Hausa: Unlocked Literal Bible for 1 Korintiyawa, 1 Tassalunikawa, 2 Korantiyawa, 2 Tasalonikawa, 2 Yahaya, 3 Yahaya, Afisawa, Ayyukan manzanni, Bitrus ta fari, Filibiyawa, Filimon, Galatiyawa, Ibraniyawa, Kolosiyawa, Littafin farawa, Littafin alƙalai, Littafin amos, Littafin ayuba, Littafin daniyel, Littafin esta, Littafin ezekiyel, Littafin ezra, Littafin fitowa, Littafin habakuk, Littafin haggai, Littafin hosiya, Littafin irmiya, Littafin ishaya, Littafin lebitikus, Littafin lissafi, Littafin mai wa'azi, Littafin maimaitawar shari'a, Littafin makoki, Littafin malakai, Littafin mika, Littafin misalai, Littafin nahum, Littafin nehemiya, Littafin obadiya, Littafin rut, Littafin sama'ila na biyu, Littafin sama'ila na farko, Littafin sarakuna na biyu, Littafin sarakuna na ɗaya, Littafin tarihi na biyu, Littafin tarihi na ɗaya, Littafin yona, Littafin yoshuwa, Littafin yowel, Littafin zabura, Littafin zafaniya, Littafin zakariya, Luka, Markus, Matiyu, Romawa, Titus, Wahayin yahaya, Wasikar bitrus ta biyu, Wasikar bulus manzo ta biyu zuwa ga timoti, Wasikar bulus manzo ta fari zuwa ga timoti, Wasikar yahaya ta fari, Wa‌ƙar suleman, Yahaya, Yahuda, Yakubu

Formatted for Translators

©2022 Wycliffe Associates
Released under a Creative Commons Attribution-ShareAlike 4.0 International License.
Bible Text: The English Unlocked Literal Bible (ULB)
©2017 Wycliffe Associates
Available at https://bibleineverylanguage.org/translations
The English Unlocked Literal Bible is based on the unfoldingWord® Literal Text, CC BY-SA 4.0. The original work of the unfoldingWord® Literal Text is available at https://unfoldingword.bible/ult/.
The ULB is licensed under the Creative Commons Attribution-ShareAlike 4.0 International License.
Notes: English ULB Translation Notes
©2017 Wycliffe Associates
Available at https://bibleineverylanguage.org/translations
The English ULB Translation Notes is based on the unfoldingWord translationNotes, under CC BY-SA 4.0. The original unfoldingWord work is available at https://unfoldingword.bible/utn.
The ULB Notes is licensed under the Creative Commons Attribution-ShareAlike 4.0 International License.
To view a copy of the CC BY-SA 4.0 license visit http://creativecommons.org/licenses/by-sa/4.0/
Below is a human-readable summary of (and not a substitute for) the license.
You are free to:
The licensor cannot revoke these freedoms as long as you follow the license terms.
Under the following conditions:
Notices:
You do not have to comply with the license for elements of the material in the public domain or where your use is permitted by an applicable exception or limitation.
No warranties are given. The license may not give you all of the permissions necessary for your intended use. For example, other rights such as publicity, privacy, or moral rights may limit how you use the material.

Littafin farawa

1

1A cikin farko, Allah ya hallici sammai da duniya.2Duniya bata da siffa, sarari ce kawai. Duhu kuma ya rufe dukkan zurfafa. Ruhun Allah kuma yana kewayawa a bisa fuskar ruwaye.

3Allah yace, "Bari haske ya kasance, haske kuwa ya kasance."4Allah kuma ya ga hasken, ya kuma ƙayatar. Sai ya raba haske da duhu.5Allah ya kira haske "yini," duhu kuma ya ce da shi "dare." Wannan shi ne safiya da dare, a rana ta ɗaya.
6Allah yace, "Bari a sami fili tsakanin ruwaye, Sai ya rarraba tsakanin ruwaye."7Allah yayi tsakani ga ruwayen dake ƙarƙas da kuma ruwayen dake sammai. Haka kuma ya kasance.8Allah ya kira tsakanin "sararin sama." Wannan shi ne maraice da safiya, rana ta biyu kenan.
9Allah yace, ruwayen dake ƙarƙashin sammai su tattaru wuri ɗaya, kuma sandararriyar ƙasa ta bayyana," haka kuma ya faru.10Allah ya kira sandararriyar ƙasa "duniya," ruwayen da suka tattaru kuma ya kira su "tekuna" ya kuma ga suna da kyau.
11Allah yace, "Duniya ta fitar da ciyayi da itatuwa masu fitar da iri da kuma 'ya'ya waɗanda ke cikin 'ya'yan, kowanne bisa ga irinsa." Haka kuma ya kasance.12Ƙasa ta fitar da ganyayyaki, da itatuwa masu bada iri kowanne bisa ga irinsa, da kuma itatuwa masu bada 'ya'ya dake cikinsu, kowanne bisa ga irinsa. Allah kuma ya ga yana da kyau.13Wannan ce safiya da maraice, rana ta uku.
14Allah yace, "Haske ya kasance a sararin sama domin ya raba tsakanin haske da duhu, su kuma zama alamu na yanayi, domin ranaku da shekaru.15Sai su zama haske a sararin sama domin su haskaka duniya." Haka kuwa ya kasance.
16Allah yayi manyan haskoki guda biyu, babban hasken yayi mulkin yini, ƙaramin hasken kuma yayi mulkin dare. Ya kuma yi taurari.17Allah ya shirya su a sama domin su bada haske ga duniya,18su kuma yi mulki kan yini da kuma dare, su kuma raba tsakanin haske da duhu. Allah kuma ya ga yana da kyau.19Wannan ce safiya da yammaci, rana ta huɗu.
20Allah yace, "Ruwaye su kasance da manyan halittu masu rai, ya kuma bar tsuntsaye suyi ta firiya a saman duniya a sararin sama."21Allah ya hallici manyan hallittu na tekuna, da kuma sauran halittu kowanne bisa ga irinsa, da masu tafiya da kuma waɗanda suka cika ruwaye a ko'ina, da kuma dukkan tsuntsaye masu fukafukai, kowanne bisa ga irinsa. Allah kuma ya ga yana da kyau.
22Allah ya albarkace su, cewa, "Ku ruɓanɓanya, ku hayayyafa, ku cika ruwaye a cikin tekuna. Ya ce tsuntsaye su ruɓanɓanya a duniya."23Wannan ne asubahi da yammaci, rana ta biyar.
24Allah yace, "Ƙasa ta bada hallittu masu rai, kowanne bisa ga irinsa, dabbobin gida, masu rarrafe dana daji kowanne bisa ga irinsa." Haka kuma ya kasance.25Allah kuma ya yi dabbobin duniya kowanne bisa ga irinsu, dabbobin gida kowanne bisa ga irinsa da duk masu jan jiki a ƙasa kowanne bisa ga irinsa. Ya kuma ga suna da kyau.
26Allah yace "Bari muyi mutum cikin kamanninmu, bisa surarmu. Su yi mulkin kifaye na tekuna, da tsuntsayen sararin sama, da dabbobi, da kuma dukkan duniya, da dukkan abu mai rarrafe a bisa duniya."27Allah ya hallici mutum cikin kamanninsa. Cikin kamanninsa ya hallice shi. Mace da namiji ya hallice su.
28Allah ya albarkace su ya ce da su,"Ku hayayyafa ku kuma ruɓaɓɓanya. Ku cika duniya ku nome ta. Kuyi mulkin kifaye na tekuna da tsuntsayen sama, da kuma duk abu mai rai dake tafiya bisa duniya."29Allah yace, "Duba na baka kowanne tsiro dake bada iri wanda yake a fuskar duniya, da dukkan bishiyoyi dake da iri a cikinsu. za su zama abinci a gare ku.
30Ga kowacce dabba ta duniya, da kuma dukkan tsuntsaye na sammai, da kowanne abu mai rarrafe a doron duniya, da kuma dukkan halittu masu numfashin rai na baku kowanne irin koren ganye domin abinci." Haka kuma ya kasance.31Allah kuma ya ga dukkan abin da ya halitta na da kyau. Wannan ne asubahi da yammaci, rana ta shida.

2

1To an kammala sammai da duniya, da duk abubuwa masu rai da suka cika su.2A rana ta bakwai Allah ya kammala aikinsa da ya yi, domin haka sai ya huta a rana ta bakwai daga dukkan aikinsa.3Allah ya albarkaci rana ta bakwai ya kuma tsarkaketa, domin a cikinta ya huta daga dukkan aikinsa na halitta da ya yi.

4Waɗannan sune al'amuran da suka shafi sammai da duniya, a lokacin da aka hallice su, a ranar da Yahweh ya yi sammai da duniya.5Ba wani filin daji kuma a duniya, ba tsire-tsire kuma a cikin filaye, domin Yahweh bai sa a yi ruwa ba tukuna a duniya, kuma ba mutumin da zai nome ƙasa.6Amma raɓa ta sauka a ƙasa ta jiƙe dukkan ƙasar.
7Yahweh Allah ya halitta mutum daga cikin ƙasa, ya kuma hura masa numfashin rai a cikin kafafen hancinsa, sai mutum ya zama rayayyen taliki.8Yahweh ya yi lambun itatuwa a bangon gabas a cikin Aidan, a can ya sa mutumin daya halitta.
9Daga cikin ƙasa Yahweh Allah ya sa ko waɗanne irin itatuwa masu ƙayatarwa da abinci su tsiro. Wannan ya haɗa da itacen rai wanda ke a tsakiyar gonar, da kuma itacen sanin nagarta da mugunta.10Rafi ya bi ta tsakiyar lambun Aidan domin ya jiƙa lambun. Daga can ne ya rabu ya zama rafuka huɗu.
11Sunan na farko shi ne Fishon. Shi ne wanda ya malala a dukkan ƙasar Habila, inda akwai zinariya. Zinariyar wannan ƙasar tana da kyau.12Akwai kuma itatuwa masu ƙamshi da kyawawan duwatsu.
13Sunan rafi na biyun shi ne Gishon. Wannan shi ne wanda ya malala zuwa Kush.14Sunan rafi na ukun shi ne Tigris, wanda ya malala gabashin Asshur. Rafi na huɗu shi ne Yufaretis.
15Yahweh Allah ya ɗauki mutumin ya sa shi a lambun Aidin domin ya nome shi ya kula da shi.16Yahweh Allah ya umarci mutumin, da cewa, "Daga kowanne irin 'ya'yan itace na cikin lambun kana da 'yancin ci.17Amma ba za ka ci daga cikin itace na sanin nagarta da mugunta ba, domin ranar daka ci daga cikinsa, tabbas za ka mutu."
18Yahweh Allah yace, "ba shi da kyau mutumin ya zauna shi kaɗai. Zan yi masa mataimakiyar da ta dace da shi."19Daga cikin ƙasa ne Yahweh Allah ya siffatta kowacce irin dabba ta saura da kuma tsuntsun sararin sama. Sai ya kawo su wurin mutumin domin ya ga yadda zai kira su. Duk abin da mutumin ya kira kowacce halitta sunanta kenan.20Mutumin ya ba dukkan dabbobi suna da kuma dukkan tsuntsayen sararin sama. Amma ga mutumin ba a sami mataimakin da ya dace da shi ba.
21Yahweh Allah ya sa barci mai nauyi ya kwashe mutumin domin haka mutumin ya yi barci. Yahweh Allah ya cire ɗaya daga cikin haƙarƙarinsa ya yi mace ya kuma kawo ta ga mutumin22Da haƙarƙarin da Yahweh ya ciro daga jikin mutumin, ya yi mace da shi ya kuma kawo ta ga mutumin.23Sai mutumin yace, "A wannan lokacin, wannan ƙashi ne na ƙasusuwana, tsoka ce daga tsokata. Za a kira ta 'mace,' saboda daga jikin mutum aka ciro ta."
24Domin haka mutum zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, zai zama haɗe da matarsa, kuma za su zama jiki ɗaya.25Dukkan su biyu tsirara suke, mijin da matar, amma ba su jin kunya.

3

1To maciji ya fi dukkan sauran dabbobin saura da Yahweh yayi wayau. Sai ya ce da macen, "Ko da gaske ne Allah yace ba zaku taɓa ci daga kowanne 'ya'yan itacen dake cikin lambun ba?"2Sai matar ta ce da macijin, "Ma iya ci daga cikin itatuwan lambun,3amma game da itacen dake tsakiyar lambun, Allah yace, 'Ba zaku ci shi ba, ba kuma zaku taɓa shi ba, in ba haka ba, zaku mutu."'

4Sai maciji yace da macen, "Hakika ba zaku mutu ba.5Domin Allah ya san cewa a ranar da kuka ci idanunku zasu buɗe, zaku kuma zama kamar Allah, kuna sanin nagarta da mugunta."6Da matar ta duba ta ga itacen yana da kyau domin abinci, yana kuma ƙayatar da idanu, kuma itacen abin marmari ne yana sa mutum ya zama mai hikima, sai ta tsinki waɗansu daga cikin 'ya'yan ta ci shi. Sai ta bada waɗansu ga mijinta, shi kuma ya ci.
7Idanun dukkan su biyun suka buɗe, sai suka gane tsirara su ke. Sai suka ɗinka ganyayyakin ɓaure suka yi wa kansu sutura.8Sai suka ji motsin Yahweh Allah ya na tafiya cikin lambun da sanyin yamma, domin haka mijin da matar suka ɓuya a cikin itatuwan lambun daga fuskar Yahweh Allah.
9Sai Yahweh Allah ya kira mutumin yace da shi, "Ina ka ke?"10Mutumin yace "Na ji ka a cikin lambun, na kuma ji tsoro, domin tsirara na ke. Domin haka na ɓoye kaina."11Allah yace, "Wane ne ya faɗa maka cewa tsirara ka ke? Ko ka ci 'ya'yan itacen da na dokace ka kada ka ci daga cikinsa ne?"
12Sai mutumin yace, "Macen daka ba ni ta kasance tare da ni, ta ba ni 'ya'yan itacen, na kuwa ci shi."13Yahweh Allah yace da matar, "Me ki ka yi kenan?" Sai macen ta ce, "Maciji ne ya yi mini ƙarya, na kuwa ci."
14Yahweh Allah yace da maciji, "Saboda ka yi wannan, kai kaɗai ne la'ananne a cikin dukkan dabbobin saura da dukkan dabbobin sama. A kan cikinka za ka yi tafiya, kuma ƙasa za ka ci dukkan kwanakin ranka.15Zan sa magaftaka tsakaninka da matar, da kuma tsakanin zuriyarka da zuriyarta. Zai ƙuje kanka, kai kuma za ka ƙuje diddigensa."
16Ga macen yace, "Zan ninka shan wuyarki sosai a samun 'ya'ya; a cikin shan wuya za ki haifi 'ya'ya. Duk marmarinki zai zama domin mijinki, amma zai yi mulkin ki."
17Ga Adamu yace, "Domin ka saurari muryar matarka, ka ci daga cikin itacen da na dokace ka cewa, 'Kada ka ci daga cikinsa,' saboda kai na la'anta ƙasa; ta wurin aiki mai zafi za ka ci daga cikinta dukkan kwanakin ranka.18Za ta fitar da ƙaya da sarƙaƙƙiya domin ka, za ka kuma ci tsire-tsiren ƙasar.19Ta wurin zufarka za ka ci gurasa, har sai randa ka koma turɓaya, domin daga cikinta aka ciro ka. Domin kai ƙura ne, ƙura kuma za ka koma."
20Mutumin ya kira sunan matarsa Hauwa ita ce mahaifiyar dukkan rayayyu.21Yahweh Allah ya yi wa Adamu da matarsa sutura ta fatu ya rufe su.
22Yahweh Allah yace, "Yanzu mutumin ya zama kamar ɗaya daga cikinmu, yana sane da mugunta da nagarta. To yanzu ba za mu taɓa barinsa ya sa hannunsa, ya tsinka daga itacen rai ba, ya ci, ya kuma rayu har abada."23Saboda haka Yahweh Allah ya fitar da shi daga cikin lambun Aidin, domin ya noma ƙasa wanda daga ita aka ciro shi.24To sai Allah ya kori mutumin daga lambun, ya sa kerubim a gabashin lambun Aidin da kuma takobi mai walƙiya dake jujjuyawa ta kowanne fanni, domin su yi tsaron hanya ta zuwa itacen rai.

4

1Mutumin ya kwana da matarsa, sai ta yi ciki ta haifi Kayinu. Ta ce,"Na haifi mutum da taimakon Yahweh."2Sai ta sake haifar ɗan'uwansa Habila. Sai Habila ya zama makiyayi, amma Kayinu ya zama manomi.

3Sai ya zamana wata rana Kayinu ya kawo wani sashe daga cikin amfanin gonar da ya noma daga ƙasa a matsayin baiko ga Yahweh.4Shi kuma Habila, sai ya kawo waɗansu 'ya'yan fari daga cikin garkensa da kuma sashe na kitse. Yahweh ya karɓi Habila da baikonsa,5amma Kayinu da baikonsa bai karɓa ba. Domin haka Kayinu ya fusata sosai, ya kuma ɓata fuska.
6Yahweh yace da Kayinu, "Meyasa ka yi fushi meyasa fuskarka ta ɓaci haka?7In da ka yi abin dake nagari, da ba a karɓe ka ba? Amma in ba ka yi abin dake nagari ba, zunubi na ƙwanƙwasa ƙofa kuma marmarinsa shi ne ya mallake ka, amma dole ne ka yi mulkinsa."
8Sai Kayinu ya yi magana da ɗan'uwansa Habila. Sai ya zamana a lokacin da suke cikin saura, sai Kayinu ya tasar wa Habila ya kashe shi.9Daga nan Yahweh yace da Kayinu, "Ina ɗan'uwanka Habila?" Ya ce, "Ban sani ba. Ni makiyayin ɗan'uwana ne?"
10Yahweh yace, "Me ka yi kenan? Jinin ɗan'uwanka yana kira na daga ƙasa.11Yanzu kai la'ananne ne daga ƙasar da ta buɗe baki ta karɓi jinin ɗan'uwanka daga hannunka.12Daga yanzu duk lokacin daka noma ƙasa, ba za ta baka issashen amfaninta ba. Za ka zama mai yawo barkatai a cikin duniya."
13Kayinu yace da Yahweh, "Horona ya yi girma fiye da yadda zan iya ɗauka.14Hakika ka kore ni waje yau daga wannan ƙasa, zan kuma riƙa ɓuya daga fuskarka. Zan zama mai yawo barkatai a cikin duniya, kuma duk wanda ya same ni zai kashe ni."15Yahweh yace da shi, In har wani ya kashe Kayinu za ayi masa ramako har niki bakwai." Daga nan Yahweh ya sa alama a jikin Kayinu, domin in wani ya gan shi kada wannan mutumin ya kai masa hari.
16Sai Kayinu ya tafi daga fuskar Yahweh ya zauna a ƙasar Nod, a gabashin Aidin.17Kayinu ya kwana da matarsa sai ta yi ciki ta haifi Enok. Ya gina birni ya bashi sunan ɗansa Enok.
18Ga Enok sai aka haifa masa Irad. Irad ya zama mahaifin Mehuyawel. Mehuyawel ya zama mahaifin Metushawel. Metushawel ya zama mahaifin19Lamek. Lamek ya aura wa kansa mata biyu: sunan ɗayar Ada, ɗayar kuma sunanta Zilla.
20Ada ta haifi Yabal. Shi ne mahaifin masu zama a cikin rumfuna waɗanda ke da dabbobi.21Ɗan'uwansa shi ne Yubal. Shi ne mahaifin makaɗan molo da algaita.22Ita kuma Zilla, ta haifi Tubal Kayinu, shi ne mai samar da kayayyaki na jan ƙarfe. 'Yar'uwar Tubal Kayinu ita ce Na'ama.
23Sai Lamek yace da matansa, Ada da Zilla, ku saurari muryata; ku matan Lamek, ku saurari abin da na ce. Domin na kashe mutum saboda ya yi mani rauni, saurayi domin ya ƙuje ni.24In an saka wa Kayinu sau bakwai, to za a saka wa Lamek sau saba'in."
25Sai Adamu ya sake kwana da matarsa, sai ta sake haifar wani ɗan. Sai ta kira sunansa Set, ta kuma ce, "Allah ya bani wani ɗan a madadin Habila, domin Kayinu ya kashe shi."26Aka haifa wa Set ɗa, sai ya kira sunansa Enosh. A wancan lokacin ne mutane suka fara kiran bisa sunan Yahweh.

5

1Wannan shi ne lissafin zuriyar Adamu. A ranar da Allah ya hallici mutum, ya yi su a cikin kamanninsa.2Namiji da mace ya hallice su. Ya albarkace su ya basu suna mutane a lokacin da ya hallice su.

3Da Adamu ya yi shekaru130 sai ya zama mahaifin ɗa a cikin kamanninsa sai ya kira sunansa Set.4Bayan Adamu ya haifi Set, ya yi rayuwa tsawon shekaru ɗari takwas. Sai ya zama mahaifin waɗansu 'ya'ya maza da mata masu yawa.5Adamu ya yi rayuwa har shekaru 930 daga nan ya mutu.
6Da Set ya yi shekaru 105, sai ya haifi Enosh.7Bayan ya haifi Enosh, ya rayu har tsawon shekaru 807 ya zama mahaifin 'ya'ya maza da mata da yawa.8Set ya rayu har shekaru 912 daga nan ya mutu.
9Bayan Enosh ya rayu na tsawon shekaru tasa'in, sai ya haifi Kenan.10Bayan ya haifi Kenan, Enosh ya rayu na tsawon shekaru 815. Sai ya haifi waɗansu 'ya'ya maza da mata masu yawa.11Enosh ya rayu tsawon shekaru 905 daga nan ya mutu.
12Da Kenan ya yi shekaru saba'in, sai ya haifi Mahalalel.13Bayan ya haifi Mahalalel, Kenan ya yi shekaru 840. Sai ya haifi sauran waɗansu 'ya'ya maza da mata.14Kenan ya rayu na tsawon shekaru 910, daga nan ya mutu.
15Mahalalel ya rayu shekaru sittin da biyar, sai ya haifi Yared,16Mahalalel yana da shekaru 830. Sai ya haifi sauran 'ya'ya maza da mata masu yawa.17Mahalalel ya rayu na tsawon shekaru 895, daga nan ya mutu.
18Da Yared ya yi shekaru 162, sai ya haifi Enok.19Bayan ya haifi Enok, Yared ya yi shekaru ɗari takwas. Sai ya haifi waɗansu 'ya'ya maza da mata.20Yared ya rayu na tsawon shekaru 962, daga nan ya mutu.
21Da Enok ya yi shekaru sittin da biyar, sai ya haifi Metusela.22Enok ya yi tafiya tare da Allah shekaru ɗari uku daga nan ya haifi Metusela, ya kuma haifi waɗansu 'ya'ya maza da mata.23Enok ya yi shekaru ɗari uku da sittin da biyar.24Enok ya yi tafiya tare da Allah, daga bisani ya tafi, domin Allah ya fyauce shi.
25Da Metusela ya yi shekaru 187, ya haifi Lamek.26Bayan ya haifi Lamek, Metusela ya yi shekaru 782. Sai ya haifi waɗansu 'ya'ya maza da mata.27Metusela ya rayu na tsawon shekaru 965 daga nan ya mutu.
28Bayan ya yi shekaru182, sai ya haifi ɗa.29Sai ya kira sunansa Nuhu, yana cewa, "Wannan zai bamu hutu daga aikinmu daga kuma aikin hannuwanmu mai wuya, da zamu yi saboda Allah ya la'anta ƙasa."
30Lamek ya yi shekaru 595 daga nan ya haifi Nuhu. Daga nan ya haifi sauran 'ya'ya maza da mata.31Lamek ya rayu na tsawon shekaru 777, daga nan ya mutu.
32Bayan Nuhu ya yi shekaru ɗari biyar, sai ya haifi Shem, da Ham, da Yafet.

6

1Sai ya zamana da mutane suka fara ruɓamɓanya a duniya aka kuma haifa masu 'ya'ya mata,2sai 'ya'yan Allah suka ga 'ya'yan mutane na da ban sha'awa. Sai suka auri mata daga cikinsu, dukkan su da suka zaɓa.3Yahweh yace "Ruhuna ba zai dawwama a cikin mutum ba har abada, domin su jiki ne. Za su rayu shekaru 120 ne."

4A waɗancan kwanakin akwai ƙarfafan mutane sosai, kuma haka ya faru ne bayan 'ya'yan Allah sun auri 'ya'ya mata na mutane, sun kuma sami 'ya'ya tare da su. Waɗannan sune manyan mutanen dã can, mutane masu jaruntaka.
5Yahweh ya ga muguntar mutum ta haɓaka a duniya, kuma dukkan tunane-tunanen zuciyarsa kullum mugunta ce.6Yahweh ya yi takaicin halitar mutum a duniya, kuma abin ya dame shi a zuciyarsa.
7Domin haka Yahweh yace,"Zan shafe mutum wanda na halitta daga fuskar duniya; mutum da manyan dabbobi, da abubuwa masu rarrafe da tsuntsayen sammai, domin na yi takaici dana halicce su."8Amma Nuhu ya sami tagomashi a idanun Yahweh.
9Waɗannan sune abubuwa game da Nuhu. Nuhu adalin mutum ne, kuma ba shi da abin zargi a cikin mutanen kwanakinsa.10Nuhu yayi tafiya tare da Allah. Nuhu ya haifi 'ya'ya uku: Wato Shem da Ham da Yafet.
11Duniya ta ƙazanta a gaban Allah, ta kuma cika da hargitsi.12Allah ya ga duniya; duba, ta gurɓanta, domin dukkan mutane sun ɓata tafarkinsu a duniya.
13Allah yace da Nuhu, Na ga cewa lokacin ƙarshen dukkan hallita ya yi domin duniya ta cika da hargitsi ta wurin su, hakika, zan hallaka su tare da duniya.14Ka yi wa kanka jirgi da itacen sida ka yi ɗakuna a cikin jirgin, ka rufe shi ciki da waje.15Ga fasalin yadda zaka yi shi: tsawon jirgin kamu ɗari uku, faɗinsa kamu hamsin, bisansa kamu talatin.
16Ka yi wa jirgin rufi, ka kuma kammala shi ka dalaye shi daga sama har ƙasa. Ka sa ƙofa ta gefen jirgin, ka yi masa matakala, ƙarama, da ta biyu, da kuma matakala ta uku.17Ka saurara, Na kusa kawo ambaliyar ruwa a duniya domin in hallakar da dukkan masu rai dake da numfashi rai dake a ƙarƙashin sama. Duk abin dake a duniya zai mutu.
18Amma zan kafa alƙawarina da kai. Zaka shiga cikin jirgin, da kai da 'ya'yanka da matarka da matan 'ya'yanka tare da kai.19Da dukkan hallitu masu rai, kowanne iri biyu dole ne kuma ka shigar dasu cikin jirgin, ka ajiye su, su tsira tare da kai, dukkan su namiji da mace.
20Da tsuntsaye bisa ga irinsu, da manyan dabbobi bisa ga irinsu, dukkan wani abu mai rarrafe a ƙasa bisa ga irinsu, biyu daga cikin kowanne iri daga cikinsu za su zo tare da kai, domin ka tsirar da rayukansu21Ka kuma yi wa kanka tanadin kowanne irin abinci na ci ka adana shi, domin ya zamar maka abinci da kuma dominsu."22Sai Nuhu ya yi wannan. Bisa yadda Allah ya umarce shi, haka ya yi.

7

1Yahweh yace da Nuhu, "Ka zo, da kai da dukkan gidanka, zuwa cikin jirgin, domin na ga kai mai adalci ne a gabana a wannan tsara.2Da dukkan dabbobi masu tsarki tare da kai, maza bakwai mata bakwai. Daga dukkan dabbobi marasa tsarki ka ɗauko biyu-biyu.3Hakanan daga tsuntsayen sararin sama, ka kawo maza bakwai da mata bakwai daga cikinsu, domin a tanadi irinsu a faɗin duniya.

4Domin a rana ta bakwai zan sa a yi ruwa a dukkan duniya har kwana arba'in dare da rana. Zan hallakar da dukkan masu rai dana halitta daga fuskar duniya"5Nuhu ya yi dukkan abin da Yahweh ya umarce shi.
6Nuhu yana da shekaru ɗari shida a lokacin da aka yi ruwan tsufana a duniya.7Da Nuhu, da 'ya'yansa maza, da matarsa, da matan 'ya'yansa maza suka shiga jirgin saboda ruwan tsufana.
8Dabbobi masu tsarki da tsuntsaye da duk abu mai rarrafe a ƙasa,9biyu-biyu, namiji da mace, suka zo wurin Nuhu suka shiga akwatin, kamar yadda Allah ya umarci Nuhu.10Sai ya zamana bayan kwanaki bakwai, ruwan tsufana ya sauko a duniya.
11A shekaru ɗari shida na Nuhu, a wata na biyu, a ranar sha bakwai ga wata, a dai wannan ranar, sai dukkan taskoki na zurfafa suka buɗe suka fashe, sakatun sama suka buɗe,12Ruwa ya fara sauka a duniya har kwanaki arba'in dare da rana.
13A wannan ranar dai Nuhu da 'ya'yansa, Shem da Ham da Yafet da matar Nuhu, da matan 'ya'yan Nuhu uku na tare da su, suka shiga jirgin.14Suka shiga tare da dukkan dabbobin jeji kowanne bisa ga irinsa, da kuma kowacce irin dabba ta gida bisa ga irinta, da kuma duk abu mai rarrafe da kowaɗanne irin tsuntsaye bisa ga irinsu, da dukkan wata hallitta mai fuka-fukai.
15Biyu daga dukkan hallitar dake da numfashin rai suka shiga jirgin tare da Nuhu.16Dabbobi da dukkan hallitun da suka shiga sun shiga ne kamar yadda Allah ya umarce shi. Sai Yahweh ya kulle ƙofar bayan sun shiga.
17Sai ruwan tsufana ya sauko a duniya kwanaki arba'in, ruwan kuma ya ƙaru ya ɗaga akwatin sama da ƙasa.18Ruwa ya rufe duniya gaba ɗaya jirgin kuma yana ta lilo a saman ruwa.
19Ruwa ya tumbatsa sosai a duniya har ya rufe dukkan duwatsu dake ƙarƙashin sama.20Ruwan ya kai har taki shida a bisa duwatsu
21Dukkan halittu dake motsi bisa duniya suka mutu; tsuntsaye, da dabbobin gida dana daji, dukkan dabbobi dake da yawa waɗanda ke duniya da kuma dukkan mutane.22Da dukkan hallitun dake bisa ƙasa, waɗanda ke da numfashin rai a hancinsu, suka mutu.
23Kowanne abu mai rai dake bisa duniya an shafe su, daga mutane ya zuwa manyan dabbobobi, da duk masu rarrafe, ya zuwa tsuntsayen sama. Dukkan su an hallakar da su daga duniya. Sai Nuhu da waɗanda ke tare da shi ne suka rage.24Ruwan bai janye daga ƙasa ba har kwanaki ɗari da hamsin.

8

1Sai Allah ya yi la'akari da Nuhu, da dukkan dabbobin jeji, da dukkan dabbobin gida dake tare da shi a cikin jirgin ruwan. Allah ya sa iska ta hura a kan ƙasa, sai ruwaye suka fara sauka ƙasa.2Maɓuɓɓugai na ƙarƙas da sakatun sama aka rufe su, ruwa kuma ya ɗauke.3Ambaliyar ruwa kuma ta kwanta sannu a hankali daga ƙasa, bayan kuma kwanaki ɗari da hamsin, sai ruwa ya yi ƙasa.

4Sai jirgin ruwan ya sami sauka a wata na bakwai, a ranar sha bakwai ga wannan watan, a kan duwatsun Ararat.5Ruwan ya ci gaba da sauka har wattanni goma. A rana ta farko ta watan, sai ƙonƙolin duwatsu suka bayyana.
6Sai ya zamana bayan kwanaki arba'in, sai Nuhu ya buɗe tagar jirgin ruwan da ya yi.7Ya aiki hankaka ya yi ta kai da komowa har sai da ruwa ya tsane daga duniya.
8Daga nan sai ya aiki kurciya ta ga yadda ruwan ya tsane daga ƙasa,9amma kurciyar ba ta sami wurin sauka ba, sai ta koma gare shi cikin jirgin ruwan, domin har ya zuwa lokacin ruwa na rufe da ƙasa baki ɗaya. Sai ya miƙa hannunsa ya kamo ta ya shigar da ita cikin jirgin ruwan tare da shi.
10Sai ya jira na tsawon ƙarin kwanaki bakwai, sa'an nan sai ya sake aiken kurciyar daga cikin jirgin ruwan.11Kurciyar ta koma wurinsa da yamma. Duba! a cikin bakinta ta tsinko sabon ganyen zaitun. Daga nan Nuhu ya san cewa ruwa ya janye daga ƙasa12Sai ya ƙara jira na waɗansu kwanaki bakwai, sai ya sake aiken kurciyar. Ba ta sake komawa wurinsa ba.
13Sai ya zamana a shekara ta ɗari shida a farkon shekara, a wata na farko, a ranar farko ta wata, sai dukkan ruwa ya bushe daga dukkan ƙasa. Nuhu ya buɗe rufin jirgin ruwan, ya dudduba ya ga ƙasa ta bushe.14A cikin wata na biyu, a ranar ashirin da bakwai ga wata, ƙasa ta bushe.
15Sai Allah yace da Nuhu,16"Ka fito daga cikin jirgin ruwan da kai da matarka da 'ya'yanka da matan 'ya'yanka tare da kai.17Ka kuma kwaso kowacce halitta mai rai dake tare da kai, da tsutsaye, da dabbobi da duk abin da ke rarrafe a doron ƙasa - domin su hayayyafa, su zama babbar runduna ta masu rai a ko'ina a duniya, su hayayyafa, su ruɓamɓanya a cikin duniya."
18Sai Nuhu ya fita tare da 'ya'yansa, da matarsa da matan 'ya'yansa.19Da kowacce irin hallitta dake tare da shi da dukkan masu rarrafe da dukkan tsuntsaye da duk wani abu mai motsi bisa duniya, bisa ga irinsu, suka fito daga cikin jirgin ruwan.
20Nuhu ya gina bagadi ga Yahweh. Ya ɗauki waɗansu daga cikin dabbobi masu tsarki da tsuntsaye masu tsarki ya miƙa hadaya ta ƙonawa da su akan bagadin.21Yahweh ya shaƙi ƙanshin hadayar sai ya ce a cikin zuciyarsa, "Ba zan sake la'anta ƙasa saboda mutum ba, koda yake nufe-nufen mutane a zukatansu mugunta ne tun daga yarantakarsu. Ba zan ƙara hallakar da duk masu rai ba kamar yadda na yi.22Muddin duniya tana nan, lokacin iri da lokacin girbi, sanyi, da zafi, bazara da damuna, dare da rana ba za su taɓa ƙarewa ba."

