wealth to their children.
15 As for me, I will see your face in righteousness;
I will be satisfied, when I awake, with a sight of you.
1 Ka kasa kunne ga roƙona don adalci, Yahweh; ka saurari kirana na neman taimako! Ka kasa kunne ga addu'ata daga leɓuna marasa yaudara. 2 Bari baratarwata ta zo daga wurinka; bari idanuwanka su ga abin dake dai-dai! 3 Idan zaka gwada zuciyata, idan zaka zo gare ni da dare, zaka tsarkakeni ba kuma za a sami wata mugunta a shirye-shiryena ba; bakina ba zai yi saɓo ba. 4 Game kuma da ayyukan mutane; sune a cikin maganar leɓunanka waɗanda na tsare kaina daga hanyoyi na marasa bin doka. 5 Na yi tafiya a kan tafarkinka sosai; sawayena basu kauce ba. 6 Na yi kira a gare ka, domin ka amsa mani, ya Allah; ka juyo da kunnenka gare ni ka kuma saurara a lokacin da na yi magana. 7 Ka nuna mani amintaccen alƙawarinka ta hanya mai banmamaki, kai da ke yin ceto ta hannun damarka ga waɗanda ke neman mafaka a gare ka daga maƙiyansu! 8 Ka tsare ni kamar ƙwayar idanunka; ka ɓoye ni a ƙarƙashin inuwar fukafukanka 9 daga fuskar miyagu waɗanda ke zargi na, maƙiyana da suka kewaye ni. 10 Basa jin tausayin kowa; bakunansu na magana da fahariya. 11 Sun kewaye sawayena. Sun sa idanuwansu don su fyaɗa ni ƙasa. 12 Su kamar zakoki ne sun ƙosa su ga abin da zasu hallaka, kamar 'ya'yan zakoki suna laɓe a ɓoyayyun wurare. 13 Ka tashi, Yahweh! Ka hare su! Ka jefar da su a ƙasa a kan fuskokinsu! Ka cece raina daga takobin mugaye! 14 Yahweh, ka cece ni daga gare su da hannun ka, daga mutanen wannan duniya waɗanda arziƙinsu a cikin wannan rayuwa ne kaɗai! Za ka cike wuraren ajiyar mutanenka da arziki; zasu zama da 'ya'ya dayawa kuma zasu bar wadatarsu ga 'ya'yansu. 15 Amma ni, zan ga fuskarka a cikin adalci; zan gamsu, sa'ad da na farka, da ganin ka.
1 I love you, Yahweh, my strength.
2 Yahweh is my rock, my fortress, the one who brings me to safety;
he is my God, my rock; I take refuge in him.
He is my shield, the horn of my salvation, and my stronghold.
3 I will call on Yahweh who is worthy to be praised,
and I will be saved from my enemies.
4 The cords of death surrounded me,
and the rushing waters of worthlessness overwhelmed me.
5 The cords of Sheol surrounded me;
the snares of death trapped me.
6 In my distress I called to Yahweh;
I called for help to my God.
He heard my voice from his temple;
my cry for help went into his presence;
it went into his ears.
7 Then the earth shook and trembled;
the foundations of the mountains also trembled
and were shaken because God was angry.
8 Smoke went up from out of his nostrils,
and blazing fire came out of his mouth.
Coals were kindled by it.
9 He opened the heavens and came down,
and thick darkness was under his feet.
10 He rode on a cherub and flew;
he glided on the wings of the wind.
11 He made darkness a tent around him,
heavy rainclouds in the skies.
12 Hailstones and coals of fire fell from the lightning before him.
13 Yahweh thundered in the heavens!
The voice of the Most High shouted. [1]
14 He shot his arrows and scattered his enemies;
many lightning bolts dispersed them.
15 Then the water channels appeared;
the foundations of the world were laid bare
at your rebuke, Yahweh,
at the blast of the breath of your nostrils.
16 He reached down from above; he took hold of me!
He pulled me out of the surging water.
17 He rescued me from my strong enemy,
from those who hated me, for they were too strong for me.
18 They came against me on the day of my distress
but Yahweh was my support!
19 He set me free in a wide open place;
he saved me because he was pleased with me.
20 Yahweh has rewarded me because of my righteousness;
he has restored me because my hands were clean.
21 For I have kept the ways of Yahweh
and have not wickedly turned away from my God.
22 For all his righteous decrees have been before me;
as for his statutes, I have not turned away from them.
23 I have also been innocent before him,
and I have kept myself from iniquity.
24 Therefore Yahweh has restored me because of my righteousness,
because my hands were clean before his eyes.
25 To one who is faithful, you show yourself to be faithful;
to a man who is blameless, you show yourself to be blameless.
26 To one who is pure, you show yourself to be pure;
but to one who is perverse, you show yourself to be shrewd.
27 For you save afflicted people,
but you abase those with proud, uplifted eyes!
28 For you give light to my lamp;
Yahweh my God lights up my darkness.
29 For by you I can run over a barricade;
by my God I can leap over a wall.
30 As for God—his way is perfect!
The word of Yahweh is pure!
He is a shield to everyone who takes refuge in him.
31 For who is God except Yahweh?
Who is a rock except our God?
32 It is God who puts strength on me like a belt,
who places the blameless person on his path.
33 He makes my feet swift like a deer
and places me on the heights!
34 He trains my hands for war
and my arms to bend a bow of bronze.
35 You have given me the shield of your salvation.
Your right hand has supported me,
and your favor has made me great.
36 You have made a wide place for my feet beneath me
so that my feet have not slipped.
37 I pursued my enemies and caught them;
I did not turn back until they were destroyed.
38 I smashed them so that they were unable to rise;
they have fallen under my feet.
39 For you have girded me with strength for battle;
you put under me those who rise up against me.
40 You gave me the back of my enemies' necks;
I annihilated those who hated me.
41 They called for help, but no one saved them;
they called out to Yahweh, but he did not answer them.
42 I beat them into fine pieces like dust before the wind;
I threw them out like mud in the streets.
43 You rescued me from the disputes of people;
you have made me head over nations;
people whom I have not known serve me.
44 As soon as they heard of me, they obeyed me;
foreigners were forced to bow to me.
45 The foreigners came trembling out of their strongholds.
46 Yahweh lives; may my rock be praised.
May the God of my salvation be exalted.
47 He is the God who executes vengeance for me,
who subdues the nations under me.
48 I am set free from my enemies!
Indeed, you lifted me above the ones who rose against me!
You rescued me from violent men.
49 Therefore I will give thanks to you, Yahweh, among the nations;
I will sing praises to your name!
50 God gives great victory to his king,
and he shows his covenant loyalty to his anointed one,
to David and to his descendants forever.
1 Ina ƙaunarka, Yahweh, ƙarfina. 2 Yahweh ne dutsena, hasumiya ta, wanda ke kawo mani tsaro; shi ne Allahna, dutsena; zan ɓoye a cikinsa. Shi ne garkuwata, ƙahon cetona, shi ne kuma ƙarfina. 3 Zan yi kira ga Yahweh wanda ya cancanci a yabe shi, za a kuma cece ni daga maƙiyana. 4 Sarƙoƙin mutuwa sun kewaye ni, hargowar ruwaye marasa daraja sun sha kaina. 5 Sarƙoƙin Lahira sun kewaye ni; tarkon mutuwa kuwa ya kama ni. 6 A cikin ƙuncina na yi kira ga Yahweh; na yi kiran neman taimako ga Allahna. Ya ji muryata daga haikalinsa; kirana na neman taimako ya kai gare shi; ya shiga har cikin kunnuwansa. 7 Sai duniya ta raurawa ta girgiza; ginshiƙan duwatsu kuwa suka jijjigu suka kuma yi rawar jiki saboda Allah ya husata. 8 Hayaƙi kuwa ya yi ta tuƙaƙowa daga kafofin hancinsa, harshen wuta ya fito daga bakinsa. Gawayin garwashi suka fita ta wurinsa. 9 Ya buɗe sammai ya sauko ƙasa, duhu kuma baƙiƙƙirin na ƙarƙashin ƙafafunsa. 10 Ya hau kan kerub ya tashi; ya yi tafiya a kan fikafikan iska. 11 Ya maida duhu rumfa a kewaye da shi, gizagizan ruwan sama masu nauyi a sararin sama. 12 Ƙanƙara da garwashin wuta sun faɗo daga walƙiya dake gabansa. 13 Yahweh ya yi tsawa a cikin sammai! Muryar Maɗaukaki ta yi tsawa. 14 Ya harba kibansa, ya warwatsar da magabtansa; walƙatawar walƙiyoyi ta warwatsar da su. 15 Daga nan hanyoyin ruwa suka bayyana; ginshiƙan duniya dukka aka bayyana su a cikin kukan yaƙinka, Yahweh- a cikin hurawa mai ƙarfi ta numfashin kafofin hancinka. 16 Ya miƙo hannunsa ƙasa daga samaniya; ya riƙe ni! Ya tsamo ni daga cikin ruwa mai zurfi. 17 Ya kuɓutar da ni daga ƙaƙƙarfan abokin gãbata, daga waɗanda ke ƙi na, domin sun fi ni ƙarfi sosai. 18 Sun tasar mani a ranar shan ƙuncina amma Yahweh ne mai taimako na! 19 Ya fitar da ni daga hatsari a buɗaɗɗen wuri; ya cece ni domin yana farinciki dani. 20 Yahweh ya sãka mani saboda adalcina; ya dawo da ni saboda hannuwana na da tsarki. 21 Domin na kiyaye tafarkun Yahweh ban kuma juya ga mugunta daga Allahna ba. 22 Gama dukkan ka'idodinsa na adalci suna gaba na; game kuma da fariilansa, ban kauce daga gare su ba. 23 Na kuma zama marar laifi a gabansa, na kiyaye kaina daga zunubi. 24 Domin haka Yahweh ya dawo dani saboda adalcina, domin hannuwana masu tsafta ne a idanunsa. 25 Ga kowanne mai aminci, kana nuna kanka mai aminci; ga mutum marar laifi, ka nuna kanka marar laifi. 26 Ga duk wani mai tsarki, ka nuna kanka mai tsarki; amma kana da dabara ga duk mai aikin mugunta. 27 Gama kana ceton mutane daga wahala, amma ka kan ƙasƙantar da masu girmankai da suka ɗaga idanunsu! 28 Domin ka bada haske ga fitilata; Yahweh Allahna ka haskaka duhuna. 29 Gama ta wurinka zan iya tserewa maƙiyana; ta wurin Allahna zan iya tsallake saman katanga. 30 Kamar yadda Allah ya ke, hanyarsa dai-dai take. Maganar Yahweh tsartsarka ce! Shi garkuwane ga duk wanda yake neman mafaka a wurinsa. 31 Gama wane ne Allah sai Yahweh? Wane ne dutse in ba Allahnmu ba? 32 Shi ne Allahn dake ƙarfafa ni kamar ɗammara, wanda ya ke sa mutanen da basu da aibu a kan hanyarsa. 33 Yana tabbatar da lafiyar ƙafafuna kamar barewa ya kuma sa ni a bisa! 34 Yakan koyar da hannuwana don yaƙi makamaina kuma za su tankware bakan tagulla. 35 Kai ka bani garguwar cetona. Hannunka na dama yana ƙarfafa ni, tagomashinka kuma ya maida ni babba. 36 Kayi mani buɗaɗɗen wuri don ƙafafuwana suna ƙarƙashina saboda kada santsi ya ɗauke ƙafafuwana. 37 Na kori maƙiyana har na kama su; ban juya ba har sai da na lalata su dukka. 38 Na buga su har ba wanda zai iya tashi; sun faɗi a ƙarƙashin ƙafafuna. 39 Gama ka sa ƙarfi a kaina kamar ɗamara don yaƙi; ka sa waɗanda ke gãba da ni a ƙarƙashina. 40 Ka bani nasara akan maƙiyana; zan hallaka waɗanda ke gãba da ni. 41 Suna kira don taimako, amma babu wani da ya cece su; sun yi kira ga Yahweh, amma bai amsa masu ba. 42 Na buge su har sun zama gutsu-gutsu kamar ƙura a fuskar iska; na jefar da su waje kamar laka a tituna. 43 Ka cece ni daga mutane masu husuma. Ka maida ni shugaba a kan al'ummai. Mutanen da ban san su ba, ban ma yi masu aiki ba. 44 Yayin da suka ji ni, zasu yi mani biyayya; bãƙi zasu rusuna mani dole. 45 Bãƙin zasu zo da rawar jiki daga kagarunsu. 46 Yahweh mai rai ne; dutsena abin yabo. Allah mai cetona a gimama shi. 47 Shi ne Allah wanda ya ke ɗaukar fansa domina, yana sawa a rinjaye al'ummai a ƙarƙashina. 48 Ni 'yantacce ne daga maƙiyana! Lalle, ka ɗaukaka ni sama da waɗanda suka taso suna gãba da ni! Ka cece ni daga mutane masu tawaye. 49 Saboda haka zan yi yabo a gare ka, Yahweh, a cikin al'ummai; zan raira maka waƙar yabon sunanka! 50 Allah yana bada babbar nasara ga sarkinsa, ya kan nuna amintaccen alƙawarinsa ga wanda ya zaɓa, ga Dauda da zuriyarsa har abada.
1 The heavens declare the glory of God,
and the skies make known the work of his hands!
2 Day after day speech pours out;
night after night it reveals knowledge.
3 There is no speech or spoken words;
their voice is not heard.
4 Yet their words go out over all the earth,
and their speech to the end of the world.
He has pitched a tent for the sun among them.
5 The sun is like a bridegroom coming out of his chamber
and like a strong man who rejoices when he runs his race.
6 The sun rises from the one horizon
and crosses the sky to the other;
nothing escapes its heat.
7 The law of Yahweh is perfect,
restoring the soul;
the testimony of Yahweh is reliable,
making the simple wise.
8 The instructions of Yahweh are right,
making the heart glad;
the commandment of Yahweh is pure,
bringing light to the eyes.
9 The fear of Yahweh is pure,
enduring forever;
the righteous decrees of Yahweh are true
and altogether right!
10 They are of greater value than gold,
even more than much fine gold;
they are sweeter than honey
and the dripping honey from the honeycomb.
11 Yes, by them your servant is warned;
in obeying them there is great reward.
12 Who can discern all his own errors?
Cleanse me from hidden faults.
13 Keep your servant also from arrogant sins;
let them not rule over me.
Then I will be perfect,
and I will be innocent from many transgressions.
14 May the words of my mouth and the meditation of my heart
be acceptable in your sight,
Yahweh, my rock and my redeemer.
1 Sammai na bayyana ɗaukakar Allah, sararin sama kuma na bayyana ayyukan hannunsa! 2 A kowacce rana ana fitar da magana; dare bisa dare na bayyana ilimi. 3 Babu magana ko kalma da aka furta; ba a ji amonsu ba. 4 Duk da haka maganarsu ta tafi dukkan duniya, jawabinsu kuma har ƙarshen duniya. Ya kafa rumfa domin rana a cikinsu. 5 Rana kamar ango na taƙama daga kagararsa, kuma kamar ƙaƙƙarfan mutum wanda ke farinciki idan ya ƙosa ya yi tsere. 6 Rana tana fitowa daga ɗaya gefen zuwa ɗaya tsallaken; ba abin da zai tsere daga zafinta. 7 Dokar Yahweh cikakkiya ce, tana wartsakar da rai; shaidar Yahweh kuwa abar dogara ce, tana ba da hikima ga masu buƙata. 8 Ka'idodin Yahweh dai-dai suke, tana sa zuciya ta ji daɗi; umarnin Yahweh na da kyau, yana kawo haske ga idanuwa. 9 Tsoron Yahweh tsabbatacce ne, tabbatacce ne har abada; dokokin Yahweh gaskiya ne dukkansu dai-dai suke! 10 Suna da girma da daraja fiye da zinariya, fiye ma da zinariyar da aka tace; sun fi zuma zaƙi, zuman dake ɗigowa daga saƙarsa. 11 I, ta wurinsu bawanka ya sami gargaɗi; akwai lada mai girma idan an yi biyayya dasu. 12 Wane ne zai iya rarrrabe kuskuren kansa? Ka tsabtacce ni daga ɓoyayyun laifuffuka. 13 Ka tsare bawanka kuma daga zunubai marasa kangado; kada ka bari su yi mulki a kaina. Sa'an nan ne zan zama kamili, zan kuma zama mara laifi daga laifuffukana masu yawa. 14 Ka sa maganar baƙina da tunanin zuciyata su zama abin karɓa a wurinka, Yahweh, dutsena da fansata.
1 May Yahweh help you in the day of trouble;
may the name of the God of Jacob protect you
2 and send help from the holy place
to support you from Zion.
3 May he call to mind all your offerings
and accept your burnt sacrifice. Selah
4 May he grant you your heart's desire
and fulfill all your plans.
5 Then we will rejoice in your victory,
and, in the name of our God, we will raise banners.
May Yahweh grant all your petitions.
6 Now I know that Yahweh will rescue his anointed one;
he will answer him from his holy heaven
with the saving strength of his right hand.
7 Some trust in chariots and others in horses,
but we trust in the name of Yahweh our God.
8 They will be brought down and fall,
but we will rise and stand upright!
9 Yahweh, rescue the king;
help us when we call.
1 Bari Yahweh ya taimake ka a ranar wahala; bari sunan Allah na Yakubu ya tsare ka, 2 ya kuma aika taimako daga wuri mai tsarki ya kawo maka tallafi daga Sihiyona. 3 Bari ya tuna da dukkanbaye-bayenka ya kuma karɓi hadayun ƙonawarka. Selah 4 Ya biya maka buƙatar zuciyarka, ya kuma cika maka dukkan shirye-shiryenka. 5 Sai mu yi sowa ta farinciki saboda ka ci nasara, a cikin sunan Allahnmu, zamu ɗaga tutoci. Yahweh zai biya dukkan roƙe-roƙenmu. 6 Yanzu dai na sani Yahweh zai ceci zaɓaɓɓensa; zai amsa masa daga wurinsa mai tsarki a sama da iko a hannun damarsa wanda ya cece shi. 7 Waɗansu sun dogara ga karusansu wasu kuma ga dawakansu, amma mu muna kira ga Yahweh Allahnmu. 8 Su zasu yi tuntuɓe har su faɗi ƙasa, amma mu zamu tashi mu tsaya daram! 9 Yahweh, ka ceci sarki; ka taimake mu sa'ad da muka yi kira.
1 The king rejoices in your strength, Yahweh!
How greatly he rejoices in the salvation you provide!
2 You have given him his heart's desire
and have not held back the request of his lips. Selah
3 For you bring him rich blessings;
you placed on his head a crown of purest gold.
4 He asked you for life; you gave it to him;
you gave him the length of his days forever and ever.
5 His glory is great because of your victory;
you have bestowed on him splendor and majesty.
6 For you grant him lasting blessings;
you make him glad with the joy of your presence.
7 For the king trusts in Yahweh;
through the covenant faithfulness of the Most High
he will not be moved.
8 Your hand will seize all your enemies;
your right hand will seize those who hate you.
9 At the time of your anger,
you will burn them up as in a fiery furnace.
Yahweh will consume them in his wrath,
and the fire will devour them.
10 You will destroy their offspring from the earth
and their descendants from among the human race.
11 For they intended evil against you;
they conceived a plot with which they will not succeed!
12 For you will turn them back;
you will draw your bow before them.
13 Be exalted, Yahweh, in your strength;
we will sing and praise your power.
1 Sarki na yi farinciki cikin ƙarfinka, Yahweh! Babu iyaka ga farincikinsa daga cikin ceton da ka tanada! 2 Ka biya masa buƙatar zuciyarsa baka kuma hana masa roƙon leɓunansa ba. Selah. 3 Gama ka kawo masa albarku masu wadata; ka sanya bisa kansa kambi na tsabar zinariya. 4 Ya nemi rai daga gare ka; ka bashi; ka bashi tsawon kwanaki har abada abadin. 5 Darajarsa na da girma sabili da nasarar ka; ka ɗibiya masa daraja da ɗaukaka. 6 Gama ka bashi madawwaman albarku; ka sashi jin daɗi da farinciki da ke a gabanka. 7 Gama sarki yana dogara ga Yahweh; ta wurin alƙawarin amincin Maɗaukaki ba zaya jijjigu ba. 8 Hannunka zaya kama dukkan maƙiyanka; Hannunka na dama zaya kama waɗanda suka ƙi ka. 9 A lokacin hasalarka; zaka ƙona su sarai kamar daga cikin tanderu mai ƙuna. Yahweh zai haɗiye su cikin hasalarsa, kuma wutar za ta cinye su. 10 Zaka hallakar da zuriyarsu daga ƙasar kuma zuriyarsu daga cikin 'yan adam. 11 Gama sun shirya yi maka mugunta; sun tsiro da shiri wanda ba za su iya yin nasara ba! 12 Gama za ka sa su koma da baya; zaka jã kwarinka a fuskarsu. 13 Ka ɗaukaka, Yahweh, cikin ƙarfin ka; zamu raira waƙa mu kuma yaɓi ikonka.
1 My God, my God, why have you abandoned me?
Why are you so far from saving me
and far from the words of my anguish?
2 My God, I cry out in the daytime, but you do not answer,
and at night I am not silent!
3 Yet you are holy;
you sit as king with the praises of Israel.
4 Our ancestors trusted in you;
they trusted in you, and you rescued them.
5 They cried to you and they were rescued.
They trusted in you and were not disappointed.
6 But I am a worm and not a man,
a disgrace to humanity and despised by the people.
7 All those who see me taunt me;
they mock me; they shake their heads at me.
8 They say, "He trusts in Yahweh;
let Yahweh rescue him.
Let him rescue him, for he delights in him."
9 For you brought me from the womb;
you made me trust you when I was on my mother's breasts.
10 I have been thrown on you from the womb;
you are my God since I was in my mother's womb!
11 Do not be far away from me, for trouble is near;
there is no one to help.
12 Many bulls surround me;
strong bulls of Bashan surround me.
13 They open their mouths wide against me
like a roaring lion ripping its victim.
14 I am being poured out like water,
and all my bones are dislocated.
My heart is like wax;
it melts away within my inner parts.
15 My strength has dried up like a piece of pottery;
my tongue sticks to the roof of my mouth.
You have laid me in the dust of death.
16 For dogs have surrounded me;
a company of evildoers has encircled me;
they have pierced my hands and my feet.
17 I can count all my bones.
They look and stare at me.
18 They divide my garments among themselves,
they cast lots for my clothes.
19 Do not be far away, Yahweh;
please hurry to help me, my strength!
20 Rescue my soul from the sword,
my only life from the claws of wild dogs.
21 Save me from the lion's mouth;
rescue me from the horns of the wild oxen.
22 I will declare your name to my brothers;
in the midst of the assembly I will praise you.
23 You who fear Yahweh, praise him!
All you descendants of Jacob, honor him!
Stand in awe of him, all you descendants of Israel!
24 For he has not despised or abhorred
the suffering of the afflicted one;
Yahweh has not hidden his face from him;
when the afflicted one cried to him, he heard.
25 My praise will be because of you in the great assembly;
I will fulfill my vows before those who fear him.
26 The oppressed will eat and be satisfied;
those who seek Yahweh will praise him.
May your hearts live forever.
27 All the peoples of the earth will remember and turn to Yahweh;
all the families of the nations will bow down before you.
28 For the kingdom is Yahweh's;
he is the ruler over the nations.
29 All the prosperous people of the earth will feast and will worship;
all those who are descending into the dust will bow before him,
those who cannot preserve their own souls alive.
30 A generation to come will serve him;
they will tell the next generation of the Lord.
31 They will come and tell of his righteousness;
they will tell to a people not yet born what he has done!
1 Allahna, Allahna, me yasa ka yashe ni? Me yasa ka yi nisa daga ƙubutar da ni kuma kayi nisa daga muryata ta azaba? 2 Allahna, na yi kuka da tsakar rana, amma baka amsa mani ba, da dare kuma ban yi shuru ba! 3 Amma kai mai tsarki ne; kana zaman sarki tare da yabon Isra'ila. 4 Iyayenmu sun dogara gare ka; sun dogara gare ka, ka kuma ƙubutar da su. Sun yi kira gare ka an kuma ƙuɓutar da su. 5 Sun dogara gare ka basu kuma kunyata ba. 6 Amma ni tsutsa ne ba mutum ba, abin kunya ga "yan adam da kuma abin raini ga mutane. 7 Dukkan waɗanda suka ganni suka cakune ni; suka yi mani haibaici; suka kaɗa mani kai. 8 Suka ce, "Ya dogara ga Yahweh; bari Yahweh ya kuɓutar da shi. Bari ya kuɓutar da shi, gama yana fahariya da shi." 9 Gama ka fito dani daga mahaifa; ka sa in dogara gare ka a sa'ad da nake shan nono wurin mahaifiyata. 10 Tun daga mahaifa aka jefo ni gare ka; kai Allahna ne tun daga mahaifar mahaifiyata! 11 Kada ka yi nisa dani, gama damuwa na kusa; babu wani mai taimako. 12 Bajimai masu yawa sun kewaye ni; Bajimai masu ƙarfi na Bashan suna zagaye dani. 13 Sun buɗe bakinsu da girma gãba dani kamar zaki mai ruri yana yagar abin da ya kama. 14 An kwararo ni kamar ruwa, kuma dukkan ƙasusuwana sun goce. Zuciyata kamar kitse; ta narke daga cikin cikina. 15 Ƙarfina ya bushe kaf kamar fasasshiyar tukunya; harshena ya manne sama a bakina. Ka kwantar da ni a cikin ƙurar mutuwa. 16 Gama karnuka suka zagaye ni; taron masu aikata mugunta suka kewaye ni; suka huda hannuwana da ƙafafuna. 17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana. Suka duba suka kuma zura mani ido. 18 Suka rarraba tufafina a tsakaninsu, suka jefa ƙuri'a a bisa kayana. 19 Kada ka yi nisa, Yahweh; ina roƙon ka kayi sauri domin ka taimake ni, ƙarfina! 20 Ka kuɓutar da raina daga takobi, raina ɗaya daga hannuwan karnukan daji. 21 Ka cece ni daga bakin zaki; ka kuɓutar dani daga ƙahonni na shanun daji. 22 Zan furta sunanka ga 'yan'uwana; a tsakiyar taruwar jama'a zan yabe ka. 23 Ku da kuke tsoron Yahweh, yabe shi! Dukkan ku zuriyar Yakubu, girmama shi! Ku tsaya cik cikin tsoronsa, dukkan ku zuriyar Isra'ila! 24 Gama baya rena ko yayi banza da wahalar ƙuntattu ba; Yahweh baya ɓoye fuskarsa daga gare shi ba; a lokacin da ƙuntacce yayi kira gare shi, ya ji. 25 Yabona zai zama sabili da kai a cikin babban taron jama'a; Zan cika wa'adina a gaban waɗanda ke tsoron sa. 26 Tsanantattu za su ci su ƙoshi; Waɗanda suka nemi Yahweh zasu yabe shi. Bari zukatanku su rayu har abada. 27 Dukkan mazamnan duniya zasu tuna su kuma juyo ga Yahweh; dukkan iyalan al'ummai zasu durƙusa a gabanka. 28 Gama mulki na Yahweh ne; shi yake mulki bisa al'ummai. 29 Dukkan mawadatan mutanen duniya za su yi buki su kuma yi sujada; dukkan su masu gangarawa zuwa turɓaya zasu durƙusa a gabansa, su waɗanda baza su iya adana rayyukansu ba. 30 Tsara mai zuwa zata yi masa hidima; zasu gaya wa tsara ta gaba game da Ubangiji. 31 Zasu zo su kuma yi magana game da adalcinsa; zasu faɗi abin da yayi ga mutanen da ba a haife su ba.
1 Yahweh is my shepherd; I will lack nothing.
2 He makes me to lie down in green pastures;
he leads me beside tranquil water.
3 He brings back my life;
he guides me along paths that are right
for his name's sake.
4 Even though I walk through the darkest valley,
I will fear no harm, for you are with me;
your rod and your staff comfort me.
5 You prepare a table before me in the presence of my enemies;
you have anointed my head with oil;
my cup runs over.
6 Surely goodness and covenant faithfulness will pursue me
all the days of my life;
and I will live in the house of Yahweh
for the length of my days!
1 Yahweh makiyayina ne; ba zan rasa komai ba. 2 Yana sa ni in kwanta a cikin korayen makiyayu; yana bi da ni kurkusa da kwantaccen ruwa. 3 Ya maido da raina; yana bishe ni ta tafarku madaidaita domin sunansa. 4 Ko da ina tafiya ta cikin kwari na inuwa mafi duhu, ba zan ji tsoron cutarwa ba tun da kana tare da ni; sandarka da kerenka na ta'azantar da ni. 5 Ka shirya teburi a gabana a fuskar maƙiyana; ka shafe kaina da mai; ƙoƙona ya cika har yana zuba. 6 Tabbas nagarta da amintaccen alƙawari zasu bi ni dukkan kwanakin raina; zan kuma zauna a cikin gidan Yahweh na lokaci mai tsawo sosai!
1 The earth is Yahweh's, and its fullness,
the world, and all who live in it.
2 For he has founded it upon the seas
and established it on the rivers.
3 Who will ascend the mountain of Yahweh?
Who will stand in his holy place?
4 He who has clean hands and a pure heart;
who has not lifted up a falsehood,
and has not sworn an oath in order to deceive.
5 He will receive a blessing from Yahweh
and righteousness from the God of his salvation.
6 Such is the generation of those who seek him,
those who seek the face of the God of Jacob. Selah
7 Lift up your heads, you gates;
be lifted up, everlasting doors,
so that the King of glory may come in!
8 Who is this King of glory?
Yahweh, strong and mighty;
Yahweh, mighty in battle.
9 Lift up your heads, you gates;
be lifted up, everlasting doors,
so that the King of glory may come in!
10 Who is this King of glory?
Yahweh of hosts,
he is the King of glory. Selah
1 Ƙasa ta Yahweh ce, da dukkan cikarta, duniyar, da dukkan mazauna cikinta. 2 Gama ya gina ta a bisa tekuna ya kuma ƙafa ta a bisa koguna. 3 Wane ne zai haura tudun Yahweh? Wane ne zai tsaya a cikin wurinsa mai tsarki? 4 Shi wanda ke da hannuwa masu tsarki da kuma zuciya mai tsabta; wanda baya faɗar ƙarya, ba ya kuma yin rantsuwa domin yayi yaudara. 5 Zai karɓi albarka daga wurin Yahweh da kuma adalci daga Allah na cetonsa. 6 Haka ya ke ga tsarar masu neman sa, masu neman fuskar Allah na Yakubu. Selah 7 Tãda kanku, ku ƙyamare; ku tashi, madawwaman ƙofofi, domin Sarkin daraja ya shigo ciki! 8 Wane ne wannan Sarkin daraja? Yahweh, mai ƙarfi da girma; Yahweh, mai girma cikin yaƙi. 9 Tãda kanku, ku ƙyamare; ku tashi, madawaman ƙofofi, domin Sarki na daraja ya shigo ciki! 10 Wane ne wannan Sarkin daraja? Yahweh mai runduna, shi ne Sarkin daraja. Selah
1 To you, Yahweh,
I lift up my life!
2 My God, I trust in you.
Do not let me be humiliated;
do not let my enemies rejoice triumphantly over me.
3 May no one who hopes in you be disgraced;
may those who act treacherously without cause be ashamed!
4 Make known to me your ways, Yahweh;
teach me your paths.
5 Guide me into your truth and teach me,
for you are the God of my salvation;
I hope in you all day long.
6 Call to mind, Yahweh, your acts of compassion and of covenant faithfulness;
for they have always existed.
7 Do not think about the sins of my youth
or my rebelliousness;
Call me to mind with covenant faithfulness
because of your goodness, Yahweh!
8 Yahweh is good and upright;
therefore he teaches sinners the way.
9 He guides the humble in what is right
and he teaches them his way.
10 All the paths of Yahweh are steadfast love and faithfulness
to those who keep his covenant and his solemn commands.
11 For your name's sake, Yahweh,
pardon my iniquity, for it is great.
12 Who is the man who fears Yahweh?
The Lord will instruct him in the way that he should choose.
13 His life will go along in goodness;
and his descendants will inherit the land.
14 The friendship of Yahweh is for those who honor him,
and he makes his covenant known to them.
15 My eyes are always on Yahweh,
for he will free my feet from the net.
16 Turn toward me and have mercy on me;
for I am alone and afflicted.
17 The troubles of my heart are enlarged;
draw me out from my distress!
18 See my affliction and my toils;
forgive all my sins.
19 See my enemies, for they are many;
they hate me with violent hatred.
20 Protect my life and rescue me;
do not let me be humiliated,
for I take refuge in you!
21 May integrity and uprightness preserve me,
for I hope in you.
22 Rescue Israel, God,
from all of his troubles!
1 A gare ka, Yahweh, na miƙa raina! 2 Allahna, Na dogara gare ka. Kar ka bari a wulaƙanta ni; kar ka bari maƙiyana suyi farincikin nasara a kaina. 3 Duk wanda yasa begensa a kan kada shi kunyata bari waɗanda suke aikata makirci babu dalili su ji kunya! 4 Ka bayyana mani hanyarka, Yahweh; koya mani tafarkinka. 5 Bishe ni cikin gaskiyarka ka kuma koyar dani, gama kai ne Allah na cetona; na sa begena bisan ka a koda yaushe. 6 Ka tuna, Yahweh, ayyukanka na tausayi da kuma amintaccen alƙawari; gama sun kasance tun tuni. 7 Kada kayi tunanin zunubaina na ƙuruciyata ko tayarwata; ka tuna da ni game da amintaccen alƙawarinka sabili da alherinka, Yahweh! 8 Yahweh yana da nagarta kuma yana da alheri saboda haka yana koyawa masu zunubi tafarki. 9 Yana bi da kamili ga abin da ke dai-dai kuma yana koya masu hanyarsa. 10 Dukkan tafarkun Yahweh na dawwamammiyar ƙauna ne da kuma aminci ga waɗanda ke kiyaye alƙawarinsa da kuma umarnansa tabbatattu. 11 Sabili da sunanka, Yahweh, ka gafarta zunubina, gama yana da girma sosai. 12 Wane ne mutumin dake tsoron Yahweh? Ubangiji zaya umarce shi a hanyar da zaya zaɓa. 13 Rayuwarsa zata bi ta hanya mai kyau; kuma zuriyarsa zasu gaji ƙasar. 14 Abokantakar Yahweh na ga waɗanda ke girmama shi, kuma yana sanar da alƙawarinsa gare su. 15 Idanuna suna bisa Yahweh koda yaushe, gama zaya ƙuɓutar da sawayena daga tarko. 16 Ka juyo gare ni kayi mani jinƙai; gama ni kaɗai ne kuma cikin ƙunci. 17 Damuwoyin zuciyata sun yawaita; ka tsamo ni daga nawayata! 18 Ka dubi wahalata da kuma matsalolina; ka gafarta zunubaina. 19 Ka dubi maƙiyana, gama suna da yawa; suna ƙina da ƙiyayya mai zafi. 20 Ka kare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari a wulaƙanta ni, gama ina samun mafaka a wurinka! 21 Bari nagarta da aminci su kiyaye ni, gama begena a cikinka ya ke. 22 Ka kuɓutar da Isra'ila, Allah, daga dukkan wahalolinsa!
1 Judge me, Yahweh,
for I have walked with integrity;
I have trusted in Yahweh without wavering.
2 Examine me, Yahweh, and test me;
test the purity of my inner parts and my heart!
3 For your covenant faithfulness is before my eyes,
and I walk about in your faithfulness.
4 I do not associate with deceitful people,
nor do I mingle with dishonest people.
5 I hate the assembly of evildoers,
and I do not live with the wicked.
6 I wash my hands in innocence,
and I go around your altar, Yahweh,
7 to sing a loud song of praise
and report all your wonderful deeds.
8 Yahweh, I love the house where you live,
the place where your glory lives!
9 Do not sweep me away with sinners,
or my life with men of bloodshed,
10 in whose hands there is a plot,
and whose right hand is full of bribes.
11 But as for me, I will walk in integrity;
redeem me and have mercy on me.
12 My foot stands on level ground;
in the assemblies will I bless Yahweh!
1 Yi mani shari'a, Yahweh, gama nayi tafiya da aminci; na dogara ga Yahweh babu ja da baya. 2 Ka gwada ni, Yahweh, ka kuma jaraba ni; jaraba tsabtar cikin raina da zuciyata! 3 Gama amintaccen alƙawarinka na gaban idanuna, kuma ina tafiya cikin amincinka. 4 Ban yi hurɗa da mutane marasa gaskiya ba, ko in yi cuɗanya da mutane macuta ba. 5 Na ƙi jinin taruwar masu aikata mugunta, ban kuma zauna da mugaye ba. 6 Na wanke hannuna cikin rashin laifi, ina kuma zagaya bagadinka, Yahweh, 7 domin in raira waƙar yabo da ƙarfi in kuma shaida dukkan ayyukanka masu ban girma. 8 Yahweh, ina ƙaunar gidan da kake zama, inda ɗaukakarka take! 9 Kada ka kawar dani tare da masu zunubi, ko raina tare da mutane masu marmarin shan jini, 10 waɗanda a cikin hannuwansu akwai mugun shiri, kuma hanunsa na dama ke cike da rashawa. 11 Amma ni, zan yi tafiya cikin aminci; ka fanshe ni ka kuma yi mani jinƙai. 12 Sawayena suna tsaye a shimfiɗarɗiyar ƙasa; a cikin taruwa zan albarkaci Yahweh!
1 Yahweh is my light and my salvation;
whom should I fear?
Yahweh is my life's refuge;
whom should I dread?
2 When evildoers approached me to devour my flesh,
my adversaries and my enemies stumbled and fell.
3 Though an army encamps against me,
my heart will not fear;
though war rises up against me,
even then I will remain confident.
4 One thing have I asked of Yahweh,
and I will seek that:
that I may live in the house of Yahweh
all the days of my life,
to see the beauty of Yahweh
and to meditate in his temple.
5 For in the day of trouble
he will hide me in his shelter;
in the cover of his tent he will conceal me.
He will lift me high on a rock!
6 Then my head will be lifted up above my enemies all around me,
and I will offer sacrifices of joy in his tent!
I will sing and make songs to Yahweh!
7 Hear, Yahweh, my voice when I cry out!
Have mercy on me, and answer me!
8 My heart says about you,
"Seek his face!" I seek your face, Yahweh!
9 Do not hide your face from me;
do not turn your servant away in anger!
You have been my helper;
do not abandon me or reject me,
God of my salvation!
10 Even if my father and my mother abandon me,
Yahweh will take me in.
11 Teach me your way, Yahweh!
Lead me on a level path
because of my enemies.
12 Do not give me up to the desires of my enemies,
for false witnesses have risen up against me,
and they breathe out violence!
13 What would have happened to me
if I had not believed that I would see the goodness of Yahweh
in the land of the living?
14 Wait for Yahweh;
be strong, and let your heart be courageous!
Wait for Yahweh!
1 Yahweh ne haske na da cetona; wane ne zan ji tsoro? Yahweh ne mafakar raina; wane ne zai razana ni? 2 Lokacin da masu aikata mugunta suka taso mani domin su cinye namana, magabtana da maƙiyana suka yi tuntuɓe suka kuma faɗi. 3 Koda runduna zasu zagaye ni da gãba, zuciyata baza ta ji tsoro ba; koda yaƙi zai taso gãba dani, duk da haka zan kasance da ƙarfin hali. 4 Abu guda ɗaya nayi roƙo ga Yahweh, zan kuma biɗi wannan; shi ne in zauna a cikin gidan Yahweh dukkan kwanakin raina, in dubi kyawun Yahweh in kuma yi bimbini a cikin haikalinsa. 5 Gama a ranar wahala zaya ɓoye ni a cikin fukafukansa; a ƙarƙashin inuwar rumfarsa zaya suturce ni. Zaya ɗaukaka ni a bisa dutse mai tsawo! 6 Sa'an nan za a ɗaukaka kaina fiye da maƙiyana dake kewaye dani, zan kuma miƙa hadayu na farinciki a cikin rumfarsa! Zan raira waƙa in kuma yi waƙoƙi ga Yahweh! 7 Yahweh ka ji, muryata a lokacin da nayi kuka! Kayi mani jinƙai, ka kuma amsa mani! 8 Zuciyata na ce da kai, "Nemi fuskarsa!" Na nemi fuskarka, Yahweh! 9 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni; kada ka juyar da bawanka daga gare ka cikin fushi! Tun dama kaine mai taimakona; kada ka yashe ni ko kayi banza dani, Allah na cetona! 10 Koda mahaifina ko mahaifiyata sun yashe ni, Yahweh zaya karɓeni. 11 Ka koya mani tafarkinka, Yahweh! Ka bishe ni a daidaitacciyar hanya saboda maƙiyana. 12 Kada ka bayar da ni ga nufin maƙiyana, gama shaidun ƙarya sun tashi gãba dani, suna kuma huro da ta'addanci! 13 Da mene ne zai faru dani da ba domin na yarda cewa zan ga alherin Yahweh a cikin ƙasar masu rai ba? 14 Ka jira ga Yahweh; yi ƙarfi, bari zuciyarka ta ƙarfafa! Saurari Yahweh!
1 To you, Yahweh, I cry out;
my rock, do not ignore me.
If you do not respond to me,
I will join those who go down to the pit.
2 Hear the sound of my pleading
when I call for help from you,
when I lift up my hands
toward your most holy place!
3 Do not drag me away with the wicked,
those who behave wickedly,
who speak peace with their neighbors
but have evil in their hearts.
4 Give them what their deeds deserve
and repay them what their wickedness demands;
repay them for the work of their hands
and render to them their due.
5 Because they do not understand the deeds of Yahweh
or the work of his hands,
he will break them down
and never rebuild them.
6 Blessed be Yahweh
because he has heard the sound of my pleading!
7 Yahweh is my strength and my shield;
my heart trusts in him, and I am helped.
Therefore my heart greatly rejoices,
and I will praise him with singing.
8 Yahweh is the strength of his people,
and he is the saving refuge of his anointed one.
9 Save your people and bless your inheritance.
Be their shepherd and carry them forever.
1 A gare ka, Yahweh, nayi kuka; dutsena, kada kayi banza da ni. Idan baka amsa mani ba, zan harɗe da waɗanda ke gangarawa zuwa kabari. 2 Kaji ƙarar roƙona a lokacin da nayi kira domin taimako daga gare ka, a lokacin da na tãda hannuwa na zuwa wurinka mai tsarki! 3 Kada ka kawar dani tare da masu aikata mugunta, su masu aikata laifuffuka, su dake faɗin alheri da maƙwabtansu da baki amma zuciyarsu cike take da mugunta. 4 Ka basu dai-dai abin da ayyukansu ya dace dasu da kuma abin da muguntarsu ta wajaba, ka biya su bisa ga aikin hannuwansu ka kuma mayar masu bisa ga ladarsu. 5 Domin basu gane da ayyukan Yahweh ba ko ayyukan hannuwansa, zaya buga su ƙasa baza a ƙara gina su ba. 6 Albarka ga Yahweh domin ya ji muryar kukana! 7 Yahweh ne ƙarfina da garkuwata; zuciyata ta dogara gare shi, na kuma sami taimako. Saboda haka zuciyata tayi farinciki ƙwarai, zan kuma yabe shi da raira waƙoƙi. 8 Yahweh ne karfin mutanensa, kuma shi ne maɓoyar ceto na shafaffensa. 9 Ka ceci mutanenka ka kuma albarkaci gãdonka. Ka zama makiyayinsu ka kuma ɗauke su har abada.
1 Ascribe to Yahweh, you sons of God,
ascribe to Yahweh glory and strength!
2 Ascribe to Yahweh the glory his name deserves.
Bow down to Yahweh in the splendor of holiness!
3 The voice of Yahweh is heard over the waters;
the God of glory thunders,
Yahweh thunders over many waters.
4 The voice of Yahweh is powerful;
the voice of Yahweh is majestic.
5 The voice of Yahweh breaks the cedars;
Yahweh breaks in pieces the cedars of Lebanon.
6 He makes Lebanon skip like a calf
and Sirion like a young ox.
7 The voice of Yahweh sends out flames of fire.
8 The voice of Yahweh shakes the wilderness;
Yahweh shakes the wilderness of Kadesh.
9 The voice of Yahweh causes the oaks to twist
and strips the forests bare.
Everyone in his temple says, "Glory!"
10 Yahweh sits as king over the flood;
Yahweh sits as king forever.
11 Yahweh gives strength to his people;
Yahweh blesses his people with peace.
1 Bada yabo ga Yahweh, ku 'ya'yan Allah! Bada yabo ga Yahweh domin ɗaukakarsa da ƙarfinsa. 2 Ba Yahweh ɗaukakar da ta cancanci sunansa. Durƙusa ƙasa ga Yahweh cikin jamalin tsarkinsa. 3 An ji muryar Yahweh har bisa ruwaye; Allah maɗaukaki ya yi tsawa, Yahweh na tsawa bisa ruwaye masu yawa. 4 Muryar Yahweh na da cikakken iko; Muryar Yahweh mai daraja ne. 5 Muryar Yahweh na fasa itatuwan sida; Yahweh na fasa gutsu-gutsu itatuwan sida na Lebanon. 6 Yana sa Lebanon tayi tsalle kamar ɗan maraki da kuma Dutsen Hamon kamar ɗan shanu. 7 Muryar Yahweh na aikar da harshen wuta. 8 Muryar Yahweh na girgiza hamada; Yahweh na girgiza hamadar Kadesh. 9 Muryar Yahweh nasa rimaye su tanƙware tana kuma kware daji a fili. Kowanne a cikin haikali na cewa, "Daukaka!" 10 Yahweh na zaman sarki a bisa ruwa mai ambaliya; Yahweh na zaman sarki har abada. 11 Yahweh yana bada karfi ga mutanensa; Yahweh yana albarkatar mutanensa da salama.
1 I will exalt you, Yahweh,
for you have raised me up
and have not allowed my enemies to rejoice over me.
2 Yahweh my God, I cried to you for help,
and you healed me.
3 Yahweh, you have brought up my soul from Sheol;
you have kept me alive from going down to the pit.
4 Sing praises to Yahweh, you his faithful ones!
Give thanks when you remember his holiness.
5 For his anger is only for a moment;
but his favor is for a lifetime.
Weeping comes for a night,
but joy comes in the morning.
6 In confidence I said, "I will never be shaken."
7 Yahweh, by your favor
you established me as a strong mountain;
but when you hid your face,
I was troubled.
8 I cried to you, Yahweh,
and sought favor from my Lord!
9 What advantage is there in my blood,
if I go down to the grave?
Will the dust praise you?
Will it declare your trustworthiness?
10 Hear, Yahweh, and have mercy on me!
Yahweh, be my helper.
11 You have turned my mourning into dancing;
you have removed my sackcloth and clothed me with gladness.
12 So now my glory will sing praise to you and not be silent;
Yahweh my God, I will give thanks to you forever!
1 Zan girmama ka, Yahweh, gama ka tã dani sama kuma baka bari maƙiyana sun yi farinciki bisa na ba. 2 Yahweh Allahna, nayi kuka gare ka domin taimako, ka kuma warkar dani. 3 Yahweh, ka tsamo raina daga Lahira; ka adana ni da rai kada in gangara ƙasa zuwa kabari. 4 Raira yabbai ga Yahweh, ku amintattunsa! Ku bada godiya a lokacin da kuka tuna da tsarkinsa. 5 Gama fushin sa na lokaci kaɗan ne; amma tagomashinsa na har abada ne. Kuka na zuwa da dare ne, amma farinciki na zuwa da safe. 6 Da ƙarfin hali nace. "Ba zan jijjigu ba." 7 Yahweh, da tagomashinka ka kafa ni kamar ƙaƙƙarfan tsauni; amma daka ɓoye fuskarka, na shiga damuwa. 8 Nayi kira gare ka, na kuma nemi tagomashi daga wurin Ubangijina! 9 Wacce riba ce ke cikin mutuwata, idan na gangara cikin kabari? Ko turɓaya zata yabe ka? Zata furta tabbatattun amincinka? 10 Ka saurara, Yahweh, kayi mani jinƙai! Yahweh, ka zama mai taimakona. 11 Ka juyar da makokina zuwa rawa; ka cire mani tsumma ka kuma sanya mani rigar farinciki. 12 Yanzu ɗaukakata zata yi maka waƙar yabo kuma ba zata yi shuru ba; Yahweh Allahna, zan yi maka godiya har abada!
1 In you, Yahweh, I take refuge;
never let me be humiliated.
Rescue me in your righteousness.
2 Listen to me; rescue me quickly;
be my rock of refuge,
a stronghold to save me.
3 For you are my rock and my fortress;
therefore for your name's sake, lead and guide me.
4 Pluck me out of the net that they have hidden for me,
for you are my refuge.
5 Into your hands I entrust my spirit;
you will redeem me, Yahweh, God of trustworthiness.
6 I hate those who serve worthless idols,
but I trust in Yahweh.
7 I will be glad and rejoice in your covenant faithfulness,
for you saw my affliction;
you knew the distress of my soul.
8 You have not given me into the hand of my enemy.
You have set my feet in a wide open place.
9 Have mercy upon me, Yahweh, for I am in distress;
my eyes grow weary with grief
with my soul and my body.
10 For my life is weary with sorrow
and my years with groaning.
My strength fails because of my iniquity,
and my bones are wasting away.
11 Because of all my enemies, I have become contemptible;
my neighbors are appalled at my situation,
and those who know me are horrified.
Those who see me in the street run from me.
12 I am forgotten as a dead man whom no one thinks about.
I am like a broken pot.
13 For I have heard the whispering of many,
terrifying news from every side
as they plot together against me.
They plot to take away my life.
14 But I trust in you, Yahweh;
I say, "You are my God."
15 My times are in your hand.
Rescue me from the hands of my enemies
and from those who pursue me.
16 Make your face shine on your servant;
save me in your covenant faithfulness.
17 Do not let me be humiliated, Yahweh;
for I call out to you!
May the wicked be humiliated!
May they be silent in Sheol.
18 May lying lips be silenced
that speak against the righteous defiantly
with arrogance and contempt.
19 How great is your goodness
that you have stored up for those who revere you,
that you perform for those who take refuge in you
before all the children of mankind!
20 In the shelter of your presence, you hide them from the plots of men.
You hide them in a shelter from the strife of tongues.
21 Blessed be Yahweh,
for he showed me his marvelous covenant faithfulness when I was in a besieged city.
22 Though I said in my alarm,
"I am cut off from your eyes,"
yet you heard my plea for help
when I cried to you.
23 Love Yahweh, all you faithful ones.
Yahweh protects the faithful,
but he pays back the arrogant in full.
24 Be strong and let your heart take courage,
all you who trust in Yahweh for help.
1 A cikin ka, Yahweh, na sami mafaka; kada ka barni in wulaƙanta. Ka kuɓutar dani cikin adalcinka. 2 Ka saurare ni; Ka kuɓutar dani da sauri; ka zama dutsen mafakata, ƙaƙƙarfar maɓoya domin cetona. 3 Gama kai ne dutsena da kuma mafakata; Saboda haka sabili da sunanka, ka shugabance ni ka kuma bishe ni. 4 Ka ƙwato ni daga cikin tãrun da suka ɓoye domi na, gama kai ne maɓuyata. 5 A cikin hannuwanka nake bada ruhuna; zaka fanshe ni, Yahweh, Allah madogarata. 6 Na ƙi jinin waɗandɑ suke bautawa gumakan banza, amma na dogara ga Yahweh. 7 Zan yi murna da kuma farinciki cikin amintaccen alƙawarinka, gama ka ga ƙuncina; ka san matsalar raina. 8 Baka miƙa ni a cikin hannuwan maƙiyana ba. Ka kafa ƙafafuwana a buɗaɗɗen wuri mai faɗi. 9 Kayi mani jinƙai, Yahweh, gama ina cikin ƙunci; idanuna sun yi nauyi da azaba tare da raina da jikina. 10 Gama raina yayi nauyi da makoki kuma shekaruna na cike da nishe-nishe. Ƙarfina ya gaza sabili da zunubina, ƙasusuwana suna lalacewa sarai. 11 Sabili da maƙiyana, mutane sun yi banza dani; maƙwabtana suka gaji da yanayina, kuma waɗanda suka san ni suka tsorata. Waɗanda suka gamu dani a hanya suka gudu daga gare ni. 12 An manta da ni kamar mataccen mutum wanda babu wanda ke tunaninsa. Ina kama da fasasshiyar tukunya. 13 Gama na ji raɗe-raɗe masu yawa, labarai masu ban tsoro daga kowanne sashe sa'ad da suke shiri gãba da ni. Sun yi shiri domin su ɗauke raina. 14 Amma na dogara gare ka, Yahweh; Na ce, "Kai ne Allahna." 15 Ƙaddarata na cikin hannuwanka. Ka kuɓutar dani daga hannuwan magabtana daga kuma waɗanda suke fafarata. 16 Bari fuskarka ta haskaka bisa bawanka; ka cece ni cikin amintaccen alƙawarinka. 17 Kada ka bar ni in wulaƙantu, Yahweh; gama na yi kira gare ka! Bari mugu ya wulaƙanta! Bari suyi shuru a cikin Lahira. 18 Bari harsuna masu ƙarya suyi shuru su dake magana gãba da mai adalci da renin girma da kuma tozartarwa. 19 girman alherinka da ka shirya wa masu girmama ka, abin da kake aiwatar wa domin waɗanda suka yi mafaka a cikinka a gaban dukkan 'ya'yan talikai! 20 A cikin mahallin bayyanuwarka, ka ɓoye su daga makircin mutane. Ka ɓoye su a cikin mahalli daga ta'addancin harsuna. 21 Mai albarka ne Yahweh, gama ya nuna mani amintaccen alƙawarinsa mai ban mamaki a lokacin da nake a cikin birnin kwanto. 22 Ko da ya ke na faɗa cikin gaggawata, "An datse ni daga fuskarka," duk da haka ka ji roƙona domin taimako lokacin da nayi kuka gare ka. 23 Oh, ƙaunaci Yahweh, dukkan ku amintattun mabiya. Yahweh yana tsare amintattu, amma yana sãka wa masu girman kai. 24 Ku ƙarfafa kuyi ƙarfi, dukkan ku dake dogara cikin Yahweh domin taimako.
1 Blessed is the person
whose transgression is forgiven,
whose sin is covered.
2 Blessed is the man to whom Yahweh reckons no guilt
and in whose spirit there is no deceit.
3 When I remained silent,
my bones were wasting away
while I groaned all day long.
4 For day and night your hand was heavy upon me.
My strength withered as in summer drought. Selah
5 Then I acknowledged my sin to you,
and I no longer hid my iniquity.
I said, "I will confess my transgressions to Yahweh,"
and you forgave the guilt of my sin. Selah
6 For this reason every one of your faithful followers should pray to you
at a time of great distress.
When the surging waters overflow,
the waters will not reach them.
7 You are my hiding place;
you will guard me from trouble.
You will surround me with the songs of victory. Selah
8 I will instruct you and teach you in the way which you should go.
I will counsel you with my eye upon you.
9 Do not be like a horse or like a mule,
which have no understanding;
it is only with bridle and bit to control them
that they will go where you want them to.
10 The wicked have many sorrows,
but Yahweh's covenant faithfulness will surround the one who trusts in him.
11 Be glad in Yahweh, and rejoice, you righteous;
shout for joy, all you who are upright in heart.
1 Mai albarka ne taliki wanda an gafarta masa kurakuransa, wanda aka rufe zunubinsa. 2 Mai albarka ne mutum wanda Yahweh ba ya lisafta laifi bisansa kuma wanda babu algus cikin ruhunsa. 3 Da na yi shuru, ƙasusuwana suna lalacewa sa'ad da nake nishe-nishe dukkan yini. 4 Gama rana da dare hannunka na da nauyi bisana. ƙarfina ya gaza kamar lokacin fãrin kaka. 5 Sa'an nan na furta zunubi na gare ka, ban kuma ƙara ɓoye laifi na ba. Na ce, "Zan furta kurakuraina ga Yahweh," ka kuma gafarta mani ladar zunubina. 6 Saboda wannan, dukkan waɗanda ke na allahntaka suna adu'a a gare ka a lokacin gwagwarmaya mai girma. Sa'an nan lokacin da ruwaye masu hauka suka taso, baza su cimma waɗannan mutane ba. 7 Kai ne maɓuyata; zaka tsare ni daga wahala. Zaka zagaye ni da waƙoƙin nasara. 8 Zan umarce ka in koya maka hanyar da zaka bi. Zan umarce ka da idanuna a bisanka. 9 Kada ka zama kamar doki ko kamar alfadari, wanda ba shi da fahimta; sai tare da linzami da ragama domin a bi da su inda ake so su tafi. 10 Mugu yana da baƙinciki mai yawa, amma amintaccen alƙawarin Yahweh zai zagaye wanda ya dogara gare shi. 11 Yi murna cikin Yahweh, da farinciki, ku adalai; yi sowa ta farinciki, dukkan ku masu tsabta cikin zuciya.
1 Rejoice in Yahweh, you righteous;
praise is appropriate for the upright.
2 Give thanks to Yahweh with the harp;
sing praises to him with the lute having ten strings.
3 Sing to him a new song;
play skillfully and shout for joy.
4 For Yahweh's word is upright,
and all his deeds are done in faithfulness.
5 He loves righteousness and justice.
The earth is full of Yahweh's covenant faithfulness.
6 By the word of Yahweh the heavens were made,
and all the stars were made by the breath of his mouth.
7 He gathers the waters of the sea together like a heap;
he puts the oceans in storehouses.
8 Let the whole earth fear Yahweh;
let all the inhabitants of the world stand in awe of him.
9 For he spoke, and it was done;
he commanded, and it stood in place.