9

1Sai Allah ya albarkaci Nuhu da 'ya'yansa, ya ce da su, "Ku ruɓanɓanya ku hayayyafa, ku cika duniya.2Tsoronku da tsoratarwarku za ta zama a kan dukkan dabbobi masu rai dake duniya, da kowanne tsuntsu dake sararin sama, da duk wani abu dake motsi bisa ƙasa, da dukkan kifayen teku. An bada su a hannunka.

3Dukkan wani abu mai motsi dake rayuwa zai zama abinci a gare ku. Na baku koren ganyayyaki, yanzu na ba ku kowanne abu.4Amma ba za ku ci naman da jininsa da ransa ke cikinsa ba.
5Amma a bisa jininka, da ran dake cikin jininka, zan bukaci diyya. Daga dukkan dabbobi zan bukace ta. Daga hannun kowanne mutum, wato, mutumin da ya aikata kisan kai ga ɗan'uwansa,6zan bukaci bada lissafi na wannan mutum. Duk wanda ya zubar da jinin mutum ta wurin mutum za a zubar da jininsa, domin cikin kammanin Allah aka hallici mutum.7Ku kuma, ku hayayyafa, ku ruɓanɓanya, ku warwatsu a ko'ina a duniya, ku ruɓanɓanya a cikinta."
8Sai Allah ya yi magana da Nuhu da 'ya'yansa dake tare da shi cewa,9Amma, "Ka saurara! Zan tabbatar da alƙawarina da ku da zuriyarku dake biye da ku, da kuma10dukkan halittu masu rai dake tare da ku, da tsuntsaye, da dabbobin gida, da kowacce halitta ta duniya dake tare da ku, da kuma duk abin da ya fito daga cikin jirgin, da kuma dukkan halittu masu rai dake duniya.
11Na tabbatar da alƙawarina da ku, cewa ba zan ƙara hallakar da dukkan halittu da ruwa ba, ba za a sake yin ruwan da zai hallaka duniya ba."12Allah yace, "Wannan ce alamar alƙawarin da nake yi tsakanina da ku da dukkan halittun dake tare da ku, domin kuma dukkan tsararraki masu zuwa:13Na sa bakangizona a cikin girgije, zai kuma zama alamar alƙawarina da ku da kuma duniya.
14Zai kuma zamana a lokacin da na sauko da girgije a kan duniya aka kuma ga bakangizo a cikin girgijen,15to zan tuna da alƙawarina da ku da dukkan halitta mai rai. Ruwaye ba zasu ƙara zama abin hallakarwa ga mutane ba.
16Bakangizon zai kasance a cikin girgije, zan kuma gan shi, domin in tuna da alƙawarina madawwami, tsakanin Allah da dukkan halittu masu rai a duniya.17"Sai Allah yace da Nuhu, "Wannan ita ce alamar alƙawarin da na tabbatar tsakanina da dukkan masu rai na duniya."
18'Ya'ya maza na Nuhu da suka fito daga cikin jirgin sune Shem, Ham, da kuma Yafet. Ham shi ne mahaifin Kan'ana.19Waɗannan guda uku sune 'ya'yan Nuhu, daga waɗannan ne aka sami dukkan mutanen duniya.
20Nuhu ne ya fara zama manomi, ya kuma shuka garkar inabi.21Sai ya sha waɗansu 'ya'yan inabin, ya kuma bugu. Yana kwance a cikin rumfarsa tsirara.
22Sai Ham mahaifin Kan'ana, ya ga tsiraicin mahaifinsa, ya kuma faɗawa 'yan'uwansa guda biyu a waje.23Sai Shem da Yafet suka ɗauki mayafi suka ɗora a kafaɗunsu, suka tafi da baya suka rufe tsiraicin mahaifinsu. Fuskokinsu na fuskantar wani bangon, domin haka ba su ga tsiraicin mahaifinsu ba.
24Da Nuhu ya tashi daga mayensa, sai ya gane abin da ɗansa ƙarami ya yi masa.25Domin haka ya ce, "Kan'ana zai zama la'annanne. Ya zama baran barorin 'yan'uwansa."
26Hakan nan ya ce, "Yahweh Allah na Shem, ya zama da albarka, Kan'ana kuma ya zama baransa.27Allah ya faɗaɗa abin mulkin Yafet, ya kuma sa gidansa a cikin rumfunan Shem. Kan'ana kuma ya zama baransa."
28Bayan ruwan tsufana, Nuhu ya yi shekaru ɗari uku da hamsin.29Dukkan kwanakin Nuhu shekaru ɗari tara ne da hamsin, daga nan ya mutu.

10

1Waɗannan sune zuriyar 'ya'yan Nuhu maza, wato Shem da Ham da Yafet. An haifa masu 'ya'ya maza bayan ruwan tsufana.

2'Ya'yan Yafet maza sune Gomar, Magog, Madai, Yaban, Tubal, Meshek da Tiras.3'Ya'yan Gomar maza sune Ashkenaz, Rifhat da Togarma.4'Ya'yan Yaban maza sune Elisha, Tarshish, Kittim da Dodanim.5Daga waɗannan ƙasashe mutane suka watsu suka tafi ƙasashensu, kowanne da nasu harshe bisa ga kabilarsu, da kuma janhuriyunsu.
6'Ya'yan Ham maza sune Kush, Mizraim, Fut da Kan'ana.7"Ya'yan Kush maza sune Seba, Habila, Sabta, Ra'ama da Sabteka. 'Ya'ya maza na Ra'ama sune Sheba da Dedan.
8Kush ya zama maihaifin Nimrod, wanda shi ne ya fara mamaye duniya.9Shi riƙaƙƙen maharbi ne a fuskar Yahweh. Wannan ya sa ake cewa "Kamar Nimrod riƙaƙƙen maharbi a fuskar Yahweh."10Wurin mulkinsa na farko shi ne Babila, Erek, Akkad, da Kalne a ƙasar Shinar.
11Daga cikin ƙasar ya fita zuwa Assiriya ya gina Nineba da Rehobot Ir, Kala,12da Resen wadda take a tsakanin Nineba da Kalash. Ita babban birni ce.13Mizraim ya zama mahaifin Ludatiyawa, Anamitiyawa, da Lehabiteyawa, Naftuhitawa,14Fatrusitiyawa da Kasluhiyatawa (waɗanda daga cikinsu ne Filistiyawa suka fito) da kuma Kaftoriyawa.
15Kan'ana ya zama mahaifin Sidom, ɗansa na fari, da kuma Het,16har kuma da Yebusawa, Amoriyawa, Girgashiyawa,17Hibiyatawa, da Arkittawa, da Sinitawa,18da Arbaditiyawa, da Zemaritiyawa, Hammatiyawa. Bayan haka kabilar Kan'aniyawa ta yaɗu waje.
19Kan iyakar Kan'ana tana daga Sidon, wajen Gerar har zuwa Gaza da kuma kamar mutum zai yi wajen Sodom, da Gomara, Adma da Zeboyim, har zuwa Lasha.20Waɗannan sune 'ya'yan Ham bisa ga kabilarsu, da kuma harsunansu, a cikin ƙasarsu, da al'ummarsu.
21Hakanan an haifawa Shem 'ya'ya maza, babban ɗan'uwan Yafet. Shem shi ne kãkan dukkan mutanen Eber22'Ya'yan Shem maza sune Elam, Asshur, Arfakshad, Lud da kuma Aram.23'Ya'yan Aram maza kuwa sune Uz, Hul, Gezar, da Meshek.
24Arfakshad ya zama mahaifin Shela, Shela kuma ya haifi Eber.25Eber na da 'ya'ya biyu sunan ɗayan shi ne Feleg, domin a cikin kwanakinsa aka raba duniya. Ɗan'uwansa shi ne Yoktan.
26Yoktan ya zama mahaifin Almodad, Shelef, Hazamabi, Yerah,27Hadoram, Uzal, Diklah28Obal, Abimawel, Sheba,29Ofir, Habila, da Yobab. Duk waɗannan 'ya'ya maza ne na Yoktan.
30Iyakarsu ta kama daga Mesha, har ya zuwa hanyar Sefhar da tsauni na gabas.31Waɗannan sune 'ya'yan Shem maza, bisa ga kabilarsu da harsunansu, a cikin ƙasashensu, bisa ga al'ummarsu.
32Waɗannan sune kabilar 'ya'yan Nuhu, bisa ga ƙididdigar asali, ta hanyar janhuriyarsu. Daga waɗannan janhuroriyoyi suka rarrabu suka shiga ko'ina a duniya bayan ruwan tsufana.

11

1To dukkan duniya sun yi magana da harshe ɗaya, kalmominsu kuma ɗaya ne.2Da suka yi tafiya zuwa gabas a hayin filin Shinar suka zauna a can.

3Suka ce da juna, "Zo mu yi tubula mu gasa su sosai." Suka yi aiki da tubali a madadin dutse, katsi kuma a maimakon yunɓu,4"Suka ce, "Ku zo, mu gina wa kanmu birni da kuma hasumiya wadda tsawonta zai kai har sararin sama, kuma mu yi wa kanmu suna. In ba mu yi ba, za a warwatsu mu a fuskar duniya dukka."
5Sai Yahweh ya zo daga sama domin ya ga birnin da hasumiyar da zuriyar Adamu suka gina.6Yahweh yace "Duba su mutane ɗaya ne da harshe ɗaya, kuma sun fara yin wannan! Ba da jimawa ba zasu iya yin duk wani abin da suka yi niyya, ba abin da zai gagare su.7Zo, mu sauka mu rikirkitar da harshensu a can, domin kada su fahimci juna."
8Sai Yahweh ya warwatsa su daga can zuwa ko'ina a duniya, sai kuma suka dena ginin birnin.9Domin haka sunansa ya zama Babila, domin a can ne Yahweh ya rikirkitar da harsunan duniya baki ɗaya, kuma daga can ne Yahweh ya watsa mutane ko'ina a sararin duniya.
10Waɗannan sune zuriyar Shem, Shem na da shekaru ɗari, sai ya zama mahaifin Arfakshad shekaru biyu bayan ruwan tsufana.11Shem ya rayu har shekaru ɗari biyar bayan ya haifi Arfakshad. Hakanan ya haifi 'ya'ya maza da mata ma su yawa.
12Da Arkfashad ya yi shekaru talatin da biyar, sai zama mahaifin Shela.13Arkfashad ya rayu na tsawon shekaru 403 bayan ya haifi Shela. Hakanan ya haifi waɗansu sauran 'ya'ya maza da mata.
14Da Shelah ya kai shekaru talatin, ya haifi Ebar.15Shelah ya rayu har shekaru 403 bayan ya haifi Ebar. Hakanan ya haifi sauran waɗansu 'ya'ya maza da mata.
16Da Ebar ya yi shekaru talatin da huɗu sai ya haifi Felag.17Ebar ya yi shekaru 430 bayan ya haifi Felag, Hakanan ya haifi sauran waɗansu 'ya'ya maza da mata.
18Da Felag ya yi shekaru talatin, sai ya haifi Reu,19bayan Felag ya haifi Reu ya rayu har shekaru 209, ya kuma haifi sauran waɗansu 'ya'ya maza da mata.
20Da Reu ya kai shekaru 32 sai ya haifi Serug.21Reu ya yi shekaru 207 bayan ya haifi Serug. Hakanan ya haifi sauran waɗansu 'ya'ya maza da mata.
22Da Serug ya kai shekaru talatin sai ya haifi Nahor.23Bayan Serug ya haifi Nahor, ya rayu na tsawon shekaru ɗari biyu sai kuma ya haifi sauran waɗansu 'ya'ya maza da mata.
24Bayan Nahor ya rayu shekaru ashirin da tara, sai ya zama mahaifin Tera.25Nahor ya rayu shekaru 119 bayan ya haifi Tera. Hakanan ya zama mahaifin waɗansu 'ya'ya maza da mata.26Bayan Tera ya rayu na tsawon shekaru saba'in sai ya zama mahaifin Abram, da Nahor, da Haran.
27To waɗannan sune zuriyar Tera, Tera ya haifi Ibram, Nahor, Haran, Haran kuma ya haifi Lot.28Haran ya mutu a fuskar mahaifinsa Tera a ƙasar haihuwarsa, a Ur ta Kaldiyawa.
29Ibram da Nahor suka yi aure. Sunan matar Ibram Sarai matar Nahor kuma sunanta Milka, 'yar Haran wanda shi ne mahaifin Milka da Iskah.30To Sarai bakarariya ce; ba ta da ɗa.
31Tera ya ɗauki ɗansa, da Lot ɗan ɗansa Haran, da kuma surukarsa Sarai matar ɗansa Ibram, tare suka bar Ur ta Kaldiyawa, zuwa ƙasar Kan'ana. Amma suka zo Haran suka zauna a can.32Tera ya rayu shekaru 205 daga nan ya mutu a Haran.

12

1Sai Yahweh yace da Ibram "Ka tashi ka bar ƙasarka da danginka, da kuma ƙasar mahaifinka, zuwa ƙasar da zan nuna maka,2zan maishe ka babbar al'umma, zan albarkace ka in kuma sa sunanka ya yi girma, kuma za ka zama albarka.3Zan albarkaci duk wanda ya albarkace ka, zan kuma la'anta duk wanda ya tozarta ka. Ta wurin ka dukkan al'ummar duniya za ta sami albarka."

4To Ibram ya tafi, kamar yadda Yahweh ya faɗa masa ya yi, Lot kuma ya tafi tare da shi. Ibram yana da shekaru saba'in da biyar a lokacin da ya tafi ya bar Haran.5Ibram ya ɗauki matarsa Sarai, da Lot ɗan ɗan'uwansa da dukkan mallakarsu da suka tara, da kuma dukkan mutanen da suka samu a Haran. Suka tafi zuwa ƙasar Kan'ana, suka kuwa isa ƙasar Kan'ana.
6Ibram ya wuce ƙasar har zuwa Shekem, zuwa al'ul na Moreh. A wancan lokacin Kan'aniyawa na zaune a ƙasar.7Yahweh ya bayyana ga Ibram, ya ce, "Ga zuriyarka Zan ba da wannan ƙasa." Daga nan Ibram ya gina bagadi domin Yahweh, wanda ya bayyana a gare shi.
8Daga can ya tafi zuwa ƙasar duwatsu a gabashin Betal, inda ya kafa rumfarsa, ga Betal a yammaci, Ai kuwa a gabashi. A can ya kafa bagadi domin Yahweh, ya kuma yi kira bisa sunan Yahweh.9Daga nan Ibram ya ci gaba da tafiya, zuwa wajen Negeb.
10A kwai yunwa a cikin ƙasar, don haka Ibram ya gangara zuwa Masar ya zauna domin yunwar ta tsananta sosai a cikin ƙasar.11Da ya kusa shiga Masar sai ya ce da matarsa Sarai, "Duba na san ke mace ce kyakkyawa.12In Masarawa suka gan ki za su ce, 'Wannan matarsa ce; za su kuma kashe ni, amma za su bar ki da rai.13Ki ce ke 'yar'uwata ce, domin komai ya yi mani dai-dai saboda ke, don a bar ni in rayu saboda ke."
14Sai ya zamana bayan Ibram ya shiga cikin Masar, Masarawa suka ga cewa Sarai kyakkyawa ce.15'Ya'yan sarki suka gan ta, suka kuma yaba mata a gaban Fir'auna, sai aka ɗauki matar zuwa gidan sarki.16FIr'auna ya kyautatawa Ibram saboda ita, ya ba shi tumaki, takarkarai, da jakai maza da mata da bayi maza da mata da kuma raƙuma.
17Sai Yahweh ya bugi gidan Fir'auna da annoba mai zafi saboda Sarai matar Ibram.18Fir'auna ya kira Ibram ya ce da shi me kenan ka yi mini? Meyasa ba ka faɗa mini cewa ita matarka ba ce?19Meyasa ka ce ita 'yar'uwarka ce; don in ɗauke ta ta zama matata? To yanzu ga matarka nan. Ka ɗauke ta ku tafi."20Sai Fir'auna ya bada umarni game da shi daga nan suka sallame shi ya tafi, tare da matarsa da duk abin da yake da shi.

13

1Sai Ibram ya bar Masar ya tafi Negeb, shi da matarsa da duk abin da ya mallaka. Lot ya tafi tare da su.2Ibram ya wadata sosai ta fannin dabbobi da zinariya da azurfa.

3Ya ci gaba da tafiya daga Negeb har zuwa wurin da ya kafa rumfarsa a dã baya, tsakanin Betal da Ai.4Ya tafi har zuwa inda ya kafa rumfa a baya. A nan ya fara kiran sunan Yahweh.
5To Lot wanda ke tare da Ibram shi ma yana da garke da sauran bisashe da rumfuna.6Ƙasar kuma ta yi masu kaɗan, su da mallakarsu domin suna da mallaka da yawa, saboda haka ba su iya tsayawa a wuri ɗaya ba.7Hakanan akwai rashin jituwa tsakanin makiyayan dabbobin Ibram da kuma makiyayan dabbobin Lot. Feriziyawa da Kan'aniyawa ne ke zama a wannan ƙasar a wancan lokacin.
8Sai Ibram yace da Lot, "bai kamata a sami rashin jituwa tsakanina da kai ba, ko kuma tsakanin makiyayan dabbobina da makiyayan dabbobinka.9Fiye ma da haka mu dangi ne, duba ba fili ne nan gabanka ba? Ka zaɓi duk inda kake so, in ka zaɓi hagu, ni sai in zaɓi dama, in ka zaɓi dama ni sai in zaɓi hagu"
10Sai Lot ya duba yankin Yodan, ya kuma gan shi kore shar har zuwa yankin Zowar, kamar lambun Yahweh, kamar kuma ƙasar Masar. Haka yake kafin a hallaka Sodom da Gomora.11Sai Lot ya zaɓi wannan filin na Yodan ya tafi gabas, dangin suka rabu da juna.
12Ibram ya zauna a ƙasar Kan'ana Lot kuma ya zauna a biranen filin ƙasa. Ya kakkafa rumfunansa har zuwa Sodom,13To mutanen Sodom miyagu ne sosai, masu yi wa Yahweh zunubi ne.
14Yahweh yace da Ibram bayan Lot ya rabu da shi. "Duba daga inda kake tsayuwa zuwa arewa, kudu da gabas da yamma.15Dukkan wannan ƙasar da ka ke gani, na bada ita ga zuriyarka har abada.
16Zan haɓaka zuriyarka ta zama kamar turɓayar ƙasa, domin in har mutum zai iya ƙirga turɓayar ƙasa to zai iya ƙirga zuriyarka.17Tashi ka kewaya faɗin ƙasar da tsawonta, domin zan bada ita gare ka.18Sai Ibram ya tashi ya ɗauki rumfarsa ya je ya zauna kusa da itatuwan rimayen Mamre, wanda ke a Hebron. A can ya kafa bagadi domin Yahweh.

14

1Sai ya zamana a kwanakin Amrafel, sarkin Shinar, Ariyok sarkin El'asar, Kedorlaoma sarkin Elam, da Tidal sarkin Goyim,2suka kai yaƙi kan Bera sarkin Sodom, Birsha, sarkin Gomora, Shinab, sarkin Adma, Shemebar, Sarkin Zeboyim, da sarkin Bela (wato wanda ake kira Zowar).

3Waɗancan sarakuna na baya suka taru a kwarin Siddim (wanda kuma ake kira Tekun Gishiri).4Suka bautawa Kedorlawoma shekaru sha biyu, amma a shekara tasha uku suka yi tayawe.5A shekara ta sha huɗu kuma, da sarakunan dake tare da shi suka zo suka kawo hari kan Rafaim a Ashterot Karnaim, da Zuzim a Ham, na Emim a Shaba Kiriataim,6da Horitiyawa a ƙasar duwatsu ta Se'ir, har zuwa El Faran dake kusa da hamada.
7Daga nan sai suka juyo suka zo En Mishfat (wadda kuma ake kira Kadesh), suka cinye dukkan ƙasar Amelikawa, da kuma ta Amoriyawa waɗanda ke zama a Hazazon Tamar.8Daga nan sai sarkin Sodom, da sarkin Gomora, da sarkin Admah da sarkin Zeboim da sarkin Bela (da ake kira Zowar) suka je suka yi shirin yaƙi9găba da Kedorlawomar sarkin Elam, Tidal, sarkin Goim, Amrafel sarkin Shinar, Ariok, sarkin Ellasar; sarakuna huɗu găba da biyar.
10To kwarin Siddim ya cika da ramukan yaƙi, da sarakunan Sodom da Gomora suka gudu sai suka faɗa cikinsu a can. Waɗanda suka rage suka gudu kan duwatsu.11Domin haka maƙiya suka kwashe dukkan kayayyakin Sodom da Gomora suka tafi abin su12Da suka tafi, suka kame Lot, ɗan ɗan'uwan Ibram, wanda ke zama a Sodom tare da dukkan malakarsa.
13Wani da ya tsira ya zo ya gaya wa Ibram Ba'ibirane. Yana zama a gefen rimin Mamre Ba'amore, ɗan'uwan Eshkol da Aner, Waɗanda dukkansu abokan Ibram ne.14To da Ibram ya ji maƙiya sun kame ɗan'uwansa, sai ya jagoranci horarrun mazajensa guda 318 waɗanda aka haifa a gidansa ya bi su har zuwa Dan.
15Ya rarrraba mazajensa găba da su a wannan daren ya kai masu hari, ya bi su har zuwa Hoba wadda ta ke arewa da Damaskus.16Daga nan ya dawo da dukkan mallakar, ya kuma dawo da ɗan'uwansa Lot da duk kayansa, da mataye da sauran mutane.
17Bayan Ibram ya dawo daga yin nasara da Kedorlawoma da sarakunan dake tare da shi, sarkin Sodom ya tafi ya tare shi a kwarin Shabe (Wanda kuma ake kira Kwarin Sarki)18Melkizedek, sarkin Salem ya kawo gurasa da ruwan inabi. Shi firist ne na Allah Maɗaukaki.
19Ya albarkace shi cewa, Mai albarka ne Ibram ta wurin Allah Mafi Ɗaukaka, Mahallicin sama da duniya.20Albarka ta tabbata ga Allah Mafi Ɗaukaka, wanda ya bada maƙiyanka a hannunka." Sai Ibram ya ba shi kaso ɗaya bisa goma na komai.
21Sarkin Sodom yace da Ibram, "Ka bani mutane, ka ɗauki kayayyakin domin kanka.22"Ibram yace da sarkin Sodom, "Na ɗaga hannunna sama zuwa ga Yahweh, Allah Maɗaukaki, Mahallicin sama da duniya,23cewa ba zan ɗauki koda tsinkin zare ko takalmi ko dukkan wani abu dake naka ba, domin kada ka ce, 'Na sa Ibram ya azurta,'24Ba zan ɗauki komai ba sai abin da matasa samari suka ci da kuma rabon mazajen dake tare da ni. Let Aner, Eshkol, da Mamre su ɗauki nasu kason."

15

1Bayan waɗannan abubuwa sai maganar Yahweh ta zo wurin Ibram a wahayi, cewa, "Ibram kada ka ji tsoro ni ne garkuwarka da kuma babban ladanka."2Ibram yace, ya Ubangiji Yahweh, me za ka bani tunda yake har yanzu bani da ɗa. Magajin gidana kuma Eliyazar ne daga Damaskus,"3Ibram yace, da yake baka bani zuriya ba, duba, ɗan aikin gida ne ya zama magajina.

4Sai ga maganar Yahweh ta zo gare shi, cewa "Ba wannan mutumin ne zai gaje ka ba, amma wanda zai fito daga cikin jikinka ne zai zama magajinka."5Daga nan sai ya fito da shi waje ya ce, "Duba sama, ka kuma ƙidaya taurari, in za ka iya ƙirga su. Daga nan ya ce da shi, haka zuriyarka za ta zama."
6Ya yi imani da Yahweh, sai ya lisafta masa shi a matsayin adalci.7Ya ce da shi, "Ni ne Yahweh, wanda ya fito da kai daga Ur ta Kaldiyawa, domin in baka wannan ƙasar ka gãje ta."8Ya ce ya Ubangiji Yahweh, ta yaya zan sani cewa zan gãje ta?"
9Daga nan ya ce da shi, "Ka kawo mini bijimi ɗan shekara uku da kuma akuya 'yar shekara uku da kurciya, da tantabara."10Ya kawo masa dukkan waɗannan ya kuma datsa su biyu-biyu ya kuma ajiye kowanne tsagi a gefen ɗayan, amma bai raba tsuntsayen ba.11Lokacin da tsuntsayen dake yawo suka zo wurin mushen sai Ibram ya kore su.
12Daga nan bayan rana ta kusa faɗuwa, Ibram ya yi barci mai nauyi, sai ga wani babban duhu mai ban razana ya sha kan shi.13Daga nan Yahweh yace da Ibram, hakika ka san cewa zuriyarka zasu yi baƙunci a ƙasar da ba tasu ba, za a kuma bautar da su, a tsananta musu har tsawon shekaru ɗari huɗu.
14Zan hukunta waccan al'ummar da zasu bauta wa, bayan haka kuma zasu fita da mallaka mai yawa.15Amma za ka je wurin ubanninka da salama, kuma za a yi maka jana'iza a shekaru ma su kyau.16A cikin tsara ta huɗu zasu sake zuwa nan kuma, saboda muguntar Amoriyawa ba ta kai iyakarta ba tukuna."
17Da rana ta faɗi dare kuma ya yi, sai ga hayaƙin wuta da kuma harshen wutar tukunya da tartsatsi suka wuce a tsakanin yankin naman.18A wannan lokaci Yahweh ya yi yarjejeniya da Ibram cewa ga zuriyarka zan bada wannan ƙasa tun daga kogin Masar zuwa babban kogin Yuferetis-19da Kan'aniyawa da Kanizitawa20da Hitiyawa da Feriziyawa da Refatiyawa,21da Amoriyawa da Kan'aniyawa da Girgashiyawa da Yebusiyawa."

16

1To Sarai, matar Ibram, ba ta haifa masa 'ya'ya ba tukuna, amma tana da baiwa, mutumiyar Masar, sunanta Hajara.2To sai Sarai ta ce da Ibram, "Duba Yahweh ya hana mani 'ya'ya, ka je ka kwana da baiwata. Watakila na sami 'ya'ya ta wurinta." Ibram ya saurari muryar Sarai.3Bayan Ibram ya yi shekaru goma a Kan'ana ne Sarai ta miƙa baiwarta Hajara ga Ibram a matsayin mata.4Sai ya yi tarayya da Hajara ta kuwa yi juna biyu. Da taga ta yi juna biyu sai ta fara duban uwargijiyarta da reni.

5Daga nan Sarai ta ce da Ibram, "Wannan kuskuren a kaina saboda kai ne. Na bada baiwata gare ka, kuma bayan ta ga ta yi juna biyu, sai aka sayar da ni a idonta. Bari Ubangiji ya shari'anta tsakanina da kai."6Amma Ibram yace da Sarai, "Duba ita baiwarki ce, tana ƙarƙashin ikonki, ki yi mata abin da kike tunanin ya fi kyau," Sai Sarai ta takura mata sosai, sai ta gudu daga gare ta
7Sai mala'ikan Yahweh ya same ta a maɓulɓular ruwa a jeji, wannan maɓulɓular dake kan hanya zuwa Shur.8Ya ce da ita, Hajara baiwar Sarai daga ina ki ka zo kuma ina za ki? sai ta ce "ina gujewa uwargijiyata ne Sarai."
9Mala'ikan Yahweh yace da ita, "Ki koma wurin uwargiyarki, ki miƙa kai ga shugabancinta."10Sai mala'ikan Yahweh yace da ita, "Zan ruɓanɓaya zuriyarki sosai, domin su zama da yawa, su wuce ƙirge."
11Hakanan mala'ikan Yahweh yace da ita, Duba kina ɗauke da juna biyu na ɗa namiji, kuma za ki kira sunansa Isma'ila, saboda Yahweh ya ji ƙuncinki.12Zai zama jakin jeji, zai yi magaftaka da dukkan mutane, dukkan mutane kuma na gãba da shi, zai kuma zauna a ware da 'yan, uwansa."
13Sai ta bada wannan sunan ga Yahweh wanda ya yi magana da ita, "Kai Allah ne mai ganina," domin ta ce, "Ko zan ci gaba da gani, bayanda ya gan ni?"14Saboda haka ake kiran rijiyar Beyer Lahai Roi; tana nan tsakanin Kadesh da Bered.
15Hajara ta haifa wa Ibram ɗa namiji ta ba shi suna Isma'ila.16Ibram na da shekaru tamanin da shida a lokacin da Hajara ta haifi Isma'ila.

17

1Da Ibram ya kai shekaru tasa'in da tara, lokacin da Yahweh ya bayyana a gare shi ya kuma ce masa, "Ni ne Allah mai iko dukka. Ka yi tafiya a gabana ka zama da rashin laifi.2Daga nan zan cika alƙawarina tsakani na da kai, zan kuma kuma ruɓanɓanya ka sosai."

3Ibram ya sunkuyar da fuskarsa ƙasa sai Allah ya yi magana da shi cewa,4"Ni kam, duba, alƙawarina na tare da kai. Zaka zama uban al'ummai masu yawa.5Ba za a ƙara kiran sunanka Ibram ba, amma sunanka zai zama Ibrahim - domin na zaɓe ka ka zama uban al'ummai masu yawa.6Zan sa ka ruɓanɓanya sosai, daga cikinka kuma zan samar da al'ummai, daga cikinka kuma za a sami sarakuna.
7Zan kafa alƙawarina tsakanina da kai da kuma zuriyarka dake biye da kai, a dukkan tsararrakinsu domin alƙawari na har abada, in zama Allah a gare ka da kuma zuriyarka dake biye da kai.8Zan bada ƙasar da kake zama gare ka da kuma zuriyarka, dukkan ƙasar Kan'ana domin ta zama mallakarka ta har abada, zan kuma zama Allahnsu."
9Sai Allah yace wa Ibrahim, "Amma kai dole ka kiyaye alƙawarina, da kai da zuriyarka dake biye da kai a dukkan tsararrakinsu.10Wannan shi ne alƙawarina da dole zaka kiyaye, tsakanina da kai da dukkan tsararrakin dake biye da kai:11Dole ka yi wa kanka kaciya, kuma wannan nan zai zama alamar alƙawarina da kai.
12Kowanne ɗa namiji a cikinku da ya kai shekaru takwas, dole ne a yi masa kaciya, a dukkan tsararrakin mutanenka. Wannan ya haɗa da wanda aka haifa a gidanka, da kuma wanda aka saya da kuɗinka daga kowanne irin bãƙo wanda ba ya cikin zuriyarka.13Da wanda aka haifa maka da wanda ka saya dole ne ayi masa kaciya. Da haka alƙawarina zai kasance a jikinka domin zama alƙawari na har abada.14Duk wani namiji wanda ba shi da kaciya za a fitar da shi daga cikin mutanensa. Ya karya alƙawarina."
15Allah yace da Ibrahim, "Game da Sarai matarka kuma Kada ka ƙara kiranta Sarai. A maimakon Sarai za a kira sunanta Saratu.16Zan albarkace ta, kuma za ta zama uwar al'ummai. Sarakunan mutane za su fito daga cikinta."
17Daga nan sai Ibrahim ya sunkuyar da fuskarsa ƙasa ya yi dariya, a cikin zuciyarsa ya ce, "Ko za a haifa wa ɗan shekara ɗari ɗa? Ta yaya Saratu wadda ta kai shekaru tasa'in za ta iya haifar ɗa?"18Ibrahim yace da Allah, "Ah Isma'ila zai zauna tare da kai!"
19Allah yace, "A 'a, amma Saratu matarka za ta haifa maka ɗa, kuma za ka ba shi suna Ishaku. Zan kafa alƙawarina da shi wato alƙawari na har abada da zuriyarsa dake biye da shi.20Shi kuma Isma'ila na ji ka. Duba na sa masa albarka, zan kuma ruɓaɓɓanya shi zan wadata shi sosai. Zai zama uban kabilu goma sha biyu. Zan kuma mai da shi babbar al'umma.21Amma alƙawarina zan kafa shi da Ishaku, wanda Saratu za ta haifa maka baɗi war haka."
22Da ya gama yi masa magana, sai Allah ya rabu da Ibrahim.23Sai Ibrahim ya ɗauki Isma'ila ɗansa, da duk waɗanda aka haifa a cikin iyalinsa, da duk waɗanda ya saya da kuɗinsa da dukkan mazaje na mutanensa duk suka yi kaciya a rana ɗaya kamar yadda Allah ya faɗa masa.
24Ibrahim yana da shekaru tasa'in da tara lokacin da ya yi kaciya.25Ɗansa Isma'ila kuma yana da shekaru sha uku a lokacin da aka yi masa kaciya.26A wannan ranar aka yi wa Ibrahim da ishaku kaciya a rana ɗaya.27Aka yi masa kaciya tare da dukkan mazajensa, da waɗanda aka haifa masa da waɗanda ya saya da kuɗi daga bãƙi.

18

1Yahweh ya bayyana ga Ibrahim a gefen itatuwan rimi na Mamre a lokacin da yake zaune a ƙofar rumfa da tsakar rana.2Ya duba sama, sai ga mutane uku na tsaye kewaye da shi. Da ya gan su, sai ya ruga daga ga ƙofar rumfar domin ya gamu da su, ya sunkuya ƙasa.

3Ya ce, "Ubangiji, in na sami tagomashi a wurin ka, kada ka wuce ka rabu da bawanka.4Sai a kawo maku ɗan ruwa, ku wanke ƙafafu, ku kuma shaƙata a ƙarƙashin itace.5Sai in kawo maku abinci domin ku sami ƙarfi tun da kun zo wurin bawanku. "Suka amsa, Ka yi kamar yadda ka ce."
6Sai Ibrahim ya yi hanzari ya shiga rumfa wurin Saratu, ya ce, "Hanzarto ki samo awo uku na gãri ki cuɗa shi ki yi gurasa."7Sai Ibrahim ya ruga garke ya ɗauko ɗan maraƙi ƙosasshe ya ba bayinsa su yi sauri su gyara shi.8Ya ɗauki curin da madara da maraƙin da aka gyara ya kai musu ya tsaya a gefensu a lokacin da suke ci.
9Suka ce da shi, "Ina Saratu matarka?" Ya amsa, Ta na can, cikin rumfa,"10Ya ce, hakika zan komo wurinka baɗi war haka, kuma duba, Saratu matarka za ta sami ɗa." Saratu tana ji a bakin ƙofa cikin rumfa dake bayansa.
11To Ibrahim da Saratu sun tsufa, shekarunsu sun yi nisa sosai, Saratu kuma ta wuce lokacin da mata ke iya haifar 'ya'ya.12Domin haka Saratu ta yi wa kanta dariya, tana cewa da kanta, "Bayan na tsufa, shugabana kuma ya tsufa, ko zan sami wannan jin daɗin?"
13Yahweh yace da Ibrahim, "Meyasa Saratu ta yi dariya ta kuma ce, "Ko hakika zan iya haifar ɗa Yanzu dana tsufa"?14Ko akwai abin da ke da wuya ne ga Yahweh? A daidai lokacin dana sa, kamar war haka, zan komo wurinka a shekara mai zuwa Saratu za ta sami ɗa,"15Sai Saratu ta yi musu, ta ce "Ban yi dariya ba domin tana jin tsoro. Ya amsa mata ya ce, "A'a, kin yi dariya."
16Sai mutanen suka tashi suka tashi suka duba wajen Sodom. Sai Ibrahim ya tafi tare dasu ya raka su a kan hanyarsu.17Amma Yahweh yace "Ko zan ɓoye wa Ibrahim abin da zan aikata,18da yake Ibrahim zai zama babbar al'umma kuma dukkan al'umman duniya zasu sami albarka ta wurinsa?19Domin na zaɓe shi domin ya umarci 'ya'yansa da gidansa dake biye da shi domin su bi tafarkin Yahweh, su aikata adalci da aikin adalci, domin Yahweh ya cika abin da ya faɗa wa Ibrahim zai aikata a gare shi."
20Daga nan sai Yahweh yace, "Saboda kukan Sodom da Gomora ya yi yawa, kuma zunubinsu ya haɓaka,21Yanzu zan sauka in ga kukan da ake yi a kan su wanda ya zo gare ni, ko hakika sun aikata al'amarin. In ba haka ba zan sani."
22To sai mazajen suka juya daga can, suka nufi wajen Sodom, amma Ibrahim ya tsaya a gaban Yahweh.23Sai Ibrahim ya matso ya ce "Ko zaka share adalai tare da mugaye?
24In a ce za a sami adalai hamsin a cikin birnin. Ko zaka hallaka shi ba tare da la'akari da adalan nan hamsin ba dake can?25Ba zai yiwu ba ka yi haka wato ka kashe adalai tare da miyagu, domin a hori adalai kamar yadda aka hori miyagu. Ba zai yiwu ba mai hukunta duniya ya yi abin da ke dai-dai?"26Yahweh yace, "In na sami adalai hamsin a cikin birnin Sodom, to zan kuɓutar da dukkan birnin saboda su."
27Ibrahim ya amsa ya ce, "Duba na jawo wa kaina magana da Ubangijina, koda yake ni ƙura ne kawai da toka!28To in ace adalan sun gaza hamsin ba mutum biyar? Zaka hallaka birnin saboda rashin biyar?" Daga nan sai ya ce, "Ba zan hallaka shi ba, in na sami mutane arba'in da biyar."
29Sai ya sake yi masa magana, ya ce "To a ce za a sami arba'in a can fa?" Ya amsa, "Saboda mutane arba'in ɗin ba zan yi ba."30"Ya ce, "Har yanzu dai ina roƙo Ubangiji kada ka yi fushi in na yi magana. To in a ce za a sami talatin a can fa." Ya amsa ba zai yi hakan ba, in a kwai mutane talatin a can."31Ya ce "Ga shi na dage in yi magana da Ubangijina! In a ce za a sami ashirin a can fa." Ya amsa "Saboda mutane ashirin ɗin ba zan hallakar da shi ba."
32Ya ce, "Ina roƙo kada ka yi fushi, Ubangiji, zan sake faɗin wannan karo na ƙarshe. In a ce za a sami goma fa a can." Sai ya ce, "Ba zan hallaka shi ba saboda mutane goman nan."33Sai Yahweh ya tafi a lokacin da ya gama yin magana da Ibrahim, shi kuma Ibrahim ya koma gida.

19

1Mala'ikun guda biyu suka zo Sodom da yamma, a lokacin da Lot ke zaune a ƙofar Sodom. Da Lot ya gan su sai ya tashi ya tare su, ya sunkuyar da fuskarsa har ƙasa.2"Ya ce, "Ya shugabannina, ina roƙon ku daku biyo ta gidan baranku, ku kwana ku wanke ƙafafunku. Da safe sai ku tashi ku yi tafiyarku." Suka amsa, "A'a za mu je mu kwana a kwararo."3Amma ya yi ta roƙon su, sai suka tafi tare da shi, suka shiga gidansa. Ya shirya musu abinci ya kuma soya musu gurasa marar gami suka ci.

4Amma kafin su kwanta, mazajen birnin, wato mazajen Sodom, suka kewaye gidan, da tsofaffinsu da matasansu, da dukkan mazajen birnin.5Suka kira Lot, suka ce da shi, "Ina mutanen da suka zo gidanka yanzu? Fito da su gare mu, domin mu kwana da su."
6To sai Lot ya fita wajen ƙofa ya kulle ƙofar a bayansa.7Ya ce da su, "Ina roƙon ku 'yan'uwana, kada ku yi aikin mugunta irin wannan.8Duba ina da 'ya'ya mata guda biyu da ba su taɓa kwana da maza ba. Ina roƙon ku in kawo muku su, ku yi duk abin da kuka so da su. Amma kada ku yi wa mazajen nan komai, domin suna nan ne a ƙarƙashin kulawata
9Suka ce, "Ka tsaya can!" Haka kuma suka ce, "Shi da ya zo baƙunta, yanzu kuma ya zama alƙalinmu! Yanzu za mu ci mutuncika fiye da yadda za mu yi musu." Suka matsa wa Lot da kuma mutanen, suka zo kusa da ƙofar domin su ɓarke ta.
10Amma sai mutanen suka miƙa hannuwansu suka shigo da Lot ciki suka kulle ƙofar.11Sai bãƙin na Lot suka bugi mutanen da makanta, wato mutanen dake wajen ƙofar gidan, duk da matasansu da tsofaffinsu duk ƙarfinsu ya ƙare a lokacin da suke ƙoƙarin ɓarke ƙofar
12Sai mutanen suka ce da Lot, "Ko kana da wani naka a nan? Ko surukai, ko 'ya'ya maza da mata da duk wanda kake da shi a cikin birnin, ka fitar da su daga birnin nan.13Domin mu na gab da hallaka wannan wurin, saboda zargin da ake yi wa birnin a gaban Yahweh ya yi yawa shi ya sa ya aiko mu domin mu hallaka shi."
14Sai Lot ya tafi ya yi magana da surukansa, wato mazajen da suka yi alƙawari zasu auri 'ya'yansa mata, ya ce "Ku hanzarta, ku fita daga wannan wurin, domin Yahweh na gab da hallaka birnin." Amma surukansa suka ɗauka wasa yake yi.15Da safiya ta yi, mala'ikun suka hanzarta Lot, "Ka fito da kai da matarka da 'ya'yanka mata guda biyu dake a wannan wuri, domin kada a share ku tare a cikin wannan hukunci na birni."
16Amma ya yi jinkiri. Sai mazajen suka kama hannuwansa, da hannun matarsa, da hannuwan 'ya'yansa mata guda biyu, saboda Yahweh ya yi masa jinƙai. Suka fitar dasu bayan birnin.17Da suka fitar dasu waje, ɗaya daga cikin mazajen ya ce, "Ku tserar da rayukanku! Kada ku waiga baya, ko kuma ku tsaya a wannan filin. Ku gudu kan duwatsu domin kada a hallakar da ku."
18Lot yace da su, "A'a shugabannina ina roƙon ku!19Baranku ya sami tagomashi a wurinku, kuma kun nuna mini kirki sosai da kuka ceci raina, amma ba zan iya kai wa kan duwatsu ba, masifar za ta same ni, kuma zan mutu.20Duba ga wani birni can, ya isa in je can domin tsira, kuma ƙarami ne, ina roƙo ku bar ni in je can in tsira (ba ɗan ƙarami ba ne?), rayuwata kuma za ta cetu."
21Ya ce da shi, "Shikenan, na biya maka wannan buƙata, kuma ba zan hallaka birnin da ka faɗa ba.22Ka yi hanzari ka gudu can, domin ba zan yi wani abu ba sai ka isa can." Shi ya sa ake kiran wurin Zowar.
23Rana ta ɗaga bisa duniya a lokacin da Lot ya isa Zowar.24Sai Yahweh ya saukar da ruwan wuta da matsanancin zafi bisa Sodom da Gomora.25Ya hallaka waɗannan biranen, da filayen, da duk mazauna biranen da tsire-tsire da suka yi girma a ƙasa.
26Amma matar Lot dake bayansa, ta waiwaya baya, sai ta zama umudin gishiri. Ibrahim ya tashi da sassafe ya je wurin da ya tsaya tare da Yahweh.27Ya duba wajen Sodom da Gomora da kuma dukkan filayen.28Da ya duba sai ya ga hayaƙi na tashi daga filin kamar na hayaƙin matoya.
29To lokacin da Allah ya hallakar da biranen da filayen, Allah ya tuna da Ibrahim Ya fitar da Lot daga wannan hallakarwar a lokacin da ya hallaka biranen da Lot ya zauna.
30Amma Lot ya fita daga Zowar zuwa duwatsu tare da 'ya'yansa mata guda biyu, domin yana jin tsoron zama a Zowar. Sai ya zauna a cikin kogon dutse, shi da 'ya'yansa mata guda biyu.
31Babbar ta ce da ƙaramar, "Mahaifinmu ya tsufa, kuma babu wanda zai kwana damu bisa ga tsarin dukkan duniya.32Ki zo, mu sa mahaifinmu ya sha ruwan inabi ya bugu, sai mu kwana da shi, domin mu wanzar da sunan mahaifinmu."33Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi ya bugu a wannan daren. Sai babbar ta je ta kwana da mahaifinta, bai ma san lokacin da ta kwanta ba, bai kuma san lokacin da tashi ba.
34Washegari Sai babbar ta ce da ƙaramar, "Kin ga, jiya na kwana da mahaifina. Yau kuma sai mu sa shi ya sake buguwa da ruwan inabi, ke kuma sai ki je ki kwana da shi, domin mu wanzar da sunan mahaifinmu."35Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi ya bugu, sai ƙaramar ta je ta kwana da shi. Bai san lokacin da ta kwanta ba haka kuma bai san lokacin da ta tashi ba.
36Ta haka 'ya'yan Lot guda biyu suka yi juna biyu ta wurin mahaifinsu.37Ta farin ta haifi ɗa namji ta sa masa suna Mowab. Shi ne ya zama uban Mowabawa a yau.38Ita ma ƙaramar 'yar ta haifi ɗa namiji sai ta ba shi suna Ben Ammi. Shi ne ya zama uban mutanen Ammon na yau.

20

1Ibrahim ya bar wurin ya gangara zuwa Negeb, ya zauna tsakanin Kadesh da Shur. Shi baƙo ne mazaunin Gerar.2Ibrahim yace game kuma da Saratu matarsa, "Ita 'yar'uwata ce" Sai Abimelek sarkin Gerar ya aika mazajensa suka ɗauko Saratu.3Amma Allah ya zo wurin Abimelek a mafarki da duhu, ya ce da shi, "Duba kai mataccen mutum ne saboda matar daka ɗauko, domin ita matar mutumin ce."

4Abimelek kuma bai kusance ta ba ya ce, "Ubangiji ko zaka kashe har ma al'umma mai adalci? Ashe ba shi da kansa ne ya ce da ni 'ita 'yar'uwataba ce?'5Har ma ita da kanta ta faɗa, cewa 'Shi ɗan'uwana ne.' Na yi wannan bisa nagartar zuciyata, da kuma rashin laifofin hannuwana."
6Sai Allah yace da shi a cikin mafarki, I nima na sani ka yi haka ne bisa ga nagartar zuciyarka, Ni ma kuma na hana ka yi mini zunubi. Saboda haka ne ban bar ka ka taɓa ta ba.7Saboda haka ka mayar wa mutumin matarsa domin shi annabi ne. Zai yi maka addu'a kuma za ka rayu. Amma in ba ka mayar da ita ba, ka sani tabbas kai da dukkan abin da ke naka zaku hallaka."
8Abimelek ya tashi da asuba ya kira dukkan bayinsa gare shi. Ya faɗa musu duk waɗanna abubuwa, sai mazajensa suka firgita.9Sai Abimelek ya kira Ibrahim yace da shi, "Me kenan ka yi mana? Yaya nayi maka laifi, da ka jawo wa mulkina da ni kaina wannan zunubi? Ka yi mini abin da bai kamata a yi ba."
10Abimelek yace da Ibrahim, "Meyasa ka yi wannan abin?"11Ibrahim yace, domin na yi tsammanin cewa hakika babu tsoron Allah a wannan wurin, kuma zasu kashe ni saboda matata.'12Bayan haka kuma hakika ita 'yar'uwata ce, 'yar mahaifina ce, amma ba 'yar mahaifiyata ba, sai kuma ta zama matata.
13Lokacin da Allah ya sa na bar gidan mahaifina in yi tafiya daga wannan wuri zuwa wancan wuri, na ce da ita dole ne ki nuna mini wannan aminci a matsayin matata: A duk inda muka je ki faɗi haka game da ni, "Shi ɗan'uwana ne.""14Sai Abimelek ya kwashi tumaki da takarkari da maza da mata na bayi ya bada su ga Ibrahim. Daga nan ya mayar da Saratu, matar Ibrahim a gare shi.
15Abimelek yace, "Duba, wannan ƙasar tawa tana gabanka. Ka zauna a duk inda ya yi maka kyau."16Ga Saratu kuma ya ce, duba, na ba ɗan'uwanki azurfa dubu. Wannan domin ya shafe duk wani laifi dana yi maku ne a fuskarku dukka, da kuma a gaban kowa da kowa, hakika kun yi abin da ke dai-dai."
17Sai Ibrahim ya yi addu'a sai Allah ya warkar da Abimelek, da matarsa, da bayinsa mata domin su iya haifar 'ya'ya.18Domin Yahweh yasa dukkan matan gidan Abimelek su zama marasa haihuwa baki ɗaya, Saboda Saratu matar Ibrahim.

21

1Yahweh ya saurari Saratu kamar yadda ya ce zai yi, Yahweh kuwa ya yi wa Saratu kamar yadda ya alƙawarta.2Saratu kuwa ta yi juna biyu ta haifa wa Ibrahim ɗa a cikin kwanakin tsufansa, a daidai lokacin da Yahweh ya yi masa magana.3Ibrahim kuma ya raɗa wa ɗansa suna, wato wannan ɗa da aka haifa masa, wannan da Saratu ta haifa masa wato Ishaku.4Ibrahim ya yi wa ɗansa Ishaku kaciya da yayi kwana takwas, kamar dai yadda Allah ya umarce shi.

5Ibrahim na da shekaru ɗari a lokacin da aka haifa masa Ishaku.6Saratu ta ce, "Allah ya sa ni dariya, duk wanda ya ji zai yi dariya tare da ni."7Wane ne zai ce da Ibrahim cewa Saratu za ta yi masa renon 'ya'ya, kuma duk da haka na haifa masa ɗa a kwanakin tsufansa!"
8Yaron ya yi girma aka yaye shi, Ibrahim ya yi babbar liyafa a ranar da aka yaye Ishaku.9Saratu ta ga ɗan Hajara Bamasariya, da ta haifa wa Ibrahim, na ba'a.
10Saboda haka ta ce da Ibrahim, "Ka kori wannan baiwar matar da ɗanta: domin ɗan wannan baiwar ba zai ci gãdo, tare da ɗana Ishaku ba."11Wannan abin ya yi wa Ibrahim zafi a rai saboda ɗansa.
12Amma Allah yace da Ibrahim, "Kada ka damu saboda yaron, da kuma saboda wannan matar baiwarka. Ka saurari kalmominta kan duk abin da ta faɗa maka kan wannan al'amari, saboda ta wurin Ishaku ne za a kira zuriyarka.13Hakanan zan sa ɗan baiwar matar ya zama al'umma, domin shi zuriyarka ne."
14Ibrahim ya ta shi da asuba, ya ɗauki gurasa da goran ruwa, ya ba da shi ga Hajara ya ɗora shi a kafaɗarta. Ya ba ta ɗan ya sallame ta ta tafi. Ta tafi ta yi ta yawo cikin jejin Beyersheba.15Da ruwan da ke cikin goran ruwan ya ƙare, sai ta yashe da ɗan a gindin wasu ciyayi.16Sai ta tafi ta zauna can nesa dai-dai harbin kibiya, domin ta ce, "Kada in ga mutuwar ɗana." Da ta zauna daura da shi sai ta ta da murya ta yi kuka.
17Allah ya ji kukan ɗan, sai mala'ikan Allah ya kira Hajara daga can sama, ya ce da ita, "Me ke damun ki, Hajara? Kada ki ji tsoro, domin Allah ya ji kukan ɗan a inda yake.18Tashi ki ɗauki yaron, ki ƙarfafa shi, domin zan maishe shi babbar al'umma."
19Sai Allah ya buɗe idanunta, sai ta ga rijiyar ruwa. ta je ta cika gorar da ruwa, ta ba ɗan ya sha.20Allah na tare da ɗan, ya kuma yi girma. Ya yi rayuwa cikin jeji sai ya zama mafarauci.21Ya yi rayuwa a jejin Faran, mahaifiyarsa kuma ta aura masa mata daga ƙasar Masar
22Sai ya zamana a lokacin da Abimelek da Fikol shugaban sojojinsa ya yi magana da Ibrahim, cewa, "Allah na tare da kai a cikin dukkan al'amuranka.23Yanzu sai ka rantse mini cewa ba zaka yi mini ƙarya ba, haka kuma 'ya'yana, da zuriyata. Ka nuna mini da kuma ƙasar da kake zaune a ciki irin wannan alƙawari mai aminci da na nuna gare ka."24Ibrahim yace "Na rantse."
25Ibrahim kuma ya miƙa kukansa ga Abimelek game da rijiyar ruwa da bayin Abimelek su ka ƙwace daga wurinsa.26Abimelek yace "Ban san wanda ya yi wannan abu ba. Ba ka faɗa mini ba tuntuni; Ban ji al'amarin ba sai yau."27Sai Ibrahim ya ɗauki tumaki da shanu ya ba Abimelek, su biyun suka yi yarjejeniya.
28Sai Ibrahim ya ware raguna bakwai na garken da kansu.29Abimelek yace da Ibrahim, "Mene ne ma'anar waɗannan matan tumakin daka shirya su da kansu?"30Ya amsa, waɗannan matan tumakin guda bakwai zaka karɓa daga hannuna, domin su zama shaida domina, cewa ni na haƙa wannan rijiya."
31Sai ya kira wannan wurin Biyasheba, saboda a can ne dukkan su suka yi rantsuwa.32Suka yi yarjejeniya, Daga nan sai Abimelek da Fikol, shugaban sojojinsa, ya koma ƙasar Filistiyawa.
33Ibrahim ya dasa itacen sabara a Biyasheba. a can ya yi sujada ga Yahweh, Allah madawwami.34Ibrahim ya zauna a matsayin baƙo a ƙasar filistiyawa na kwanaki masu yawa.

22

1Sai ya zamana bayan waɗannan abubuwa Allah ya gwada Ibrahim. Ya ce da shi, "Ibrahim" Ibrahim yace, "Ga ni nan,"2Sai Allah yace, "Ka ɗauki ɗanka, tilon ɗanka, wanda kake ƙauna, Ishaku, sai ku je ƙasar Moriya. A can za ka miƙa shi baiko na ƙonawa akan ɗaya daga cikin duwatsun dake can, wanda zan faɗa maka game da shi."3Sai Ibrahim ya tashi da asuba ya ɗaura wa jakinsa sirdi, ya kuma ɗauki biyu daga cikin matasan mazajensa tare da shi, haɗe kuma da Ishaku ɗansa. Ya sassari itace domin baiko na ƙonawa, daga nan ya kama hanyarsa zuwa inda Allah ya faɗa masa.

4A rana ta uku Ibrahim ya duba sama sai ya hangi wurin daga nesa.5Sai Ibrahim yace da matasansa, "Ku tsaya nan da jakin, ni da yaron zamu haura can. Za mu yi sujada daga nan sai mu dawo wurinku."6Sai Ibrahim ya ɗauki itace domin hadaya ta ƙonawa ya ɗora wa Ishaku ɗansa. Sai ya ɗauki wuƙa da wuta a hannunsa; sai kuma suka tafi tare.
7Ishaku ya yi magana da Ibrahim mahaifinsa ya ce, "Babana," sai ya ce, "Ga ni nan ɗana." Ya ce, Ga wuta anan da itace, amma ina ɗan ragon baikon ƙonawa?"8Ibrahim yace, "Ɗana Allah da kansa zai tanada ɗan rago domin baikon ƙonawa." Sai suka ci gaba da tafiya tare su dukka.
9Sa'ad da suka zo wurin da Allah ya faɗa masa, Sai Ibrahim ya gina bagadi a can ya zuba itace a kansa. Sai ya ɗaure ɗansa Ishaku, ya ɗora shi akan bagadin bisa itacen.10Ibrahim ya miƙa hannunsa ya ɗauko wuƙa domin ya yanka ɗansa.
11Sai mala'ikan Yahweh ya kira shi daga sama ya ce, "Ibrahim, Ibrahim!" sai ya ce, "Ga ni nan."12Ya ce, "Kada ka ɗora hannunka a kan yaron, kar ka yi duk wani abu da zai cutar da shi, domin yanzu na sani kana tsoron Allah, ganin cewa ba ka hana mini ɗanka ba, tilon ɗanka."
13Ibrahim ya duba sama, sai ga ɗan rago a sarƙafe da ƙahonsa. Ibrahim ya ɗauki ɗan ragon ya miƙa shi baiko na ƙonawa a maimakon ɗansa.14Saboda haka Ibrahim ya kira wurin, "Yahweh zai tanada," haka kuma ake kiran wurin har yau,"A kan tsaunin Yahweh za a tanada shi."
15Mala'ikan Yahweh ya kira Ibrahim daga sama a karo na biyu16ya ce - wannan shi ne furcin Yahweh - na yi rantsuwa da kaina cewa da yake ka yi wannan abu, ba ka hana ɗanka ba tilon ɗanka,17Hakika zan albarkace ka zan kuma ruɓanɓanya zuriyarka kamar taurarin sammai, kamar kuma yashin dake gaɓar teku; zuriyarka kuma zasu mallaki ƙofar maƙiyansu.
18Ta wurin tsatsonka za a albarkaci dukkan al'ummar duniya, saboda ka yi biyayya da muryata."19Sai Ibrahim ya koma wurin barorinsa, suka tafi Beyarsheba tare sai ya zauna a Beyarsheba.
20Ya zamana bayan waɗannan abubuwa sai, aka ce da Ibrahim "Milka ta haifi 'ya'ya, haka kuma ɗan'uwanka Nahor."21Su ne Uz ɗansa na fari, Buz shi ne ɗan'uwansa, Kemuwal shi ne mahaifin Aram, da22Kesed da Hazo, da Fildash da Yidlaf da Betuwel.
23Betuwel ya haifi Rebeka. Waɗannan sune 'ya'ya takwas da Milka ta haifa wa Nahor, ɗan'uwan Ibrahim.24Ƙwarƙwararsa mai suna Reuma ita ma ta haifi Tebah da Gaham Tahash da Ma'aka.

23

1Saratu ta rayu tsawon shekaru ɗari da ashirin da bakwai. Waɗannan sune shekarun Saratu.2Saratu ta mutu a Kiriyat Arba wato Hebron, a ƙasar Kan'ana. Ibrahim ya yi makoki da kuka domin Saratu.

3Sai Ibrahim ya tashi ya bar wurin da matarsa ta mutu, ya yi magana da 'ya'yan Het, cewa.4"Ni bãƙo ne a cikin ku Ina roƙo ku bani mallakar wurin maƙabarta a cikinku domin in bizne matattuna."
5Sai 'ya'yan Het suka amsa wa Ibrahim cewa,6"Ka saurare mu shugabana. Kai yariman Allah ne a cikin mu. Bizne matattunka a duk inda ka zaɓa a maƙabartunmu, ba wanda zai hana maka maƙabartarsa domin ka bizne matattunka."
7Sai Ibrahim ya tashi ya rusuna wa mutanen ƙasar, ga "ya'yan Het.8Ya yi musu magana cewa, "In kun yarda cewa in bizne matacciyata, sai ku saurare ni ku roƙi Ifron ɗan Zohar domi na.9Ku tambaye shi ya sayar mini da kogon Makfela, wadda ya mallaka, wadda yake a ƙarshen filinsa. Domin cikakken farashi ya kuma sayar mini da shi a gaban mutane domin ya zama mallakata, da maƙabarta."
10Ifron kuma na zaune a cikin 'ya'yan Het, sai Ifron Bahitte ya amsa wa Ibrahim a kunnuwan 'ya'yan Het maza da kuma duk waɗanda suka zo ƙofar birninsa, cewa,11"A'a shugabana, ka saurare ni. Na baka filin da kuma kogon dake cikinsa. Na baka shi a gaban 'ya'yan mutanena maza. Na baka shi domin bizne matacciyarka."
12Sai Ibrahim ya sunkuyar da kansa ƙasa a gaban mutanen ƙasar.13Ya yi magana da Ifron a kunnen mutanen ƙasar cewa. "Amma in ka amince, inka yarda ka saurareni. Zan biya kuɗin filin. Ka karɓi kuɗi daga wuri na, ni kuma zan bizne mattaciyata a can."
14Ifron ya amsa wa Ibrahim, da cewa,15"Ina roƙo, ya shugabana, ka saurare ni.‌ Ɗan yankin ƙasa na shekel ɗari huɗu na azurfa, mene ne wannan a tsakanina da kai? Ka bizne mamaciyarka."16Ibrahim ya saurari Ifron, ya auna shekel ɗari huɗu kamar yadda Ifron ya ambata a kunnuwan dukkan 'ya'yan Het maza, mudu ɗari huɗu na zinariya, bisa ga mizanin ma'aunin fatake.
17Domin haka filin Ifron dake a Makfela wanda ke gaban Mamre, wato da filin da kogon dake cikinsa, da duk itatuwan dake cikin filin, da dukkan iyakarsa,18aka ba Ibrahim tawurin sayarwa a gaban 'ya'yan Het maza, da kuma duk waɗanda suka zo ƙofar birninsa.
19Bayan wannan Ibrahim ya bizne Saratu matarsa a cikin kogon filin Makfela, wanda ke gaba da Mamre wato Hebron, a cikin ƙasar Kan'ana.20Domin haka da filin da kogon dake cikinsa aka miƙa su ga Ibrahim daga 'ya'yan Het maza domin ya zama maƙabarta.

24

1Ya zamana kuma Ibrahim ya tsufa ainun, kuma Yahweh ya albarka ce shi a cikin komai.2Sai Ibrahim yace da baransa, wanda ya fi daɗewa da kuma ke kula da komai da ya mallaka, ya ce "Sa hannunka a ƙarƙashin cinyata,3zan sa ka ka rantse da Yahweh, Allah na sama da kuma Allah na duniya, cewa ba zaka auro wa ɗana mata daga cikin Kan'aniyawan da nake zama a cikinsu ba.4Amma zaka je cikin ƙasata da dangina ka auro wa ɗana Ishaku mata daga can."

5Sai baran yace da shi, "To yaya kenan, in matar ta ce ba za ta biyo ni zuwa wannan ƙasar ba fa? Ko ya zama tilas in mayar da ɗanka zuwa ƙasar da ka baro?"6Ibrahim yace da shi, "Ka tabbata cewa ba ka komar da ɗana can ba!7Yahweh Allah na sama, wanda ya ɗauko ni daga gidan mahaifina da kuma ƙasar dangina, wanda kuma ya yi mini tabbataccen alƙawari cewa, 'Ga zuriyarka zan bada wannan ƙasa,' zai aiko mala'ikansa a gabanka, kuma zaka samo wa ɗana mata daga can.
8Amma in matar ba ta son ta biyo ka, to ka kuɓuta daga rantsuwata, kada ka komar da ɗana can,"9Sai baran ya sa hannunsa a ƙarƙashin cinyoyin Ibrahim shugabansa, ya yi masa rantsuwa game da wannan al'amari.
10To sai baran ya ɗauki raƙuma goma na shugabansa ya tafi. Haka nan ya ɗauki duk waɗansu kyaututtuka da suka kamata daga wurin shugabansa ya tafi da su yankin Aram Naharaim zuwa birnin Nahor.11Ya sa raƙuman suka kwakkwanta a gefen rijiyar ruwa. Da yamma ne daidai lokacin da mata ke fita ɗiban ruwa.
12Daga nan sai ya ce, "Yahweh, Allah na shugabana Ibrahim, ka ba ni nasara a yau ka kuma nuna amintaccen alƙawarinka ga shugabana Ibrahim.13Duba yanzu ina tsaye a bakin ƙoramar ruwa, kuma 'yan'matan mutanen birnin suna fitowa domin su ɗibi ruwa.14Ka sa abin ya kasance kamar haka. In na ce da budurwar ina roƙon ki ki saukar da abin ɗiban ruwanki domin in sha; sai kuma ta ce da ni, ka sha, zan kuma shayar da raƙumanka ma; to bari ta zama matar daka nufa ta zama matar bawanka Ishaku. Da haka zan sani cewa ka nuna amintaccen alƙawarinka ga shugabana."
15Sai ya zamana kafin ma ya gama magana sai ga Rebeka ta zo da abin ɗiban ruwanta a kafaɗarta. Rebeka 'yar Betuwel ce ɗan Milka, matar Nahor, ɗan'uwan Ibrahim.16Budurwar kyakkyawa ce kuma ba ta ɓata budurcinta ba. Ba mutumin da ya taɓa kwana da ita. Sai ta tafi ƙoramar ta cika abin ɗiban ruwanta, ta hauro.
17Sai baran ya yi gudu domin ya gamu da ita ya ce, "Ina roƙo ki sam mani ruwa in ɗan sha daga cikin abin ɗiban ruwanki."18Ta ce ya shugabana ka sha sai ta yi sauri ta sauke abin ɗiban ruwan ƙasa a hannunta ta ba shi ya sha.
19Bayan ta gama ba shi ya sha, sai ta ce, "Zan ɗebowa raƙumanka ma su sha har sai sun kammala sha."20Sai ta yi sauri ta juye abin ɗebo ruwan, ta yi gudu ta sake komawa rijiyar domin ta ɗebo ruwa domin dukkan raƙumansa.
21Sai mutumin ya dube ta a natse domin ya gani ko Yahweh ya ba tafiyarsa nasara ko kuwa a'a.22Bayan raƙuman sun gama shan ruwan, sai mutumin ya ciro zoben zinariya na hanci mai nauyin rabin ma'auni, da ƙarau guda biyu na azurfa na sawa a dantse wanda ya kai nauyin ma'auni goma,23sai ya tambaya, "Ke "yar wane ne? Ina roƙon ki ki faɗa mini, ko akwai masauki a gidan mahaifinku da za mu kwana?"
24Ta ce da shi, "Ni 'yar Batuwel ce ɗan Milka wanda ta haifawa Nahor."25Ta kuma ce da shi muna kuma da ciyawa da abincin dabbobi da kuma ɗaki domin ku kwana."
26Sai mutumin ya sunkuya ƙasa ya yi sujada ga Yahweh.27Ya ce, "Albarka ta tabbata ga Yahweh, Allah na shugabana Ibrahim, wanda bai yashe da alƙawarinsa mai aminci ba da kuma amincinsa ga shugabana. Ni da kaina Yahweh ya bi da ni kai tsaye zuwa gidan dangin shugabana."
28Sai budurwar ta yi gudu ta je ta faɗa wa iyalin gidan mahaifiyarta duk abin da ya faru dangane da waɗannan al'amura.29Rebeka kuma tana da ɗan'uwa, sunansa Laban. Sai Laban ya ruga zuwa wurin mutumin wanda ke can kan hanyar ƙoramar.30Da ya ga wannnan zobe na hanci da ƙarau na dantse a dantsen 'yar'uwarsa, kuma bayan ya ji duk abin da Rebeka 'yar'uwarsa ta faɗa, "Wannan shi ne abin da mutumin ya ce da ni," sai ya tafi wurin mutumin, sai ga shi a tsaye a gefen raƙuma a wurin ƙoramar.
31Sai Laban yace, "Zo, kai mai albarka na Yahweh. Meyasa kake tsayuwa a waje? Na shirya gida da kuma wuri domin raƙuman."32Sai mutumin ya zo gidan ya kuma sauke wa raƙuman kaya. Sai aka ba raƙuman ciyawa da abincin dabbobi aka kuma tanadi ruwa domin ya wanke ƙafafunsa da kuma na mutanen dake tare da shi.
33Suka kawo masa abinci domin ya ci, amma ya ce, "Ba zan ci ba sai na faɗi abin da zan faɗa. "Sai Laban yace to faɗi abin da zaka faɗa."34Ya ce, "Ni baran Ibrahim ne.35Yahweh ya albarkaci shugabana sosai ya kuma yi girma sosai. Ya ba shi garkuna da dabbobi da zinariya da azurfa, da bayi maza da mata da raƙuma da jakuna.
36Saratu matar shugabana ta haifi ɗa ga shugabana a lokacin da ya tsufa, ya kuma bayar da duk abin da ya mallaka gare shi.37Shugabana ya sa na rantse, cewa, 'Ba za ka auro wa ɗana mata daga cikin 'yanmatan Kan'aniyawa ba, waɗanda a ƙasarsu na yi gidana.38Maimakon haka dole ka je wajen dangin mahaifina, cikin 'yan'uwana ka samo wa ɗana matar aure.'
39Na ce da shugabana, in a ce matar ba zata biyo ni ba fa.'40Amma ya ce da ni, Yahweh wanda nayi tafiya a gabansa, zai aiko mala'ikansa ya kasance tare da kai ya kuma baka nasara bisa tafiyarka, domin ka auro wa ɗana mata daga cikin dangina da kuma iyalin mahaifina.41Amma zaka kuɓuta daga rantsuwata in ka zo wurin 'yan'uwana in ba su baka ita ba. To zaka kuɓuta daga rantsuwata.'
42To da na kawo wurin ƙorama, na ce, 'Ya Yahweh, Allah na shugabana Ibrahim, ina roƙon ka, in har ka so ka ba tafiyata nasara-43gani nan a tsaye a bakin ƙorama-ka sa budurwar da ta zo ɗiban ruwa, wato macen da zan ce, "Ina roƙo ki ɗan san mani ruwa in sha daga abin ɗiban ruwanki,"44macen da ta ce da ni, "Sha, zan kuma shayar da raƙumanka"_Bari ta zama macen da kai, Yahweh, ka zaɓa domin ɗan shugabana.'
45Tun ma kafin in gama magana a cikin zuciyata, sai ga, Rebeka ta zo da abin ɗiban ruwanta a kafaɗarta sai ta gangara ƙoramar ta ɗebo ruwa. Sai na ce da ita, 'Ina roƙo ki bani ruwa in sha.'46Sai ta yi sauri ta sauko da abin ɗiban ruwan daga kafaɗarta ta ce, 'Ka sha, zan kuma shayar da raƙumanka.' Sai na sha, ta kuma shayar da raƙuman.
47Na tambaye ta cewa, 'Ke 'yar wane ne?' Ta ce, 'Yar Betuwel, ɗan Nahor, wanda Milka ta haifa masa.' Daga nan sai na sa zoben a hancinta da kuma ƙarau a damtsenta.48Sai na sunkuya na yi sujada ga Yahweh, na albarkaci Yahweh Allah na shugabana Ibrahim, wanda ya bishe ni a madaidaiciyar hanya domin in sami 'yar dangin shugabana domin ɗansa.
49Yanzu kuma, in kuna shirye ku nuna zumunci mai aminci da amana, ku faɗa mini. Amma in ba haka ba, ku faɗa mini, domin in bi dama ko hagu."
50Sai Laban da Betuwel suka amsa suka ce, Al'amarin daga Yahweh ya zo; ba zamu iya ce maka ya yi kyau ko bai yi kyau ba.51Duba Rebeka na gabanka. Ɗauke ta ku tafi, domin ta zama matar ɗan shugabanka, kamar yadda Yahweh ya faɗa."
52Da baran Ibrahim ya ji maganarsu, sai ya sunkuyar da kansa ƙasa ga Yahweh.53Sai baran ya fito da kayayyaki na zinariya da azurfa da sutura ya miƙa su ga Rebeka. Hakanan ya bada kyautai masu daraja ga ɗan'uwanta da kuma mahaifiyarta.
54Daga nan shi da mazajen dake tare da shi suka ci, suka sha. Suka kwana har gari ya waye, bayan sun tashi da safe, ya ce "Ku sallame ni zuwa gun shugabana."55Ɗan'uwanta da mahaifiyarta suka ce, "Bari budurwar ta ɗan yi waɗansu 'yan kwanaki kamar goma tukuna. Bayan nan za ta iya ta tafi."
56Amma ya ce da su kada ku hana ni da yake Yahweh ya sa tafiyata ta yi nasara. Ku sallame ni domin in koma wurin shugabana."57Suka ce za mu kira budurwar mu tambaye ta."58Sai suka kira Rebeka suka tambaye ta, "Za ki tafi tare da wannan mutumin?" Ta amsa "zan tafi."
59Sai suka aika 'yar'uwarsu Rebeka, tare da baranyarta, a cikin tafiyarta tare da baran Ibrahim da mazajensa.60Suka albarkaci Rebeka, suka ce da ita, "Yar'uwarmu, muna addu'a ki zama uwar dubun dubbai goma, da ma zuriyarki ta mallaki ƙofar maƙiyansu."
61Sai Rebeka ta tashi, ita da barorinta mata suka hau raƙuma, suka bi mutumin. Da haka baran ya ɗauki Rebeka ya yi tafiyarsa.62Ya zamana Ishaku na zama a Negeb, ya dawo kenan daga Beyerlahairoi.
63Ishaku ya fita domin yin nazari a saura da yammaci. Da ya duba tudu, ya hanga, sai ya ga raƙuma na tafe!64Rebeka ta duba, da ta ga Ishaku sai ta diro daga kan raƙumin.65Ta ce da baran, "Wane ne wancan dake tafiya a cikin saura domin ya tarbe mu?" Baran yace, "'Shugabana ne." Sai ta ɗauki gyale ta yi lulluɓi.
66Baran ya zaiyana wa Ishaku dukkan abin da ya yi.67Sai Ishaku ya kawo ta rumfar mahaifiyarsa Saratu ya ɗauki Rebeka, ta zama matarsa, ya kuma ƙaunace ta. Da haka Ishaku ya ta'azantu bayan mutuwar mahaifiyarsa.