10 Yahweh frustrates the alliances of nations;
he overrules the plans of the peoples.
11 The plans of Yahweh stand forever,
the plans of his heart for all generations.
12 Blessed is the nation whose God is Yahweh,
the people whom he has chosen as his own inheritance.
13 Yahweh looks from heaven;
he sees all the people.
14 From the place where he lives,
he looks down on all who live on the earth.
15 He who shapes the hearts of them all
observes all their deeds.
16 No king is saved by a vast army;
a warrior is not saved by his great strength.
17 A horse is a false hope for victory;
in spite of his great strength, he cannot rescue.
18 See, Yahweh's eye is on those who fear him,
on those who hope in his covenant faithfulness
19 to deliver their lives from death
and to keep them alive in times of famine.
20 We wait for Yahweh;
he is our help and our shield.
21 Our hearts rejoice in him,
for we trust in his holy name.
22 Let your covenant faithfulness, Yahweh, be with us
as we put our hope in you.
1 Yi farinciki cikin Yahweh, ku adalai; Yin yabo ya dace ga adalai. 2 Kuyi godiya ga Yahweh da molo; yi waƙoƙin yabo gare shi da molo mai tsarkiya goma. 3 Raira sabuwar waƙa gare shi; ku yi kiɗa da ƙwarewarku kuna raira waƙa tare da farinciki. 4 Gama maganar Yahweh mai adalci ce, kuma dukkan abin da ya aikata dai-dai ne. 5 Yana ƙaunar adalci da shari'a. Duniya na cike da amintaccen alƙawarinsa. 6 Da maganar Yahweh aka hallici sammai, kuma dukkan taurari sun kasance ne ta numfashin bakinsa. 7 Yana tara ruwayen teku wuri ɗaya kamar tudu; ya ajiye tekuna cikin ɗakunan ajiya. 8 Bari dukkan ƙasar taji tsoron Yahweh; Bari dukkan mazaunan duniya su tsaya cik a gabansa. 9 Gama ya yi magana, aka kuma aikata; ya umarta, ya kuma tabbata. 10 Yahweh yana lalatar da ƙawancen al'ummai; yana mulki akan shirye-shiryen mutane. 11 Shirin Yahweh ya tsaya har abada, shirye-shiryen zuciyarsa ga dukkan tsararraki. 12 Mai albarka ce al'ummar da Yahweh ne Allahnta, mutanen da ya zaɓa abin gãdonsa. 13 Yahweh yana gani daga sama; yana ganin dukkan mutane. 14 Daga wurin da ya ke zama, yana duban dukkan masu zama cikin ƙasar. 15 Shi wanda ya ke shirya zuciyarsu dukka yana la'akari da ayyukansu. 16 Babu sarkin da zai tsira sabili da yawan runduna; jarumi baya tsira ta dalilin ƙarfinsa. 17 Doki tsaro ne na banza domin nasara; duk da ƙarfinsa, ba zai iya ƙubutarwa ba. 18 Duba, idanun Yahweh na bisan waɗanda ke tsoronsa, a bisa waɗanda suka dangana bisa amintaccen alƙawarinsa 19 domin ya kuɓutar da rayukansu daga mutuwa ya kuma kiyaye su da rai a lokacin yunwa. 20 Muna jiran Yahweh; shi ne taimakonmu da kuma garkuwarmu. 21 Zuciyarmu tayi farinciki cikinsa, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki. 22 Bari amintaccen alƙawarinka, Yahweh, ya kasance da mu a lokacin da muka kafa begenmu cikinka.
1 I will praise Yahweh at all times,
his praise will always be in my mouth.
2 I will praise Yahweh!
May the oppressed hear and rejoice.
3 Praise Yahweh with me,
let us lift up his name together.
4 I sought Yahweh and he answered me,
and he gave me victory over all my fears.
5 Those who look to him are radiant,
and their faces are not ashamed.
6 This oppressed man cried and Yahweh heard him
and saved him from all his troubles.
7 The angel of Yahweh camps around those who fear him
and rescues them.
8 Taste and see that Yahweh is good.
Blessed is the man who takes refuge in him.
9 Fear Yahweh, you his holy people.
There is no lack for those who fear him.
10 The young lions sometimes lack food and suffer hunger,
but those who seek Yahweh will not lack anything good.
11 Come, sons, listen to me.
I will teach you the fear of Yahweh.
12 What man is there who delights in life
and loves many days,
that he may see good?
13 Then keep your tongue from evil
and keep your lips from speaking lies.
14 Turn away from evil and do good.
Seek peace and go after it.
15 The eyes of Yahweh are on the righteous
and his ears are directed toward their cry.
16 The face of Yahweh is against those who do evil,
to cut off the memory of them from the earth.
17 The righteous cry out and Yahweh hears
and he rescues them from all their troubles.
18 Yahweh is close to the brokenhearted,
and he saves those who are crushed in spirit.
19 Many are the troubles of the righteous,
but Yahweh delivers them out of them all.
20 He keeps all his bones,
not one of them will be broken.
21 Evil will kill the wicked.
Those who hate the righteous will be condemned.
22 Yahweh rescues the lives of his servants.
None of those who take refuge in him will be condemned.
1 Zan yabi Yahweh a dukkan lokaci, Yabonsa zai kasance a bakina koda yaushe. 2 Zan yabi Yahweh! Bari ƙuntattu su ji su kuma yi farinciki. 3 Ku yabi Yahweh tare da ni, bari mu ɗaukaka sunansa tare. 4 Na nemi Yahweh kuma ya amsa mani, ya kuma ba ni nasara bisa dukkan tsorona. 5 Waɗanda ke duban sa suna haskakawa, kuma fuskarsu ba ta ji kunya ba. 6 Wannan matsattsen mutum yayi kuka Yahweh kuma ya ji ya kuma cece shi daga dukkan matsalolinsa. 7 Mala'ikan Yahweh na zagaye waɗanda ke tsoronsa ya kuma ƙubutar da su. 8 Ku ɗanɗana ku kuma gani cewa Yahweh na da kyau. Mai albarka ne mutum wanda ke ɓuya cikinsa. 9 Ku ji tsoron Yahweh, ku mutanensa masu tsarki. Babu rashi ga waɗanda ke tsoronsa. 10 'Ya'yan zakuna wasu lokuttan suna rasa abinci su kuma ji yunwa, amma waɗanda suka nemi Yahweh baza su rasa kowanne abu mai kyau ba. 11 Ku zo, 'ya'ya maza, ku saurare ni. Zan koya maku jin tsoron Yahweh. 12 Wanne mutum ne mai biɗar rai ya ke kuma ƙaunar ranaku masu yawa, domin ya ga alheri? 13 To, sai ka tsare harshenka daga faɗin mugunta leɓunanka kuma daga faɗin ƙarya. 14 Ka juyo daga barin mugunta ka kuma aikata nagarta. Nemi salama ka kuma bi ta. 15 Idanun Yahweh suna bisa masu adalci kuma kunnuwansa suna karkatawa zuwa ga kukansu. 16 Fuskar Yahweh na gãba da waɗanda ke aikata mugunta, domin a datse tunawa da su daga duniya. 17 Masu adalci sun yi kira Yahweh kuma yana kuɓutar da su daga dukkan matsalolinsu. 18 Yahweh yana kurkusa da masu karyayyar zuciya, kuma yana ceton waɗanda aka ƙuntatawa a cikin ruhu. 19 Da yawa suke matsalolin masu adalci, amma Yahweh yana ƙubutar da su daga dukkan su. 20 Ya kare dukkan ƙasusuwansa, babu ko ɗaya daga cikinsu da za a karya. 21 Mugunta zata kashe mai mugunta. Waɗanda suka ƙi masu adalci za a hallakar da su. 22 Yahweh yana ƙubutar da rayukan bayinsa. Babu ɗaya daga cikin waɗanda ke neman mafaka wurinsa da za a kayar.
1 Yahweh, work against those who work against me;
fight against those who fight against me.
2 Grab your small shield and large shield;
rise up and help me.
3 Use your spear and battle ax
against those who chase me;
say to my soul,
"I am your salvation."
4 May those who seek my life
be shamed and dishonored.
May those who plan to harm me
be turned back and ashamed.
5 May they be as chaff before the wind,
as the angel of Yahweh drives them away.
6 May their way be dark and slippery,
as the angel of Yahweh chases them.
7 Without cause they set their net for me;
without cause they dug a pit for my life.
8 Let destruction overtake them by surprise.
Let the net that they have set catch them.
Let them fall into it, to their destruction.
9 But I will be joyful in Yahweh
and rejoice in his salvation.
10 All my bones will say,
"Yahweh, who is like you,
who rescues the oppressed from those who are too strong for them
and the poor and needy from those who try to rob them?"
11 Unrighteous witnesses rise up;
they accuse me falsely.
12 They repay me evil for good.
I am sorrowful.
13 As for me, when they were sick, my clothing was sackcloth;
I fasted for them,
and my prayer returned to my bosom.
14 I went about in grief as for my brother;
I bent down in mourning as for my mother.
15 But when I stumbled, they rejoiced and gathered together;
they gathered together against me, and I was surprised by them.
They tore at me without stopping.
16 With no respect at all they mocked me;
they grind their teeth at me in rage.
17 Lord, how long will you look on?
Rescue my soul from their destructive attacks,
my only life from the lions.
18 Then I will thank you in the great assembly;
I will praise you among many people.
19 Do not let my deceitful enemies rejoice over me;
do not let them carry out their wicked schemes.
20 For they do not speak peace,
but they devise deceitful words
against those in our land who live in peace.
21 They open their mouths wide against me;
they said, "Aha, Aha, our eyes have seen it."
22 You have seen it, Yahweh, do not be silent;
Lord, do not be far from me.
23 Arouse yourself and awake to my defense;
My God and my Lord, defend my cause.
24 Defend me, Yahweh my God, because of your righteousness;
do not let them rejoice over me.
25 Do not let them say in their heart, "Aha, we have what we wanted."
Do not let them say, "We have devoured him."
26 May they be put to shame and may they be humiliated who rejoice at my distress.
May those who exalt themselves over me be clothed with shame and dishonor.
27 Let those who desire my vindication
shout for joy and be glad;
may they say continually, "Yahweh be praised,
he who delights in the welfare of his servant."
28 Then I will tell of your justice
and praise you all day long.
1 Yahweh, ka yi gãba da waɗanda ke aiki gãba da ni; ka yaƙi waɗanda ke yaƙi da ni. 2 Ka ɗauki garkuwarka ƙarama da babba; tashi ka taimake ni. 3 Yi amfani da mashi da gatarin yaƙin ka gãba da waɗanda ke runtuma ta; ka ce da raina, "Ni ne cetonka." 4 Bari su waɗanda ke neman raina su ji kunya su kuma faɗi. Bari waɗanda ke shirin cuta na a juyar da su a kuma hargitsa su. 5 Bari su zama kamar ƙaiƙayi a fuskar isaka, a sa'ad da mala'ikan Yahweh ke korar su. 6 Bari hanyar su ta duhunta tana kuma zamewa, a sa'ad da mala'ikan Yahweh ke runtumar su. 7 Babu dalili suka shirya mani tarkonsu; Babu dalili suka haƙa rami domin raina. 8 Bari halakarwa ta auko masu ba zato. Bari tarkon da suka ɗana ya kama su. Bari su faɗa ciki, ga hallakarsu. 9 Amma zan yi farinciki cikin Yahweh in kuma yi murna cikin cetonsa. 10 Dukkan ƙasusuwana za su ce, "Yahweh, wane ne kamar ka, wanda ke ƙuɓutar da ƙuntattu daga waɗanda suka fi ƙarfinsu da kuma matalauta da kuma mabuƙata daga waɗanda ke ƙoƙarin yi masu fashi?" 11 Shaidu marasa adalci sun tashi; sun yi mani zargin ƙarya. 12 Sun sãka mani nagarta da mugunta. Ina cike da ɓacin rai. 13 Amma a lokacin da suke ciwo, na sanya tsummokara; na yi azumi a madadinsu da kaina sunkuye ga ƙirjina. 14 Na yi tafiya cikin ƙunci domin ɗan'uwana; Na durƙusa cikin makoki domin mahaifiyata. 15 Amma da nayi tuntuɓe, suka yi murna suka taru wuri ɗaya; suka taru wuri ɗaya gãba da ni, kuma suka bani mamaki. Suka kawo mani farmaƙi babu fasawa. 16 Da rashin girmamawa samsam suka yi mani ba'a; suka tauna mani haƙoransu. 17 Ubangiji, har yaushe zaka duba? Ka ƙuɓutar da raina daga farmaƙinsu mai hallakarwa, raina daga zakuna. 18 Sa'an nan zan gode maka a babban taro mai girma; Zan yabe ka a cikin mutane masu yawa. 19 Kada ka bar maƙiyana masu ƙarya su yi murna a kaina; kada ka barsu su aiwatar da mugun shirinsu. 20 Gama basu maganar salama, amma suka shirya maganganun ƙarya gãba da waɗanda ke zaman salama cikin ƙasar. 21 Sun buɗe bakunansu da girma gãba da ni; suka ce, "Aha, Aha, idanunmu sun gan shi." 22 Ka gan shi, Yahweh, kada ka yi shuru; Ubangiji, kada kayi nisa dani. 23 Ka tãda kanka ka kuma farka domin ka kare ni; Allahna da Ubangijina, ka kare bukatata. 24 Ka kãre ni, Yahweh Allahna, sabili da adalcinka; kada ka bar su suyi murna a kaina. 25 Kada ka bari su faɗa a cikin zuciyarsu, Aha, mun sami abin da muke nema." Kada ka bar su su ce, "Mun haɗiye shi." 26 Ka basu kunya ka kuma ruɗar da waɗanda ke niyyar cutar da ni. Bari waɗanda ke cakuna ta a rufe su da kunya da ƙasƙanci. 27 Bari su dake marmarin kuɓutata suyi sowa ta murna su kuma ji daɗi; bari koyaushe su ce, "Bari Yahweh ya ɗaukaka, shi da ya ke jin daɗi cikin wadatar bawansa." 28 Sa'an nan zan faɗi game da shari'arka in kuma yabe ka dukkan yini.
1 An evil man speaks of his transgression from deep in his heart,
there is no fear of God in his eyes.
2 For he comforts himself,
thinking that his iniquity will not be discovered and be hated.
3 The words of his mouth are wickedness and deceit;
he does not want to be wise and do good.
4 While he lies in bed, he plans ways to sin;
he sets out on an evil way;
he does not reject evil.
5 Your covenant faithfulness, Yahweh, reaches to the heavens;
your faithfulness reaches to the clouds.
6 Your righteousness is like the mountains of God;
your judgments are like the great deep.
Yahweh, you preserve both mankind and the animals.
7 How precious is your covenant faithfulness, God!
Humanity takes refuge under the shadow of your wings.
8 They feast upon the abundance of your house;
you let them drink from the river of your delights.
9 For with you is the fountain of life;
in your light we will see light.
10 Extend your covenant faithfulness fully to those who know you,
your defense to the upright of heart.
11 Do not let the foot of the arrogant man come near to me.
Do not let the hand of the wicked drive me away.
12 Over there those who behave wickedly have fallen;
they have been pushed down and are not able to get up.
1 Mugun mutum yana zancen kurakuransa daga cikin zuciyarsa, babu tsoron Allah a idanunsa. 2 Gama yana yiwa kansa ta'aziya, da tunanin cewar zunubansa ba zasu tonu ba ko kuma a ƙi su. 3 Maganganunsa na zunubi ne da yaudara; ba ya son ya zama mai hikima ya kuma aikata nagarta. 4 A lokacin da ya ke kwance a gado, yana shirya yadda zai yi zunubi; ba ya ƙin mugunta. 5 Amintaccen alƙawarinka, Yahweh, na kaiwa har zuwa sammai; amincinka na kaiwa zuwa cikin giza-gizai. 6 Adalcinka na kama da duwatsun Allah; shari'unka na kama da manyan zurfafa. Yahweh, ka kare talikai da dabbobi. 7 Yaya darajar amintaccen alƙawarinka ya ke, Allah! Bil'adama na fakewa a ƙarƙashin inuwar fukafukanka. 8 Zasu ƙoshi daga yalwar abincin gidanka; zaka sa su sha daga cikin koginka mai manyan albarku. 9 Domin a gare ka akwai maɓulɓular rai; cikin haskenka zamu ga haske. 10 Ka kawo gare ni amintaccen alƙawarinka cikakke ga waɗanda suka san ka, kariyarka zuwa ga kamilai a zuci. 11 Ka da ka bar ƙafafun mai girman kai shi zo kusa dani. Ka da ka bar hannun mugaye su kore ni da nisa. 12 A can mugaye suka faɗi; aka buga su ƙasa basu kuma iya tashi ba.
1 Do not be irritated because of evildoers;
do not be envious of those who act unrighteously.
2 For they will soon dry up as the grass
and wither as the green plants.
3 Trust in Yahweh and do what is good;
settle in the land and graze in faithfulness.
4 Then delight yourself in Yahweh,
and he will give you the desires of your heart.
5 Give your ways to Yahweh;
trust in him, and he will act on your behalf.
6 He will display your justice like the daylight
and your innocence like the day at noon.
7 Be still before Yahweh
and wait patiently for him.
Do not be angry if someone succeeds in what he does,
or when he makes evil plots.
8 Do not be angry and frustrated.
Do not worry. This only makes trouble.
9 Evildoers will be cut off,
but those who wait for Yahweh will inherit the land.
10 In a little while the evil man will disappear;
you will look at his place, but he will be gone.
11 But the meek will inherit the land
and will delight in great prosperity.
12 The wicked man plots against the righteous
and he grinds his teeth in rage against him.
13 The Lord laughs at him,
for he sees that his day is coming.
14 The wicked have drawn out their swords
and have bent their bows
to cast down the oppressed and needy,
to kill those who are upright.
15 Their swords will pierce their own hearts,
and their bows will be broken.
16 Better is the little that the righteous has
than the abundance of many wicked people.
17 For the arms of the wicked people will be broken,
but Yahweh supports the righteous people.
18 Yahweh watches over the blameless day by day,
and their heritage will be forever.
19 They will not be ashamed when times are bad.
When famine comes, they will have enough to eat.
20 But evil men will perish.
Yahweh's enemies will be like the splendor of the pastures;
they will be consumed and disappear in the smoke.
21 The wicked person borrows but does not repay,
but the righteous person is generous and gives.
22 Those who are blessed by God will inherit the land;
those who are cursed by him will be cut off.
23 It is by Yahweh that a man's steps are established,
the man whose way is commendable in God's sight.
24 Though he stumbles, he will not fall down,
for Yahweh is holding him with his hand.
25 I was young and now am old;
I have never seen the righteous person abandoned
or his children begging for bread.
26 All the day long he is gracious and lends,
and his children become a blessing.
27 Turn away from evil and do what is right;
then you will be safe forever.
28 For Yahweh loves justice
and does not abandon his faithful ones.
They are preserved forever,
but the descendants of the wicked will be cut off.
29 The righteous will inherit the land
and live there forever.
30 The mouth of the righteous person speaks wisdom
and increases justice.
31 The law of his God is in his heart;
his feet will not slip.
32 The wicked person spies on the righteous person
and seeks to kill him.
33 Yahweh will not abandon him into the evil person's hand
or condemn him when he is judged.
34 Wait for Yahweh and keep his way,
and he will raise you up to possess the land.
You will see when the wicked are cut off.
35 I have seen the wicked and terrifying person
spread out like a green tree in its native soil.
36 But when I passed by again, he was not there.
I looked for him, but he could not be found.
37 Observe the man of integrity, and mark the upright;
there is a good future for a man of peace.
38 Rebels will be totally destroyed;
the future for the wicked man is cut off.
39 Salvation of the righteous comes from Yahweh;
he is their place of safety in the times of trouble.
40 Yahweh helps them and rescues them.
He rescues them from evil men and saves them
because they have taken refuge in him.
1 Kada ka damu da masu mugunta; kada ka ji ƙyashin waɗanda ke ayyukan rashin adalci. 2 Gama zasu bushe da wuri kamar ciyawa, su kuma yanƙwane kamar korayen tsire-tsire. 3 Ka dogara ga Yahweh kuma ka yi abin da ke nagari; ka zauna a ƙasar ka yi kiwo cikin aminci. 4 Sa'an nan ka yi murna da al'amuran Yahweh, kuma zai biya maka buƙatun zuciyarka. 5 Ka miƙa hanyoyinka ga Yahweh; ka dagara gare shi, kuma zai yi abu a madadinka. 6 Zai nuna aɗalcinka kamar hasken rana da rashin laifinka kamar rana tsaka. 7 Ka natsu a gaban Yahweh kuma kayi jira da haƙuri domin sa. Kada ka ji haushi idan wani ya yi nasara da abin da ya ke yi, ko sa'ad da ya ke ƙulla mugunta. 8 Kada ka ji haushi da takaici. Kada ka damu. Wannan na bada damuwa ne kawai. 9 Za a datse miyagu, amma waɗanda ke jiran Yahweh zasu gãji ƙasar. 10 A ɗan lokaci ƙaɗan mugun mutum zai ɓace; zaka dubi wurinsa, amma ba zai kasance ba. 11 Amma masu tawali'u zasu gãji ƙasar kuma zasu yi murna da gagarumar wadata. 12 Mugun mutum yana shirya maƙarƙashiya gãba da adali yana kuma cizon haƙora gãba da shi. 13 Ubangiji yana yi masa dariya, gama yana ganin zuwan ranarsa. 14 Mugaye sun zare takubbansu suka kuma tanƙware bakkunansu don su kãda waɗanda ake masu danniya da masu buƙata, su kashe waɗanda ke da nagarta. 15 Takkubansu zasu soke zukatansu, kuma bakkunansu zasu kakkarye. 16 Gara ƙanƙanen abin da mutumin kirki ya ke da shi da yawan abubuwan mugayen mutane. 17 Gama za a ƙarɓe ƙarfin mugayen mutane, amma Yahweh zai taimaki adalai 18 Yahweh yana lura da marasa abin zargi a kowacce rana, kuma gãdonsu zai kasance har abada. 19 Ba za su ji kunya a lokacin masifa ba. Sa'ad da Yunwa tazo, zasu samu isasshen abinci. 20 Amma mugaye zasu lalace. Maƙiyan Yahweh za su zama kamar darajar ciyawa; za a cinye su su ɓace kamar hayaƙi. 21 Mugu yakan ci bashi amma ba ya biya, amma adali yana bayarwa hannu sake. 22 Waɗanda Allah ya sawa albarka zasu gãji ƙasar; waɗanda ya la'anta zasu zama korarru. 23 Ta wurin Yahweh ne hanyoyin mutum ke kafuwa, mutumin da hanyarsa amintacciya ce a fuskar Allah. 24 Ko da ya ke yana tuntuɓe, ba zai faɗi ba, gama Yahweh na riƙe shi da hannunsa. 25 Dã ni yaro ne kuma yanzu na tsufa; ban taɓa ganin an yashe da adali ba ko kuma 'ya'yansa na roƙon abinci. 26 Dukkan yini yana yin alheri yana ba da rance, kuma 'ya'yansa sun zama albarka. 27 Ka bar mugunta kayi abin da ke dai-dai; zaka cetu har abada. 28 Gama Yahweh yana ƙaunar adalci kuma baya rabuwa da amintattun masu binsa. Yana kiyaye su har abada, amma zuriyar mugaye zasu zama korarru. 29 Adalai zasu gãji ƙasar su zauna ciki har abada. 30 Bakin adali yana maganar hikima da kuma ƙara adalci. 31 Shari'ar Allahnsa na zuciyarsa; ƙafafunsa ba za su yi santsi ba. 32 Mugu yakan yi fakon adali ya nemi hanyar kashe shi. 33 Yahweh ba zai bar shi a hannun mugun ba ko kuwa ya yanke masa hukunci sa'ad da ya ke masa shari'a. 34 Ka jira Yahweh ka kuma kiyaye hanyoyinsa, zaya kuma ɗaga ka sama ka mallaki ƙasar. Za ka gani sa'ad da ake korar mugaye. 35 Na ga mugu da azzalumin taliki ya baje kamar koren itace a ƙasarsa ta asali. 36 Amma sa'ad da na sãke wucewa kuma, bai kasance a wurin ba. Na neme shi, amma ba ya samuwa. 37 Dubi mutumin kirki, ka kuma lura da adali; gaba zai zama da kyau ga mutumin salama, 38 Masu zunubi kuwa za a hallaka su ƙaƙaf; za a kuma share zuriyar mugun mutum. 39 Ceton adalai yakan zo daga Yahweh ne; yakan kiyaye su a lokatan damuwa. 40 Yahwe ya taimake su ya kuɓutar da su, Ya kuɓutar dasu daga mugaye ya cece su saboda sun sami garkuwa a cikinsa.
1 Yahweh, do not rebuke me in your anger;
do not punish me in your wrath.
2 For your arrows pierce me,
and your hand presses me down.
3 There is no soundness in my body because of your anger;
there is no health in my bones because of my sin.
4 For my iniquities overwhelm me;
they are a burden too heavy for me.
5 My wounds are infected and smell
because of my foolish sins.
6 I am stooped over and humiliated every day;
I go about mourning all day long.
7 For within me, I am filled with burning;
there is no health in my flesh.
8 I am numb and utterly crushed;
I groan because of the anguish of my heart.
9 Lord, you understand my heart's deepest yearnings,
and my groanings are not hidden from you.
10 My heart pounds, my strength fades,
and the light of my eyes, even that is not with me.
11 My friends and companions shun me because of my condition;
my neighbors stand far off.
12 Those who seek my life lay snares for me.
They who seek my harm speak destructive words
and say deceitful words all day long.
13 But I, I am like a deaf man and hear nothing;
I am like a mute man who says nothing.
14 I am like a man who does not hear
and who has no reply.
15 Surely I wait for you, Yahweh;
you will answer, Lord my God.
16 I say this so that my enemies will not rejoice over me.
If my foot slips, they will do terrible things to me.
17 For I am about to stumble,
and I am in constant pain.
18 I confess my guilt;
I am anxious about my sin.
19 But my enemies are numerous;
those who hate me wrongfully are many.
20 They repay me evil for good;
they hurl accusations at me
although I have pursued what is good.
21 Do not abandon me, Yahweh;
my God, do not stay far away from me.
22 Come quickly to help me,
Lord, my salvation.
1 Yahweh, kada ka tsauta mani a cikin fushinka; kada ka hukunta ni a cikin hasalarka. 2 Gama kibiyoyinka suna sukana, kuma hannunka na matse ni har ƙasa. 3 Dukkan jikina na ciwo saboda hasalarka; babu lafiya a ƙasusuwana saboda laifina. 4 Gama zunubaina sun fi ƙarfina; sun zamar mani kaya mai nauyi da yawa. 5 Raunukana sun harbu suna wari saboda wawancin zunubaina. 6 Ana dakatar dani ana wulaƙanta ni kowacce rana; Ina ta makoki dukkan tsawon rana. 7 Gama daga ciki, ina cike da zafin ciwo; babu lafiya a jikina. 8 An sandare ni an ragargaza ni; ina gunaguni saboda fushin zuciyata. 9 Ubangiji kana sane da buƙatar zuciyata, kuma gunagunina basa ɓoyu ba daga gare ka. 10 Zuciyata na bugawa, ƙarfina na ƙarewa, bana kuma gani sosai. 11 Abokaina da aminai sun ƙaurace mani saboda yanayina; maƙwabtana na tsaye daga nesa. 12 Waɗanda ke so su kashe ni sun ƙafa mani tarko. Su waɗanda ke neman yi mani rauni suna maganar hallakarwa da faɗin kalmomin ruɗu dukkan tsawon rana. 13 Amma ni, ina kamar kurman mutum kuma bana jin komai; ina kamar beben da ba ya iya faɗin komai. 14 Ina kamar mutumin da ba ya ji kuma ba shi da amsa. 15 Tabbas ina jiranka, Yahweh; zaka amsa, Ubangiji, Allahna. 16 Na faɗi haka saboda maƙiyana ba zasu yi murna a kan damuwata ba. Idan tafin ƙafata ya zame, zasu yi mani mugayen abubuwa. 17 Gama ina gab da mutuwa, kuma ina cikin wahala kowacce sa'a. 18 Na furta laifofina; na kuma damu da zunubina. 19 Amma maƙiyana na da yawa; waɗanda suka ƙi ni cikin kuskure na da yawa. 20 Suna rama mani nagarta da mugunta; suna ta tuhuma ta koda ya ke ina neman abin da ke nagari. 21 Kada ka yashe ni, Yahweh; Allahna, kada ka tsaya nesa dani. 22 Ka zo da sauri ka taimakeni, Ubangiji, cetona.
1 I decided, "I will watch what I say
so that I do not sin with my tongue.
I will muzzle my mouth
while in the presence of an evil man."
2 I kept silent;
I kept back my words even from saying anything good,
and my pain grew worse.
3 My heart became hot;
when I thought about these things,
it burned like a fire.
Then finally I spoke.
4 "Yahweh, make me know when will be the end of my life
and the extent of my days.
Show me how transient I am.
5 See, you have made my days only the width of my hand,
and my lifetime is like nothing before you.
Surely every man is a single breath. Selah
6 Surely every man walks about like a shadow.
Surely everyone hurries about
to accumulate riches although they do not know who will receive them.
7 Now, Lord, for what am I waiting?
You are my only hope.
8 Rescue me from my sins;
do not make me the scorn of fools.
9 I am silent and cannot open my mouth,
because it is you who has done it.
10 Stop wounding me;
I am overwhelmed by the blow of your hand.
11 When you discipline people for iniquity,
you consume the things they desire like a moth;
surely all people are nothing but vapor. Selah
12 Hear my prayer, Yahweh,
and give ear to my cry for help;
do not be deaf to my tears!
for I am like a foreigner with you,
a sojourner like all my ancestors were.
13 Turn your gaze from me so that I may smile again
before I die."
1 Na yi shiri, "Zan lura da furcin da zan yi saboda kada in yi zunubi da harshe na. Zan sa wa bakina takunkumi a lokacin da nake wurin da mugu ya kasance." 2 Na yi shiru; Na riƙe maganganuna daga faɗin wani abu koda nagari ne, shanwuta kuma ta ƙaru. 3 Zuciyata ta yi zafi; sa'ad da nayi tunani a kan abubuwan nan, yana ci kamar wuta. Sa'an nan a ƙarshe nayi magana. 4 "Yahweh, kasa in san yaushe ne ƙarshen rayuwata da tsawon kwanakina. Ka nuna mani ina kurkusa da matuwa. 5 Duba, kã maida kwanakina kamar tsawon hannuna, kuma rayuwata kamar ba komai take ba a wurinka. Hakika kowanne mutum lumfashi ɗaya ne. Selah 6 Hakika kowanne mutum yana tafiya kamar inuwa. Hakika dukkan kowa yana hanzari ya tattara arziki ko da yake basu san wanda zai karbe su ba. 7 Yanzu, Ubangiji, domin me nake jira? Kai ƙaɗai ne begena. 8 Ka cece ni daga zunubaina; kada ka bari in zama abin ba'a ga wawaye. 9 Na yi shiru kuma bazan iya buɗe bakina ba, saboda kai ne kayi haka. 10 Ka daina yi mani rauni; na karaya ta wurin bugun hannunka. 11 Sa'ad da kake horar da mutane don zunubi, kakan cinye abubuwan da suke marmari kamar asu; hakika dukkan mutane ba komai bane banda tururi kawai. Seleh 12 Ka ji addu'ata, Yahweh, ka saurare ni; ka saurari kukana! Kada ka zama kurma a gare ni, gama ni kamar baƙo ne tare da kai, ɗan gudun hijira kamar yadda dukkan kakannina suke. 13 Ka juyar da harararka daga gare ni domin in sake yin murmushi kafin in mutu,"
1 I waited patiently for Yahweh;
he listened to me and heard my cry.
2 He brought me up out of a horrible pit,
out of the miry clay,
and he set my feet on a rock
and made my steps secure.
3 He has put a new song in my mouth,
praise to our God.
Many will see it and honor him
and will trust in Yahweh.
4 Blessed is the man
who makes Yahweh his trust
and does not honor the proud
or those who turn away from him to lies.
5 Many, Yahweh my God,
are the wonderful deeds that you have done,
and your thoughts which are about us cannot be numbered;
if I declared and spoke of them,
they would be more than could be counted.
6 You have no delight in sacrifice or offering,
but you have opened my ears;
you have not required burnt offerings or sin offerings.
7 Then said I, "See, I have come;
it is written about me in the scroll of the document.
8 I delight to do your will, my God;
your laws are in my heart."
9 I have proclaimed good news of your righteousness in the great assembly;
Yahweh, you know that my lips have not kept back from doing this.
10 I have not concealed your righteousness in my heart;
I have declared your faithfulness and your salvation;
I have not concealed your covenant faithfulness
or your trustworthiness from the great assembly.
11 Do not keep back your acts of mercy from me, Yahweh;
let your covenant faithfulness and your trustworthiness always preserve me.
12 Troubles that cannot be numbered surround me;
my iniquities have caught up with me so that I am no longer able to see anything;
they are more than the hairs on my head,
and my heart has failed me.
13 Be pleased, Yahweh, to rescue me;
hurry to help me, Yahweh.
14 Let them be ashamed and completely disappointed
who pursue my life to sweep it away.
Let them be turned back and brought to dishonor,
those who delight in hurting me.
15 Let them be appalled because of their shame,
those who say to me, "Aha, aha!"
16 But may all those who seek you rejoice
and be glad in you;
let everyone who loves your salvation say continually,
"May Yahweh be praised."
17 I am poor and needy;
yet the Lord thinks about me.
You are my help and you come to my rescue;
do not delay, my God.
1 Na jira Yahweh da haƙuri; ya saurare ni ya ji kukana. 2 Ya fitar dani daga rami mai furgitarwa, daga taɓo, ya sa ƙafafuna a kan dutse ya tsare takawata. 3 Ya sa sabuwar waƙa a bakina, yabo ga Allahnmu. Da yawa zasu gani su kuma girmama shi su dogara ga Yahweh. 4 Mai albarka ne mutumin da ya maida Yahweh madogararsa kuma baya girmama masu fahariya ko waɗanda suka juya daga gare shi zuwa ƙarairayi. 5 Da yawa suke, Yahweh Allahna, ayyukan al'ajiban da ka yi, kuma babu wanda zai iya ƙirga abubuwan da kake tunani gme da mu; Idan na yanke shawara in yi magana a kan su, za su fi abin da za a iya ƙirgawa. 6 Ba ka buƙatar hadaya ko baiko, amma ka buɗe kunnuwana; ba ka buƙatar baye-baye na ƙonawa ko baye-baye na zunubi. 7 Sa'an nan na ce, "Duba, Na zo; a rubuce ya ke a game dani cikin littafin Yahweh. 8 Ina jin daɗin yin nufinka, Allahna, shari'unka na cikin zuciyata." 9 Na yi shelar nagartattun labaran ayyukanka na adalci a babban taron jama'a; Yahweh, ka san leɓunana basu dena yin wannan ba. 10 Ban ɓoye ayyukan adalcinka a zuciyata kaɗai ba; Na furta amincinka da cetonka; Ban ɓoye amintaccen alƙawarinka ko madawwamiyar ƙaunarka daga babban taron jama'a ba. 11 Kada ka yi jinkirin yi mani ayyukan jinƙai; ka bar amintaccen alƙawarinka da madawwamiyar ƙaunarka su kiyaye ni. 12 Damuwoyin da basu ƙidayuwa sun kewaye ni; alhakin zunubaina ya tarar da ni har yasa bana iya ganin wani abu; Sun fi gashin kaina yawa, kuma zuciyata ta karaya. 13 In ka yarda, Yahweh, ka cece ni; ka yi hanzari ka taimake ni, Yahweh. 14 Ka sa waɗanda suke son kashe ni su sha kunya da yawa. Kasa su koma baya a ci nasara a kansu, ka kawo waɗanda ke murna saboda wahalar da nake sha, cikin ƙasƙanci. 15 Kasa su razana saboda kunya, su waɗanda ke yi mani ba'a, " 16 Amma bari dukkan waɗanda ke neman ka su yi farinciki da murna a cikinka; ka sa duk mai ƙaunar cetonka ya ci gaba da cewa, "A yabi Yahweh." 17 Na talauce na zama mabuƙaci; duk da haka Ubangiji yana tunani a kai na. Kai ne mai taimako na kuma ka zo domin ka cece ni; kada ka yi jinkiri, Allahna.
1 Blessed is he who is concerned for the weak;
in the day of trouble, Yahweh will rescue him.
2 Yahweh will preserve him and keep him alive,
and he will be blessed on the earth;
Yahweh will not turn him over to the will of his enemies.
3 Yahweh will support him on the bed of suffering;
you will make his bed of sickness into a bed of healing.
4 I said, "Yahweh, have mercy on me!
Heal me, for I have sinned against you."
5 My enemies speak evil against me, saying,
'When will he die and his name perish?'
6 If my enemy comes to see me,
he says worthless things;
his heart gathers up wickedness for itself;
when he goes away from me, he tells others about it.
7 All who hate me whisper together against me;
against me they hope for my hurt.
8 They say, "An evil disease holds on tightly to him;
now that he is lying down, he will rise up no more."
9 Indeed, even my own close friend, in whom I trusted,
who ate my bread,
has lifted up his heel against me.
10 But you, Yahweh, have mercy on me and raise me up
so that I may pay them back.
11 By this I know that you delight in me,
for my enemy does not triumph over me.
12 As for me, you support me in my integrity
and will keep me before your face forever.
13 May Yahweh, the God of Israel be praised
from everlasting to everlasting.
Amen and Amen.
1 Mai albarka ne wanda ke kulawa da marasa ƙarfi; a ranar masifa, Yahweh zai 'yantar da shi. 2 Yahweh zai kiyaye shi ya kare shi, kuma zai zama da albarka a duniya; Yahweh ba zai bar shi ga nufin maƙiyansa ba. 3 Yahweh zai yi masa gudummawa a gadon wahalarsa; zaka maida gadonsa na ciwo zuwa gadonsa na warkarwa. 4 Na ce, "Yahweh, ka yi mani jinƙai! Ka warkar dani, gama na yi maka laifi." 5 Maƙiyana suna muguwar magana gãba da ni, cewa, 'Yaushe ne zai mutu kuma sunansa ya lalace?' 6 Idan maƙiyina ya zo gani na, ya furta maganganun banza; zuciyarsa na ƙoƙarin sanin dukkan matsalolina; sa'ad da ya tafi daga gare ni, sai ya gaya wa kowa game da su. 7 Dukkan waɗanda ke ƙi na na raɗa da juna gãba da ni; gãba da ni suna fatan shan wahalata. 8 Suna cewa, "Mugun ciwo ya make shi; yanzu da ya ke kwance ƙasa, ba zai ƙara tashi ba." 9 Lallai, ko abokina na ƙut da ƙut, da na yarda da shi, wanda ya ci gurasata, ya juya mani baya. 10 Amma kai, Yahweh, ka yi mani jinƙai ka ɗaga ni sama saboda in mai da martani. 11 Ta wannan na san kana farinciki dani, gama maƙiyina bai yi murna a kaina ba. 12 Amma ni, ka tallefe ni cikin aminncina kuma zaka kiyaye ni a fuskarka har abada. 13 Bari Yahweh, Allah na Isra'ila a yabe shi daga dawwama zuwa dawwama. Amin da Amin. Littafi Biyu
1 As the deer pants after streams of water,
so I thirst for you, God.
2 I thirst for God, for the living God,
when will I come and appear before God?
3 My tears have been my food
day and night,
while my enemies are always saying to me,
"Where is your God?"
4 These things I call to mind
as I pour out my soul:
how I went with the throng
and led them to the house of God
with the voice of joy and praise,
a multitude celebrating a festival.
5 Why are you bowed down, my soul?
Why are you upset within me?
Hope in God,
for again I will praise him who is my salvation.
6 My God, my soul is bowed down within me,
therefore I call you to mind from the land of the Jordan,
from the three peaks of Mount Hermon, and from the hill of Mizar.
7 Deep calls to deep at the noise of your waterfalls;
all your waves and your billows have gone over me.
8 Yet Yahweh will command his covenant faithfulness in the daytime;
in the night his song will be with me,
a prayer to the God of my life.
9 I will say to God, my rock,
"Why have you forgotten me?
Why do I go mourning
because of the oppression of the enemy?"
10 As with a sword in my bones, my adversaries rebuke me,
while they always say to me, "Where is your God?"
11 Why are you bowed down, my soul?
Why are you upset within me?
Hope in God,
for again I will praise him who is my salvation and my God.
1 Kamar yadda mariri ke marmarin rafukan ruwa, haka nake ƙishinka, Allah. 2 Ina ƙishin Allah, Allah mai rai, yaushe zan zo in bayyana a gaban Allah? 3 Hawayena sun zama abincina dare da rana, lokacin da maƙiyana kullum suna cewa dani, "Ina Allahnka?" 4 Waɗannan abubuwan nake tunawa da su yayin da nake zubo raina: yadda na tafi tare da taron mutane na jagorance su zuwa gidan Allah tare da muryar jin daɗi da yabo, babban taro na shagalin buki. 5 Me yasa ka rusuna ƙasa, raina? Me yasa kake damuwa daga can ciki? Yi bege ga Allah, gama zan ƙara yabonsa wanda shi ne cetona. 6 Allahna, raina ya rusuna ƙasa a can ciki, don haka na tuna da kai daga ƙasar Yordan, daga ƙololuwar Dutsen Hamon, kuma daga tudun Miza. 7 Zurfi na kira ga zurfi da jin ƙarar kwararowar ruwanka; dukkan raƙuman ruwanka da matsirgan ruwanka sun mamaye ni. 8 Duk da haka Yahweh zai umarci amintaccen alƙawarinsa da rana; da dare waƙarsa zata kasance tare da ni, addu'a ce ga Allah na rayuwata. 9 Zan yi magana ga Allah, dutsena, "Me yasa ka mance da ni" Me yasa nake makoki saboda danniyar maƙiyina?" 10 Kamar da takobi a ƙasusuwana, maƙiyana ke yi mani zargi, yayin da kullum suke cewa dani, "Ina Allahnka?" 11 Me yasa kake rusuna a ƙasa, raina? Me yasa kake damuwa can ciki? Yi bege cikin Allah, gama kuma zan yabe shi wanda shi ne cetona da Allahna.
1 Bring me justice, God,
and plead my case against a nation that is not faithful.
Deliver me from the deceitful and unjust man.
2 For you are the God of my strength.
Why have you rejected me?
Why do I go about in mourning
because of the oppression of the enemy?
3 Oh, send out your light and your truth,
let them lead me.
Let them bring me to your holy hill
and to your dwelling.
4 Then I will go to the altar of God,
to God my exceeding joy.
I will praise you with the harp,
God, my God.
5 Why are you bowed down, my soul?
Why are you upset within me?
Hope in God,
for again I will praise him who is my salvation and my God.
1 Kawo mani adalci, Allah, kayi mani taimakon kãriya a kan al'umma marasa tsoron ka. 2 Gama kai ne Allah na ƙarfina. Meyasa ka yashe ni? Me yasa nake tafiya cikin makoki saboda muzgunawar maƙiya? 3 Oh, ka aiko da haskenka da gaskiyarka, su jagorance ni. su kawo ni ga tudunka mai tsarki da wurin zamanka. 4 Sa'an nan zan yi tafya zuwa ga bagadin Allah, ga Allah matuƙar jin daɗina. Zan yabeka da garaya, Allah, Allahna. 5 Me yasa ka rusuna ƙasa, raina? Me ya sa kake damuwa can ciki? Yi bege cikin Allah, gama zan ƙara yabonsa wanda shi ne cetona da Allahna.
1 We have heard with our ears, God,
our fathers have told us
what work you did in their days,
in the days of old.
2 You drove out the nations with your hand,
but you planted our people;
you afflicted the peoples,
but you spread our people out in the land.
3 For they did not obtain the land for their possession by their own sword,
neither did their own arm save them;
but your right hand, your arm, and the light of your face,
because you were favorable to them.
4 God, You are my King;
command victory for Jacob.
5 Through you we will push down our adversaries;
through your name we will tread them under,
those who rise up against us.
6 For I will not trust in my bow,
neither will my sword save me.
7 But you have saved us from our adversaries,
and have put to shame those who hate us.
8 In God we have made our boast all the day long,
and we will give thanks to your name forever. Selah
9 But now you have rejected us and brought us dishonor,
and you do not go out with our armies.
10 You make us turn back from the adversary;
and those who hate us take spoil for themselves.
11 You have made us like sheep to be slaughtered
and have scattered us among the nations.
12 You sell your people for nothing;
you have not increased your wealth by doing so.
13 You make us a rebuke to our neighbors,
scoffed and mocked by those around us.
14 You make us an insult among the nations,
a shaking of the head among the peoples.
15 All the day long my dishonor is before me,
and the shame of my face has covered me
16 because of the voice of him who rebukes and insults,
because of the enemy and the avenger.
17 All this has come on us; yet we have not forgotten you
or dealt falsely with your covenant.
18 Our heart has not turned back;
our steps have not gone from your way.
19 Yet you have severely broken us in the place of jackals
and covered us with the shadow of death.
20 If we have forgotten the name of our God
or spread out our hands to a strange god,
21 would not God search this out?
For he knows the secrets of the heart.
22 Indeed, for your sake we are being killed all day long;
we are considered to be sheep for the slaughter.
23 Awake, why do you sleep, Lord?
Arise, do not reject us forever.
24 Why do you hide your face
and forget our affliction and our oppression?
25 For we have sunk down into the dust;
our bodies cling to the earth.
26 Rise up for our help
and redeem us for the sake of your covenant faithfulness.
1 Mun ji da kunnuwanmu, Allah, Kakanninmu suka faɗa mana irin aikin da ka yi a kwanakinsu, a kwanakin dã. 2 Ka kore al'ummai da hannunka, amma ka dasa mutanenmu; ka azabci mutane, amma ka baza mutanenmu cikin ƙasar. 3 Gama basu samu mallakar ƙasar ta takobin kansu ba, ba kuma ƙarfin kansu ba ne ya cece su; amma hannun damanka da ƙarfinka da hasken fuskarka ne, saboda yi tagomashi gare su. 4 Allah, kai ne sarkina; ka umarta nasara domin Yakubu. 5 Da taimakonka zamu tura maƙiyanmu; da sunanka za mu tattakesu, waɗanda suka tashi gãba da mu. 6 Gama ba zan dogara ga bakana ba, takobina kuma ba zai cece ni ba. 7 Amma ka cece mu daga maƙiyanmu, ka ba masu ƙinmu kunya. 8 A cikin Allah muke fahariya a kullum, kuma za mu yi godiya ga sunanka har abada. Selah 9 Amma yanzu ka ƙi mu ka kawo mu ga kunya, kuma baka yi tafiya tare da mayaƙanmu ba. 10 Ka sa muka juya baya daga maƙiyin; kuma waɗanda suka ƙi mu suna ɗibi ganima domin kansu. 11 Ka maida mu kamar tumakin da aka ƙaddara don abinci ka warwatsar da mu cikin al'ummai. 12 Ba a bakin komai ka sayar da mutanenka ba; ba ka ƙara wadatarka ta yin haka ba. 13 Ka maida mu abin zargi ga maƙwabtanmu, waɗanda ke kewaye da mu suna yi mana reni da ba'a. 14 Ka sa mun zama abin zãgi cikin al'ummai, abin girgiza kai cikin tarrukan mutane. 15 A dukkan tsawon rana ƙasƙancina na gabana, kuma kunyar fuskata ta rufe ni 16 saboda muryar wanda ke tsautarwa da zage-zage, saboda maƙiyi da mai ɗaukar fansa. 17 Dukkan waɗannan sun zo a kanmu; duk da haka ba mu mance da kai ba ko kuwa mu yi aiki cikin rahin gaskiya da alƙawaranka. 18 Zuciyarmu bata juya ba; ƙafafunmu ba su yi nisa daga hanyarka ba. 19 Duk da haka ka kakkarya mu a wurin diloli ka rufe mu da inuwar mutuwa. 20 Idan mun mance da sunan Allahnmu ko kuwa muka buɗe hannuwanmu ga wani bãƙon allah, 21 Allah ba zai bincika haka ba? Gama ya san asiran zuciya. 22 Hakika, ta dalilinka ake karkashe mu dukkan rana; ana yi mana kallon tumaki domin yanka. 23 Farka, me yasa kake barci, Ubangiji? Tashi, kada ka jefar da mu da daɗewa. 24 Me yasa ka ɓoye fuskarka ka mance da matsananciyar azabarmu da wahalarmu? 25 Gama mun narke mun zama ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa. 26 Tashi tsaye domin taimakonmu ka 'yantar da mu ta dalilin amintaccen alƙawarinka.
1 My heart overflows on a good subject;
I will read aloud the words I have composed about the king;
my tongue is the pen of a ready writer.
2 You are fairer than the children of mankind;
grace is poured onto your lips;
therefore we know that God has blessed you forever.
3 Gird your sword to your side, mighty one,
in your glory and your majesty.
4 In your majesty ride on triumphantly
because of trustworthiness, meekness, and righteousness;
your right hand will teach you fearful things.
5 Your arrows are sharp;
the peoples fall under you;
your arrows are in the hearts of the king's enemies.
6 Your throne, God, is forever and ever;
a scepter of justice is the scepter of your kingdom.
7 You have loved righteousness and hated wickedness;
therefore God, your God, has anointed you
with the oil of gladness more than your companions.
8 All your garments smell of myrrh, aloes, and cassia;
out of ivory palaces
stringed instruments have made you glad.
9 Kings' daughters are among your honorable women;
at your right hand stands the queen clothed in gold of Ophir.
10 Listen, daughter, consider and incline your ear;
forget your own people and your father's house.
11 In this way the king will desire your beauty;
he is your master; revere him.
12 The daughter of Tyre will be there with a gift;
the rich among the people will beg for your favor.
13 The royal daughter in the palace is all glorious;
her clothing is worked with gold.
14 She will be led to the king in embroidered dress;
the virgins, her companions who follow her,
will be brought to you.
15 They will be led by gladness and rejoicing;
they will enter into the king's palace.
16 In the place of your fathers will be your children,
whom you will make princes in all the earth.
17 I will make your name to be remembered in all generations;
therefore the peoples will give you thanks forever and ever.
1 Zuciyata na jin daɗi da nagartaccen zance; Zan karanta kalmomin da na harhaɗo a kan sarki da ƙarfi; harshena shi ne al'ƙalamin shiryayyen marubuci. 2 Ka fi 'ya'yan ɗan Adam kyau; an zuba alheri a leɓunanka; saboda haka mun san Allah ya albarkaceka har abada. 3 Kasa takobinka a gefenka, mai girma, cikin ɗaukakarka da martabarka. 4 Cikin darajarka ka hau dokinka cikin murna saboda yarda da tawali'u da ayyukan adalci; hannun damanka zai koya maka abubuwan bantsoro. 5 Kibawunka na da ƙaifi; mutane sun faɗa ƙarƙashinka; kibawunka na cikin zukatan maƙiyan sarki. 6 Kursiyinka, Allah, yana nan har abada, sandar adalci shi ne sandar mulkinka. 7 Kana ƙaunar ayyukan adalci kuma kana ƙin mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya shafe ka da mai na murna fiye da abokan taraiyarka. 8 Dukkan tufafinka na ƙamshin turaren mur da aloyes da ƙahonnin da aka samo; daga kowacce fadar hauren giwa kayyakin busa da kiɗe-kiɗe sun saka murna. 9 'Ya'ya mata na sarakuna na cikin matayenka masu martaba; sarauniya na tsaye da tufafin zinariya da Ofir a hannun damanka, 10 Saurara, ɗiya, ki maida hankali ki buɗe kunne, ki mance da mutanenki da gidan mahaifinki. 11 Ta haka sarkin zai yi marmarin kyanki; shi shugabanki ne; ki girmama shi. 12 Ɗiyar Taya zata kasance a wurin da kyauta; masu arziki cikin mutanen za su nemi alfarmarku. 13 Ɗiya gimbiya a fãda tana cikin dukkan ɗaukaka; an yi aikin tufafinta da zinariya. 14 Za a kaita wurin sarki cikin kyawawan tufafi masu ado kala-kala; budurwai, ƙawayenta dake binta, za a kawo maka. 15 Za a jagorance su da murna da farinciki; za su shiga cikin fadar sarki. 16 A fãdar ubanninka 'ya'yanka zasu kasance, waɗanda zaka maida su yarimai a dukkan duniya. 17 Zan sa sunanka ya dawwama a dukkan tsararraki; saboda haka mutanen zasu yi maka godiya har abada abadin.
1 God is our refuge and strength,
a very present help in trouble.
2 Therefore we will not fear, though the earth should change,
though the mountains should be shaken into the heart of the seas,
3 though its waters roar and rage, and
though the mountains tremble with their swelling. Selah
4 There is a river whose streams make the city of God happy,
the holy place where the Most High dwells.
5 God is in the middle of her; she will not be moved;
God will help her, and he will do so at the dawn of morning.
6 The nations raged and the kingdoms were shaken;
he lifted up his voice, and the earth melted.
7 Yahweh of hosts is with us;
the God of Jacob is our refuge. Selah
8 Come, behold the deeds of Yahweh,
who has set up objects of horror on earth.
9 He makes wars cease to the ends of the earth;
he breaks the bow and cuts the spear into pieces;
he burns up the shields.
10 Be quiet and know that I am God;
I will be exalted among the nations;
I will be exalted on the earth.
11 Yahweh of hosts is with us;
the God of Jacob is our refuge. Selah
1 Allah shi ne mafakarmu da ƙarfinmu, Mai matuƙar taimako a lokacin wahala. 2 Domin haka ba za mu ji tsoro ba, ko duniya zata canza, ko an girgiza duwatsu har cikin tekuna, 3 ko ruwayenta sun yi ruri da tangaɗi, duwatsu kuma suna motsi saboda kumburinsu. Selah 4 Akwai kogi, da ƙoramu waɗanda ke sa birnin Allah farinciki, wuri mai tsarki na shirayi na Maɗaukaki. 5 Allah yana cikin tsakiyarta; ba zata kawu ba; Allah zai taimake ta, kuma zai yi haka da sassafen safiya. 6 Al'ummai suka fusata kuma mulkoki suka girgiza; ya tayar da muryarsa, kuma duniya ta narke. 7 Yahweh mai runduna na tare da mu; Allah na Yakubu shi ne mafakarmu. Selah 8 Zo, dubi ayyukan Yahweh, hallakar da ya kawo wa duniya. 9 Ya sa yaƙe-yaƙe su ƙare har zuwa iyakar duniya; ya kakkarya baka ya daddatsa mãsu gutsu--gutsu; ya ƙone garkuwoyi. 10 Ku yi shiru ku sani Ni ne Allah; Zan sami ɗaukaka a cikin al'ummai; Za a ɗaukaka ni a duniya. 11 Yahweh mai runduna na tare da mu; Allah na Yakubu ne mafakarmu. Saleh
1 Clap your hands, all you peoples;
shout to God with the sound of celebration.
2 For Yahweh Most High is terrifying;
he is a great King over all the earth.
3 He subdues peoples under us
and nations under our feet.
4 He chooses our inheritance for us,
the pride of Jacob whom he loved. Selah
5 God has gone up with a shout,
Yahweh with the sound of a ram's horn.
6 Sing praises to God, sing praises;
sing praises to our King, sing praises.
7 For God is the King over all the earth;
sing praises with understanding.
8 God reigns over the nations;
God sits on his holy throne.
9 The princes of the peoples have gathered together
to the people of the God of Abraham;
for the shields of the earth belong to God;
he is greatly exalted.
1 Ku tafa hannuwanku, ku dukkan mutane; ku yi sowa ga Allah da muryar nasara. 2 Gama Yahweh Maɗaukaki abin tsoro ne; shi Sarki ne mai girma bisa dukkan duniya. 3 Ya mayar da mutane ƙarƙashinmu, ya sa al'ummai a ƙarƙƙashin ƙafafunmu. 4 Ya zaɓi gãdonmu dominmu, ɗaukakar Yakubu wanda ya ke ƙauna. Selah 5 Allah ya tafi sama da sowa, Yahweh da ƙarar kakaki. 6 Raira waƙoƙin yabo ga Allah. raira waƙoƙin yabo; raira waƙoƙin yabo ga Sarkinmu, raira waƙoƙin yabo. 7 Gama Allah Sarki ne a kan dukkan duniya; raira woƙoƙin yabo da ganewa. 8 Allah yana mulki a kan al'ummai; Allah na zaune a tsattsarkan kursiyinsa. 9 'Ya'yan sarakuna sun tattaru wurin mutanen Allah na Ibrahim; gama garkuwoyin duniya na Allah ne; yana da ɗaukaka mai girma.
1 Great is Yahweh and greatly to be praised,
in the city of our God on his holy mountain.
2 Beautiful in elevation,
the joy of the whole earth,
is Mount Zion, on the sides of the north,
the city of the great King.
3 God has made himself known in her palaces as a refuge.
4 For, see, the kings assembled themselves;
they passed by together.
5 They saw it, then they were amazed;
they were dismayed, and they hurried away.
6 Trembling took hold of them there,
pain as when a woman is in labor.
7 With the east wind
you break the ships of Tarshish.
8 As we have heard,
so have we seen
in the city of Yahweh of hosts,
in the city of our God;
God will establish it
forever. Selah
9 We have thought about your covenant faithfulness, God,
in the middle of your temple.
10 As your name is, God,
so is your praise to the ends of the earth;
your right hand is full of righteousness.
11 Let Mount Zion be glad,
let the daughters of Judah rejoice
because of your righteous decrees.
12 Walk around Mount Zion, go round about her;
count her towers,
13 notice well her walls,
and look at her palaces
so that you may tell it to the next generation.
14 For this God is our God forever and ever;
he will be our guide to death.