25

1Sai Ibrahim ya auro wata mata mai suna Ketura.2Ta haifa masa Zimra, Yokshan, Medan, Midiyan, Ishbak, da Shuwa.3Yokshan ya haifi Sheba da Dedan. Zuriyar Dedan su ne mutanen Asiriya, da mutanen Letush, da mutanen Leyum.4'Ya'yan Midiyan sune Efa, Efer, Hanok, Abida, da Elda'ah. Duk waɗannan sune zuriyar Ketura.

5Ibrahim ya mallaka duk abin da yake da shi ga Ishaku.6Duk da haka, a lokacin da yake raye ya ba da kyautai ga 'ya'yan ƙwaraƙwaransa ya aika su ƙasar gabas nesa da ɗansa Ishaku.
7Waɗannan sune kwanakin shekarun rayuwar Ibrahim da ya yi shekaru, 175.8Ibrahim ya yi numfashinsa na ƙarshe ya mutu a cikin kyakkyawan tsufa, tsohon mutum mai cike da kuzari, sai aka tattara shi ga mutanensa.
9Ishaku da Isma'ila, 'ya'yansa suka bizne shi a kogon Makfela, a filin Ifron ɗan Zohar Bahitte, wadda ke kusa da Mamre.10Wannan filin Ibrahim ya saya daga'ya'yan Het maza. A can aka bizne Ibrahim da matarsa Saratu.11Bayan mutuwar Ibrahim Allah ya albarkaci ɗansa Ishaku, Ishaku ya zauna kusa da Beyer Lahai Roi.
12To Waɗannan sune zuriyar Isma'ila ɗan Ibrahim, da Hajara Bamasariya baiwar Saratu, ta haifa wa Ibrahim.
13Waɗannan sune sunayen 'ya'yan Isma'ila bisa ga tsarin haihuwarsu: Nebaiyot - shi ne ɗan fari na Isma'ila, da Kedar, da Adbe'el, da Mibsam,14da Mishma, da Massa,15Hadad, da Tema, da Yetur, da Nafish, da Kedema.16Waɗannan su ne 'ya'yan Isma'ila, kuma waɗannan sune sunayensu bisa ƙauyukansu, suna kuma da sarakuna sha biyu bisa ga kabilarsu.
17Waɗannan su ne shekarun rayuwar Isma'ila, shekaru, 137 ya yi numfashinsa na ƙarshe sa'an nan ya mutu, sai aka tattara shi ga mutanensa.18Sun yi rayuwa daga Habila zuwa Ashur, wadda take kusa da Masar, ɗaya kuma ya nufi Asiriya. Sun yi zaman tankiya da juna.
19Waɗannan su ne al'amura game da Ishaku, ɗan Ibrahim: Ibrahim ya haifi Ishaku.20Ishaku nada shekaru arba'in a lokacin da ya ɗauki Rebeka a matsayin matarsa, 'yar Betuwel mutumin Aramiya ta Faddan Aram, 'yar'uwar Laban na Aramiya.
21Ishaku ya yi addu'a ga Yahweh domin matarsa saboda ba ta da ɗa, Yahweh kuma ya amsa addu'arsa, Rebeka matarsa kuma ta yi juna biyu.22'Ya'yan na ta fama tare tun daga cikinta, sai ta ce, "Meyasa wannan ke faruwa da ni?" Ta je ta tambayi Yahweh game da haka.
23Yahweh yace da ita, "Al'umma biyu ce a mahaifarki, mutane biyu kuma zasu rabu daga gare ki. Ɗaya jama'ar za ta fi ɗayar ƙarfi, babban kuma zai bauta wa ƙaramin."
24Da lokacin haihuwarta yayi, sai ta kasance da 'yan biyu a mahaifarta.25Na farkon ya fito da gargasa a ko'ina kamar tufafin gashi. Suka kira sunansa Isuwa.26Bayan haka, ɗan'uwansa ya fito hannuwansa na‌ riƙ‌e da diddigen Isuwa. Sai aka kira shi Yakubu. Ishaku na da shekaru sittin lokacin da matarsa ta haifa masa su.
27Samarin suka yi girma, Isuwa ya zama shahararren mafarauci mai yawo a saura; amma Yakubu mai shiru-shiru ne, wanda ya kashe lokacinsa cikin runfofi.28Sai ishaku ya ƙaunaci Isuwa domin yakan ci namomin jejin da ya harbo, amma Rebeka ta ƙaunaci Yakubu.
29Yakubu ya shirya ɗan dage-dage. Isuwa ya zo daga saura, ya kuma raunana saboda yunwa.30Isuwa yace da Yakubu, "Ka ciyar da ni da dage-dagenka mana. Ina roƙonka ƙarfina ya ƙare!" Shiyasa aka kira sunansa Idom.
31Yakubu yace, "Da farko ka sayar mani da matsayinka na ɗan fari tukuna."32Isuwa yace, "Duba, Na kusa mutuwa. Wanne amfani ne matsayin ɗan fari ke da shi a gare ni?"33Yakubu yace, "Da farko sai ka rantse mani" ta haka Isuwa ya yi rantsuwa kuma ta haka Isuwa ya sayar da matsayinsa na ɗan fari ga Yakubu.34Yakubu ya ba Isuwa dage-dagen wake da gurasa. Ya ci ya sha, daga nan ya tashi ya tafi abinsa. Ta wannan hali Isuwa ya banzantar da matsayinsa na ɗan fari.

26

1Sai aka yi yunwa a ƙasar, bayan wacce aka yi ta fari a kwanakin Ibrahim, Ishaku ya tafi wurin Abimelek, sarkin Filistiyawa a Gerar.

2Sai Yahweh ya bayyana gare shi ya ce, "Kada ka gangara Masar; ka zauna a ƙasar dana ce ka zauna a ciki.3Ka zauna a wannan ƙasar, zan kasance tare da kai, in kuma albarkace ka; domin a gare ka da zuriyarka ne zan bayar da ƙasashen al'ummai, kuma zan cika alƙawarin dana yi wa Ibrahim mahaifinka.
4Zan ruɓanɓanya zuriyarka kamar taurarin sama zan kuma bada waɗannan ƙasashe ga zuriyarka. Ta wurin al'ummarka dukkan ai'umman duniya zasu sami albarka.5Zan yi wannan domin Ibrahim ya yi biyayya da muryata ya kuma kiyaye dokokina, da farillaina, da shari'una. da ka'idodina."
6Don haka Ishaku ya zauna a Gerar.7Da mutanen wurin suka tambaye shi game da matarsa, sai ya ce, "Ita 'yar'uwata ce". Ya ji tsoro ya ce, "Ita matata ce," saboda ya yi tunanin cewa, mutanen zasu kashe ni su ɗauke Rebeka domin ita kyakkyawa ce."8Bayan Ishaku ya daɗe a can, sai Abimelek sarkin Filistiyawa ya duba ta taga. Sai ya ga Ishaku na shafa Rebeka, matarsa.
9Abimelek ya kira Ishaku gare shi ya ce, "Duba hakika ita matarka ce. Don me ka ce, ita 'yar'uwata ce'?" Ishaku yace da shi, "Saboda na yi tsammanin wani zai iya ya kashe ni don ya same ta."10Abimelek yace, "Me kenan ka yi mana? Da kuwa wani ya kwana da matarka cikin sauƙi, da kuma ka jawo mana laifi."11Sai Abimelek ya gargaɗi mutene ya ce, "Duk wanda ya taɓa mutumin nan ko matarsa hakika za a kashe shi."
12Ishaku ya shuka hatsi a waccan ƙasar, ya kuma yi girbi a wannan shekara, ya sami riɓi ɗari, saboda Yahweh ya albarkace shi.13Mutumin ya azurta, ya dinga bunƙasa sosai har sai da ya yi girma sosai.14Yana da tumakai masu yawa da dabbobi, da iyalai masu yawa. Filistiyawa suka yi kishinsa.
15To dukkan rijiyoyin da barorin mahaifinsa suka haƙa a kwanakin Ibrahim mahaifinsa, Filistiyawa suka cike su da ƙasa.16Abimelek yace da Ishaku, "Ka tafi ka ba mu wuri, domin ka fi mu ƙarfi."17Sai Ishaku ya bar garin ya koma Kwarin Gerar ya zauna a can.
18Haka kuma Ishaku ya tone rijiyoyi na ruwa waɗanda aka haƙa a kwanakin Ibrahim mahaifinsa. Filistiyawa suka ɓata su bayan mutuwar Ibrahim. Ishaku ya kira rijiyoyin da ainihin sunan da mahaifinsa ya kira su.
19Bayan barorin Ishaku sun yi tono a cikin kwarin, sai suka sami wata rijiya mai fitar da ruwa a can.20Makiyayan Gerar suka yi faɗa da makiyayan Ishaku suka ce, "Wannan ruwan namu ne." Domin haka Ishaku ya kira rijiyar "Esek" wato rikici, saboda sun yi rikici da shi.
21Sai suka sake haƙa wata rijiyar, sai suka sake yin rikici akan itama wannan rijiyar, sai ya ba ta suna "Sitnah."22Sai ya bar wurin ya ƙara haƙa wata rijiyar, amma ba su yi rikici kan wannan ba. Don haka ya kira ta Rehobot, ya ce, "Yanzu Yahweh ya samar mana masauki, kuma za mu wadata a cikin ƙasar."
23Sai Ishaku ya haura daga can zuwa Bayersheba.24Yahweh ya bayyana a gare shi a cikin wannan daren ya ce, "Ni ne Allah na Ibrahim mahaifinka. Kada ka ji tsoro, domin ina tare da kai zan kuma albarkace ka in ruɓanɓanya zuriyarka, saboda barana Ibrahim."25Ishaku ya gina bagadi ya yi kira bisa sunan Yahweh. A can ya kafa rumfarsa, barorinsa kuma suka haƙa rijiya.
26Sai Abimelek ya je wurinsa daga Gerar, tare da Ahuzat, abokinsa, da Fikol, jagoran sojojinsa.27Ishaku yace da su, "Meyasa kuke zuwa gare ni, tun da yake kun ƙi ni, kun kuma kore ni daga wurinku?"
28Sai suka ce, "Zahiri mun ga Yahweh na tare da kai. Shi yasa muka ga ya fi kyau a sami rantsuwa tsakaninmu, i, tsakaninmu da kai, To in ka yarda sai mu yi yarjejeniya da kai,29cewa ba zaka wahalshe mu ba, kamar yadda muka yi maka muka sallame ka cikin lumana, hakika Yahweh ya albarkace ka."
30Sai ishaku ya shirya liyafa domin su, suka ci suka sha.31Suka tashi da asuba suka yi rantsuwar alƙawari da juna. Daga nan Ishaku ya sallame su, suka bar shi cikin salama.
32A wannan ranar dai barorin Ishaku suka zo suka ba shi labari game da rijiyar da suka haƙa. Suka ce, Mun sami ruwa."33Ya kira rijiyar da suna Shiba, shi ya sa a ke kiran wannan birni da suna Bayersheba har ya zuwa yau.
34Da Isuwa ya kai shekaru arba'in, ya auri mata mai suna Yudit 'yar Be'eri Bahitte, da kuma Basemat "yar Elon Bahitte.35Suka kawo baƙinciki ga Ishaku da Rebeka.

27

1Da Ishaku ya tsufa har ta kai ga ba ya iya gani, sai ya kira Isuwa, babban ɗansa, ya ce da shi, "Ɗana." Ya ce da shi "Ga ni."2Ya ce, "Gashi yanzu, na tsufa. Ban kuma san ranar mutuwata ba.

3Domin haka, ka ɗauki kwarinka da bakanka da makamanka, ka je daji ka yiwo mini farauta.4Ka yi mani dage-dage, irin wanda nake ƙauna, ka kawo shi gare ni domin in ci in albarkace ka kafin in mutu."
5Sai Rebeka ta ji lokacin da Ishaku ke magana da Isuwa ɗansa. Isuwa ya tafi daji domin ya yiwo farauta ya kawo.6Sai Rebeka ta yi magana da Yakubu ɗanta ta ce, "Duba, na ji mahaifinka ya yi magana da Isuwa ɗan'uwanka. Ya ce,7'Ka farauto mani nama ka shirya mani dage-dage domin in ci in albarkace ka a gaban Yahweh kafin mutuwata.'
8Yanzu fa ɗana, ka yi biyayya da muryata kamar yadda zan umarce ka.9Ka je garke, ka kawo mini "yan awaki guda biyu; zan kuma shirya dage-dage mai daɗi da su domin mahaifinka, kamar yadda yake ƙauna.10Zaka kai shi wurin mahaifinka, domin ya ci, ya albarkace ka kafin ya mutu."
11Yakubu yace da Rebeka mahaifiyarsa, "Gashi, Isuwa ɗan'uwana gargasa ne, ni kuma sulɓi ne.12In mahaifina ya taɓa ni, na kuma zama mayaudari a gare shi. Zan jawo wa kaina la'ana ba albarka ba."
13Mahaifiyarsa ta ce da shi, "Ɗana, bari duk wata la'ana ta auko mani. kai dai ka yi biyayya da muryata, ka je ka kawo su wurina."14Sai Yakubu ya tafi ya samo 'yan awaki guda biyu ya kawo su ga mahafiyarsa, mahaifiyarsa kuwa ta shirya dage-dage, kamar yadda mahaifinsa ke ƙauna.
15Sai Rebeka ta ɗauki tufafin Isuwa babban ɗanta, mafi kyau, wanda ke tare da ita a gida, sai ta sa wa Yakubu, ƙaramin ɗanta.16Sai ta sa fatar 'yan awaki a hannunsa da kuma tattausan sashen wuyansa.17Sai ta sa dage-dagen mai daɗi da gurasar da ta shirya a hannun ɗanta Yakubu.
18Sai Yakubu ya tafi wurin mahaifinsa ya ce, "Mahaifina." Ya ce,"Ga ni nan; Wane ne kai ɗana?"19Yakubu yace da mahaifinsa, "Ni ne Isuwa ɗanka na fari; Na yi kamar yadda ka ce da ni. Yanzu sai ka tashi ka zauna ka ci ɗan dage-dagen, domin ka albarkace ni."
20Ishaku yace da ɗansa, "Ɗana yaya aka yi ka samo shi da sauri haka?" Ya ce, "Domin Yahweh Allanka ya kawo su wurina".21Ishaku yace da Yakubu, "Ɗana ka matso kusa da ni, domin in taɓa ka, domin in san ko kai ɗana ne."
22Yakubu ya matsa ga Ishaku mahaifinsa, Ishaku kuma ya taɓa shi ya ce, "Muyar kamar ta Yakubu ce, amma jikin na23Isuwa ne." Ishaku bai iya gane shi ba, domin hannuwansa gargasa ne kamar na hannuwan ɗan'uwansa Isuwa, domin haka Ishaku ya albarka ce shi.
24Ya ce "Kai ne ɗana Isuwa kuwa?" Ya amsa "Ni ne."25Ishaku yace, "Kawo abincin wurina, zan ci in kuma albarkace ka. Yakubu ya kawo abincin gare shi. Ishaku ya ci, Yakubu kuma ya kawo masa ruwan inabi, ya kuwa sha.
26Sai babansa Ishaku yace da shi, "Ɗana ka zo nan kusa ka sumbace ni."27Yakubu ya matso kusa ya sumbace shi' ya sunsuni ƙamshin suturarsa ya albarkace shi. Ya ce, "Duba, ƙamshin ɗana yana kama da ƙamshin ganyayyakin da Yahweh ya sa wa albarka.
28Allah ya baka rabo na raɓar sama, rabo na sashin ƙasa mafi dausayi, ya baka hatsi da ruwan Inabi mai yawa.
29Mutane da al'ummai kuma su rusuna maka. Ka zama shugaban 'yan'uwanka maza, 'ya'yan mahaifiyarka maza kuma su rusuna maka. Duk kuma wanda ya la'ance ka ya zama la'annanne, duk wanda kuma ya albarkace ka ya zama mai albarka."
30Ishaku na gama sa wa Yakubu albarka kenan, bayan ya fita daga wurin mahaifinsa Ishaku, sai ga Isuwa ɗan'uwansa ya shigo daga wurin farautarsa.31Shi ma ya shirya dage-dagen, abinci mai daɗi ya kawo shi wurin mahaifinsa. Ya ce da mahaifinsa, "Mahaifina, ka tashi ka ci irin dage-dagen ɗanka, domin ka albarkace ni."
32Ishaku mahaifinsa ya ce da shi, "Kai wane ne?" Ya ce, "Ni ne ɗan farinka, Isuwa.33Ishaku ya gigice sosai ya ce, "Wane ne ya yiwo farauta ya kawo mani dage-dage? Na ci a gabanin zuwanka, na kuma albarkace shi. Hakika, zai zama da albarka."
34Bayan Isuwa ya ji kalmomin mahaifinsa, ya yi kuka da baƙinciki matuƙa, ya ce da mahaifinsa, "Ni ma ka albarkace ni mana, mahaifina."35Ishaku yace, "Ɗan'uwanka ya zo cikin yaudara ya karɓe albarkarka."
36Isuwa yace, "Ashe ba haka ta sa aka ba shi suna Yakubu ba? Domin ya zambace ni sau biyu. Ya karɓe matsayina na ɗan fãri, kuma duba yanzu ya karɓe albarkata." Daga nan ya ce, "Ba ka rage wata albarka domina ba?"37Ishaku ya amsa ya ce da Isuwa, "Duba, na maishe shi ya zama shugabanka, kuma na ba shi dukkan 'yan'uwansa maza su zama bayinsa, na kuma ba shi hatsi da sabon ruwan inabi. Me kuma zan yi maka, ɗana?"
38Isuwa yace da mahaifinsa, "Ko albarka ɗaya ba ka rage mani ba mahaifina? Ka albarkace ni nima mahaifina." Isuwa yayi kuka da ƙarfi.
39Ishaku mahaifinsa ya amsa masa cewa, "Duba, wurin da zaka zauna zai zama da nisa daga wadatar duniya, nesa kuma da raɓar sararin sama.40Ta wurin takobinka zaka rayu, kuma zaka bautawa ɗan'uwanka. Amma lokacin da kayi tayarwa, zaka kawar da karkiyarsa daga wuyanka."
41Isuwa ya ƙi Yakubu saboda albarkar da mahaifinsa ya ba shi. Isuwa yace a cikin zuciyarsa, "Kwanakin makokin mahaifina sun kusa wucewa, bayan wannan zan kashe ɗan'uwana Yakubu."42Sai aka faɗa wa Rebeka kalmomin da babban ɗanta ya faɗa. Domin haka ta aika a kira Yakubu ƙaramin ɗanta ta ce da shi, "'Duba, ɗan'uwanka na tunanin yadda zai kashe ka.
43Saboda haka, ɗana, yanzu sai ka yi biyayya da muryata, ka gudu wurin Laban ɗan'uwana a Haran.44Ka zauna tare da shi na ɗan lokaci,45har sai fushin ɗan'uwanka ya huce daga gare ka, ya kuma manta abin da kayi masa. Daga nan zan aika a dawo da kai daga can. Don me zan rasa ku dukka a rana ɗaya?
46Rebeka ta ce, "Na gaji da rayuwa saboda 'ya'yan Het. In Yakubu ya auri 'yanmata irin waɗannan mataye, waɗansu daga cikin 'yan matan ƙasar, wanne abu ne mai kyau zai zama a rayuwata?"

28

1Ishaku ya kira Yakubu, ya albarkace shi, ya kuma dokace shi, "Tilas ba zaka ɗauki mata daga cikin matan Kan'aniyawa ba.2Ka tashi, ka tafi Faddan Aram, zuwa gidan Betuwel mahaifin mahaifiyarka, ka kuma ɗauki mata daga can, ɗaya daga cikin 'ya'ya mata na Laban, ɗan'uwan mahaifiyarka.

3Bari Allah mai iko dukka ya albarkace ka, yasa kayi 'ya'ya, ka kuma ruɓanɓanya, yadda zaka zama mutane tururu.4Bari ya bada albarkar Ibrahim, gare ka, da zuriyarka a bayanka, domin ka iya gãdon ƙasa inda ka ke zama, wadda Allah ya ba Ibrahim."
5Sai Ishaku ya sallami Yakubu, Yakubu ya tafi Faddan Aram, zuwa ga Laban ɗan Betuwel Ba'aramiye, ɗan'uwan Rebeka, mahaifiyar Yakubu da Isuwa.
6Yanzu Isuwa ya ga Ishaku ya albarkaci Yakubu ya kuma sallame shi zuwa Faddan Aram, ya ɗauko mata daga can. Ya kuma ga cewa Ishaku ya albarkace shi ya kuma dokace shi, cewa, "Tilas ba za ka ɗauki mata daga matan Kan'aniyawa ba."7Isuwa kuma ya ga cewa Yakubu ya yi biyayya da mahaifinsa da mahaifiyarsa, ya kuma tafi Faddan Aram.
8Isuwa ya ga cewa matan Kan'aniyawa ba su gamshi Ishaku mahaifinsa ba.9Sai ya tafi wurin Isma'ila, ya ɗauko, baya ga matan da yake da su, Mahalat ɗiyar Isma'ila, ɗan Ibrahim, 'yar'uwar Nebayot, ta zama matarsa.
10Yakubu ya bar Bayesheba ya tafi zuwa Haran.11Ya iso daidai wani wuri ya kuma tsaya wurin dukkan dare, saboda rana ta fãɗi. Ya ɗauki ɗaya daga cikin duwatsun wurin, ya sa ƙarƙashin kansa, ya kuma kwanta a wurin domin ya yi barci.
12Ya yi mafarki ya kuma ga hawan bene an kafa bisa duniya. ‌Ƙololuwarsa ta kai cikin sama kuma mala'ikun Allah suna hawa suna sauka a kansa.13Duba, Yahweh ya tsaya a bisansa ya kuma ce, "Ni ne Yahweh, Allah na Ibrahim mahaifinka, da Allah na Ishaku. ‌Ƙasar inda kake kwance, zan bayar gare ka ga kuma zuriyarka.
14Zuriyarka zasu zama kamar turɓayar ƙasa, kuma zaka bazu nesa zuwa yamma, zuwa gabas, zuwa arewa, zuwa kuma kudu. Ta wurin ka da ta wurin zuriyarka dukkan iyalan duniya zasu yi albarka.15Duba, Ina tare da kai, kuma zan kiyaye ka ko'ina ka tafi. Zan sake kawo ka cikin wannan ƙasa; gama ba zan barka ba. Zan yi dukkan abin dana yi alƙawari a gare ka."
16Yakubu ya tashi daga barci, ya kuma ce, "Tabbas Yahweh yana wannan wurin, kuma ban sani ba."17Ya ji tsoro ya kuma ce, "Wurin nan mai ban tsoro ne! Wannan ba wani wuri ba ne wanda ya wuce gidan Allah. Wannan ƙofar sama ce."
18Yakubu ya tashi da sassafe ya kuma ɗauki dutsen da ya sa ƙarƙashin kansa. Ya kafa shi a matsayin ginshiƙi ya kuma zuba mai a kansa.19Ya kira sunan wannan wuri Betel, amma asalin sunan wannan birni Luz ne.
20Yakubu ya yi wa'adi, cewa, "Idan Allah zai kasance tare da ni ya kuma kiyaye ni a cikin wannan hanya dana ke tafiya, ya kuma ba ni gurasa in ci, da suturar sanya wa,21yadda zan dawo lafiya zuwa gidan mahaifina, daga nan Yahweh zai zama Allah na.22Daga nan wannan dutse dana kafa a matsayin ginshiƙi zai zama tsarkakakken dutse. Daga kowanne abin da ka bani, babu shakka zan bayar da kashi ɗaya cikin goma a gare ka."

29

1Daga nan Yakubu ya kama tafiyarsa ya zo cikin ƙasar mutanen gabas.2Yayin da ya duba, sai ya ga rijiya a saura, kuma, duba, garkunan tumaki uku na kwance a gefen ta. Domin daga wannan rijiyar za su yi wa garkunan ban ruwa, kuma dutsen dake bakin rijiyar ƙato ne.3Sa'ad da dukkan garkunan suka taru a nan, makiyayan zasu gangarar da dutsen daga bakin rijiyar su kuma yi wa tumakin ban ruwa, sai kuma su mai da dutsen bakin rijiyar, daidai wurinsa.

4Yakubu yace masu, "Yan'uwana, daga ina ku ke?" Suka maida amsa, "Daga Haran muke."5Ya ce masu, "Kun san Laban ɗan Nahor?" Suka ce, "Mun san shi."6Ya ce masu, "Yana nan lafiya?" Suka ce, "Yana nan lafiya, kuma, duba can, Rahila ɗiyarsa na zuwa tare da tumaki."
7Yakubu yace, "Duba, yanzu rana tsaka ne. Lokaci bai yi ba da za a tattara garkuna tare. Kuyi wa tumakin ban ruwa daga nan ku tafi ku kai su kiwo."8Suka ce, "Ba za mu iya yi masu banruwa ba har sai dukkan garkunan sun tattaru tare. Daga nan mazan zasu gangarar da dutsen daga bakin rijiyar, sai kuma mu yi wa tumakin banruwa."
9Yayin da Yakubu ke magana tare da su, Rahila ta zo da tumakin mahaifinta, domin ita ke kiwon su.10Sa'ad da Yakubu ya ga Rahila, ɗiyar Laban, ɗan'uwan mahaifiyarsa, da tumakin Laban, ɗan'uwan mahaifiyarsa, Yakubu ya zo kusa, ya gangarar da dutsen daga bakin rijiyar, ya kuma yi wa garken Laban ɗan'uwan mahaifiyarsa banruwa.
11Yakubu ya sumbaci Rahila ya yi kuka da ƙarfi.12Yakubu ya gaya wa Rahila cewa shi dangin mahaifinta ne, kuma cewa shi ɗan Rebeka ne. Daga nan ta ruga ta gaya wa mahaifinta.
13Sa'ad da Laban ya ji labarin Yakubu ɗan 'yar'uwarsa, ya ruga domin ya same shi, ya rungume shi, ya sumbace shi, ya kuma kawo shi cikin gidansa. Yakubu ya gaya wa Laban dukkan waɗannan abubuwa.14Laban yace masa, "Tabbas kai ƙashina ne da namana." Daga nan Yakubu ya zauna tare da shi har wajen wata ɗaya.
15Daga nan Laban ya cewa Yakubu, "Kã bauta mani a banza saboda kai ɗan dangina ne? Gaya mani, mene ne zai zama ladanka?"16Yanzu dai Laban na da 'ya'ya mata biyu. Sunan babbar Liya, sunan ƙaramar kuma Rahila.17Idanun Liya tausasa ne amma Rahila na da kyakkyawar siffa.18Yakubu ya ƙaunaci Rahila, sai ya ce, "Zan bauta maka shekaru bakwai domin Rahila, ƙaramar ɗiyarka."
19Laban yace, "Gwamma in bayar da ita a gare ka, maimakon in bayar da ita ga wani mutumin. Ka yi zamanka da ni."20Sai Yakubu ya yi bauta shekaru bakwai domin Rahila; sai kuma suka yi masa kamar kwanaki kaɗan, domin ƙaunar da yake yi mata.
21Daga nan Yakubu ya cewa Laban, "Ka bani matata, domin kwanakina sun kammalu - domin in aure ta!"22Sai Laban ya tattara dukkan mutanen wurin ya kuma yi biki.
23Da maraice ya yi, Laban ya ɗauki ɗiyarsa Liya ya kuma kawo wa Yakubu, wanda ya kwana da ita.24Laban ya ɗauki baiwarsa Zilfa ya ba ɗiyarsa Liya, ta zama baiwarta.25Da safe, da ya duba, sai ya ga ashe Liya ce! Yakubu ya cewa Laban, "Mene ne wannan ka yi mani? Ba domin Rahila na bauta maka ba? To me ya sa ka yaudare ni?"
26Laban yace, "Ba al'adarmu ba ce mu bayar da ƙaramar ɗiya kafin ta fãrin.27Ka kammala satin amarcin wannan ɗiyar, za mu kuma baka ɗayar a sakamakon sake bauta mani na wasu shekarun bakwai."
28Yakubu ya yi haka, ya kammala satin Liya. Daga nan Laban ya ba shi Rahila ɗiyarsa a matsayin matarsa.29Laban kuma ya bayar da Bilha ga ɗiyarsa Rahila, ta zama baiwarta.30Haka kuma Yakubu ya kwana da Rahila, amma ya ƙaunaci Rahila fiye da Liya. Sai Yakubu ya bauta wa Laban na wasu shekaru bakwai.
31Yahweh ya ga cewa ba a ƙaunar Liya, sai ya buɗe mahaifarta, amma Rahila ba ta da ɗa.32Liya ta ɗauki ciki ta haifi ɗa, ta kuma kira sunansa Ruben. Domin ta ce, "Saboda Yahweh ya dubi azabata; babu shakka yanzu mijina zai ƙaunace ni."
33Daga nan ta sake ɗaukan ciki ta haifi ɗa. Ta ce, "Saboda Yahweh ya ji cewa ba a ƙauna ta, saboda haka ya bani wannan ɗan kuma," ta kuma kira sunansa Simiyon.34Daga nan ta sake ɗaukan ciki ta haifi ɗa. Ta ce, "Yanzu a wannan lokacin mijina zai haɗe da ni, saboda na haifa masa 'ya'ya maza uku." Saboda haka a ka kira sunansa Lebi.
35Ta sake ɗaukar ciki ta kuma haifar ɗa. Ta ce, "Wannan lokacin zan yabi Yahweh." Saboda haka ta kira sunansa Yahuda; Daga nan ta tsaya da haihuwar 'ya'ya.

30

1Da Rahila ta ga cewa ba ta haifa wa Yakubu 'ya'ya ba, sai Rahila ta ji kishin 'yar'uwarta. Ta ce wa Yakubu, "Ba ni 'ya'ya, ko in mutu."2Fushin Yakubu ya yi ƙuna gãba da Rahila. Ya ce, "Ina a madadin Allah ne, wanda ya hana ki samun 'ya'ya?"