1 Yahweh mai girma ne kuma a yabe shi da girma, cikin birnin Allahnmu a tsauni mai tsarki. 2 Mai kyakkyawan tsawo, farincikin duk duniya, shi ne Tsaunin Sihiyona, a kusurwoyin arewa, birnin sarki mai girma. 3 Allah ya maida kansa sananne a cikin fadodinta a matsayin mafaka. 4 Gama, duba, sarakuna sun tattaro kansu; suna wucewa tare. 5 Suka gan ta, sa'an nan suka yi mamaki; suka damu ƙwarai, sai suka wuce da sauri. 6 Firgici ya mamaye su a wurin, da azaba kamar ta mace mai naƙuda. 7 Da iskar gabas ka karya jiragen ruwan Tarshish. 8 Kamar yadda muka ji haka muka gani a birnin Yahweh mai runduna, a birnin Allahnmu; Allah zai kafa shi har abada. Selah 9 Mun yi tunanin amintaccen alƙawarinka, Allah. a tsakiyar haikalinka. 10 Kamar yadda sunanka ya ke, Allah, haka yabonka har ga iyakar duniya; hannun damanka na cike da ayyukan adalci. 11 Tsaunin Sihiyona yi murna, bari 'ya'ya mata na Yahuda su yi farinciki saboda shari'unka masu adalci. 12 Yi tafiya a kewayen Dutsen Sihiyona, je ka kewaya ta, harabarta da hasumiyarta, 13 lura da bangayenta sosai kuma ka duba fãdodinta da kyau, don ka faɗa wa tsara mai zuwa. 14 Gama wannan Allahn shi ne Allahnmu har abada abadin; shi zai bi damu har mutuwa.
1 Hear this, all you peoples;
give ear, all you inhabitants of the world,
2 both low and high,
rich and poor together.
3 My mouth will speak wisdom
and the meditation of my heart will be of understanding.
4 I will incline my ear to a parable;
I will begin my parable with the harp.
5 Why should I fear the days of evil,
when iniquity surrounds me at my heels?
6 Why should I fear those who trust in their wealth
and boast about the amount of their riches?
7 It is certain that no one can redeem his brother
or give God a ransom for him,
8 For the redemption of one's life is costly,
and no one can pay what we owe.
9 No one can live forever
so that he would not see the pit.
10 For he will see decay. Wise men die;
the fool and the brute alike perish
and leave their wealth to others.
11 Their inner thought is that their families will continue forever,
and the places where they live, to all generations;
they call their lands after their own names.
12 But man, having wealth, does not remain alive;
he is like the wild animals that perish.
13 This, their way, is their folly;
yet after them, men approve of their sayings. Selah
14 Like sheep they are appointed for Sheol,
and death will be their shepherd.
The upright will rule over them in the morning,
and their bodies will be consumed in Sheol,
with no place for them to live.
15 But God will redeem my life from the power of Sheol;
he will receive me. Selah
16 Do not be afraid when one becomes rich,
and the glory of his house increases.
17 For when he dies he will take nothing away;
his glory will not go down after him.
18 He blessed his soul while he lived—
and men praise you when you live for yourself—
19 he will go to the generation of his fathers
and they will never see the light again.
20 One who has wealth but no understanding
is like the animals that perish.
1 Ku ji wannan, dukkanku mutane; ku kasa kunne, dukkanku mazaunan duniya, ƙanana da manya, 2 masu arziki da matalauta dukka. 3 Bakina zai yi maganar hikima kuma nazarin zuciyata zai zama na ganewa. 4 Zan sa kunnena ga misali; zan fara misalina da molo. 5 Me zai sa in ji tsoron kwanakin mugunta, sa'ad da zunuban maƙiyana suka kewaye ni. 6 Me zai sa in ji tsoron waɗanda suka dogara ga wadatarsu suke kuma yin fahariya game da arzikinsu? 7 Tabbas babu wanda zai iya fansar ɗan'uwansa ko ya ba Allah fansa dominsa, 8 Gama 'yantar da ran wani na da tsada, kuma ba wanda zai iya biyan bashinmu. 9 Babu wanda zai dawwama da har jikinsa ba zai ruɓe ba. 10 Gama zai ga ruɓa. Masu hikima na mutuwa; wawaye da sakarkaru ma na lalacewa su kuma bar wadatarsu ga waɗansu. 11 Tunaninsu na can ciki shi ne iyalansu zasu cigaba har abada, wuraren da suke zama kuma, su cigaba har dukkan tsararraki; suna kiran gonakinsu da sunayensu. 12 Amma mutum, mai arziki ba shi rayuwa har abada; yana kamar dabbobi dake mutuwa. 13 Wannan, hanyarsu, ita ce wautarsu; duk da haka bayansu, mutane suna amincewa da maganganunsu. 14 Kamar tumaki an ƙaddara su ga Lahira, kuma mutuwa zata zama mai kiwon su. Adalai zasu yi mulki a kansu da safe, kuma jikunansu zasu hallaka a Lahira, tare da rashin wurin zama dominsu. 15 Amma Allah zai 'yantar da rai na daga ikon lahira; zai karɓe ni. Selah 16 Kada ka ji tsoro sa'ad da wani ya yi arziki, kuma darajar gidansa ta ƙaru. 17 Gama sa'ad da ya mutu ba zai tafi da komai ba; darajarsa ba zata tafi tare da shi ba sa'ad da ya mutu. 18 Ko da mutum yana farinciki da nasararsa saboda arzikinsa yayin da ya ke raye- kuma mutane na yabonka sa'ad da kake rayuwa don kanka- 19 zai tafi zuwa tsarar ubanninsa kuma ba za su ƙara ganin haske kuma ba. 20 Mai wadata amma ba shi da ganewa yana kamar dabbobi, dake lalacewa.
1 The Mighty One, God, Yahweh,
has spoken and called the earth
from the rising of the sun to its setting.
2 Out of Zion, the perfection of beauty,
God has shone.
3 Our God comes
and does not stay silent;
a fire devours before him,
and it is very stormy around him.
4 He calls to the heavens above
and to the earth so that he may judge his people:
5 "Gather my faithful ones together to me,
those who have made a covenant with me by sacrifice."
6 The heavens will declare his righteousness,
for God himself is judge. Selah
7 "Hear, my people, and I will speak, Israel,
and I will testify against you.
I am God, your God.
8 I will not reprove you for your sacrifices;
your burnt offerings are always before me.
9 I will take no bull out of your house,
or male goats out of your folds.
10 For every animal of the forest is mine,
and the cattle on a thousand hills.
11 I know all the birds of the mountains,
and the wild beasts of the field are mine.
12 If I were hungry, I would not tell you;
for the world is mine, and everything in it.
13 Will I eat the flesh of bulls
or drink the blood of goats?
14 Offer to God the sacrifice of thanksgiving,
and pay your vows to the Most High.
15 Call on me in the day of trouble;
I will rescue you, and you will glorify me."
16 But to the wicked God says,
"What have you to do with declaring my statutes,
that you have taken my covenant in your mouth,
17 since you hate instruction
and throw my words away?
18 When you see a thief, you agree with him;
you participate with those who commit adultery.
19 You give your mouth to evil,
and your tongue expresses deceit.
20 You sit and speak against your brother;
you slander your own mother's son.
21 You have done these things, but I have kept silent,
so you thought that I was someone just like yourself.
But I will reprove you
and bring up, right before your eyes, all the things you have done.
22 Give this careful consideration, you who forget God,
otherwise I will tear you to pieces,
and there will be no one to come to help you!
23 The one who offers a sacrifice of thanksgiving praises me,
and to anyone who plans his path in the right way
I will show God's salvation."
1 Maɗaukaki, Allah, Yahweh, ya yi magana yana kiran duniya daga fitar rana zuwa faɗuwarta. 2 Daga Sihiyona, wuri mafi kyau, Allah yana haskakawa. 3 Allahnmu ya zo kuma ba ya tsaye shiru; wuta na ci a gabansa, kuma babban hadari na kewaye da shi. 4 Ya kira sammai da duniya domin ya shar'anta mutanensa. 5 Tattaro mani amintattuna dukka gare ni, waɗanda suka yi alƙawari dani ta miƙa hadaya." 6 Sammai zasu yi shelar ayyukan adalcinsa, gama Allah da kansa alƙali ne. Selah 7 Ku ji, mutanena, kuma zan yi magana; Ni ne Allah, Allahnku. 8 Ba zan kwaɓe ku domin hadayunku ba; hadayunku na ƙonawa na gabana kullum. 9 Ba zan ƙarɓi bijimi daga gidanku ba, ko kuwa bunsurai daga garkenku ba. 10 Gama kowanne naman jeji nawa ne da shanun kan tuddai dubu. 11 Na san dukkan tsuntsayen duwatsu, kuma namomin jeji na fili nawa ne. 12 Idan ina jin yunwa, ba zan faɗa maku ba; gama duniya tawa ce, da dukkan abin da ke cikinta. 13 Ko zan ci naman bijimai ko in sha jinin awakai? 14 Ku miƙa wa Allah hadayar godiya, kuma ku bada alƙawaranku ta rantsuwa ga Mai iko dukka. 15 Ku yi kira gare ni a ranar damuwa; Zan cece ku, kuma zaku girmama ni." 16 Amma ga mugaye Allah yace, "Me zaku yi da furtawar farillaina, har da zaku ɗauki alƙawarina a bakinku, 17 tunda kun ƙi umarnina kuma kun jefar da maganganuna? 18 Sa'ad da kuka ga barawo, kuka yarda da shi; kuna ayyuka tare da waɗanda ke yin zina. 19 Kun bada bakinku ga mugunta, kuma harshenku na fitar da ruɗu. 20 Ka zauna kana magana gãba da ɗan'uwanka; ka na saran ɗan mahaifiyarka. 21 Kun aikata waɗannan abubuwan, amma na yi shiru, sai kuka zata cewa Ni kamarku nake. Amma zan kwaɓe ku in kawo a gaban idanuwanku, dukkan abubuwan da kuka yi. 22 Ku lura da wannan da kulawa, ku da kuka mance da Allah, ko kuma zan yayyaga ku gutsu-gutsu, kuma babu wanda zai zo ya taimake ku! 23 Wanda ya ke miƙa hadayar godiya yana yabona ne, kuma ga duk wanda ya ke rayuwarsa a hanyar da ta dace zan nuna masa ceton Allah."
1 Have mercy on me, God,
because of your covenant faithfulness;
for the sake of the multitude of your merciful actions,
blot out my transgressions.
2 Wash me thoroughly from my iniquity
and cleanse me from my sin.
3 For I know my transgressions,
and my sin is always before me.
4 Against you, you only, I have sinned
and done what is evil in your sight;
you are justified when you speak;
you are blameless when you judge.
5 See, I was born in iniquity;
as soon as my mother conceived me, I was in sin.
6 See, you desire trustworthiness in my inner self;
and you teach me wisdom in the secret place within.
7 Purify me with hyssop, and I will be clean;
wash me, and I will be whiter than snow.
8 Make me hear joy and gladness
so that the bones that you have broken may rejoice.
9 Hide your face from my sins
and blot out all my iniquities.
10 Create in me a clean heart, God,
and renew a right spirit within me.
11 Do not drive me away from your presence,
and do not take your holy Spirit from me.
12 Restore to me the joy of your salvation,
and sustain me with a willing spirit.
13 Then will I teach transgressors your ways,
and sinners will be converted to you.
14 Forgive me for shedding blood,
God of my salvation,
and I will shout for the joy of your righteousness.
15 Lord, open my lips,
and my mouth will express your praise.
16 For you do not delight in sacrifice, or I would give it;
you have no pleasure in burnt offerings.
17 The sacrifices of God are a broken spirit.
You, God, will not despise a broken and a contrite heart.
18 Do good in your good pleasure to Zion;
rebuild the walls of Jerusalem.
19 Then will you delight in the sacrifices of righteousness,
in burnt offerings and whole burnt offerings;
then our people will offer bulls on your altar.
1 Ka yi mani jinƙai, Allah, saboda amintaccen alƙawarinka; saboda kana yin ayyukan jinƙai masu yawa, ka tsige kurakuraina. 2 Ka wanke ni sosai daga zunubina ka share mani laifina. 3 Gama na san kurakuraina, kuma laifina yana gabana kullum. 4 Gãba da kai, kai kaɗai, na yiwa laifi kuma na yi abin mugunta a fuskarka; ka yi dai-dai sa'ad da kayi magana; baka yi kuskure ba sa'ad da ka shar'anta. 5 Duba, An haife ni a cikin zunubi; tun daga cikin mahaifiyata, ina cikin zunubi. 6 Duba, kana so in yi marmarin aminci cikin zuciyata; a cikin zuciyata zaka sa in san hikima. 7 Ka tsarkake ni da abin tsarkakewa, zan kuwa tsarkaka; ka wanke ni, zan kuwa fi auduga fari. 8 Ka sa in ji daɗin rai da murna saboda ƙasusuwan da ka karya suyi farinciki. 9 Ka ɓoye fuskarka daga laifofina ka hure dukkan zunubaina. 10 Ka sa in so yi maka biyayya kullum, Allah, ka sa kullum in so yin abin da ke dai-dai. 11 Kada ka kore ni daga gare ka, kar kuma ka ɗauke mani Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni. 12 Ka maido mani da farincikin cetonka, ka riƙe ni da ruhun yin biyayya. 13 Sa'an nan zan koya wa masu zunubi hanyoyinka, masu laifi kuma zasu komo gare ka 14 Ka gafarce ni domin zub da jini, Allahn cetona, sai in yi sowa domin farincikin ayyukan adalcinka. 15 Ubangiji, ka buɗe leɓunana, sai bakina ya furta yabonka. 16 Gama baka murna da sadaka, da zan bada ita; Baka jin daɗin baye-bayen ƙonawa. 17 Hadayu na Allah sune karyayyen ruhu. Kai, Allah, baza ka ƙi zuciya mai tuba da kuma tawali'u ba. 18 Kayi nagarta cikin managarcin jin daɗinka ga Sihiyona; ka sake gina garun Yerusalem. 19 Sa'an nan zaka yi murna da sadakokin ayyukan aɗalci da baye-bayen ƙonawa da ainihin baye-yen ƙonawa; sa'an nan mutanenmu zasu miƙa bijimai a bagadinka.
1 Why are you proud of making trouble, you mighty man?
The covenant faithfulness of God comes every day.
2 Your tongue plans destruction
like a sharp razor, working deceitfully.
3 You love evil more than good
and lying rather than speaking righteousness. Selah
4 You love all words that devour others,
you deceitful tongue.
5 God will surely destroy you forever;
he will take you up and pluck you out of your tent
and root you out of the land of the living. Selah
6 The righteous will also see it and fear;
they will laugh at him and say,
7 "See, this is a man who did not make God his refuge,
but he trusted in the abundance of his wealth,
and he was strong when he destroyed others."
8 But as for me, I am like a green olive tree in the house of God;
I will trust in the covenant faithfulness of God forever and ever.
9 I will give you thanks forever for what you have done.
I will wait for your name, because it is good,
in the presence of your faithful ones.
1 Meyasa kuke taƙama da tada fitina, ku manyan mutane? Alƙawarin Allah mai aminci yana zuwa kullum. 2 Harshenku yana shirya hallakarwa kamar reza mai kaifi, kuna aikata yaudara. 3 Kuna ƙaunar mugunta fiye da nagarta ƙarya kuma fiye da maganar adalci. Selah 4 Ka na ƙaunar maganar da zata hallaka waɗansu, kai harshe mai yaudara. 5 Haka Allah zai hallaka ka har abada, zai ɗauke ka daga rumfarka ya tumɓuke ka daga ƙasar masu rai. Selah. 6 Masu adalci zasu gani su ji tsoro; su yi masa dariya su ce, 7 "Ku dubi mutumin da bai mayar da Allah wurin fakewarsa ba, amma ya dogara ga dukiya da yawa, kuma yana da ƙarfi sa'ad da ya hallaka waɗansu." 8 Amma ni, ina kama da itacen inabi mai sheƙi a cikin gidan Allah; zan dogara ga alƙawarin Allah mai aminci har abada. 9 Zan yi godiya gare ka har abada saboda abin da kayi. Zan jira ga sunanka, saboda yana da kyau a cikin taron jama'arka masu tsoron ka.
1 A fool says in his heart,
"There is no God."
They are corrupt and have done abominable iniquity;
there is no one who does good.
2 God looks down from heaven
on the children of mankind
to see if there are any who understand,
who seek after him.
3 They have all turned away. Together they have become corrupt.
There is not one who does good,
not even one.
4 Do those who behave wickedly have no understanding—
those who devour my people as if they were eating bread
and they do not call on God?
5 There they are, in great fear,
where there was nothing to cause them to be afraid;
for God will scatter the bones of those who encamp against you;
you put them to shame,
for God has rejected them.
6 Oh, that the salvation of Israel would come from Zion!
When God brings back his people from the captivity,
then Jacob will rejoice and Israel will be glad!
1 Wawa a zuciyarsa yace, "Babu wani Allah." Dukkan su sun gurɓace sun yi aikin mugunta; babu ko ɗaya dake aikata abin kirki. 2 Allah ya dubo 'yan Adam daga sama, ya gani ko akwai wani mai fahimta, wanda ke neman sa. 3 Dukkan su sun fanɗare. Gabaɗayan su sun gurɓace. Ba wani mai aikata abin kirki, babu ko guda ɗaya. 4 Waɗanda ke aikata mugunta basu da fahimta ne--waɗanda ke cin naman mutanena kamar suna cin gurasa kuma ba su kira ga Allah ba? 5 Suna cikin tsoro mai yawa ko da ya ke ba wani abin tsoratarwa; gama Allah zai tarwatsa duk wanda ya yi maku kwanto; irin waɗannan mutane zasu sha kunya gama Allah ya ƙi su. 6 Oh, dama ceton Isra'ila ya zo daga Sihiyona! Sa'ad da Allah ya dawo da mutanensa daga bauta, Yakubu zai yi farinciki, Isra'ila kuma zai yi murna!
1 Save me, God, by your name,
and judge me in your might.
2 Hear my prayer, God;
give ear to the words of my mouth.
3 For strangers have risen up against me,
and ruthless men have sought after my life;
they have not set God before them. Selah
4 See, God is my helper;
the Lord is the one who upholds me.
5 He will repay my enemies with evil;
in your faithfulness, destroy them!
6 I will sacrifice to you with a freewill offering;
I will give thanks to your name, Yahweh, for it is good.
7 For he has rescued me from every trouble;
my eye has looked in triumph on my enemies.
1 Ka cece ni ya Allah, ta wurin sunanka, ka yi mani shari'a cikin ƙarfin ikonka. 2 Allah, ka ji addu'ata, ka saurari kalmomin bakina. 3 Gama bãƙi sun afko mani, lalatattun mutane na neman raina, basu sa Allah a gabansu ba. Selah. 4 Duba, Allah shi ne mai taimako na, Ubangiji shi ne mai tallafa ta. 5 Zai saka wa maƙiyana da mugunta; cikin amincinka, ka hallaka su! 6 Zan baka hadaya ta yardar rai, zan yi godiya ga sunanka, Yahweh gama haka na da kyau. 7 Gama ya kuɓutar dani daga kowacce damuwa; idona na duban nasara a kan maƙiyana.
1 Give ear to my prayer, God;
and do not hide yourself from my plea.
2 Pay attention to me and answer me;
I am restless in my troubles
3 because of the voice of my enemies,
because of the oppression of the wicked;
for they bring trouble on me,
they are hostile to me with wickedness and anger.
4 My heart trembles within me,
and the terrors of death have fallen on me.
5 Fear and trembling have come on me,
and horror has overwhelmed me.
6 I said, "Oh, if only I had wings like a dove!
Then would I fly away and be at rest.
7 See, then I would wander far away;
I would stay in the wilderness. Selah
8 I would hurry to a shelter
from the stormy wind and tempest."
9 Destroy, Lord, and divide their tongue;
for I see violence and strife in the city.
10 Day and night they go about on its walls;
wickedness and trouble are in the middle of it.
11 Wickedness is in the middle of it;
oppression and deceit do not leave its streets.
12 For it was not an enemy who rebuked me,
then I could have borne it;
neither was it he who hated me who raised himself up against me,
then I would have hidden myself from him.
13 But it was you, a man equal to myself,
my companion and my close friend.
14 We had sweet fellowship together;
we walked in the house of God with the throng.
15 Let death come deceitfully on them;
let them go down alive to Sheol,
for wickedness is where they live, right among them.
16 As for me, I will call on God,
and Yahweh will save me.
17 In the evening, morning, and at noonday I complain and moan;
he will hear my voice.
18 He will safely rescue my life from the battle that was against me,
for those who fought against me were many.
19 God, the one who rules from eternity,
will hear them and humiliate them. Selah
They never change,
and they do not fear God.
20 My friend has raised his hands against those who were at peace with him;
he has not respected the covenant that he had.
21 His mouth was smooth as butter,
but his heart was hostile;
his words were softer than oil,
yet they were actually drawn swords.
22 Place your burdens on Yahweh,
and he will sustain you;
he will never allow a righteous person to totter.
23 But you, God, will bring the wicked down into the pit of destruction;
men of bloodshed and deceit will not live even half as long as others,
but I will trust in you.
1 Allah, ka ji addu'ata, kada ka ɓoye kanka daga roƙona. 2 Ka saurare ni ka amsa mani, gama bani da hutu cikin wahaluna, 3 saboda muryar maƙiyana, saboda matsin masu mugunta, gama suna tsananta mani cikin fushi. 4 Zuciyata tana kiɗima a cikina, tsoron mutuwa ya faɗo kaina. 5 Firgita da razana sun zo kaina, kuma fargaba ya sha kaina. 6 Na ce, "Oh, dãma ina da fukafukai kamar kurciya! Da na tashi in je in huta. 7 Da zan tafi can nesa in zauna a cikin jeji. Selah 8 Da zan yi hanzari in sami mafaka daga hadari mai iska da guguwa. 9 Ka haɗiye su, Ubangiji, kasa ruɗami cikin harsunansu! Gama na ga ta'addanci da hargitsi a cikin birnin. 10 Suna ta yawo a kan ganuwarsa dare da rana. Mugunta da lalata suna cikin tsakiyarsa. 11 Aikin mugunta na cikin tsakiyarsu; Tsanani da zamba ba su bar hanyoyinsu ba. 12 Gama da maƙiyi ne ke tsauta mani, da na iya jurewa; ba kuma wanda ya ke gaba dani ne ya tada kansa gaba dani ba, da na ɓoye kaina daga wurin sa. 13 Amma kai ne mutum kamar ni, abokina, da aminina kuma. 14 Mun yi zumunci mai kyau tare, mun je gidan Yahweh tare da ƙarfafa. 15 Bari mutuwa ta afko masu, bara su gangara lahira, gama mugunta ce kaɗai rayuwarsu, haka suke. 16 Ni kuwa zan kira ga Allah, Yahweh zai cece ni. 17 Ko da yamma ko da rana ko da safe, idan na yi ƙara da nishi zai ji muryata. 18 Zai kuɓutar da raina daga masu kawo mani hari, gama waɗanda ke faɗa dani suna da yawa. 19 Yahweh, wanda ya ke mulki tun daga farko, zai ji su ya ƙasƙantar dasu. Ba zasu taɓa canzawa ba, kuma ba sa tsoron Yahweh. 20 Abokina ya tada hannuwansa gaba da waɗanda ke zaman salama dani. Bai cika alƙawarin da ya yi ba. 21 Bakinsa yana da taushi kamar mai, amma zuciyarsa tana da hasala; kalmominsa suna da taushi kamar mai, amma a gaskiya takubba ne zararru. 22 Ka ɗora wa Yahweh matsalolinka, shi zai riƙe ka, ba zai bari adalai su lalace ba. 23 Amma kai Allah, za ka kawo miyagu cikin ramin hallakarwa. Masu shan jini da mayaudaran mutane ba za su rayu koda kamar na rabin sauran mutane ba, amma zan dogara gare ka.
1 Be merciful to me, God,
for men are attacking me!
All the day long those who fight me oppress me.
2 My enemies trample me all day long;
for there are many who arrogantly fight against me.
3 When I am afraid,
I will put my trust in you.
4 In God, whose word I praise—
in God I have put my trust; I will not be afraid;
what can mere man do to me?
5 All the day long they twist my words;
all their thoughts are against me for evil.
6 They gather themselves together, they hide themselves,
and they mark my steps,
just as they have waited for my life.
7 Do not let them escape doing iniquity.
Bring down the peoples in your anger, God.
8 You number my wanderings
and put my tears into your bottle;
are they not in your book?
9 Then my enemies will turn back on the day that I call to you;
this I know, that God is for me.
10 In God—whose word I praise,
in Yahweh—whose word I praise,
11 in God I trust,
I will not be afraid.
What can anyone do to me?
12 The duty to fulfill my vows to you is on me, God;
I will give thank offerings to you.
13 For you have rescued my life from death;
you have kept my feet from stumbling,
so that I may walk before God
in the light of the living.
1 Ka ji ƙaina ya Allah, gama mutane na kawo mani hari! Dukkan yini suna tsananta ɓatancin da suke yi mani. 2 Maƙiyana na musguna mani dukkan yini, gama waɗanda ke yin faɗa dani cikin wauta suna da yawa. 3 Sa'anda na ji tsoro, zan dogara gare ka. 4 Ina jin daɗin maganar Allah, ga Allah zan dogara; ba zan ji tsoro ba; me mutum kawai zai iya yi ma ni? 5 Juya maganata suke yi dukkan yini, dukkan tunaninsu a kaina na mugunta ne. 6 Sun tattara kansu, sun yi kwanto, suna bin sawuna, suna neman raina. 7 Kada ka bari su dena yin mugunta. Ya Allah, ka kayar da su a cikin fushinka. 8 Ka lissafa yawace-yawacena ka kuma sa hawayena cikin kwalba; ko ba a cikin littafinka suke ba? 9 Sa'ad da na kira ka, maƙiyana zasu koma da baya, abin da na sani kenan, Allah yana tare da ni. 10 A cikin Allah --wanda maganarsa nake yabo, a cikin Yahweh-- 11 a cikin Allah na dogara, bazan ji tsoro ba. Me wani zai iya yi mani? 12 Aikina shi ne in cika wa'adina gare ka, Yahweh. Zan miƙa baye-baye na godiya a gare ka. 13 Gama ka kuɓutar da raina daga mutuwa, ka tsare ƙafafuna daga faɗuwa, domin in yi tafiya a gaban Allah a cikin masu rai.
1 Be merciful to me, God, be merciful to me,
for I take refuge in you until these troubles are over.
I stay under your wings for protection
until this destruction is over.
2 I will cry to God Most High,
to God, who does all things for me.
3 He will send help from heaven and save me,
he rebukes those who hotly pursue me. Selah
God will send me his steadfast love and his faithfulness.
4 My life is among lions;
I am among those who are ready to devour me.
I am among people whose teeth are spears and arrows,
and whose tongues are sharp swords.
5 Be exalted, God, above the heavens;
let your glory be above all the earth.
6 They spread out a net for my feet;
I was bowed down.
They dug a pit in front of me.
They themselves have fallen into the middle of it! Selah
7 My heart is fixed, God, my heart is fixed;
I will sing, yes, I will sing praises.
8 Wake up, my glory!
Wake up, lute and harp!
I will wake up the dawn!
9 I will give thanks to you, Lord, among the peoples;
I will sing praises to you among the nations.
10 For great is your unfailing love, reaching to the heavens;
and your faithfulness to the clouds.
11 Be exalted, God, above the heavens;
may your glory be exalted over all the earth.
1 Ka yi mani jinƙai, Yahweh, ka yi mani jinƙai, gama na fake wurin ka har sai waɗannan wahalu sun wuce. Na tsaya a ƙarƙashin inuwar fukafukanka har sai wannan hallaka ta ƙare. 2 Zan yi kuka ga Allah Maɗaukaki, ga Allah, wanda ya ke yi mani komai. 3 Zai aiko da taimako daga sama ya cece ni, yana jin haushin waɗanda ke ƙuje ni. Allah zai aiko mani da jinƙansa da amincinsa. 4 Raina yana cikin zakuna, ina cikin waɗanda suke a shirye su cinye ni. Ina cikin mutanen da haƙoransu mãsu ne da kibau, haƙoransu kuma kamar takubba masu kaifi. 5 Ya Yahweh, ka ɗaukaka a bisa sammai, bari ɗaukakarka ta zama a bisa duniya. 6 Sun baza taru saboda ƙafafuna; Na shiga cikin ƙunci. Sun gina rami a gabana. Amma su da kansu ne suka faɗa a cikin tsakiyarsa! Selah 7 Zuciyata ta kafu, Allah, zuciyata a kafe take; Zan raira, I, zan raira yabbai. 8 Tashi, ke zuciyata mai daraja, tashi, ke sarewa da molo, nima tun da asuba zan tashi. 9 A cikin jama'a zan yi maka godiya, ya Ubangiji; zan raira yabo gare ka a cikin al'ummai. 10 Gama ƙaunarka tana da girma ƙwarai, ta kai har sama, amincika kuma ya kai gizagizai. 11 Ka ɗaukaka ya Allah, sama da sammai, darajarka ta ɗaukaka bisa dukkan duniya.
1 Do you rulers speak righteousness?
Do you judge uprightly, you people?
2 No, you commit wickedness in your heart;
you distribute violence throughout the land with your hands.
3 The wicked go astray even when they are in the womb;
they go astray from birth, speaking lies.
4 Their poison is like a snake's poison;
they are like a deaf asp that stops up its ears,
5 that pays no attention to the voice of charmers,
no matter how skillful they are.
6 Shatter their teeth in their mouths, God;
break out the great teeth of the young lions, Yahweh.
7 Let them melt away as water that runs off;
when they shoot their arrows, let them be as though they had no points.
8 Let them be like a snail that melts and passes away,
like the untimely born child of a woman that never sees the sunlight.
9 Before your pots can feel the thorn's burning heat,
he will take them away with a whirlwind,
the green thorns and the burning thorns alike.
10 The righteous will rejoice when he sees God's vengeance;
he will wash his feet in the blood of the wicked,
11 so that men will say,
"Truly, there is a reward for the righteous person;
truly there is a God who judges the earth."
1 Ku shugabanni kuna faɗin gaskiya? Ku jama'a kuna yin shari'ar gaskiya? 2 Babu, kun yi aikin mugunta cikin zuciyarku; kun baza tashin hankali da hannuwanku a cikin ƙasar dukka. 3 Tun daga cikin ciki, masu mugunta ke fanɗarewa, tun daga haihuwarsu suke ratsewa, suna faɗin ƙarya. 4 Dafinsu kamar dafin maciji ya ke, suna kama da kurmar ƙasa wadda take toshe kunnuwanta, 5 wadda bata jin muryar masu layu, komai gwanintarsu. 6 Ka karairaya haƙoransu a cikin bakunansu, ya Allah; ka ciccire manyan haƙoran 'yan zakuna, ya Yahweh. 7 Bari su narke kamar ruwan dake gangarewa; idan suka harba kibansu, bari su zama kamar basu yi saiti ba. 8 Bari su zama kamar dodon koɗi wanda ke narkewa ya lalace, kamar jaririn da mace ta haifa kafin lokacinsa yayi wanda bai taɓa ganin hasken rana ba. 9 Kafin tukunyarka ta ji zafin wuta, zai kwashe su da guguwa, da ɗanye da wanda a ke ƙonawa dukka. 10 Mai adalci zai yi farinciki sa'ad da ya ga ramako daga Allah, zai wanke ƙafafunsa da jinin masu mugunta, 11 domin mutane su ce, "Gaskiya ne akwai lada ga mutum mai adalci, gaskiya ne akwai Allah wanda ke shar'anta duniya.
1 Rescue me from my enemies, my God;
set me on high away from those who rise up against me.
2 Keep me safe from those who behave wickedly,
and save me from men of bloodshed.
3 For, see, they wait in ambush to take my life.
The powerful men gather themselves together against me,
but not because of my transgression or my sin, Yahweh.
4 For no guilt of mine they prepare to run at me;
awake and help me and see.
5 You, Yahweh God of hosts,
the God of Israel,
arise and punish all the nations;
do not be merciful to any wicked transgressors. Selah
6 They return at evening, they howl like dogs
and go around the city.
7 See, they belch out with their mouths;
swords are in their lips,
for they say, "Who hears us?"
8 But you, Yahweh, laugh at them;
you mock at all the nations.
9 God, my strength, I will pay attention to you;
you are my high tower.
10 My God will meet me with his covenant faithfulness;
God will let me see my desire on my enemies.
11 Do not kill them,
or my people will forget.
Scatter them by your power and make them fall,
Lord our shield.
12 For the sins of their mouths and the words of their lips,
let them be captured in their pride,
and for the curses and lies that they express.
13 Consume them in wrath,
consume them so that they will be no more;
let them know that God rules in Jacob
and to the ends of the earth. Selah
14 At evening they return,
howling like dogs going around the city.
15 They wander about looking for food
and they growl like a dog if they are not satisfied.
16 But I will sing about your strength,
and in the morning I will praise your steadfast love!
For you have been my high tower
and a refuge in the day of my distress.
17 To you, my strength, I will sing praises;
for God is my high tower, the God of covenant faithfulness.
1 Ka kuɓutar dani daga maƙiyana, ya Allahna; ka ɗora ni can sama nesa daga waɗanda suke taso mani. 2 Ka tsare ni daga waɗanda suke aikata mugunta, ka cece ni daga mutane waɗanda suke zubar da jini. 3 Gama, duba, sun yi kwanto domin su ɗauki raina. Manya manyan masu aika mugunta sun tattara kansu gãba dani, amma ba saboda nayi kuskure ko zunubi ba, Yahweh. 4 Sun shirya domin su tattake ni ba tare da laifina ba, duba, tashi ka taimake ni. 5 Kai Yahweh, Allah Mai Runduna, Allah na Isra'ila, tashi ka hori dukkan al'ummai. Kada ka ji tausan wani mai laifin aika mugunta ko ɗaya. 6 Sukan dawo da yamma, su zagaya birnin suna haushi kamar karnuka. 7 Duba suna yin gyatsa da bakunansu, takubba suna kan leɓunansu, suna cewa, "Wane ne ya ke sauraren mu?" 8 Amma kai, Yahweh, kana yi masu dariya, dukkan al'ummai ba a bakin komai suke a gare ka ba. 9 Allah, ƙarfina, zan kasa kunne gare ka, kaine hasumiyata mai tsawo. 10 Allahna zai same ni da alƙawarin amincinsa, Yahweh, zai biya muradina a kan maƙiyana. 11 Kada ka kashe su domin kada jama'ata su mance. Yahweh, garkuwarmu, ka warwatsa su, ka sa su faɗi. 12 Saboda kalmomin bakinsa, da maganar leɓunansu, ka bari a kwashe su cikin girman kansu, kuma saboda la'ana da ƙarairayin da suka bayyana. 13 Ka hallaka su cikin hasalarka, ka hallaka su domin kada su ƙara kasancewa. Bari su sani, Allah ne ke mulki cikin Yakubu kuma har iyakar duniya. Selah 14 Sukan dawo da yamma, su zagaya birnin suna haushi kamar karnuka. 15 Sukan yi yawo suna neman abinci, sukan yi gurnani idan ba su ƙoshi ba. 16 Amma zan yi rairawa game da ƙarfinka, da safe kuma zan yi rairawa saboda ƙaunarka madawwamiya! Gama ka zama hasumiyata mai tsawo, mafaka a lokacin dani ke cikin matsala. 17 A gare ka ƙarfina zan raira yabo, gama Yahweh ne hasumiyata mai tsawo, Allah mai amincin alƙawari.
1 God, you have rejected us; you have broken through our defenses;
you have been angry; restore us again.
2 You have made the land tremble; you have torn it apart;
heal its cracks, for it is shaking.
3 You have made your people see difficult things;
you have made us drink the wine of staggering.
4 For those who honor you,
you have set up a banner
to be displayed against those who carry the bow. Selah
5 So that those you love may be rescued,
rescue us with your right hand and answer me.
6 God has spoken in his holiness, "I will rejoice;
I will divide Shechem
and apportion out the Valley of Sukkoth.
7 Gilead is mine, and Manasseh is mine;
Ephraim also is my helmet;
Judah is my scepter.
8 Moab is my washbasin;
over Edom I will throw my sandal;
I will shout in triumph because of Philistia."
9 Who will bring me into the strong city?
Who will lead me to Edom?
10 But you, God, have you not rejected us?
You do not go into battle with our army.
11 Give us help against the enemy,
for man's help is futile.
12 We will triumph with God's help;
he will trample down our enemies.
1 Yahweh, ka yashe mu, ka kutsa cikin matsararmu, ka yi fushi, ka dawo da mu. 2 Kasa ƙasar ta girgiza, ka ɓarke ta; tana girgiza, ka warkar da ɓarakarta. 3 Kasa mutanenka su ga abubuwa masu wuya, kasa mun sha ruwan inabin tangaɗi. 4 Saboda waɗanda ke darjantaka, kasa an tada tuta gãba da masu ɗaukar baka. 5 Saboda waɗanda kake ƙauna su kuɓuta, ka amsa mani ka kuɓutar da mu da hannun damanka. 6 Allah ya yi magana cikin tsarkinsa, "Zan yi farinciki, zan raba Shekem, zan karkasa Kwarin Sukot. 7 Giliyad tawa ce Manasse ma tawa ce, Ifraim kuma hular kwanona ce, Yahuda kuma sandar girmana ce. 8 Mowab bangajin wankina ne, zan ajiye takalmina a kan Idom, zan yi sowa ta murna saboda Filistiya." 9 Wa zai kawo ni birni mai ƙarfi? Wa zai kai ni Idom? 10 Amma kai Yahweh, ba ka yashe mu ba? Gama ba ka tafi yaƙi tare da sojojinmu ba. 11 Ka taimake mu gãba da maƙiyanmu gama taimakon mutum banza ne. 12 Da taimakon Allah za mu yi nasara; shi zai tattake maƙiyanmu.
1 Hear my cry, God;
attend to my prayer.
2 From the ends of the earth will I call to you when my heart is faint;
lead me to the rock that is higher than I.
3 For you have been a refuge for me,
a strong tower from the enemy.
4 Let me live in your tabernacle forever!
Let me take refuge under the shelter of your wings. Selah
5 For you, God, have heard my vows,
you have given me the inheritance of those who honor your name.
6 You will prolong the king's life;
his years will be like many generations.
7 He will reign before God forever;
appoint your steadfast love and faithfulness to protect him.
8 I will sing praise to your name forever
so that I may perform my vows every day. 2
1 Ka ji kukana Yahweh, ka amsa addu'ata. 2 Daga iyakar duniya zan kira gare ka lokacin da zuciyata ta ruɗe, ka kai ni wurin dutsen da ya fi ni tsawo. 3 Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi daga maƙiyana. 4 Ka bar ni in zauna a shirayinka har abada! Ka bar ni in ɓoye cikin inuwar fukafukanka. Selah 5 Gama kai Allah, ka ji wa'adina, ka bani gãdon waɗanda suke darjanta sunanka. 6 Za ka sa ran sarki ya yi tsawo, shekarunsa kuma kamar tsararraki da yawa. 7 Zai kasance a gaban Yahweh har abada. 8 Zan raira yabo ga sunanka har abada, domin in cika wa'dina gare ka kowacce rana.
1 I wait in silence for God alone;
my salvation comes from him.
2 He alone is my rock and my salvation;
he is my high tower;
I will not be greatly moved.
3 How long, all of you, will you attack a man,
that you may murder him,
like a leaning wall or a shaky fence?
4 They consult with him
only to bring him down from his honorable position;
they love to tell lies;
they bless him with their mouths,
but in their hearts they curse him. Selah
5 I wait in silence for God alone;
for my hope is set on him.
6 He alone is my rock and my salvation;
he is my high tower; I will not be moved.
7 With God is my salvation and my glory;
the rock of my strength and my refuge are in God.
8 Trust in him at all times, you people;
pour out your heart before him;
God is a refuge for us. Selah
9 Surely men of low standing are vanity,
and men of high standing are a lie;
they will weigh lightly in the scales;
weighed together, they are lighter than nothing.
10 Do not trust in oppression or robbery;
and do not hope uselessly in riches,
for they will bear no fruit;
do not fix your heart on them.
11 God has spoken once,
twice have I heard this:
power belongs to God.
12 Also to you, Lord, belongs covenant faithfulness,
for you pay back every person for what he has done.
1 Na yi shiru a gaban Yahweh kaɗai, daga wurin sa cetona ya ke zuwa. 2 Shi kaɗai ne cetona, shi ne hasumiyata mai tsawo, ba zan girgiza ba sosai. 3 Har yaushe ku dukka, zaku kai hari ga mutum ɗaya? Domin ku rufe shi kamar bangon da a ke jigina da shi, shinge mai rawa? 4 Suna shawara da shi ne domin su ture shi daga matsayinsa mai daraja kaɗai; su na ƙaunar faɗin ƙarya, suna sa masa albarka da bakinsu, amma cikin zuciyarsu suna la'antar sa. Selah 5 Ga Allah kaɗai nake saurare, gama shi ne begena. 6 Shi kaɗai ne dutsena da cetona, shi ne hasumiyata mai tsawo ba zan jijjigu ba. 7 Allah ne cetona da ɗaukakata, dutsen ƙarfina da mafakata a cikin Allah suke. 8 Ku dogara gare shi kowanne lokaci, ku mutane, ku kafa zuciyarku a gaban sa, Allah shi ne mafakarmu. Selah 9 Ba shakka mutanen da basu da matsayi ba komai bane, waɗanda ke da matsayin kuma ƙarya ne. Idan a ka auna su a ma'auni ba su da nauyi, inda za a haɗa su a auna ba su da nauyin komai. 10 Kada ku dogara ga aikin zalunci ko ƙwace, kada ku sa begenku ga dukiyar wofi, gama ba su da amfanin komai, kada ku sa zuciya gare su. 11 Allah ya yi magana sau ɗaya, sau biyu kuwa na ji wannan: iko na Allah ne. 12 Kuma Ubangiji, a gare ka alƙawarin gaskiya yake. Gama kana ramawa kowanne mutum bisa ga abin da ya yi.
1 God, you are my God!
I earnestly search for you,
my soul thirsts for you,
and my flesh longs for you,
in a dry and weary land
where there is no water.
2 So I have looked on you in the sanctuary,
to see your power and your glory.
3 Because your covenant faithfulness is better than life,
my lips will praise you.
4 So I will bless you while I live;
I will lift up my hands in your name.
5 It will be as if I ate a meal of marrow and fatness;
with joyful lips my mouth will praise you,
6 when I think about you on my bed
and meditate on you in the night watches.
7 For you have been my help,
and in the shadow of your wings I rejoice.
8 I cling to you;
your right hand supports me.
9 But those who seek to destroy my life
will go down into the lowest parts of the earth;
10 they will be given over to those whose hands use the sword,
and they will become food for the jackals.
11 But the king will rejoice in God;
everyone who swears by him will be proud of him,
but the mouth of those who speak lies will be stopped up.
1 Allah, kai ne Allahna, da gaske raina ya ke neman ka, raina yana ƙishin ka, jikina ya ƙagara ya gan ka, a cikin ƙasa da turɓaya in da babu ruwa. 2 Na dubo zuwa gare ka a cikin mutane masu tsarki domin in ga ikonka da ɗaukakarka. 3 Saboda alƙawarin ka mai aminci yafi rai, leɓunana zasu yabe ka. 4 Zan albarkace ka sa'ad da nake da rai, a cikin sunanka zan tada hannuwana. 5 Zai zama kamar na ci abinci mai ɓargo da kitse, zan yabe ka da leɓuna masu farinciki, 6 sa'ad da ni ke tunaninka a kan gadona, sa'ad da nake nazarin ka a cikin dare. 7 Gama kai ne taimakona, a ƙarƙashin inuwar fukafukanka nake yin farinciki. 8 Na manne maka hannun damanka yana tallafa ta. 9 Amma waɗanda ke nema su hallaka raina, zasu faɗa cikin wuri mai zurfi na duniya; 10 za a bashe su ga hannun masu aiki da takobi, zasu zama abicin diloli. 11 Amma sarki zai yi farinciki cikin Allah, dukkan wanda ya rantse da shi, zai yi fahariya da shi kuma, amma bakin masu faɗin ƙarya za a kwaɓe shi.
1 Hear my voice, God, listen to my complaint;
preserve my life from fear of my enemies.
2 Hide me from the secret plotting of evildoers,
from the commotion of those who behave wickedly.
3 They have sharpened their tongues like swords;
they have aimed their arrows, bitter words,
4 so that they may shoot from secret places at someone who is innocent;
suddenly they shoot at him and fear nothing.
5 They encourage themselves in an evil plan;
they consult privately together in order to set traps;
they say, "Who will see us?"
6 They invent injustices;
"We have finished," they say, "a careful plan."
The inner thoughts and hearts of man are deep.
7 But God will shoot them;
suddenly they will be wounded with his arrows.
8 They will be made to stumble, since their own tongues are against them;
all who see them will wag their heads.
9 All people will fear
and will declare God's deeds.
They will wisely think about what he has done.
10 The righteous will be glad about Yahweh and will take refuge in him;
all the upright in heart will take pride in him.
1 Ka ji muryata, Allah, ka saurari ƙarata; ka tsare raina daga tsoron maƙiyana. 2 Ka ɓoye ni daga shirin miyagu, daga hargowar masu aika mugunta. 3 Sun wasa harsunansu kamar takubba, sun haro kibansu, wato maganganu masu ɗaci, 4 domin su harbi wanda ba shi da laifi daga wurin da suke ɓoye, nan da nan suka harbe shi ba tare da sun ji tsoro ba. 5 Suna ƙarfafa kansu cikin shirya mugunta, suna shawara a asirce domin su ɗana tarkuna, suna cewa, "Wa zai gan mu?" 6 Suna ƙulla mugunta; "Mun gama" suka ce, "Natsastsen shiri" Tunanin ciki da zuciyar mutum suna da zurfi. 7 Amma Yahweh, zai harbe su, nan da nan kibau zasu ji masu ciwo. 8 Zasu yi tuntuɓe tun da ya ke harshensu yana gãba da su; dukkan waɗanda suka gan su zasu kaɗa kansu. 9 Dukkan mutane zasu ji tsoro su bayyana ayyukan Allah. Cikin hikima zasu yi tunani a kan abin da ya yi. 10 Masu adalci zasu yi murna da Yahweh, zasu sami mafaka a wurinsa. Dukkan waɗanda ke tafiya dai-dai zasu yi fahariya a cikin sa.
1 For you, God in Zion, our praise waits;
our vows will be carried out to you.
2 You who hear prayer,
to you all flesh will come.
3 Iniquities prevail against us;
as for our transgressions, you will forgive them.
4 Blessed is the man whom you choose to bring near to you
so that he may live in your courts.
We will be satisfied with the goodness of your house,
your holy temple.
5 In righteousness you will answer us by doing awesome deeds,
God of our salvation;
you who are hope of all the ends of the earth
and of those who are far across the sea.
6 For it is you who made the mountains firm,
you who are girded with strength.
7 It is you who quiet the roaring of the seas,
the roaring of their waves,
and the commotion of the peoples.
8 Those who live in the uttermost parts of the earth
are afraid of the evidence of your deeds;
you make the east and the west rejoice.
9 You come to help the earth; you water it;
you greatly enrich it;
the river of God is full of water;
you provide mankind grain when you have prepared the earth.
10 You water its furrows abundantly;
you settle down the furrows' ridges;
you make them soft with rain showers;
you bless the sprouts between them.
11 You crown the year with your goodness,
and your wagon tracks overflow with abundance.
12 The pastures in the wilderness drip with dew,
and the hills are girded with joy.
13 The pastures are clothed with flocks;
the valleys also are covered over with grain;
they shout for joy, and they sing.
1 Domin kai Allah a Sihiyona ne, yabonmu; da wa'adodinmu, za a kawo maka su a cikin Sihiyona. 2 Kai da kake jin addu'a, a gare ka dukkan mutane za su zo. 3 Laifofi sun yi mana tsayayya, amma za ka gafarta zunubanmu, za ka kuma gafarta su. 4 Mai albarka ne mutumin daka zaɓa ya zo ya zauna a kusa da kai a cikin harabarka. Za mu gamsu da kyawawan abubuwan dake a gidanka, haikalinka mai tsarki. 5 Cikin adalci za ka amsa mana ka yi abubuwan mamaki, kai Allah na cetonmu, Kai wanda dukkan mutane ke dagara gake ka har da waɗanda ke a can hayin teku. 6 Gama kai ne ka kafa duwatsu suka yi ƙarfi, kai wanda ka yi ɗamara da iko. 7 Kai ne ka kwantar da rurin tekuna da balalloƙansu da hargowar mutane 8 Su waɗanda ke zama a can ƙarshen duniya suna jin tsoron alamun ayyukanka, kasa gabas da yamma suna farinciki. 9 Ka zo domin ka taimaki duniya; ka yi mata banruwa, kasa ta yi arziki, kogin Allah na cike da ruwa; tun da ka hallicci duniya ka tanadawa ɗan Adam hatsi. 10 Ka jiƙe kwarin kunyai a wadace, ka dai-daita kwarin kunyai sosai, kakan sa su yi taushi, kasa albarka a kan yabanyarsu. 11 Ka yi wa shekara dajiyar alherai, sawayen karusanka suka zubo da kitse a kan duniya. 12 Wuraren kiwo a jeji sun jiƙe da raɓa, ka sa tsire--tsire suyi farinciki. 13 Wuraren kiwo sun cika da garkuna, kwarurruka sun cika da hatsi, suna shewa ta farinciki, suna rairawa.
1 Shout out loud to God, all the earth;
2 Sing out the glory of his name;
make his praise glorious.
3 Say to God, "How terrifying are your deeds!
By the greatness of your power
your enemies will submit to you.
4 All the earth will worship you
and will sing to you;
they will sing praises to your name." Selah
5 Come and see the works of God;
he is fearsome in his deeds toward the sons of mankind.
6 He turned the sea into dry land;
they went through the river on foot;
there we rejoiced in him.
7 He rules forever by his might;
his eyes observe the nations;
let not the rebellious exalt themselves. Selah
8 Give blessing to God, you people,
let the sound of his praise be heard.
9 He keeps us among the living,
and he does not permit our feet to slip.
10 For you, God, have tested us;
you have tested us as silver is tested.
11 You brought us into a net;
you laid a heavy burden on our backs.
12 You made people ride over our heads;
we went through fire and water,
but you brought us out into a spacious place.
13 I will come into your house with burnt offerings;
I will pay you my vows
14 which my lips promised
and my mouth spoke when I was in distress.
15 I will offer to you burnt offerings of fat animals
with the sweet aroma of rams;
I will offer bulls and goats. Selah
16 Come and listen, all you who fear God,
and I will declare what he has done for my soul.
17 I cried to him with my mouth,
and he was praised with my tongue.
18 If I had seen wickedness within my heart,
the Lord would not have listened to me.
19 But God has truly heard;
he has paid attention to the voice of my prayer.
20 Blessed be God,
who has not turned away my prayer
or his covenant faithfulness from me.
1 Ku yi sowa ta farinciki ga Yahweh, ku duniya dukka. 2 Ku raira ɗaukakar sunansa, ku sa yabonsa ya zama ɗaukakakke. 3 Ku ce da Allah, "Ayyukanka suna da ban tsoro! Da girman ikonka kasa maƙiyanka su yi ladabi a gabanka. 4 Dukkan duniya zasu bauta maka su raira yabo gare ka, zasu yi rairawa ga sunanka." Selah 5 Ku zo ku ga ayyukan Yahweh, ayyukansa na da ban mamaki ga 'yan Adam. 6 Ya mayar da teku busasshiyar ƙasa; sun bi ta cikin teku da ƙafa; can muka yi farinciki a cikin sa. 7 Da ikonsa ya ke mulki har abada, idanunsa suna lura da al'ummai; kada masu tawaye su ɗaukaka kansu. Selah 8 Ku albarkaci Allah, ku mutane, bari a ji amon yabonsa. 9 Ya bar mu cikin masu rai, bai bari ƙafafunmu suka yi tuntuɓe ba. 10 Gama kai Yahweh ka gwada mu, ka gwada mu kamar yadda a ke gwada azurfa. 11 Ka kawo mu cikin taru, ka ɗora mana kaya mai nauyi a kanmu. 12 Ka bari mutane su tattaka mu, mun shiga cikin wuta da ruwa, amma ka kawo mu cikin wuri mai faɗi. 13 Zan zo cikin gidanka da baiko na ƙonawa, zan cika wa'adodina gare ka, 14 waɗanda leɓunana suka yi alƙawarin su, bakina kuma ya furta, sa'ad da nake cikin wahala. 15 Zan kawo maka baiko na ƙonawa da dabbobi masu ƙiba da ƙamshin raguna; zan miƙa bijjimai da awaki. 16 Ku zo ku saurara, dukkan ku dake tsoron Allah, zan bayyana abin da ya yi domin raina. 17 Na yi kuka gare shi da bakina, harshena kuma ya yabe shi. 18 Idan dana dubi zunubi a cikin zuciyata, da Ubangiji bai saurare ni ba. 19 Amma da gaske Allah ya ji; ya kula da muryar addu'ata. 20 Albarka ta tabbata ga Allah, wanda bai yi watsi da addu'ata ba ko ya ɗauke alƙawarinsa mai aminci daga gare ni ba.
1 May God be merciful to us and bless us
and cause his face to shine on us Selah
2 so that your ways may be known on earth,
your salvation among all nations.
3 Let the peoples praise you, God;
let all the peoples praise you.
4 Oh, let the nations be glad and sing for joy,
for you will judge the peoples with justice
and govern the nations on earth. Selah
5 Let the peoples praise you, God;
let all the peoples praise you.
6 The earth has yielded its produce
and God, our God, has blessed us.
7 God has blessed us,
and all the ends of the earth honor him.
1 Bari Allah ya yi mana jinƙai, yasa fuskarsa ta haskaka wajenmu. Selah 2 domin a san hanyoyinka a duniya, cetonka kuma cikin al'ummai dukka. 3 Bari mutane su yabi Allah, dukkan mutane su yabe ka. 4 Oh, bari al'ummai suyi murna su raira domin farinciki, gama za ka hukunta mutane cikin adalci, ka shugabanci mutanen duniya. Selah 5 Bari mutane su yabe ka Allah, bari dukkan mutane su yabe ka. 6 Ƙasa ta ba da amfaninta kuma Allah, Allahnmu ya albarkace mu. 7 Allah ya albarkace mu kuma dukkan ƙarshen duniya na darjanta shi.
1 Let God arise; let his enemies be scattered;
let those also who hate him flee before him.
2 As smoke is driven away, so drive them away;
as wax melts before the fire,
so let the wicked perish in the presence of God.
3 But let the righteous be glad;
let them rejoice before God;
may they rejoice with gladness.
4 Sing to God! Sing praises to his name!
Praise the one who rides through the plains of the Jordan River valley!
Yah is his name! Rejoice before him! [1]
5 A Father of the fatherless, a judge of the widows,
is God in the holy place where he lives.
6 God puts the lonely into families;
he brings out the prisoners with singing;
but the rebellious live in a parched land.
7 God, when you went out before your people,
when you marched through the wilderness, Selah
8 the earth trembled;
the heavens also dropped rain in God's presence,
in the presence of God when he came to Sinai, in the presence of God, the God of Israel.
9 You, God, sent a plentiful rain;
you strengthened your inheritance when it was weary.
10 Your people lived in it;
You, God, gave from your goodness to the poor.
11 The Lord gave the word,
and those who announced them were a great army.
12 Kings of armies flee, they flee,
and the women waiting at home divide the plunder:
13 the wings of a dove are covered with silver,
its feathers with shining gold.
Yet some of you people lie down among the sheepfolds.
14 The Almighty scattered kings there,
it was as when it snowed on Mount Zalmon.
15 A mighty mountain is the hill country of Bashan;
a high mountain is the hill country of Bashan.
16 Why do you look in envy, you high hill country,
at the mountain which God desires for the place he will live?
Indeed, Yahweh will live in it forever.
17 The chariots of God are twenty thousand,
thousands upon thousands;
the Lord is among them in the holy place, as at Sinai.
18 You have ascended on high;
you have led away captives;
you have received gifts from among men,
even from the rebellious,
so that Yah, God, might live there. [2]
19 Blessed be the Lord, who daily bears our burdens,
the God who is our salvation. Selah
20 Our God is a God who saves;
Yahweh the Lord is the one who is able to rescue us from death.
21 But God will strike through the heads of his enemies,
through the hairy scalps of those who walk in offenses against him.
22 The Lord said, "I will bring my enemies back from Bashan;
I will bring them back from the depths of the sea
23 so that you may crush your enemies, dipping your foot in blood,
and so that the tongues of your dogs may have their share from your enemies."
24 They have seen your processions, God,
the processions of my God, my King, into the holy place.
25 The singers went first, the minstrels followed after,
and in the middle were the unmarried girls playing tambourines.
26 Bless God in the assemblies;
praise Yahweh, you who are from the fountain [3] of Israel.
27 There is Benjamin, the smallest tribe, ruling them,
then the leaders of Judah and their multitudes,
the leaders of Zebulun and the leaders of Naphtali.
28 Your God, Israel, has decreed your strength;
reveal to us your power, God, as you have revealed it in times past.
29 Reveal your power to us from your temple at Jerusalem,
where kings bring tribute to you.
30 Rebuke the wild beasts in the reeds,
against the peoples, that multitude of bulls and calves.
Humiliate them and make them bring you silver;
scatter the peoples who love to wage war.
31 Princes will come out of Egypt;
Cush will hurry to reach out with her hands to God.
32 Sing to God, you kingdoms of the earth. Selah
Sing praises to the Lord,
33 to him who rides on the heaven of heavens, which exist from ancient times;
see, he lifts up his voice with power.