3Ta ce, "Duba, wannan baiwata ce Bilha. Ka kwana da ita, saboda ta haifi 'ya'ya bisa gwiwoyina, kuma in sami 'ya'ya ta wurin ta."4Sai ta bayar da baiwarta Bilha a matsayin mata, Yakubu kuma ya kwana da ita.
5Bilha ta ɗauki ciki ta haifa wa Yakubu ɗa.6Daga nan Rahila ta ce, "Allah ya baratar da ni, ya kuma ji muryata ya kuma bani ɗa." Domin wannan dalili ta kira sunansa Dan.
7Bilha, baiwar Rahila, ta sake ɗaukar ciki ta haifa wa Yakubu ɗa na biyu.8Rahila ta ce, "Da kokowa mai girma na yi kokowa da 'yar'uwata na kuma yi nasara." Ta kira sunansa Naftali.
9Sa'ad da Liya ta ga cewa ta tsaya da haihuwar 'ya'ya, ta ɗauki Zilfa, baiwarta, ta bayar da ita ga Yakubu a matsayin mata.10Zilfa, baiwar Liya, ta haifa wa Yakubu ɗa.11Liya ta ce, "Wannan rabo ne!" Sai ta kira sunansa Gad.
12Daga nan Zilfa, baiwar Liya, ta haifa wa Yakubu ɗa na biyu.13Liya ta ce, "Na yi murna! domin 'ya'ya mata zasu kira ni murna." Sai ta kira sunansa Asha.
14Ruben ya fita a lokacin yankan alkama ya kuma samo 'ya'yan itacen manta'uwa daga saura. Ya kuma kawo su wurin mahaifiyarsa Liya. Daga nan Rahila ta ce wa Liya, "Ki ba ni daga cikin 'ya'yan itacen manta'uwa na ɗanki."15Liya ta ce mata, "‌Ƙaramin al'amari ne a gare ki, cewa kin ɗauke mani miji? Ki na so yanzu ki ɗauke 'ya'yan manta'uwa na ɗana, kuma?" Rahila ta ce, "To zai kwana dake a daren nan, a matsayin musanya domin 'ya'yan manta uwa na ɗanki."
16Yakubu ya dawo daga gona da yamma. Liya ta fita ta same shi ta ce, "Tilas ka kwana da ni a daren nan, domin nayi hayar ka da 'ya'yan manta'uwa na ɗana." Sai Yakubu ya kwana da Liya a wannan daren.17Allah ya saurari Liya, ta kuma ɗauki ciki ta haifa wa Yakubu ɗa na biyar.18Liya ta ce, "Allah ya bani ladana, saboda na bayar da baiwata ga mijina." Sai ta kira sunansa Issaka.
19Liya ta sake ɗaukan ciki ta haifa wa Yakubu ɗa na shida.20Liya ta ce, "Allah ya bani kyauta mai kyau. Yanzu mijina zai girmama ni, saboda na haifa masa 'ya'ya maza shida." Ta kira sunansa Zebulun.21Daga baya ta haifi ɗiya ta kuma kira sunanta Dina.
22Allah ya tuna da Rahila ya kuma saurare ta. Ya sa ta ɗauki ciki.23Ta ɗauki ciki ta haifi ɗa. Ta ce, "Allah ya ɗauke kunyata."24Ta kira sunansa Yosef, cewa, "Yahweh ya ƙara mani wani ɗan."
25Bayan da Rahila ta haifi Yosef, sai Yakubu yace wa Laban, "Ka sallame ni saboda in tafi nawa gidan da ƙasata.26Ka bani matayena da 'ya'yana waɗanda domin su na yi maka bauta, bari kuma in tafi, gama ka san hidimar dana yi maka."
27Laban yace masa, "Idan yanzu na sami tagomashi a gaban ka, ka jira, saboda ta wurin amfani da sihiri na gane cewa Yahweh ya albarkace ni saboda kai."28Daga nan ya ce, "Ka faɗi ladanka, zan kuma biya su."
29Yakubu yace masa, "Ka san dai yadda na bauta maka, da yadda dabbobinka suka kasance tare da ni.30Domin 'yan kaɗan kake da su kafin in zo, kuma sun ƙaru a yalwace. Yahweh ya albarkace ka a duk inda na yi aiki. Yanzu yaushe zan samar wa nawa gidan shi ma?"
31Sai Laban yace, "Me zan biya ka?" Yakubu yace, "Ba zaka bani komai ba. Idan zaka yi wannan domina, zan sake ciyar da dabbobinka in kiwata su kuma.32Bari in ratsa cikin dukkan dabbobinka a yau, zan ware daga cikin su duk wasu tumaki dabbare-dabbare da masu ɗigo, da waɗanda ke baƙaƙe daga cikin tumakin, da masu ɗigo da kyalloli daga cikin awakin. Waɗannan ne zasu zama ladana.
33Amincina zai yi shaida game da ni daga bisani, sa'ad da zaka zo ka duba ladana. Duk wadda ba kyalla ba ce ko mai ɗigo daga cikin awaki, da baƙa daga cikin tumaki, duk wadda a ka samu a wurina, a ɗauke shi a matsayin sata."34Laban yace, "Na yarda. Bari ya kasance bisa ga maganarka."
35A wannan rana Laban ya ware dukkan bunsurai masu zãne da masu ɗigo, da dukkan awaki kyalloli da masu ɗigo, duk wata mai fari a jikinta, da dukkan baƙaƙe daga cikin tumaki, ya kuma bayar da su cikin hannun 'ya'yansa.36Laban kuma ya sa tafiya ta kwana uku tsakaninsa da Yakubu. Sai Yakubu ya ci gaba da kiwon sauran dabbobin Laban.
37Sai Yakubu ya ɗauko ɗanyun tsabgun auduga, da rassan itacen almond da rassan itacen durumi, ya kuma fera fararen zãne a kan su, ya sanya fararen itatuwan dake cikin ƙiraren su bayyana.38Daga nan ya jera ƙiraren da ya feffere a gaban dabbobin, a gaban kwamamen ruwa in da suke zuwa su sha. Suna ɗaukar ciki sa'ad da suka zo shan ruwa.
39Dabbobin suka yi ta barbara a gaban ƙiraren; dabbobin kuma suka yi ta haihuwar 'ya'yai masu zãne, da kyalloli, da masu ɗigo.40Yakubu ya ware waɗannan 'yan raguna, amma ya sanya sauran su fuskanci dabbobin masu zãne da dukkan baƙaƙen tumaki a garken Laban. Daga nan sai ya ware nasa dabbobin domin kansa kaɗai ba ya kuma haɗa su tare da dabbobin Laban ba.
41A duk sa'ad da ƙarfafan tumakin ke barbara, sai Yakubu ya shimfiɗa ƙiraren nan a cikin kwamamen ruwan nan a gaban idanun dabbobin, saboda su ɗauki ciki a tsakiyar ƙiraren.42Amma idan dabbobi marasa ƙarfi daga cikin garken suka zo, ba ya sanya ƙiraren a gabansu. Sai ya zama dabbobin marasa ƙarfi na Laban ne, ƙarfafan kuma na Yakubu ne.
43Mutumin ya zama wadatacce sosai. Yana da manyan garkuna, bayi mata da bayi maza, da raƙuma da jakuna.

31

1Yanzu Yakubu ya ji maganganun 'ya'yan Laban maza, cewa sun ce, "Yakubu ya ɗauke dukkan abin dake na mahaifinmu, kuma daga mallakar mahaifinmu ne ya samo dukkan wannan dukiyar."2Yakubu ya kalli yanayin fuskar Laban. Ya ga cewa halinsa zuwa gare shi ya canza.3Daga nan Yahweh ya cewa Yakubu, "Ka koma ƙasar ubanninka da danginka, zan kuma kasance tare da kai."

4Yakubu ya aika a ka kira Rahila da Liya zuwa saura a garkensa5ya kuma ce masu, "Na ga halin mahaifinku zuwa gare ni ya canza, amma Allah na mahaifina yana tare da ni.6Kun san cewa da dukkan karfina ne na bautawa mahaifinku.
7Mahaifinku ya ruɗe ni ya canza ladana sau goma, amma Allah bai ba shi damar cutar da ni ba.8Idan ya ce, "Dabbobin kyalloli zasu zama ladanka,' daga nan dukkan garken suka haifi jarirai kyalloli. Idan ya ce, "Ma su zãne zasu zama ladanka,' daga nan dukkan garken suka haifi 'ya'ya masu zãne.9Ta wannan hanya Allah ya ɗauke dabbobin mahaifinku ya kuma bayar da su a gare ni.
10Sau ɗaya a lokacin yin barbara, na gani a mafarki cewa bunsuran na barbara da dabbobin. Bunsuran masu zãne ne, da kyalloli, da masu ɗigo.11Mala'ikan Allah yace da ni a cikin mafarkin, 'Yakubu.' Na ce, 'Ga ni nan.'
12Ya ce, 'Ka ɗaga idanunka ka ga dukkan bunsuran dake barbara da dabbobin. Masu zãne ne, da kyalloli, da masu ɗigo, gama na ga dukkan abin da Laban yake yi maka.13Ni ne Allah na Betel, in da ka yi wa ginshiƙi shafewa, in da ka ɗaukar mani wa'adi. Yanzu ka tashi ka bar wannan ƙasar ka kuma koma ƙasar haihuwarka."'
14Rahila da Liya suka amsa suka ce masa, "Akwai kuma wani rabo ko gãdo dominmu a gidan mahaifinmu?15Ba kamar bãre ya maida mu ba? Gama ya sayar da mu kuma ya lanƙwame kuɗinmu gabaɗaya.16Domin dukkan arzikin da Allah ya ɗauke daga wurin mahaifinmu yanzu na mu ne da 'ya'yanmu. To yanzu duk abin da Allah yace maka, sai ka yi."
17Daga nan Yakubu ya tashi ya ɗora 'ya'yansa da matayensa bisa raƙumma.18Ya kora dukkan dabbobinsa gaba da shi, tare da dukkan kaddarorinsa, har da dabbobin da ya samu a Faddan Aram. Daga nan ya kama tafiya zuwa wurin mahaifinsa Ishaku a cikin ƙasar Kan'ana.
19Sa'ad da Laban ya tafi yi wa tumakinsa sausaya, Rahila ta ɗauke allolin gidan mahaifinta.20Yakubu shi ma ya ruɗi Laban Ba'aramiye, ta wurin ƙin gaya masa cewa zai tashi.21Sai ya tsere da dukkan abin da yake da shi, nan da nan kuma ya wuce ƙetaren Kogi, ya kuma doshi zuwa ƙasar tudu ta Giliyad.
22A rana ta uku a ka gaya wa Laban cewa Yakubu ya gudu.23Sai ya ɗauki danginsa ya kuma bi shi na tsawon tafiyar kwana bakwai. Ya sha kansa a ƙasar tudu ta Giliyad.
24Sai Allah ya zo wurin Laban Ba'aramiye a cikin mafarki da dare ya kuma ce masa, "Ka yi hankali kada kayi magana da Yakubu mai kyau ko marar kyau."25Laban ya sha kan Yakubu. Yanzu Yakubu ya kafa rumfarsa a ƙasar tudu. Laban shi ma ya kafa sansani tare da danginsa a ƙasar tudu ta Giliyad.
26Laban ya cewa Yakubu, "Mene ne ka yi, da ka ruɗe ni ka kuma ɗauke 'ya'yana mata kamar kamammun yaƙi?27Meyasa ka tsere a asirce ka kuma yi mani dabara ba ka kuma gaya mani ba? Da na sallame ka da biki da waƙe-waƙe, tare da tambari da garayu.28Ba ka bar ni na yi sumbar sallama ga jikokina da 'ya'yana ba. Yanzu ka aikata wawanci.
29A cikin ikona ne in cutar da kai, amma Allah na mahaifinka ya yi magana da ni a daren da ya wuce ya ce, 'Ka yi hankali kada ka yi magana da Yakubu mai kyau ko marar kyau.'30Yanzu ka gudu saboda kana marmarin ka koma gidan mahaifinka. Amma me ya sa ka sace allolina?"
31Yakubu ya amsa kuma ya ce wa Laban, "Saboda na ji tsoro kuma na yi tunanin za ka karɓe 'ya'yanka mata da ƙarfi daga gare ni sai na gudu a asirce.32Duk wanda ya sace allolinka ba zai ci gaba da rayuwa ba. A gaban dangoginmu, ka tantance abin da ke naka tare da ni ka ɗauka." Gama Yakubu bai san cewa Rahila ta sace su ba.
33Laban ya shiga cikin rumfar Yakubu, cikin rumfar Liya, da cikin rumfar bayi matan biyu, amma bai gan su ba. Ya fita daga rumfar Liya ya shiga cikin rumfar Rahila.
34A she Rahila ta ɗauki allolin gidan, ta sanya su a sirdin raƙumi, ta kuma zauna a bisansu. Laban ya bincike rumfar gabaɗaya, amma bai same su ba.35Ta ce wa mahaifinta, "Kada ka ji haushi, shugabana, cewa ba zan iya tashi ba a gabanka, domin ina cikin al'adata." Sai ya bincike amma bai ga allolin gidansa ba.
36Yakubu ya husata ya yi gardama da Laban. Ya ce masa, "Mene ne laifi na? Mene ne zunubi na, da ka runtumo ni da zafi?37Gama ka duba dukkan mallakata. Me ka samu daga dukkan kayayyakin gidanka? Ka fito da su yanzu a gaban dangoginmu, sai su shar'anta a tsakanin mu biyu.
38Shekaru ashirin ina tare da kai. Tumakinka da awakinka ba su yi ɓarin ciki ba, ban kuma ci wani rago ba daga garkunanka.39Abin da bisashe suka yayyage ban kawo maka ba. Maimako, na ɗauki asararsa. Ko yaushe kana sa in biya duk wata dabbar da ta bace, ko wadda a ka sace da rana ko wadda a ka sace da dare.40Nan ni ke; da rana zafi na cinye ni, da dare cikin sanyin dusar ƙanƙara; na yi tafiya kuma babu barci.
41Waɗannan shekaru ashirin ina cikin gidanka. Na yi maka aiki shekaru sha huɗu domin 'ya'yanka biyu mata, shekaru shida kuma domin dabbobinka. Ka canza ladana sau goma.42Idan ba domin Allah na mahaifina, Allah na Ibrahim, da wanda Ishaku ke tsoro, yana tare da ni ba, tabbas da yanzu ka kore ni hannu wofi. Allah ya dubi tsanantawata da aiki tuƙuru dana yi, ya kuma tsauta ma ka a daren jiya."
43Laban ya amsa ya ce wa Yakubu, "'Ya'yan mata 'ya'yana ne, jikokin jikokina ne, dabbobin kuma dabbobina ne. Dukkan abin da kake gani nawa ne. Amma me zan iya yi a yau game da waɗannan 'ya'ya matan nawa, ko kuma game da 'ya'yansu da suka haifa?44To yanzu, bari mu ɗauki alƙawari, kai da ni, bari kuma ya zama domin shaida tsakanin kai da ni."
45Sai Yakubu ya ɗauki dutse ya kuma dasa shi a matsayin ginshiƙi.46Yakubu ya cewa danginsa, "Ku tattara duwatsu." Sai suka ɗebo duwatsu suka tattara su.47Laban ya kira shi Yagar Saha Duta, amma Yakubu ya kira shi Galid.
48Laban yace, "Wannan tarin shaida ne tsakani na da kai a yau." saboda haka a ka kira sunansa Galid.49A na kuma kiransa Mizfa, saboda Laban yace, "Bari Yahweh ya duba tsakanin ka da ni, yayin da muka ɓace daga juna.50Idan ka wulaƙanta 'ya'yana mata, ko kuma ka auri wasu matan baya ga 'ya'ya na, ko da yake babu wanda ke tare da mu, duba, Allah ne shaida tsakanin ka da ni."
51Laban ya cewa Yakubu, "Dubi wannan tarin, ka kuma dubi ginshiƙin, wanda na kafa tsakanin ka da ni.52Wannan tarin shaida ne, ginshiƙin kuma shaida ne, cewa ba zan ƙetare gaba da wannan tarin ba zuwa gare ka, kai kuma ba zaka ƙetare gaba da wannan tarin ba da wannan ginshiƙin zuwa gare ni ba, domin cutarwa.53Bari Allah na Ibrahim, da allahn Naho, da allolin mahaifinsu, su shar'anta tsakaninmu." Yakubu ya rantse da tsoron mahaifinsa Ishaku.
54Yakubu ya miƙa hadaya a bisa tsaunin ya kuma kira danginsa su ci abinci. Suka ci suka zauna tsawon dare a tsaunin.55Tun da sassafe Laban ya tashi, ya sumbaci jikokinsa da 'ya'yansa mata ya albarkace su. Daga nan Laban ya tafi ya koma gida.

32

1Yakubu shima ya tafi hanyarsa, mala'ikun Allah suka same shi.2Sa'ad da Yakubu ya gan su, ya ce, "Wannan sansanin Allah ne." sai ya kira sunan wannan wuri Mahanayim.

3Yakubu ya aiki manzanni gaba da shi zuwa ga ɗan'uwansa Isuwa a cikin ƙasar Seyir, a cikin lardin Idom.4Ya dokace su, cewa, "Ga abin da zaku cewa shugabana Isuwa: Ga abin da bawanka Yakubu yace: 'Ina zaune tare da Laban, na kuma yi jinkirin dawowata har zuwa yanzu.5Ina da shanu, da jakkai, da garkunan tumaki, da awaki, bayi maza da bayi mata. Na aiko da wannan saƙon ga shugabana, domin in sami tagomashi a idanunka."'
6Manzannin suka dawo wurin Yakubu suka kuma ce, "Munje wurin ɗan'uwanka Isuwa. Yana zuwa ya same ka, da mutane ɗari huɗu tare da shi."7Daga nan Yakubu ya tsorata kuma ya ji haushi. Sai ya raba mutanen dake tare da shi ya yi sansani biyu, da garkunan tumaki, da awaki, da garkunan shanu, da raƙumma.8Ya ce, "Idan Isuwa ya zo ga sansani ɗaya ya kawo mana hari, daga nan sansanin da ya rage zasu kuɓuce."
9Yakubu yace, "Allah na mahaifina Ibrahim, da Allah na mahaifina Ishaku, Yahweh, wanda ya ce mani, 'Ka koma ga ƙasarka da danginka, zan kuma wadata ka,'10Ban cancanci dukkan ayyukanka na alƙawarin aminci ba da dukkan yarda da ka yi domin bawanka ba. Domin da sandana kawai na ƙetare wannan Yodan, yanzu kuma na zama sansanai biyu.
11Ina roƙonka ka cece ni daga hannun ɗan'uwana, daga hannun Isuwa, domin ina jin tsoronsa, cewa zai kawo mani hari tare da iyaye matan da 'ya'yan.12Amma ka ce, 'Babu shakka zan sa ka wadata. Zan maida zuriyarka kamar rairayin teku, waɗanda ba za a iya lissafawa ba domin yawansu."'
13Yakubu ya zauna nan a wannan daren. Ya ɗauki wasu daga cikin abin da yake da su a matsayin kyauta domin Isuwa, ɗan'uwansa:14awaki ɗari biyu da bunsuru ashirin, tumaki ɗari biyu da raguna ashirin,15raƙuma talatin masu shayarwa da 'ya'yansu, shanu arba'in, bijimai goma, jakkai mata ashirin da jakkai maza goma.16Waɗannan ya bayar dasu cikin hannun bayinsa, kowanne garke daban. Ya cewa bayinsa, "Ku tafi gaba da ni, ku sanya tazara tsakanin kowanne garken."
17Ya umarci bawa na farko, cewa, "Idan Isuwa ɗan'uwana ya gamu da kai ya tambaye ka, cewa, 'Kai na wane ne? Ina za ka je? Dabbobin wane ne waɗannan da ke gabanka?'18Daga nan za ka ce, 'Na bawanka ne Yakubu. Kyauta ce a ka aiko wa shugabana Isuwa. Duba, shi ma yana zuwa bayanmu."'
19Yakubu ya sake bada umarnai ga ƙungiya ta biyu, ta uku, da dukkan mutanen da suka bi garkunan. Ya ce, "Zaku faɗi abu iri ɗaya ga Isuwa idan kuka same shi.20Tilas kuma ku ce, 'Bawanka Yakubu yana zuwa bayanmu."' Gama ya yi tunani, "Zan tausar da shi da kyaututtukan da nake aikawa da su a gabana. Sai daga baya, sa'ad da zan gan shi, wataƙila zai karɓe ni."21Sai kyaututtukan suka tafi gaba da shi. Shi kuwa da kansa ya tsaya a wannan daren a cikin sansani.
22Yakubu ya tashi da daddare, ya kuma ɗauki matayensa biyu, da matayensa barori su biyu, da 'ya'yansa maza sha ɗaya. Ya aika da su ƙetaren kududdufin Yabbok.23Ta wannan hanyar ya aika da su ƙetaren rafin tare da dukkan mallakarsa.
24A ka bar Yakubu shi kaɗai, wani mutum kuwa ya yi kokowa da shi har wayewar gari.25Sa'ad da mutumin ya ga cewa ba zai kayar da shi ba, sai ya mazge shi a kwankwaso. Sai kwankwason Yakubu ya goce sa'ad da yake kokowa da shi.26Mutumin yace, "Bari in tafi, domin gari yana wayewa." Yakubu yace, "Ba zan bar ka ka tafi ba sai ka albarkace ni."
27Mutumin yace masa, "Yayã sunanka?" Yakubu yace, "Yakubu."28Mutumin yace, "Ba za a sake kiran sunanka Yakubu ba, amma Isra'ila. Gama ka yi gwagwarmaya tare da Allah tare da mutane ka kuma yi nasara."
29Yakubu yace masa, "Ina roƙon ka, ka faɗi mani sunanka." Ya ce, "Meyasa kake tambayar sunana?" Daga nan ya albarkace shi a wurin.30Yakubu ya kira sunan wurin Feniyel, gama ya ce, "Na ga Allah fuska da fuska, kuma rayuwata ta kuɓuta."
31Rana ta taso bisa Yakubu sa'ad da yake wuce Feniyel. Yana ɗangyashi saboda kwankwasonsa.32Shi ya sanya har wa yau mutanen Isra'ila ba su cin jijiyoyin kwankwaso waɗanda suke mahaɗin kwankwaso, saboda mutumin ya yi wa jijiyoyin rauni sa'ad da ya sa kwankwason Yakubu ya goce.

33

1Yakubu ya hango, kuma, duba, Isuwa na zuwa, tare da shi kuma mutane ɗari huɗu. Yakubu ya raba 'ya'yan tsakanin Liya, Rahila, da matayen biyu barori.2Daga nan ya sanya matayen barori da 'ya'yansu a gaba, a biye kuma Liya da 'ya'yanta, a biye kuma Rahila da Yosef na ƙarshen su dukka.3Shi da kansa kuma ya tafi gaba da su. Ya rusuna zuwa ƙasa sau bakwai, har sai da ya zo kusa da ɗan'uwansa.

4Isuwa ya rugo ya same shi, ya rungume shi, ya rungumi wuyansa, ya sumbace shi kuma. Daga nan suka yi kuka.5Sa'ad da Isuwa ya hanga, sai ya ga matayen da 'ya'yan. Ya ce, "Su wane ne waɗannan mutanen tare da kai?" Yakubu yace, "'Ya'yan da Allah ta wurin alherinsa ya ba bawanka ne."
6Daga nan bayi matan suka zo gaba tare da 'ya'yansu, suka kuma rusuna.7Sai Liya ita ma da 'ya'yanta suka zo gaba suka rusuna. A ƙarshe kuma Yosef da Rahila suka zo gaba suka rusuna.8Isuwa yace, "Mene ne kake nufi da dukkan waɗannan ƙungiyoyi da na tarar?" Yakubu yace, "Domin in sami tagomashi a gaban shugabana ne."
9Isuwa yace, "Ina da isassu, ɗan'uwana. Ka ajiye abin da kake da shi domin kanka."10Yakubu yace, "A'a, ina roƙon ka, idan na sami tagomashi a idanunka, to ka karɓi kyautata daga hannuna, gama babu shakka, na ga fuskar ka, kuma kamar ganin fuskar Allah ne, kuma ka karɓe ni.11Ina roƙon ka ka karɓi kyautata da a ka kawo maka, saboda Allah ya aiwatar da alheri zuwa gare ni, saboda kuma ina da isassu." Haka nan Yakubu ya lallashe shi, Isuwa kuma ya karɓe su.
12Daga nan Isuwa yace, "Mu kama hanya. Zan tafi gaba kafin kai."13Yakubu yace masa, "Shugabana yasan cewa yaran ƙanana ne, kuma tumakin da garken dabbobin suna renon ƙananansu. Idan a ka kora su da ƙarfi a rana ɗaya, dukkan dabbobin zasu mutu.14Ina roƙon ka bari shugabana ya tafi gaba da bawansa. Zan yi tafiya a hankali, bisa ga saurin dabbobin dake a gabana, bisa kuma ga saurin yaran, har sai na zo ga shugabana a Seyir."
15Isuwa yace, "Bari in bar maka wasu daga cikin mutane na dake tare da ni." Amma Yakubu yace, "Meyasa zaka yi haka? Bari in sami tagomashi a idanun ubangijina."16Sai Isuwa a wannan ranar ya fara tafiya bisa hanyarsa ta komawa Seyir.17Yakubu ya tafi Sukkot, ya gina wa kansa gida, ya yi wa dabbobinsa kuma wurin zama. Saboda haka sunan wannan wuri ana kiransa Sukkot.
18Sa'ad da Yakubu ya zo daga Faddan Aram, ya isa lafiya a birnin Shekem, wanda ke a cikin ƙasar Kan'ana. Ya kafa sansani kusa da birnin.19Daga nan ya sayi filin da ya kafa rumfarsa daga hannun 'ya'yan Hamo, mahaifin Shekem, a kan jimillar azurfa ɗari.20A nan ya kafa bagadi, ya kuma kira shi El Elohi Isra'ila.

34

1Sai Dinah, ɗiyar Liya wadda ta haifawa Yakubu, ta fita ta tafi wurin 'yanmatan ƙasar.2Shekem ɗan Hamo Bahibiye, yariman ƙasar, ya ganta ya kuma cafke ta, ya ɓata ta, ya kuma kwana da ita.3Ya shaƙu da Dinah, ɗiyar Yakubu. Ya ƙaunaci yarinyar, ya kuma yi mata magana mai taushi.

4Shekem ya yi magana da mahaifinsa, cewa, "Ka samo mani wannan yarinyar a matsayin mata."5Yanzu Yakubu ya ji cewa ya lalata ɗiyarsa Dina. 'Ya'yansa kuma na tare da dabbobinsa a saura, sai Yakubu ya kame bakinsa har sai da su ka zo.
6Hamo mahaifin Shekem ya tafi wurin Yakubu domin ya yi magana da shi.7'Ya'yan Yakubu suka dawo daga saura sa'ad da suka ji batun al'amarin. Mutanen ransu ya ɓaci. Suka fusata sosai saboda ya kunyatar da Isra'ila ta wurin tilasta kansa bisa ɗiyar Yakubu, domin bai kamata a aiwatar da irin haka ba.
8Hamo ya yi magana da shi, cewa, "‌Ɗana Shekem na ƙaunar ɗiyarka. Ina roƙon ka. ka bayar da ita a gare shi a matsayin mata.9Ku yi auratayya da mu, ku bayar da 'ya'yanku mata a gare mu, ku kuma ɗauki 'ya'yanmu mata domin kanku.10Zaku zauna tare da mu, za a buɗe ƙasar kuma a gare ku domin ku zauna ku kuma yi sana'a a ciki, ku kuma mallaki kaddarori."
11Shekem yace wa mahaifinta da 'yan'uwanta maza, "Bari in sami tagomashi a idanunku, duk kuma abin da kuka ce mani zan bayar.12Ku tambaye ni komai yawan sadakin da kyautar da kuke so, kuma zan bayar da duk abin da kuka ce, amma dai ku bani yarinyar a matsayin mata."13'Ya'yan Yakubu suka amsa wa Shekem da Hamo mahaifinsa tare da zamba, saboda Shekem ya ɓata Dina 'yar'uwarsu.
14Suka ce masu, "Ba za mu iya yin wannan abu ba, mu bayar da 'yar'uwarmu ga duk wani wanda ba shi da kaciya; domin zai zama abin kunya a gare mu.15Sai dai a kan wannan matakin kaɗai za mu yarda da ku: Idan zaku zama masu kaciya kamar mu, idan kowanne namiji a cikin ku an yi masa kaciya.16Daga nan ne za mu bayar da 'ya'yanmu mata a gare ku, mu kuma zamu ɗauki 'ya'yanku mata a gare mu, mu kuma zauna daku mu zama mutane ɗaya.17Amma idan baku saurare mu ba kuka zama masu kaciya, daga nan zamu ɗauki 'yar'uwarmu kuma za mu tashi."
18Maganganunsu suka gamshi Hamo da ɗansa Shekem.19Saurayin bai ɓata lokaci ba wurin yin abin da suka ce, saboda yana jin daɗin ɗiyar Yakubu, saboda kuma shi ne taliki mafi daraja a dukkan gidan mahaifinsa.
20Hamo da ɗansa Shekem suka tafi ƙofar birninsu suka kuma yi magana da mutanen birninsu, cewa,21"Mutanen nan suna zaman salama da mu, bari su zauna cikin ƙasar su kuma yi sana'a a ciki domin, tabbas, ƙasar na da isasshen girma domin su. Bari mu ɗauki 'ya'yansu mata a matsayin matayen aure, bari kuma mu bayar da 'ya'yanmu mata a gare su.
22A wannan matakin kaɗai mutanen za su yarda su zauna da mu kuma mu zama mutane ɗaya. Idan a ka yi wa kowanne namiji a cikin mu kaciya, kamar yarda suke da kaciya.23Ba dukkan dabbobinsu da kaddarorinsu - dukkan dabbobinsu zasu zama namu ba? Don haka mu yarda da su, zasu kuma zauna a cikinmu."
24Dukkan mutanen birnin suka saurari Hamo da Shekem, ɗansa. Kowanne namiji a ka yi masa kaciya.25A rana ta uku, sa'ad da suke cikin zafi tukuna, 'ya'yan Yakubu biyu (Simiyon da Lebi 'yan'uwan Dina), kowannen su ya ɗauki takobinsa suka kuma kai hari ga birnin dake da tabbacin tsaro, suka kuma kashe dukkan mazajen.26Suka kashe Hamo da ɗansa Shekem ta kaifin takobi. Suka ɗauke Dina daga gidan Shekem suka yi tafiyar su.
27Sauran 'ya'yan Yakubu suka zo wurin gawawwakin suka washe birnin, saboda mutanen sun ɓata 'yar'uwarsu.28Suka ɗauki garkunan tumakinsu dana awaki, da garkunan shanunsu, da jakkansu, da duk wani abu dake cikin birnin da gonakin dake kewaye tare da29dukkan dukiyarsu. Dukkan 'ya'yayensu da matayensu, suka kame. Suka ma ɗauke kowanne abu dake cikin gidajen.
30Yakubu ya cewa Simiyon da Lebi, "Kun kawo mani matsala, domin kun sa in yi ɗoyi ga mazaunan ƙasar, da Kan'aniyawa da Feriziyawa. Ni kima ne a lissafi. Idan suka tattara kansu tare gãba da ni, su kuma kawo ma ni hari, daga nan zan hallaka, ni da gidana."31Amma Simiyon da Lebi suka ce, "Ya kamata Shekem ya yi da 'yar'uwarmu kamar karuwa?"

35

1Allah ya cewa Yakubu, "Ka tashi, ka nufi sama zuwa Betel, ka kuma zauna a can. Ka ginawa Allah bagadi a wurin, wanda ya bayyana a gare ka sa'ad da kake gujewa Isuwa ɗan'uwanka."2Daga nan Yakubu ya cewa gidansa da dukkan waɗanda ke tare da shi, "Ku fitar da bãƙin alloli dake a tsakaninku, ku tsarkake kanku, ku kuma canza suturarku.3Daga nan mu bar nan, mu nufi sama zuwa Betel. Zan ginawa Allah bagadi a can, wanda ya amsa mani a ranar ƙuncina, kuma ya kasance tare da ni dukkan inda na nufa."

4Sai suka ba Yakubu dukkan bãƙin alloli da suke a hannunsu, da zobban da suke a kunnuwansu. Yakubu ya bizne su a ƙarƙashin rimi dake kusa da Shekem.5Yayin da suke tafiya, Allah ya sanya tsoronsu ya fãɗo a bisa biranen dake kewaye da su, domin haka waɗannan mutane ba su runtumi 'ya'yan Yakubu ba.
6Sai Yakubu ya iso Luz (wato, Betel), wadda ke cikin ƙasar Kan'ana, shi da dukkan mutanen dake tare da shi.7Ya gina bagadi a nan ya kira sunan wurin El Betel, saboda a wurin ne Allah ya bayyana kansa a gare shi, sa'ad da yake gudu daga ɗan'uwansa.8Debora, mai kula da Rebeka, ta mutu. A ka bizne ta a gangare daga Betel ƙarƙashin itacen rimi, domin haka ana kiran wurin Allon Bakut.
9Sa'ad da Yakubu ya zo daga Faddan Aram, Allah ya sake bayyana a gare shi ya kuma albarkace shi.10Allah yace masa, "Sunanka Yakubu, amma ba za a sake kiran sunanka Yakubu ba. Sunanka zai zama Isra'ila ne." Sai Allah ya kira sunansa Isra'ila.
11Allah yace masa, "Ni ne Allah Mai Iko Dukka. Ka hayayyafa ka kuma ruɓanɓanya. ‌Ƙasa da ƙungiyar ƙasashe zasu fito daga gare ka, kuma sarakuna zasu kasance cikin zuriyarka.12‌Ƙasar dana bayar ga Ibrahim da Ishaku, zan bayar a gare ka. Ga zuriyarka bayanka kuma zan bayar da ƙasar."13Allah ya tafi daga gare shi a wurin da ya yi magana da shi.
14Yakubu ya kafa ginshiƙi a wurin da Allah ya yi magana da shi, ginshiƙin dutse. Ya zuba baikon sha a bisansa ya kuma zuba mai a kansa.15Yakubu ya kira sunan wurin inda Allah ya yi magana da shi, Betel.
16Suka kama tafiya daga Betel. Yayin da suke da 'yar tazara daga Efrat, Rahila ta fãra naƙuda. Ta yi naƙuda mai wuya.17Yayin da take cikin azabar naƙuda, unguwar zomar ta ce mata, "Kada ki ji tsoro, domin yanzu za ki sami wani ɗan."18Yayin da take mutuwa, da numfashinta na mutuwa ta raɗa masa suna Ben-Oni, amma mahaifinsa ya kira shi da suna Benyamin.19Rahila ta mutu a ka kuma bizne ta a kan hanyar zuwa Efrat (wato, Betlehem).20Yakubu ya kafa ginshiƙi bisa kabarinta. Shi ne shaidar kabarin Rahila har ya zuwa yau.
21Isra'ila ya ci gaba da tafiya ya kafa rumfarsa a gaba da hasumiyar tsaron garke.22Yayin da Isra'ila ke zaune a wannan ƙasa, Ruben ya kwana da Bilha ƙwarƙwarar mahaifinsa, Isra'ila kuma ya ji labari. Yakubu dai na da 'ya'ya maza sha biyu.
23'Ya'yansa maza daga Liya su ne Ruben, ɗan fãrin Yakubu, da Simiyon, Lebi, Yahuda, Issaka, da Zebulun.24'Ya'yansa maza daga Rahila su ne Yosef da Benyamin.25'Ya'yansa maza daga Bilha, baiwar Rahila, sune Dan da Naftali.
26'Ya'ya maza na Zilfa, baiwar Liya, su ne Gad da Asha. Dukkan waɗannan 'ya'yan Yakubu ne waɗanda a ka haifa masa a Faddan Aram.27Yakubu ya zo wurin Ishaku a Mamri a Kiriyat Arba (ita ce dai Hebron), inda Ibrahim da Ishaku suka zauna.
28Ishaku ya rayu shekaru ɗari da tamanin.29Ishaku ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu, a ka kuma tattara shi ga kakanninsa, tsohon mutum cike da kwanaki. Isuwa da Yakubu, 'ya'yansa, suka bizne shi.

36

1Waɗannan ne zuriyar Isuwa (wanda kuma a ke kira Idom).2Isuwa ya ɗauki matayensa daga Kan'aniyawa. Waɗannan ne matayensa: Ada ɗiyar Elon Bahittiye; Oholibama ɗiyar Ana, jikar Zibiyon Bahibbiye;3da Bashemat, ɗiyar Isma'il, 'yar'uwar Nebayot.