34 Ascribe strength to God;
his majesty is over Israel,
and his strength is in the skies.
35 God, you are fearsome in your holy place;
the God of Israel—he gives strength and power to his people.
Blessed be God.
1 Bari Allah ya tashi, bari maƙiyansa su warwatse, bari kuma waɗanda ke ƙin sa su gudu daga gabansa. 2 Ka kore su kamar yadda hayaƙi ke watsewa, kamar yadda saƙar zuma kan narke a gaban wuta, haka masu mugunta zasu lalace a gaban Allah. 3 Amma bari masu adalci suyi murna, su ɗaukaka a gaban Allah; bari su yi farinciki su kuma ji daɗi. 4 Ku raira ga Allah! Ku raira yabbai ga sunansa! Ku yabe shi wanda ke ratsawa ta filin kwarin Kogin Yodan! Yahweh ne sunansa! Ku yi farinciki a gabansa! 5 Uban marar uba, alƙali saboda gwauraye, shi ne Allah daga wurin zamansa mai tsarki. 6 Allah yakan sa masu kaɗaici cikin iyali, ya kan fito da 'yan kurkuku cikin waƙa, amma 'yan tawaye suna zama a faƙo. 7 Allah idan da kayi tafiya a gaban mutanenka, idan ka bi ta cikin jeji, Selah 8 Ƙasa takan girgiza, sama kan zubo da ruwa a gaban Allah, a gaban Allah sa'ad da ya zo Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra'ila. 9 Kai, Allah, ka aiko da ruwa isasshe, ka ƙarfafa abin gãdonka sa'ad da suka gaji. 10 Mutanenka suka zauna a ciki; kai, Allah, daga cikin alherinka ka bayar ga matalauta. 11 Ubangiji ya bada umarnai, waɗanda suka sanar da su kuwa manyan sojoji ne. 12 Sarakunan sojoji sun gudu, suka gudu, matayen dake zama a gida kuwa suka raba ganima. 13 Kurciyoyi rufe da azurfa, da fukafukan zinariya rawaya. Sa'ad da waɗansu ku mutane kuka tsaya a garkunan tumaki, me ya sa kuka yi haka? 14 Mai iko dukka ya tarwatsa sarakuna a wurin, sai ya zama kamar dusar ƙanƙara a Dutsen Zalmon. 15 Babban dutse shi ne tudun ƙasar Bashan, dutse mai tsawo shi ne tudun ƙasar Bashan. 16 Me yasa ki ke ƙyashi ke ƙasar kan tudu, a kan dutsen da Allah ya zaɓi ya zauna a wurin? Tabbas, Yahweh zai zauna a cikinta har abada. 17 Karusan Allah dubu ashirin ne, dubbai bisa dubbai; Ubangiji na cikinsu a wuri mai tsarki, kamar a Sinai. 18 Ka haye sama, ka kwashi 'yan bauta, ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga waɗanda suka yi faɗa da kai, domin kai Yahweh Allah, ka zauna a can. 19 Albarka ga Ubangiji, wanda kullum ya ke kula da mu, Allah wanda shi ne cetonmu. 20 Allahnmu, Allah ne wanda ke yin ceto. Yahweh, Ubangiji, shi ne kaɗai wanda zai iya kuɓutar da mu daga mutuwa. 21 Amma Allah zai rotsa kan maƙiyansa, ta wurin fatar kai mai gashi ta waɗanda ke tafiya cikin yi masa laifi. 22 Ubangiji yace, "Zan dawo da maƙiyana daga Bashan, zan dawo da su daga cikin zurfin teku 23 domin ka ragargaza maƙiyanka, kana tsoma ƙafarka cikin jini, domin harsunan karnukanka su sami rabo daga cikin maƙiyanka." 24 Sun ga shigowar ka, Allah, shigowar Allahna, Sarkina cikin wuri mai tsarki. 25 Mawaƙa suka fara yin gaba, masu busa na bin baya, a tsakiya kuwa 'yammata na kaɗa molo. 26 Ku albarkaci Allah a cikin taro, ku yabi Yahweh, ku zuriyar Isra'ila na gaskiya. 27 Da fari akwai Benyamin, kabila mafi ƙanƙanta, sai kuma shugabannin Yahuda da jama'arsu, shugabannin Zebulun da shugannin Naftali. 28 Allahnka, ya Isra'ila ya umarta ƙarfinka, ka nuna ikonka, Allah, kamar yadda ka nuna shi a lokacin dã. 29 Ka nuna mana ikonka daga Yerusalem inda sarakuna ke kawo maka kyautai. 30 Yi ruri cikin yaƙi gãba da namomin jejin dake zama cikin iwa, a kan mutane, da bijimai masu yawa da 'yan maruƙa. Kunyatar dasu kasa su kawo maka kyautai, ka tarwatsa mutanen dake ƙaunar yin yaƙi. 31 Sarakuna zasu fito daga Masar; Itofiya zata yi sauri ta kawo hannuwanta ga Allah. 32 Ku raira yabbai ga Allah ku mulkokin duniya; Selah ku raira yabbai ga Yahweh. 33 Gare shi wanda ke sukuwa kan saman sammai, shi wanda ya kasance tun zamanin dã; duba, ya tada muryarsa da iko. 34 Ku furta ƙarfi ga Allah, darajarsa tana kan Isra'ila, ikonsa na cikin sararin sama. 35 Allah, kai abin tsoro ne a cikin wurinka mai tsarki, Allah na Isra'la yana ba da ƙarfi da iko ga mutanensa. Albarka ga Allah.
1 Save me, God;
for the waters have put my life in danger.
2 I sink in deep mire, where there is no place to stand;
I have come into deep waters, where the floods flow over me.
3 I am weary with my crying; my throat is dry;
my eyes fail while I wait for my God.
4 Those who hate me without a cause
are more than the hairs on my head;
those who would cut me off,
being my enemies for wrong reasons, are mighty;
what I did not steal,
I have to give back.
5 God, you know my foolishness,
and my sins are not hidden from you.
6 Let not those who hope in you be put to shame because of me,
Lord Yahweh of hosts;
let not those who seek you be brought to dishonor because of me,
God of Israel.
7 For your sake I have borne rebuke;
shame has covered my face.
8 I have become a stranger to my brothers,
an alien to my mother's children.
9 For the zeal of your house has eaten me up,
and the rebukes of those who rebuke you have fallen on me.
10 When I weep and fast,
I must endure scorn.
11 When I put on sackcloth,
I became a byword to them.
12 Those who sit in the city gate talk about me;
I am a song of drunkards.
13 But as for me, my prayer is to you, Yahweh,
at a time that you will accept;
answer me in the trustworthiness of your salvation.
14 Pull me out of the mire,
and do not let me sink;
let me be taken away from those who hate me
and rescued out of the deep waters.
15 Do not let the floods of water overwhelm me,
neither let the deep swallow me up.
Do not let the pit shut its mouth on me.
16 Answer me, Yahweh, for your covenant faithfulness is good;
because your mercies for me are many, turn to me.
17 Do not hide your face from your servant,
for I am in distress; answer me quickly.
18 Come to me and redeem me.
Because of my enemies, ransom me.
19 You know my rebuke, my shame, and my dishonor;
my adversaries are all before you.
20 Rebuke has broken my heart;
I am full of heaviness;
I looked for someone to take pity, but there was none;
I looked for comforters, but I found none.
21 They gave me poison for my food;
in my thirst they gave me vinegar to drink.
22 Let their table before them become a snare;
when they think they are in safety, let it become a trap.
23 Let their eyes be darkened so that they cannot see;
and always make their loins shake.
24 Pour out your indignation on them,
and let your raging anger overtake them.
25 Let their encampment be a desolation;
let no one live in their tents.
26 For they persecuted the one you struck down.
They repeated the account of the pain of those you have wounded.
27 Accuse them of having committed iniquity after iniquity;
do not let them come into your righteous victory.
28 Let them be blotted out of the Book of Life
and not be written down along with the righteous.
29 But I am poor and in pain;
let your salvation, God, set me up on high.
30 I will praise the name of God with a song
and will exalt him with thanksgiving.
31 That will please Yahweh better than an ox
or a bull that has horns and hooves.
32 The meek have seen it and are glad;
you who seek after God, let your hearts live.
33 For Yahweh hears the needy
and does not despise his prisoners.
34 Let heaven and earth praise him,
the seas and everything that moves in them.
35 For God will save Zion and will rebuild the cities of Judah;
the people will live there and have it as a possession.
36 His servants' descendants will inherit it;
and those who love his name will live there.
1 Ka cece ni Allah, gama ruwaye sun sa raina cikin hatsari. 2 Na nutse cikin laka, mai zurfi inda ba wurin tsayawa; na zo cikin ruwa mai zurfi, rigyawa ta sha kaina. 3 Na gaji da kuka, maƙogwarona ya bushe, idanuna sun dishe sa'ad da nake jiran Allahna. 4 Waɗanda ke ƙi jinina ba dalili sun fi gashin kaina yawa, su waɗanda zasu datse ni saboda dalilan da ba dai-dai ba, suna da ƙarfi, abin da ban sata ba, sai na mayar. 5 Allah, ka san wawancina, zunubaina kuma ba ɓoye suke a gare ka ba. 6 Kada waɗanda ke jiran ka su ji kunya saboda ni, Ubangiji Yahweh Mai Runduna, kada masu neman ka su ƙasƙanta saboda ni, Allah na Isra'ila. 7 Saboda kai na jure da tsautawa; kunya ta rufe fuskata. 8 Na zama bãƙo ga 'ya'uwana, bare kuma ga 'ya'yan mahaifiyata. 9 Gama niyyar zuwa gidanka ta ɗauke hankalina, tsautawar waɗanda ke tsauta maka ta faɗo kaina. 10 Idan na yi kuka na ƙi cin abinci, sai su zage ni. 11 Idan kayan makoki suka zama kayan sawata, sai in zama abin misali gare su. 12 Waɗanda ke zama a ƙofar birni magana suke yi a kaina, mashaya waƙa su ke yi a kaina. 13 Amma ni addu'ata gare ka take, Yahweh, sa'ad da ka ga yayi dai-dai, ka amsa mani cikin aminci cetonka. 14 Ka tsamo ni daga cikin laka, kada ka bari ni nutse; bari a ɗauke ni daga waɗanda ke ƙina, a kuma tsamo ni daga cikin ruwaye masu zurfi. 15 Kada ka bari rigyawa ta sha kai na, kada ka bari zurfi ya haɗiye ni. Kada ka bari rami ya rufe bakinsa a kaina. 16 Ka amsa mani Yahweh, gama alƙawarin amincinka yana da kyau; domin jiye-jiyen ƙanka suna da yawa zuwa gare ni, ka juyo wajena. 17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka, gama ina cikin wahala, ka amsa mani da sauri. 18 Ka zo wuri na ka cece ni, saboda maƙiyana ka fanshe ni. 19 Ka san tsautawar da a ke yi mani, ka san kunyata, ka san ƙasƙancin da nake sha; dukkan magabtana a gabana suke. 20 Tsautawa ta karya zuciyata; cike nake da nauyi; na duba ko wani zai ji tausayi na, amma ban samu ba. 21 Sun ba ni dafi shi ne abincina, cikin ƙishina kuma sai suka ba ni ruwan tsami domin in sha. 22 Bari teburin gabansu ya zama tarko, sa'ad da suke tsammanin suna lafiya bari ya zama tarko a gare su. 23 Bari idanunsu su dishe yadda ba zasu iya gani ba; bari kwankwasonsu su riƙa yin rawa. 24 Ka zuba masu hasalarka, bari zafin fushinka ya yi ƙuna a kan su. 25 Bari wurin zamansu ya zama kufai; kada kowa ya zauna a rumfunansu. 26 Gama sun tsanantawa wanda ka fyaɗe ƙasa. Sun ƙarawa waɗanda suka ji rauni zafin ciwo. 27 Ka zarge su a kan aikata mugunta a kan mugunta; kada ka bari su zo cikin nasararka mai adalci. 28 Bari a shafe su daga cikin lattafin rai, kada a rubutasu tare da tsarkaka. 29 Amma ni matalauci ne mai baƙinciki, bari cetonka; Allah, ya sanya ni can sama. 30 Zan yabi sunan Allah da waƙa, zan ɗaukaka shi da shaidar godiya. 31 Wannan zai gamshi Yahweh fiye da sã da bijimi mai ƙahonni da kofatai. 32 Masu taushin zuciya za su gani suyi murna, ku da kuke neman Yahweh, zukatanku zasu rayu. 33 Gama Yahweh na sauraron mabuƙata, ba ya kuma raina 'yan sarƙarsa. 34 Bari sama da ƙasa su yabe shi da tekuna da dukkan abubuwan dake iyo a cikinsu. 35 Gama Allah zai ceci Sihiyona, zai sake gina biranen Yahuda; mutane zasu zauna a can ya zama nasu. 36 Zuriyar bayinsa zasu gaje shi, waɗanda ke ƙaunar sunansa zasu zauna a can.
1 Save me, God!
Yahweh, come quickly and help me.
2 Let those who try to take my life
be ashamed and humiliated;
let them be turned back and brought to dishonor,
those who take pleasure in my pain.
3 Let them be turned back because of their shame,
those who say, "Aha, aha."
4 Let all those who seek you
rejoice and be glad in you;
let those who love your salvation always say,
"May God be praised."
5 But I am poor and needy;
hurry to me, God;
you are my help and you rescue me.
Yahweh, do not delay.
1 Ka cece ni ya Allah, Yahweh, ka zo da sauri ka taimake ni. 2 Bari waɗanda ke so su ɗauki raina su ji kunya su ƙasƙanta; bari su koma baya a wulaƙance, su waɗanda ke murna da raɗaɗina. 3 Bari su koma baya cikin kunya, su waɗanda ke cewa, "Aha, aha." 4 Bari dukkan waɗanda ke neman ka suyi farinciki, suyi murna a cikin ka, bari waɗanda ke ƙaunar cetonka koyaushe su ce, "A yabi Allah." 5 Amma ni matalauci ne mai bukata, ka yiwo sauri wurina Allah, kai ne taimakona ka kuɓutar dani, Yahweh, kada ka yi jinkiri.
1 In you, Yahweh, I take refuge;
let me never be put to shame.
2 Rescue me and make me safe in your righteousness;
turn your ear to me and save me.
3 Be to me a rock for refuge
where I may always go;
you have given a command to save me,
for you are my rock and my fortress.
4 Rescue me, my God, out of the hand of the wicked,
out of the hand of the unrighteous and ruthless.
5 For you are my hope, Lord Yahweh.
I have trusted in you ever since I was a child.
6 By you I have been supported from the womb;
you are he who took me out of my mother's belly;
my praise will be always about you.
7 I am a marvel to many people;
you are my strong refuge.
8 My mouth will be filled with your praise,
all the day with your honor.
9 Do not throw me away in my time of old age;
do not abandon me when my strength fails.
10 For my enemies are talking about me;
those who watch for my life are plotting together.
11 They say, "God has abandoned him;
pursue and take him,
for there is no one to save him."
12 God, do not be far from me;
my God, hurry to help me.
13 Let them be put to shame and destroyed,
those who are hostile to my life;
let them be covered with rebuke and dishonor,
those who seek my hurt.
14 But I will always hope in you
and will praise you more and more.
15 My mouth will tell about your righteousness
and your salvation all the day,
although I cannot understand it.
16 I will come with the mighty acts of the Lord Yahweh;
I will make mention of your righteousness, yours alone.
17 God, you have taught me from my youth;
even now I declare your wonderful deeds.
18 Indeed, even when I am old and gray-headed, God,
do not abandon me,
as I have been declaring your strength to the next generation,
your power to everyone who is to come.
19 Your righteousness also, God, is very high;
you who have done great things,
God, who is like you?
20 You who made me see many troubles
will revive us again
and will bring us up again
from the depths of the earth.
21 May you increase my honor;
turn again and comfort me.
22 I will also give thanks to you with the harp
for your trustworthiness, my God;
to you I will sing praises with the harp,
Holy One of Israel.
23 My lips will shout for joy when I sing praises to you—
even my soul, which you have redeemed.
24 My tongue will also talk about your righteousness
all day long;
for they have been put to shame and are confused,
those who sought my hurt.
1 Yahweh, a gare ka nake samun mafaka, kada ka taɓa bari in ji kunya. 2 Ka kuɓutar da ni ka sa in zauna lafiya cikin adalcinka. 3 Ka zama dutsen fakewa a gare ni inda zan zo ko yaushe, ka bada umarni a cece ni, gama kai ne dutsena da kagarata. 4 Ka cece ni, Allahna daga hannun miyagu, daga masu shirya mugunta. 5 Gama kai ne begena, Ubangiji Yahweh. Na dogara gare ka tun ina yaro. 6 Kai ne kake ta taimako na tun daga cikin ciki; kai ne ka fito dani daga cikin mahaifiyata; yabona a gare ka ya ke koyaushe. 7 Na zama misali ga mutane da yawa, kai ne mafakata mai ƙarfi. 8 Bakina zai cika da yabonka, da ɗaukakarka dukkan yini. 9 Kada ka yashe ni a lokacin dana tsufa, kada ka manta dani lokacin da ƙarfina ya ƙare. 10 Gama maƙiyana maganata, waɗanda ke neman raina suna shiri tare. 11 Sun ce, "Allah ya yashe shi, ku bi ku ɗauko shi, gama ba wanda zai cece shi." 12 Allah, kada ka yi nisa dani, Allahna, ka yi sauri ka taimake ni. 13 Bari su sha kunya su hallaka su waɗanda suka hasalar da raina; su ji kunya su hallaka. bari zarga da raini su rufe su, su waɗanda ke so su lahanta ni. 14 Amma zan sa begena a gare ka, zan yabe ka gaba-gaba. 15 Bakina zai yi maganar adalcinka da cetonka dukkan yini, koda yake ba zan iya gane shi ba. 16 Zan zo da manyan ayyukan Ubangiji Yahweh, zan faɗi adalcinka, naka kaɗai. 17 Allah, ka koya mani tun ina saurayi, har yanzu ina shelar ayyukanka na ban mamaki. 18 I, ko lokacin da kaina ya yi furfura, Allah, kada ka yashe ni, ina ta shelar ƙarfinka ga tsara mai zuwa, ikonka kuma ga kowanne mai zuwa. 19 Adalcinka kuma, ya Allah yana da tsawo ƙwarai, kai da ka yi manyan abubuwa, Allah, wane ne kamar ka? 20 Kai da ka nuna mana wahalhalu da yawa masu tsanani, za ka farfaɗo damu, ka fito damu daga ƙarƙashin ƙasa. 21 Ka ƙara mani martaba, ka juyo ka ƙarfafa ni. 22 Zan kuma yi maka godiya da molo saboda amincinka, Allahna; gare ka zan yi yabo da molo, mai tsarki na Isra'ila. 23 Leɓunana zasu yi sowa ta farinciki, sa'ad da nake raira yabo a gare ka-har da raina, wanda ka fanso. 24 Harshena kuma zai yi maganar adalcinka dukkan yini; gama sun ji kunya sun rikice, su waɗanda ke nema su lahanta ni.
1 Give the king your righteous decrees, God,
your righteousness to the king's son.
2 May he judge your people with righteousness
and your poor with justice.
3 May the mountains produce peace for the people;
may the hills produce righteousness.
4 May he judge the poor of the people;
may he save the children of the needy
and break in pieces the oppressor.
5 May they honor you while the sun endures,
and as long as the moon lasts throughout all generations.
6 May he come down like rain on the mown grass,
like showers that water the earth.
7 May the righteous flourish in his days,
and may there be an abundance of peace till the moon is no more.
8 May he have dominion from sea to sea,
and from the River to the ends of the earth.
9 May those who live in the wilderness bow down before him;
may his enemies lick the dust.
10 May the kings of Tarshish and of the islands render tribute;
may the kings of Sheba and Seba offer gifts.
11 Indeed, may all kings fall down before him;
may all nations serve him.
12 For he helps the needy person who cries out
and the poor person who has no other helper.
13 He has pity on the poor and needy,
and he saves the lives of needy people.
14 He redeems their lives from oppression and violence,
and their blood is precious in his sight.
15 May he live!
May the gold of Sheba be given to him.
May people always pray for him;
may God bless him all day long.
16 May there be abundance of grain in the land;
on the mountaintops may their crops wave.
May the fruit of it be like Lebanon;
may the people flourish in the cities like the grass of the field.
17 May his name endure forever;
may his name continue as long as the sun;
may people be blessed in him;
may all nations call him blessed.
18 May Yahweh God, the God of Israel, be blessed,
who alone does wonderful things.
19 May his glorious name be blessed forever,
and may the whole earth be filled with his glory.
Amen and Amen.
20 The prayers of David son of Jesse are finished.
1 Ka ba sarki dokokinka masu adalci, Allah, adalcinka kuma ga ɗan sarkin. 2 Dãma ya hukunta jama'arka da adalci, matalautanka kuma da adalci. 3 Dãma duwatsu su fito da salama saboda mutanenka; dãma tuddai kuma su fito da adalci. 4 Dãma ya hukunta mutane matalauta; dãma ya ceci 'ya'yan mabuƙata, ya ragargaza azzalumi. 5 Dãma su ba ka daraja muddin rana tana haskakawa, wata kuma yana nan har zuwa tsararraki dukka. 6 Dãma ya sauko kamar ruwan sama a kan ciyawar da a ka tattake, kamar zubowar ruwan sama a kan ƙasa. 7 Dãma masu adalci su yalwata a kwanakinsa, dãma kuma a sami salama a yalwace har sai wata ya shuɗe. 8 Dãma ya yi mulki daga teku zuwa teku, daga kogi har zuwa ƙarshen duniya. 9 Dãma waɗanda ke zama a jeji su rusuna a gabansa; dãma maƙiyansa kuma su lashi turɓaya. 10 Dãma sarkunan Tarshish da na tsibirai su kawo gaisuwa a gare shi, dãma sarakunan Sheba da Seba su ba shi kyautai. 11 I, dãma dukkan sarakuna su rusuna a gabansa, dãma kuma dukkan al'ummai su bauta masa. 12 Gama ya kan taimaki mabuƙacin da yayi kuka da matalaucin da ba shi da mai taimako. 13 Ya ji tausayin mabuƙata da matalauta, ya kuma ceci ran mabuƙata. 14 Ya fanshi rayukansu daga wahala da kuma wulaƙanci, jininsu kuma yana da daraja a idanunsa. 15 Dãma ya rayu! Dãma a ba da zinariyar Sheba a gare shi. Bari mutane su yi masa addu'a koyaushe; dãma Yahweh ya albarkace shi dukkan yini. 16 Dãma a sami hatsi a yalwace a cikin ƙasa, na kan tudu kuma amfaninsu ya yi yabanya. Dãma kawunan hatsinsu ya zama kamar Lebanon, dãma jama'a su sami albarka kamar ciyawa ta saura. 17 Dãma sunansa ya kasance har abada, dãma sunansa ya ci gaba muddin rana ta nan; dãma jama'a su sami albarka ta wurinsa; dãma dukkan al'ummai su kira shi mai albarka. 18 Dãma Allah Yahweh, Allah na Isra'ila, ya zama mai albarka; wanda shi kaɗai ne ke yin abubuwan ban mamaki. 19 Dãma sunansa mai daraja ya zama mai albarka har abada, dãma kuma dukkan duniya ta cika da ɗaukakarsa. Amin -- Amin. 20 Dauda ɗan Yesse ya gama yin addu'o'insa. Littafi na Uku.
1 Surely God is good to Israel,
to those with a pure heart.
2 But as for me, my feet almost slipped;
my feet almost slipped out from under me
3 because I was envious of the arrogant
when I saw the prosperity of the wicked.
4 For they have no pain until their death,
but they are strong and well fed.
5 They are not in trouble like other men;
they are not afflicted like other men.
6 Pride adorns them like a necklace around their neck;
violence clothes them like a robe.
7 Out of such blindness comes sin;
evil thoughts pass through their hearts.
8 They mock and speak wickedly;
in their arrogance they threaten oppression.
9 They set their mouth against the heavens,
and their tongues march through the earth.
10 Therefore his people turn to them
and abundant waters are drained out.
11 They say, "How does God know?
Is there knowledge with the Most High?"
12 Take notice: these people are wicked;
they are always at ease, becoming richer and richer.
13 Surely it is in vain that I have guarded my heart
and washed my hands in innocence.
14 For all the day long I have been afflicted
and disciplined every morning.
15 If I had said, "I will say these things,"
then I would have betrayed this generation of your children.
16 Though I tried to understand these things,
it was too difficult for me.
17 Then I went into God's sanctuary
and came to understand their fate.
18 Surely you put them in slippery places;
you bring them down to ruin.
19 How they become a wilderness in a moment!
They come to an end and are finished in awful terrors.
20 They are like a dream after one wakes up;
Lord, when you arise,
you will despise their image.
21 For my heart was embittered,
and I was deeply wounded.
22 I was ignorant and lacked insight;
I was like a senseless animal before you.
23 Yet I am always with you;
you hold my right hand.
24 You will guide me with your advice
and afterward receive me to glory.
25 Whom have I in heaven but you?
There is no one on earth that I desire but you.
26 My flesh and my heart grow weak,
but God is the strength of my heart
and my portion forever.
27 Those who are far from you will perish;
you will destroy all those who are unfaithful to you.
28 But as for me, all I need to do is to approach God.
I have made the Lord Yahweh my refuge.
I will declare all your deeds.
1 Hakika Allah mai alheri ne ga Isra'ila, gare su da suke da tsabtar zuciya. 2 Amma a gare ni kafafuna sun kusa su zame; kafafuna sun kusa su zame waje daga karkashina. 3 saboda na ji kishin masu girmankai sa'ad da na ga wadatar masu mugunta. 4 Gama basu da raɗaɗi har ranar mutuwarsu, amma suna da ƙarfi kuma suna ci da kyau. Basu da nawayar sauran mutane; 5 Basu da masifu kamar na sauran mutane. 6 Girmankai na rataye a wuyansu kamar sarƙa; tashin hankali ya rufe su kamar riga. 7 Daga irin wannan makantar zunubi ke zuwa; mugayen tunani sun ratsa zukatansu 8 Suna ba'a kuma suna magana cikin mugunta; cikin fankamarsu suna yin kurarin zalunci. 9 Suna magana gãba da sammai, harsunan su kuma na tattaki a ƙasa. 10 Domin haka mutanensa sun juya gare su isassun ruwaye sun cika kwararo. 11 Suka ce, "Ta yaya Allah ya sani? Akwai wani sani a wurin maɗaukaki?" 12 Kula: waɗannan mutane mugayene; a koyaushe a huce suke, sai ƙara zama mawadata suke yi. 13 Lallai a banza na kiyaye zuciyata kuma na wanke hannuwana cikin rashin laifi. 14 Kowacce rana ina shan azaba da horo kowacce safiya. 15 Idan nace, "Zan faɗi waɗannan abubuwa," da naci amanar wannan tsarar ta 'ya'yanka. 16 Ko da shike na yi ƙoƙarin fahimtar waɗannan abubuwa, ya zama da wahala a gare ni. 17 Daga nan sai na tafi cikin wuri mai tsarki na Allah daga nan na fahimci makomarsu. 18 Hakika ka sanya su a wurare masu santsi; ka kawo su ƙasa ga hallaka. 19 Yadda suka zama jeji farat ɗaya! ƙarshensu yazo sun ƙarasa cikin babban tsoro. 20 Sun zama kamar mafarki bayan da mutum ya farka; Ya Ubangiji, sa'ad da ka tashi, ba zaka yi tunanin komai game da waɗannan mafarkan ba. 21 Gama zuciyata ta damu, a cikina nayi rauni. Na zama jahili na kuma rasa basira; 22 Na zama kamar dabba marar tunani a gabanka. 23 Duk da haka kullum ina tare da kai; Ka riƙe hannuna na dama. 24 Zaka bishe ni da shawarar ka bayan wannan ka karɓe ni zuwa ɗaukaka. 25 Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba wani a duniya da nake marmari in ba kai ba. 26 Jikina da zuciyata sun yi sanyi, amma Allah shi ne ƙarfin zuciyata har abada. 27 Waɗanda suke nesa da kai zasu lalace; zaka hallaka dukkan marasa aminci gare ka. 28 Amma ni, abin da nake bukata shi ne in kusanci Allah. Na mai da Ubangiji Yahweh mafakata. Zan bayyana dukkan ayyukanka.
1 God, why have you rejected us forever?
Why does your anger burn against the sheep of your pasture?
2 Call to mind your people, whom you purchased in ancient times,
the tribe whom you have redeemed to be your own heritage,
and Mount Zion, where you live.
3 Come look at the everlasting ruins,
all the damage that the enemy has done in the holy place.
4 Your adversaries roared in the middle of your appointed place;
they set up their battle flags.
5 They hacked away with axes
as in a thick forest.
6 They smashed and broke down all the engravings;
they broke them with axes and hammers.
7 They set your sanctuary on fire, knocking it to the ground;
they desecrated the dwelling place of your name.
8 They said in their hearts, "We will destroy them all."
They burned up all the meeting places of God in the land.
9 We do not see any more signs;
there is no prophet any more,
and no one among us knows how long this will last.
10 How long, God, will the enemy throw insults at you?
Will the enemy blaspheme your name forever?
11 Why do you hold back your hand, your right hand?
Take your right hand from your garment and destroy them.
12 Yet God has been my king from ancient times,
bringing salvation on the earth.
13 You divided the sea by your strength;
you smashed the heads of the sea monsters in the waters.
14 You crushed the heads of leviathan;
you fed him to those living in the wilderness.
15 You broke open springs and streams;
you dried up flowing rivers.
16 The day is yours, and the night is yours also;
you set the light and the sun in place.
17 You have set all the borders of the earth;
you have made summer and winter.
18 Call to mind how the enemy hurled insults at you, Yahweh,
and that a foolish people has blasphemed your name.
19 Do not give the life of your dove to a wild animal.
Do not forget forever the life of your oppressed people.
20 Remember your covenant,
for the dark regions of the land are full of places of violence.
21 Do not let the oppressed be turned back in shame;
let the poor and oppressed praise your name.
22 Arise, God; plead your own cause;
call to mind how fools mock you all day long.
23 Do not forget the voice of your adversaries
or the uproar of those who continually defy you.
1 Ya Allah, don me ka yashe mu har abada? Don me fushin ka yayi ƙuna a kan tumakin makiyayarka? 2 Ka da tuna mutanenka, waɗanda ka saya a zamanin dã, kabila wadda ka fãnsa su zama abin gãdonka, da Tsaunin Sihiyona, inda kake zama. 3 Kazo ka dubi dukkan hallakarwa, dukkan ɓarnar da maƙiyi yayi a cikin wuri mai tsarki. 4 Abokan gãbar ka sun yi ruri a tsakiyar zaɓaɓɓen wurinka; sun kafa tutocin yaƙinsu. 5 Sun sassare ruƙuƙin kurmi da gatura. 6 Sun ragargaza sun kuma sassake su dukka; sun karya su da gatura da gudumai. 7 Sun kunna wa wurinka mai tsarki wuta; sun tozarta wurin zaman ka, sun buga shi har ƙasa. 8 A cikin zuciyarsu suka ce, "Zamu hallakar dasu dukka," Sun ƙone dukkan wuraren taruwarka cikin ƙasar. 9 Bamu ga wasu alamu ba; ba sauran wani annabi, ba wani a cikin mu da yasan har yaushe wannan zai ƙare. 10 Ya Allah, har yaushe maƙiyi zai yi ta cin mutuncin ka? Maƙiyi zai yi ta saɓon sunanka har abada? 11 Donme ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fito da hannunka na dama daga cikin rigarka ka hallaka su. 12 Duk da haka Allah sarkina ne tun zamanun dã, mai kawo ceto a duniya. 13 Ka raba teku da ƙarfinka; ka farfasa kawunan dodannin teku cikin ruwaye. 14 Ka murƙushe kan Lebiyatan; ka ciyar da waɗanda suke zama cikin jeji da shi. 15 Ka karya buɗaɗɗun maɓuɓɓulai da ƙoramai; kasa koguna masu gudu su ƙafe. 16 Yini naka ne, dare kuma naka ne; kaine ka sanya rana da wata. 17 Kaine ka sanya dukkan iyakokin duniya; kayi damina da rani. 18 Yahweh, Ka tuna yadda maƙiyi yayi ta jefa maganganun banza a kanka, wawayen mutanen nan sun yi saɓon sunanka. 19 Kada ka miƙa ran kurciyarka ga naman jeji. Kada ka manta da ran mutanenka da ake zalunta har abada. 20 Katuna da alƙawarinka, gama wurare masu duhu na ƙasa suna cike da tashin hankali. 21 Kada ka bari waɗanda ake zalunta su dawo cikin kunya; bari talakawa da waɗanda ake zalunta su yabi sunanka. 22 Ka tashi, ya Allah; ka kãre mutuncinka; ka tuna yadda wawaye suke zaginka dukkan yini. 23 Kada ka manta da muryar magabtanka ko hargowar waɗannan da suke ci gaba da adawa da kai.
1 We give thanks to you, God;
we give thanks, for your name is near;
people tell of your wondrous works.
2 At the appointed time
I will judge fairly.
3 Though the earth and all the inhabitants shake in fear,
I make steady the earth's pillars. Selah
4 I said to the arrogant, "Do not be arrogant,"
and to the wicked, "Do not lift up the horn.
5 Do not lift up your horn to the heights;
do not speak with an arrogant neck."
6 It is not from the east or from the west,
and it is not from the wilderness that lifting up comes.
7 But God is the judge;
he brings down and he lifts up.
8 For Yahweh holds in his hand a cup of foaming wine,
which is mixed with spices, and pours it out.
Surely all the wicked of the earth
will drink it to the last drop.
9 But I will continually tell what you have done;
I will sing praises to the God of Jacob.
10 He says, "I will cut off all the horns of the wicked,
but the horns of the righteous will be raised up."
1 Muna yi maka godiya, ya Allah; muna godiya, domin ka bayyana kasancewarka; mutane suna faɗin ayyukanka na al'ajabi. 2 A ƙayyadajjen lokaci zanyi hukunci da dai-daita. 3 Koda ya ke duniya da mazauna cikinta sun girgiza cikin tsoro, na kafa wa duniya ginshiƙai. Selah 4 Nace wa masu girmankai, "Kada kuyi girmankai," ga masu mugunta kuma, "Kada ku ɗaga ƙaho; 5 kada ku ɗaga ƙahonku ga sammai; kada kuyi magana da ɗaga wuya na rashin mutuntawa." 6 Ba daga gabas bane ko daga yamma, kuma ba daga jeji bane ɗaukaka take fitowa ba. 7 Amma Allah ne mai shari'a; yakan ƙasƙantar yakan kuma ɗaukaka sama. 8 Gama Yahweh ya riƙe ƙoƙon inabi cikin hannunsa mai sa buguwa, wanda yake gauraye da kayan yaji, yana tsiyayar da shi. Hakika dukkan miyagun duniya zasu shanye shi dukka. 9 Amma zan ci gaba da faɗin abin da kayi; Zan raira yabbai ga Allah na Yakubu. 10 Yace, zan datse dukkan ƙahonnin miyagu, amma ƙahonnin masu adalci zasu ɗaukaka."
1 God has made himself known in Judah;
his name is great in Israel.
2 His tent is in Salem;
his dwelling place is in Zion.
3 There he broke the arrows of the bow,
the shield, the sword, and the other weapons of war. Selah
4 You shine brightly and are majestic
as you descend from the mountains, where you killed your victims.
5 The brave of heart were plundered;
they fell asleep.
All the warriors were helpless.
6 At your rebuke, God of Jacob,
both charioteer and horse fell asleep.
7 You, yes you, are to be feared;
who can stand in your sight when you are angry?
8 From heaven you made your judgment heard;
the earth was afraid and silent
9 when you, God, arose to execute judgment
and to save all the oppressed of the earth. Selah
10 Surely your angry judgment against humanity will bring you praise;
you gird yourself with the remnant of your anger.
11 Make vows to Yahweh your God and keep them.
May all who surround him bring tribute to him who is to be feared.
12 He cuts off the spirit of the princes;
he is feared by the kings of the earth.
1 Allah ya sanar da kansa cikin Yahuda; sunansa mai girma ne cikin Isra'ila. 2 Rumfarsa cikin Salem take; wurin zaman sa cikin Sihiyona ya ke. 3 A can ya kakkarya kibawu na baka, garkuwa da takobi da sauran kayan yaƙi. Selah 4 Ka haskaka da sheƙi kuma ka bayyana ɗaukakarka, daka sauka daga duwatsu, wurin daka kashe masu azabtar da kai. 5 Masu ƙarfin zuciya an washe su; an kashe su. Dukkan jarumawa sun rasa mai taimako. 6 Bisa ga tsautawarka, Allah na Yakubu, doki da mahayinsa sun faɗi sun mutu. 7 Kai, I kaine za a ji tsoro; wa zai tsaya gabanka lokacin da kayi fushi? 8 Daga sama kasa aji hukuncinka; duniya ta ji tsoro tayi shiru 9 lokacin da kai, Allah, ka tashi don tabbatar da hukunci kuma ka ceci dukkan waɗanda ake zalunta na duniya. Selah 10 Hakika fushin hukuncin ka akan ɗan adam zai kawo maka yabo; ka yiwa kanka ɗamara da sauran abin da ya ragu na fushinka. 11 Kayi alƙawura ga Yahweh Allahnka ka kumaa cika su. Bari duk waɗanda suke kewaye da shi su kawo kyautai gare shi wanda ya isa a ji tsoronsa. 12 Ya datse ruhun 'ya'yan sarakai; sarakunan duniya sun ji tsoron sa.
1 I will call with my voice to God;
I will call out with my voice to God,
and my God will give ear to me.
2 In the day of my trouble I sought the Lord;
at night I stretched my hands out, and they would not become tired.
My soul refused to be comforted.
3 I thought of God as I groaned;
I thought about him as I grew faint. Selah
4 You held my eyes open;
I was too troubled to speak.
5 I thought about the days of old,
about years long past.
6 During the night I called to mind the song I once sang.
I thought carefully
and tried to understand what had happened.
7 Will the Lord reject me forever?
Will he never again show me favor?
8 Was his covenant faithfulness gone forever?
Had his promise failed forever?
9 Had God forgotten to be gracious?
Had his anger shut off his compassion? Selah
10 I said, "This is my sorrow:
the changing of the right hand of the Most High toward us."
11 But I will remember the deeds of Yah; [1]
I will remember your miracles of long ago.
12 I will ponder all your deeds
and will reflect on them.
13 Your way, God, is holy;
what god compares to our great God?
14 You are the God who does wonders;
you have revealed your strength among the peoples.
15 You gave your people victory by your great power—
the descendants of Jacob and Joseph. Selah
16 The waters saw you, God;
the waters saw you, and they were afraid;
the depths trembled.
17 The clouds poured down water;
the cloudy skies gave voice;
your arrows flew about.
18 Your thunderous voice was heard in the wind;
the lightning lit up the world;
the earth trembled and shook.
19 Your path went through the sea
and your way through the surging waters,
but your footprints were not seen.
20 You led your people like a flock
by the hand of Moses and Aaron.
1 Da muryata zan yi kira ga Allah; Zan yi kira da muryata ga Allah, Allah zai ji ni. 2 A cikin ranar masifata na biɗi Ubangiji; da dare na miƙar da hannuwana waje, ba kuwa zasu gaji ba. Raina yaƙi ta'azantuwa. 3 Na tuna da Allah yayin da nayi nishi; Nayi tunaninsa yayin dana sụma. Selah 4 Ka riƙe idanuna a buɗe; na damu ƙwarai na kasa magana. 5 Na tuna da kwanakin dã, game da lokuttan da suka wuce tun-tuni. 6 A cikin dare na tuna da waƙar dana taɓa rairawa. Nayi tunani a hankali kuma nayi ƙoƙarin fahimtar abin da ya faru. 7 Ko Ubangiji zai ƙini har abada? Ba zai ƙara nuna cewa ya ji ɗaɗi na ba? 8 Amintaccen alƙawarinsa ya tafi har abada? Ko alƙawarinsa ya tsinke har abada? 9 Ko Allah ya manta zama mai alheri? Ko fushinsa ya kulle jinƙansa ne? Selah 10 Nace, "Wannan baƙinciki na ne: Canjin hannun dama na Maɗaukaki a kanmu." 11 Amma zan tuna da ayyukanka; Zan yi tunani game da ayyukanka na al'ajabi na dã. 12 Zan yi bin-binin dukkan ayyukanka kuma in yi tunani a kansu. 13 Hanyarka, ya Allah, mai tsarki ce, ba wani allah da za a kwatanta shi da Allahnmu babba? 14 Kaine Allah wanda kake aikata al'ajibai; ka bayyana ƙarfinka tsakanin dangogi. 15 Ka ba mutanenka nasara ta wurin girman ikonka - zuriyar Yakubu da Yosef. Selah 16 Ruwaye sun ganka, ya Allah; ruwaye sun ganka, kuma sunji tsoro; zurfafa sun raurawa. 17 Giza-gizai sun zubo da ruwa ƙasa; hadarin sammai sun yi tsawa; hasken walƙiyarka sun tashi kamar kibau. 18 Muryar tsawarka an ji ta cikin guguwa; hasken ya ɗaga duniya; duniya ta raurawa ta girgiza kuma. 19 Hanyarka tabi ta teku tafarkin ka kuma ta manyan ruwaye, amma ba a ga sawayenka ba. 20 Ka bi da mutanenka kamar garken tumaki ta hannun Musa da Haruna.
1 Hear my teaching, my people,
listen to the words of my mouth.
2 I will open my mouth in parables;
I will sing about hidden things about the past.
3 These are things that we have heard and learned,
things that our ancestors have told us.
4 We will not keep them from their descendants.
We will tell the next generation
about the praiseworthy deeds of Yahweh,
his strength, and the wonders that he has done.
5 For he established covenant decrees in Jacob
and appointed a law in Israel.
He commanded our ancestors
that they were to teach them to their children.
6 He commanded this so that the generation to come might know his decrees,
the children not yet born,
who should tell them in turn to their own children.
7 Then they would place their hope in God
and not forget his deeds
but keep his commandments.
8 Then they would not be like their ancestors,
who were a stubborn and rebellious generation,
a generation whose hearts were not right,
and whose spirits were not committed and faithful to God.
9 The Ephraimites were armed with bows,
but they turned back on the day of battle.
10 They did not keep the covenant with God,
and they refused to obey his law.
11 They forgot his deeds,
the wonderful things that he had shown them.
12 They forgot the marvelous things he did in the sight of their ancestors
in the land of Egypt, in the land of Zoan.
13 He divided the sea and led them across it;
he made the waters to stand like walls.
14 In the daytime he led them with a cloud
and all the night with the light of fire.
15 He split the rocks in the wilderness,
and he gave them water abundantly,
enough to fill the depths of the sea.
16 He made streams flow out of the rock
and made the water flow like rivers.
17 Yet they continued to sin against him,
rebelling against the Most High in the wilderness.
18 They challenged God in their hearts
by asking for food to satisfy their appetites.
19 They spoke against God;
they said, "Can God really lay out a table for us in the wilderness?
20 See, when he struck the rock,
waters gushed out
and streams overflowed.
But can he give bread also?
Will he provide meat for his people?"
21 When Yahweh heard this, he was angry;
so his fire burned against Jacob,
and his anger attacked Israel,
22 because they did not believe in God
and did not trust in his salvation.
23 Yet he commanded the skies above
and opened the doors of the sky.
24 He rained down manna for them to eat,
and gave them the grain from heaven.
25 People ate the bread of angels.
He sent them food in abundance.
26 He caused the east wind to blow in the sky,
and by his power he guided the south wind.
27 He rained down meat on them like dust,
birds as numerous as the sands of the sea.
28 They fell in the middle of their camp,
all around their tents.
29 So they ate and were full.
He gave them what they craved.
30 But they had not yet filled up;
their food was still in their mouths.
31 Then God's anger attacked them
and killed the strongest of them.
He brought down the young men of Israel.
32 Despite this, they continued to sin
and did not believe his wonderful deeds.
33 Therefore God cut short their days;
their years were filled with terror.
34 Whenever God killed them, they would start to seek him,
and they would return and look earnestly for him.
35 They would call to mind that God was their rock
and that the Most High God was their rescuer.
36 But they would flatter him with their mouth
and lie to him with their words.
37 For their hearts were not firmly fixed on him,
and they were not faithful to his covenant.
38 Yet he, being merciful,
forgave their iniquity
and did not destroy them.
Yes, many times he held back his anger
and did not stir up all his wrath.
39 He called to mind that they were made of flesh,
a wind that passes away and does not return.
40 How often they rebelled against him in the wilderness
and grieved him in the barren regions!
41 Again and again they challenged God
and offended the Holy One of Israel.
42 They did not think about his power,
how he had rescued them from the enemy
43 when he performed his terrifying signs in Egypt
and his wonders in the region of Zoan.
44 He turned the Egyptians' rivers to blood
so that they could not drink from their streams.
45 He sent swarms of flies that devoured them
and frogs that destroyed them.
46 He gave their crops to the grasshopper
and their labor to the locust.
47 He destroyed their vines with hail
and their sycamore trees with more hail.
48 He rained hail on their cattle
and hurled lightning bolts at their livestock.
49 The fierceness of his anger lashed out against them.
He sent wrath, fury, and trouble
like angels who bring disaster.
50 He leveled a path for his anger;
he did not spare them from death
but gave them over to the plague.
51 He killed all the firstborn in Egypt,
the firstborn of their strength in the tents of Ham.
52 He led his own people out like sheep
and guided them through the wilderness like a flock.
53 He led them secure and unafraid,
but the sea overwhelmed their enemies.
54 Then he brought them to the border of his holy land,
to this mountain that his right hand acquired.
55 He drove out the nations from before them
and assigned them their inheritance.
He settled the tribes of Israel in their tents.
56 Yet they challenged and rebelled
against the Most High God
and did not keep his solemn commands.
57 They were unfaithful
and acted treacherously like their fathers;
they were as undependable as a faulty bow.
58 For they made him angry with their high places
and provoked him to jealous anger with their idols.
59 When God heard this, he was angry
and completely rejected Israel.
60 He abandoned the sanctuary of Shiloh,
the tent where he had lived among people.
61 He allowed his strength to be captured
and gave his glory into the enemy's hand.
62 He handed his people over to the sword,
and he was angry with his heritage.
63 Fire devoured their young men,
and their virgins had no wedding songs.
64 Their priests fell by the sword,
and their widows could not weep.
65 Then the Lord awakened as one from sleep,
like a warrior who shouts because of wine.
66 He drove his adversaries back;
he put them to everlasting shame.
67 He rejected the tent of Joseph,
and he did not choose the tribe of Ephraim.
68 He chose the tribe of Judah
and Mount Zion that he loved.
69 He built his sanctuary like the heavens,
like the earth that he has established forever.
70 He chose David, his servant,
and took him from the sheepfolds.
71 He took him from following the ewes with their young,
and he brought him to be shepherd of Jacob,
his people, and of Israel, his heritage.
72 David shepherded them with the integrity of his heart,
and he guided them with the skill of his hands.
1 Ku ji koyarwata, ya mutanena, ku saurari maganar bakina. 2 Zan buɗe bakina cikin misalai; Zan raira game da ɓoyayyun abubuwa na dã. 3 Waɗannan sune abubuwan da muka ji muka kuma koya, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana. Ba zamu ɓoye su daga zuriyarsu ba. 4 Zamu sanar da tsara mai zuwa game da yabban ayyukan Yahweh, ƙarfinsa, da al'ajiban da ya aikata. 5 Gama ya tabbatadda shaidar alƙawari cikin Yakubu ya sanya shari'a cikin Isra'ila. Ya umarci kakanninmu cewa su koyar dasu ga 'ya'yansu. 6 Ya umarta wannan domin tsara mai zuwa ta iya sanin umarnansa, 'ya'yan da ba a haifa ba, su kuma su faɗi wa 'ya'yansu. 7 Daga nan sai su sa zuciyarsu ga Allah kada su manta da ayyukansa amma su kiyaye dokokinsa. 8 Daga nan ba zasu zama kamar kakanninsu ba, da suka zama da taurin kai da tsara mai tayarwa, tsarar da zukatansu ba dai-dai suke ba, waɗanda ruhohinsu basu tsaya sun yi aminci ga Allah ba. 9 'Ya'yan Ifraim sun riƙe makamai tare da bakukkuna, amma suka juya baya a ranar yaƙi. 10 Basu kiyaye alƙawari da Allah ba, suka ƙi yin biyayya da dokarsa. 11 Suka manta da ayyukansa, ayyukan al'ajiban daya nuna masu. 12 Sun manta da ayyukan mamaki da yayi a idanun kakanninsu a cikin ƙasar masar, cikin ƙasar Zowan. 13 Ya raba teku ya ƙetaradda su; ya sa ruwa ya tsaya kamar bangaye. 14 Da rana ya bishe su da girgije dukkan dare kuma da hasken wuta. 15 Ya tsaga duwatsu cikin jeji, ya basu ruwa a yalwace, isasshe dake iya cika zurfafan teku. 16 Yasa rafuffuka su malala daga cikin dutse ya kuma sa ruwan ya gudana kamar koguna. 17 Duk da haka suka ci gaba da yi masa zunubi, suna tayar wa Maɗaukaki cikin ƙasa busasshiya. 18 Suka ƙalubalanci Allah cikin zukatansu ta wurin tambayar abinci domin ƙosar da marmarinsu. 19 Sun yi wa Allah baƙar magana; suka ce, "Zai yiwu Allah ya shirya teburi a cikin jeji? 20 Duba, lokacin da ya bugi dutsen, ruwaye suka ɓullo rafuffuka suka yi ambaliya. Amma zai yiwu ya bada gurasa kuma? Zai iya tanada nama domin mutanensa?" 21 Lokacin da Yahweh ya ji wannan, yayi fushi; wutarsa tayi ƙuna akan Yakubu, fushinsa kuma ya hari Isra'ila, 22 saboda basu gaskata Allah ba basu kuma dogara ga cetonsa ba. 23 Duk da haka ya umarci sammai a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sararin sama. 24 Ya zuba masu manna su ci, ya kuma basu hatsi daga sama. 25 Mutane suka ci abincin mala'iku. Ya aika masu da abinci isasshe. 26 Yasa iskar gabas ta hura cikin sama, ta wurin ikonsa kuma ya jagoranci iskar kudu. 27 Ya zuba masu nama kamar ƙura, tsuntsaye da yawa kamar yashin teku. 28 Suka faɗo a tsakiyar sansaninsu, ko'ina kewaye da rumfunansu. 29 Suka ci suka ƙoshi sosai. Ya basu abin da suke marmari. 30 Amma duk da haka basu cika ba; tun abincinsu na cikin bakinsu. 31 Daga nan fushin Allah ya buge su ya kashe mafi ƙarfin su. Majiya ƙarfin Isra'ila ya buga su ƙasa. 32 Duk da wannan, sun ci gaba da yin zunubi kuma basu gaskata ayyukan al'ajabansa ba. 33 Domin haka Allah ya taƙaita kwanakin su; shekarunsu suna cike da razana. 34 Duk sa'ad da Allah ya buge su, sai su fara neman sa, za su juyo su neme shi da gaske. 35 Zasu tuna cewa Allah ne dutsensu Allah maɗaukaki kuma shi ne mai fansarsu. 36 Amma suka yi masa daɗin baki suka kuma yi masa ƙarya da maganganunsu. 37 Gama zukatansu basu dogara gare shi ba, basu yi aminci ga alƙawarinsa ba. 38 Amma shi, mai tausayi ne, ya gafarta laifofinsu bai hallaka su ba. I, lokuta da yawa yakan janye fushinsa bai tayar da dukkan hasalarsa ba. 39 Ya tuna cikin jiki aka yi su, iska mai wucewa da bata dawowa. 40 Sau nawa suka yi ta tayar masa cikin jeji suka ɓata masa rai cikin hamada! 41 Akai akai suka tuhunci Allah suka cakuni Mai tsarki na Isra'ila. 42 Ba su tuna da ikonsa ba, yadda ya fanso su daga abokin gaba. 43 Lokacin da ya aikata alamominsa masu tsoratarwa cikin Masar da al'ajabansa cikin yankin Zowan. 44 Ya juyarda kogunan Masarawa su zama jini don kada su sha daga rafuffukansu. 45 Ya aika da cincirindon ƙudaje da suka cinye su da kwaɗi da suka mamaye ƙasar. 46 Ya bada amfaninsu ga fãra aikin hannun su kuma ga babe. 47 Ya lalata inabinsu da ƙanƙara itatuwansu masu bada 'ya'ya ga jaura. 48 Ya saukar da ƙanƙara ga garkunansu aradu kuma ta fãɗa akan dabbobinsu. 49 Ya zuba masu zafin fushinsa. Ya aika da fushi, hasala, da wahala kamar wakili mai kawo masifa. 50 Ya baje wa fushinsa hanya; bai barsu su rayu ba amma ya ba she su ga annoba. 51 Ya kashe dukkan 'ya'yan fari cikin Masar, ɗan farin ƙarfinsu cikin rumfunan Ham. 52 Ya fitar da mutanensa waje kamar tumaki ya bishe su cikin jeji kamar garke. 53 Ya kare su kuma ba su ji tsoro ba, amma teku ya dulmiyadda abokan gabarsu. 54 Daga nan ya kawo su kan iyakar ƙasarsa mai tsarki, zuwa tsaunin nan da hannun damansa ya saya. 55 Ya kori al'ummai daga gaban su ya raba masu gadonsu. Ya sa kabilun Isra'ila suka zauna cikin rumfunansu. 56 Duk da haka suka ƙalubalanci da tozartar da Allah Maɗaukaki kuma ba su kiyaye umarnansa ba. 57 Sun yi rashin aminci suka yi yaudara kamar ubanninsu; suka zama marasa abin dogaro kamar tanƙwararren baka. 58 Gama sun sa shi fushi da masujadansu kuma suka harzuƙa shi ga yin kishi da gumakansu. 59 Sa'ad da Allah ya ji wannan, ya hasala ya ƙi Isra'ila gaba ɗaya. 60 Ya yashe da wuri mai tsarki na Shilo, rumfar in da ya zauna a tsakiyar mutane. 61 Ya bari a ƙwace ƙarfinsa ya bada ɗaukakarsa a cikin hannun abokan gãba. 62 Ya miƙa mutanensa ga takobi, yayi fushi da abin gãdonsa. 63 Wuta ta cinye majiya ƙarfinsu, "yanmatansu kuma ba su sami waƙar aure ba. 64 Firistocinsu sun faɗi ta kaifin takobi, gwaurayensu kuma suka kasa yin kuka. 65 Sa'an nan sai Ubangiji ya farka sai ka ce mai tashi daga barci, kamar jarumi wanda ya fasa kuwwa saboda buguwa da ruwan inabi. 66 Ya kori magabtansa baya; ya sa su cikin kunya ta har abada. 67 Ya ƙi rumfar Yosef, bai kuma zaɓi kabilar Ifraim ba. 68 Ya zaɓi kabilar Yahuda da Tsaunin Sihiyona wanda yake ƙauna. 69 Ya gina tsatsarkan wurinsa kamar sammai, kamar duniya wadda ya kafa ta har abada. 70 Ya zaɓi Dauda, bawansa, ya ɗauke shi daga wurin tsaron tumaki. 71 Ya ɗauke shi daga bin tumaki da ƙananan su, ya kawo shi ya zama makiyayin Yakubu, mutanensa, da Isra'ila, abin gãdonsa. 72 Dauda yayi kiwonsu da mutuncin zuciyarsa, ya bishe su da gwanintar hannuwansa.
1 God, foreign nations have come into your inheritance;
they have defiled your holy temple;
they have turned Jerusalem into a heap of ruins.
2 They have given the dead bodies of your servants
as food to the birds of the skies,
the bodies of your faithful ones to the beasts of the earth.
3 They have shed their blood like water around Jerusalem,
and there was none to bury them.
4 We are objects of contempt to our neighbors,
mocking and derision to those who are around us.
5 How long, Yahweh? Will you stay angry forever?
How long will your jealous anger burn like fire?
6 Pour out your wrath on the nations
that do not know you
and on the kingdoms
that do not call upon your name.
7 For they have devoured Jacob
and laid waste his villages.
8 Do not hold the iniquities of our forefathers against us;
may your merciful actions come to us,
for we are very low.
9 Help us, God of our salvation,
for the sake of the glory of your name;
save us and forgive our sins
for your name's sake.
10 Why should the nations say,
"Where is their God?"
May the blood of your servants that was shed
be avenged on the nations before our eyes.
11 May the groans of the prisoners come before you;
with the greatness of your power keep the children of death alive.
12 Pay back into the laps of our neighboring countries seven times as much
as the contempt with which they have taunted you, Lord.
13 So we your people and sheep of your pasture
will give you thanks forever.
We will tell your praises
to all generations.