4Ada ta haifi Elifaz da Isuwa, Bashemat kuma ta haifi Ruwel.5Oholibama kuma ta haifi Yewish, Yalam da Kora. Waɗannan ne 'ya'yan Isuwa waɗanda a ka haifa masa a ƙasar Kan'ana.
6Isuwa ya ɗauki matayensa, da 'ya'yansa maza, da 'ya'yansa mata, da mutanen dake gidansa, da dabbobinsa - dukkan dabbobinsa, da dukkan mallakarsa, wadda ya tattara a ƙasar Kan'ana, ya tafi cikin wata ƙasa nesa da ɗan'uwansa Yakubu.7Ya yi haka ne saboda mallakarsu ta yi yawan da ba zasu iya zama tare ba. ‌Ƙasar da suka zauna ba za ta iya ɗaukar su ba saboda yawan dabbobinsu.8Sai Isuwa, wanda kuma a ka sa ni da Idom, ya zauna a ƙasar tudu ta Seyir.
9Waɗannan ne zuriyar Isuwa, kakan Idomawa a ƙasar tudu ta Seyir.10Waɗannan ne sunayen 'ya'ya maza na Isuwa: Elifaz ɗan Ada, matar Isuwa; Ruwel ɗan Bashemat, matar Isuwa.11'Ya'ya maza na Elifaz sune Teman, Omar, Zefo, Gatam, da Kenaz.12Timna, wata ƙwarƙwarar Elifaz, ɗan Isuwa, ta haifi Amalek. Waɗannan ne jikoki maza na Ada, matar Isuwa.
13Waɗannan ne 'ya'ya maza na Ruwel: Nahat, Zera, Shamma, da Mizza. Waɗannan ne jikoki maza na Bashemat, matar Isuwa.14Waɗannan ne 'ya'ya maza na Oholibama, matar Isuwa, wadda ita ce ɗiyar Ana da jikar Zibiyon. Ta haifa wa Isuwa Yewish, Yalam, da Kora.
15Waɗannan ne kabilu a cikin zuriyar Isuwa: Zuriyar Elifaz, ɗan fãrin Isuwa: Teman, Omar, Zefo, Kenaz,16Kora, Gatam, da Amalek. Waɗannan ne dangogin da suka fito daga Elifaz a ƙasar Idom. Su ne jikoki maza na Ada.
17Waɗannan ne dangogi daga Ruwel, ɗan Isuwa: Nahat, Zera, Shamma, Mizza. Waɗannan ne dangogin da suka fito daga Ruwel a cikin ƙasar Idom. Su ne jikokin Bashemat, matar Isuwa.18Waɗannan ne dangogin Oholibama, matar Isuwa: Yewish, Yalam, Kora. Waɗannan ne dangogin da suka fito daga matar Isuwa Oholibama, ɗiyar Ana.19Waɗannan ne 'ya'ya maza na Isuwa (wanda a ka sa ni da Idom), kuma waɗannan ne hakimansu.
20Waɗannan ne 'ya'ya maza na Seyir Bahorite, mazauna ƙasar: Lotan, Shobal, Zibiyon, Ana,21Dishon, Eza, da Dishan. Waɗannan ne dangogin Horitiyawa, mazauna Seyir a cikin ƙasar Idom.22'Ya'ya maza na Lotan su ne Hori da Heman, kuma Timna 'yar'uwar Lotan ce.
23Waɗannan ne 'ya'ya maza na Shobal: Alban, Manahat, Ebal, Shefo, da Onam.24Waɗannan ne 'ya'ya maza na Zibiyon: Aiya da Ana. Wannan Ana shi ne ya gano maɓulɓular ruwa mai zafi a jeji, yayin da yake kiwon jakkan Zibiyon mahaifinsa.
25Waɗannan ne 'ya'yan Ana: Dishon da Oholibama, ɗiyar Ana.26Waɗannan ne 'ya'ya maza na Dishon: Hemdan, Eshban, Itran, da Keran.27Waɗannan ne 'ya'ya maza na Eza: Bilhan, Za'aban, da Akan.28Waɗannan ne "ya'ya maza na Dishan: Uz da Aran.
29Waɗannan ne dangogin Horitiyawa: Lotan, Shobal, Zibiyon, da Ana,30Dishon, Eza, Dishan: Waɗannan ne dangogin Horitiyawa, bisa ga dangoginsu da aka lissafa a ƙasar Seyir.
31Waɗannan ne sarakunan da suka yi mulki a ƙasar Idom kafin wani sarki ya yi mulki a bisa Isra'ilawa:32Bela ɗan Beyor, ya yi mulki a Idom, sunan birninsa kuma Dinhaba ne.33Sa'ad da Bela ya mutu, daga nan Yobab ɗan Zera da Bozra, ya yi mulki a gurbinsa.
34Sa'ad da Yobab ya mutu, Husham wanda ke daga ƙasar Temanawa, ya yi mulki a gurbinsa.35Sa'ad da Husham ya mutu, Hadad ɗan Bedad wanda ya ci Midiyanawa da yaƙi a ƙasar Mowab, ya yi mulki a gurbinsa. Sunan birninsa Abit ne.36Sa'ad da Hadad ya mutu, daga nan Samla na Masreka ya yi mulki a gurbinsa.
37Sa'ad da Samla ya mutu, daga nan Shawul na Rehobot ta gefen kogi ya yi mulki a gurbinsa.38Sa'ad da Shawul ya mutu, daga nan Ba'al Hanan ɗan Akbor ya yi mulki a gurbinsa.39Sa'ad da Ba'al-hanan ɗan Akbo, ya mutu, daga nan Hadar ya yi mulki a gurbinsa. Sunan birninsa Fawu ne. Sunan matarsa Mehetabel, ɗiyar Matred, jikar Me Zahab.
40Waɗannan ne sunayen shugabannin kabilu daga zuriyar Isuwa, bisa ga dangoginsu da lardunansu, bisa ga sunayensu: Timna, Alba, Yetet,41Oholibama, Ela, Finon,42Kenaz, Teman, Mibzar,43Magdiyel, da Iram. Waɗannan ne shugabannin dangogin Idom, bisa ga mazaunansu a cikin ƙasar da suka mallaka. Wannan ne Isuwa, mahaifin Idomawa.

37

1Yakubu ya zauna ƙasar da mahaifinsa ke zama, a cikin ƙasar Kan'ana.2Waɗannan ne al'amura game da Yakubu. Yosef, wanda ke saurayi ɗan shekaru sha bakwai, yana kiwon tumaki da awaki tare da 'yan'uwansa. Yana tare da 'ya'yan Bilha da 'ya'yan Zilfa, matan mahaifinsa. Yosef yana kawo labarai marasa daɗi game da su wurin mahaifinsu.

3Isra'ila dai yana ƙaunar Yosef fiye da dukkan 'ya'yansa maza saboda shi ɗan tsufansa ne. Ya yi masa wata riga mai kyau.4'Yan'uwansa suka ga cewa mahaifinsu na ƙaunarsa fiye da dukkan 'yan'uwansa maza. Suka ƙi jininsa, kuma ba su maganar alheri da shi.
5Yosef ya yi wani mafarki, ya kuma gaya wa 'yan'uwansa game da mafarkin. Suka ƙara ƙin jininsa.6Yace masu, "Ina roƙon ku da ku saurari wannan mafarkin da na yi.
7Duba, muna ta ɗaurin dammunan hatsi a gona, gashi kuwa, sai damina ya tashi ya kuma tsaya a tsaye, sai kuma, dammunanku suka zo a kewaye suka rusuna wa damina."8'Yan'uwansa suka ce masa, "Lallai zaka yi sarauta a kanmu? Lallai kuwa zaka yi mulki a kanmu?" Suka ƙara ƙin jininsa saboda mafarkansa saboda kuma maganganunsa.
9Ya sake yin wani mafarkin ya gaya wa 'yan'uwansa. Yace, "Duba, Na yi wani mafarkin: Rana da wata da taurari sha ɗaya sun rusuna mani."10Ya gaya wa mahaifinsa kamar yadda ya gaya wa 'yan'uwansa, mahaifinsa kuma ya tsauta masa. Yace masa, "Wanne irin mafarki ne ka yi haka? Ko hakika mahaifiyarka da Ni da 'yan'uwanka maza za mu zo mu rusuna ƙasa a gare ka?"11'Yan'uwansa suka yi kishin sa, amma mahaifinsa ya ajiye al'amarin a rai.
12'Yan'uwansa suka tafi kiwon dabbobin mahaifinsu a Shekem.13Isra'ila ya cewa Yosef, "Ba 'yan'uwanka na kiwon dabbobin a Shekem ba? Zo, zan kuma aike ka wurin su." Yosef yace masa, "Na shirya."14Yace masa, "Ka tafi yanzu, ka duba ko 'yan'uwanka na lafiya ko dabbobin kuma na lafiya, sai ka kawo mani magana." Sai Yakubu ya aike shi daga Kwarin Hebron, Yosef kuma ya tafi Shekem.
15Wani mutum ya sami Yosef. Duba, Yosef yana ta gararanba a saura. Mutumin ya tambaye shi, "Me kake nema?"16Yosef yace, "Ina neman 'yan'uwana ne. Ka gaya mani, ina roƙon ka, inda suke kiwon dabbobin."17Mutumin yace, "Sun bar nan wurin, domin na ji suna cewa, 'Bari mu tafi Dotan."' Yosef ya bi bayan 'yan'uwansa ya kuma same su a Dotan.
18Suka hange shi daga nesa, kafin kuma ya iso kusa da su, suka shirya makirci gãba da shi su kashe shi.19'Yan'uwansa suka ce wa junansu, "Duba, mai mafarkin nan yana tafe.20Ku zo yanzu, saboda haka, bari mu kashe shi mu kuma jefa shi cikin ɗaya daga cikin ramukan. Za mu ce, 'Naman jeji ya cinye shi.' Za mu ga abin da zai fãru da mafarkansa."
21Ruben ya ji labari, kuma ya ceto shi daga hannunsu. Ya ce, "Kada mu ɗauki ransa."22Ruben yace masu, "Kada ku zubar da jini. Ku jefa shi cikin wannan ramin dake cikin jeji, amma kada ku ɗora hannu a kansa" - domin ya ceto shi daga hannunsu ya maida shi wurin mahaifinsa.
23Sai ya kasance da Yosef ya iso wurin 'yan'uwansa, suka tuɓe masa kyakkyawar rigarsa.24Suka ɗauke shi suka jefa shi cikin ramin. Ramin ba komai a ciki babu ma ruwa a ciki.
25Suka zauna, su ci abinci. Suka ɗaga idanuwansu suka duba, kuma, duba, zangon Isma'ilawa na tafe daga Giliyad, tare da raƙummansu ɗauke da kayan yaji da man ƙanshi da kayan ƙanshi. Suna tafiya zasu kai su Masar.26Yahuda ya cewa 'yan'uwansa, "Ina ribar da ke ciki idan muka kashe ɗan'uwanmu muka kuma rufe jininsa?
27Ku zo, mu sayar da shi ga Isma'ilawa, kada dai mu ɗora hannunmu a kansa. Gama shi ɗan'uwanmu ne, jikinmu." 'Yan'uwansa suka saurare shi.28Midiyawan fatake suna wuce wa. 'Yan'uwan Yosef suka jawo shi, suka fito da shi daga rijiyar. Suka sayar da Yosef ga Isma'ilawa a kan azurfa ashirin. Isma'ilawa suka ɗauki Yosef zuwa cikin Masar.
29Ruben ya dawo ga ramin, kuma, duba, Yosef ba shi cikin ramin. Ya yage tufafinsa.30Ya dawo wurin 'yan'uwansa ya ce, "Yaron ba shi a wurin! Ni kuma, ina zan tafi?"
31Suka yanka akuya, daga nan kuma suka ɗauki rigar Yosef suka tsoma a cikin jinin.32Sa'an nan suka kawo ta wurin mahaifinsu suka ce, "Mun tsinci wannan. Muna roƙon ka, ka duba ko rigar ɗanka ce ko a'a."33Yakubu ya gane ta ya ce, "Rigar ɗana ce. Naman daji ya cinye shi. Babu shakka an yayyaga Yosef gutsu-gutsu."
34Yakubu ya yayyage tufafinsa, ya sanya tsummokara a kwankwasonsa. Ya yi makokin ɗansa kwanaki da yawa.35Dukkan 'ya'yansa maza da 'ya'yansa mata suka tashi domin su ta'azantar da shi, amma ya ƙi ya ta'azantu. Ya ce, "Tabbas zan gangara zuwa Lahira cikin makoki domin ɗana." Mahaifinsa ya yi kuka domin sa.36Midiyawa kuwa suka saida shi a Masar ga Fotifa, wani maƙaddashin Fir'auna, hafsan masu tsaro.

38

1Sai ya kasance a wannan lokaci Yahuda ya bar 'yan'uwansa ya je ya zauna da wani Ba'addulmiye, mai suna Hira.2Ya haɗu da wa ta ɗiyar wani mutum Bakananiye mai suna Shuwa. Ya aure ta ya kuma kwana da ita.

3Ta ɗauki ciki ta sami ɗa, a ka sa masa suna Er.4Ta sake ɗaukar ciki ta sami ɗa. Ta kira sunansa Onan.5Ta sake samun wani ɗan ta kira sunansa Shela. A Kezib ne wurin da ta haife shi.
6Yahuda ya samar wa Er mata, ɗan fãrinsa. Sunanta Tama ne.7Er, ɗan fãrin Yahuda, mugu ne a idanun Yahweh. Yahweh ya kashe shi.
8Yahuda ya cewa Onan, "Ka kwana da matar ɗan'uwanka. Ka yi aikin ɗan'uwan miji a gare ta, ka samar wa ɗan'uwanka ɗa."9Onan ya san cewa ɗan ba zai zama na shi ba. Duk lokacin da ya kwana da matar ɗan'uwansa, sai ya zubar da maniyin a ƙasa domin kada ya samar wa ɗan'uwansa ɗa.10Abin nan da ya yi kuwa mugunta ce a idanun Yahweh. Yahweh ya kashe shi shima.
11Daga nan Yahuda ya cewa Tama, surukarsa, "Ki yi zaman gwauruwa a gidan mahaifinki har sai Shela, ɗana, ya girma." Gama ya ji tsoro, "Shi ma wataƙila ya mutu, kamar 'yan'uwansa." Tama ta tashi ta kuma koma da zama gidan mahaifinta.
12Bayan lokaci mai tsawo, ɗiyar Shuwa, matar Yahuda, ta mutu. Yahuda ya ta'azantu ya kuma tafi wurin sausayar tumakinsa a Timna, shi da abokinsa Hira Ba'addulmiye.13Aka gaya wa Tama, "Duba, surukinki zai tafi Timna domin sausayar tumakinsa."14Sai ta tuɓe tufafin gwaurancinta ta rufe kanta da gyale ta kuma lulluɓe jikinta. Ta zauna a ƙofar Enayim, wadda ke kan hanyar zuwa Timna. Domin ta ga Shela ya girma, amma ba a bayar da ita ba a gare shi a matsayin mata.
15Sa'ad da Yahuda ya ganta ya zaci cewa karuwa ce saboda ta lulluɓe fuskarta.16Ya je wurin ta a bakin hanya ya kuma ce, "Zo, ina roƙon ki bari in kwana da ke" - domin bai san cewa surukarsa ba ce - sai kuma ta ce, "Mezaka bani domin ka kwana da ni?"
17Ya ce, "Zan aiko maki da 'yar akuya daga garke." Ta ce, "Zaka bani diyya har sai ka aiko da ita?"18Ya ce, "Wacce irin diyya zan ba ki?" Ta maida amsa, "Zoben hatiminka da ɗamararka, da sandar dake a hannunka." Ya bayar dasu a gare ta ya kuma kwana da ita, sai ta sami ciki daga gare shi.
19Ta tashi ta yi tafiyarta. Ta tuɓe lulluɓinta ta sanya tufafin gwaurancinta.20Yahuda ya aika da 'yar akuyar ta hannun abokinsa Ba'addulmiye saboda ya karɓo diyyar daga hannun matar, amma bai same ta ba.
21Sai Ba'addulmiyen ya tambayi mutanen dake wurin, "Ina karuwar asiri dake zaune a Enayim a bakin hanya?" Suka ce, "Babu wata karuwar asiri dake zaune a nan."22Ya dawo wurin Yahuda yace, "Ban same ta ba. Kuma, mutanen wurin sun ce, 'Babu wata karuwar asiri dake zaune a nan."'23Yahuda yace, "Bari ta ajiye abubuwan, domin kada mu sha kunya. Tabbas, na aika da 'yar akuyar nan, amma ba ka same ta ba."
24Sai ya kasance bayan wajen wata uku, sai a ka gaya wa Yahuda, "Tama surukarka ta aikata karuwanci, kuma tabbas, ta sami ciki ta haka." Yahuda yace, "Ku kawo ta nan bari a ƙona ta kuma."25Sa'ad da aka fito da ita, sai ta aika wa surukinta da saƙo, "Ta wurin mutumin dake da waɗannan nake da ciki." Ta ce, "Ina roƙon ka da ka gano mani waɗannan na waye, zoben tambarin da ɗamarar da sandar."26Yahuda ya gane su ya kuma ce, "Ta fi ni adalci, tunda ban bayar da ita ba a matsayin mata ga Shela, ɗana." Bai sake kwana da ita ba kuma.
27Sai ya kasance da lokacin haihuwarta ya kai, duba, tagwaye ne ke cikin mahaifarta.28Sai ya kasance a lokacin da take haihuwar ɗaya ya fito da hannunsa waje, unguwar zomar ta ɗauki jan zare ta ɗaura masa a hannu ta kuma ce, "Wannan ne ya fãra fitowa."
29Amma daga nan sai ya maida hannunsa, kuma, duba, sai ɗan'uwansa ya fito farko. Unguwar zomar ta ce, "Ya ya ka faso waje!" Sai aka sa masa suna Ferez.30Daga nan ɗan'uwansa ya fito, wanda yake da jan zare a hannu, aka kuma sa masa suna Zera.

39

1Aka kawo Yosef zuwa Masar. Fotifa, maƙaddashin Fir'auna kuma hafsan masu tsaro kuma Bamasare, ya sawo shi daga Isma'ilawa, waɗanda suka kawo shi nan.2Yahweh yana tare da Yosef ya kuma zama wadataccen mutum. Yana zaune cikin gidan ubangidansa Bamasare.

3Ubangidansa ya ga cewa Yahweh na tare da shi kuma Yahweh na wadata kowanne abu da ya yi.4Yosef ya sami tagomashi a idanunsa. Ya bautawa Fotifa. Fotifa ya maida Yosef shugaban gidansa, da kowanne abu da ya mallaka, ya sanya ƙarƙashin lurarsa.
5Sai ya kasance tun lokacin da ya maida shi shugaba bisa gidansa da bisa kowanne abu da ya mallaka, sai Yahweh ya albarkaci gidan Bamasaren saboda Yosef. Albarkar Yahweh tana bisa kowanne abu da Fotifa yake da shi a cikin gida da gona.6Fotifa ya sanya kowanne abu da yake da shi a ƙarƙashin lurar Yosef. Ba ya buƙatar ya yi tunani game da komai sai dai kawai abincin da zai ci. Shi dai Yosef kyakkyawa ne gwanin sha'awa kuma.
7Sai ya kasance bayan wannan matar ubangidansa ta yi sha'awar Yosef. Ta ce, "Ka kwana da ni."8Amma ya ƙi, ya kuma ce wa matar ubangidansa, "Duba, ubangidana ba ya kulawa da abin da nake yi a cikin gidan nan, kuma ya sanya kowanne abu da yake da shi a ƙarƙashin lura ta.9Babu wanda ya fi ni girma a cikin gidan nan. Bai hana mani komai ba sai dai ke, saboda ke matarsa ce. Ta yaya daga nan zan yi wannan irin babbar mugunta da zunubi gãba da Allah?"
10Ta dinga magana da Yosef rana bayan rana, amma ya ƙi ya kwana da ita ko ya kasance tare da ita.11Sai ya kasance wata rana, Yosef ya shiga cikin gidan domin ya yi aikinsa. Babu ko ɗaya daga cikin mutanen gidan dake cikin gidan.12Ta kama shi ta tufafinsa ta ce kuma, "Ka kwana da ni." Ya bar tufafinsa a hannunta, ya tsere, ya fita waje kuma.
13Sai ya kasance, sa'ad da taga cewa ya bar tufafinsa a cikin hannunta ya kuma tsere waje,14sai ta kira mutanen gidanta ta ce masu, "Duba, Fotifa ya kawo Ba'ibraniye ya wulaƙanta mu. Ya shigo wurina ya kwana da ni, na kuwa yi ihu.15Sai ya kasance sa'ad da ya ji ina ihu, sai ya bar tufafinsa tare da ni, ya tsere, ya kuma fita waje."
16Ta ajiye tufafinsa a kusa da ita har sai da ubangidansa ya zo gida.17Ta faɗi masa wannan bayyani, "Ba'ibraniyen nan bawa wanda ka kawo mana, ya shigo domin ya wulaƙanta ni.18Sai ya kasance sa'ad da nayi ihu, ya bar tufafinsa tare da ni ya kuma tsere waje."
19Sai ya kasance, sa'ad da ya ji bayanin da matarsa ta faɗi masa, "Wannan ne abin da bawanka ya yi mani," sai ya fusata sosai.20Ubangidan Yosef ya ɗauke shi ya saka shi cikin kurkuku, wurin da a ke tsaron 'yan kurkukun sarki. Ya na nan a cikin kurkukun.
21Amma Yahweh na tare da Yosef ya kuma nuna alƙawarin aminci a gare shi. Ya kuma ba shi tagomashi a idanun shugaban kurkukun.22Shugaban kurkukun ya bayar da dukkan 'yan kurkukun dake cikin kurkukun cikin hannun Yosef. Duk abin da suka yi a nan, Yosef ne ke shugabancin sa.23Shugaban kurkuku ba ya kulawa da kowanne abu dake cikin hannunsa, saboda Yahweh na tare da shi. Duk abin da ya yi Yahweh na wadatar da shi.

40

1Sai ya kasance bayan waɗannan abubuwa, mai riƙon ƙoƙon sha na sarkin Masar da mai toye-toye na sarki suka ɓata wa ubangidansu, sarkin Masar rai.2Fir'auna ya ji haushin ofisoshinsa biyu, da shugaban ma su riƙon ƙoƙon sha da shugaban masu toye-toye.3Ya sa aka tsare su a cikin gidan shugaban masu tsaro, a cikin wannan kurkuku inda aka tsare Yosef.

4Shugaban masu tsaron ya miƙa Yosef a gare su, ya kuma yi masu hidima. Suka ci gaba a tsare na wani lokaci.5Dukkan su biyu sai suka yi wani mafarki - mai riƙon ƙoƙon sha da mai toye-toye na sarkin Masar waɗanda ke tsare a kurkukun - kowanne mutum ya yi nasa mafarki a dare ɗaya, kuma kowanne mafarkin da tasa fassarar.
6Yosef ya zo wurin su da safe ya kuma gan su. Duba, suna cikin baƙinciki.7Ya tambayi ofisoshin Fir'auna waɗanda ke tare da shi a tsare a cikin gidan ubangidansa, ya ce, "Meyasa kuke baƙinciki a yau?"8Suka ce masa, "Dukkan mu biyu munyi wani mafarki kuma babu wanda ya iya fassara su." Yosef yace masu, "Fassarori ba ta Allah ba ce?" Ku faɗa mani, ina roƙon ku."
9Shugaban masu riƙon ƙoƙon sha ya gaya wa Yosef mafarkinsa. Ya ce masa, "A cikin mafarkina, duba, itacen inabi na gabana.10A itacen inabin akwai rassa uku. Suka tsiro, suka yaɗu da 'ya'ya nan da nan inabin kuma suka nuna.11‌Ƙoƙon Fir'auna yana hannuna. Na ɗauki 'ya'yan inabin na matse su cikin ƙoƙon Fir'auna, sai kuma na miƙa ƙoƙon cikin hannun Fir'auna."
12Yosef yace masa, "Wannan ce fassarar sa. Rassan uku kwanaki uku ne.13A cikin kwanaki uku Fir'auna zai ɗaga kanka ya kuma mai da kai wurin aikinka. Za ka sanya ƙoƙon Fir'auna cikin hannunsa, kamar dai sa'ad da kake mai riƙon ƙoƙon shansa.
14Amma ka tuna da ni sa'ad da komai ya tafi lafiya da kai, ina roƙon ka kuma ka nuna mani alheri. Ka ambace ni wurin Fir'auna a fito da ni daga wannan kurkuku.15Domin tabbas an sato ni ne daga ƙasar Ibraniyawa. A nan kuma banyi wani abu ba da zai sanya su su sani cikin wannan rami ba."
16Sa'ad da shugaban masu toye-toye ya ga cewa fassarar ta yi daɗi, ya cewa Yosef, "Ni ma nayi mafarki, kuma, duba, kwanduna uku na gurasa suna bisa kaina.17A cikin kwandon na sama akwai kowanne irin kayan toye-toye domin Fir'auna, amma tsuntsaye suka cinye su daga cikin kwandon a bisa kaina."
18Yosef ya amsa ya ce, "Wannan ce fassarar sa. Kwandunan uku kwanaki uku ne.19A cikin kwanaki uku Fir'auna zai ɗaga kanka daga gare ka zai kuma sarƙafe ka bisa itace. Tsuntsaye kuma zasu cinye namanka daga gare ka."
20Sai ya kasance a rana ta uku ranar tunawa da haihuwar Fir'auna ce. Sai ya yi wa dukkan bayinsa biki. Sai ya ɗaga kan shugaban masu riƙon ƙoƙon sha da shugaban masu toye-toye, daga cikin bayinsa.21Ya maido da shugaban masu riƙon ƙoƙon sha ga hidimarsa, ya kuma sake sanya ƙoƙon cikin hannun Fir'auna.22Amma ya sargafe shugaban masu toye-toye, kamar yadda Yosef ya yi masu fassara.23Duk da haka shugaban masu riƙon ƙoƙon shan bai tuna da Yosef ba, amma ya manta da shi.

41

1Sai ya kasance bayan shekaru biyu cur Fir'auna ya yi wani mafarki. Duba, yana tsaye bakin Nilu.2Duba, sai ga wasu shanu bakwai sun fito daga Nilu, masu ban sha'awa da ƙiba, suna kuma kiwo a cikin iwa.3Duba, ga wasu shanun bakwai sun fito bayan su daga cikin Nilu, marasa ban sha'awa ramammu kuma. Suka tsaya gefen waɗancan shanun a bakin kogin.

4Daga nan shanun marasa ban sha'awa ramammu kuma suka cinye shanun masu ban sha'awa da ƙiba. Daga nan Fir'auna ya farka.5Daga nan kuma ya sake yin barci ya kuma sake yin mafarki karo na biyu. Duba, kawunan hatsi bakwai sun fito bisa kara ɗaya, cikakku masu kyau kuma.6Gashi, kawuna bakwai, ƙanana waɗanda kuma iskar gabas ke kakkaɓewa, suka fito bayan su.
7‌Ƙananan kawunan suka haɗiye kawunan cikakku masu kyau kuma. Fir'auna ya farka, kuma, duba, ashe mafarki ne.8Sai ya kasance da safe ruhunsa ya damu. Ya aika aka kira dukkan 'yan dabo da masu hikima na Masar. Fir'auna ya gaya masu mafarkansa, amma babu wani da ya iya fassara su ga Fir'auna.
9Daga nan shugaban masu riƙon ƙoƙon sha ya ce wa Fir'auna, "A yau ina tunani game da laifuffukana.10Fir'auna ya yi fushi da bayinsa, ya kuma sanya ni cikin tsaro a cikin gidan shugaban masu tsaro, shugaban masu tuya tare da ni.11Muka yi mafarki a cikin dare ɗaya, shi da ni. Muka yi mafarki kowanne mutum bisa ga fassarar mafarkinsa.
12Tare da mu a can akwai wani saurayin mutum Ba'ibraniye, bawan shugaban masu tsaro. Muka faɗi masa kuma ya fassara mana mafarkanmu. Ya fassara wa kowannen mu bisa ga mafarkinsa.13Sai ya kasance kamar yadda ya fassara mana, haka ya faru. Fir'auna ya maido ni bisa aikina, amma ɗayan ya sarƙafe shi."
14Daga nan Fir'auna ya aika aka kuma kirawo Yosef. Nan da nan suka fito da shi daga ramin. Ya kuma yi aski, ya canza sutura, ya kuma fito zuwa wurin Fir'auna.15Fir'auna ya cewa Yosef, "Na yi mafarki, amma babu mai fassara. Amma na ji labarinka, cewa idan ka ji mafarki kana iya fassara shi."16Yosef ya amsawa Fir'auna, cewa, "Ba ni ba ne. Allah zai amsawa Fir'auna da tagomashi."
17Fir'auna ya yi magana da Yosef, "A cikin mafarkina, duba, ina tsaye a bakin Nilu.18Gashi, shanu bakwai suka fito daga cikin Nilu, masu ƙiba da ban sha'awa, suna kuma kiwo cikin iwa.
19Gashi, wasu shanun bakwai suka fito bayan su, marasa ƙarfi, marasa ban sha'awa, ramammu kuma. A cikin dukkan ƙasar Masar ban taɓa ganin wani abin rashin ban sha'awa ba kamar su.20Shanun marasa ƙiba da rashin ban sha'awa suka cinye shanun na farko masu ƙiba.21Sa'ad da suka cinye su, ba za a ma san cewa sun cinye su ba, domin sun kasance marasa ban sha'awa kamar dã. Daga nan na farka.
22Na duba a cikin mafarkina, kuma, duba, kawuna bakwai na hatsi suka fito bisa kara ɗaya, cikakku masu kyau.23Gashi kuwa, ƙarin kawuna bakwai - busassu, ƙanana, waɗanda kuma iskar gabas ke kakkaɓewa - suka fito bayansu.24‌Ƙananan kawunan suka haɗiye kawunan bakwai masu kyau. Na faɗi waɗannan mafarkai ga masu dabo, amma babu wani da zai yi bayyanin su a gare ni."
25Yosef ya cewa Fir'auna, "Mafarkan Fir'auna ɗaya ne. Abin da Allah ke gaf da aiwatar wa, ya bayyana wa Fir'auna.26Shanun masu kyau guda bakwai shekaru bakwai ne, kawunan hatsin bakwai kuma shekaru bakwai ne. Mafarkan iri ɗaya ne.
27Shanun bakwai ramammu marasa ban sha'awa da suka fito bayan su shekaru bakwai ne, haka nan kuma kawunan hatsin ƙanana da iskar gabas ke kakkaɓe wa shekaru ne bakwai na yunwa.28Wannan batun ne na faɗawa Fir'auna. Abin da Allah ke gaf da aiwatar wa ya bayyana wa Fir'auna.29Duba, shekaru bakwai na yalwa zasu zo cikin dukkan ƙasar Masar.
30Shekaru bakwai na yunwa zasu zo bayan su, za a kuma manta da dukkan yalwar da aka yi a ƙasar Masar, kuma yunwar za ta lalata ƙasar.31Ba za a tuna da yalwar ba a cikin ƙasar saboda yunwar da za ta biyo baya, domin za ta zama da tsanani sosai.32Cewa an maimaita wa Fir'auna mafarkin saboda Allah ya tabbatar da al'amarin ne, kuma Allah zai aiwatar ba da daɗewa ba.
33Yanzu bari Fir'auna ya nemi wani mutum mai fahimta da hikima, ya kuma ɗora shi bisa ƙasar Masar.34Bari Fir'auna ya zaɓi shugabanni bisa ƙasar, bari kuma su ɗauki kashi biyar na dukkan amfanin Masar a cikin shekaru bakwai na yalwa.
35Bari su tattara dukkan abincin waɗannan shekaru masu kyau dake zuwa su kuma ajiye hatsi a ƙarƙashin ikon Fir'auna, domin abincin da za a yi amfani da shi a cikin biranen. Su adana shi.36Abincin zai zama abin wadatar wa domin ƙasar domin kuma shekaru bakwai na yunwa da zasu kasance a ƙasar Masar. Ta wannan hanyar ƙasar ba zata lalace ba ta wurin yunwar."
37Wannan shawara ta yi kyau a idanun Fir'auna da idanun dukkan bayinsa.38Fir'auna ya cewa bayinsa, "Za mu iya samun wani mutum kamar wannan, wanda Ruhun Allah ke cikinsa?"
39Sai Fir'auna ya cewa Yosef, "Tunda Allah ya nuna maka dukkan waɗannan abubuwa, babu wani mafi fahimta da hikima kamar kai.40Zaka kasance bisa gidana, kuma bisa ga maganar ka za a yi mulkin dukkan mutanena. A bisa kursiyi ne kawai zan fi ka girma."41Fir'auna ya cewa Yosef, "Duba, na sanya ka bisa dukkan ƙasar Masar."
42Fir'auna ya cire zoben hatiminsa daga hannunsa ya sanya a hannun Yosef. Ya yi masa sutura da suturar linin mai laushi, ya kuma sanya sarƙar zinariya a wuyansa.43Ya sanya shi ya tuƙa karusarsa ta biyu da ya mallaka. Mutane suka yi sowa a gabansa, "Gwiwa a durƙushe." Fir'auna ya sanya shi bisa dukkan ƙasar Masar.
44Fir'auna ya cewa Yosef, "Ni ne Fir'auna, baya gare ka kuma, babu mutumin da zai ɗaga hannunsa ko ƙafarsa a cikin dukkan ƙasar Masar."45Fir'auna ya kira Yosef da suna "Zafenat-Faniya." Ya ba shi Asenat, ɗiyar Fotifera firist na On, a matsayin mata. Yosef ya fita bisa ƙasar Masar.
46Yosef yana da shekaru talatin sa'ad da ya tsaya a gaban Fir'auna, sarkin Masar. Yosef ya fita daga gaban Fir'auna, ya kuma tafi cikin dukkan ƙasar Masar.47A cikin shekaru bakwai na yalwa ƙasar ta fitar da amfani a yalwace.
48Ya tattara dukkan abinci na shekaru bakwai dake cikin ƙasar Masar ya kuma sanya abincin a cikin biranen. Ya sanya a cikin kowanne birni abincin gonakin dake kewaye da shi.49Yosef ya ajiye hatsi kamar rairayin teku, da yawan gaske har ya daina ƙirgawa, saboda ya zarce ƙirgawa.
50Yosef ya haifi 'ya'ya biyu kafin zuwan shekarun yunwa, waɗanda Asenat, ɗiyar Fotifa firist na On, ta haifa masa.51Yosef ya kira sunan ɗan fãrinsa Manasse, domin ya ce, "Allah ya sa na manta da dukkan damuwata da dukkan gidan mahaifina."52Ya kira sunan ɗan na biyu Ifraim, domin ya ce, "Allah ya maida ni mai bada 'ya'ya a cikin ƙasar wahalata."
53Shekaru bakwai na yalwa da suka kasance a ƙasar Masar suka kawo ƙarshe.54Aka fãra shekaru bakwai na yunwa, kamar yadda Yosef ya faɗa. Aka yi yunwa a cikin dukkan ƙasashen, amma a cikin dukkan ƙasar Masar akwai abinci.
55Sa'ad da dukkan ƙasar Masar suka fãra yunwa, mutanen suka kira ga Fir'auna da ƙarfi domin abinci. Fir'auna ya cewa dukkan Masarawa, "Ku je wurin Yosef ku kuma yi abin da ya ce."56Yunwa tana bisa dukkan fuskar ƙasar. Yosef ya buɗe dukkan gidajen ajiya ya sayar wa da Masarawa. Yunwa ta yi tsanani a ƙasar Masar.57Dukkan duniya na zuwa Masar su sayi hatsi daga wurin Yosef, saboda yunwar ta yi tsanani a dukkan duniya.