1 Ya Allah bãƙin alummai sun zo cikin gãdonka; sun kazantar da haikalinka maitsarki; sun maida Yerusalem ta zama tsibin kangaye. 2 Sun bada gawawwakin bayinka a matsayin abinci ga tsuntsayen sararin sama, jikkunan amintattun mutanenka ga dabbobin duniya. 3 Sun zubar da jininsu kamar ruwa kewaye da Yerusalem, ba wanda zai yi jana'izar su. 4 Mun zama abin ba'a ga makwabtanmu, ba'a da reni ga waɗanda ke kewaye damu. Har yaushe, Yahweh? Zaka yi ta fushi har abada? 5 Har yaushe kishin fushinka zai yi ta ci har abada? 6 Ka zubo da fushinka kan al'umman da basu san ka ba da bisa mulkokin da basu kira bisa sunanka ba. 7 Gama sun cinye Yakubu sun hallaka ƙauyukansa. 8 Kada kayi ta tunawa da zunubin kakanninmu har su shafe mu; bari ayyukan jinƙanka su zo kanmu, gama mun yi sanyi ƙwarai. 9 Ka taimake mu, ya Allah na cetonmu, domin ɗaukakar sunanka; ka cece mu ka yafe zunubanmu sabili da sunanka. 10 Don me al'ummai zasu ce, "Ina Allahn su?" Bari jinin bayinka da aka zubar yayi ramako akan al'ummai a idanunmu. 11 Bari nishin ɗaurarru ya zo gabanka; da girman ikonka ka tsare 'ya'yan waɗanda aka yanke wa mutuwa da rai. 12 Ya Ubangiji. Ka maida zagin da ƙasashe maƙwabtanmu suka zazzageka ka sau bakwai bisa cinyoyinsu. 13 Don haka mu mutanenka da tumakin makiyayarka zamu yi maka godiya har abada. Za mu faɗi yabbanka ga dukkan tsararraki.
1 Give ear, Shepherd of Israel,
you who lead Joseph like a flock;
you who sit above the cherubim,
shine on us!
2 In the sight of Ephraim and Benjamin and Manasseh,
stir up your power;
come and save us.
3 God, restore us;
make your face shine on us,
and we will be saved.
4 Yahweh God of hosts,
how long will you be angry at your people when they pray?
5 You have fed them with the bread of tears
and given them tears to drink in great quantities.
6 You make us an object of strife for our neighbors,
and our enemies laugh in mockery about us among themselves.
7 God of hosts, restore us;
make your face shine on us,
and we will be saved.
8 You brought a vine out of Egypt;
you drove out nations and transplanted it.
9 You cleared the land for it;
it took root and filled the land.
10 The mountains were covered with its shade,
the cedars of God by its branches.
11 It sent out its branches as far as the sea
and its shoots to the Euphrates River.
12 Why have you broken down its walls
so that all who pass by along the road pluck its fruit?
13 The boars out of the forest ruin it,
and the beasts of the field feed on it.
14 Turn back, God of hosts;
look down from heaven and take notice
and take care of this vine.
15 This is the root that your right hand planted,
the son that you have strengthened for yourself.
16 It has been burned and cut down;
they perish because of your rebuke.
17 May your hand be on the man of your right hand,
on the son of man whom you strengthened for yourself.
18 Then we will not turn away from you;
revive us, and we will call on your name.
19 Yahweh God of hosts, restore us;
make your face shine on us, and we will be saved.
1 Ka kasa kunne, Ya Makiyayi na Isra'ila, kai mai bida Yosef kamar tumaki; kai mai zama bisan Kerubim, ka haskaka a bisanmu! 2 A idon Ifraim da Benyamin da Manasse, ka motsa ikon ka; zo ka cece mu. 3 Ya Allah, ka maishe mu; ka sa fuskarka ta haskaka a bisanmu, mu kuwa zamu tsira. 4 Ya Yahweh Allah mai runduna, har yaushe zaka yi fushi da addu'ar mutanenka? 5 Ka ciyar dasu da gurasar hawaye ka basu hawaye mai yawa su sha. 6 Kasa mana wani abin da zamuyi jayayya da maƙwabtanmu a kansa, maƙiyanmu kuma suna yi mana dariya tsakaninsu. 7 Ya Allah mai runduna; ka dawo damu; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu tsira. 8 Ka fito da kuringa daga Masar; Ka kori al'ummai ka dasa ta. 9 Ka gyara kasa domin ta; ta kafa saiwa ta cika ƙasa. 10 Duwatsu sun rufe ta da inuwarta, Rassanta suna kama da itacen sida na Allah. 11 Ta miƙa rassanta har bakin teku tohonta kuma har bakin Kogin Yuferitis. 12 Don me ka rushe garunta har dukkan masu wucewa ta hanyar zasu tsinki 'ya'yanta. 13 Aladun kurmi sun batata, namomin jeji kuma suna kiwo cikin ta. 14 Ya Allah mai runduna; ka juyo, ka duba daga sama kayi la'akari ka kula da wannan kuringar. 15 Wannan itace sauyar daka dasa da hannunka na dama, reshen da kasa ya girma. 16 An ƙone shi da wuta an sare shi ƙasa; sun hallaka saboda tsautawarka. 17 Bari hannunka ya kasance bisa mutumin hannunka na dama, bisa ɗan mutum wanda kasa ya zama da karfi domin kanka. 18 Daga nan ba zamu juya daga gare ka ba; ka farkar da mu, mu kuwa zamu kira bisa sunanka. 19 Ya Yahweh, Allah mai runduna, ka dawo damu; kasa fuskarka ta haskaka a kanmu, ta haka zamu tsira.
1 Shout joyfullly to God our strength;
shout out for joy to the God of Jacob.
2 Sing a song and play the tambourine,
the pleasant harp with the lute.
3 Blow the ram's horn on the day of the new moon,
on the day of the full moon, when our feast day begins.
4 For it is a statute for Israel,
a decree given by the God of Jacob.
5 He issued it as a regulation in Joseph
when he went against the land of Egypt,
where I heard a voice that I did not recognize:
6 "I removed the burden from his shoulder;
his hands were freed from holding the basket.
7 In your distress you called out, and I helped you;
I answered you from a dark thundercloud.
I tested you at the waters of Meribah. Selah
8 Listen, my people, for I will warn you,
Israel, if you would only listen to me!
9 There must be no foreign god among you;
you must not worship any foreign god.
10 I am Yahweh your God,
who brought you out of the land of Egypt.
Open your mouth wide, and I will fill it.
11 But my people did not listen to my words;
Israel did not obey me.
12 So I gave them over to their own stubborn way
so that they might follow their own devices.
13 Oh, that my people would listen to me;
oh, that my people would walk in my paths.
14 Then I would quickly subdue their enemies
and turn my hand against their oppressors.
15 May those who hate Yahweh cringe in fear before him!
May they be humiliated forever.
16 I would feed Israel with the finest wheat;
I would satisfy you with honey out of the rock."
1 Ku raira da ƙarfi ga Allah karfinmu; ku tada muryar farinciki ga Allah na Yakubu. 2 Ku raira waƙa ku kaɗa ganga, garaya mai daɗi da molo. 3 Ku busa ƙahon rago a ranar tsayawar sabon wata, a ranar cikar wata, ranar da bukukuwanmu ke farawa. 4 Gama farilla ce ga Isra'ila, sharia da Allah na Yakubu ya bayar. 5 Ya bada ita a matsayin doka cikin Yosef lokacin da ya tafi gãba da kasar Masar, in da naji muryar da ban fahimta ba. 6 Na kawar da nauyin daga kafaɗarsa; an raba hannunsa daga ɗaukar kwando. 7 A cikin masifa ka yi kira, na taimake ka; Na amsa maka daga duhun tsawar girgije. Na gwada ka a bakin ruwayen Meriba. Selah 8 Ku saurara, mutanena, gama zan gargaɗe ku, zan so da kun saurare ni! 9 Kada wani bãƙon allah ya kasance a cikinku; baza kuyi sujada ga wani bãƙon allah ba. 10 Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya fito da ku daga kasar Masar. Ku wage bakinku, ni ma in cika shi. 11 Amma mutanena basu saurara ga maganata ba; Isra'ila bata yi mani biyayya ba. 12 Domin haka na bar su da taurinkansu domin suyi abin da suka ga dama. 13 Ina ma, mutanena zasu saurare ni; ina ma, mutanena zasu yi tafiya cikin tafarkuna. 14 Dana hanzarta mamaye abokan gabarsu in kuma juya hannuna akan masu zaluntar su. 15 Dama waɗanda suka ƙi Yahweh su faɗi cikin tsoro gabansa! Dama su ƙasƙanta har abada. Zan ciyar da Isra'ila da alkama mai kyau; 16 Zan ƙosarda ku da zuma daga cikin dutse."
1 God stands in the divine assembly;
in the midst of the gods he renders judgment.
2 How long will you judge unjustly
and show favoritism to the wicked? Selah
3 Give justice to the poor and fatherless;
maintain the rights of the afflicted and destitute.
4 Rescue the poor and needy;
take them out of the hand of the wicked.
5 They neither know nor understand;
they wander around in the darkness;
all the foundations of the earth crumble.
6 I said, "You are gods,
and all of you are sons of the Most High.
7 Nevertheless you will die like men
and fall like one of the princes."
8 Arise, God, judge the earth,
for you have an inheritance in all the nations.
1 Allah yana tsaye cikin taron jama'ar Allah; cikin tsakiyar alloli yana zartar da hukunci. 2 Har yaushe zaka yi hukuncin rashin gaskiya ka nuna kana goyon bayan masu mugunta? Selah 3 Ka kare talakawa da marasa mahaifa; ka kare hakkin masu shan azaba da marasa galihu. 4 Ka ceci fakirai da mabukata; ka fisshe su daga hannun mugu. 5 Basu da sani basu kuwa da fahimta; suna kai da komowa cikin duhu; dukkan harsasun duniya sun rugurguje. 6 Na ce, ku alloline, dukkan ku kuma 'ya'yan Maɗaukaki ne. 7 Duk da haka za ku mutu kamar mutane kuma ku faɗi kamar ɗaya daga cikin sarakuna." 8 Ya Allah, ka tashi, ka shar'anta duniya, gama kana da gãdo cikin dukkan al'ummai.
1 God, do not be silent!
Do not ignore us and remain unmoved, God.
2 Look, your enemies are making a commotion,
and those who hate you have raised their heads.
3 They make shrewd plans against your people
and plan together against your protected ones.
4 They have said, "Come, and let us destroy them as a nation.
Then the name of Israel will no longer be remembered."
5 They schemed together with one strategy;
they made an alliance against you—
6 the tents of Edom and the Ishmaelites,
of Moab and the Hagrites, 7 Byblos, [1] Ammon, Amalek;
and also Philistia and the inhabitants of Tyre.
8 Assyria also has joined with them;
they have become an arm for the descendants of Lot. Selah
9 Do to them as you did to Midian,
as you did to Sisera and to Jabin at the Kishon River.
10 They perished at Endor
and became like manure for the earth.
11 Make their nobles like Oreb and Zeeb,
and all their princes like Zebah and Zalmunna.
12 They said, "Let us take for ourselves
the pastures of God."
13 My God, make them like the whirling dust,
like chaff before the wind,
14 like the fire that burns the forest,
and like the flame that sets the mountains on fire.
15 Chase them with your strong wind,
and terrify them with your windstorm.
16 Fill their faces with shame
so that they might seek your name, Yahweh.
17 May they be put to shame and be terrified forever;
may they perish in disgrace.
18 Then they will know that you alone,
whose name is Yahweh,
are the Most High over all the earth.
1 Ya Allah, kada kayi shiru! Kada ka manta damu kada kuma kaƙi taimakon mu, ya Allah. 2 Duba, abokan gabarka suna tada hankali, su da suka ƙi ka sun tada kansu. 3 Sun shirya wa mutanenka makirci suna ƙulli gaba da waɗanda ka kãre. 4 Suka ce, "Ku zo mu hallaka su a matsayin al'umma. Daga nan ba za'a ƙara tunawa da sunan Yahweh ba. 5 "Sun ƙulla Makirci tare dabararsu ɗaya ce; don suyi gãba dakai suka yi ƙawance. 6 Wannan ya haɗa da rumfunan Idom da na Ishma'ilawa, da mutanen Mowab da Hagarawa, waɗanda suka ƙulla tare da 7 Gebal, Ammon, Amalek; ya kuma haɗa da Filistiya da mazaunan Taya. 8 Assuriya kuma ta hada kai dasu; suna taimakon zuriyar Lot. Selah 9 Kayi masu kamar yadda kayi wa Midiyan kamar yadda kayi da Sisera da Yabin a Kogin Kishon. 10 Suka hallaka a Endo suka zama kamar taki domin ƙasa. 11 Ka sa shugabanninsu sun zama kamar Oreb da Zib, da dukkan sarakunansu kamar Ziba da Zalmunna. 12 Suka ce, "Bari mu ɗaukar wa kanmu makiyayar Allah." 13 Ya Allahna, ka maishe su kamar ƙurar guguwa, kamar ƙaiƙai gaban iska, 14 kamar wuta mai cin kurmi, kamar harshen wuta mai kama duwatsu. 15 Ka koresu da iskarka mai ƙarfi, ka razanar dasu da guguwar hadari. 16 Ka cika fuskokinsu da kunya domin su nemi sunanka, Ya Yahweh, 17 bari su sha kunya su firgita har abada; dama su lalace cikin kunya. 18 Daga nan zasu sani kai kaɗai ne, Yahweh, kai ne Maɗaukaki bisa dukkan duniya.
1 How lovely is the place where you live,
Yahweh of hosts!
2 I long for the courts of Yahweh;
my desire for it has made me exhausted.
My heart and all of my being
shout for joy to the living God.
3 Even the sparrow has found herself a house
and the swallow a nest for herself
where she may lay her young
near your altars, Yahweh of hosts,
my King, and my God.
4 Blessed are they who live in your house;
they praise you continually. Selah
5 Blessed is the man whose strength is in you,
in whose heart are the highways up to Zion.
6 As they go through the Valley of Tears
they make it a place of springs.
The early rains cover it with blessings. [1]
7 They go from strength to strength;
every one of them appears before God in Zion.
8 Yahweh God of hosts, hear my prayer;
give ear, God of Jacob! Selah
9 God, watch over our shield;
show concern for your anointed.
10 For one day in your courts is better
than a thousand elsewhere.
I would rather be a doorkeeper in the house of my God,
than to live within the tents of the wicked.
11 For Yahweh God is our sun and shield;
Yahweh will give grace and glory;
he does not withhold any good thing
from those who walk in integrity.
12 Yahweh of hosts,
blessed is the man who trusts in you.
1 Ina misalin ƙaunar wurin da kake zaune, Yahweh mai runduna! 2 Ina marmarin harabun Yahweh, marmarin da nake da shi dominsa yasa na suƙe. Zuciyata da dukkan kome nawa ya kira ga Allah mai rai. 3 Har tsaddu ta samar wa kanta gida mashillira ta yi wa kanta sheka inda zata ajiye 'ya'yanta kusa da bagadanka, Yahweh mai runduna, sarkina, Allahna kuma. 4 Masu albarkane waɗanda suka zauna cikin gidanka, zasu yita ci gaba da yabonka. Selah 5 Mai albarkane mutumin da ƙarfinsa yana cikinka, wanda zuciyarsa ke marmarin zuwa Sihiyona. 6 Cikin ratsawa zuwa kwarin Hawaye, sun iske maɓulɓulan ruwa domin sha. Ruwan farko ya rufe shi da albarku. 7 Suna tafiya daga karfi zuwa karfi; kowanne ɗayan su ya bayyana gaban Allah cikin Sihiyona. 8 Yahweh Allah mai runduna, kaji addu'ata; Allahn Yakubu, ka saurari abin da nake cewa! Selah 9 Ya Allah, ka duba garkuwarmu; ka nuna damuwarka ga shafaffenka. 10 Gama yini ɗaya cikin harabunka ya fi dubu a wani wuri. Na gwammace in zama mai tsaron ƙofa cikin gidan Allahna, da in zauna tsakanin rumfuna na masu mugunta. 11 Gama Yahweh Allah shi ne ranar mu da garkuwa; 12 Yahweh zai bada alheri da ɗaukaka; ba ya hana wani abu mai kyau ga waɗanda suke tafiya cikin gaskiya. Yahweh mai runduna, mai albarkane mutumin da ya ke dogara gare ka.
1 Yahweh, you have shown favor to your land;
you have restored the well-being of Jacob.
2 You have forgiven the iniquity of your people;
you have covered all their sin. Selah
3 You have withdrawn all your wrath;
you have turned back from your hot anger.
4 Restore us, God of our salvation,
and let go of your displeasure with us.
5 Will you be angry with us forever?
Will you remain angry throughout future generations?
6 Will you not revive us again?
Then your people will rejoice in you.
7 Show us your covenant faithfulness, Yahweh;
grant us your salvation.
8 I will listen to what Yahweh God says,
for he will make peace with his people, his faithful ones.
Yet they must not turn again to foolish ways.
9 Surely his salvation is near to those who fear him;
then glory will remain in our land.
10 Steadfast love and faithfulness have met together;
righteousness and peace have kissed each other.
11 Trustworthiness springs up from the ground,
and righteousness looks down from the sky.
12 Yes, Yahweh will give his good blessings,
and our land will yield its crops.
13 Righteousness will go before him
and make a way for his footsteps.
1 Yahweh ka nuna wa ƙasarka tagomashi; ka dawo da lafiya da arzikin Yakubu. 2 Ka yafe zunubin mutanenka; ka rufe dukkan zunubinsu. 3 Ka janye dukkan fushinka; ka juya baya daga zafin fushinka. 4 Ka dawo damu, Allahn cetonmu, kasa rashin jindaɗinka tare da mu ya wuce. 5 Zaka yi ta fushi da mu har abada? Zaka yi ta yin fushi har ga tsararraki masu zuwa? 6 Ba zaka sake falkar damu ba? Daga nan mutanenka za suyi murna a cikin ka. 7 Ka nuna ma na amincin alƙawarinka ya Yahweh, ka bamu cetonka. 8 Zan saurari abin da Yahweh Allah zai ce, gama zai kawo salama ga mutanensa, amintattun mabiyansa. duk da haka ba zasu koma ga bin hanyoyinsu na wauta ba. 9 Hakika cetonsa yana kusa da masu tsoronsa; daga nan ɗaukaka zata zauna cikin ƙasarmu. 10 Alƙawarin aminci da gaskiya sun haɗu tare; adalci da salama sun yi wa juna sumba. 11 Gaskiya tana tsirowa daga ƙasa, adalci yana kallo daga sama. 12 I, Yahweh zai ba da albarku masu kyau, ƙasarmu zata bada amfaninta. 13 Adalci zai tafi gabansa kuma zai yi hanya domin sawayensa.
1 Listen, Yahweh, and answer me,
for I am poor and needy.
2 Protect me, for I am faithful;
my God, save your servant who trusts in you.
3 Be merciful to me, Lord,
for I cry out to you all day long.
4 Make your servant glad,
for to you, Lord, I lift up my soul.
5 You, Lord, are good, and ready to forgive,
abounding in steadfast love to all those who cry out to you.
6 Give ear, Yahweh, to my prayer;
hear the sound of my pleas.
7 In the day of my trouble I call on you,
for you will answer me.
8 There is no one who compares to you among the gods, Lord.
There are no deeds like your deeds.
9 All the nations that you have made
will come and bow before you, Lord.
They will honor your name.
10 For you are great and do wonderful things;
you only are God.
11 Teach me your ways, Yahweh.
Then I will walk in your truth.
Unite my heart
to reverence your name.
12 Lord my God, I will praise you with my whole heart;
I will glorify your name forever.
13 For great is your covenant faithfulness toward me;
you have rescued my life from the depths of Sheol.
14 God, the arrogant have risen up against me.
A company of violent men seek my life.
They have no regard for you.
15 But you, Lord, are a merciful and gracious God,
slow to anger, and abounding in steadfast love and faithfulness.
16 Turn toward me and have mercy on me;
give your strength to your servant;
save the son of your servant woman.
17 Show me a sign of your favor.
Then those who hate me will see it and be put to shame
because you, Yahweh, have helped me and comforted me.
1 Ka saurara, Yahweh, ka kuma amsa mani, domin ni matalauci ne, wanda aka tsanantawa. 2 Ka kare ni domin ina biyayya, ya Allahna, ka ceci bawanka wanda ya ke dogara a gare ka. 3 Ka yi mani jinƙai, ya Ubangiji, don a gare ka nake kuka dukkan yini. 4 Kasa bawanka yayi murna domin a gare ka nayi addu'a ya Ubangiji. 5 Ubangiji, kai nagari ne, kuma kana shirye kayi gafara. Kana kuma nuna jinƙai ga duk waɗanda suka yi kuka gare ka. 6 Yahweh, ka ji addu'ata, ka kuma ji muryar roƙona. 7 A ranar masifata nayi kira gare ka, domin zaka amsa mani. 8 Ya Ubangiji ba wanda za a kwatanta shi da kai a cikin alloli, ba ayyukan da za a kwatanta su da naka. 9 Dukkan al, umman da kayi zasu zo su rusuna maka. Za su girmama sunanka. 10 Domin kana da girma kana kuma yin abubuwan al'ajabi, kai kaɗai ne Allah. 11 Ka koya mani tafarkinka Yahweh. Sa'an nan zan yi tafiya cikin gaskiyarka. Ka haɗa zuciyata ta girmamaka. 12 Ubangiji Allahna zan yabe ka da dukkan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada. 13 Domin alƙawarinka mai aminci yana da girma a gare ni, domin ka ceto raina daga zurfafan Lahira. 14 Ya Allah marasa hankali sun tasar mani. Ƙungiyar masu husuma sun tasar mani suna neman raina, ba su kula da kai ba. 15 Amma kai, Ubangiji, Allah ne mai jinƙai da alheri, mai jinkirin fushi, mai mayalwacin alƙawari mai aminci da kuma madogara. 16 Ka juyo wurina kayi mani jinƙai; ka bada ƙarfinka ga bawanka; ka ceci ɗan baiwarka. 17 Ka nuna mani alamar jinƙanka. Sa'an nan waɗanda ke ƙi na zasu gani su kunyata saboda kai, Yahweh, ka taimake ni ka kuma ta'azantar dani.
1 On the holy mount stands the city he founded;
2 Yahweh loves the gates of Zion
more than all the tents of Jacob.
3 Glorious things are said of you,
city of God. Selah
4 "I mention Rahab and Babylon to my followers.
See, there are Philistia, and Tyre, along with Cush—
and will say, 'This one was born there.'"
5 Of Zion it will be said,
"Each of these was born in her;
and the Most High himself will establish her."
6 Yahweh writes in the census book of the nations,
"This one was born there." Selah
7 So also the singers and the dancers say together,
"All my fountains are in you."
1 Akan dutse mai tsarki birninsa da ya samo ya tsaya; 2 Yahweh yana ƙaunar ƙofofin Sihiyona fiye da rumfuna na Yakubu. 3 An faɗi maɗaukakan abubuwa game da kai birnin Allah. Selah. 4 Na ambaci Rahab da Babila ga masu bi na. Duba, akwai Filistiya, da Taya, tare da Itofiya- kuma zasu ce, 'Wannan an haife shi a can.'" 5 Ga Sihiyona za'a ce, "Dukkan wɗannan an haife su a cikinta, kuma Mafi Girma dukka da kansa zai kafa ta." 6 Yahweh ya rubuta a cikin littafin ƙidaya na al'ummai, "Wannan an haife shi a can." Selah 7 Haka kuma mawaƙa da masu rawa suka faɗa tare, "Dukkan maɓulɓulaina suna cikinka."
1 Yahweh, God of my salvation,
I cry out day and night before you.
2 Listen to my prayer;
pay attention to my cry.
3 For I am filled with troubles,
and my life has reached Sheol.
4 People treat me like those who go down into the pit;
I am a man with no strength.
5 I am free among the dead;
I am like the dead who lie in the grave,
about whom you care no more
because they are cut off from your power.
6 You place me in the lowest part of the pit,
in the dark and deep places.
7 Your wrath lies heavy on me,
and all your waves crash over me. Selah
8 Because of you, my acquaintances avoid me.
You have made me an abomination to them.
I am hemmed in and I cannot escape.
9 My eyes grow weary from trouble;
All day long I call out to you, Yahweh;
I spread out my hands to you.
10 Will you do wonders for the dead?
Will those who have died rise and praise you? Selah
11 Will your covenant faithfulness be proclaimed in the grave,
your faithfulness in the place of the dead?
12 Will your wonderful deeds be known in the darkness,
or your righteousness in the place of forgetfulness?
13 But I cry to you, Yahweh;
in the morning my prayer comes before you.
14 Yahweh, why do you reject me?
Why do you hide your face from me?
15 I have always been afflicted and on the verge of death since my youth.
I have suffered from your terrors;
I am in despair.
16 Your burning anger has passed over me,
and your terrifying deeds have annihilated me.
17 They surround me like water all the day long;
they have all encircled me.
18 You have removed every friend and acquaintance from me.
My only acquaintance is the darkness.
1 Yahweh, Allah na cetona, Na yi kuka a gabanka dare da rana. 2 Ka ji addu'ata, ka saurari kukana. 3 Domin na cika da damuwoyi, raina kuma ya kai Lahira. 4 Mutane sun ɗauke ni kamar waɗanda suka faɗa rami; Mutumin da ba shi da ƙarfi. 5 An yi watsi da ni a cikin matattu; Ina kama da matacce dake kwance a kabari, game da wanda ka daina kula da shi saboda an datse su daga ikonka. 6 Ka ajiye ni a wuri mafi ƙasƙanci na cikin rami, a wuri mai zurfi da kuma duhu. 7 Fushinka yayi nauyi a kaina, kuma dukkan rigyawarka tabi ta kaina. Selah 8 Saboda kai, abokan tarayyata suka yashe ni. Ka maishe ni abin rawar jiki a gare su. An shinge ni a ciki ba kuma zan tsira ba. 9 Idanuna sun gaji da damuwa; Dukkan yini ina kira gare ka, Yahweh; na buɗe hannuwana gare ka. 10 Ko zaka yi mu'ujuzai ga matattu? Ko waɗanda suka mutu zasu tashi su yabe ka? Selah 11 Ko za'a yi shelar alƙawarin amincinka a kabari, amincinka kuma a wurin matattu? 12 Ko za'a san ayyukanka na al'ajibai a cikin duhu, ko kuma adalcinka a wurare na mantuwa? 13 Amma nayi kuka gare ka, Yahweh; da safe addu'ata tana zuwa gare ka. 14 Yahweh me yasa ka ƙi ni? Me yasa ka ɓoye fuskarka daga gare ni? 15 Har kullum an tsananta mani kamar a hallaka ni tun daga ƙuruciyata. Na sha hukuncin horonka ina cikin fargaba. 16 Ayyukanka na fushi sun bi ta kaina, kuma ayyukanka masu ban razana sun kawar da ni. 17 Sun kewaye ni kamar ruwa a dukkan yini; dukkan su sun kewaye ni. 18 Ka kawar da abokaina da duk waɗanda suka shaƙu dani daga gare ni. Wanda ya shaƙu dani duhu ne kaɗai.
1 I will sing of Yahweh's acts of covenant faithfulness forever.
I will proclaim your truthfulness to future generations.
2 For I have said, “Covenant faithfulness has been established forever;
your truthfulness you have established in the heavens.”
3 You said, “I have made a covenant with my chosen one,
I have made an oath to David my servant:
4 ‘I will establish your descendants forever,
and I will establish your throne through all generations.‘” Selah
5 The heavens praise your wonders, Yahweh;
your truthfulness is praised in the assembly of the holy ones.
6 For who in the skies can be compared to Yahweh?
Who among the sons of the gods is like Yahweh?
7 He is a God who is greatly honored in the council of the holy ones
and is awesome among all who surround him.
8 Yahweh God of hosts,
who is strong like Yah? [1]
Your truthfulness surrounds you.
9 You rule the raging sea;
when the waves surge, you calm them.
10 You crushed Rahab as one who is killed.
You scattered your enemies with your strong arm.
11 The heavens belong to you, and the earth also.
You established the world and all it contains.
12 You created the north and the south.
Tabor and Hermon rejoice in your name.
13 You have a mighty arm
and a strong hand, and your right hand is high.
14 Righteousness and justice are the foundation of your throne.
Steadfast love and faithfulness come before you.
15 Blessed are the people who know the joyful sound!
Yahweh, they walk in the light of your face.
16 They rejoice in your name all day long,
and in your righteousness they exalt you.
17 You are their glorious strength,
and by your favor our horn is exalted.
18 For our shield belongs to Yahweh;
our king belongs to the Holy One of Israel.
19 Long ago you spoke in a vision
to your faithful ones; [2]
you said, "I have set a crown on a mighty one." [3]
I have raised up one chosen from among the people.
20 I have chosen David my servant;
with my holy oil have I anointed him.
21 My hand will support him;
my arm will strengthen him.
22 No enemy will deceive him;
no son of wickedness will oppress him.
23 I will crush his enemies before him;
I will kill those who hate him.
24 My truth and my covenant faithfulness will be with him;
by my name his horn will be exalted.
25 I will place his hand over the sea
and his right hand over the rivers.
26 He will call out to me, 'You are my Father,
my God, and the rock of my salvation.'
27 I also will place him as my firstborn son,
the most exalted of the kings of the earth.
28 I will extend my covenant faithfulness to him forever;
and my covenant with him will be secure.
29 I will make his descendants endure forever
and his throne as enduring as the skies above.
30 If his children abandon my law
and do not walk in my regulations,
31 if they break my rules
and do not keep my commands,
32 then will I punish their rebellion with a rod
and their iniquity with blows.
33 But I will not remove my steadfast love from him
or be unfaithful to my promise.
34 I will not break my covenant
or change the words of my lips.
35 Once and for all I have sworn by my holiness—
I will not lie to David:
36 his descendants will continue forever
and his throne as long as the sun before me.
37 It will be established forever like the moon,
the faithful witness in the sky." Selah
38 But you have refused and rejected;
you have been angry with your anointed king.
39 You have renounced the covenant of your servant.
You have desecrated his crown on the ground.
40 You have broken down all his walls.
You have ruined his strongholds.
41 All who pass by have robbed him.
He has become the scorn of his neighbors.
42 You have raised the right hand of his enemies;
you have made all his enemies rejoice.
43 You turn back the edge of his sword
and have not made him stand when in battle.
44 You have brought his splendor to an end;
you have brought down his throne to the ground.
45 You have shortened the days of his youth.
You have covered him with shame. Selah
46 How long, Yahweh? Will you hide yourself forever?
How long will your anger burn like fire?
47 Oh, think about how short my time is,
and for what vanity you have created all the children of mankind!
48 Who can live and not die,
or rescue his own life from the hand of Sheol? Selah
49 Lord, where are your former acts of covenant faithfulness
that you swore to David in your truthfulness?
50 Call to mind, Lord, the mocking directed against your servants
and how I bear in my heart so many insults from the nations.
51 Your enemies hurl insults, Yahweh;
they mock the footsteps of your anointed one.
52 Blessed be Yahweh forever.
Amen and Amen.
1 Zan raira yabon ayyukan alƙawarin amincin Yahweh na har abada, Zan yi shelar gaskiyarka ga tsararraki masu zuwa. 2 Domin na ce "Anyi amintaccen alƙawari na har abada; ka kuma kafa gaskiyarka a cikin sammai." 3 Na yi alƙawari da zaɓaɓɓena, nayi alƙawari ga Dauda bawana. 4 Zan kafa zuriyarka har abada, kuma zan kafa kursiyinka a dukkan tsararraki." Selah 5 Sammai na yabon al'ajibanka, Yahweh; a na yabon gaskiyarka a taron tsarkaka. 6 Domin da wane ne za a kwatanta shi da Yahweh a sammai? Wane ne za a kwatanta shi da Yahweh? 7 Shi Allah ne dake da girmamawa a taron tsarkaka yana kuma da kwarjini ga dukkan waɗanda suka kewaye shi. 8 Yahweh Allah mai runduna, wa keda ƙarfi kamar ka? amincinka ya kewaye ka. 9 Kana mulkin haukan teku; lokacin da ambaliyoyi su ka tashi ka kwantar da su. 10 Ka buge Rahab kamar wadda aka kashe. Ka warwatsa maƙiyanka da ƙarfin damtsenka. 11 Sammai naka ne, haka kuma duniya. Ka hallici duniya da dukkan abin da ke cikin ta. 12 Ka hallici arewa da kudu. Tabor da Harmon na murna a cikin sunanka. 13 Kana da damtse mai iko da kuma hannu mai ƙarfi, hannunka na dama kuma yana da tsayi. 14 Aikin adalci da adalci su ne ginshiƙan mulkinka. Alƙawari mai aminci da kuma dogara daga gare ka suke zuwa. 15 Masu albarka ne waɗanda ke yi maka sujada! Yahweh, suna tafiya a cikin hasken fuskarka, 16 Suna murna da sunanka dukkan yini. Ayyukan adalcinka kuma sun ɗaukaka ka. 17 Kai ne ƙarfin ikonsu, ta wurin jinƙanka kuma mun yi nasara. 18 Domin garkuwoyinmu na Yahweh ne; sarkinmu kuma na Mai tsarki na Isra'ila ne. 19 Tun da daɗewa kayi magana da tsarkakanka ta wurin wahayi; kace "Na sa kambi bisa mai iko; Na tayar da wani da aka zaɓa daga cikin mutane. 20 Na zaɓi Dauda bawana, da maina na keɓe shi. 21 Hannuna zai taimake shi. Damtsena kuma zai ƙarfafa shi. 22 Ba maƙiyin da zai yaudare shi; ba kuma ɗan magabcin da zai ƙuntata masa. 23 Zan buge maƙiyansa a gabansa, masu ƙin sa kuma zan hallaka su. 24 Gaskiyata da alƙawarin amincina zai kasance tare da shi, ta wurin sunana zai yi nasara. 25 Zan ɗora hannunsa a kan teku, hannunsa na dama kuma bisa koguna. 26 Zai yi kira gare ni yace kai ne ubana, 'Kai ne Ubana kuma Allahna, da kuma dutsen cetona.' 27 Zan ɗora shi a matsayin ɗan farina, mafi ɗaukaka a cikin sarakunan duniya. 28 Zan tsawaita alƙawarin amincina a gare shi har abada; zan kuma riƙe alƙawarina da shi. 29 Zan kafa zuriyarsa har abada, mulkinsa kuma zai kai har sammai. 30 Idan 'ya'yansa suka yi watsi da shari'una suka kuma yi rashin biyayya ga sharuɗɗana, 31 idan kuma sun karya dokokina basu kuma kiyaye umarnaina ba, 32 to sai in hori rashin biyayyarsu da sandar ƙarfe laifofinsu kuma da nushe-nushe. 33 Amma ba zan janye madawammiyar ƙaunata ba daga gare shi ko kuma in yi rashin aminci a kan alƙawarina ba, 34 Ba zan karya alƙawarina ba ko kuma in canza maganganun leɓuna na ba. 35 Sau ɗaya tak na rantse da tsarkina-Ba zan yiwa Dauda ƙarya ba: 36 zuriyarsa zata ɗore har abada mulkinsa kuma zai zama kamar rana a gabana. 37 Za a kafa shi har abada kamar wata, amintaccen mashaidi a sararin sama." Selah 38 Amma ka ƙi ka kuma yi watsi; kana kuma fushi da shafaffen sarki. 39 Ka kuma musunta alƙawarin bawanka. Ka ƙazamtar da rawaninsa a ƙasa. 40 Ka kuma rushe katangunsa dukka. Ka kuma mayar da ƙarfafan kagarunsa kufai. 41 Duk masu wucewa suka yi masa ƙwace. Ya zama abin ƙyama a cikin maƙwabta. 42 Ka tayar da hannun damar maƙiyansa; ka kuma sa dukkan maƙiyansa suyi farinciki. 43 Ka juya takobinsa ka kuma hana shi ya tsaya a lokacin yaƙi. 44 Ka kawo ƙarshen martabarsa; ka kuma karya mulkinsa 45 Ka gajarta kwanakin ƙuruciyarsa. Ka kuma rufe shi da kunya. Selah 46 Yahweh har yaushe? Ko zaka ɓoye kanka, har abada? Har yaushe zaka bar fushinka yayi ta ƙuna kamar wuta? 47 Oh, ka yi tunanin yadda gajartar lokacina ya ke, da kuma rashin amfanin yadda ka hallici dukkan mutane! 48 Wane ne zai rayu ba zai mutu ba, ko kuma ya iya kuɓutar da ransa daga Lahira? Selah 49 Ya Ubangiji, ina ayyukanka na dã a kan alƙawarin amincinka da ka rantsewa Dauda a cikin gaskiyarka? 50 Ka tuna ya Ubangiji da rainin da aka yi wa bayinka da kuma yadda na ji a zuciyata ire-iren cin mutunci daga al'ummai. 51 Maƙiyanka suna nuna wulaƙanci, Yahweh; suna wulaƙanta sawayen keɓaɓɓenka. 52 Albarka ta tabbata ga Yahweh har abada. Amin da Amin. Littafi na Huɗu
1 Lord, you have been our refuge
throughout all generations.
2 Before the mountains were formed,
or you formed the earth and the world,
from everlasting to everlasting, you are God.
3 You return man to dust,
and you say, "Return, you descendants of mankind."
4 For a thousand years in your sight
are as yesterday when it is past,
and as a watch in the night.
5 You sweep them away as with a flood and they sleep;
in the morning they are like the grass that sprouts up.
6 In the morning it blooms and grows up;
in the evening it withers and dries up.
7 Truly, we are consumed in your anger,
and in your wrath we are terrified.
8 You have set our iniquities before you,
our hidden sins in the light of your presence.
9 Our life passes away under your wrath;
our years quickly pass like a sigh.
10 Our years are seventy,
or even eighty if we are healthy;
but even our best years are marked by trouble and sorrow.
Yes, they pass quickly, and we fly away.
11 Who knows the power of your anger,
and your wrath that is equal to the fear of you?
12 So teach us to consider our life
so that we might gain a heart of wisdom.
13 Turn back, Yahweh! How long will it be?
Have pity on your servants.
14 Satisfy us in the morning with your covenant faithfulness
so that we may rejoice and be glad all our days.
15 Make us glad in proportion to the days you afflicted us
and to the years we have experienced trouble.
16 Let your servants see your work,
and let our children see your majesty.
17 May the favor of the Lord our God be ours;
prosper the work of our hands;
indeed, prosper the work of our hands.
1 Ubangiji kai ne mafakarmu a dukkan tsararraki. 2 Kafin a kafa duwatsu, ko kuma ka hallici duniya da abin dake cikinta, har abada abadin, kai Allah ne. 3 Ka kan komar da mutum ƙura, ka ce "ku koma ku zuriyar ɗan adam." 4 Domin shekaru dubu a gare ka kamar jiya ne data wuce, kamar kuma sa'ar tsaro ce ta dare. 5 Ka share su kamar da rigyawa sun kuma yi barci; da safe suna kama da ciyayi da suka yi girma. 6 Da safe sukan yi yabanya suyi girma; da yamma kuma su kan yanƙwane su bushe. 7 Hakika, an cinye mu a cikin fushinka, a cikin fushinka kuma mun gigice. 8 Ka jejjera zunubanmu a gabanka, laifofinmu na ɓoye kuma kasa su a hasken gabanka. 9 Ran mu yana shuɗewa a ƙarƙashin fushinka; 10 shekarunmu kuma sun wuce da sauri kamar ajiyar zuciya. Shekarunmu saba'in ne, ko kuma tamanin in muna da lafiya; amma koma da shekarunmu mafiya kyau suna cike da damuwa da baƙinciki. Hakika, sukan wuce da sauri sai kuma mu ɓace. 11 Wa ya san ƙarfin fushinka, da kuma fushinka da ke dai-dai da tsoronka? 12 ka koya mana yadda zamu yi la'akari da rayuwarmu domin mu yi rayuwa cikin hikima. 13 Juya, Yahweh! Har yaushe zai zama? Ka ji tausayin bayinka. 14 Ka ƙosar da mu da alƙawarin amincinka da safe domin muyi farinciki a cikin dukkan kwanakinmu. 15 Ka samu muyi murna gwargwadon kwanakin daka azabtar damu da kuma shekarun da muka fuskanci matsala. 16 Ka bar bayinka suga aikinka, kuma ka bar 'ya'yanmu suga darajarka. 17 Da ma jinƙan Ubangiji Allahnmu ya zama namu; ka wadata aikin hannuwanmu; hakika, ka wadata aikin hannuwanmu.
1 He who lives in the shelter of the Most High
will stay in the shadow of the Almighty.
2 I will say of Yahweh, "He is my refuge and my fortress,
my God, in whom I trust."
3 For he will rescue you
from the snare of the hunter
and from the destructive plague.
4 He will cover you with his wings,
and under his wings you will find refuge.
His faithfulness is a shield and protection.
5 You will not be afraid of terror in the night,
or of the arrow that flies by day,
6 or of the plague that stalks in the darkness,
or of the destruction that lays waste at noon.
7 A thousand may fall at your side
and ten thousand at your right hand,
but it will not reach you.
8 You will only observe
and see the punishment of the wicked.
9 For Yahweh is my refuge!
Make the Most High your refuge also.
10 No evil will overtake you;
no affliction will come near your tent.
11 For he will put his angels in charge over you,
to guard you in all your ways.
12 They will lift you up with their hand
so that you will not hit your foot on a stone.
13 You will crush lions and asps under your feet;
you will trample on young lions and serpents.
14 Because he delights in me, I will rescue him.
I will protect him because he acknowledges my name.
15 When he calls to me, I will answer him.
I will be with him in trouble;
I will give him victory and will honor him.
16 I will satisfy him with the length of his days,
and show him my salvation.
1 Wanda ya ke rayuwa a bukkar Mafi Ɗaukaka zai zauna a inuwar Mai Iko Dukka. 2 Zan ce da Yahweh, "Shi ne mafakata da kagarata, Allahna, wanda na dogara a gare shi." 3 Domin zai kuɓutar da kai daga wayon tarkon maharbi kuma daga annoba mai hallakarwa. 4 Zai rufe ka da fukafukansa, kuma a ƙarƙashin fukafukansa zaka sami mafaka. Madogararsa garkuwa ce da kuma kariya. 5 Ba za ka ji tsoron masifa ba da dare, ko kuma kibiyoyin dake shawagi da rana. 6 Ko kuma annobar dake aukowa da dare ba. 7 Ko cutar dake samuwa da tsakar rana ba. Dubu zasu faɗi a gefenka dubu goma kuma a hannunka na dama, amma ba zasu iso wurinka ba. 8 Zaka duba ne kawai kaga hukuncin da za'a yiwa miyagu, 9 Domin Yahweh ne mafakata! Kuma ka maida Maɗaukaki mafakarka. 10 Ba mugun abin da zai same ka; ba wani abu mai cutarwa da zai kusanci gidanka. 11 Domin zai umarci mala'ikunsa su kare ka, su kuma yi tsaronka a cikin dukkan hanyoyinka. 12 Zasu tayar da kai tsaye da hannunsu domin kada kayi tuntuɓe a kan dutse. 13 Zaka hamɓare zãkuna da damisoshi a ƙarƙashin ƙafafunka; zaka tattake 'yan zãkoki da kuma macizai. 14 Saboda ya sadaukar da kansa gare ni, zan cece shi. Zan kare shi saboda yana yi mani biyayya. 15 Sa'ad da yayi kira gare ni zan amsa masa. Zan kasance tare da shi a cikin masifa; Zan ba shi nasara zan kuma girmama shi. 16 Zan ƙosar da shi da tsawon rai in kuma nuna masa cetona.
1 It is a good thing to give thanks to Yahweh
and to sing praises to your name, Most High,
2 to proclaim your covenant faithfulness in the morning
and your truthfulness every night,
3 with a lute of ten strings
and the resounding music of the harp.
4 For you, Yahweh, have made me glad through your deeds.
I will sing for joy because of the deeds of your hands.
5 How great are your deeds, Yahweh!
Your thoughts are very deep.
6 A brutish person does not know,
nor does a fool understand this:
7 When the wicked sprout like the grass,
and even when all those who behave wickedly thrive,
still they are doomed to eternal destruction.
8 But you, Yahweh, will reign forever.
9 Indeed, look at your enemies, Yahweh!
Indeed, look at your enemies. They will perish!
All those who behave wickedly will be scattered.
10 You have lifted up my horn like the horn of the wild ox;
I am anointed with fresh oil.
11 My eyes have seen the downfall of my enemies;
my ears have heard of the doom of my evil foes.
12 The righteous will flourish like the palm tree;
they will grow like a cedar in Lebanon.
13 They are planted in the house of Yahweh;
they flourish in the courts of our God.
14 They bear fruit even when they are old;
they stay fresh and green,
15 to proclaim that Yahweh is just.
He is my rock, and there is no unrighteousness in him.
1 Abu mai kyau ne a yi godiya ga Yahweh, a kuma yi waƙar yabo ga sunanka, Maɗaukaki, 2 a kuma yi shelar alƙawarin amincinka da safe gaskiyarka kuma kowanne dare, 3 da garaya mai tsarkiya goma da kuma kayan kaɗe-kaɗe masu daɗi. 4 Domin kai, Yahweh, kasa ni murna ta wurin ayyukanka. Zanyi waƙar farinciki saboda ayyukan hannuwanka. 5 Ina misalin girman ayyukanka, Yahweh! Tunane-tunanenka suna da zurfi. 6 Daƙiƙin mutun bai sani ba, haka ma wawa bai fahimci wannan ba: 7 Lokacin da miyagu suka firfito kamar ciyawa, ko ma a lokacin da miyagu suka taru, duk da haka an miƙa su ga hallaka ta har abada. 8 Amma kai Yahweh zaka yi mulki har abada. 9 Hakika ka duba maƙiyanka, Yahweh! Hakika ka duba maƙiyanka. Hakika zasu hallaka! Duk masu aikin mugunta za'a warwatsa su. 10 Ka tada ƙahona kamar na bijimin sã; An keɓe ni da sabon mai. 11 Idanuna sun ga faɗuwar maƙiyana; kunnuwana kuma sun ji hallakar miyagun maƙiyana. 12 Masu adalci zasu yi yaɗo kamar gazarin dabino; zasu yi girma kamar itacen sida na Lebonon. 13 An dasa sune a gidan Yahweh; Suna sheƙi a harabar Allahnmu. 14 Suna ba da 'ya'ya har ma a kwanakin tsufansu; suna nan kore shar, 15 Don ayi shela cewa Yahweh mai adalci ne. Shi ne dutsena, ba kuma rashin adalci a cikinsa.
1 Yahweh reigns; he is robed in majesty;
Yahweh has clothed and girded himself with strength.
The world is firmly established; it cannot be moved.
2 Your throne is established from ancient times;
you are from everlasting.
3 The oceans rise, Yahweh;
they have lifted up their voice;
the oceans' waves crash and roar.
4 Above the crashing of many waves,
the mighty breakers of the sea,
Yahweh on high is mighty.
5 Your solemn commands are very trustworthy;
holiness adorns your house,
Yahweh, for the length of your days.
1 Yahweh yana mulki; Yana saye da daraja; Yahweh yasa sutura ya kuma yiwa kansa ɗammara da ƙarfi. An kafa duniya daram; kuma ba zata gusa ba. 2 Kursiyinka ya kafu tun zamanin dã can; kana nan tun fil azal. 3 Tekuna suka tashe, Yahweh; sun ta da muryarsu; raƙuman tekuna sunyi tumbotso sunyi ruri. 4 Sun fi dukkan sauran ambaliyoyi masu ikon karya teku, Yahweh na sama maigirma ne. 5 Manyan umarnanka abin dogara ne na hakika; Yahweh, tsarki ya ƙayata gidanka, har abada.
1 Yahweh, God who avenges,
God who avenges, shine over us.
2 Rise up, judge of the earth,
give recompense to the proud.
3 How long will the wicked, Yahweh,
how long will the wicked rejoice?
4 They pour out their arrogant words;
all those who behave wickedly boast.
5 They crush your people, Yahweh;
they afflict your heritage.
6 They kill the widow and foreigner who lives in their country,
and they murder the fatherless.
7 They say, "Yah does not see;
the God of Jacob does not take notice of it." [1]
8 Pay attention, you stupid people!
You fools, when will you gain understanding?
9 He who made the ear, does he not hear?
He who formed the eye, does he not see?
10 He who disciplines the nations, does he not correct?
He is the one who gives knowledge to man.
11 Yahweh knows the thoughts of men,
that they are vapor.
12 Blessed is the one whom Yah instructs,
the one whom you teach from your law. [2]
13 You give him rest in times of trouble
until a pit is dug for the wicked.
14 For Yahweh will not abandon his people
or abandon his inheritance.
15 For judgment will again be righteous;
and all the upright in heart will follow it.
16 Who will rise up to defend me against the evildoers?
Who will stand up for me against those who behave wickedly?
17 Unless Yahweh had been my help,
I would soon be lying down in the place of silence.
18 When I said, "My foot is slipping,"
Your covenant faithfulness, Yahweh, held me up.
19 When cares within me are many,
your consolations delight my soul.
20 Can a throne of destruction be allied with you,
one that creates trouble by statute?
21 They conspire together to take the life of the righteous
and they declare guilty the blood of the innocent.
22 But Yahweh has been my high tower,
and my God has been the rock of my refuge.
23 He will bring on them their own iniquity
and will cut them off in their own wickedness.
Yahweh our God will cut them off.
1 Yahweh, Allah mai sakayya, Allah mai sakayya ka haskaka a bisan mu. 2 Ka tashi tsaye mai shari'ar duniya ka ba masu girman kai abin da ya kamance su. 3 Har yaushe miyagu, Yahweh har yaushe miyagu za suyi farinciki 4 Dukkan masu aikin mugunta suna ta yin maganganunsu na wauta; Duk masu mugunta suna fahariya. 5 Yahweh; sun buge mutanenka, Sun ƙuntata wa al'ummarka. 6 Sun kashe gwauruwa da bãƙon dake zaune a ƙasarsu, sun kuma kashe marayu. 7 Suka ce, "Allah ba zai gani ba, Yahweh na Yakubu bai kula da abin ba." 8 Ku lura mutane marasa hankali! Ku wawaye, har sai yaushe zaku koyi darasi? 9 Shi wanda yayi kunne ashe ba zai ji ba? Shi wanda yayi ido ba ya gani ne? 10 Shi dake horon al'ummai, ashe ba zai tsautar ba? Shi ne mai ba da ilimi ga mutum. 11 Yahweh ya san tunanin mutane, cewa turiri ne kawai. 12 Mai albarka ne wanda ka yiwa gargaɗi, Yahweh wanda ka koyar daga cikin shari'arka 13 Ka bashi hutu a lokutan damuwa har sai da aka gina rami domin miyagu. 14 Domin Yahweh ba zai yashe da mutanensa ba ko kuma yayi watsi da abin gãdonsa ba. 15 Domin hukunci zai sake zama da adalci; kuma dukkan masu tsarkin rai zasu bi shi. 16 Wa zai tashi ya kuɓutar dani daga masu mugunta? 17 In da ba domin Yahweh ya taimake ni ba da yanzu ina can kwance a lahira. 18 Lokacin dana ce ƙafafuna na barci," Yahweh alƙawarin amincinka ya ɗaga ni sama. 19 Lokacin da fargaba ya cika ni ta'aziyarka ta kan sani in cika da murna. 20 Ko akwai hurɗa tsakaninka da mulkin hallakarwa da ya kafa rashin adalci? 21 Sun shirya maƙarƙashiya tare domin su kashe mai adalci sun kuma hukuntawa marar laifi mutuwa. 22 Amma Yahweh ne babbar hasumiyata, Allahna kuma shi ne dutsen fakewa ta. 23 Zai saukar masu da laifofinsu zai kuma daddatsa su a cikin aikin muguntarsu. Yahweh Allahnmu zai daddatse su.
1 Oh come, let us sing to Yahweh;
let us shout joyfully to the rock of our salvation.
2 Let us enter his presence with thanksgiving;
let us shout joyfully to him with psalms of praise.
3 For Yahweh is a great God
and a great King superior to all gods.
4 In his hand are the depths of the earth;
the heights of the mountains are his.
5 The sea is his, for he made it,
and his hands formed the dry land.
6 Oh come, let us worship and bow down;
let us kneel before Yahweh, our Creator:
7 For he is our God,
and we are the people of his pasture and the sheep of his hand.
Today—oh, that you would hear his voice!
8 "Do not harden your heart, as at Meribah,
or as on the day of Massah in the wilderness,
9 where your forefathers tested me;
they put me to the test, though they had seen my deeds.
10 For forty years I was angry with that generation
and said, 'This is a people whose hearts wander astray;
they have not known my ways.'
11 Therefore I swore in my anger
that they would never enter into my resting place."
1 Ku zo mu raira yabo ga Yahweh, Sai mu raira waƙar farinciki ga dutsen cetonmu. 2 Sai mu zo gabansa da godiya, sai mu raira masa yabo da waƙoƙin zabura. 3 Domin Yahweh Allah ne mai girma, sarki ne mai girma da yafi dukkan alloli. 4 Zurfafan duniya dukka a hannunsa suke; Duwatsu masu tsawo kuma nasa ne. 5 Teku tasa ce, shi ne yayi ta. Hannuwansa kuma suka yi busasshiyar ƙasa. 6 Ku zo muyi sujada mu durƙusa ƙasa, sai mu durƙusa a gaban Yahweh mahallicinmu; 7 Domin shi ne Allahnmu, mu mutanen makiyayarsa ne, tumakin hannunsa kuma. Yau ace dai za ku ji muryarsa! 8 Kada ku taurare zuciyarku, kamar a Meriba, ko kuma kamar ranar Massa a cikin jeji, 9 inda ubanninku suka gwada ni suka kuma jaraba ni, koda ya ke sun ga aikina. 10 Shekaru arba'in ina fushi da waccan tsarar na ce, "Waɗannan mutane ne da zuciyarsu ta karkace; basu san hanyoyina ba. 11 'Domin haka cikn fushina na rantse cewa ba zasu taɓa shiga wurin hutu na ba
1 Oh, sing to Yahweh a new song;
sing to Yahweh, all the earth.
2 Sing to Yahweh, bless his name;
announce his salvation day after day.
3 Declare his glory among the nations,
his marvelous deeds among all the nations.
4 For Yahweh is great and is to be praised greatly.
He is to be feared above all other gods.
5 For all the gods of the nations are idols,
but it is Yahweh who made the heavens.
6 Splendor and majesty are in his presence.
Strength and beauty are in his sanctuary.
7 Ascribe to Yahweh, you clans of peoples,
ascribe praise to Yahweh for his glory and strength.
8 Give to Yahweh the glory that his name deserves.
Bring an offering and come into his courts.
9 Bow down to Yahweh in the splendor of holiness;
tremble before him, all the earth.
10 Say among the nations, "Yahweh reigns."
The world also is established; it cannot be shaken.
He judges the peoples fairly.
11 Let the heavens be glad, and let the earth rejoice;
let the sea roar and that which fills it shout with joy.
12 Let the fields rejoice and all that is in them.
Then let all the trees in the forest shout for joy
13 before Yahweh, for he is coming.
He is coming to judge the earth.
He will judge the world with righteousness
and the peoples with his faithfulness.
1 Ku raira sabuwar waƙa ga Yahweh; ku raira waƙa ga Yahweh, dukkan duniya. 2 Ku raira waƙa ga Yahweh, ku albarkaci sunansa; kuyi shelar cetonsa a kowacce rana. 3 Ku furta ɗaukakarsa a cikin al'ummai, ayyukansa na ban mamaki a cikin al'ummai. 4 Domin Yahweh yana da girma ya kuma isa yabo sosai. A ji tsoron sa fiye da dukkan sauran alloli. 5 Saboda allolin al'ummai gumaka ne, amma Yahweh ne ya hallici sammai, martaba da wadata suna gabansa. 6 Jamali da ƙarfi suna cikin wurinsa mai tsarki. 7 Kuyi yabo ga yahweh ku dukkan kabilu na mutane, ku yabi Yahweh sabili da ɗaukakarsa da ƙarfinsa. 8 Ku ba yahweh ɗaukakar da ta dace da sunansa. Ku kawo baiko a haikalinsa. 9 Ku durƙusa a gaban Yahweh saye da tufafin dake girmama tsarkinsa. Yi rawar jiki a gabansa, dukkan duniya. 10 Ku faɗa a cikin al'ummai cewa,"Yahweh ne ke mulki." Hakannan kuma aka kafa duniya; ba kuma zata jijjigu ba. Yana yiwa mutane shari'ar dake dai-dai. 11 Sai sammai suyi murna, sai duniya kuma ta yi farinciki; sai teku yayi ruri abin da ke cikinsa kuma su cika da murna. 12 Filaye suyi murna da duk abin da ke cikin su. Sa'an nan kuma dukkan bishiyoyin duniya su ɓarke da yabo 13 a gaban Yahweh, domin yana tafe. Yana zuwa domin ya shar'anta duniya. Zai shar'anta duniya da adalci da mutane kuma cikin amincinsa.
1 Yahweh reigns; let the earth rejoice;
let the many coastlands be glad.
2 Clouds and darkness surround him.
Righteousness and justice are the foundation of his throne.
3 Fire goes before him
and consumes his adversaries on every side.
4 His lightning lights up the world;
the earth sees and trembles.
5 The mountains melt like wax before Yahweh,
the Lord of the whole earth.
6 The skies declare his justice,
and all the nations see his glory.
7 All those who worship carved figures will be shamed,
those who boast in worthless idols—
bow down to him, all you gods!
8 Zion heard and was glad,
and the towns of Judah rejoiced
because of your righteous decrees, Yahweh.
9 For you, Yahweh, are most high above all the earth.
You are exalted far above all gods.
10 You who love Yahweh, hate evil!
He protects the lives of his faithful ones,
and he takes them out of the hand of the wicked.
11 Light is sown for the righteous
and gladness for those with honest hearts.
12 Be glad in Yahweh, you righteous;
and give thanks when you remember his holiness.