42

1Yanzu Yakubu ya sami sani cewa akwai hatsi a Masar. Ya ce wa 'ya'yansa maza, "Meyasa kuke kallon juna?"2Ya ce, "Ku saurara, Na ji cewa akwai hatsi a Masar. Ku gangara can ku sawo domin mu dagacan domin mu rayu kada kuma mu mutu."3'Yan'uwan Yosef goma suka gangara domin su sawo hatsi daga Masar.4Amma Benyamin, ɗan'uwan Yosef, Yakubu bai aike shi ba tare da 'yan'uwansa, saboda ya ji tsoron cewa wani bala'i na iya afko masa.

5'Ya'yan Isra'ila na cikin waɗanda suka zo saye, domin akwai yunwa a cikin ƙasar Kan'ana.6Yanzu dai Yosef shi ne gwamna a ƙasar. Shi ne ke saida wa dukkan mutanen ƙasar. 'Yan'uwan Yosef suka zo suka kuma rusuna masa da fuskokinsu ƙasa.
7Yosef ya ga 'yan'uwansa ya kuma gãne su, amma ya ɓadda masu kamarsa ya kuma yi magana da su da zafi. Ya ce masu, "Daga ina kuka fito?" Suka ce, "Daga ƙasar Kan'ana domin mu sayi abinci."8Yosef ya gãne 'yan'uwansa, amma su basu gãne shi ba.
9Daga nan Yosef ya tuna da mafarkan da ya yi game da su, ya kuma ce masu, "Ku 'yan leƙen asirin ƙasa ne! kun zo ku ga sassan ƙasar da basu da tsaro."10Suka ce masa, "A'a, shugabana. Bayinka sun zo sayen abinci ne.11Dukkan mu 'ya'yan mutum ɗaya ne. Mu mutane ne masu gaskiya. Bayinka ba 'yan leƙen asirin ƙasa ba ne."
12Ya ce masu, "A'a, kun zo ku ga sassan ƙasar da ba su da tsaro."13Suka ce, "Mu bayinka 'yan'uwa sha biyu ne, 'ya'yan mutum ɗaya a cikin ƙasar Kan'ana. Duba, ƙaramin mu a yau yana tare da mahaifinmu, ɗayan ɗan'uwan kuma baya da rai."
14Yosef yace masu, "Abin da na ce maku ke nan; ku 'yan leƙen asirin ƙasa ne.15Ta haka za a gwada ku. Da ran Fir'auna, ba zaku bar nan ba, sai idan ƙaramin ɗan'uwanku ya zo nan.16Ku aiki ɗaya daga cikin ku ya je ya zo da ɗan'uwanku. Zaku zauna a kurkuku, domin a gwada maganganunku, ko akwai gaskiya a cikin ku."17Ya sa dukkan su a ka kulle su har kwana uku.
18A rana ta uku Yosef yace masu, "Ku yi haka kuma ku rayu, domin ina tsoron Allah.19Idan ku mutane ne masu gaskiya, bari ɗaya daga cikin 'yan'uwanku a tsare shi a kurkuku, amma ku ku tafi, ku ɗauki hatsi domin yunwar gidajenku.20Ku kawo mani ƙaramin ɗan'uwanku domin a tabbatar da maganganunku kuma ba za ku mutu ba." Sai suka yi haka.
21Suka cewa juna, "Babu shakka mun yi laifi game da ɗan'uwanmu yadda muka ga ƙuncin ransa sa'ad da ya roƙe mu, amma muka ƙi sauraron sa. Saboda haka wannan ƙunci ya zo bisanmu."22Ruben ya amsa masu, "Ban gaya maku ba, 'Kada kuyi zunubi game da saurayin, amma baku saurare ni ba? Yanzu, duba, ana neman jininsa daga hannunmu."
23Basu san cewa Yosef ya fahimce su ba, domin akwai mai fassara a tsakanin su.24Ya juya daga gare su ya yi kuka. Ya kuma dawo gare su ya yi magana da su. Ya ɗauki Simiyon daga cikin su ya ɗaure shi a gaban idanunsu.25Daga nan Yosef ya umarci bayinsa su cika buhunan 'yan'uwansa da hatsi, kuma su maida wa kowa kuɗinsa cikin buhunsa, su kuma basu kayan masarufi domin tafiyarsu. A ka yi haka domin su.
26Suka ɗora wa jakunansu hatsi suka kuma yi tafiyar su daga wurin.27Yayin da ɗaya daga cikin su ya buɗe buhunsa domin ya ciyar da jakinsa a wurin hutawar su, ya ga kuɗinsa. Duba, suna bakin buhunsa.28Ya cewa 'yan'uwansa, "An maida mani kuɗina, ku dube su; suna bakin buhuna." Zukatansu suka nitse, suka kuma juya suna rawar jiki ga junansu, suna cewa, "Mene ne haka da Allah ya yi mana?"
29Suka tafi wurin Yakubu, mahaifinsu a cikin ƙasar Kan'ana suka kuma gaya masa dukkan abin da ya faru da su. Suka ce,30"Mutumin, ubangijin ƙasar, ya yi magana da mu da zafi ya zaci cewa mu 'yan leƙen asirin ƙasa ne.31Muka ce masa, "Mu mutane ne masu gaskiya. Ba 'yan leƙen asirin ƙasa bane.32Mu 'yan'uwa ne sha biyu, 'ya'ya maza na mahaifinmu. ‌Ɗaya baya da rai, ƙaramin kuma yau yana tare da mahaifinmu a ƙasar Kan'ana.'
33Mutumin, ubangijin ƙasar, ya ce mana, 'Ta haka zan sani cewa ku mutane ne masu gaskiya. Ku bar ɗaya daga cikin 'yan'uwanku tare da ni, ku ɗauki hatsi domin yunwar dake gidajenku, ku kuma yi tafiyarku.34Ku kawo ƙaramin ɗan'uwanku wuri na. Daga nan zan sani cewa ku ba 'yan leƙen asirin ƙasa ba ne, amma ku mutane ne masu gaskiya. Daga nan zan saki ɗan'uwanku a gare ku, kuma zaku yi sana'a a ƙasar."'
35Sai ya kasance yayin da suka zazzage buhunansu, duba, kowanne mutum jakkar azurfarsa na cikin buhunsa. Sa'ad da su da mahaifinsu suka ga jakkunan azurfarsu, sai suka tsorata.36Yakubu mahaifinsu ya ce masu, "Kun salwantar mani da 'ya'yana. Yosef ba shi da rai, Simiyon kuma ya tafi, kuma zaku ɗauke Benyamin. Waɗannan abubuwa dukka gãba suke da ni."
37Ruben ya yi magana da mahaifinsa, cewa, "Kana iya kashe 'ya'yana biyu idan ban maido maka da Benyamin ba. Ka sanya shi cikin hannuwana, kuma zan sake maido maka da shi."38Yakubu yace, '‌Ɗana ba zai tafi tare da ku ba. Domin ɗan'uwansa ya mutu shi kaɗai kuma ya rage. Idan wani bala'i ya zo masa a hanyar da zaku tafi, daga nan zaku kawo furfurata da baƙinciki zuwa Lahira."

43

1Yunwa ta yi tsanani a ƙasar.2Sai ya kasance sa'ad da suka cinye hatsin da suka kawo daga Masar, mahaifinsu ya ce masu, "Ku sake komawa; ku sayo mana ɗan abinci."

3Yahuda yace masa, "Mutumin ya yi mana kashedi sosai, 'Ba za ku ga fuskata ba har sai ɗan'uwanku na tare da ku.'4Idan ka aika ɗan'uwanmu tare da mu, to za mu gangara mu je mu sayo maka abinci.5Amma idan ba ka aika da shi ba, ba za mu tafi ba. Domin mutumin ya ce mana, 'Ba za ku ga fuskata ba har sai ɗan'uwanku na tare da ku."'
6Isra'ila yace, "Meyasa kuka yi mani mummunan abu haka ta wurin gaya wa mutumin cewa kuna da wani ɗan'uwan?"7Suka ce, "Mutumin ya yi tambaya dalla-dalla game da mu da iyalinmu. Ya ce, 'Mahaifinku yana nan da rai? Kuna da wani ɗan'uwan? Muka amsa masa bisa ga waɗannan tambayoyi. Ta yaya zamu san cewa zai ce, 'Ku kawo ɗan'uwanku nan?"'
8Yahuda ya cewa Isra'ila mahaifinsa, "Ka aiki saurayin tare da ni. Zamu tashi mu tafi domin mu rayu kada kuma mu mutu, dukkanmu, da kai, da kuma 'ya'yanmu dukka.9Ni zan tsaya domin sa. Zaka riƙe ni hakkinsa. Idan ban dawo maka da shi ba na kuma tsaida shi a gabanka ba, daga nan bari in ɗauki laifin har abada.10Domin idan da ba mu yi jinkiri ba, tabbas da yanzu mun dawo karo na biyu.
11Mahaifinsu Isar'ila yace masu, "Idan haka abin yake, yanzu kuyi haka. Ku ɗauki mafi kyau daga cikin amfanin ƙasar a cikin jakkunanku. Ku tafi da su kyauta ga mutumin - su man shafawa da zuma, kayan yaji da ƙaro, tsabar 'ya'yan itace dana almond.12Ku ɗauki kuɗi ka shi biyu a hannunku. Kuɗaɗen da aka maido maku da aka buɗe buhunanku, ku ɗauka a cikin hannunku. Wataƙila kuskure ne.
13Ku ɗauki ɗan'uwanku kuma. Ku tashi ku sake tafiya wurin mutumin.14Bari Allah maɗaukaki ya baku jinƙai a gaban mutumin, domin ya sakar maku ɗaya ɗan'uwanku da Benyamin. Idan na rasa 'ya'yana, na rasa su."15Mutanen suka ɗauki kyautar, a hannunsu kuma suka ɗauki kuɗi kashi biyu, tare da Benyamin. Suka tashi kuma suka tafi suka gangara zuwa Masar suka je suka tsaya kuma a gaban Yosef.
16Sa'ad da Yosef yaga Benyamin tare da su, ya cewa ma'aikacin gidansa, "Ka kawo mutanen cikin gida, ka yanka dabba ka shirya ta, domin mutanen zasu ci tare da ni da rana."17Ma'aikacin ya yi yadda Yosef ya ce. Ya kawo mutanen cikin gidan Yosef.
18Mutanen suka tsorata saboda an kawo su cikin gidan Yosef. Suka ce, "Saboda kuɗaɗen da aka maido mana cikin buhunanmu a zuwanmu na farko aka kawo mu ciki, domin ya sami zarafin gãba da mu. Zai iya ɗaure mu ya ɗauke mu a matsayin bayi, ya kuma karɓe jakkunanmu."19Suka kusanci ma'aikacin gidan Yosef,20suka kuma yi magana da shi a bakin ƙofar gidan, cewa, "Shugabana, mun zo karo na farko sayen abinci.
21Sai ya kasance, da muka isa wurin hutawa, sai muka buɗe buhunanmu, kuma, duba, kuɗin kowanne mutum na bakin buhunsa, kuɗaɗenmu kuma nada nauyinsu dai-dai. Mun sake kawo su a hannuwanmu.22Mun sake kuma kawo wasu kuɗaɗen domin mu sayi abinci. Ba mu san wanda ya sanya kuɗaɗenmu cikin buhunanmu ba."23Ma'aikacin yace, "Salama a gareku, kada ku ji tsoro. Allahnku da Allahn mahaifinku ne ya sanya kuɗaɗenku a buhunanku. Na karɓi kuɗaɗenku." Daga nan ma'aikacin ya fito da Simiyon wurinsu.
24Ma'aikacin ya kai mutanen cikin gidan Yosef. Ya basu ruwa, suka kuma wanke ƙafafunsu. Ya ciyar da jakkunansu.25Suka shirya kyaututtukan domin zuwan Yosef da rana, domin sun ji cewa zasu ci abinci a nan.
26Sa'ad da Yosef ya zo gida, suka kawo kyaututtukan dake hannuwansu cikin gidan, suka kuma rusuna a gabansa har ƙasa.27Ya tambayi lafiyarsu ya kuma ce, "Mahaifinku na nan lafiya, tsohon da kuka yi maganar sa? Har yau yana nan da rai?"
28Suka ce, "Bawanka mahaifinmu yana nan lafiya lau. Har yau yana nan da rai." Suka kwanta kuma suka rusuna har ƙasa.29Sa'ad da ya ɗaga idanunsa ya kalli Benyamin ɗan'uwansa, ɗan mahaifiyarsa, sai ya ce, "Wannan ne ƙaramin ɗan'uwanku da kuka yi mani maganarsa?" Daga nan ya ce, "Allah ya yi maka alheri, ɗana."
30Yosef ya yi hanzari ya fita daga ɗakin, saboda ya motsu sosai game da ɗan'uwansa. Ya nemi wurin da zai yi kuka. Ya tafi ɗakinsa ya yi kuka a can.31Ya wanke fuskarsa ya kuma fito. Ya kame kansa, ya ce, "A raba abincin."
32Bayin suka yi wa Yosef hidima shi kaɗai, suka kuma yi wa 'yan'uwan hidima su kaɗai. Masarawan suka ci tare da shi su kaɗai, saboda Masarawa ba zasu ci abinci tare da Ibraniyawa ba, domin yin haka abin ƙyama ne ga Masarawa.33'Yan'uwan suka zauna a gabansa, na farko bisa ga matsayin haihuwarsa, ƙaramin kuma bisa ga samartakarsa. Mutanen suka yi mamaki tare.34Yosef ya aika masu kaso daga abincin dake gabansa. Amma kason Benyamin ya yi sau biyar fiye dana 'yan'uwansa. Suka sha suka kuma yi murna tare da shi.

44

1Yosef ya umarci ma'aikacin gidansa, ya ce, "Ka cika buhunan mutanen da abinci, iya yadda zasu iya ɗauka, ka kuma maida wa kowannen su kuɗinsa cikin bakin buhunsa.2Ka sanya kofina, kofin azurfa, cikin bakin buhun ƙaramin, da kuɗinsa na hatsi." Ma'aikacin ya yi yadda Yosef ya ce.

3Da asuba, aka kuma sallami mutanen, su da jakkunansu.4Sa'ad da suka fice daga birnin ba su riga sun yi nisa ba, Yosef ya cewa ma'aikacinsa, "Tashi, ka bi bayan mutanen, idan kuma ka sha kansu, ka ce masu, 'Meyasa kuka maida mugunta domin nagarta?5Wannan ba kofin da maigidana ke sha bane, kofin da yake amfani da shi domin sihiri? Kun yi mugunta, wannan abin da kuka yi."'
6Ma'aikacin ya sha kansu ya kuma faɗi waɗannan maganganu a gare su.7Suka ce masa, "Meyasa shugabana yake faɗin waɗannan maganganu haka? Bari ya yi nesa daga bayinka da zasu aikata irin wannan.
8Duba, kuɗaɗen da muka samu a bakin buhunanmu, mun sake kawo maka su daga ƙasar Kan'ana. Ta yaya daga nan zamu yi sãtar azurfa ko zinariya daga gidan shugabanmu?9Duk wanda aka same shi a wurinsa daga cikin bayinka, bari ya mutu, mu kuma zamu zama bayin shugabana."10Ma'aikacin yace, "Yanzu kuma bari ya kasance bisa ga maganganunku. Shi wanda aka sami kofin a wurinsa zai zama bawana, ku kuma sauran zaku fita daga zargi."
11Daga nan kowanne mutum ya yi hanzari ya sauko da buhunsa ƙasa, kowanne mutum kuma ya buɗe buhunsa.12Ma'aikacin ya bincike. Ya fãra da babban ya kuma ƙarashe da ƙaramin, aka kuma sami kofin a buhun Benyamin.13Daga nan suka kece tufafinsu. Kowanne mutum ya ɗora kaya a jakinsa suka kuma dawo cikin birni.
14Yahuda da 'yan'uwansa suka zo gidan Yosef. Har yanzu yana nan, suka kuma rusuna a gabansa har ƙasa.15Yosef yace masu, "Mene ne kuka yi haka? Ba ku san cewa mutum kamar ni ina aikata sihiri ba?"
16Yahuda yace, "Me za mu cewa shugabana? Me za mu faɗa? Ko yaya zamu baratar da kanmu? Allah ya gãno laifin bayinka. Duba, mu bayin shugabana ne, dukkan mu da wanda aka iske kofin a hannunsa." Yosef yace,17"Bari yayi nesa da ni da in aikata haka. Mutumin da aka iske kofin a hannunsa, wannan taliki zai zama bawana, amma game da ku sauran, ku tafi cikin salama ga mahaifinku."
18Daga nan Yahuda ya matso kusa da shi ya kuma ce, "Shugabana, na roƙe ka bari bawanka ya faɗi magana cikin kunnuwan shugabana, bari kuma fushinka ya yi ƙuna gãba da bawanka, domin kamar dai Fir'auna kake.19Shugabana ya tambayi bayinsa, cewa, 'Kuna da mahaifi ko ɗan'uwa?'
20Muka cewa shugabana, 'Muna da mahaifi, tsohon mutum, kuma da ɗan tsufansa, ƙarami ne. Amma ɗan'uwansa ya mutu, shi kaɗai kuma ya rage ga mahaifiyarsa, kuma mahaifinsa na ƙaunarsa.'21Daga nan ka cewa bayinka, 'Ku kawo shi nan a gare ni domin in gan shi.'22Bayan haka, muka cewa shugabana, 'Yaron ba zai iya barin mahaifinsa ba. Domin idan har ya bar mahaifinsa to mahaifinsa zai mutu.'
23Daga nan ka cewa bayinka, 'Har sai ƙaramin ɗan'uwanku ya zo tare da ku, ba zaku sake ganin fuskata ba.'24Daga nan ya kasance sa'ad da muka tafi wurin bawanka mahaifina, muka faɗi masa maganganun shugabana.25Mahaifinmu yace, 'Ku sake komawa, ku sawo mana ɗan abinci.'26Daga nan muka ce, 'Ba za mu iya komawa ba. Idan ƙaramin ɗan'uwanmu yana tare da mu, daga nan zamu gangara mu tafi, domin ba za mu iya ganin fuskar mutumin ba har sai ƙaramin ɗan'uwanmu yana tare da mu.'
27Bawanka mahaifina ya ce mana, 'Kun san cewa matata ta haifa mani 'ya'ya maza biyu.28‌Ɗaya daga cikin su ya fita daga gare ni kuma na ce, "Tabbas an yage shi gutsu-gutsu, ban sake ganin sa ba kuma tuni."29Yanzu idan kuka sake ɗauke wannan daga gare ni, kuma bala'i ya zo masa, zaku gangarar da furfurata da baƙinciki zuwa Lahira.'
30Yanzu, saboda haka, sa'ad dana koma wurin bawanka mahaifina, kuma saurayin baya tare da mu, tun da rayuwarsa ɗaure take da rayuwar yaron,31zai kasance, sa'ad da ya ga yaron ba ya tare da mu, zai mutu. Bayinka zasu gangara da furfurar bawanka mahaifinmu da baƙinciki zuwa Lahira.32Gama bawanka ya zama wanda ya tsaya domin yaron ga mahaifina na kuma ce, 'Idan ban maido maka da shi ba, daga nan zan ɗauki laifin ga mahaifina har abada."
33Saboda haka yanzu, ina roƙon ka bari bawanka ya tsaya a maimakon yaron a matsayin bawan shugabana, bari kuma yaron ya tafi tare da 'yan'uwansa.34Gama ta yaya zan tafi wurin mahaifina idan yaron ba ya tare da ni? Ina tsoron in ga mugun abin da zai zo bisa mahaifina."

45

1Daga nan Yosef bai iya kame kansa ba a gaban dukkan bayin dake tsaye a gefensa. Ya ce da ƙarfi, "Kowa ya bar ni tilas. "Babu bawan da ya tsaya a gefensa sa'ad da Yosef ya sanar da kansa ga 'yan'uwansa.2Ya yi kuka da ƙarfi, Masarawa suka ji, gidan Fir'auna kuma suka sami labari.3Yosef ya cewa 'yan'uwansa, "Ni ne Yosef. Har yanzu mahaifina nada rai?" 'Yan'uwansa ba su iya amsa masa ba, domin sun gigice a gabansa.

4Daga nan Yosef ya cewa 'yan'uwansa, "Ku zo kusa da ni, ina roƙon ku." Suka zo kusa da shi. Ya ce, "Ni ne Yosef ɗan'uwanku, wanda kuka sayar zuwa cikin Masar.5Kada kuyi baƙinciki ko kuji haushin kanku saboda kun sayar da ni zuwa nan, domin Allah ya aiko ni ne gaba da ku saboda a ceci rai.6Domin shekaru biyu kenan yunwa na cikin ƙasar, har yanzu kuma akwai shekaru biyar inda ba za a yi huɗa ko girbi ba.
7Allah ya aiko ni gaba da ku domin ya adana ku a matsayin ragowa a duniya, ya kuma ajiye ku da rai ta wurin babbar kuɓutarwa.8Saboda haka yanzu ba ku ne kuka aiko ni nan ba amma Allah ne, kuma ya maida ni uba ga Fir'auna, shugaban dukkan gidansa, kuma mai mulki a cikin dukkan ƙasar Masar.
9Ku yi hanzari ku tafi wurin mahaifina ku ce masa, 'Wannan ne abin da ɗanka Yosef yace, "Allah ya maida ni shugaban dukkan Masar. Ka gangaro zuwa gare ni, kada ka yi jinkiri.10Zaka zauna a ƙasar Goshen, zaka kuma kasance kusa da ni, kai da 'ya'yanka da 'ya'yan 'ya'yanka, da garkunan tumakinka dana awaki da garkunan shanunka, da dukkan abin da kake da shi.11Zan biya buƙatunka a can, domin har yanzu akwai shekaru biyar na yunwa, domin kada ku kai ga talaucewa, kai, da gidanka, da dukkan abin da kake da shi."'
12Duba, idanunku sun ga ni, da idanun ɗan'uwanku Benyamin, cewa bakina ne ya yi magana da ku.13Zaku gayawa mahaifina game da dukkan ɗaukakata a Masar da dukkan abin da kuka gani. Zaku yi hanzari ku kawo mahaifina a nan."
14Ya rungume wuyan ɗan'uwansa Benyamin ya kuma yi kuka, Benyamin kuma ya yi kuka a wuyansa.15Ya sumbaci dukkan 'yan'uwansa kuma ya yi kuka a kansu. Bayan wannan 'yan'uwansa suka yi magana da shi.
16Aka faɗi labarin al'amarin a gidan Fir'auna: "'Yan'uwan Yosef sun zo." Abin ya gamshi Fir'auna da bayinsa sosai.17Fir'auna ya cewa Yosef, "Ka cewa 'yan'uwanka, 'Ku yi haka: Ku yi wa dabbobinku kaya ku kuma tafi ƙasar Kan'ana.18Ku ɗauko mahaifinku da gidanku dukka ku kuma zo wurina. Zan baku nagartar ƙasar Masar, kuma zaku ci dausayin ƙasar.'
19Yanzu an umarce ku, 'Ku yi haka, ku ɗauki kekunan shanu daga ƙasar Masar domin 'ya'yanku domin matayenku kuma. Ku kuma ɗauko mahaifinku ku zo.20Kada ku damu da mallakokinku, domin nagartar dukkan ƙasar Masar taku ce."'
21'Ya'ya maza na Isra'ila suka yi haka. Yosef ya basu kekunan shanu, bisa ga dokar Fir'auna, ya kuma basu guzuri domin tafiyar.22Ga dukkan su ya ba kowanne mutum canjin tufafi, amma ga Benyamin ya bayar da azurfa ɗari uku da canjin tufafi biyar.23Ya aika wannan domin mahaifinsa: jakuna goma ɗauke da kyawawan abubuwan Masar; da matan jakuna goma ɗauke da hatsi, gurasa, da sauran kayan masarufi domin mahaifinsa domin tafiyar.
24Sai ya sallami 'yan'uwansa suka kuma yi tafiyarsu. Ya ce masu, "Ku tabbatar cewa ba ku yi faɗa ba a kan hanya."25Suka tafi daga Masar suka zo ƙasar Kan'ana, ga Yakubu mahaifinsu.26Suka gaya masa cewa, "Yosef yana nan da rai, kuma shi ne shugaba bisa dukkan ƙasar Masar." Zuciyarsa ta yi mamaki, domin bai gaskata da abin da suka faɗa masa ba.
27Suka gaya masa dukkan maganganun Yosef da ya faɗi masu. Sa'ad da Yakubu ya ga kekunan shanun da Yosef ya aiko su da su, ruhun Yakubu mahaifinsu ya farfaɗo.28Isra'ila yace, "Ya isa. Yosef ɗana yana nan da rai. Zan tafi in gan shi kafin in mutu."

46

1Isra'ila ya kama hanyarsa da dukkan abin da yake da shi, ya kuma tafi Bayersheba. A can ya miƙa hadayu ga Allah na mahaifinsa Ishaku.2Allah ya yi magana da Isra'ila a cikin wahayi da dare, cewa, "Yakubu, Yakubu." Ya ce, "Ga ni nan."3Ya ce, "Ni ne Allah, Allah na mahaifinka. Kada ka ji tsoron gangarawa zuwa Masar, domin a can zan maida kai babbar al'umma.4Zan gangara da kai zuwa cikin Masar, kuma tabbas zan sake hawo da kai kuma Yosef zai rufe idanunka da hannunsa."

5Yakubu ya taso daga Bayersheba. 'Ya'yan Isra'ila suka tafi da Yakubu mahaifinsu, 'ya'yansu, da matayensu, a cikin kekunan shanun da Fir'auna ya aiko a ɗauke shi.6Suka ɗauki dabbobinsu da mallakarsu da suka tattara a ƙasar Kan'ana. Suka zo cikin Masar, Yakubu da dukkan zuriyarsa tare da shi.7Ya taho Masar tare da 'ya'yansa maza da 'ya'yan 'ya'yansa maza, da 'ya'yansa mata da 'ya'yan 'ya'yansa mata, da dukkan zuriyarsa.
8Waɗannan ne sunayen 'ya'yan Isra'ila waɗanda suka zo Masar: Yakubu da 'ya'yansa, Ruben, ɗan fãrin Yakubu;9'ya'yan Ruben, Hanok, Fallu, Hezron, da Karmi;10'ya'yan Simiyon, Yemuwel, Yamin, Ohad, Yakin, Zohar, da Shawul, ɗan Bakan'aniya;11'ya'yan Lebi kuma, Gashon, Kohat, da Merari.
12'Ya'yan Yahuda su ne Er, Onan, Shela, Ferez, da Zera, (amma Er da Onan sun mutu a ƙasar Kan'ana). 'Ya'yan Ferez su ne Hezron da Hamul.13'Ya'yan Issaka su ne Tola, Fuwa, Lob, da Shimron;14'ya'yan Zebulun sune Sered, Elon, da Yalil15Waɗannan ne 'ya'yan Liya waɗanda ta haifa wa Yakubu a Faddan Aram, tare da ɗiyarsa Dina. Lissafin 'ya'yansa maza da mata talatin da uku.
16'Ya'yan Gad su ne Zefon, Haggi, Shuni, Ezbon, Eri, Arodi, da Areli.17'Ya'yan Asha su ne Imna, Ishba, Ishbi, da Beriya; kuma Sera ce 'yar'uwarsu. 'Ya'yan Beriya su ne Heba da Malkiyel18Waɗannan ne 'ya'yan Zilfa, wadda Laban ya bayar ga ɗiyarsa Liya. Waɗannan 'ya'ya ta haifa wa Yakubu - sha shida dukka dukkansu.
19'Ya'yan Rahila matar Yakubu su ne Yosef da Benyamin.20A Masar Asenat ɗiyar Fotifera firist na On, ta haifa wa Yosef Manasse da Ifraim.21'Ya'yan Benyamin su ne Bela, Beka, Ashbel, Gera, Na'aman, Ehi, Rosh, Muffim, Huffim, da Ard.22Waɗannan ne 'ya'yan Rahila da aka haifa wa Yakubu - sha huɗu dukkan su.
23‌Ɗan Dan shi ne Hushim.24'Ya'yan Naftali su ne Yaziyel, Guni, Yeza, da Shillem.25Waɗannan ne 'ya'yan da Bilha ta haifa wa Yakubu, wadda Laban ya bayar ga Rahila ɗiyarsa - bakwai dukka dukkansu.
26Dukkan waɗanda suka tafi Masar tare da Yakubu, waɗanda ke zuriyarsa, ba a ƙidaya da matayen 'ya'yan Yakubu ba, su sittin da shida ne dukkansu.27Tare da 'ya'yan Yosef maza biyu da aka haifa masa a Masar, yawan iyalinsa da suka tafi Masar su saba'in ne dukkansu.
28Yakubu ya aiki Yahuda zuwa ga Yosef saboda ya nuna masa hanya a gabansa ta zuwa Goshen, suka kuma zo ƙasar Goshen.29Yosef ya shirya karusarsa ya kuma tafi domin ya sami Isra'ila mahaifinsa a Goshen. Ya gan shi, ya rungumi wuyansa, ya kuma yi kuka na dogon lokaci bisa wuyansa.30Isra'ila yace wa Yosef, "Yanzu bari in mutu, tunda na ga fuskarka, cewa kana nan da rai."
31Yosef ya cewa 'yan'uwansa da gidan mahaifinsa, "Zan tafi in gaya wa Fir'auna, cewa, "Yan'uwana da gidan mahaifina, waɗanda suke a ƙasar Kan'ana, sun zo wurina.32Mutanen makiyaya ne, domin suna kiwon dabbobi ne. Sun kawo garkunan tumakinsu dana awakinsu, da garkunan shanunsu, da dukkan abin da suke da shi.'
33Zai kasance, sa'ad da Fir'auna zai kira ku ya yi tambaya, 'Mene ne sana'arku?'34To zaku ce masa, 'Bayinka masu kiwon dabbobi ne tun daga ƙuruciyarmu har zuwa yanzu, dukkanmu, da ubanninmu.' Ku yi haka domin ku zauna a ƙasar Goshen, domin kowanne makiyayi haramtacce ne ga Masarawa."

47

1Daga nan Yosef ya shiga ya gaya wa Fir'auna, "Mahaifina da 'yan'uwana, da garkunan tumakinsu da na awaki, da garkunan shanunsu, da dukkan abin da ke nasu, sun iso daga ƙasar Kan'ana. Duba, suna ƙasar Goshen."2Ya ɗauki biyar daga cikin 'yan'uwansa ya kuma gabatar da su ga Fir'auna.

3Fir'auna ya cewa 'yan'uwansa, "Mene ne sana'arku?" Suka cewa Fir'auna, "Bayinka makiyaya ne, kamar kakanninmu."4Daga nan suka cewa Fir'auna, "Mun zo ɗan zama ne a ƙasar. Babu makiyaya domin garkunan bayinka, saboda yunwar ta yi tsanani a ƙasar Kan'ana. To yanzu, muna roƙonka bari bayinka su zauna a ƙasar Goshen."
5Daga nan Fir'auna ya yi magana da Yosef, ya ce, "Mahaifinka da 'yan'uwanka sun zo wurinka.6‌Ƙasar Masar na gabanka. Ka zaunar da mahaifinka da 'yan'uwanka a lardi mafi kyau, ƙasar Goshen. Idan ka san maza ƙwararru daga cikinsu, ka sanya su kiwon dabbobi na."
7Daga nan Yosef ya shigo da Yakubu mahaifinsa ya kuma gabatar da shi ga Fir'auna. Yakubu ya albarkaci Fir'auna.8Fir'auna ya cewa Yakubu, "Tsawon rayuwarka nawa?"9Yakubu ya cewa Fir'auna, "Shekarun yawace-yawace na ɗari ne da talatin. Shekarun rayuwata kima ne kuma cike da wahala. Ba su kai yawan na kakannina ba."10Daga nan Yakubu ya albarkaci Fir'auna ya kuma fita daga gabansa.
11Daga nan Yosef ya zaunar da mahaifinsa da 'yan'uwansa. Ya ba su gunduma a ƙasar Masar, yankin ƙasar mafi kyau, a ƙasar Ramesis, kamar yadda Fir'auna ya umarta.12Yosef ya wadata abinci domin mahaifinsa, da 'yan'uwansa, da dukkan gidan mahaifinsa, bisa ga lissafin masu dogara da su.
13Yanzu dai babu abinci a dukkan ƙasar; domin yunwar ta yi tsanani. ‌Ƙasar Masar da ƙasar Kan'ana suka lalace saboda yunwar.14Yosef ya tattara dukkan kuɗaɗen dake ƙasar Masar da ƙasar Kan'ana, ta wurin sayar da hatsi ga mazaunan. Daga nan Yosef ya kawo kuɗaɗen fãdar Fir'auna.
15Sa'ad da aka gama kashe dukkan kuɗaɗen dake ƙasashen Masar da Kan'ana, dukkan Masarawa suka zo wurin Yosef suka ce, "Ka bamu abinci! Ya ya zamu mutu a gabanka saboda kuɗaɗenmu sun ƙare?"16Yosef yace, "Idan kuɗaɗenku sun ƙare, ku kawo dabbobinku ni zan kuma baku abinci misanya domin dabbobinku."17Sai suka kawo dabbobinsu wurin Yosef. Yosef ya basu abinci misanya domin dawakai, domin garkunan tumaki da awaki, domin garkunan shanu, domin kuma jakuna. A wannan shekarar ya ciyar dasu da abinci a misanyar dukkan dabbobinsu.
18Sa'ad da shekara ta ƙare, suka zo wurinsa a shekara ta gaba suka kuma ce masa, "Ba zamu ɓoye ba daga shugabanmu cewa kuɗaɗenmu sun tafi, kuma garkunan shanun na shugabanmu ne. Babu abin da ya rage a idanun shugabana, sai jikkunanmu kawai da ƙasarmu.19Yaya zamu mutu a gaban idanunka, dukkanmu da ƙasarmu? Ka saye mu da ƙasarmu a musanya domin abinci, mu da ƙasarmu mu zama bayi ga Fir'auna. Ka bamu iri domin mu rayu kada mu mutu, kada kuma ƙasar ta zama kufai."
20Saboda haka Yosef ya saye wa Fir'auna dukkan ƙasar Masar. Domin kowanne Bamasare ya sayar da gonarsa, saboda yunwar ta yi tsanani sosai. Ta wannan hanya, ƙasar ta zama ta Fir'auna.21Game da mutanen, ya mayar dasu bayi daga ƙarshen kan iyakar Masar zuwa ɗaya ƙarshen.22‌Ƙasar firistoci ce kawai Yosef bai saya ba, saboda ana ba firistocin albashi. Suna ci daga kason da Fir'auna yake ba su. Saboda haka basu sayar da gonarsu ba.
23Daga nan Yosef ya cewa mutanen, "Duba, na saye wa Fir'auna ku da ƙasarku. Yanzu ga iri domin ku, zaku kuma noma ƙasar.24Da kaka tilas ku bada kaso biyar ga Fir'auna, kashi huɗu kuma zai zama naku, domin iri na gonaki domin kuma abinci domin gidajenku da 'ya'yanku."
25Suka ce, "Ka ceci rayukanmu. Bari mu sami tagomashi a idanunka. Zamu zama bayin Fir'auna."26Sai Yosef ya maida haka doka mai aiki har wayau a ƙasar Masar, cewa kashi biyar na Fir'auna ne. ‌Ƙasar firistoci ce kawai ba ta zama ta Fir'auna ba.
27Saboda haka Isra'ila ya zauna a ƙasar Masar, a ƙasar Goshen. Mutanensa suka sami mallakar wurin. Suka hayayyafa suka ruɓanɓanya sosai.28Yakubu ya zauna a ƙasar Masar shekaru sha bakwai, saboda haka shekarun rayuwar Yakubu ɗari da arba'in da bakwai ne.
29Sa'ad da lokaci ya kusato da Isra'ila zai mutu, ya kira ɗansa Yosef yace masa, "Yanzu idan na sami tagomashi a idanunka, ka sanya hannunka a ƙarƙashin cinyata, ka kuma nuna mani aminci da yarda. Ina roƙon ka kada ka bizne ni a Masar.30Sa'ad da na yi barci da ubannina, zaka ɗauke ni ka fitar da ni daga Masar ka kuma bizne ni a maƙabartar kakannina." Yosef yace, "Zan yi yadda ka ce."31Isra'ila yace, "Ka rantse mani," Yosef kuma ya rantse masa. Daga nan Isra'ila ya rusuna a bisa kan gadonsa.