1 Yahweh na mulki sai duniya ta yi murna, sai dukkan ƙasashe masu nisa suyi murna. 2 Gizagizai da duhu na kewaye da shi. Adalci da gaskiya ne harsashen kursiyinsa. 3 Wuta na tafe a gabansa tana cinye magafta ko ina 4 Walƙiyarsa ta haskaka duniya; duniya ta gani ta furgita. 5 Duwatsu kuma sun narke kamar tufa a gaban Yahweh Ubangijin dukkan duniya. 6 Sararin sama na shaida adalcinsa, dukkan al'ummai kuma sun ga ɗaukakarsa. 7 Duk waɗanda ke bauta wa abin da hannu ya sassaƙa zasu kunyata, masu taƙama da gumaka marasa amfani- ku rusuna masa da dukkan allolinku! 8 Sihiyona taji sai tayi farinciki, biranen Yahuda kuma suka yi murna saboda dokokinka na adalci, Yahweh. 9 Domin kai, Yahweh, kafi kowa ɗaukaka a cikin dukkan duniya. An ɗaukaka ka fiye da dukkan alloli. 10 Ku dake ƙaunar Yahweh ku ƙi mugunta! Yana kare ran tsarkakansa, ya karɓo su daga hannun mugun. 11 An shuka haske domin adalai farinciki kuma domin masu zukata masu aminci. 12 Kuyi murna cikin Yahweh ku adalai; ku kuma yi masa godiya lokacin da kuka tuna da tsarkinsa.
1 Oh, sing to Yahweh a new song,
for he has done marvelous things;
his right hand and his holy arm
have given him victory.
2 Yahweh has made known his salvation;
he has openly showed his justice to all the nations.
3 He calls to mind his steadfast love
and faithfulness for the house of Israel;
all the ends of the earth will see
the victory of our God.
4 Shout for joy to Yahweh, all the earth;
burst into song, sing for joy, and sing praises.
5 Sing praises to Yahweh with the harp,
with the harp and melodious song.
6 With trumpets and the sound of the horn,
shout joyfully before the King, Yahweh.
7 Let the sea shout and everything in it,
the world and those who live in it!
8 Let the rivers clap their hands,
and let the mountains shout for joy.
9 Yahweh is coming to judge the earth;
he will judge the world with righteousness
and the nations with fairness.
1 Oh, ku raira sabuwar waƙa ga Yahweh domin yayi ayyuka masu ban mamaki; hannunsa na dama da damtsensa sun ba shi nasara. 2 Yahweh ya sa cetonsa ya sanu; ya nuna adalcinsa a fili ga dukkan al'ummai. 3 Ya tuna da alƙawarinsa mai aminci da gaskiya ga gidan Isra'ila; dukkan iyakokin duniya zasu ga nasarar Allahnmu. 4 Ku raira waƙar farinciki ga Yahweh, dukkan duniya ku ɓarke da waƙa, kuyi waƙa domin murna, kuyi waƙoƙin yabo. 5 Ku raira yabo ga Yahweh da garaya, tare da garaya haɗe da waƙoƙi masu daɗi. 6 Tare da kakaki da ƙarar ƙaho, ku tada muryoyi masu daɗi a gaban Sarki, Yahweh. 7 Sai teku yayi ihu da dukkan abin dake cikinsa! 8 Sai rafuffuka su tafa hannuwansu, sai duwatsu kuma su raira waƙar yabo. 9 Yahweh yana zuwa domin ya yi wa duniya shari'a da adalci da kuma al'ummai tare da gaskiya.
1 Yahweh reigns;
let the nations tremble.
He sits enthroned above the cherubim;
the earth quakes.
2 Yahweh is great in Zion;
he is exalted above all the nations.
3 Let them praise your great and awesome name;
he is holy.
4 The king is strong, and he loves justice.
You have established fairness;
you have done righteousness
and justice in Jacob.
5 Praise Yahweh our God
and worship at his footstool.
He is holy.
6 Moses and Aaron were among his priests,
and Samuel was among those who called on his name.
They called to Yahweh,
and he answered them.
7 He spoke to them from the pillar of cloud.
They kept his solemn commands
and the statutes that he gave them.
8 You answered them,
Yahweh our God.
A forgiving God you were to them,
but also an avenger of their sinful deeds.
9 Praise Yahweh our God,
and worship at his holy hill,
for Yahweh our God is holy.
1 Yahweh na mulki; bari al'ummai suyi rawar jiki, yana zaune kan kursiyi sama da Kerubim, duniya ta girgiza, 2 Yahweh yana da girma a Sihiyona yana da ɗaukaka fiye da dukkan al'ummai. 3 Sai a yabi sunanka mai jamali da girma; yana da tsarki. 4 Sarki yana da ƙarfi, yana kuma ƙaunar adalci. ka kafa gaskiya; ka aikata adalci akwai adalci kuma a cikin Yakubu. 5 A yabi Yahweh Allahnmu a kuma yi sujada a digadigansa. Ya na da tsarki. 6 Musa da Haruna na cikin firistocinsa, Sama'ila kuma na cikin waɗanda suka yi addu'a gare shi. Sun yi addu'a ga Yahweh, ya kuma amsa masu. 7 Ya yi masu magana daga ginshinƙin girgije. Sun kiyaye tsattsarkan umarninsa da farillan da ya basu. 8 Ka amsa masu, Yahweh Allahnmu. Kai Allah ne mai gafara a gare su, amma kuma kana horon ayyukansu na zunubi. 9 Ku yabi Yahweh Allahnmu, ku kuma yi sujada akan tudunsa mai tsarki, gama Yahweh Allahnmu yana da tsarki.
1 Shout joyfully to Yahweh, all the earth.
2 Serve Yahweh with gladness;
come before his presence with joyful singing.
3 Know that Yahweh is God;
he made us, and we are his.
We are his people and the sheep of his pasture.
4 Enter into his gates with thanksgiving
and into his courts with praise.
Give thanks to him and bless his name.
5 For Yahweh is good; his covenant faithfulness endures forever
and his truthfulness through all generations.
1 Kuyi ihu da farinciki ga Yahweh ku dukkan duniya, 2 Ku bautawa yahweh da farar zuciya, kuzo gabansa da waƙoƙin farinciki. 3 Ku sani Yahweh Allah ne; yayi mu, mu kuma nasa ne. Tumakin makiyayarsa kuma. 4 Ku shiga ƙofofinsa da godiya cikin gidansa da yabo. Kuyi masa godiya ku albarkaci sunansa. 5 Domin Yahweh nagari ne; alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada gaskiyarsa kuma har dukkan tsararraki ne.
1 I will sing of covenant faithfulness and justice;
to you, Yahweh, I will sing praises.
2 I will pay attention to the way of integrity.
Oh, when will you come to me?
I will walk with integrity of heart within my house.
3 I will not put wrongdoing before my eyes;
I hate worthless evil;
it will not cling to me.
4 A perverse heart will leave me;
I am not loyal to evil.
5 I will destroy whoever secretly slanders his neighbor.
I will not tolerate the haughty of eye and arrogant of heart.
6 I will look to the faithful of the land to sit at my side.
Those who walk in the way of integrity may serve me.
7 Deceitful people will not remain within my house;
liars will not be welcome before my eyes.
8 Morning by morning
I will destroy all the wicked from the land;
I will remove all who behave wickedly
from the city of Yahweh.
1 Zan raira alƙawarin aminci da gaskiya; a gare ka, Yahweh, zan raira yabbai. 2 Zan yi tafiya cikin aminci. Oh, yaushe zaka zo wurina ne? Ni da gidana za muyi tafiya cikin nagarta. 3 Ba zan ƙyale mugunta a idanuna ba; Na ƙi mugun aiki marar cancanta; ba zai manne mani ba. 4 Ɓatattun mutane zasu rabu dani; bana yin biyayya ga mugunta. 5 Zan hallaka duk wanda ya yiwa maƙwabcinsa yanke a asirce. Ba zan ƙyale duk wani mai fankama da rashin hankali ba. 6 Zan nemi masu aminci na ƙasar su zauna a gefena. Masu tafiya cikin gaskiya da riƙon amana ne zasu bauta mani. 7 Mayaudara ba zasu kasance a gidana ba; maƙaryata bazan marabce su a idona ba. 8 Duk safiya zan hallakar da miyagu dukka daga ƙasar; Zan kawar da dukkan miyagu daga birnin Yahweh.
1 Hear my prayer, Yahweh;
hear my cry to you.
2 Do not hide your face from me in my time of trouble.
Listen to me.
When I call out to you,
answer me quickly.
3 For my days pass away like smoke,
and my bones burn like fire.
4 My heart is crushed, and I am like grass that has withered.
I forget to eat any food.
5 With my continual groaning,
I have become very thin.
6 I am like a pelican of the wilderness;
I have become like an owl in the ruins.
7 I lie awake like a solitary bird,
alone on the housetop.
8 My enemies taunt me all day long;
those who mock me use my name in curses.
9 I eat ashes like bread
and mix my drink with tears.
10 Because of your raging anger,
you have lifted me up to throw me down.
11 My days are like a shadow that fades,
and I have withered like grass.
12 But you, Yahweh, live forever,
and your fame is for all generations.
13 You will rise up and have mercy on Zion.
Now is the time to have mercy upon her;
the appointed time has come.
14 For your servants hold her stones dear
and feel compassion for the dust of her ruins.
15 The nations will respect your name, Yahweh,
and all the kings of the earth will honor your glory.
16 Yahweh will rebuild Zion
and will appear in his glory.
17 At that time, he will respond to the prayer of the destitute;
he will not reject their prayer.
18 This will be written for future generations,
and a people not yet created will praise Yah. [1]
19 For he has looked down from the holy heights;
from heaven Yahweh has viewed the earth,
20 to hear the groaning of the prisoners,
to release those who were condemned to death.
21 Then men will proclaim the name of Yahweh in Zion
and his praise in Jerusalem
22 when the peoples and kingdoms gather together
to serve Yahweh.
23 He has taken away my strength in the middle of life.
He has shortened my days.
24 I said, "My God, do not take me away in the middle of life;
you are here throughout all generations.
25 In ancient times you established the earth;
the heavens are the work of your hands.
26 They will perish, but you will remain;
they will all grow old like a garment;
like clothing, you will remove them,
and they will disappear.
27 But you are the same,
and your years will have no end.
28 The children of your servants will live on,
and their descendants will live in your presence."
1 Yahweh ka ji addu'ata, Yahweh ka ji kukana dana keyi gare ka. 2 Kada ka ɓoye mani fuskarka a lokacin da nake damuwa. Ka ji ni. A lokacin da nayi kira gare ka, ka amsa mani da sauri. 3 Gama kwanakina sun wuce kamar hayaƙi, ƙasusuwana kuma na ƙuna kamar wuta. 4 An buge zuciyata na zama kamar ciyawar data bushe. Na manta in ci wani abinci. 5 Da nishe-nishena na kullum, na rame. 6 Na zama kamar zalɓe a hamada; na zama kamar mujiya a kufai. 7 Na kwanta ba tare da yin barci ba, kamar tsuntsun dake kaɗaici, shi kaɗai a bisa kan gida. 8 Maƙiyana nayi mani ba'a; masu yi mani habaici na la'anta sunana. 9 Toka ce abincina kuma gurasa abin shana ya gauraye da hawaye na. 10 Saboda fargaban fushinka ka ɗaga ni sama domin ka fyaɗa ni ƙasa. 11 Kwanakina sun zama kamar inuwar data gushe, na kuma yanƙwane kamar ciyawa. 12 Amma kai Yahweh, kana raye har abada, kuma shahararka ta dukkan tsararraki ce. 13 Zaka tashi kayi jinƙai ga Sihiyona. Yanzu ne lokacin nuna mata jinƙai; lokacinta da kasa yayi. 14 Domin bayinka sun riƙe duwatsunta ƙaunatacce ka ji tausayi saboda ƙurar kufanta. 15 Al'ummai zasu girmama sunanka, Yahweh, kuma dukkan sarakunan duniya zasu girmama ɗaukakarka. 16 Yahweh zai sake gina Sihiyona ya kuma bayyana a cikin ɗaukakarsa. 17 A wancan lokacin, zai amsa addu'ar wulaƙantattu; ba zai ƙi addu'arsu ba. 18 Za a rubuta wannan saboda tsararraki masu zuwa, da mutanen da ba'a haifa ba tukuna zasu yabi Yahweh. 19 Domin ya dubo ƙasa daga can sammai; Daga samaniya Yahweh ya dubi duniya, 20 domin ya ji nishe-nishen 'yan sarƙa, ya kuɓutar da waɗanda aka hukuntawa mutuwa. 21 Mutane zasu yi shelar sunan Yahweh a Sihiyona da kuma yabonsa a Yerusalem 22 lokacin da mutane da mulkoki suka tattaru tare su bauta wa yahweh. 23 Ya ɗauke ƙarfina a tsakiyar rayuwata. Ya gajarta kwanakina. 24 Na ce Allahna kada ka kawar dani a tsakiyar rayuwa; kana nan a dukkan tsararraki. 25 A can lokacin dã ka kafa duniya a wurinta; sammai kuma aikin hannuwanka ne. 26 Zasu lalace amma kai zaka dawwama; duk zasu tsufa kamar sutura; kamar tufafi, zaka cire su, zasu kuma ɓace. 27 Amma kai kana nan yadda kake, shekarunka kuma basu da iyaka. 28 'Ya'yan bayinka zasu rayu, zuriyarsu kuma zasu rayu a gabanka."
1 I give praise to Yahweh with all my life,
and with all that is within me,
I give praise to his holy name.
2 I give praise to Yahweh with all my life,
and I remember all of his good deeds.
3 He forgives all your iniquities;
he heals all your diseases.
4 He redeems your life from the pit;
he crowns you with covenant faithfulness and acts of tender mercy.
5 He satisfies your life with good things
so that your youth is renewed like the eagle.
6 Yahweh does what is fair
and does acts of justice for all who are oppressed.
7 He made known his ways to Moses,
his deeds to the descendants of Israel.
8 Yahweh is merciful and gracious;
slow to anger and abounding in steadfast love.
9 He will not discipline forever;
he will not be angry to eternity.
10 He does not deal with us as our sins deserve
or repay us for what our iniquities demand.
11 For as the skies are high above the earth,
so great is his covenant faithfulness toward those who honor him.
12 As far as the east is from the west,
this is how far he has removed the guilt of our sins from us.
13 As a father has compassion on his children,
so Yahweh has compassion on those who honor him.
14 For he knows how we are formed;
he knows that we are dust.
15 As for man, his days are like grass;
he flourishes like a flower in a field.
16 The wind blows over it, and it disappears,
and no one can even tell where it once grew.
17 But the covenant faithfulness of Yahweh is from everlasting to everlasting
on those who honor him.
His righteousness extends to their descendants.
18 They keep his covenant
and remember to obey his instructions.
19 Yahweh has established his throne in the heavens,
and his kingdom rules over everyone.
20 Give praise to Yahweh, you his angels,
you mighty ones who are strong and do his word,
and obey the sound of his word.
21 Give praise to Yahweh, all his hosts,
his servants who do his will.
22 Give praise to Yahweh, all his creatures,
in all the places where he reigns.
I will give praise to Yahweh with all my life.
1 Ina godiya ga Yahweh da dukkan raina, da dukkan abin da ke cikina, Ina yabon sunansa mai tsarki. 2 Ina godiya ga Yahweh da dukkan raina, na kuma tuna da dukkan ayyukansa nagari. 3 Ya gafarta dukkan zunubanka, ya kuma warkar da dukkan cututtukanka. 4 Ya ceci ranka daga hallaka yayi maka rawani da alƙawarin aminci da ayyukan jinƙai. 5 Ya ƙosar da ranka da abubuwa masu kyau domin haka ƙuruciyarka ta sabunta kamar gaggafa. 6 Yahweh yakan yi abin dake dai-dai da adalci ga duk waɗanda aka tsanantawa. 7 ya sanar da hanyoyinsa ga Musa, ayyukansa kuma ga zuriyar Isra'ila. 8 Yahweh mai jinƙai ne da alheri; yana da haƙuri; yana da matuƙar amincin alƙawari. 9 Ba kullum ya kanyi horo ba; ba kullum kuma ya kanyi fushi ba. 10 Baya yi mana bisa ga gwargwadon zunubanmu ko ya saka mana kan hukuncin zunubanmu ba. 11 Domin kamar yadda sammai ke nesa da duniya, to haka girman alƙawarinsa ya ke ga masu girmama shi. 12 Kamar yadda gabas tayi nisa da yamma hakannan ya kawar da laifofin zunubanmu daga gare mu. 13 Kamar yadda mahaifi ke tausayin 'ya'yansa, haka Yahweh ke tausayin masu girmama shi. 14 Domin yasan yadda aka yi mu; ya sani cewa mu ƙura ne. 15 mutum kwanakinsa kamar ciyawa ce yakan yi yabanya kamar furen saura. 16 Iska ta kan hura ta kansa, sai kuma ya ɓace kuma ba wanda zai san yadda yayi girma. 17 Amma alƙawarin Yahweh mai aminci har abada abadin ne ga masu girmama shi. Adalcinsa ya kai har ga zuriyar su. 18 Sun kiyaye alƙawarinsa sun kuma tuna su yi biyayya da dokokinsa. 19 Yahweh ya kafa kursiyinsa a sammai, masarautarsa kuma na mulkin kowa. 20 A yi yabo ga Yahweh, ku mala'ikunsa, ku masu iko dukka dake yin biyayya da maganarsa. 21 Ku yabi Yahweh, dukkan rundunoninsa, ku bayinsa ne dake yin nufinsa. 22 A yabi Yahweh, dukkan halittunsa, a dukkan wuraren da ya ke mulki. Zan yabi Yahweh da dukkan raina.
1 I give praise to Yahweh with all my life,
Yahweh my God, you are very magnificent;
you are clothed with splendor and majesty.
2 You cover yourself with light as with a garment;
you spread out the heavens like a tent curtain.
3 You lay the beams of your chambers on the clouds;
you make the clouds your chariot;
you walk on the wings of the wind.
4 He makes the winds his messengers,
flames of fire his servants.
5 He laid the foundations of the earth,
so that it will not totter forever and ever.
6 You covered the earth with water like a garment;
the water covered the mountains.
7 At your rebuke the waters retreated;
at the sound of your thunder they hurried away.
8 The mountains rose and the valleys went down
to the places that you had appointed for them.
9 You have set a boundary for them that they will not cross;
they will not cover the earth again.
10 He made springs flow into the valleys;
the streams flow between the mountains.
11 They supply water for all the animals of the field;
the wild donkeys quench their thirst.
12 By the riverbanks the birds build their nests;
they sing among the branches.
13 He waters the mountains from his water chambers in the sky.
The earth is filled with the fruit of his labor.
14 He makes the grass grow for the cattle
and plants for man to cultivate,
so that man may produce food from the earth.
15 He makes wine to make man happy,
oil to make his face shine,
and food to sustain his life.
16 The trees of Yahweh get plenty of rain;
the cedars of Lebanon which he planted.
17 There the birds make their nests.
The stork makes the cypress tree her home.
18 The wild goats live on the high mountains;
the mountain heights are a refuge for the hyraxes.
19 He appointed the moon to mark the seasons;
the sun knows its time for setting.
20 You make the darkness of the night
when all the beasts of the forest come out.
21 The young lions roar for their prey
and seek their food from God.
22 When the sun rises, they retreat
and sleep in their dens.
23 Meanwhile, people go out to their work
and labor away until the evening.
24 Yahweh, how many and varied are your works!
With wisdom you made them all;
the earth overflows with your works.
25 Over there is the sea, deep and wide,
teeming with innumerable creatures,
both small and great.
26 The ships travel there,
and Leviathan is also there, which you formed to play in the sea.
27 All these look to you in hope
that you will give them their food on time.
28 When you give to them, they gather;
when you open your hand, they are satisfied.
29 When you hide your face, they are troubled;
if you take away their breath, they die
and return to dust.
30 When you send out your Spirit,
they are created,
and you renew the surface of the ground.
31 May the glory of Yahweh last forever;
may Yahweh enjoy his creation.
32 He looks down on the earth, and it shakes;
he touches the mountains, and they smoke.
33 I will sing to Yahweh all my life;
I will sing praise to my God as long as I live.
34 May my thoughts be sweet to him;
I will rejoice in Yahweh.
35 May sinners vanish from the earth,
and let the wicked be no more.
I give praise to Yahweh with all my life.
Give praise to Yah. [1]
1 Na bada yabo ga Yahweh da dukkan raina, Yahweh Allahna, kai mai girma ne da ƙawa; Kayi sutura da martaba da daraja. 2 Ka rufe kanka da haske kamar da sutura; ka shimfiɗa sammai kamar yadda ake simfiɗa labulen rumfa. 3 Ka shimfiɗa katakan fadodinka a kan gajimarai; ka mai da gajimarai karusanka; kana tafiya akan fika-fikan iska. 4 Ya mai da iskoki manzanninsa, harsunan wuta kuma bayinsa. 5 Ya kafa tushen duniya ba kuma zata jijjigu ba. 6 Ka rufe duniya da ruwa kamar sutura; ruwa ya rufe duwatsu. 7 Tsautawarka nasa ruwaye su janye; da jin ƙarar tsawarka sai suka gudu. 8 Duwatsu sun tashi, kwarurruka kuma suka bazu zuwa wuraren da ka shirya masu. 9 Ka yi masu iyakar da ba zasu tsallake ba; ba zasu ƙara rufe duniya ba. 10 Yasa maɓuɓɓugan ruwa su gudana zuwa kwarurruka; maɓulɓulan sun kwarara tsakanin duwatsu. 11 Suna bayar da ruwa ga dukkan dabbobin saura; jakunan jeji a wurin ne suke kashe ƙishinsu. 12 A bakin kogunan ruwa tsuntsaye suka yi sheƙunansu; suna raira waƙa a cikin rassa. 13 Ya shayar da duwatsu daga ruwansa ya kafa kursiyinsa a sammai. Duniya ta cika da 'ya'yan aikinsa. 14 Yasa ciyawa ta fito domin dabbobi da kuma tsire-tsire domin mutum ya nome ya sami abinci daga ƙasa. 15 Yayi inabi domin mutum yayi murna, mai kuma domin fuskarsa tayi haske, abinci kuma domin rayuwarsa. 16 Itatuwan Yahweh suna samun ruwa; Sidar Lebanon da ya dasa 17 Acan tsuntsaye ke yin sheƙunansu. Shamuwa ta mai da itacen sifurus gidanta. 18 Awakin jeji kuma suna zama a kan duwatsu; rimaye kuma sun mayar da ƙonƙolin duwatsu mafakarsu. 19 Yasa wata ya nuna lokuta; rana kuma ta san lokacin faɗuwarta. 20 Ka yi duhun dare lokacin da duk daji ke fitowa waje. 21 Sagarun zakuna kan yi gurnani domin neman abincinsu daga wurin Allah. 22 Lokacin da rana ta fito sai su koma suyi barci a kogunansu. 23 Hakanan mutane kan je waje wurin aikinsu suyi ta aiki har yamma. 24 Yahweh ayyukanka iri-iri guda nawa ne! Da hikima kayi su dukka; duniya ta cika maƙil da ayyukanka. 25 A can kuma sai teku, mai zurfi da faɗi cike da manya da ƙananan hallitu marasa ƙidayuwa, 26 Jiragen ruwa sukan je can, Lebiyatan kuma a can ya ke, wanda ka yi domin yayi wasa a cikin teku. 27 Duk waɗannan gare ka suke zuba ido domin samun abinci a kan lokaci 28 Lokacin da ka basu, su kan tara; lokacin daka buɗe hannunka, sukan ƙoshi. 29 Lokacin da ka ɓoye fuskarka, sukan shiga damuwa; in ka ɗauke numfashinsu sukan mutu su koma ƙura. 30 Lokacin da ka aiko Ruhunka, aka hallice su, ka kuma sabunta gefen ƙasarsu. 31 Dãma ɗaukakar Yahweh ta dawwama har abada; dãma Yahweh ya ji daɗin hallitarsa. 32 Ya dubi duniya, sai ta girgiza; yakan taɓa duwatsu suyi hayaƙi. 33 Zan raira yabo ga Yahweh a dukkan kwanakin raina; zan raira waƙar yabo ga Allah muddin ina raye. 34 Dãma tunane-tunanena su zama da zaƙi a gare shi; Zan yi murna cikin Yahweh. 35 Dãma masu zunubi su hallaka daga duniya, dãma miyagu su ɓace daga duniya. Ina yabon Yahweh dukkan kwanakin raina. A yabi Yahweh.
1 Give thanks to Yahweh, call on his name;
make known his deeds among the nations.
2 Sing to him, sing praises to him;
speak of all his marvelous deeds.
3 Boast in his holy name;
let the heart of those who seek Yahweh rejoice.
4 Seek Yahweh and his strength;
seek his presence continually.
5 Recall the marvelous things he has done,
his miracles and the decrees from his mouth,
6 you descendants of Abraham his servant,
you people of Jacob, his chosen ones.
7 He is Yahweh, our God.
His decrees are on all the earth.
8 He keeps in mind his covenant forever,
the word that he commanded for a thousand generations.
9 He calls to mind the covenant that he made with Abraham
and his oath to Isaac.
10 This is what he confirmed to Jacob as a statute
and to Israel as an everlasting covenant.
11 He said, "I will give you the land of Canaan
as your share of your inheritance."
12 He said this when they were only few in number,
so very few, and were strangers in the land.
13 They went from nation to nation
and from one kingdom to another.
14 He did not allow anyone to oppress them;
he rebuked kings for their sakes.
15 He said, "Do not touch my anointed ones,
and do not harm my prophets."
16 He called for a famine on the land;
he cut off the whole staff of bread.
17 He sent a man ahead of them;
Joseph was sold as a servant.
18 His feet were bound by shackles;
on his neck was put an iron collar,
19 until what he had said came to pass.
The word of Yahweh tested him.
20 The king sent servants to release him;
the ruler of the people set him free.
21 He put him in charge of his house
as ruler of all his possessions
22 to instruct his princes as he wished
and to teach his elders wisdom.
23 Then Israel came into Egypt,
and Jacob lived for a time in the land of Ham.
24 Yahweh made his people fruitful,
and made them stronger than their enemies.
25 He caused their enemies to hate his people,
to mistreat his servants.
26 He sent Moses, his servant,
and Aaron, whom he had chosen.
27 They performed his signs among the Egyptians,
his wonders in the land of Ham.
28 He sent darkness and made that land dark,
and they did not rebel against his commands.
29 He turned their water into blood
and killed their fish.
30 Their land swarmed with frogs,
even in the rooms of their rulers.
31 He spoke, and swarms of flies and gnats came
throughout their country.
32 He turned their rain into hail,
with fire flaming on their land.
33 He destroyed their vines and fig trees;
he broke the trees of their country.
34 He spoke, and the locusts came,
so many locusts.
35 The locusts ate up all of the vegetation in their land;
They ate up all the crops of the ground.
36 He killed every firstborn in their land,
the firstfruits of all their strength.
37 He brought the Israelites out with silver and gold;
none of his tribes stumbled on the way.
38 Egypt was glad when they went away,
for the Egyptians were afraid of them.
39 He spread a cloud for a covering
and made a fire to light up the night.
40 The Israelites asked for food, and he brought quail
and satisfied them with bread from heaven.
41 He split the rock, and waters gushed from it;
they flowed in the wilderness like a river.
42 For he called to mind his holy promise
that he made to Abraham his servant.
43 He led his people out with joy,
his chosen with shouts of triumph.
44 He gave them the lands of the nations;
they took possession of the fruit of the peoples' labors
45 so that they might keep his statutes
and obey his laws.
Give praise to Yah. [1]
1 Ku bada godiya ga Yahweh, ku kira bisa sunansa; ku sanar da ayyukansa cikin al'ummai. 2 Ku raira gare shi, ku raira yabbai gare shi; kuyi maganar dukkan ayyukansa na ban mamaki. 3 Kuyi taƙama cikin sunan sa mai tsarki; bari zuciyar waɗanda ke biɗar Yahweh ta yi farinciki. 4 Ku biɗi Yahweh da ƙarfinsa kuma; ku biɗi bayyanuwarsa ba fasawa. 5 Ku tuna da abubuwan ban mamaki da yayi, al'ajibansa da kuma dokoki daga bakinsa, 6 ku zuriyar Ibrahim bawansa, ku mutanen Yakubu, zaɓaɓɓunsa. 7 Shi ne Yahweh, Allahnmu. Dokokin sa suna bisan dukkan duniya. 8 Cikin ransa yana ajiye alƙawarinsa har abada, maganarsa da ya umarta domin dubun tsararraki. 9 Yana tunawa a cikin ransa alƙawarin da yayi da Ibrahim da kuma rantsuwarsa ga Ishaku. 10 Wannan ne abin da ya tabbatar wa Yakubu a matsayin farilla da Isra'ila a matsayin madawwamin alƙawari. 11 Ya ce, "Zan baku ƙasar kan'ana a matsayin kasonku na gãdonku." 12 Ya faɗi wannan sa'ad da suke kaɗan a lissafi, 'yan kima sosai, kuma suna baƙi a ƙasar. 13 Suka tafi daga al'umma zuwa al'umma kuma daga masarauta zuwa wata. 14 Bai bar wani ya tsananta masu ba; ya tsautawa sarakuna sabili da su. 15 Ya ce, "Kada ku taɓa shafaffuna, kada kuma ku yi lahani ga annabawana." 16 Yayi kira domin yunwa bisa ƙasar; ya yanke dukkan biyan buƙatar gurasa. 17 Ya aika da mutum gaba da su; Yosef a ka sayar da shi a matsayin bawa. 18 Aka ɗaure ƙafafunsa da sarƙoƙi; a bisa wuyansa aka sa maɗaurin ƙarfe, 19 har sai lokacin da maganganun sa suka zama gaskiya, kuma maganar Yahweh ta gwada shi. 20 Sarki ya aika da bayi su sake shi; shugaban mutanen ya 'yantar da shi. 21 Ya sanya shi lura da gidansa a matsayin shugaban dukkan mallakarsa 22 ya bayar da umarni ga shugabanninsa yadda ya so ya kuma koyar da dattawansa hikima. 23 Daga nan Isra'ila ya zo cikin Masar, Yakubu kuma ya zauna na wani lokaci a cikin ƙasar Ham. 24 Yahweh yasa mutanen sa suka yi 'ya'ya, ya kuma sa suka yi ƙarfi fiye da maƙiyansu. 25 Ya kuma sa maƙiyansa suka ƙi Jinin mutanensa, suka muzguna wa bayinsa. 26 Ya aika da Musa, bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa. 27 Suka aikata alamunsa a tsakiyar masarawa, al'ajibansa a ƙasar Ham. 28 Ya aika da duhu ya maida ƙasar duhu, amma mutanen ta basu yi biyayya da umarninsa ba. 29 Ya maida ruwansu ya zama jini ya kuma kashe kifinsu. 30 Ƙasar ta cika da gungun kwaɗi, har ma cikin ɗakunan shugabanninsu. 31 Yayi magana, kuma gungun ƙudaje da ƙwari suka zo cikin dukkan ƙasar. 32 Ya maida ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da wuta mai ci balbal bisa ƙasarsu. 33 Ya lalata kuringun inabinsu da itatuwan ɓaurensu; ya karya itatuwan ƙasarsu. 34 Yayi magana, fãri suka zo, fãri masu yawan gaske. 35 Fãrin suka cinye dukkan ganyayyaki a ƙasar; suka cinye dukkan amfanin gona. 36 Ya kashe kowanne ɗan fãri a cikin ƙasar, 'ya'yan fãrin dukkan ƙarfinsu. 37 Ya fito da Isra'ilawa tare da azurfa da zinariya; babu wani cikin kabilunsa da yayi tuntuɓe a hanya. 38 Masar ta yi farinciki da suka tafi, domin masarawa sunji tsoronsu. 39 Ya shimfiɗa girgije a matsayin abin rufa ya kuma yi wuta ta haskaka dare. 40 Isra'ilawa suka yi roƙon abinci, ya kuma kawo makwarwa ya kuma ƙosar da su da gurasa daga sama. 41 Ya fasa dutse ruwa kuma ya ɓulɓulo daga gare shi; ya malala cikin jeji kamar kogi. 42 Domin ya tuna a ransa da alƙawarin sa mai tsarki wanda yayi wa Ibrahim bawansa. 43 Ya bida mutanen sa suka fita da farinciki, zaɓaɓɓunsa da sowace-sowace fiye da gaban masu nasara. 44 Ya basu ƙasashen al'ummai; suka ɗauki mallakar dukiyar mutanen 45 domin su kiyaye farillansa su kuma yi biyayya da shari'unsa. A yabi Yahweh.
1 Give praise to Yah. [1]
Give thanks to Yahweh, for he is good,
for his covenant faithfulness endures forever.
2 Who can recount the mighty acts of Yahweh
or proclaim in full all his praiseworthy deeds?
3 Blessed are those who do what is right,
and whose deeds are always just.
4 Call me to mind, Yahweh, when you show favor to your people;
help me when you save them.
5 Then I will see the prosperity of your chosen,
rejoice in the gladness of your nation,
and glory with your inheritance.
6 We have sinned like our ancestors;
we have done wrong, and we have done evil.
7 Our fathers did not pay attention to your marvelous deeds in Egypt;
they ignored your many acts of covenant faithfulness;
they were rebellious at the sea, the Sea of Reeds.
8 Nevertheless, he saved them for his name's sake
so that he might reveal his power.
9 He rebuked the Sea of Reeds, and it dried up.
Then he led them through the depths, as through a wilderness.
10 He saved them from the hand of those who hated them,
and he rescued them from the hand of the enemy.
11 But the waters covered their adversaries;
not one of them survived.
12 Then they believed his words,
and they sang his praise.
13 But they quickly forgot his deeds;
they did not wait for his instructions.
14 They had insatiable cravings in the wilderness,
and they challenged God in the desert.
15 So he gave them what they requested,
but he sent a horrible disease upon them.
16 In the camp they became jealous of Moses
and Aaron, the holy priest of Yahweh.
17 The earth opened and swallowed up Dathan
and covered the company of Abiram.
18 Fire broke out in their company;
the fire consumed the wicked.
19 They made a calf at Horeb
and worshiped a cast metal figure.
20 They traded the glory of God
for the image of a bull that eats grass.
21 They forgot God their Savior,
who had done great deeds in Egypt.
22 He had done wonderful things in the land of Ham
and awesome deeds at the Sea of Reeds.
23 So he said he would destroy them—
had not Moses, his chosen one, stood in the breach before him,
to turn away his anger from destroying them.
24 Then they despised the delightful land;
they did not believe his promise,
25 but grumbled in their tents,
and did not obey Yahweh.
26 Therefore he raised his hand and swore to them
that he would let them die in the desert,
27 scatter their descendants among the nations,
and scatter them in foreign lands.
28 They worshiped the Baal of Peor
and ate the sacrifices offered to the dead.
29 They provoked him to anger with their actions,
and a plague broke out among them.
30 Then Phinehas stood up and mediated,
and the plague subsided.
31 It was counted to him as a righteous deed
to all generations forever.
32 They also angered Yahweh at the waters of Meribah,
and Moses suffered because of them.
33 They made his spirit bitter,
and he spoke thoughtlessly with his lips.
34 They did not destroy the nations
as Yahweh had commanded them,
35 but they mingled with the nations,
learned their practices,
36 and worshiped their idols,
which became a snare to them.
37 They sacrificed their sons and their daughters to demons.
38 They shed innocent blood,
the blood of their sons and of their daughters,
whom they sacrificed to the idols of Canaan,
desecrating the land with blood.
39 They were defiled by their deeds;
in their actions they were like prostitutes.
40 So Yahweh was angry with his people,
and he abhorred his inheritance.
41 He gave them into the hand of the nations,
and those who hated them ruled over them.
42 Their enemies oppressed them,
and they were brought into subjection to their authority.
43 Many times he came to help them,
but they were rebellious in their purposes
and were brought low by their own iniquity.
44 Nevertheless, he paid attention to their distress
when he heard their cry for help.
45 He called to mind his covenant with them
and relented because of his steadfast love.
46 He caused all their captors
to have pity on them.
47 Save us, Yahweh, our God.
Gather us from among the nations
so that we may give thanks to your holy name
and glory in your praises.
48 May Yahweh, the God of Israel, be praised
from everlasting to everlasting.
All the people said, "Amen."
Give praise to Yah. [2]
1 A yabi Yahweh. A bada girma ga Yahweh, domin shi nagari ne, domin alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada. 2 Wa zai lissafa manyan ayyukan Yahweh ko yayi cikakken shelar dukkan ayyukansa da suka cancanci yabo? 3 Masu albarka ne waɗanda suke yin abin dake dai-dai, waɗanda kuma a koyaushe ayyukansu baratattu ne. 4 Ka tuna dani a rai, Yahweh, sa'ad da ka nuna tagomashi ga mutanenka; ka taimake ni sa'ad da ka cece su. 5 Daga nan zan ga wadatar zaɓaɓɓun ka, in yi farinciki cikin murnar ƙasarka, da ɗaukaka tare da gãdonka. 6 Mun yi zunubi kamar Kakanninmu; mun yi laifi, mun kuma aikata mugunta. 7 Ubanninmu basu yaba wa ayyukanka masu ban mamaki ba a Masar; suka yi banza da ayyukanka masu yawa na alƙawarin aminci; suka yi tawaye a bakin teku, Tekun Iwa. 8 Duk da haka, ya cece su domin sunansa saboda ya bayyana ikonsa. 9 Ya tsautawa Tekun Iwa, ya kuwa bushe. Daga nan ya bida su ta cikin zurfafan, kamar ta cikin jeji. 10 Ya cece su daga hannun waɗanda suka ƙi su, ya kuma ƙwato su daga hannun maƙiyansu. 11 Amma ruwayen suka rufe magaftansu; babu wanin su da ya tsira. 12 Daga nan suka gaskata maganganunsa, kuma suka raira yabonsa. 13 Amma nan da nan suka manta da abin da yayi; ba su jira umarninsa ba. 14 Suka yi kwaɗayi marar ƙosarwa a jeji, kuma suka ƙalubalanci Allah a cikin hamada. 15 Ya basu abin da suka roƙa, amma ya aika da cuta wadda ta cinye jikkunansu. 16 A sansanin suka zama masu kishin Musa da Haruna, firist mai tsarki na Yahweh. 17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta kuma rufe mabiyan Abiram. 18 Wuta ta ɓarke a tsakaninsu; wutar ta cinye mãsu mugunta. 19 Suka yi maraƙi a Horeb suka kuma yi sujada ga sarrafaffar siffar ƙarfe. 20 Suka musanya ɗaukakar Allah domin siffar maraƙi mai cin ciyawa. 21 Suka manta da Allah Maicetonsu, wanda yayi manyan ayyuka a Masar. 22 Yayi abubuwan ban mamaki a ƙasar Ham ya kuma yi ayyuka masu iko a Tekun Iwa. 23 Da ya zartar da dokar hallakar dasu, inda ba domin Musa, zaɓaɓɓensa, ya shiga tsakaninsu da shi ba ya juya fushinsa daga hallakar dasu. 24 Daga nan suka raina ƙasa mai bayar da amfani; ba su gaskata da alƙawarinsa ba, 25 amma suka yi gunaguni a rumfunansu, ba su kuma yi biyayya da Yahweh ba. 26 Saboda haka ya ɗaga hannunsa kuma ya rantse masu cewa zai barsu su mutu a hamada, 27 ya warwatsa zuriyarsu cikin al'ummai, ya kuma warwatsa su cikin bãƙin ƙasashe. 28 Suka yi sujada ga Ba'al na fowa suka kuma ci hadayun da a ke miƙawa ga matattu. 29 Suka cakune shi ya yi fushi da ayyukansu, annoba kuwa ta faso a tsakaninsu. 30 Daga nan Fenihas ya tashi ya kai ɗauki, annobar kuwa ta tsagaita. 31 Aka lissafa masa shi a matsayin aikin adalci ga dukkan tsara har abada. 32 Suka kuma ba Yahweh haushi a ruwayen Meriba, Musa kuma ya sha wahala saboda su. 33 Suka sa Musa ya ji haushi, ya kuma yi magana da fushi. 34 Basu hallakar da al'ummai ba kamar yadda Yahweh ya dokace su, 35 amma suka gauraye da al'ummai suka kuma koyi hanyoyinsu 36 kuma suka yi sujada ga gumakansu, waɗanda suka zamar masu tarko. 37 Suka yi hadayar 'ya'yansu maza da 'ya'yansu mata ga aljanu. 38 Suka zubar da jini marar laifi, jinin 'ya'yansu maza da 'ya'yansu mata, waɗanda suka yi hadaya dasu ga gumakan Kan'ana, suka ƙazantar da ƙasar da jini. 39 Suka ɓãci da ayyukansu; cikin ayyukansu suka zama kamar karuwai. 40 Saboda haka Yahweh ya yi fushi da mutanensa, ya kuma rena nasa mutanen. 41 Ya bayar dasu cikin hannun al'ummai, waɗanda kuma suka ƙi su suka yi mulki a kansu. 42 Maƙiyan su suka tsananta masu, aka kuma kawo su ƙarƙashin hukuncinsu. 43 Lokutta da yawa yazo ya taimake su, amma suka ci gaba da yin tawaye aka kuma kawo su ƙasa ta wurin zunubinsu. 44 Duk da haka, ya lura da ƙuncin su sa'ad da ya ji kukansu domin taimako. 45 Ya tuna a ransa da alƙawarin sa tare dasu ya kuma yi jinkiri saboda matuƙar ƙaunarsa. 46 Ya sa dukkan waɗanda suka yi nasara dasu suka ji tausayin su. 47 Ka cece mu, Yahweh, Allahnmu. Ka tattaro mu daga cikin al'ummai domin mu ba da godiya ga sunan ka mai tsarki mu kuma yi ɗaukaka cikin yabban ka. 48 Bari Yahweh, Allah na Isra'ila, ya sami yabo daga matuƙa zuwa matuƙa. Dukkan mutane sukace, "Amin." A yabi Yahweh. Littafi na Biyar
1 Give thanks to Yahweh, for he is good,
and his covenant faithfulness endures forever.
2 Let the redeemed of Yahweh speak out,
those he has rescued from the hand of the enemy.
3 He has gathered them out of foreign lands,
from the east and from the west,
from the north and from the south.
4 They wandered in the wilderness on a desert road
and found no city in which to live.
5 Because they were hungry and thirsty,
they fainted from exhaustion.
6 Then they called out to Yahweh in their trouble,
and he rescued them out of their distress.
7 He led them by a direct path
so that they would go to a city to live in.
8 Oh that people would praise Yahweh for his covenant faithfulness
and for the amazing things he has done for humanity!
9 For he satisfies the longings of those who are thirsty,
and the desires of those who are hungry he fills up with good things.
10 Some sat in darkness and in the shadow of death,
prisoners in affliction and chains.
11 This was because they had rebelled against God's word
and rejected the instruction of the Most High.
12 He humbled their hearts through hardship;
they stumbled and there was no one to help them up.
13 Then they called out to Yahweh in their trouble,
and he saved them out of their distress.
14 He brought them out of darkness and gloom
and broke their bonds.
15 Oh that people would praise Yahweh for his covenant faithfulness
and for the amazing things he has done for humanity!
16 For he has broken the gates of bronze
and cut through the bars of iron.
17 They were foolish in their rebellious ways
and afflicted because of their iniquities.
18 Their soul abhorred all food,
and they came close to the gates of death.
19 Then they called out to Yahweh in their trouble,
and he saved them out of their distress.
20 He sent his word and healed them,
and he rescued them from the pits in which they were trapped.
21 Oh that people would praise Yahweh for his covenant faithfulness
and for the amazing things he has done for humanity!
22 Let them offer the sacrifices of thanksgiving
and proclaim his deeds with shouts of joy.
23 Some travel on the sea in ships
and do business overseas.
24 These saw the deeds of Yahweh
and his wonders on the seas.
25 For he commanded and aroused the windstorm
that stirs up the seas.
26 They reached up to the sky; they went down to the depths.
Their lives melted away in distress.
27 They swayed and staggered like drunkards
and were at their wits' end.
28 Then they called out to Yahweh in their trouble,
and he brought them out of their distress.
29 He calmed the storm,
and the waves were stilled.
30 Then they rejoiced because the sea was calm,
and he brought them to their desired harbor.
31 Oh that people would praise Yahweh for his covenant faithfulness
and for the amazing things he has done for humanity!
32 Let them exalt him in the assembly of the people
and praise him in the council of the elders.
33 He turns rivers into a wilderness,
springs of water into dry land,
34 and a fruitful land into a barren place
because of the wickedness of its people.
35 He turns the wilderness into a pool of water
and dry land into springs of water.
36 He settles the hungry there,
and they build a city to live in.
37 They sowed fields and planted vineyards
that yielded a fruitful harvest.
38 He blesses them so they are very numerous.
He does not let their livestock decrease in number.
39 They were diminished and brought low
by oppression, distress, and suffering.
40 He pours contempt on the leaders
and causes them to wander in the wilderness, where there are no roads.
41 But he protects the needy from affliction
and cares for his families like a flock.
42 The upright will see this and rejoice,
and all wickedness shuts its mouth.
43 Whoever is wise should take note of these things
and meditate on Yahweh's acts of covenant faithfulness.
1 Ku ba da godiya ga Yahweh, domin shi nagari ne, kuma alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada. 2 Bari fansassun Yahweh suyi magana, waɗanda ya cafko daga hannun maƙiyi. 3 Ya tattaro su daga bãƙin ƙasashe, daga gabas daga kuma yamma, daga arewa daga kuma kudu. 4 Suka yi yawo a jeji bisa hanyar hamada ba su kuma sami birnin da zasu zauna ba. 5 Saboda sunji yunwa da ƙishi, suka some cikin gajiya. 6 Daga nan suka yi kira ga Yahweh cikin damuwarsu, ya kuma ceto su daga ƙuncinsu. 7 Ya bida su ta miƙaƙƙen tafarki saboda su tafi cikin birnin da zasu zauna. 8 Da ma mutane su yabi Yahweh domin alƙawarin amincinsa domin kuma abubuwan ban mamaki da yayi domin 'yan adam! 9 Domin ya biya buƙatun begen masu jin ƙishi, da marmarin masu jin yunwa ya cika da abubuwa masu kyau. 10 Waɗansu suka zauna cikin duhu da ɓoyewa, 'yan kurkuku cikin ƙunci da sarƙoƙi. 11 Wannan kuwa saboda sun yi tawaye gãba da maganar Yahweh suka kuma yi watsi da umarnin Maɗaukaki. 12 Ya ƙasƙantar da zukatansu ta wurin shan wuya; suka yi tuntuɓe kuma babu wanda zai taimake su ya ɗaga su. 13 Daga nan suka yi kira ga Yahweh a cikin damuwarsu, ya kuma fito dasu daga cikin ƙuncinsu. 14 Ya fito dasu daga cikin duhu da ɓoyewa ya kuma karya karkiyarsu. 15 Dãma mutane su yabi Yahweh domin alƙawarin amincinsa domin kuma abubuwan ban mamaki da ya yi domin 'yan adam! 16 Domin ya karya ƙofofin tagulla ya kuma datse ginshiƙan ƙarfe. 17 Sun yi wawanci a cikin hanyoyinsu na tawaye suka kuma ƙuntata saboda zunubansu. 18 Marmarinsu na cin abinci ya ɓace, suka kuma zo kusa da ƙofofin mutuwa. 19 Daga nan suka yi kira ga Yahweh a cikin damuwarsu, ya kuma fito dasu daga cikin ƙuncin su. 20 Ya aika da maganarsa ya warkar da su, ya kuma ceto su daga hallakarsu. 21 Dãma mutane su yabi Yahweh domin alƙawarin amincinsa domin kuma abubuwan ban mamaki da yayi domin 'yan adam! 22 Bari su miƙa hadayun godiya su kuma yi shelar ayyukansa cikin waƙa. 23 Waɗansu suka yi tafiya bisa teku cikin jiragen ruwa suka kuma yi sana'o'i bisa tekuna. 24 Waɗannan sun ga ayyukan Yahweh da al'ajibansa bisa tekuna. 25 Domin ya bada umarni ya kuma zuga iskar guguwa dake motsa tekuna. 26 Suna kaiwa ga sararin sama; su tafi ƙasa cikin zurfafa. Rayuwar suna narkewa cikin ƙunci. 27 Suna gushewa suyi tangaɗi kamar bugaggu waɗanda kuma suka kawo ga ƙarshen iyawarsu. 28 Daga nan suka yi kira ga Yahweh cikin damuwarsu, ya kuma fito dasu daga cikin ƙuncinsu. 29 Ya tausar da guguwar, kuma raƙuman suka yi tsit. 30 Daga nan suka yi farinciki saboda tekun ya tausu, ya kuma kawo su in da suke so su sauka. 31 Dãma mutane su yabi Yahweh domin alƙawarin amincinsa domin kuma abubuwan ban mamaki da ya yi domin 'yan adam! 32 Bari su ɗaukaka shi a cikin taron mutane su kuma yabe shi a majalisar dattawa. 33 Ya maida koguna suka koma jeji, maɓulɓulan ruwa suka koma busasshiyar ƙasa, 34 da ƙasa mai bada 'ya'ya zuwa bakararen wuri saboda muguntar mutanenta. 35 Ya maida jeji kuma ya zama tafkin ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulan ruwa. 36 Ya wadatar da masu jin yunwa a wurin, suka kuma gina birni su zauna a ciki. 37 Suka gina birni su dasa gonaki a ciki, su dasa garkunan inabi, su kuma kawo yalwar kaka. 38 Ya albarkace su suka zama fiye da lissafi sosai. Bai bar garken dabbobinsu ba su ragu a lissafi. 39 Suka ragu aka kuma ƙasƙantar dasu ta wurin ƙunci mai zafi da wahala. 40 Ya zubo raini bisa shugabanninsu yasa kuma suka yi yawo cikin jeji, in da babu hanyoyi. 41 Amma ya kiyaye mabuƙata daga ƙunci ya kuma lura da iyalinsa kamar garken tumaki. 42 Masu adalci zasu dubi wannan suyi farinciki, dukkan mugunta kuma ta rufe bakinta. 43 Duk mai hikima ya yi la'akari da waɗannan abubuwa ya kuma yi tunani bisa ayyukan Yahweh na alƙawarin aminci.
1 My heart is fixed, God!
I will sing, yes, I will sing praises with all my glory.
2 Wake up, lute and harp;
I will wake up the dawn.
3 I will give thanks to you, Yahweh, among the peoples;
I will sing praises to you among the nations.
4 For your covenant faithfulness is great above the heavens;
and your trustworthiness reaches to the skies.
5 Be exalted, God, above the heavens,
and may your glory be exalted over all the earth.
6 So that those you love may be rescued,
rescue us with your right hand and answer me.
7 God has spoken in his holiness; "I will rejoice;
I will divide Shechem
and apportion out the Valley of Sukkoth.
8 Gilead is mine, and Manasseh is mine;
Ephraim also is my helmet;
Judah is my scepter.
9 Moab is my washbasin;
over Edom I will throw my sandal;
I will shout in triumph because of Philistia.
10 Who will bring me into the fortified city?
Who will lead me to Edom?"
11 God, have you not rejected us?
You do not go into battle with our army.
12 Give us help against the enemy,
for man's help is futile.
13 We will triumph with God's help;
he will trample down our enemies.
1 Zuciyata ta kafu, Allah; zan raira, I, zan raira yabbai kuma tare da zuciyata ta girmamawa. 2 Ku tashi, sarewa da garaya; zan tashi da asuba. 3 Zan bada godiya gare ka, Yahweh, a tsakanin mutane; zan raira yabbai gareka a tsakanin al'ummai. 4 Domin alƙawarin amincinka mai girma ne sama da sammai; amincin ka kuma ya kai sararin sama. 5 Ka ɗaukaka, Allah, sama da sammai, bari kuma darajarka ta ɗaukaka sama da dukkan duniya. 6 Domin waɗanda kake ƙauna su sami ceto, ka ceto mu da hannunka na dama ka kuma amsa mani. 7 Allah yayi magana cikin tsarkinsa; "Zan yi farinciki; zan raba Shekem in kuma yi kason kwarin Sukkot. 8 Giliyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Ifraim ma ƙwalƙwali nane; Yahuda kuma sandar sarautana ne. 9 Mowab kwanon wankina ne; bisa Idom zan jefa takalmina; Zanyi sowa cikin nasara saboda Filitiya. 10 Wa zai kawo ni ckin birni mai karfi? Wa zai bida ni zuwa Idom?" 11 Allah, baka watsar damu ba? Baka tafi cikin yaƙi tare da mayaƙanmu ba. 12 Ka ba mu taimako gãba da maƙiyinmu, domin taimakon mutum wofi ne. 13 Zamu yi nasara da taimakon Allah; zaya tattake maƙiyanmu.
1 God whom I praise,
do not be silent.
2 For the wicked and deceitful attack me;
they speak lies against me.
3 They surround me and say hateful things,
and they attack me without cause.
4 In return for my love they accuse me,
but I pray for them.
5 They repay me evil for good,
and hatred for my love.
6 Appoint a wicked man over such an enemy as these people;
appoint an accuser to stand at his right hand.
7 When he is judged, may he be found guilty;
may his prayer be considered sinful.
8 May his days be few;
may another take his office.
9 May his children be fatherless,
and may his wife be a widow.
10 May his children wander about and beg,
seeking food far from their ruined home.
11 May the creditor seize all he owns;
may strangers plunder the product of his labor.
12 May no one extend any kindness to him;
may no one have pity on his fatherless children.
13 May his descendants be cut off;
may their name be blotted out in the next generation.
14 May his ancestors' iniquity be remembered before Yahweh;
and may the sin of his mother not be forgotten.
15 May their sins always be before Yahweh;
may he cut off their memory from the earth.
16 May Yahweh do this, for that man never bothered to show any covenant faithfulness,
but harassed the oppressed, the needy,
and the brokenhearted to death.
17 He loved cursing;
may it come back upon him.
He hated blessing;
may it be far from him.
18 He clothed himself with cursing as his garment,
and his curse came into his body like water,
like oil into his bones.
19 May his curses be to him like the clothes he wears to cover himself,
like the belt he always wears.
20 May this be the reward of my accusers from Yahweh,
of those who say evil things about me.
21 Yahweh my Lord, deal kindly with me for your name's sake.
Because your covenant faithfulness is good, save me.
22 For I am oppressed and needy,
and my heart is wounded within me.
23 I am fading away like the shadow of the evening;
I am shaken off like a locust.
24 My knees are weak from fasting;
my body has become thin and has no fat.
25 I have become an object of scorn to my accusers;
when they see me, they shake their heads.
26 Help me, Yahweh my God;
save me by your covenant faithfulness.
27 Let them know that this is your hand,
that you, Yahweh, have done this.
28 They curse, but you bless;
when they attack, may they be put to shame,
but may your servant rejoice.
29 May my adversaries be clothed with shame;
may they wear their shame like a robe.
30 With my mouth I give great thanks to Yahweh;
I will praise him in the midst of a crowd.
31 For he will stand at the right hand of the one who is needy,
to save him from those who condemn him.
1 Allah wanda nake yabo, kada ka yi shiru, 2 Domin miyagu da macuta sun kawo mani hari; sun faɗi ƙarairayi game dani. 3 Sun kewaye ni kuma sun faɗi abubuwan ƙiyayya, kuma sun kawo mani hari babu dalili. 4 A ramuwar ƙaunata sun kawo mani sãra, amma nayi addu'a domin su. 5 Sun biya nagarta ta da mugunta, kuma sun ƙi ƙauna ta. 6 Ka naɗa mugun mutum bisa irin waɗannan maƙiya kamar waɗannan mutanen; ka naɗa mai sãra ya tsaya a hannun damansa. 7 Idan aka shar'anta shi, bari a same shi mai laifi; bari addu'arsa a ɗauke ta zunubi. 8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani ya ɗauki gurbinsa. 9 Bari 'ya'yansa su zama marasa mahaifi, matar sa kuma gwauruwa. 10 Bari 'ya'yan sa su tafi gantali da bara. Suna roƙon abin da aka rage yayin da suka bar rusassun gidajensu. 11 Bari mai bin bashi ya ɗauke dukkan abin da ya mallaka; bari bãƙi su washe abin da ya ke samu. 12 Kada wani ya miƙa wani halin kirki gare shi; kada wani ya ji tausayin 'ya'yansa marasa mahaifi. 13 Bari a datse 'ya'yan sa; bari a share sunansu daga tsara ta gaba. 14 Bari a faɗi zunuban kakanninsa ga Yahweh; bari kuma kada a manta da zunubin mahaifiyarsa. 15 Bari laifinsu a koyaushe ya kasance a gaban Yahweh; Bari Yahweh ya datse tunawa dasu daga duniya. 16 Bari Yahweh yayi haka saboda mutumin nan bai kula daya nuna wani alƙawarin aminci ba, amma a maimako ya firgitar da masu shan tsanani, masu buƙata, da masu ɓacin zuciya har ga mutuwa. 17 Yana ƙaunar la'ana; bari ta dawo kansa. Yaƙi albarka; bari kada albarka ta zo gareshi. 18 Ya lulluɓe kansa da la'ana kamar tufafi, kuma la'anarsa ta shiga cikin sa kamar ruwa, kamar mai cikin ƙasusuwansa. 19 Bari la'anoninsa su zame masa kamar suturar da ya ke sanyawa ya rufe kansa, kamar ɗamarar da ya ke sanyawa koyaushe. 20 Bari wannan ya zama rabon masu zargina daga Yahweh, ga waɗanda ke faɗin miyagun abubuwa game dani. 21 Yahweh Ubangijina, ka yi mani alheri sabili da sunanka. Saboda alƙawarin amincinka nagari ne, ka cece ni. 22 Domin ni mai shan tsanani ne mai buƙata kuma, zuciya ta kuma taji ciwo a cikina. 23 Ina ƙarewa kamar inuwar maraice; Ina kakkaɓewa kamar fãra. 24 Gwiwowina sun rasa ƙarfi daga azumi; Ina komawa fata da ƙasusuwa. 25 Na zama wulaƙantacce wurin masu zargina; idan suka ganni, suna girgiza kawunansu. 26 Ka taimake ni, Yahweh Allahna; ka cece ni ta wurin alƙawarin amincin ka. 27 Bari su san cewa wannan yinka ne, cewa kai, Yahweh, ka yi wannan. 28 Koda ya ke sun la'ance ni, ina roƙon ka ka albarkace ni; Idan suka kawo hari, bari su sha kunya, amma bari bawanka yayi farinciki. 29 Bari magafta na suyi sutura da kunya; bari su sanya kunyar su kamar alkyabba. 30 Da bakina na bada babbar godiya ga Yahweh; Zan yabe shi a tsakiyar taro. 31 Domin zai tsaya a hannun daman wanda keda buƙata; ya cece shi daga waɗanda ke shar'ianta shi.
1 The declaration of Yahweh to my lord:
"Sit at my right hand
until I make your enemies your footstool."
2 Yahweh will hold out the scepter of your strength from Zion;
rule among your enemies.
3 Your people will follow you in holy garments
of their own free will on the day of your power;
from the womb of the dawn your youth will be to you like the dew.
4 Yahweh has sworn and will not change his mind:
"You are a priest forever,
after the manner of Melchizedek."
5 The Lord is at your right hand.
He will kill kings on the day of his anger.
6 He will judge the nations;
he will fill the battlegrounds with dead bodies;
he will kill the leaders in many countries.
7 He will drink of the brook along the road,
and then he will lift his head up high after victory.
1 Yahweh ya cewa ubangijina, "Ka zauna hannun damana har sai na maida maƙiyanka abin takawar ka." 2 Yahweh zai riƙe sandar mulkin ƙarfin ka daga Sihiyona; kayi mulki a tsakiyar maƙiyanka. 3 Mutanenka zasu bi ka cikin tsarkakan tufafi da nufin kansu ranar ikonka; daga mahaifar asubahi ƙuruciyar ka zata zame maka a kamar raɓa. 4 Yahweh yayi rantsuwa, kuma ba zai canza ba: "Kai firist ne na har abada, bisa ga ɗabi'ar Melkizadek." 5 Ubangiji yana hannun damanka. Zai kashe sarakuna a ranar fushinsa. 6 Zai shar'anta al'ummai; zai cika filin yaƙi da gawarwaki; zai kashe shugabanni a ƙasashe masu yawa. 7 Zai sha daga rafin bakin hanya, daga nan kuma zai ɗaga kansa sama bayan nasara.
1 Give praise to Yah. [1]
I will give thanks to Yahweh with my whole heart
in the assembly of the upright, in their gathering.
2 The works of Yahweh are great,
eagerly awaited by all those who desire them.
3 His work is majestic and glorious,
and his righteousness endures forever.
4 He does wonderful things that will be remembered;
Yahweh is gracious and merciful.
5 He gives food to his faithful followers.
He will always call to mind his covenant.
6 He showed his powerful works to his people
in giving them the inheritance of the nations.
7 The works of his hands are trustworthy and just;
all his instructions are reliable.
8 They are established forever,
to be observed faithfully and properly.
9 He sent redemption to his people;
he ordained his covenant forever;
holy and awesome is his name.
10 To honor Yahweh is the beginning of wisdom;
those who carry out his instructions have good understanding.
His praise endures forever.
1 Ku yabi Yahweh. Zan bada godiya ga Yahweh da dukkan zuciyata a cikin taron masu adalci, a cikin tattaruwarsu. 2 Ayyukan Yahweh masu girma ne, ana jira da ɗoki ga dukkan waɗanda ke marmarin su. 3 Aikin sa mai daraja ne cike da ɗaukaka, adalcinsa kuma ya dawwama har abada. 4 Yana yin abubuwan ban mamaki daza a tuna; Yahweh cike da alheri ya ke cike kuma da jinƙai. 5 Yana bayar da abinci ga amintattun mabiyansa. Za ya tuna a ransa koyaushe da alƙawarinsa. 6 Ya nuna ayyukansa a cike da iko ga mutanensa inda ya basu gãdon al'ummai. 7 Ayyukan hannuwansa sun isa amincewa da hukunci; dukkan umarninsa abin dogara ne. 8 An kafa su har abada, domin a kiyaye su da aminci a dai-dai kuma. 9 Ya bada nasara ga mutanensa; ya naɗa alƙawarinsa har abada; tsarki da ban mamaki ne sunansa. 10 Girmama Yahweh shi ne farkon hikima; waɗanda suke aikata umarninsa suna da fahimta mai kyau. Yabonsa ya dawwama har abada.
1 Give praise to Yah. [1]
Blessed is the man who fears Yahweh,
who greatly delights in his commandments.
2 His descendants will be powerful on earth;
the descendants of the godly man will be blessed.
3 Wealth and riches are in his house;
his righteousness will endure forever.
4 Light shines in the darkness for the godly person;
he is gracious, merciful, and just.
5 It goes well for the man who deals graciously and lends money,
who conducts his affairs with honesty.
6 For he will never be moved;
the righteous person will be remembered forever.
7 He does not fear bad news;
he is confident, trusting in Yahweh.
8 His heart is tranquil, without fear,
until he looks in triumph over his adversaries.
9 He gives freely to the poor;
his righteousness endures forever;
his horn will be exalted with honor.
10 The wicked person will see this and be angry;
he will grind his teeth in rage and he will melt away;
the desire of the wicked people will perish.
1 A yabi Yahweh. Mai albarka ne mutumin dake biyayya da Yahweh, wanda ya ke jin daɗin dokokinsa sosai. 2 Zuriyarsa zasu zama cike da iko a duniya; zuriyar mutum mai tsoron Allah masu albarka ne. 3 Dukiya da arziki suna cikin gidansa; adalcinsa zai dawwama har abada. 4 Haske yana haskaka wa cikin duhu domin taliki mai tsoron Allah; yana cike da alheri, cike da jinƙai, da hukunci. 5 Yana tafiya lafiya ga mutumin dake aikata alheri da bayar da rancen kuɗi, wanda ke tafiyar da al'amuransa tare da gaskiya. 6 Domin ba zai taɓa gusawa ba; mai adalci za a tuna da shi har abada. 7 Baya jin tsoron mugun labari; yana da ƙarfin hali, dogara ga Yahweh. 8 Zuciyar sa lif, ba tare da tsoro ba, har sai ya duba cikin nasara bisa magabtansa. 9 A yalwace ya ke bayar wa ga talakawa; adalcinsa ya dawwama har abada; za a ɗaukaka shi da girmamawa. 10 Wanda ke mugu zai duba wannan kuma ya ji haushi; zai ciza haƙoransa ya kuma narke; marmarin miyagun mutane zaya lalace.
1 Give praise to Yah. [1]
Praise him, you servants of Yahweh;
praise the name of Yahweh.
2 Blessed be the name of Yahweh,
both now and forevermore.
3 From the rising of the sun to its setting,
Yahweh's name should be praised.
4 Yahweh is exalted above all nations,
and his glory reaches above the skies.
5 Who is like Yahweh our God,
who has his seat on high,
6 who humbles himself to look down
at the sky and at the earth?
7 He raises up the poor out of the dirt
and lifts up the needy from the ash heap,
8 so that he may seat him with princes,
with the princes of his people.
9 He gives a home to the barren woman of the house;
he makes her a joyful mother of children.
Give praise to Yah! [2]
1 Ku yabi Yahweh. Ku yabe shi ku bayin Yahweh; ku yabi sunan Yahweh. 2 Albarka ta tabbata ga sunan Yahweh, duk da yanzu da har abada abadin. 3 Daga tasowar rana har zuwa faɗuwarta, sunan Yahweh ya sami yabo. 4 Yahweh ya ɗaukaka sama da dukkan al'ummai, darajarsa kuma ta wuce gaban sararin sammai. 5 Wane ne kamar Yahweh Allahnmu, wanda keda mazauninsa a sama, 6 wanda ke duba sararin sama da duniya? 7 Yana taso da talaka daga datti kuma ya ɗaga mabuƙaci daga tarin toka, 8 domin ya zaunar da shi tare da shugabanni, tare da shugabannin mutanensa. 9 Yana bayar da gida ga bakarariyar macen gidan, yana mayar da ita uwar 'ya'ya cike da farinciki. A yabi Yahweh!
1 When Israel left Egypt,
the house of Jacob from a people who spoke a foreign language,
2 Judah became his holy place,
Israel his kingdom.
3 The sea looked and fled;
the Jordan turned back.
4 The mountains skipped like rams,
the hills skipped like lambs.
5 Why did you flee, sea?
Jordan, why did you turn back?
6 Mountains, why did you skip like rams?
You little hills, why did you skip like lambs?
7 Tremble, earth, before the Lord,
at the presence of the God of Jacob.
8 He turned the rock into a pool of water,
the hard rock into a spring of water.
1 Da Isra'ila suka bar Masar, gidan Yakubu daga waɗannan bãƙin mutane, 2 Yahuda ya zama wurinsa mai tsarki, Isar'ila masarautarsa. 3 Teku ya duba kuma ya gudu; Yodan ya juya baya. 4 Duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai suka yi tsalle kamar 'yan raguna. 5 Me yasa ka gudu, teku? Yodan, me yasa ka juya baya? 6 Duwatsu, me yasa kuka yi tsalle kamar raguna? Ku ƙananan tuddai, me yasa kuka yi tsalle kamar 'yan raguna? 7 Yi rawar jiki, duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allahn Yakubu. 8 Ya juya dutse ya zama tafkin ruwa, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓular ruwa.
1 Not to us, Yahweh, not to us,
but to your name bring honor,
for your covenant faithfulness
and for your trustworthiness.
2 Why should the nations say,
"Where is their God?"
3 Our God is in heaven;
he does whatever he pleases.
4 The nations' idols are silver and gold,
the work of men's hands.
5 Those idols have mouths, but they do not speak;
they have eyes, but they do not see;
6 they have ears, but they do not hear;
they have noses, but they do not smell.
7 Those idols have hands, but do not feel;
they have feet, but they cannot walk;
nor do they speak from their mouths.
8 Those who make them are like them,
as is everyone who trusts in them.
9 Israel, trust in Yahweh;
he is your help and shield.
10 House of Aaron, trust in Yahweh;
he is your help and shield.
11 You who honor Yahweh, trust in him;
he is your help and shield.
12 Yahweh takes notice of us and will bless us;
he will bless the family of Israel;
he will bless the family of Aaron.
13 He will bless those who honor him,
both young and old.
14 May Yahweh increase your numbers more and more,
yours and your descendants'.
15 May you be blessed by Yahweh,
who made heaven and earth.
16 The heavens belong to Yahweh;
but the earth he has given to mankind.
17 The dead do not give praise to Yah, [1]
nor do any who go down into silence;
18 But we will give praise to Yah,
now and forevermore.
Give praise to Yah! [2]
1 Ba gare mu ba, Yahweh, ba gare mu ba, amma ga sunanka ka kawo daraja, domin alƙawarin amincinka domin kuma isar amincewarka. 2 Me yasa al'ummai zasu ce, "Ina Allahnsu?" 3 Allahnmu yana sama; yana yin abin daya so. 4 Gumakan al'ummai azurfa ne da zinariya, aikin hannuwan mutane. 5 Waɗannan gumakai suna da baki, amma ba su magana; suna da idanu, amma basu gani; 6 suna da kunnuwa, amma basu ji; suna da hanci, amma basu sunsuna wa. 7 Waɗannan gumakai suna da hannuwa, amma basu taɓa wa; suna da tafin ƙafafu, amma basu tafiya; ko kuwa suyi magana daga bakunansu. 8 Waɗanda suka yi su kamar su suke, haka ma duk wanda ya dogara gare su. 9 Isra'ila, ku dogara ga Yahweh; shi ne taimakonku da garkuwarku. 10 Gidan Haruna, ku dogara ga Yahweh; shi ne taimakonku da garkuwarku. 11 Ku waɗanda ke girmama Yahweh, ku dogara gare shi; shi ne taimakonku da garkuwarku. 12 Yahweh yana la'akari damu kuma zai albarkace mu; zai albarkaci iyalin Isra'ila; zai albarkaci iyalin Haruna. 13 Zai albarkaci waɗanda ke girmama shi, yara da tsofaffi. 14 Bari Yahweh ya ƙara lissafin ku ƙari da ƙari, naku dana zuriyarku. 15 Bari ku yi albarka ta wurin Yahweh, wanda yayi sama da duniya. 16 Sammai na Yahweh ne; amma duniya ya bayar ga 'yan adam. 17 Matattu basu yabon Yahweh, ko kuwa wani wanda ya gangara cikin shiru; 18 Amma zamu albarkaci Yahweh yanzu da har abada abadin. A Yabi Yahweh.
1 I love Yahweh because he hears
my voice and my pleas for mercy.
2 Because he listened to me,
I will call on him as long as I live.
3 The cords of death surrounded me,
and the snares of Sheol confronted me;
I felt anguish and sorrow.
4 Then I called on the name of Yahweh:
"I beg you, Yahweh, rescue my life."
5 Yahweh is gracious and just;
our God is compassionate.
6 Yahweh protects the naive;
I was brought low, and he saved me.
7 My soul can return to its resting place,
for Yahweh has been good to me.
8 For you rescued my life from death,
my eyes from tears,
and my feet from stumbling.
9 I will serve Yahweh
in the land of the living.
10 I believed in him, even when I said,
"I am greatly afflicted."
11 In my alarm I said,
"All men are liars."
12 How can I repay Yahweh
for all his kindnesses to me?
13 I will raise the cup of salvation,
and call on the name of Yahweh.
14 I will fulfill my vows to Yahweh
in the presence of all his people.
15 Precious in the sight of Yahweh
is the death of his faithful ones.
16 Yahweh, indeed, I am your servant;
I am your servant, the son of your servant woman;
you have taken away my bonds.
17 I will offer to you the sacrifice of thanksgiving
and will call on the name of Yahweh.
18 I will fulfill my vows to Yahweh
in the presence of all his people,
19 in the courts of the house of Yahweh,
in your midst, Jerusalem.
Give praise to Yah! [1]
1 Ina ƙaunar Yahweh saboda yana jin murya ta da kuma roƙe-roƙe na domin jinƙai. 2 Saboda yana saurare na, zan yi kira a gare shi muddan ina da rai. 3 Sarƙoƙin mutuwa sun kewaye ni, tarkon Lahira kuma ya fuskance ni; naji ƙunci da baƙinciki. 4 Daga nan nayi kira ga sunan Yahweh: "Ina roƙon ka Yahweh, ka ceto rai na." 5 Yahweh yana cike da jinƙai da adalci; Allahnmu mai tausayi ne. 6 Yahweh yana kiyaye marasa sani; an kawo ni ƙasa, kuma ya cece ni. 7 Raina zai koma wurin hutawarsa, domin Yahweh yana yi mani da kyau. 8 Domin ka ceto raina daga mutuwa, idanu na daga hawaye, tafin ƙafafuna kuma daga tuntuɓe. 9 Zan bauta wa Yahweh a ƙasar masu rai. 10 Na bada gaskiya a gare shi, ko sa'ad da nace, "Ina cikin babban ƙunci." 11 Nayi garejen cewa, "Dukkan mutane maƙaryata ne." 12 Yaya zan biya Yahweh domin dukkan jiyejiyenƙansa zuwa gare ni? 13 Zan ɗaga ƙoƙon ceto, in kuma yi kira ga sunan Yahweh. 14 Zan cika alƙawaraina ga Yahweh a gaban dukkan mutanensa. 15 Abu mai daraja a gaban Yahweh shi ne mutuwar tsarkakansa. 16 Yahweh, tabbas, ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka ɗauke tsarƙoƙina. 17 Zan miƙa maka hadayar godiya in kuma yi kira ga sunan Yahweh. 18 Zan cika alƙawaraina ga Yahweh a gaban dukkan mutanensa, 19 cikin harabun gidan Yahweh, a tsakiyarki, Yerusalem. A yabi Yahweh.
1 Praise Yahweh, all you nations;
exalt him, all you peoples.
2 For his covenant faithfulness is great toward us,
and the trustworthiness of Yahweh endures forever.
Give praise to Yah! [1]
1 Ku yabi Yahweh, dukkan ku al'ummai; ku ɗaukaka shi, dukkan ku mutane. 2 Domin alƙawarin amincinsa mai girma ne zuwa gare mu, isar amincin Yahweh kuma ya dawwama har abada. A yabi Yahweh.
1 Give thanks to Yahweh, for he is good,
his covenant faithfulness endures forever.
2 Let Israel say,
"His covenant faithfulness endures forever."
3 Let the house of Aaron say,
"His covenant faithfulness endures forever."
4 Let the loyal followers of Yahweh say,
"His covenant faithfulness endures forever."
5 In my distress I called out to Yah;
Yah answered me and set me in a spacious place. [1]
6 Yahweh is with me; I will not be afraid;
what can man do to me?
7 Yahweh is on my side as my helper;
I will look in triumph on those who hate me.
8 It is better to take shelter in Yahweh
than to put confidence in man.
9 It is better to take refuge in Yahweh
than to put one's trust in princes.
10 All the nations surrounded me;
in Yahweh's name I cut them off.
11 They surrounded me; yes, they surrounded me;
in Yahweh's name I cut them off.
12 They surrounded me like bees;
they disappeared as quickly as fire among thorns;
in Yahweh's name I cut them off.
13 "You attacked me to knock me down,
but Yahweh helped me.
14 Yah is my strength and joy,
and he is the one who rescues me." [2]
15 The joyful shout of victory is heard in the tents of the righteous;
the right hand of Yahweh conquers.
16 The right hand of Yahweh is exalted;
the right hand of Yahweh conquers.
17 I will not die, but live
and declare what Yah has done. [3]
18 Yah has punished me harshly,
but he has not handed me over to death. [4]
19 Open to me the gates of righteousness;
I will enter them and I will give thanks to Yah. [5]
20 This is the gate of Yahweh;
the righteous enter through it.
21 I will give thanks to you, for you answered me,
and you have become my salvation.
22 The stone that the builders rejected
has become the cornerstone.
23 This is Yahweh's doing;
it is marvelous in our eyes.
24 This is the day on which Yahweh has acted;
we will rejoice and be glad in it.
25 We beg you, Yahweh, please give us victory!
We beg you, Yahweh, please give us success!
26 Blessed is he who comes in the name of Yahweh;
we bless you from the house of Yahweh.
27 Yahweh is God, and he has given us light;
bind the sacrifice with cords to the horns of the altar.
28 You are my God, and I will give thanks to you;
you are my God; I will exalt you.
29 Oh, give thanks to Yahweh, for he is good,
for his covenant faithfulness endures forever.
1 Ku bada godiya ga Yahweh, domin shi nagari ne, domin alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada. 2 Bari Isra'ila su ce, "Alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada." 3 Bari gidan Haruna su ce, "Alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada." 4 Bari amintattun masu bin Yahweh su ce, "Alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada." 5 A cikin ƙuncina nayi kira ga Yahweh; Yahweh ya amsa mani ya kuma 'yantar dani. 6 Yahweh yana tare dani; ba zan ji tsoro ba; me mutum zai yi mani? 7 Yahweh yana gefe na a matsayin mai taimako na; zan duba cikin nasara bisa waɗanda suka ƙi ni. 8 Ya fi kyau a ɗauki mahalli cikin Yahweh da a sa dogara cikin mutum. 9 Gwamma a ɗauki mafaka cikin Yahweh da wani yasa dogararsa cikin sarakuna. 10 Dukkan al'ummai sun kewaye ni; a cikin sunan Yahweh na datse su. 11 Sun kewaye ni; I, sun kewaye ni; a cikin sunan Yahweh na datse su. 12 Sun kewaye ni kamar zuma; sun ɓace da sauri kamar wuta a tsakiyar sarƙaƙiya; a cikin sunan Yahweh na datse su. 13 Sun kawo mani hari saboda su mãke ni ƙasa, amma Yahweh ya taimake ni. 14 Yahweh ne ƙarfina da farincikina, shi ne kuma ya ceto ni. 15 Sowar farinciki ta nasara aka ji a cikin rumfunan adalai; hannun dama na Yahweh ya ci nasara. 16 Hannun dama na Yahweh ya ɗaukaka; hannun dama na Yahweh yaci nasara. 17 Ba zan mutu ba, amma zan rayu kuma inyi shelar ayyukan Yahweh. 18 Yahweh ya horar da ni da zafi; amma bai miƙa ni ga mutuwa ba. 19 Ka buɗe mani ƙofofin adalci; zan shige su kuma zan bada godiya ga Yahweh. 20 Wannan ce ƙofar Yahweh; adali yana bi ta ciki. 21 Zan bada godiya a gare ka, domin ka amsa mani, kuma ka zama cetona. 22 Dutsen da magina suka watsar ya zama dutsen kusurwa. 23 Wannan yin Yahweh ne; mai ban mamaki ne a idanunmu. 24 Wannan ce ranar da Yahweh ya yi aiki; za muyi farinciki da murna a cikin ta. 25 Ina roƙon ka, Yahweh, ka bamu nasara! Ina roƙon ka, Yahweh, ka bamu ci gaba! 26 Mai albarka ne wanda ya zo cikin sunan Yahweh; mun albarkace ka daga gidan Yahweh. 27 Yahweh Allahn ne, ya kuma bamu haske; ku ɗaure hadaya da igiyoyi a ƙahonnin bagadi. 28 Kai Allahna ne, kuma zan bada godiya a gare ka; kai Allahna ne; zan ɗaukaka ka. 29 Oh, ku bada gadiya ga Yahweh; domin shi nagari ne; domin alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.
1 Blessed are those whose ways are blameless,
who walk in the law of Yahweh.
2 Blessed are they who keep his solemn commands,
who seek him with all their heart.
3 They do no wrong;
they walk in his ways.
4 You have commanded us to keep your instructions
so that we should carefully observe them.
5 Oh, that I would be firmly established
in the observance of your statutes!
6 Then I would not be put to shame
when I think of all your commandments.
7 I will give thanks to you with an upright heart
when I learn your righteous decrees.
8 I will observe your statutes;
do not leave me alone.
9 How can a young person keep his path pure?
By obeying your word.
10 With my whole heart I seek you;
Do not let me stray from your commandments.
11 I have stored up your word in my heart
so that I might not sin against you.
12 Blessed you are, Yahweh;
teach me your statutes.
13 With my mouth I have declared
all the righteous decrees that you have revealed.
14 I rejoice in the way of your covenant decrees
more than in all riches.
15 I will meditate on your instructions
and pay attention to your ways.
16 I delight in your statutes;
I will not forget your word.
17 Be kind to your servant so that I may live
and keep your word.
18 Open my eyes so that I may see
marvelous things in your law.
19 I am a foreigner in the land;
do not hide your commandments from me.
20 My desires are crushed by the longing to know
your righteous decrees at all times.
21 You rebuke the proud, who are cursed,
who wander from your commandments.
22 Spare me from disgrace and contempt,
for I have obeyed your solemn commands.
23 Though rulers plot and slander me,
your servant meditates on your statutes.
24 Your solemn commands are my delight,
and they are my counselors.
25 My life clings to the dust!
Give me life by your word.
26 I told you my ways, and you answered me;
teach me your statutes.
27 Make me understand the ways of your instructions,
so that I can meditate on your wondrous teachings.
28 I am overwhelmed with grief!
Strengthen me by your word.
29 Turn from me the path of deceit;
graciously teach me your law.
30 I have chosen the way of faithfulness;
I have always kept your righteous decrees before me.
31 I cling to your covenant decrees;
Yahweh, do not let me be shamed.
32 I will run in the path of your commandments,
for you enlarge my heart to do so.
33 Teach me, Yahweh, the way of your statutes,
and I will keep them to the end.
34 Give me understanding, and I will keep your law;
I will observe it with all my heart.
35 Guide me in the path of your commandments,
for I delight to walk in it.
36 Direct my heart toward your covenant decrees
and away from unrighteous gain.
37 Turn my eyes from looking at worthless things;
revive me in your ways.
38 Carry out for your servant the word
that you gave to those who revere you.
39 Take away the disgrace I dread,
for your judgments are good.
40 See, I have longed for your instructions;
revive me in your righteousness.
41 Yahweh, give me your unfailing love—
your salvation, according to your word;
42 then I will have a reply for the one who mocks me,
for I trust in your word.
43 Do not take the word of truth from my mouth,
for my hope is in your righteous decrees.
44 I will observe your law continually,
forever and ever.
45 I will walk securely,
for I seek your instructions.
46 I will speak of your solemn commands before kings
and will not be ashamed.
47 I delight in your commandments,
which I love dearly.
48 I will lift up my hands to your commandments, which I love;
I will meditate on your statutes.
49 Call to mind your word to your servant
because you have given me hope.
50 This is my comfort in my affliction:
that your word has kept me alive.
51 The proud have scoffed at me,
yet I have not turned away from your law.
52 I have thought about your righteous decrees from ancient times, Yahweh,
and I comfort myself.
53 Hot anger has taken hold of me
because of the wicked who reject your law.
54 Your statutes have been my songs
in the house of my sojourn.
55 I think about your name during the night, Yahweh,
and I keep your law.
56 This has been my practice
because I have observed your instructions.
57 Yahweh is my portion;
I have determined to observe your words.
58 I earnestly request your favor with my whole heart;
be merciful to me according to your word.
59 I examined my ways
and turned my feet to your solemn commands.
60 I hurry and do not delay
to keep your commandments.
61 The cords of the wicked have ensnared me;
I have not forgotten your law.
62 At midnight I rise to give thanks to you
because of your righteous decrees.
63 I am a companion of all who honor you,
to all who observe your instructions.
64 The earth, Yahweh, is full of your covenant faithfulness;
teach me your statutes.
65 You have done good to your servant,
Yahweh, by means of your word.
66 Teach me proper discernment and understanding,
for I have believed in your commandments.
67 Before I was afflicted I went astray,
but now I observe your word.
68 You are good, and you are one who does good;
teach me your statutes.
69 The arrogant have smeared me with lies,
but I keep your instructions with my whole heart.
70 Their hearts are hardened,
but I delight in your law.
71 It is good for me that I have suffered
so that I would learn your statutes.
72 Instruction from your mouth is more precious to me
than thousands of pieces of gold and silver.
73 Your hands have made and fashioned me;
give me understanding so that I may learn your commandments.
74 Those who honor you will be glad when they see me
because I find hope in your word.
75 I know, Yahweh, that your decrees are just,
and that in faithfulness you afflicted me.
76 Let your covenant faithfulness comfort me,
according to your word to your servant.
77 Show me compassion so that I may live,
for your law is my delight.
78 Let the proud be put to shame,
for they have slandered me;
but I will meditate on your instructions.
79 May those who honor you turn to me,
those who know your solemn commands.
80 May my heart be blameless with respect to your statutes
so that I may not be put to shame.
81 I faint with longing that you might rescue me!
I hope in your word.
82 My eyes long for your word;
when will you comfort me?
83 For I have become like a wineskin in the smoke;
I do not forget your statutes.
84 How long must your servant endure this;
when will you judge those who persecute me?
85 The proud have dug pits for me,
defying your law.
86 All your commandments are reliable;
those people persecute me wrongfully; help me.
87 They have almost made an end to me on earth,
but I do not reject your instructions.
88 By your steadfast love, keep me alive,
so that I may obey the solemn commands that come from your mouth.
89 Yahweh, your word stands forever;
your word is established firmly in heaven.
90 Your faithfulness lasts for all generations;
you have established the earth, and it remains.
91 All things continue to this day, just as you said in your righteous decrees,
for all things are your servants.
92 If your law had not been my delight,
I would have perished in my affliction.
93 I will never forget your instructions,
for through them you have kept me alive.
94 I am yours; save me,
for I seek your instructions.
95 The wicked prepare to destroy me,
but I will seek to understand your solemn commands.
96 All perfection I have seen has an end;
but your command is exceedingly broad.
97 Oh how I love your law!
It is my meditation all day long.
98 Your commandments make me wiser than my enemies,
for your commandments are always with me.
99 I have more understanding than all my teachers,
for I meditate on your covenant decrees.
100 I understand more than those older than I am;
this is because I have kept your instructions.
101 I have kept my feet back from every evil path
so that I might observe your word.
102 I have not turned aside from your righteous decrees,
for you have instructed me.
103 How sweet are your words to my taste,
yes, sweeter than honey to my mouth!
104 Through your instructions I gain discernment;
therefore I hate every false way.
105 Your word is a lamp to my feet
and a light for my path.
106 I have sworn and have confirmed it,
that I will observe your righteous decrees.
107 I am very afflicted;
keep me alive, Yahweh, as you have promised in your word.
108 Yahweh, please accept the freewill offerings of my mouth,
and teach me your righteous decrees.
109 My life is always in my hand,
yet I do not forget your law.
110 The wicked have set a snare for me,
but I have not strayed from your instructions.
111 I claim your covenant decrees as my heritage forever,
for they are the joy of my heart.
112 My heart is set on obeying your statutes
forever to the very end.
113 I hate those who have a double mind,
but I love your law.
114 You are my hiding place and my shield;
I hope in your word.
115 Get away from me, you evildoers,
so that I may observe the commandments of my God.
116 Sustain me by your word so that I may live
and not be ashamed of my hope.
117 Support me, and I will be safe;
I will always meditate on your statutes.
118 You reject all those who stray from your statutes,
for their deceit is vain.
119 You remove all the wicked of the earth like slag;
therefore I love your solemn commands.
120 My body trembles in fear of you,
and I am afraid of your righteous decrees.
121 I do what is just and right;
do not abandon me to my oppressors.
122 Guarantee the welfare of your servant;
do not let the proud oppress me.
123 My eyes grow tired as I wait for your salvation
and for your righteous word.
124 Show your servant your covenant faithfulness,
and teach me your statutes.
125 I am your servant; give me understanding
so that I may know your solemn commands.
126 It is time for Yahweh to act,
for people have broken your law.
127 Truly I love your commandments
more than gold, more than fine gold.
128 Therefore I carefully follow all your instructions,
and I hate every path of falsehood.
129 Your rules are wonderful,
that is why I obey them.
130 The unfolding of your words gives light;
it gives understanding to the untrained.
131 I open my mouth and pant,
for I long for your commandments.
132 Turn to me and have mercy on me,
as you always do for those who love your name.
133 Direct my footsteps by your word;
do not let any wickedness rule me.
134 Redeem me from human oppression
so that I may observe your instructions.
135 Let your face shine on your servant,
and teach me your statutes.
136 Streams of tears run down from my eyes
because people do not observe your law.
137 You are righteous, Yahweh,
and your decrees are fair.
138 You have given your solemn commands righteously
and faithfully.
139 Zeal has destroyed me
because my adversaries forget your words.
140 Your word has been tested very much,
and your servant loves it.
141 I am insignificant and despised,
yet I do not forget your instructions.
142 Your justice is forever justice,
and your law is trustworthy.
143 Though distress and anguish have found me,
your commandments are still my delight.
144 Your covenant decrees are righteous forever;
give me understanding that I may live.
145 I cried out with my whole heart, "Answer me, Yahweh,
I will keep your statutes.
146 I call to you; save me,
and I will observe your solemn commands."
147 I rise before the dawn of the morning and cry for help.
I hope in your words.
148 My eyes are open before the night watches change
so that I might meditate on your word.
149 Hear my voice in your covenant faithfulness;
keep me alive, Yahweh, as you have promised in your righteous decrees.
150 Those who are persecuting me are coming closer to me,
but they are far from your law.
151 You are near, Yahweh,
and all your commandments are trustworthy.
152 Long ago I learned from your solemn commands
that you had set them in place forever.
153 Look on my affliction and help me,
for I do not forget your law.
154 Plead my cause and redeem me;
keep me alive according to your word.
155 Salvation is far from the wicked,
for they do not love your statutes.
156 Great are your merciful actions, Yahweh;
keep me alive, as you always do.
157 My persecutors and my foes are many,
yet I have not turned from your covenant decrees.
158 I view the treacherous with disgust
because they do not keep your word.
159 See how I love your instructions;
keep me alive, Yahweh, as you have promised by your covenant faithfulness.
160 The essence of your word is truth;
every one of your righteous decrees lasts forever.
161 Princes persecute me without cause,
but my heart stands in awe of your word.
162 I rejoice at your word
like one who finds great plunder.
163 I hate and abhor falsehood,
but I love your law.
164 Seven times a day I praise you
because of your righteous decrees.
165 Great peace they have, those who love your law;
nothing makes them stumble.
166 I hope for your salvation, Yahweh,
and I obey your commandments.
167 I observe your solemn commands,
and I love them greatly.
168 I keep your instructions and your solemn commands,
for you are aware of everything I do.
169 Listen to my cry for help, Yahweh;
give me understanding into your word.
170 May my plea come before you;
help me according to your word.
171 May my lips pour out praise,
for you teach me your statutes.
172 Let my tongue sing about your word,
for all your commandments are right.
173 May your hand help me,
for I have chosen your instructions.
174 I long for your rescue, Yahweh,
and your law is my delight.
175 May I live and praise you,
and may your righteous decrees help me.
176 I have wandered off like a lost sheep;
seek your servant,
for I have not forgotten your commandments.
1 Masu albarka ne waɗanda hanyoyinsu basu da laifi, waɗanda ke tafiya cikin shari'ar Yahweh. 2 Masu albarka ne waɗanda suka kiyaye umarnansa masu tsarki masu neman sa da dukkan zuciyarsu. 3 Sun yi abin da ke dai-dai; suna tafiya cikin hanyoyinsa. 4 Ka umarce mu mu kiyaye dokokinka, domin muyi lura mu kiyaye su, 5 Kash, ina ma zan ɗore a cikin lura da farillanka! 6 To da ba za a kunyata ni ba a lokacin da nayi tunanin dukkan dokokinka. 7 Zan yi maka godiya da zuciya mai tsarki a lokacin dana koyi sharuɗɗanka. 8 Zan kiyaye farillanka; kar ka barni ni kaɗai.
9 Yaya matashi zai tsare tafarkinsa da tsabta? Ta wurin kiyaye maganarka. 10 Da dukkan zuciyata na neme ka; Kar ka barni in kauce wa umarnanka. 11 Na adana maganarka a cikin zuciyata domin kada in yi maka zunubi. 12 Yahweh kai mai albarka ne, ka koya mani farillanka. 13 Da bakina na furta dukkan ayyukanka na jinƙai da ka bayyana mani. 14 Ina murna da umarnanka fiye da dukkan wadata. 15 Zan yi ta nazarin dokokinka in kuma saurari sharuɗɗanka. 16 Ina jin daɗin farillanka; ba kuma zan manta da maganarka ba.
17 Yiwa bawanka kirki domin in rayu in kiyaye maganarka. 18 Buɗe idanuna domin in ga ayyukan al'ajibi a cikin shari'arka. 19 Ni bãƙo ne a cikin ƙasar; kada ka ɓoye umarnanka daga gare ni. 20 An rushe marmarina ta wurin jimirin sanin umarnanka masu adalci a kowanne lokaci. 21 Ka tsauta wa masu fahariya, waɗanda aka la'anta, Waɗanda suka bauɗe wa dokokinka. 22 Kãre ni daga wulaƙanci da cin mutunci, domin na kiyaye sharuɗɗan alƙawarinka. 23 Koda ya ke shugabanni sun ƙudurta suka yi mani maƙarƙashiya, ni bawanka ina binbinin farillanka. 24 Alƙawaran farillanka sune nake jin daɗi, sune kuma ke yi mini jagora.
25 Raina yana birgima a ƙura! Ka bani rai ta wurin maganarka. 26 Na faɗa maka hanyoyina, ka kuma amsa mani; ka koya mani farillanka. 27 Ka sani in fahimci tafarkin umarninka, domin in yi ta nazarin koyarwarka mai al'ajibi. 28 Baƙinciki ya cika ni! Ka ƙarfafa ni ta wurin maganarka. 29 Ka jutar daga gare ni hanyar yaudara; ta wurin alheri ka koya mani shari'arka. 30 Na zaɓi hanyar aminci; Har kullum na kiyaye farillanka masu adalci daka sa a gabana. 31 Na manne wa umarnin alƙawarinka; Yahweh kada ka bar ni in ji kunya. 32 Zan bi hanyoyin dokokinka da gudu, gama ka faɗaɗa zuciyata tayi haka.
33 Ka koya mani, Yahweh, hanyar umarnanka, kuma zan kiyaye su har ga ƙarshe. 34 Ka bani ganewa, kuma zan kiyaye shari'arka; Zan lura da ita da dukkan zuciyata. 35 Ka bishe ni ta tafarkin dokokinka, gama ina fahariya in yi tafiya cikinta. 36 Ka jagoranci zuciyata ga alƙawarin umarnanka da kaucewa daga ƙazamar riba. 37 Ka juya idanuwana daga duban wofintattun abubuwa; ka rayar da ni cikin hanyoyinka. 38 Ka cika wa bawanka alƙawarin da kayi ga waɗanda ke girmama ka. 39 Ka ɗauke zage-zagen da nake tsoro, gama hukuncin adalcinka na da kyau. 40 Duba, na jira umarnanka; ka farkar dani cikin sanin gaskiyarka.
41 Yahweh, ka ba ni madawwamiyar ƙaunarka- cetonka bisa ga alƙawarinka; 42 sa'an nan zan sami amsa domin duk mai yi mani ba'a, gama na amince da maganarka. 43 Kada ka ɗauke maganar gaskiya daga bakina, gama Na yi jira domin umarnan sanin gaskiyarka. 44 Zan kiyaye dokarka babu fasawa, har abada abadin. 45 Zan yi tafiya cikin kwanciyar hankali, gama ina neman ka'idodinka. 46 Zan yi magana a kan hakikanin umarninka a gaban sarakuna kuma ba zan ji kunya ba. 47 Ina murna da dokokinka, waɗanda nake ƙauna sosai. 48 Zan ɗaga hannuwana ga dokokinka, waɗanda nake ƙauna; Zan yi nazari a kan farillanka.
49 Ka tuna da alƙawarinka zuwa ga bawanka domin ka ba ni bege. 50 Wannan itace ta'aziyata a cikin ƙuncina: cewa alƙawarinka ya kiyaye ni da rai. 51 Mai girman kai ya yi mani gwalo, duk da haka ban juya daga dokarka ba. 52 Nayi tunanin umarnanka masu adalci dake tun zamanun dã, Yahweh, kuma sai na yi wa kaina ta'aziya. 53 Fushi mai ƙuna ya riƙe ni sabili da mugu da ya ƙi dokarka. 54 Farillannka sun zama waƙoƙina a cikin gidan da nake zama na ɗan lokaci. 55 Na yi tunanin sunanka a cikin dare, Yahweh, na kuma riƙe dokarka. 56 Wannan ya zama abin da na ke yi domin na kula da umarnanka.
57 Yahweh ne rabona; nayi ƙudirin kula da maganganunka. 58 Nayi matuƙar neman tagomashinka da dukkan zuciyata; ka yi mani jinƙai, kamar yadda maganarka tayi alƙawari. 59 Nayi la'akari da tafarkina na kuma juyar da ƙafafuna zuwa ga umarnan alƙawarinka. 60 Nayi sauri ban kuma ɓata lokaci ba domin in kiyaye dokokin ka. 61 Igiyoyin mai mugunta suka nannaɗe ni; Ban manta da shari'arka ba. 62 Cikin dare na tashi domin inyi maka godiya sabili da dokokinka masu adalci. 63 Ni abokin dukkan waɗanda ke girmamaka ne, da dukkan waɗanda ke kula da umarnanka. 64 ƙasar, Yahweh, tana cike da amintaccen alƙawarinka; ka koya mani farillanka.
65 Kayi abin alheri ga bawanka, Yahweh, ta wurin maganarka. 66 Ka koya mani sasancewa da fahimta, gama na gaskata da dokokinka.' 67 Kamin a wahalshe ni sai da na bijire, amma yanzu ina kula da maganarka. 68 Kana da kyau, kuma kai ne mai aikata abu mai kyau; ka koya mani farillanka. 69 Mai girman kai ya rufe ni da ƙarairayi, amma na adana umarninka da dukkan zuciyata. 70 Zuciyarsu ta taurare, amma ina fahariya da shari'arka. 71 Ya dace dani dana sha wahala domin in koyi farillanka. 72 Umarni daga bakinka ya fiye mani daraja fiye da dubban zinariya da azurfa.
73 Hannayenka sunyi ni ka ƙera ni; ka ba ni fahimta domin in koyi dokokinka. 74 Waɗanda suke yi maka biyayya za suyi murna idan suka ganni saboda na sami bege cikin maganarka. 75 Yahweh, Na sani, dokokinka masu adalci ne, cikin amincinka kuma ka hukunta ni. 76 Bari alƙawarin amincinka ya ta'azantar dani, kamar yadda ka alƙawarta wa bawanka. 77 Ka nuna mani jinƙai domin in rayu, gama shari'arka ita ce jin daɗina. 78 Bari masu girmankai su sha kunya, gama sun ɓata sunana; amma zan yi nazarin umarnanka. 79 Bari masu darjanta ka su juyo gare ni, su da suka san alƙawaran dokokinka. 80 Bari zuciyata ta zama da rashin laifi da darjanta farillanka domin kada in sha kunya.
81 Na suma domin sauraron cetonka! Na sa zuciya cikin maganarka. 82 Idanuna na jiran ganin alƙawarinka; yaushe za ka ta'azantar dani? 83 Gama na zama kamar salka cikin hayaƙi; Ban manta da farillanka ba. 84 Har yaushe bawanka zai jiure da wannan; yaushe zaka hukunta waɗanda suke tsananta mani? 85 Masu girmankai sun haƙa ramuka domina, suna rena shari'arka. 86 Dukkan dokokinka abin dogaro ne; waɗannan mutanen suna tsananta mani cikin kuskure; ka taimake ni. 87 Saura kaɗan su kawo ƙarshena a duniya, amma ban ƙi umarnanka ba. 88 Ta wurin tsayayyar ƙaunarka, ka kiyaye ni a raye, domin inyi biyayya da umarnanka.
89 Yahweh, maganarka ta tsaya har abada; maganarka ta kahu da ƙarfi a cikin sama. 90 Amincinka ya dawwama ga dukkan tsararraki; ka kafa duniya, ta kuwa tsaya. 91 Dukkan abubuwa sun ci gaba har yau, kamar yadda ka faɗi cikin amintattun umarnanka, gama dukkan abubuwa bayinka ne. 92 Da shari'arka ba jin daɗina ba ce, da na hallaka a cikin ƙuncina. 93 Ba zan taɓa mantawa da umarnanka ba, gama ta wurinsu ka kiyaye ni da rai. 94 Ni naka ne; ka cece ni, gama na nemi umarnanka. 95 Masu mugunta sunyi shirin hallakar dani, amma zan nemi in san alƙawarin umarnanka. 96 Naga cewa dukkan abu yana da iyakarsa, amma dokokinka suna da fãɗi, basu da iyaka.
97 Oh ina ƙaunar shari'arka! ita ce abin bin-binina dukkan yini. 98 Dokokinka sun sani na zama da hikima fiye da maƙiyana, gama dokokinka kullum suna tare dani. 99 Ina da sani fiye da dukkan malamaina, gama ina tunani akan alƙawaran umarnanka. 100 Ina da sani fiye da waɗanda suka girmeni; wannan ya faru domin na kiyaye umarnanka. 101 Na kiyaye sawayena daga hanyar mugaye saboda in lura da maganarka. 102 Ban juya daga dokokin adalcinka ba, saboda kai ne ka bani umarni. 103 Ya ya zaƙin maganarka ga ɗanɗanona, I, tafi zuma zaƙi a bakina! 104 Ta wurin umarninka na ƙaru da basira; saboda haka ina ƙin kowacce hanyar ƙarya.
105 Maganarka fitila ce ga sawayena, haske ne kuma ga hanyata. 106 Na rantse na kuma tabbatar da ita, saboda haka zan kula da adalcin dokokinka. 107 Ina shan azaba; ka bar ni a raye, Yahweh, kamar yadda ka alƙawarta a cikin maganarka. 108 Yahweh, idan ka yarda karɓi shaidar godiyar bakina, ka koya mani adalcin dokokinka. 109 Raina kullum yana hannuna, duk da haka ban manta da shari'arka ba. 110 Mugaye sun ɗana tarko domina, amma ban ratse daga umarninka ba. 111 Na nemi alƙawaran dokokinka a matsayin gãdona har abada, gama su ne murnar zuciyata. 112 Zuciyata a shirye take don biyayya da farillanka har abada, har kuma zuwa ƙarshe.
113 Ina ƙin waɗanda ba sa son yi maka biyayya, amma ina ƙaunar shari'arka. 114 Kai ne kake tsare ni da garkuwarka; ina jiran maganarka. 115 Ku tafi daga gare ni, ku masu aikata mugunta, domin in kiyaye dokokin Allahna. 116 Ka ƙarfafa ni ta wurin maganarka saboda in rayu ba domin inji kunyar sa begena ba. 117 Ka ƙarfafa ni, zan kuma tsira. Zan yi ta nazari a kan umarninka. 118 Ka ƙi dukkan waɗanda suka ratse daga umarninka, domin waɗancan mutanen masu yaudara ne kuma ba abin dogara ba ne. 119 Ka cire dukkan mugayen duniya kamar dattin maƙera; saboda haka ina ƙaunar mahimman umarninka. 120 Na cika da tsoronka, kuma ina jin tsoron adalcin ka'idodinka.
121 Na yi abin da ke na gaskiya da adalci, kada ka bashe ni a wurin masu yi mani tsanani. 122 Ka tsare lafiyar bawanka, kada ka bari masu girman kai su wahallar da shi. 123 Idanuna sun gaji sa'ad da nake jiran cetonka da maganarka mai adalci. 124 Ka nuna wa bawanka amincin alƙawarinka, ka koya mani farillanka. 125 Ni bawanka ne, ka bani fahimta domin in sa alƙawarin farillanka. 126 Lokaci ya yi da Yahweh zai yi aiki, domin mutane sun karya shari'arka. 127 Gaskiya ne ina ƙaunar dokokinka fiye da zinariya, fiye da zinariya mai kyau. 128 Saboda haka na bi umarninka a hankali, na tsani kowacce hanya ta ƙarya.
129 Ka'idojinka suna da ban mamaki, shi yasa nake yin biyayya dasu. 130 Buɗewar maganarka tana bada haske, tana bada ganewa ga wanda ba koyayye ba. 131 Na buɗe bakina ina haki, saboda na ƙagara domin maganarka. 132 Ka juyo wajena ka yi mani jinƙai kamar yadda ka ke yiwa waɗanda ke ƙaunar sunanka. 133 Ka bida ƙafafuna da maganarka, kada ka bari wani zunubi yayi mulki a kaina. 134 Ka fanshe ni daga hannun masu zalunci domin in lura da umarninka. 135 Bari fuskarka ta haskaka a kan bawanka, ka koya mani farillanka. 136 Ƙoramun ruwaye suna gudu daga idanuna saboda mutane ba sa lura da shari'arka ba.
137 Mai adalci ne kai, Yahweh, dokokinka kuma dai-dai suke. 138 Ka bada dokokinka na alƙawari masu adalci kuma amintattu. 139 Fushi ya hallaka ni saboda maƙiyana sun manta da maganganunka. 140 An jaraba maganarka sau da yawa, bawanka kuma yana ƙaunar su. 141 Ni ba komai bane an kuma rena ni, duk da haka ban manta da umarninka ba. 142 Adalcinka dai-dai ya ke har abada, shari'arka madogara ce. 143 Koda ya ke wahala da azaba sun afko mani, duk da haka dokokinka suna faranta mani rai. 144 dokokinka na alƙawari masu adalci ne har abada.; ka bani fahimta domin in rayu.
145 Nayi kuka da dukkan zuciyata, "Ka amsa mani, Yahweh, zan yi biyayya da farillanka. 146 Na kira ka; ka cece ni, zan kuwa aikata dokokinka na alƙawari. 147 Da asussuba nake tashi in yi kukan neman taimako. Na sa begena a cikin maganarka. 148 Na kan farka kafin masu gadin dare suyi sauyi domin in yi bin-binin maganarka. 149 Ka saurari muryata a cikin alƙawarin amincinka; ka barni da rai, Yahweh, kamar yadda ka alƙawarta a cikin dokokinka na adalci. 150 Su waɗanda suke tsananta mani suna matsowa kusa dani, amma suna nesa da shari'arka. 151 Kana kusa, Yahweh, kuma duk umarnanka amintattu ne. 152 Tun dã can na koya daga dokokin alƙawaranka cewa ka tsaida su har abada.
153 Ka dubi ƙunci na kayi mani taimako, gama ban manta da shari'arka ba. 154 Ka tsaya mani ka kuma fanshe ni; ka riƙe ni, kamar yadda ka alƙawarta a maganarka. 155 Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa ƙaunar farillanka. 156 Ayyukanka na jinƙai masu girma ne, Yahweh; ka kiyaye ni da rai, kamar yadda ka saba yi. 157 Masu zaluntata da maƙiyana suna da yawa, duk da haka ban bar bin dokokinka na alƙawari ba. 158 Ina duban maciya amana a ƙyamace domin ba sa biyayya da maganarka. 159 Dubi yadda nake ƙaunar umarninka; ka kiyaye ni da rai, Yahweh, kamar yadda ka alƙawarta ta wurin alƙawarinka mai aminci. 160 Cibiyar maganarka ita ce gaskiya; kowanne ɗaya daga cikin dokokinka na adalci ne sun tabbata har abada.
161 Sarakuna suna tsananta mani ba dalili; zuciya ta ta karai, gama ina jin tsoron karya maganarka. 162 Ina farinciki da maganarka kamar wanda ya sami ɗumbin ganima. 163 Ina ƙin ƙarairayi ina kuma wofintar dasu, amma ina ƙaunar shari'arka. 164 Ina yabon ka sau bakwai a rana sabili da dokokinka na adalci. 165 Masu ƙaunar shari'arka, suna da babbar salama; ba abin da zai sasu suyi tuntuɓe. 166 Ina jiran cetonka, Yahweh, ina kuma biyayya da dokokinka. 167 Ina aikata dokokinka tabbatattu, ina kuma ƙaunarsu ƙwarai. 168 Ina biyayya da umarninka da kuma dokokinka tabbatattu, gama kana sane da duk abin da nake yi.
169 Ka saurari kukana na neman taimako, Yahweh; ka bani fahimtar maganarka. 170 Bari roƙona ya zo gaba gare ka; ka taimake ni, kamar yadda ka alƙawarta a maganarka. 171 Bari leɓunana su cika da yabo, gama kana koya mani farillanka. 172 Bari harshena yayi waƙa akan maganarka, gama dukkan dokokinka dai-dai suke. 173 Bari hannunka ya taimake ni, gama na zaɓi umarnanka. 174 Ina marmarin cetonka, Yahweh, shari'arka ce farincikina. 175 Ka rayar dani don in yabe ka, bari dokokinka na adalci su taimake ni. 176 Nayi makuwa kamar ɓatacciyar tunkiya; ka nemi bawanka, gama ban manta da dokokinka ba.
1 In my distress I called out to Yahweh,
and he answered me.
2 Rescue my life, Yahweh,
from those who lie with their lips
and deceive with their tongues.
3 How will he punish you,
and what more will he do to you,
you who have a lying tongue?
4 He will punish you with the arrows of a warrior
sharpened over burning coals of the broom tree.
5 Woe is me because I temporarily live in Meshech;
I lived previously among the tents of Kedar.
6 For too long I have lived
with those who hate peace.
7 I am for peace,
but when I speak, they are for war.
1 A cikin ƙuncina nayi kira ga Yahweh, ya kuma amsa mani. 2 Ka ƙwato raina, Yahweh, daga waɗanda ke ƙarya da leɓunansu da ruɗi da harsunansu. 3 Ta yaya zai hore ka, mene ne kuma zai ƙara yi maka, kai wanda ke da harshe na ƙarya? 4 Zai hore ka da kibiyoyin mayaƙi da aka wãsa bisa garwashin wutar ƙiraren itace. 5 Kaito na saboda ina zaune jim kaɗan cikin Meshek; Dã na zauna a rumfunan Keda. 6 Har dogon lokaci na zauna tare da waɗanda suka ƙi salama. 7 Ni domin salama nake, amma idan na yi magana, domin yaƙi suke.
1 I will lift up my eyes to the mountains.
From where will my help come?
2 My help comes from Yahweh,
who made heaven and earth.
3 He will not allow your foot to slip;
he who protects you will not slumber.
4 See, the guardian of Israel
never slumbers or sleeps.
5 Yahweh is your guardian;
Yahweh is the shade at your right hand.
6 The sun will not harm you by day,
nor the moon by night.
7 Yahweh will protect you from all harm,
and he will protect your life.
8 Yahweh will protect you in all you do
now and forevermore.
1 Zan ɗaga idanu na ga duwatsu. Daga ina taimakona zai zo? 2 Taimakona na zuwa daga Yahweh, wanda yayi sama da duniya. 3 Ba zai bar sawunka ya zãme ba; shi wanda ya ke kiyaye ka ba zai yi gyangyaɗi ba. 4 Duba, mai lura da Isra'ila ba zai taɓa gyangyaɗi ba ko barci. 5 Yahweh shi ne mai lura da kai; Yahweh shi ne inuwa a hannun damanka. 6 Rana ba zata cutar da kai ba da rana, ko kuma wata da daddare. 7 Yahweh zai kiyaye ka daga dukkan cutarwa, kuma zai kiyaye ranka. 8 Yahweh zai kiyaye ka cikin dukkan abin da kake yi yanzu da har abada abadin.
1 I was glad when they said to me,
"Let us go to the house of Yahweh."
2 Jerusalem, our feet are standing
within your gates!
3 Jerusalem, built
as a city carefully planned!
4 The tribes go up to Jerusalem—the tribes of Yah— [1]
as a testimony for Israel,
to give thanks to the name of Yahweh.
5 There thrones of judgment were set,
thrones of the house of David.
6 Pray for the peace of Jerusalem!
"May those who love you be at ease.
7 May there be peace within the walls that defend you,
and may they have peace within your fortresses."
8 For the sake of my brothers and my friends
I will say, "May there be peace within you."
9 For the sake of the house of Yahweh our God,
I will seek good for you.
1 Nayi farinciki da suka ce mani, "Bari mu tafi gidan Yahweh." 2 Yerusalem, sawayenmu na tsaye cikin ƙofofinki! 3 Yerusalem, an gina ki birnin da aka yiwa shiri a hankali! 4 Kabilun suna tafiya Yerusalem - kabilun Yahweh - a matsayin shaida ga Isra'ila, su bada godiya ga sunan Yahweh. 5 An kafa kursiyoyin hukuncinsu, kursiyoyin gidan Dauda. 6 Kuyi addu'a domin salamar Yerusalem! "Bari masu ƙaunar ki su sami salama. 7 Bari salama ta kasance cikin katangogin dake kãre ki, bari kuma su sami salama cikin ƙarfafan wurin tsaronki." 8 Domin albarkacin 'yan'uwana da abokaina zan ce, "Bari salama ta kasance a cikin ki." 9 Domin albarkacin gidan Yahweh Allahnmu, zan biɗi alheri game dake.
1 To you I lift up my eyes,
you who are enthroned in the heavens.
2 See, as the eyes of servants look to their master's hand,
as the eyes of a servant girl look to the hand of her mistress,
so our eyes look to Yahweh our God
until he has mercy on us.
3 Have mercy on us, Yahweh, have mercy on us,
for we are filled with humiliation.
4 We are more than full
of the scoffing of the insolent
and with the contempt of the proud.
1 A gare ka na ɗaga idanuna, kai wanda kake bisa kursiyi a sammai. 2 Duba, kamar yadda idanun bãyi ke duban hannun ubangijinsu, kamar yadda idanun baiwa ke duban hannun uwargijiyarta, haka idanunmu ke duban Yahweh Allahnmu har sai ya nuna mana jinƙai. 3 Kayi mana jinƙai, Yahweh, kayi mana jinƙai, domin cike muke da wulaƙanci. 4 Mun ma fi cike da ba'ar masu ba'a da kuma renin masu fahariya.
1 "If Yahweh had not been on our side,"
let Israel say now,
2 "if it had not been Yahweh who was on our side
when men rose up against us,
3 then they would have swallowed us up alive
when their anger raged against us.
4 The water would have swept us away;
the torrent would have overwhelmed us.
5 Then the raging waters would have drowned us."
6 Blessed be Yahweh,
who has not allowed us to be torn by their teeth.
7 We have escaped like a bird
out of the snare of the fowlers;
the snare has been broken,
and we have escaped.
8 Our help is in the name of Yahweh,
who made heaven and earth.
1 "Idan da ba don Yahweh yana gefenmu ba," bari Isra'ila suce yanzu, 2 "Idan da ba don Yahweh yana gefenmu ba sa'ad da mutane suka taso gãba da mu, 3 daga nan da sun haɗiye mu ɗungum da rai sa'ad da fushin su ya wo hauka gãba da mu. 4 Da ruwa ya share mu; igiyoyin da sun sha ƙarfinmu. 5 Daga nan haukan ruwayen da ya shanye mu." 6 Albarka ta tabbata ga Yahweh, wanda bai bari haƙoran sa suka yayyage mu ba. 7 Mun kucce kamar tsuntsu daga tarkon mafarauta; tarkon ya karye, mun kuma kucce. 8 Taimakonmu yana cikin Yahweh, wanda ya yi sama da ƙasa.
1 Those who trust in Yahweh
are like Mount Zion, unshakable, forever enduring.
2 As the mountains surround Jerusalem,
so Yahweh surrounds his people
now and forever.
3 The scepter of wickedness must not rule
in the assigned portion of the righteous.
Otherwise the righteous might do what is wrong.
4 Do good, Yahweh, to those who are good
and to those who are upright in their hearts.
5 But as for those who turn aside to their crooked ways,
Yahweh will lead them away with the those who behave wickedly.
May peace be on Israel.
1 Waɗanda suka sa dogararsu ga Yahweh suna kama da Tsaunin Sihiyona, marar jijjiguwa, mai dawwama har abada. 2 Kamar yadda duwatsu suka kewaye Yerusalem, haka Yahweh ya kewaye mutanensa yanzu da har abada. 3 Sandar mulkin mugunta ba za tayi mulki ba a ƙasar mai adalci. Idan ba haka ba mai adalci zai iya yin abin da ba dai-dai ba. 4 Kayi da kyau, Yahweh, ga waɗanda suke yi da kyau waɗanda kuma suke masu adalci a zukatansu. 5 Amma ga waɗanda suka kauce gefe ga karkatattun hanyoyinsu, Yahweh zai kawar dasu tare da masu aikata mugunta. Bari salama ta kasance a Isra'ila.
1 When Yahweh reversed the captivity of Zion,
we were like those who dream.
2 Then our mouths were filled with laughter
and our tongues with joyful shouting.
Then they said among the nations,
"Yahweh has done great things for them."
3 Yahweh did great things for us;
how glad we were!
4 Reverse our captivity, Yahweh,
like the streams in the Negev.
5 Those who sow in tears
will reap with shouts of joy.
6 He who goes out weeping,
carrying seed for sowing,
will return again with shouts of joy,
bringing his bundles of grain with him.
1 Sa'ad da Yahweh ya maido da kadarorin Sihiyona, mun zama kamar masu mafarki. 2 Daga nan bakunanmu suka cika da dariya harsunanmu kuma da waƙa. Daga nan suka ce a tsakanin al'ummai, "Yahweh ya yi masu manyan abubuwa." 3 Yahweh ya yi mana manyan abubuwa; mun kuwa yi murna! 4 Ka maido da kadarorinmu, Yahweh, kamar rafuffukan Negeb. 5 Su waɗanda suka yi shuka cikin hawaye zasu yi girbi tare da sowace-sowacen farinciki. 6 Shi wanda ya fita da kuka, yana ɗauke da irin shuka, zai sake dawowa da sowace-sowacen farinciki, yana kawo dammunansa tare da shi.
1 Unless Yahweh builds the house,
they work uselessly, those who build it.
Unless Yahweh guards the city,
the watchman stands guard uselessly.
2 It is useless for you to rise up early,
to come home late,
or to eat the bread of hard work,
for Yahweh provides for his beloved as they sleep.
3 See, children are a heritage from Yahweh,
and the fruit of the womb is a reward from him.
4 Like arrows in the hand of a warrior,
so are the children of one's youth.
5 How blessed is the man
that has his quiver full of them.
He will not be put to shame
when he confronts his enemies in the gate.
1 Sai idan Yahweh ne ya gina gida, sun yi aikin banza, su waɗanda ke ginin. Sai idan Yahweh ne yayi tsaron birni, masu tsaron suna tsayawa tsaro a banza. 2 Aikin banza ne a gare ka ka tashi da wuri, ka dawo gida da latti, ko ka ci gurasar aiki tuƙuru, domin Yahweh yana biyan buƙatun masu ƙaunarsa yayin da suke barci. 3 Duba, 'ya'ya gãdo ne daga Yahweh, kuma ɗiyan mahaifa lada ne daga gare shi. 4 Kamar kibiyoyi a hannun mayaƙi, haka nan 'ya'yan ƙuruciyar mutum. 5 Yaya albarkar mutumin da yake da kwarinsa cike da su. Ba zai sha kunya ba sa'ad da ya fuskanci maƙiyansa a ƙofa.
1 Blessed is everyone who honors Yahweh,
who walks in his ways.
2 The labor of your hands you will enjoy;
you will be blessed and prosper.
3 Your wife will be like a fruitful vine
in your house;
your children will be like olive plants
as they sit around your table.
4 Yes, indeed, the man will be blessed
who honors Yahweh.
5 May Yahweh bless you from Zion;
may you see the prosperity of Jerusalem
all the days of your life.
6 May you live to see your children's children.
May peace be on Israel.
1 Mai albarka ne duk wanda ya girmama Yahweh, wanda ya ke tafiya cikin hanyoyinsa. 2 Abin da hannuwanka suka wadatar, zaka ji daɗin sa; zaka yi albarka da wadata. 3 Matarka zata zama kamar inabi mai bada 'ya'ya a cikin gidanka; 'ya'yanka zasu zama kamar itatuwan zaitun yayin da suka zauna kewaye da teburinka. 4 I, tabbas, mutumin zai zama mai albarka wanda ya ke girmama Yahweh. 5 Bari Yahweh ya albarkace ka daga Sihiyona; bari kaga wadatar Yerusalem dukkan kwanakin rayuwarka. 6 Bari ka rayu ka ga 'ya'yan 'ya'yanka. Bari salama ta kasance bisa Isra'ila.
1 "Often since my youth they have attacked me,"
let Israel say.
2 "Often since my youth they have attacked me,
yet they have not defeated me.
3 The plowers plowed on my back;
they made their furrows long.
4 Yahweh is righteous;
he has cut off the ropes of the wicked."
5 May they all be put to shame and turned back,
those who hate Zion.
6 May they be like the grass on the housetops
that withers before it grows up,
7 that cannot fill the reaper's hand
or the chest of the one who binds bundles of grain together.
8 May those who pass by not say,
"May the blessing of Yahweh be on you;
we bless you in the name of Yahweh."
1 "Sau da yawa tun ƙuruciya ta suke kawo mani hari," bari Isra'ila yace. 2 "Sau da yawa tun ƙuruciya ta suke kawo mani hari, duk da haka ba su kayar dani ba. 3 Masu huɗa suna huɗa bisa bayana; sunyi kuyyoyinsu da tsawo. 4 Yahweh mai adalci ne; ya datse igiyoyin mai mugunta." 5 Bari dukkan su su sha kunya su kuma koma baya, su waɗanda suka ƙi jinin Sihiyona. 6 Bari su zama kamar ciyawar dake bisa rufin gida wadda ke yaushi kafin ta girma, 7 wadda ba zata cika hannun mai girbi ba ko ƙirjin mai ɗaure dammuna. 8 Bari waɗanda ke ratsawa su wuce kada su ce, "Bari albarkar Yahweh ta kasance a kan ka; mun albarkace ka a cikin sunan Yahweh."
1 Out of the depths I cry to you, Yahweh.
2 Lord, hear my voice;
let your ears be attentive
to my pleas for mercy.
3 If you, Yah, would mark iniquities,
Lord, who could stand? [1]
4 But there is forgiveness with you,
that you may be revered.
5 I wait for Yahweh, my soul waits,
and in his word I hope.
6 My soul waits for the Lord
more than watchmen wait for the morning.
7 Israel, hope in Yahweh.
Yahweh is merciful,
and with him is great redemption.
8 It is he who will redeem Israel
from all his iniquities.
1 Daga zurfafa nayi kuka gare ka, Yahweh. 2 Ubangiji, ka ji murya ta; bari kunnuwanka su saurari roƙe-roƙe na domin jinƙai. 3 Idan kai, Yahweh, zaka kula da kurakurai, Ubangiji, wane ne zai iya tsayawa? 4 Amma akwai gafartawa tare da kai, saboda a girmama ka. 5 Nayi jira domin ka Yahweh, raina yana jira, kuma a cikin maganarsa nake da bege. 6 Raina yana jira domin Ubangiji fiye da yadda masu tsaro ke jira domin safiya. 7 Isra'ila, kuyi bege cikin Yahweh. Yahweh yana cike da jinƙai, kuma yana da nufin gafartawa sosai. 8 Shi ne wanda zai fanshi Isra'ila daga dukkan zunubansa.
1 Yahweh, my heart is not proud
or my eyes haughty.
I do not have great hopes for myself
or concern myself with things that are beyond me.
2 Indeed I have stilled and quieted my soul;
like a weaned child with his mother,
my soul within me is like a weaned child.
3 Israel, hope in Yahweh
now and forever.
1 Yahweh, zuciyata ba tayi fahariya ba ko idanuna suyi tsauri. Bani da manyan bege domin kaina ko in dami kaina da abubuwan da suka sha kaina. 2 Tabbas na tsaida kuma na tausar da raina; kamar ɗan da aka yaye tare da mahaifiyarsa, raina a ciki na kamar ɗan yaye ya ke. 3 Isra'ila, kasa bege cikin Yahweh yanzu da har abada.
1 Yahweh, for David's sake call to mind
all his afflictions.
2 Call to mind how he swore to Yahweh,
how he vowed to the Mighty One of Jacob.
3 He said, "I will not enter the tent of my house
or get on the couch of my bed,
4 I will not give sleep to my eyes
or rest to my eyelids
5 until I find a place for Yahweh,
a tabernacle for the Mighty One of Jacob."
6 See, we heard about it in Ephrathah;
we found it in the fields of Jaar.
7 We will go into God's tabernacle;
we will worship at his footstool.
8 Arise, Yahweh, to your resting place,
you and the ark of your strength!
9 May your priests be clothed with integrity;
may your faithful ones shout for joy.
10 For your servant David's sake,
do not turn away from your anointed king.
11 Yahweh swore a sure oath to David,
a sure oath that he will not revoke:
"I will place one of your descendants on your throne.
12 If your sons keep my covenant
and the solemn commands that I will teach them,
their children also will sit on your throne forevermore."
13 Certainly Yahweh has chosen Zion,
he has desired her for his seat.
14 "This is my resting place forever.
I will live here, for I desire her.
15 I will abundantly bless her with provisions.
I will satisfy her poor with bread.
16 I will clothe her priests with salvation,
her faithful ones will shout aloud for joy.
17 There I will make a horn to sprout for David
and set up a lamp for my anointed one.
18 I will clothe his enemies with shame,
but on him his crown will shine."
1 Yahweh, albarkacin Dauda ka tuna da dukkan ƙuncinsa. 2 Ka tuna da yadda ya rantse wa Yahweh, yadda yayi wa'adi ga Mai Iko Dukka na Yakubu. 3 Yace, "Ba zan shiga gidana ba ko in kwanta a kan gadona ba, 4 ba zan ba idanuna barci ba ko kuma in rintsa 5 sai na samawa Yahweh wuri, rumfar sujada domin Maɗaukaki na Yakubu." 6 Duba, munji haka a Ifrata; mun same shi a jejin Yayir. 7 Zamu shiga rumfar sujada ta Allah; zamu yi sujada a ƙafafunsa. 8 Tashi, Yahweh, zuwa wurin hutawarka, kai da akwatin alƙawarinka mai nuna ƙarfinka! 9 Bari firistocinka su suturta da adalci; bari amintattunka suyi ihu don murna. 10 Saboda bawanka Dauda, kada ka juya wa zaɓaɓɓen sarkinka baya. 11 Yahweh ya rantse da tabbatacciyen wa'adi ga Dauda, tabbataccen wa'adi da ba zai janye ba: "Zan naɗa ɗaya daga cikin zuriyarka in sa shi bisa gadon sarautarka. 12 Idan 'ya'yanka sun yi biyayya da umarnina da kuma dokokin da zan koya masu, 'ya'yansu zasu zauna a gadon sarautarka har abada." 13 Hakika Yahweh ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa. 14 "Nan ne wurin hutawana har abada. Zan zauna a nan, gama ina marmarinta. 15 Zan albarkaceta da yalwar abin da take buƙata, zan ƙosar da matalautanta da abinci. 16 Zan suturta firistocinta da ceto, amintattunta zasu yi sowa da ƙarfi don murna. 17 Can zan sa ƙaho ya toho domin Dauda zan kuma kafa fitila domin zaɓaɓɓena. 18 Zan suturta maƙiyansa da kunya, amma a kansa kambinsa zai yi walƙiya."
1 Behold, how good and how pleasant it is
for brothers to live together!
2 It is like fine oil on the head
pouring down on the beard—
Aaron's beard,
and then it pours down on the collar of his robes.
3 It is like the dew of Hermon
which falls on the mountains of Zion.
For there Yahweh commanded the blessing—
life forevermore.
1 Duba, yadda ya ke da kyau da kuma daɗi idan 'yan'uwa suka zauna tare! 2 Wannan yana kama da mai mai kyau a kai dake gangarowa zuwa gemu - gemun Haruna, yana kuma gangarowa har kan wuyar rigarsa. 3 Kamar raɓar Hermon da take fadowa bisa duwatsun Sihiyona. Gama a nan ne Yahweh ya umarta albarka - rai na har abada.
1 Come, bless Yahweh, all you servants of Yahweh,
you who serve during the night in the house of Yahweh.
2 Lift up your hands to the holy place
and bless Yahweh.
3 May Yahweh bless you from Zion,
he who made heaven and earth.
1 Ku zo, ku albarkaci Yahweh, dukkanku bayin Yahweh, ku da kuke wa Yahweh hidima da dare a haikalinsa. 2 Ku ɗaga hannunwanku zuwa wuri mai tsarki ku albarkaci Yahweh. 3 Bari Yahweh ya albarkace ku daga Sihiyona, Shi da yayi sama da ƙasa.
1 Give praise to Yah! [1]
Praise the name of Yahweh.
Praise him, you servants of Yahweh,
2 you who stand in the house of Yahweh,
in the courtyards of the house of our God.
3 Give praise to Yah, for he is good; [2]
sing praises to his name, for it is pleasant to do so.
4 For Yah has chosen Jacob for himself, [3]
Israel as his own possession.
5 I know that Yahweh is great,
that our Lord is above all gods.
6 Whatever Yahweh desires, he does
in heaven, on earth,
in the seas and all the ocean depths.
7 He brings the clouds from far away,
making lightning bolts accompany the rain
and bringing the wind out of his storehouse.
8 He killed the firstborn of Egypt,
both of man and animals.
9 He sent signs and wonders into your midst, Egypt,
against Pharaoh and all his servants.
10 He attacked many nations
and killed mighty kings,
11 Sihon king of the Amorites
and Og king of Bashan
and all the kingdoms of Canaan.
12 He gave us their land as an inheritance,
an inheritance to Israel his people.
13 Your name, Yahweh, endures forever;
your renown, Yahweh, endures throughout all generations.
14 For Yahweh defends his people
and has compassion on his servants.
15 The nations' idols are silver and gold,
the work of men's hands.
16 Those idols have mouths, but they do not speak;
they have eyes, but they do not see;
17 they have ears, but they do not give ear,
nor is there breath in their mouths.
18 Those who make them are like them,
as is everyone who trusts in them.
19 Descendants of Israel, bless Yahweh;
descendants of Aaron, bless Yahweh.
20 Descendants of Levi, bless Yahweh;
you who honor Yahweh, bless Yahweh.
21 Blessed be Yahweh in Zion,
he who lives in Jerusalem.
Give praise to Yah. [4]
1 Ku yabi Yahweh. Ku yabi sunan Yahweh. Ku yabe shi, ku barorin Yahweh, 2 ku da kuke tsayawa a cikin haikalinsa, cikin harabun gidan Allahnmu. 3 Ku yabi Yahweh, gama shi nagari ne; ku raira waƙoƙin yabo ga sunansa, gama yana da ƙyau a yi haka. 4 Gama Yahweh ya zaɓi Yakubu domin kansa, Isra'ila abin mallakarsa. 5 Na sani Yahweh mai girma ne, kuma Ubangijinmu yafi dukkan alloli. 6 Ko mene ne Yahweh ya ke marmari, yakan yi shi a cikin sama, da ƙasa, a cikin ruwaye da dukkan zurfafan tekuna. 7 Yakan kawo gizagizai daga nesa, yakan sa walƙiya da ruwan sama su taho tare, ya kuma fito da iska daga rumbunsa. 8 Ya kashe ɗan farin Masar, na mutum dana dabbobi. 9 Ya aika da alamu da al'ajibai a tsakiyarsu, Masar, gãba da Fir'auna da dukkan barorinsa. 10 Ya hari al'ummai da yawa ya kuma kashe manyan sarkuna, 11 Sihon sarkin Amoriyawa da Og sakin Bashan da dukkan mulkokin Kan'ana. 12 Ya ba mu ƙasarsu abin gãdo, gãdo ga Isra'ila mutanensa. 13 Sunanka, Yahweh, ya dawwama har abada; ka shahara, Yahweh, dawwamamme har tsararraki dukka. 14 Gama Yahweh zai kare mutanensa, yana juyayin barorinsa. 15 Allolin al'ummai azurfa ne da zinariya, aikin hannuwan mutane. 16 Waɗannan allolin suna da bakuna, amma ba su yin magana; suna da idanu, amma ba sa gani; 17 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, babu kuma numfashi a bakunansu. 18 Waɗanda suka siffanta su kamar su suke, haka kuma wanda ya dogara gare su. 19 Zuriyar Isra'ila, ku albarkaci Yahweh; ku zuriyar Haruna, ku albarkaci Yahweh. 20 Ku zuriyar Lebi, ku albarkaci Yahweh; ku da kuke girmama Yahweh, ku albarci Yahweh. 21 Mai albarka ne Yahweh a cikin Sihiyona, shi wanda da ya ke zaune cikin Yerusalem. Ku yabi Yahweh.
1 Give thanks to Yahweh, for he is good.
(His covenant faithfulness endures forever.)
2 Give thanks to the God of gods.
(His covenant faithfulness endures forever.)
3 Give thanks to the Lord of lords;
(His covenant faithfulness endures forever.)
4 to him who alone does great wonders;
(His covenant faithfulness endures forever.)
5 to him who by wisdom made the heavens;
(His covenant faithfulness endures forever.)
6 to him who spread out the earth above the waters;
(His covenant faithfulness endures forever.)
7 to him who made great lights;
(His covenant faithfulness endures forever.)
8 to him who gave the sun to rule by day,
(His covenant faithfulness endures forever.)
9 the moon and stars to rule by night;
(His covenant faithfulness endures forever.)
10 to him who killed the firstborn of Egypt
(His covenant faithfulness endures forever.)
11 and brought out Israel from among them
(His covenant faithfulness endures forever.)
12 with a strong hand and a raised arm;
(His covenant faithfulness endures forever.)
13 to him who divided the Sea of Reeds
(His covenant faithfulness endures forever.)
14 and made Israel to pass through the middle of it,
(His covenant faithfulness endures forever.)
15 but overthrew Pharaoh and his army in the Sea of Reeds;
(His covenant faithfulness endures forever.)
16 to him who led his people through the wilderness;
(His covenant faithfulness endures forever.)
17 to him who killed great kings;
(His covenant faithfulness endures forever.)
18 to him who killed majestic kings,
(His covenant faithfulness endures forever.)
19 Sihon king of the Amorites
(His covenant faithfulness endures forever.)
20 and Og king of Bashan;
(His covenant faithfulness endures forever.)
21 to him who gave their land as an inheritance,
(His covenant faithfulness endures forever.)
22 an inheritance to Israel his servant;
(His covenant faithfulness endures forever.)
23 to him who called us to mind and helped us in our humiliation;
(His covenant faithfulness endures forever.)
24 to him who has rescued us from our enemies,
(His covenant faithfulness endures forever.)
25 who gives food to all living beings.
(His covenant faithfulness endures forever.)
26 Give thanks to the God of heaven.
(His covenant faithfulness endures forever.)
1 Oh, kuyi godiya ga Yahweh; gama nagari ne, gama alƙawarin amincisa ya dawwama har abada. 2 Oh, kuyi godiya ga Allahn alloli, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada. 3 Oh, ku yi godiya ga Ubangiji iyayengiji, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada. 4 Kuyi godiya ga wanda shi ƙaɗai ya ke manyan mu'ujizai, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada - 5 ga shi wanda ta wurin hikima yayi sammai, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada. 6 Ku yi godiya ga shi wanda ya shinfiɗa ƙasa da sama da ruwaye, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada - 7 ga shi wanda yayi manyan haske, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada. 8 Kuyi godiya ga wanda ya bada rana yayi mulkin yini, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada - 9 wata da taurari suyi mulki da dare, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada. 10 Kuyi godiya ga wanda ya karkashe 'ya'yan fari na Masar, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada - 11 ya fitar da Isra'ila daga tsakiyarsu, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada - 12 da ƙarfin hannunsa ba janyewa, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada. 13 Ku yi godiya ga wanda ya tsaga Tekun Iwa, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada - 14 yasa Isra'ila suka wuce ta tsakiyarsa, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada - 15 amma ya dulmayar da Fir'auna da rundunarsa cikin Tekun Iwa, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada. 16 Kuyi godiya ga wanda ya bida mutanensa cikin jeji, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada - 17 ga shi wanda ya kashe manyan sarakuna, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada. 18 Kuyi godiya ga wanda ya kashe shahararrun sarakuna, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada - 19 Sihon sarkin Amoriyawa, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada - 20 da Og sarkin Bashan, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada. 21 Kuyi godiya ga shi wanda ya bada ƙasarsu abin gado, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada - 22 abin gado ga Isra'ila bawansa, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada - 23 ga wanda ya tuna damu ya kuma taimake mu cikin ƙasƙancinmu, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada. 24 Kuyi godiya ga shi wanda ya bamu nasara bisa maƙiyanmu, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada - 25 ga wanda ke bada abinci ga dukkan masu rai, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada. 26 Oh, sai ku yi godiya ga Allah na sama, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.
1 By the rivers of Babylon
we sat down and wept
when we thought about Zion.
2 There on the poplars in the midst of it
we hung our harps.
3 There our captors required songs from us,
and those who mocked us required joy from us, saying,
"Sing us one of the songs of Zion."
4 How could we sing a song about Yahweh
in a foreign land?
5 If I ignore the memory of you, Jerusalem,
let my right hand forget her skill.
6 Let my tongue cling to the roof of my mouth
if I think about you no more,
if I do not prefer Jerusalem
more than my greatest delights.
7 Call to mind, Yahweh, what the Edomites did
on the day Jerusalem fell.
They said, "Tear it down, tear it down
to its foundations."
8 Daughter of Babylon, soon to be destroyed—
may the person be blessed, whoever pays you back
for what you have done to us.
9 May the person be blessed,
whoever takes and dashes your little ones against a rock.
1 Muka zauna a bakin kogunan Babila muka yi ta kuka da muka tuna da Sihiyona. 2 Muka rataye garayunmu akan itatuwa. 3 A can waɗanda suka bautar damu suka roƙa muyi masu waƙoƙi, kuma waɗanda suka yi mana ba'a suka matsa mana muyi farinciki, suna cewa, "Ku raira mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona." 4 Ƙaƙa zamu raira waƙa kan Yahweh a baƙuwar ƙasa? 5 Idan na ƙyale tunawa dake, Yerusalem, bari hannun damana ya manta da iya kaɗa garaya. 6 Bari harshena ya manne a rufin bakina, idan na dena tunaninki, idan ban fi son Yerusalem da abin da nafi jin daɗi ba. 7 Ka tuna, Yahweh, abin da Idomawa suka yi a ranar da Yerusalem ta faɗi. Suka ce, "A ragargazata, a ragargazata har harsashenta." 8 Ɗiyar Babila, an kusa hallaka ki - bari mutumin nan ya zama da albarka, ko ma wane ne wanda ya sãka maki domin abin da kika yi mana. 9 Bari mutumin nan ya sami albarka, duk wanda ya kwashe 'ya'yanki ƙanana ya fyaɗa su kan duwatsu.
1 I will give you thanks with my whole heart;
before the gods I will sing praises to you.
2 I will bow down toward your holy temple
and give thanks to your name
for your covenant faithfulness and for your trustworthiness.
You have made your word and your name
more important than anything else.
3 On the day that I called you, you answered me;
you made me bold and strengthened my soul.
4 All the kings of the earth will give you thanks, Yahweh,
for they will hear the words from your mouth.
5 Indeed, they will sing of the deeds of Yahweh,
for great is the glory of Yahweh.
6 For though Yahweh is high, yet he cares for the lowly,
but the proud he knows from far off.
7 Though I walk in the middle of trouble,
you will preserve my life;
you will reach out with your hand against the anger of my enemies,
and your right hand will save me.
8 Yahweh is with me to the end;
your covenant faithfulness, Yahweh, endures forever.
Do not abandon the works of your hands.
1 Zan yi maka godiya da dukkan zuciyata; a gaban alloli zan raira yabbai gare ka. 2 Zan rusuna ina fuskantar haikalinka mai tsarki in kuma bada godiya ga sunanka sabili da amincinka na alƙawarinka domin kuma amincewarka. Ka fifita maganarka da sunanka da muhimmanci fiye da komai. 3 A ranar dana kira ka, ka amsa mani; ka ƙarfafa ni ka bani karfin zuciya. 4 Dukkan sarakunan duniya zasu yi maka godiya, Yahweh, gama zasu ji maganganun bakinka. 5 Hakika, zasu raira waƙoƙi akan abubuwan da Yahweh yayi, gama ɗaukakar Yahweh mai girma ce. 6 Gama ko da ya ke Yahweh mafifici ne, duk da haka yana kula da masu kaɗaici, amma ya san masu girman kai tun daga nesa. 7 Koda ya ke ina tafiya a tsakiyar hatsari, zaka tsare raina; zaka miƙa hannunka gãba da hushin maƙiyana, hannun damanka zai cece ni. 8 Yahweh yana tare da ni har ƙarshe; alƙawarin amincinka, Yahweh, dawwamamme ne har abada. Kada ka yasar da waɗanda hannuwanka suka yi.
1 Yahweh, you have examined me,
and you know me.
2 You know when I sit down and when I get up;
you understand my thoughts from far away.
3 You observe my path and my lying down;
you are familiar with all my ways.
4 For before there is a word on my tongue,
you know it completely, Yahweh.
5 Behind me and before me you surround me
and place your hand upon me.
6 Such knowledge is incomprehensible to me;
it is too high, and I cannot reach it.
7 Where can I go from your Spirit?
Where can I flee from your presence?
8 If I ascend up to the heavens, you are there;
if I make my bed in Sheol, behold, you are there.
9 If I fly away on the wings of the dawn
and go to live in the uttermost parts across the sea,
10 even there your hand will lead me,
your right hand will hold on to me.
11 If I said, "Surely the darkness will cover me,
and the light will become night around me,"
12 even the darkness would not be dark to you.
The night would shine like the day,
for the darkness and the light are both alike to you.
13 You formed my inner parts;
you formed me in my mother's womb.
14 I will praise you
because I am fearfully and wonderfully made.
Your works are wonderful.
My soul knows this very well.
15 My bones were not hidden from you
when I was made in private,
when I was intricately made in the depths of the earth.
16 You saw me inside the womb;
all the days assigned to me were recorded
in your book even before the first one happened.
17 How precious are your thoughts to me, God!
How vast is their sum!
18 If I tried to count them,
they would be more in number than the sand.
When I awake, I am still with you.
19 If only you would kill the wicked, God;
get away from me, you men of bloodshed.
20 They rebel against you and act deceitfully;
your enemies tell lies.
21 Do I not hate those, Yahweh, who hate you?
Do I not despise those who rise up against you?
22 I hate them completely;
they have become my enemies.
23 Examine me, God, and know my heart;
test me and know my thoughts.
24 See if there is any wicked way in me,
and lead me in the everlasting way.
1 Yahweh, ka jaraba ni, ka kuma sanni. 2 Ka san lokacin da zan zauna da lokacin da zan tashi; ka san tunanina tun daga nesa. 3 Kana lura da tafarkina da kwanciyata; hanyoyina sanannu ne dukka a gareka. 4 Gama kafin magana ta kasance a kan harshena, ka sani sarai. 5 Ka kewaye ni gaba da baya kuma ka ɗibiya hannunka a kaina. 6 Wannan sani ya fi ƙarfina ƙwarai; yayi mani zurfi, ba zan iya fahimtar sa ba. 7 Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan guje wa fuskarka? 8 Idan na hau cikin sammai, kana can; Idan na tafi na zauna cikin Lahira, to duba, kana can. 9 Idan nayi asubanci na tashi sama akan fukafukai na tafi na zauna can nesa a ƙurewar teku, 10 ko can ma hannunka zai bishe ni, hannun damanka zai riƙe ni. 11 Idan nace, "Hakika duhu zai rufe ni, haske kuma ya zama dare kewaye dani," 12 ko duhunma ba zai zama duhu a gare ka ba. Daren zai haskaka kamar rana, gama da duhu da haske duk ɗaya suke a gare ka. 13 Kai ka yi gaɓaɓuwan cikin cikina; kai ka siffanta ni a cikin mahaifiyata. 14 Zan yabe ka, gama an yini da ƙyan gaske. Raina ya tabbatar da wannan sosai. 15 Ƙasusuwana ba a ɓoye suke ba gare ka sa'ad da aka siffanta ni a ɓoye, sa'ad da aka hallita ni a can cikin zurfin ƙasa. 16 Ka ganni a cikin mahaifa; dukkan kwanakin da an ƙaddara mani suna rubuce cikin littafinka tun kafin na farkon ya faru. 17 Tunaninka yana da daraja a guna, Allah! Tarinsu da yawa basu lisaftuwa. 18 Idan na yi ƙoƙarin ƙididdiga su, zasu fi yashi yawa. Sa'ad da na farka, ina tare da kai. 19 Dãma zaka kashe mugaye, ya Allah; ku rabu dani, ku 'yan ta'adda. 20 Suna yi maka tawaye suna aikata munafunci, maƙiyanka suna faɗar ƙarairayi. 21 Ba na ƙi waɗanda suka ƙi ka ba, Yahweh? Ba ina rena waɗanda suka tashi gãba da kai ba? 22 Na ƙi su fau-fau; sun zama maƙiyana. 23 Ka jaraba ni, ya Allah, ka san zuciyata; ka gwada ni ka san tunanina. 24 Ka duba ko akwai muguwar hanya a cikina, ka kuma bishe ni a madawwamiyar hanya.
1 Yahweh, rescue me from the wicked;
preserve me from violent men.
2 They plan evil in their hearts;
they cause battles every day.
3 Their tongues wound like serpents;
vipers' poison is on their lips. Selah
4 Keep me from the hands of the wicked, Yahweh;
preserve me from violent men
who plan to push down my steps.
5 The proud have set a trap for me;
they have spread a net;
they have set a snare for me. Selah
6 I said to Yahweh, "You are my God;
give ear to the sound of my pleas."
7 Yahweh, my Lord, you are powerfully able to save me;
you shield my head in the day of battle.
8 Yahweh, do not grant the desires of the wicked;
do not let their evil plans succeed. Selah
9 Those who surround me raise their heads;
let the mischief of their own lips cover them.
10 Let burning coals fall on them;
throw them into the fire,
into bottomless pits, never more to rise.
11 May men of tongues not be made secure on the earth;
may evil hunt down the violent man to strike him dead.
12 I know that Yahweh will judge in favor of the afflicted,
and that he will give justice to the needy.
13 Surely the righteous people will give thanks to your name;
the upright people will live in your presence.
1 Yahweh, ka cece ni daga mugaye; ka kiyaye ni daga mutane masu zafin rai. 2 Sukan shirya mugunta a zuciyarsu; sukan sa yaƙi kowacce rana. 3 Harsunansu suna sara kamar maciji; dafin kububuwa na leɓunansu. Selah 4 Ka tsare ni daga hannuwan mugaye, Yahweh; ka tsare ni daga mutane masu zafin rai waɗanda suka shirya su kada ni ƙasa. 5 Masu fariya sun ɗana mani tarko; sun baza taru; sun shirya mani tarko. Selah 6 Na cewa Yahweh, "Kai ne Allahna; ka kasa kunne ga koke-kokena na neman jinƙai. 7 Yahweh, Ubangijina, kai mai iko ne ka iya ceto na; kana kare kaina a lokacin yaƙi. 8 Yahweh, kada ka biya buƙatun mugaye; kada ka bari shirye-shiryensu yayi nasara. Selah 9 Waɗanda suka ɗaga kansu sun kewaye ni; bari makircin leɓunansu ya rufe su. 10 Bari garwashin wuta su afko masu; ka jefa su cikin wuta, cikin rami marar matuƙa, kada su ƙara tashi. 11 Kada mutane masu mugun harshe su sami kwanciyar rai a duniya; bari bala'i ya farauci ɗan ta'adda ya buge shi ya mutu. 12 Na sani Yahweh zai kyautata wa mai shan ƙunci a shari'a kuma zai yi adalci ga matalauci. 13 Hakika mutane masu adalci zasu bada godiya ga sunanka; mutanen dake yin gaskiya zasu kasance a gabanka.
1 Yahweh, I am crying out to you; come quickly to me.
Give ear to my voice when I call to you.
2 May my prayer be like incense before you;
may my lifted hands be like the evening sacrifice.
3 Yahweh, place a guard over my mouth;
guard the door of my lips.
4 Do not let my heart desire any evil thing
or participate in wicked deeds
with men who behave wickedly.
May I not eat any of their delicacies.
5 Let a righteous man hit me; it will be a kindness to me.
Let him correct me; it will be like oil on my head;
may my head not refuse to accept it.
But my prayer is always against their wicked deeds.
6 Their judges will be thrown down from the top of cliffs;
they will hear that my own words are pleasant.
7 They will have to say, "As when one plows and breaks up the ground,
so our bones have been scattered at the mouth of Sheol."
8 Surely my eyes are on you, Yahweh, Lord;
in you I take refuge; do not leave my soul defenseless.
9 Protect me from the snares that they have laid for me,
from the traps of those who behave wickedly.
10 Let the wicked fall into their own nets
while I escape.
1 Yahweh, ina kuka gare ka; ka zo wurina da sauri. Ka saurare ni sa'ad da na kira ka. 2 Bari addu'ata ta zama kamar turare a gaban ka; bari tãda hannuwana sama ya zama kamar hadayar maraice. 3 Yahweh, kasa mai tsaro a bakina; ka kiyaye ƙofar leɓunana, 4 Kada ka bari zuciyata ta yi marmarin wani mugun abu ko in haɗa kai cikin ayyukan zunubi tare da mutanen dake aikata mugunta. Kada ma in ci wani kayan lashe-lashensu. 5 Bari adilin mutum ya buge ni; zai zamar mani alheri. Bari ya tsauta mani; zai zama kamar mai a kaina; bari kada in ƙi karɓar wannan. Amma addu'ata kullum gãba take da ayyukan muguntarsu. 6 Za a jefar da shugabanninsu daga kan duwatsu; zasu ji cewa maganganuna masu daɗi ne. 7 Tilas zasu ce, "Kamar yadda mutum yakan yi huɗa ya rugurguza ƙasa, haka suka warwatsar da ƙasusuwanmu a ƙofar Lahira." 8 Hakika idanuna suna kanka, Yahweh, Ubangiji; a cikinka zan fake; kar ka bar raina ba tsaro. 9 Ka tsare ni daga tarkunan da suka ɗana mani, daga tarkunan masu mugun aiki. 10 Bari mugaye su faɗa cikin tarkonsu ni kuwa in kubce.
1 With my voice I cry out for help to Yahweh;
with my voice I plead for Yahweh's favor.
2 I pour out my lament before him;
I tell him my troubles.
3 When my spirit is weak within me,
you know my path.
In the way that I walk
they have hidden a trap for me.
4 I look to my right and see
that there is no one who cares about me.
There is no escape for me;
no one cares about my life.
5 I called out to you, Yahweh;
I said, "You are my refuge,
my portion in the land of the living.
6 Listen to my cry,
for I have been brought very low;
rescue me from my persecutors,
for they are stronger than I.
7 Bring my soul out of prison
so that I may give thanks to your name.
The righteous will gather around me
because you have been good to me."
1 Da muryata nayi kuka domin neman taimako daga Yahweh; da muryata na roƙi Yahweh tagomashi. 2 Na zuba masa koke-kokena a gabansa; na gaya masa wahaluna. 3 Sa'ad da ruhuna ya raunana a cikina, ka san tafarkina. Sun ɗana ɓoyayyen tarko domina a hanyar da nake bi. 4 Na duba hannun damana sai na ga babu wanda ya kula dani. Ba mafita domina, ba wanda ya kula da rayuwata. 5 Na kira gare ka, Yahweh; nace, "Kai ne mafakata, rabona kuma a ƙasar rayayyu. 6 Ka kasa kunne ga kirana, gama an ƙasƙantar dani; ka cece ni daga masu tsananta mani, gama sun fi ƙarfi na, 7 Ka fitar da raina daga kurkuku domin in yi godiya ga sunanka. Masu adalci zasu tattaru kewaye dani domin ka yi mani alheri."
1 Hear my prayer, Yahweh;
give ear to my pleas.
Because of your faithfulness and righteousness,
answer me!
2 Do not enter into judgment with your servant,
for in your sight no one is righteous.
3 The enemy has pursued my soul;
he has crushed me to the ground;
he has made me to live in darkness
like those who have been dead a long time.
4 My spirit is overwhelmed within me;
my heart is appalled.
5 I call to mind the old days;
I meditate on all your deeds;
I reflect on your accomplishments.
6 I spread my hands out to you;
my soul thirsts for you in a parched land. Selah
7 Answer me quickly, Yahweh,
because my spirit faints.
Do not hide your face from me,
or I will become like those who go down into the pit.
8 Let me hear your covenant faithfulness in the morning,
for I trust in you.
Show me the way where I should walk,
for I lift up my soul to you.
9 Rescue me from my enemies, Yahweh;
I flee to you to hide.
10 Teach me to do your will,
for you are my God.
May your good Spirit
lead me in the land of uprightness.
11 Yahweh, for your name's sake, keep me alive;
in your righteousness bring my soul out of trouble.
12 In your covenant faithfulness cut off my enemies
and destroy all the enemies of my life,
for I am your servant.
1 Ka ji addu'ata, Yahweh; ka ji roƙona. Saboda amincinka da adalcinka, ka amsa mani! 2 Kada ka gabatar da bawanka a gaban shari'a gama a gabanka babu mai adalci ko ɗaya. 3 Maƙiyina ya hari raina; ya ture ni ƙasa; ya sãni in zauna cikin duhu kamar waɗanda suka mutu tun-tuni. 4 Ruhuna ya karaya a cikina; babu sauran bege a raina. 5 Idan na tuna kwanakin dã; na kan yi bin-bini akan ayyukanka; ina tunani akan nasararka. 6 Na tada hannuwana zuwa gare ka cikin addu'a; raina yana da ƙishinka cikin ƙeƙasasshiyar ƙasa. Selah 7 Ka amsa mani da wuri, Yahweh, saboda ruhuna ya some. Kada ka ɓoye mani fuskarka, domin kada in zama kamar masu gangarawa cikin rami. 8 Bari inji alƙawarinka na aminci da safe, gama na dogara gare ka. Ka nuna mani tafarkin da zan bi, gama nasa zuciyata a gare ka. 9 Ka cece ni daga maƙiyana, Yahweh; ina gudu gare ka domin in ɓoye. 10 Ka koya mani in aikata nufinka, gama kai ne Allahna. Bari Ruhunka mai kyau ya bishe ni cikin ƙasar da ake adalci. 11 Yahweh, sabili da sunanka, ka barni da rai; cikin adalcinka ka fitar da raina daga wahala. 12 Cikin alƙawarin amincinka ka datse maƙiyana kuma ka hallaka dukkan maƙiyan rayuwata, gama ni baranka ne.
1 Blessed be Yahweh, my rock,
who trains my hands for war
and my fingers for battle.
2 You are my covenant faithfulness and my fortress,
my high tower and the one who rescues me,
my shield and the one in whom I take refuge,
the one who subdues nations under me.
3 Yahweh, what is man that you take notice of him
or the son of man that you think about him?
4 Man is like a breath;
his days are like a passing shadow.
5 Cause the sky to sink and come down, Yahweh;
touch the mountains and make them smoke.
6 Send flashes of lightning and scatter my enemies;
shoot your arrows and drive them back in confusion.
7 Reach out your hand from above;
rescue me out of many waters,
from the hand of foreigners.
8 Their mouths speak lies,
and their right hand is falsehood.
9 I will sing a new song to you, God;
on a lute of ten strings I will sing praises to you,
10 who gives salvation to kings,
who rescues David your servant from an evil sword.
11 Rescue me and free me
from the hand of foreigners.
Their mouths speak lies,
and their right hand is falsehood.
12 May our sons be like plants
who grow to full size in their youth
and our daughters like carved corner pillars,
shapely like those of a palace.
13 May our storehouses be full
with every kind of produce,
and may our sheep produce thousands
and ten thousands in our fields.
14 Then our oxen will have many young.
No one will break through our walls; there will be no exile
and no outcry in our streets.
15 Blessed is the people with such blessings;
happy is the people whose God is Yahweh.
1 Mai albarka ne Yahweh, dutsena, wanda ya ke horar da hannuwana domin yaƙi da yatsuna domin faɗa. 2 Kai nawane mai amintaccen alƙawari da mafakata, kaine hasumiyata mai tsawo wanda ya ke ceto na, garkuwata wanda a cikinsa nake fakewa, shi ya ke sarayar da al'ummai ƙarƙashina. 3 Yahweh, wane ne mutum har da kake kula shi ko ɗan mutum da kake tunani a kansa? 4 Mutum kamar huci ya ke; kwanakinsa kamar inuwa mai wucewa ne. 5 Ka sa sararin sama ya tsage ka sabko ƙasa, Yahweh; ka taɓa duwatsu ka sa suyi hayaƙi. 6 Ka aika walƙiyar tsawa ka warwatsar da maƙiyana; ka harba kibanka ka kore su su sheƙa a ruɗe. 7 Ka miƙo hannunka daga sama; ka cece ni daga ɗumbin ruwaye; daga hannun baƙi. 8 Bakunansu suna faɗar ƙarairayi, komai kuma dake hannunsu sun samu ne daga rashin gaskiya. 9 Zan raira maka sabuwar waƙa, ya Allah; akan garaya mai igiya goma zan raira maka yabo, 10 kai wanda ke bada ceto ga sarakai, wanda ya tsirar da Dauda bawanka daga mugun takobi. 11 Ka cece ni ka 'yantar dani daga hannun baƙi. Bakunansu suna faɗar ƙarairayi, a hannun damansu kuma akwai rashin gaskiya. 12 Bari 'ya'yanmu maza su zama kamar dashe-dashen da suka yi girma suka ƙosa a samartakarsu 'ya'yanmu mata kuma kamar sassaƙaƙƙun ginshiƙan fãda masu kyan fasali. 13 Bari rumbunanmu su cika da kowanne irin amfani, bari kuma tumakinmu su hayayyafa dubbai kan dubbai har sau goma a saura. 14 Sa'an nan shanunmu zasu haifi 'yan maruƙa da yawa. Ba wanda zai hudo ta katangunmu; baza a tafi bautar talala ba ko a ji koke-koke a tituna. 15 Masu albarka ne mutanen dake da waɗannan albarku; masu farinciki ne mutanen da Allahnsu shi ne Yahweh.
1 I will extol you, my God, King;
I will bless your name forever and ever.
2 Every day will I bless you;
I will praise your name forever and ever.
3 Great is Yahweh and greatly to be praised;
his greatness is unsearchable.
4 One generation will praise your deeds to the next
and will proclaim your mighty actions.
5 I will meditate on the majesty of your glory
and on your marvelous deeds.
6 They will speak of the power of your awesome works,
and I will declare your greatness.
7 They will declare your abounding goodness,
and they will shout joyfully about your righteousness.
8 Yahweh is gracious and merciful,
slow to anger and great in steadfast love.
9 Yahweh is good to all;
his tender mercies are over all his works.
10 All your works will give thanks to you, Yahweh;
your faithful ones will bless you.
11 They will speak of the glory of your kingdom,
and they will tell of your power.
12 They will make known to mankind God's mighty deeds
and the glorious splendor of his kingdom.
13 Your kingdom is an everlasting kingdom,
and your dominion endures throughout all generations.
14 Yahweh supports all who are falling
and raises up all those who are bent over.
15 The eyes of all wait for you;
you give them their food at the right time.
16 You open your hand
and satisfy the desire of every living thing.
17 Yahweh is righteous in all his ways
and faithful in all his deeds.
18 Yahweh is near to all those who call to him,
to all who call to him in trustworthiness.
19 He fulfills the desire of those who honor him;
he hears their cry and saves them.
20 Yahweh watches over all those who love him,
but he will destroy all the wicked.
21 My mouth will speak out the praise of Yahweh;
let all mankind bless his holy name
forever and ever.
1 Zan ɗaukaka ka, ya Allah, Sarki; zan albarkaci sunanka har abada abadin. 2 Kowace rana zan albarkace ka; zan albarkaci sunanka har abada abadin. 3 Yahweh Mai Girma ne, ƙasaitarsa ta cancanci yabo; Girmansa ba ya bincikuwa. 4 Daga wata tsara zuwa wata tsara za a yabi ayyukanka kuma za a labarta manyan ayyukanka. 5 Zan yi bin-bini akan martabar ɗaukakarka da kuma ayyukanka masu ban mamaki. 6 Zasu yi magana akan ikon manya-manyan ayyukanka, ni kuwa zan yi shelar girmanka. 7 Zasu yi shelar ayyukanka nagari masu yawa, kuma zasu raira yabo akan adalcinka. 8 Yahweh mai alheri ne kuma mai jinƙai ne, mai jinkirin fushi amincinsa kuma cikin alƙawari ba iyaka. 9 Yahweh yana yi wa kowa kirki; jinƙansa na bisa dukkan aikin hannunsa. 10 Dukkan abubuwan da kayi zasu yi maka godiya, Yahweh; amintattunka zasu sa maka albarka. 11 Amintattunka zasu yi magana akan darajar mulkinka, zasu faɗi ikonka. 12 Zasu sanar da 'yan adam ayyukan Allah masu girma da kuma ɗaukakar darajar mulkinka. 13 Mulkinka, dawwamammen mulki ne, masarautarka ta dawwama har tsararraki dukka. 14 Yahweh yakan tallafa wa dukkan waɗanda suke faɗuwa ya kuma tãda dukkan waɗanda ke a wulaƙance. 15 Idanun kowa na jiranka; ka kan basu abincinsu a madai-daicin lokaci. 16 Ka kan buɗe hannuwanka ka biya buƙatun kowanne abu mai rai. 17 Yahweh mai adalci ne a dukkan tafarkunsa mai alheri ne a dukkan abin da ya ke yi. 18 Yahweh na kusa da dukkan waɗanda suke kira gareshi, ga dukkan waɗanda suke kiransa da amincewa. 19 Yana biyan buƙatun waɗanda suke girmama shi; yana jin kukansu sai kuma ya cece su. 20 Yahweh yana lura da dukkan waɗanda ke ƙaunarsa, amma zai hallaka duk mugaye. 21 Bakina zai furta yabon Yahweh; bari duk 'yan adam su albarkaci sunansa mai tsarki har abada abadin.
1 Give praise to Yah. [1]
Praise Yahweh, my soul.
2 I give praise to Yahweh with all my life;
I will sing praises to my God as long as I exist.
3 Do not put your trust in princes
or in mankind, in whom there is no salvation.
4 When a person's life's breath stops, he returns to the ground;
on that day his plans end.
5 Blessed is he who has the God of Jacob for his help,
whose hope is in Yahweh his God.
6 Yahweh made heaven and earth,
the sea, and all that is in them;
he observes trustworthiness forever.
7 He executes justice for the oppressed
and gives food to the hungry.
Yahweh frees the prisoners;
8 Yahweh opens the eyes of the blind;
Yahweh raises up those who are bowed down;
Yahweh loves the righteous people.
9 Yahweh protects the foreigners in the land;
he supports the fatherless and widow,
but he opposes the wicked.
10 Yahweh will reign forever,
your God, Zion, for all generations.
Give praise to Yah. [2]
1 Ka yabi Yahweh, Yabi Yahweh, ya raina. 2 Ina ba da yabo ga Yahweh a dukkan rayuwata; Zan raira yabo ga Allahna muddin ina raye. 3 Kada ka dogara ga sarakuna ko ga ɗan adam, waɗanda babu ceto gare su. 4 Sa'ad da ran mutum ya dena numfashi, sai ya koma turɓaya; a ranan nan shawarwarinsa zasu watse. 5 Mai albarka ne wanda mataimakinsa Allahn Yakubu ne, wanda begensa na cikin Yahweh Allahnsa. 6 Yahweh ne yayi sama da ƙasa, da teku, da dukkan abubuwan dake cikinsu; yana kiyaye gaskiya har abada. 7 Yana zartar da hukunci domin dukkan waɗanda ake zalumta kuma yana bada abinci ga mayunwata. Yahweh yakan 'yantar da ɗaurarru; 8 Yahweh yana ba makafi ganin gari; Yahweh yana tãda waɗanda an tanƙwaresu; Yahweh yana ƙaunar mutane masu aikata adalci. 9 Yahweh yana kãre bãƙin dake cikin ƙasa; yana agajin marayu da gwauraye, amma yana tsayayya da mugaye. 10 Yahweh zai yi mulki har abada, Allahnki, Sihiyona, domin dukkan tsararraki. Mu yabi Yahweh.
1 Give praise to Yah, [1]
for it is good to sing praises to our God;
it is pleasant, and praise is suitable.
2 Yahweh rebuilds Jerusalem;
he gathers together the scattered people of Israel.
3 He heals the brokenhearted
and binds up their wounds.
4 He counts the stars;
he gives names to all of them.
5 Great is our Lord and awesome in power;
his understanding cannot be measured.
6 Yahweh supports the oppressed;
he brings the wicked down to the ground.
7 Sing to Yahweh with thanksgiving;
sing praises to our God with a harp.
8 He covers the heavens with clouds
and prepares rain for the earth,
making the grass to grow on the mountains.
9 He gives food to the animals
and to the young ravens when they cry.
10 He finds no delight in the strength of a horse;
he takes no pleasure in the strong legs of a man.
11 Yahweh takes pleasure in those who honor him,
who hope in his covenant faithfulness.
12 Praise Yahweh, Jerusalem;
praise your God, Zion.
13 For he strengthens the bars of your gates;
he blesses your children among you.
14 He brings prosperity inside your borders;
he satisfies you with the finest of wheat.
15 He sends out his commandment to earth;
his command runs very swiftly.
16 He makes the snow like wool;
he scatters the frost like ashes.
17 He dispenses the hail like crumbs;
who can withstand the cold he sends?
18 He sends out his command and melts them;
he makes the wind to blow and the water to flow.
19 He proclaimed his word to Jacob,
his statutes and his righteous decrees to Israel.
20 He has not done so with any other nation,
and as for his decrees, they do not know them.
Give praise to Yah. [2]
1 Ku yabi Yahweh gama yana da kyau a raira yabo ga Allahnmu, yana da daɗi, ya dace a yi yabo. 2 Yahweh zai sake gina Yerusalem, zai sake tattaro warwatsatsun mutanen Isra'ila. 3 Yana warkar da masu karyayyar zuciya ya ɗaure raunukansu. 4 Yana ƙididdiga taurari, ya ba dukkansu sunaye. 5 Mai girma ne Ubangijinmu mai daraja a iko, saninsa ya zarce gaban aunawa. 6 Yahweh yana tãda waɗanda aka wulaƙantasu, yakan jawo miyagu ƙasa. 7 Ku raira waƙa ga Yahweh tare da godiya, mu raira yabbai ga Allahnmu da garaya. 8 Yakan rufe sammai da gizagizai ya shirya ruwan sama domin ƙasa, ya sa ciyayi su tsiro bisa duwatsu. 9 Yana ba dabbobi abincinsu da kuma 'ya'yan hankaki lokacinda suka yi kuka. 10 Ba ya jin daɗin ƙarfin doki, ba ya dogara ga ƙarfin mutum. 11 Yahweh yana jin daɗin waɗanda suke girmama shi, waɗanda suka kafa begensu akan amintaccen alƙawarinsa. 12 Ku yabi Yahweh, Yerusalem, ki yabi Allahnki, Sihiyona. 13 Gama yana ƙarfafa ƙarafun ƙofofinki, yana albarkatar 'ya'yanki a cikinku. 14 Yana kawo wadata cikin iyakar ƙasarki, yana ƙosar dake da kyakkyawar alkama. 15 Yana aika dokokinsa cikin duniya, dokokinsa yakan sheƙa da gudu. 16 Yakan yin ƙanƙara kamar ulu, ya baza dusarta kamar toka. 17 Yakan aiko da ƙanƙara kamar 'yan gutsittsire, wa zai iya jure sanyin da ya ke aikowa? 18 Ya aika dokokinsa ya narkar dasu, yakan sa iska ta buga su sai ruwan ya kwarara. 19 Ya yi shelar maganarsa ga Yakubu, farillansa da dokokinsa masu adalci ga Isra'ila. 20 Bai taɓa yin haka ba da wata al'umma, game da dokokinsa ma, basu san su ba. Mu yabi Yahweh.
1 Give praise to Yah. [1]
Praise Yahweh, you in the heavens;
praise him, you in the heights.
2 Praise him, all his angels;
praise him, all his hosts.
3 Praise him, sun and moon;
praise him, all you shining stars.
4 Praise him, highest heaven
and you waters that are above the sky.
5 Let them praise the name of Yahweh,
for he gave the command, and they were created.
6 He has also established them forever and ever;
he issued a decree that will never change.
7 Praise him from the earth,
you sea monsters and all ocean depths,
8 fire and hail, snow and clouds,
stormy wind fulfilling his word.
9 Praise him, mountains and all hills,
fruit trees and all cedars,
10 Wild animals and all livestock,
creatures that crawl and birds with wings.
11 Praise Yahweh, you kings of the earth and all nations,
you princes, and all you judges of the earth,
12 both young men and young women,
elderly and children.
13 Let them all praise the name of Yahweh,
for his name alone is exalted
and his glory extends over the earth and the heavens.
14 He has lifted up the horn of his people
for praise from all his faithful ones,
the people of Israel, the people near to him.
Give praise to Yah. [2]
1 Ku yabi Yahweh. Ku yabi Yahweh, ku dake cikin sammai; ku yabe shi, ku dake can tuddan sama. 2 Ku yabe shi, dukkanku mala'ikunsa; ku yabe shi, dukkan rundunarsa. 3 Ku yabe shi, rana da wata; ku yabe shi, dukkanku taurari masu ƙyalli. 4 Ku yabe shi, ku sammai mafi tsayi daku ruwayen dake sama da sarari. 5 Bari su yabi sunan Yahweh, gama ya bada umarnj, sai aka hallicesu. 6 Ya kuma kafasu har abada abadin; ya zartar da doka da bazata taɓa canzawa ba. 7 Ku yabe shi daga duniya, ku dodannin ruwa, da dukkan zurfafan teku, 8 wuta da ƙanƙara, dusar ƙanƙara da giza-gizai, iskar hadari masu biyayya da maganarsa. 9 Ku yabe shi, duwatsu, da dukkan tuddai, itatuwa masu bada 'ya'ya, da duk itatuwan sida, 10 namun jeji da na gida, hallitu masu rarrafe da tsuntsaye. 11 Ku yabi Yahweh, sarakunan duniya da dukkan al'ummai, hakimai da dukkan masu mulki a duniya, 12 samari da 'yan mata, dattawa da yara. 13 Bari dukkansu su yabi sunan Yahweh, gama sunansa kaɗai aka fiffita, ɗaukakarsa kuma ta mamaye duniya da sammai. 14 Ya ɗaga ƙahon mutanensa domin yabo daga dukkan amintattunsa Isra'ilawa. Mutanen dake kurkusa da shi. Ku yabi Yahweh.
1 Give praise to Yah! [1]
Sing to Yahweh a new song;
sing his praise in the assembly of the faithful ones.
2 Let Israel rejoice in the one who made them;
let the people of Zion rejoice in their king.
3 Let them praise his name with dancing;
let them sing praises to him with tambourine and harp.
4 For Yahweh takes pleasure in his people;
he glorifies the humble with salvation.
5 Let the faithful ones rejoice in this honor;
let them sing for joy on their beds.
6 May the praises of God be in their mouths
and a two-edged sword in their hand
7 to execute vengeance on the nations
and acts of punishment on the peoples.
8 They will bind their kings with chains
and their nobles with iron shackles.
9 They will execute the judgment that is written.
This will be an honor for all his faithful ones.
Give praise to Yah. [2]
1 Ku yabi Yahweh. Ku raira wa Yahweh sabuwar waƙa; ku raira yabonsa cikin taron amintattunsa. 2 Bari Isra'ila su yi murna cikin wannan daya yi su; bari mutanen Sihiyona su yi murna da sarkin sarkinsu. 3 Bari su yabi sunansa suna rawa; bari su raira masa yabo da bandiri da molo. 4 Gama Yahweh yana jin daɗin mutanensa; yana ɗaukaka masu tawali'u da cetonsa. 5 Bari masu tsoronsa su yi murna cikin nasara; bari su yi waƙa don murna bisa gadajensu. 6 Bari yabon Allah ya kasance a bakinsu da takkuba masu kaifi biyu a hannunsu 7 domin su maida martani kan al'ummai da ayyukan hukunci akan mutane. 8 Zasu ɗaure sarakunansu da sarƙoƙi shugabanninsu kuma da baƙin ƙarfe. 9 Zasu aiwata hukunci da aka rubuta. Wannan ne zai zama ɗaukaka domin dukkan amintattunsa. Ku yabi Yahweh.
1 Give praise to Yah! [1]
Praise God in his holy place;
praise him in the mighty heavens.
2 Praise him for his mighty acts;
praise him for his surpassing greatness.
3 Praise him with the blast of the horn;
praise him with lute and harp.
4 Praise him with tambourines and dancing;
praise him with stringed instruments and pipe.
5 Praise him with loud cymbals;
praise him with high sounding cymbals.
6 Let everything that has breath give praise to Yah!
Give praise to Yah! [2]
1 Ku yabi Yahweh. Ku yabi Allah cikin wurinsa mai tsarki; ku yabi ƙarfinsa cikin sammai. 2 Ku yabe shi saboda manyan ayyukansa; ku yabe shi saboda fiffikon girmansa. 3 Ku yabe shi da ƙarar ƙaho; ku yabe shi da garayu da molaye. 4 Ku yabe shi da bandiri da rawa; ku yabe shi da garayu da sarewa. 5 Ku yabe shi da kuge masu ƙara; ku yabe shi da kuge masu amo. 6 Bari dukkan abin dake da numfashi su yabi Yahweh. Ku yabi Yahweh.