48

1Sai ya kasance bayan waɗannan abubuwa, sai wani ya cewa Yosef, "Duba, mahaifinka bai da lafiya." Sai ya ɗauki 'ya'yansa maza biyu tare da shi, Manasse da Ifraim.2Sa'ad da aka gaya wa Yakubu, "Duba, ɗanka Yosef ya iso ya ganka," Isra'ila ya ƙoƙarta kuma ya zauna bakin gado.

3Yakubu ya cewa Yosef, "Allah maɗaukaki ya bayyana a gare ni a Luz cikin ƙasar Kan'ana.4Ya albarkace ni ya kuma ce mani, 'Duba, zan sa ka hayayyafa, ka kuma ruɓanɓanya. Zan maida kai taron al'ummai. Zan bayar da wannan ƙasar ga zuriyarka a matsayin madawwamiyar mallaka.'
5Yanzu 'ya'yanka biyu maza, waɗanda aka haifa maka a ƙasar Masar kafin in zo wurinka a Masar, nawa ne. Ifraim da Manasse zasu zama nawa, kamar yadda Ruben da Simiyon suke nawa.6'Ya'yan da zaka haifa bayan su zasu zama naka; za a lissafa su ƙarƙashin sunayen 'yan'uwansu a cikin gãdonsu.7Amma game da ni, sa'ad dana zo daga Faddan, cikin baƙincikina Rahila ta mutu a ƙasar Kan'ana a kan hanya, yayin da da sauran tazara a isa Ifrat. Na bizne ta a nan a kan hanyar zuwa Ifrat" (wannan ce, Betlehem).
8Sa'ad da Isra'ila ya ga 'ya'yan Yosef maza, ya ce, "Na wane ne waɗannan?"9Yosef yace wa mahaifinsa, "'Ya'yana ne, waɗanda Allah ya bani a nan." Isra'ila yace, "Kawo su wurina, domin in sa masu albarka."10Yanzu dai idanun Isra'ila na kasawa saboda shekarunsa, har baya iya gani. Sai Yosef ya kawo su kusa da shi, kuma ya sumbace su ya kuma rungume su.
11Isra'ila ya cewa Yosef, "Banyi tsammanin zan sa ke ganin fuskarka ba, amma Allah ya bar ni inga 'ya'yanka ma."12Yosef ya fito da su daga tsakanin guiwoyin Isra'ila, Daga nan kuma ya rusuna da fuskarsa ƙasa.13Yosef ya ɗauke su biyun, Ifraim a hannun damansa zuwa hannun hagun Isra'ila, Manasse kuma a hannun hagunsa zuwa hannun damar Isra'ila, ya kuma matso da su kusa da shi.
14Isra'ila ya miƙa hannunsa na dama ya kuma ɗora bisa kan Ifraim, wanda shi ne ƙarami, hannun hagunsa kuma bisa kan Manasse. Ya gitta hannuwansa, domin Manasse shi ne ɗan fãri.15Isra'ila ya albarkaci Yosef, yana cewa, "Allah wanda a gabansa ubannina Ibrahim da Ishaku suka yi tafiya, Allah wanda ya lura da ni har ya zuwa yau,16mala'ikan da ya kiyaye ni daga dukkan bala'i, bari ya albarkaci waɗannan samari. Bari a raɗa sunana a sunansu, da sunan ubannina Ibrahim da Ishaku. Bari su yaɗu su yi tururu a bisa duniya."
17Sa'ad da Yosef ya ga cewa mahaifinsa ya ɗora hannunsa na dama bisa kan Ifraim, bai ji daɗi ba. Ya ɗauke hannun mahaifinsa domin ya matsa da shi daga bisa kan Ifraim zuwa bisa kan Manasse.18Yosef yace wa mahaifinsa, "Ba haka ba, babana; domin wannan shi ne ɗan fãrin. Ka ɗora hannunka na dama bisa kansa."
19Mahaifinsa ya ƙi ya kuma ce, "Na sani, ɗana, Na sani. Shi ma zai zama jama'a, shima kuma zai zama babba. Duk da haka ƙanensa zai fi shi girma, kuma zuriyarsa zasu zama al'ummai tururu."20Isra'ila ya albarkace su a wannan rana da waɗannan maganganu, "Mutanen Isra'ila zasu furta albarku da sunayenku suna cewa, 'Bari Allah ya maida ku kamar Ifraim kamar Manasse kuma'." Ta wannan hanya, Isra'ila ya sanya Ifraim gaba da Manasse.
21"Isra'ila ya cewa Yosef, "Duba, ina gaf da mutuwa, amma Allah zai kasance tare da ku, zai kuma maida ku ƙasar ubanninku.22Game da kai, a matsayin wanda aka ɗora sama da 'yan'uwansa, Na baka gangaren tsaunin dana karɓe daga hannun Amoriyawa da takobina da kuma bakana."

49

1Daga nan Yakubu ya kirawo 'ya'yansa maza, ya kuma ce: "Ku tattara kanku tare, domin in gaya maku abin da zai faru daku a gaba.2Ku tattara kanku ku kuma saurara, ku 'ya'yan Yakubu. Ku saurari Isra'ila, mahaifinku.

3Ruben, kai ne ɗan fãrina, ƙarfina, da farkon ƙarfina, ka yi fice wajen jamali, ka kuma yi fice wajen iko.4Marar kamewa kamar ruwan dake ambaliya, ba zaka yi muhimmanci ba, saboda ka hau bisa gadon mahaifinka. Daga nan ka gurɓata shi; ka hau bisa gadona.
5Simiyon da Lebi 'yan'uwa ne. Makaman ta'addanci ne takubbansu.6Ya raina, kada ka zo cikin shawararsu; kada ka shiga cikin taruwarsu, domin zuciyata ta fi haka daraja sosai. Domin cikin fushinsu sun kashe mutane. Saboda annashuwa ne suka turke shanu.
7Bari fushinsu ya la'ana, domin mai zafi ne - hasalarsu kuma domin mai tsanani ce. Zan rarraba su a Yakubu in kuma warwatsa su a Isra'ila.
8Yahuda, 'yan'uwanka zasu yabe ka. Hannunka zai kasance bisa wuyan maƙiyanka. 'Ya'yan mahaifinka za su rusuna a gabanka.
9Yahuda ɗan zaki ne. ‌Ɗana, ka haura daga kamammunka. Ka duƙa, ka rarrafa kamar zaki, kamar zakanya. Wa zai kuskura ya tada kai?
10Sandan sarauta ba za ta fita daga Yahuda ba, ko sandar mulki daga tsakanin ƙafafunsa, har sai Shilo ya zo. Al'ummai zasu yi masa biyayya.
11Yana ɗaure jakinsa ga kuringar inabinsa, da ɗan jakinsa ga zaɓaɓɓiyar kuringar inabinsa, ya wanke tufafinsa cikin ruwan inabi, da alkyabbarsa cikin jinin inabi.12Idanunsa zasu yi duhu kamar ruwan inabi, haƙoransa kuma farare kamar madara.
13Zebulun zai zauna a gaɓar teku. Zai zama masaukin jiragen ruwa, kuma kan iyakarsa za ta zarce har zuwa Sidon.
14Issaka jaki ne mai ƙarfi, yana zaune a tsakiyar turakun tumaki.15Yana ganin wurin hutawa mai kyau da ƙasa mai gamsarwa. Zai sunkuyar da kafaɗarsa domin kaya ya kuma zama bawa domin hidimar.
16Dan zai hukunta mutanensa a matsayin ɗaya daga cikin kabilun Isra'ila.17Dan zai zama maciji a gefen hanya, maciji mai dafi a tafarki dake cizon kofaton doki, saboda mahayinsa ya fãɗi ta baya.18Ina jiran cetonka, Yahweh.
19Gad - mahaya zasu kai masa hari, amma zai kai masu hari ta diddigensu.20Abincin Asha zai zama wadatacce, zai kuma bayar da girke-girken sarauta.21Naftali sakakkiyar barewa ce; zai haifi kyawawan 'ya'ya.
22Yosef mai hayayyafa ne, mai bayar da 'ya'ya ne, mai bayar da 'ya'ya dake gefen ƙorama wanda rassansa ke hawan katanga.23Maharba zasu kai masa hari, su kuma harbe shi, su firgita shi.
24Amma bakansa zai tsaya dai-dai, kuma hannayensa zasu ƙware saboda hannayen Mai Iko na Yakubu, saboda sunan Makiyayi, Dutsen Isra'ila.
25Allah na mahaifinka zai taimakeka kuma Allah Mai Iko Dukka zai albarkace ka da albarkun sararin sama, albarkun zurfafa dake kwance ƙarƙashin ƙasa, da albarkun nonna da mahaifa.
26Albarkun mahaifinka sun fi albarkun duwatsun zamanin dã ko abubuwan marmari na tuddan dã. Bari su kasance bisa kan Yosef, har bisa rawanin dake kan yariman 'yan'uwansa.
27Benyamin damisa ne mayunwaci. Da safe zai lanƙwame kamammensa, da yamma kuma zai raba ganimarsa."
28Waɗannan ne kabilu sha biyu na Isra'ila. Wannan ne abin da mahaifinsu ya ce masu sa'ad da ya albarkace su. Kowannen su ya albarkace shi bisa ga albarkar da ta dace.29Daga nan ya umarce su ya ce masu, "Ina gaf da tafiya ga mutanena. Ku bizne ni tare da kakannina a kogon dake cikin gonar Ifron Bahittiye,30a cikin kogon dake cikin gonar Makfela, wadda ke kusa da Mamri a ƙasar Kan'ana, gonar da Ibrahim ya saya a matsayin maƙabarta daga hannun Ifron Bahittiye.
31A nan ne aka bizne Ibrahim da matarsa Saratu; a nan ne suka bizne Ishaku da matarsa Rebeka; a nan ne kuma na bizne Liya.32Gonar da kogon dake cikin ta an saye su ne daga mutanen Het."33Da Yakubu ya gama waɗannan umarnai ga 'ya'yansa, ya ja ƙafafunsa cikin gadonsa, ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma tafi wurin mutanensa.

50

1Daga nan Yosef ya rikice, ya faɗi bisa fuskar mahaifinsa, ya kuma yi kuka a bisansa, ya kuma sumbace shi.2Yosef ya umarci bayinsa masu ilimin magani su nannaɗe mahaifinsa. Masu ilimin maganin suka nannaɗe Isra'ila da maganin hana ruɓewa.3Suka ɗauki kwana arba'in, domin wannan ne tsawon lokaci idan an naɗe gawa. Masarawa suka yi masa kuka na kwana saba'in.

4Da kwanakin makoki suka cika, Yosef ya yi magana da gidan Fir'auna, cewa, "Idan yanzu na sami tagomashi a idanunku, ina roƙonku ku yi magana da Fir'auna, ku ce,5'Mahaifina yasa in yi rantsuwa, cewa, "Duba, ina gaf da mutuwa. Ka bizne ni a kabarin dana gina domin kaina a ƙasar Kan'ana. A can zaka bizne ni." Yanzu bari in haye in tafi, in kuma bizne mahaifina, daga nan kuma zan dawo."'6Fir'auna ya amsa, "Ka tafi ka bizne mahaifinka, kamar yadda yasa ka yi rantsuwa."
7Yosef ya haye ya tafi bizne mahaifinsa. Dukkan 'yan majalisar Fir'auna suka tafi tare da shi - dattawan gidansa, dukkan manyan masu gari na ƙasar Masar,8tare da dukkan gidan Yosef da 'yan'uwansa, da gidan mahaifinsa. Amma 'ya'yansu, da garkunan tumakinsu, dana awaki, da garkunan shanunsu aka bari a ƙasar Goshen.9Karusai da mahaya dawaki suka tafi tare da shi. Babbar ƙungiyar mutane ce sosai.
10Sa'ad da suka iso bakin masussukar Atad a ɗayan gefen Yodan, suka yi makoki da babban makoki da baƙinciki mai tsanani. A can Yosef ya yi makokin kwana bakwai domin mahaifinsa.11Sa'ad da mazauna ƙasar, Kan'aniyawa, suka ga makokin a masussukar Atad, suka ce, "Wannan taro ne na baƙinciki sosai ga Masarawa." Shi yasa ake kiran wurin da suna Abel Mizrayim, wanda ke tsallaken Yodan.
12Daga nan 'ya'yan Yakubu suka yi masa kamar yadda ya umarta.13'Ya'yansa suka ɗauke shi zuwa ƙasar Kan'ana suka kuma bizne shi a kogon cikin gonar Makfela, kusa da Mamri. Ibrahim ya sayi kogon tare da gonar a matsayin maƙabarta. Ya saya ne daga Ifron Bahittiye.14Bayan da Yosef ya bizne mahaifinsa, sai ya koma cikin ƙasar Masar, shi, tare da 'yan'uwansa, da dukkan waɗanda suka raka shi bizne mahaifinsa.
15Sa'ad da 'yan'uwan Yosef suka ga cewa mahaifinsu ya mutu, suka ce, "To idan Yosef ya riƙe mu da fushi gãba da mu fa, kuma yana so ya yi mana cikakkiyar sakayya domin dukkan muguntar da muka yi masa?"16Sai suka umarci kasancewar Yosef, suka ce, "Mahaifinka ya bada umarni kafin ya mutu, cewa,17'Ku gaya wa Yosef haka, "Mu na roƙonka ka gafarta laifin 'yan'uwanka da zunubinsu sa'ad da suka yi maka mugunta."' Yanzu muna roƙonka ka gafartawa bayin Allah na mahaifinka. Yosef ya yi kuka sa'ad da suka yi masa magana.
18'Yan'uwansa kuma suka zo suka kwanta fuska ƙasa a gabansa. Suka ce, "Duba, mu bayinka ne."19Amma Yosef ya amsa masu, "Kada ku ji tsoro. Ina gurbin Allah ne?20Game da ku, kun yi niyyar mugunta a gare ni, amma Allah ya yi niyyar alheri ne, saboda a adana rayuwar mutane da yawa, kamar yadda kuka gani a yau.21Saboda haka, yanzu kada ku ji tsoro. Zan tanada maku da ƙananan 'ya'yanku." Ya ta'azantar dasu ta wannan hanyar ya kuma yi maganar mutunci ga zukatansu.
22Yosef ya zauna a Masar, tare da iyalin mahaifinsa. Ya yi rayuwa shekaru ɗari da goma.23Yosef ya ga 'ya'yan Ifraim har zuwa tsara ta uku. Ya kuma ga 'ya'yan Makir ɗan Manasse, waɗanda aka sanya a gwiwoyin Yosef.
24Yosef ya cewa 'yan'uwansa, "Ina gaf da mutuwa; amma tabbas Allah zai zo gare ku, ya kuma bida ku hayewa daga wannan ƙasa zuwa ƙasar da ya rantse zai ba Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu."25Daga nan Yosef ya sa mutanen Isra'ila suka rantse da alƙawari. Ya ce, "Tabbas Allah zai zo gare ku. A wannan lokacin tilas ku ɗauki ƙasusuwana daga nan."26Sai Yosef ya mutu, da shekaru 110. Aka nannaɗe shi da maganin hana ruɓa, kuma aka ajiye shi cikin akwati.

Littafin fitowa

1

1Ga sunanyen 'ya'yan Isra'ila da suka zo cikin Masar tare da Yakubu, kowannen su tare da iyalansa:2Ruben, da Simiyon, da Lebi, da kuma Yahuda,3da Issaka, da Zebulun da kuma Benyamin,4da Dan, da Naftali, da Gad, da Asha.5Dukkan zuriyar Yakubu su saba'in ne. Yosef yana nan a Masar.

6Sai Yosef, dukkan 'yan uwansa, da duk wannan tsãra suka mutu.7Isra'ilawa suka yi albarka, suka riɓaɓɓanya, da kuma ƙara ƙarfi sosai; ƙasar kuma ta cika da su.
8Yanzu dai sai wani sabon sarki ya taso a Masar, wanda bai san da Yosef ba.9Ya cewa mutanensa, "Ku duba, Isra'ilawan sun fi mu yawa da kuma ƙarfi.10Ku zo, bari mu bi da su cikin hikima, idan ba haka ba za su ci gaba da haɓɓaƙa, idan yaƙi ya taso, za su haɗa kai da maƙiyanmu, su yaƙe mu, su kuma bar ƙasar."
11Sai suka ɗora shugabannin aikin tilas a bisansu domin su wahalshe su da bauta mai zafi. Isra'ilawan suka gina wa Fir'auna biranen ajiya: Fitom da Ramesis.12Amma sa'ad da Masarawan suke ƙuntata masu, da haka Isra'ilawa ke ƙaruwa suna kuma yaɗuwa. Don haka Masarawan suka fara tsorata da Isra'ilawa.
13Masarawan suka sa Isra'ilawa su yi aiki mai tsanani.14Suka sa rayukan su suka yi ɗaci cikin hidimarsu a kwaɓa ƙasa da ginin tubali, da kuma dukkan ayyuka a cikin filaye. Dukkan aikin da ake so suyi masu wuya ne.
15Sai sarkin Masar ya yi magana da mataye unguwarzoma na Ibraniyawa; ɗaya sunanta Shifra, ɗayan kuma Fuwa.16Ya ce, "Lokacin da kuke taimaka wa matan Ibraniyawa a kujeran haihuwa, ku kula da lokacin da suka haihu. Idan ɗa namiji ne, to sai ku kashe shi; amma idan mace ce, to tana iya rayuwa."17Amma matan unguwarzoma suka ji tsoron Allah ba su kuma aikata yadda sarkin Masar ya umarce su ba; a maimakon haka, suka bar 'ya'ya maza su rayu.
18Sarkin Masar ya kirawo mataye unguwarzoman ya ce masu, "Don me kuka yi haka, da kuka bar 'ya'ya maza su rayu?"19Unguwarzoman suka ce wa Fir'auna, "Matayen Ibraniyawa ba kamar matayen Masar ba ne. Suna da ƙarfi kuma kamin mu iso gare su sun rigaya sun haihu."
20Allah kuma ya tsare waɗannan mata unguwarzoma. Mutanen kuma suka riɓaɓanya suka zama da ƙarfi sosai.21Domin mataye unguwarzoman sun ji tsoron Allah, sai ya ba su iyalai.22Sai Fir'auna ya ba dukkan mutanensa doka, "Dole ku jefa kowanne ɗan da aka haifa cikin kogi, amma kowacce ɗiya ku bar ta da rai."

2

1To akwai wani mutum daga kabilar Lebi wanda ke auren wata mace mutumiyar Lebi.2Macen ta yi juna biyu ta kuma haifi ɗan yaro. Da ta ga cewa yaron lafiyayye ne, sai ta ɓoye shi har wata uku.

3Amma da ya kai wani lokacin da ta ga ba za ta iya ɓoye shi ba, sai ta ɗauki kwandon iwa ta dalaye shi da katsi da ƙaro. Sai ta sanya jaririn ciki ta kuma saka shi cikin ruwan a cikin ciyayin bakin teku.4'Yar'uwarsa na tsaye daga nesa don ta ga abin da zai faru da shi.
5Ɗiyar Fir'auna ta gangaro zuwa kogin domin ta yi wanka yayin da kuyanginta na tafiya a gefen kogin. Sai ta hango kwandon cikin ciyayi sai ta aika kuyanginta su kawo shi.6Da ta buɗe, sai ta ga jaririn. Duba, jaririn na kuka. Sai ta yi juyayinsa ta kuma ce, "Wannan lallai ɗaya daga cikin 'ya'yan Ibraniyawa ne."
7Sai 'yar uwar jaririn ta ce ma ɗiyar Fir'auna, "In je in nemo maki mai reno daga cikin matan Ibraniyawa?"8Sai ɗiyar Fir'auna ta ce ma ta, "Je ki." Sai yarinyar ta tafi ta kuma samo uwar jaririn.
9Sai ɗiyar Fir'auna ta cewa uwar jaririn, "Ɗauki jaririn nan ki yi mani renon sa, ni kuma zan biya ki albashi." Sai matar ta ɗauki jaririn ta yi renon sa.10Da jaririn ya yi girma, sai ta kawo shi wurin ɗiyar Fir'auna, sai ya zama ɗanta. Ta raɗa masa suna Musa ta kuma ce, "Domin na tsamo shi daga ruwa."
11Da Musa ya yi girma, ya tafi wurin mutanensa ya kuma lura da nawayarsu. Sai ya ga wani Bamasare na bugun Ba'ibrane, ɗaya daga cikin mutanensa.12Sai ya waiga nan da can, da ya ga babu kowa a wurin, sai ya kashe Bamasaren ya kuma binne jikinsa cikin yashi.
13Washegari ya sake fita, kuma, gashi kuwa, biyu daga cikin mazajen Ibraniyawa suna faɗa da juna. Ya cewa wanda shi ke da rashin gaskiya, "Me ya sa kake dukan ɗan'uwan ka?"14Amma mutumin yace, "Waye ya sanya ka shugaba da mai shari'a bisanmu? Ko kana shirin kashe ni kamar yadda ka kashe wancan Bamasaren?" Sai Musa ya ji tsoro ya kuma ce, "Abin da na yi tabbas ba a ɓoye yake ga sauran ba."
15Ya zama kuma da Fir'auna ya ji abin da ya faru, sai ya yi ƙoƙarin kashe Musa. Amma Musa ya tsere daga gaban Fir'auna zuwa ƙasar Midiyan. A nan ya zauna a bakin wata rijiya.16Ya zama cewa firist na Midiyan na da 'yan mata guda bakwai. Suka zo, su ɗebi ruwa, su cika kwamayensu don su shayar da garkunan mahaifinsu.17Sai wasu makiyaya suka zo suka yi ƙoƙarin korar su, amma Musa ya tashi ya taimake su. Sai kuma ya shayar da dabbobinsu.
18Da 'yan matan suka komo wurin Ruwel mahaifinsu, ya ce, "Me ya sa kuka yi saurin dawo wa gida yau?"19Suka ce, "Wani Bamasare ne ya kuɓutar da mu daga hannun makiyayan. Har ma ya jawo mana ruwa ya shayar da garken."20Sai ya ce da 'yan matansa, "To ina yake? Don me kuka bar mutumin? Ku kira shi domin ya ci abinci tare da mu."
21Sai Musa ya yarda da ya zauna tare da mutumin, shi ma sai ya ba shi ɗiyarsa Ziffora ya aura.22Ta haifa masa ɗan yaro, sai Musa ya kira shi da suna Gashom; yana cewa, "Na zama mai baƙonci a cikin baƙuwar ƙasa."
23Bayan lokaci mai tsawo, sai sarkin Masar ya mutu. Isra'ilawa suka yi nishi saboda aikin bautarsu. Suka yi kukan neman taimako, sai kuma roƙon su ya kai ga Allah saboda bautarsu.24Sa'ad da Allah ya ga ƙuncinsu, Allah ya tuna da alƙawarinsa da Ibrahim, da Ishaku, da kuma Yakubu.25Allah ya ga Isra'ilawa, ya kuma fahimci matsalarsu.

3

1Yanzu dai Musa yana ta kiwon garken Yetro surukinsa, firist na Midiyan. Musa ya kai garken har iyakar sashen hamada ya kuma iso Horeb, tsaunin Allah.2A nan mala'ikan Yahweh ya bayyana gare shi cikin harshen wuta mai ci a kurmi. Sai Musa ya duba, ga shi, kurmin na ci da wuta, amma kurmin bai ƙone sarai ba.3Sai Musa yace, "Zan juya nan inga wannan abin ban mamaki, don me kurmin bai cinye ƙurmus da wutar ba."

4Sa'ad da Yahweh ya ga cewa ya juya garin ya duba, sai Allah ya yi kira gare shi daga cikin kurmin ya ce, "Musa, Musa." Musa yace, "Ga ni nan."5Allah yace, "Kada ka iso nan! Ka kwaɓe takalmanka daga kafafun ka, gama inda kake tsaye ƙasa ce keɓaɓɓiya a gare ni."6Ya kuma ce, "Ni ne Allahn mahaifinka, Allahn Ibrahim, da na Ishaku, da kuma na Yakubu." Sai Musa ya rufe fuskarsa, gama yana tsoron duban Allah.
7Yahweh yace, "Na ga azabar mutanena da suke a Masar. Na ji kururuwarsu sabili da shugabanninsu na aikin tilas, gama ina sane da wahalarsu.8Na sauko domin in kuɓutar da su daga ikon Masarawa in kuma fito da su daga wannan ƙasa zuwa ƙasa mai kyau, mai girma, ƙasa mai ɓulɓulo da madara da zuma; zuwa ƙasashen Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Amoriyawa, da Ferizziyawa, da Hibiyawa, da kuma Yebusiyawa.
9Yanzu dai kururuwar mutanen Isra'ila ta hau zuwa gare ni. Fiye da haka, na ga zaluncin da Masarawa suke gwada masu.10Ga shi yanzu, zan aike ka wurin Fir'auna domin ka fito da mutanena, Isra'ilawa, daga cikin Masar."
11Amma Musa ya cewa Allah, "Ni, wane ne, har da zan tafi wurin Fir'auna in kuma fito da Isra'ilawa daga cikin Masar?"12Allah ya amsa, "Ni zan kasance tare da kai tabbas. Wannan zai zama maka alama da cewa Ni na aike ka. Yayin da ka fito da mutanen daga Masar, za ku yi mani sujada a kan wannan n."
13Sai Musa ya cewa Allah, "Sa'ad da na tafi wurin Isra'ilawa na kuma ce masu, 'Allah na kakanninku ya aiko ni gare ku,' in kuma suka ce mani, 'Mene ne sunansa?' to me zan amsa masu?"14Sai Allah ya cewa Musa, "NI NE DA NAKE NI NE." Allah yace, "Dole ka faɗi wa Isra'ilawa, 'NI NE ya aiko ni gare ku."'15Allah ya kuma ce wa Musa, "Dole ka gaya wa Isra'ilawa, 'Yahweh, Allah na kakanninku, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da Allah na Yakubu, ya aiko gare ku. Wannan ne sunana har abada, kuma da haka za a tuna da ni cikin dukkan tsararraki.
16Ka tafi ka tara shugabannin Isra'ila tare. Ka ce masu, 'Yahweh, Allah na kakanninku, Allah na Ibrahim, na Ishaku, kuma da na Yakubu, ya bayyana gare ni ya ce, "Lallai na kula da ku na kuma ga abin da aka yi maku a Masar.17Na yi alƙawarin in fito da ku daga zaluncin Masar zuwa ƙasar Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Amoriyawa, da Feriziyawa, da Hibiyawa, da kuma Yebusiyawa, ƙasa mai zubo da madara da kuma zuma."'18Za su saurare ka. Da kai da shugabannin Isra'ila dole ku je wurin sarkin Masar, dole kuma ku faɗi masa, 'Yahweh, Allah na Ibraniyawa, ya gamu da mu. Saboda haka yanzu bari mu yi tafiyar kwana uku cikin jeji, domin mu yi hadaya ga Yahweh Allahnmu.'
19Amma na san da cewa sarkin Masar ba zai bar ku ku tafi ba, sai in an tilasta hannunsa.20Zan miƙa hannuna in kuma kai wa Masarawa farmaki da dukkan al'ajiban da zan aikata a tsakaninsu. Bayan haka, zai ƙyale ku ku tafi.21Zan bai wa mutanen nan tagomashi daga Masarawa, don haka lokacin da kuka fito, ba za ku fita hannu wofi ba.22Kowacce mace za ta roƙi ƙarafan azurfa da zinariya da kuma tuffafi daga maƙwabtansu Masarawa da kuma kowacce mace dake zama gidan maƙwabtanta. Za ku sanya su bisa 'ya'yanku maza da mata. Da haka za ku washe Masarawa."

4

1Sai Musa ya amsa, "Amma idan basu gaskata da ni ko su saurare ni ba amma suka ce a maimako, 'Yahweh bai bayyana gare ka ba'?"2Yahweh yace masa, "Menene wannan a hannunka?" Musa yace, "Sanda ce.3Yahweh yace, "Jefa ƙasa." Sai Musa ya jefar da ita ƙasa, sai ta zama maciji. Sai Musa ya guje masa.

4Yahweh ya cewa Musa, "Ka miƙa hannu ka riƙe wutsiyar." Sai ya miƙa hannu ya kuma kama macijin. Sai ta sake zama sanda cikin hannunsa.5"Wannan ya faru domin su gaskata da Yahweh, Allahn kakanninsu, Allah na Ibrahim, da Allah na Ishaku, da kuma Allah na Yakubu, ya bayyana gare ka."
6Yahweh ya sake ce masa, "Yanzu ka sanya hannun ka cikin rigarka." Sai Musa ya sanya hannunsa a cikin rigarsa. Da ya fito da shi, gashi kuwa, hannunsa ya kama kuturta, fari fat kamar ƙanƙara.7Yahweh yace, "Ka sake maida hannunka cikin riga, kuma da ya fito da shi, sai ya ga cewa an maido da lafiyarsa kuma, kamar sauran sashen fatarsa.
8Yahweh yace, "Idan basu gaskanta da kai ba - idan har basu kula da alama ta ikona na farko ba ko su gaskanta da ita ba, to za su gaskanta da alama ta biyun.9Idan kuma basu gaskanta da dukka waɗannan alamu biyu na ikona ba, ko su saurare ka, sai ka ɗebo ruwa daga kogi ka kuma tsiyaye shi a busasshiyar ƙasa. Ruwan daka ɗebo zai zama jini a bisa busasshiyar ƙasar."
10Sai Musa ya cewa Yahweh, "Ubangiji, ban taɓa iya magana da kyau ba, ko a dã ko tun lokacin daka yi magana da bawanka. Ni ba mai magana da sauri ba ne kuma harshena mai nauyi ne."11Yahweh yace dashi, "Wanene ya yi bakin mutum? Wa ke maida mutum bebe ko kurma ko mai gani ko makaho? Ba Ni ba ne, Yahweh?12Saboda haka yanzu ka tafi, Ni kuma zan kasance da kai in kuma koya maka abin da za ka faɗi."13Amma Musa yace, "Ubangiji, na roƙe ka ka aika da wani, duk wanda ka so ka aika."
14Sai Yahweh ya yi fushi da Musa. Yace, "To Haruna fa, ɗan'uwanka, Ba'lebi? Na san da cewar ya iya magana da kyau. Ga shi ma, yana fitowa don ya tarye ka, kuma sa'ad da ya ganka, zai yi murna cikin zuciyarsa.15Za ka yi magana dashi ka kuma sanya maganganun da zai faɗi a bakinsa. Zan kasance da bakinka da kuma bakin sa, kuma zan bayyana maku ku biyun abin da za ku yi.16Shi za ya yi magana ga mutanen a madadin ka. Zai zama bakinka, kai kuma za ka zama gareshi kamar ni, Allah.17Za ka ɗauki wannan sanda a hannunka. Da ita za ka aiwatar da alamun."
18Sai Musa ya komo wurin Yetro surukinsa ya kuma ce dashi, "Bari in tafi domin in koma ga dangina da su ke a Masar in kuma ga ko suna nan da rai." Sai Yetro ya cewa Musa, "Ka tafi cikin salama."19Yahweh ya cewa Musa cikin Midiyan, "Tafi, ka koma Masar, gama dukkan mazajen dake neman su ɗauke ranka sun mutu."20Musa ya ɗauki matarsa da 'ya'yansa ya ɗora su bisa jaki. Ya dawo zuwa ƙasar Masar, ya kuma ɗauki sandar Allah cikin hannunsa.
21Yahweh ya cewa Musa, "Lokacin da ka iso Masar, ka tabbata ka aikata a gaban Fir'auna dukkan abubuwan banmamaki da na sanya cikin ikonka. Amma zan taurare zuciyarsa, ba kuwa zai bar mutanen su tafi ba.22Dole ka cewa Fir'auna, 'Ga abin da Yahweh yace: Isra'ila ɗana ne, ɗan fãrina,23kuma ina ce maka, "Ka bar ɗana ya tafi, domin ya yi mani sujada." Amma tunda ka ƙi ka bar shi ya tafi, lallai zan kashe ɗanka, ɗanka na fãri.'"
24Yayin da suke kan hanya, da suka tsaya don su kwana a daren nan, Yahweh ya gamu da Musa ya kuma yi ƙoƙarin ya kashe shi.25Sai Ziffora ta ɗauki wuƙa mai kaifi ta yanke loɓar fatar ɗanta, ta taɓa shi da ita ga sawayensa. Sai ta ce, "Tabbas kai ango ne a gare ni ta wurin jini."26Sai Yahweh ya ƙyale shi. Ta ce, "Kai angon jini ne" sabili da kaciyar.
27Yahweh yace da Haruna, "Tafi cikin jeji ka gamu da Musa." Haruna ya tafi, ya gamu dashi a tsaunin Allah, ya yi masa sumba.28Sai Musa ya faɗa wa Haruna dukkan maganganun Yahweh da ya aike shi ya faɗi da dukkan alamu na ikon Yahweh da ya umarce shi ya aikata.
29Sai Musa da Haruna suka tafi suka tãra dukkan dattawan Isra'ila.30Haruna ya faɗi dukkan maganganun da Yahweh ya faɗa wa Musa. Ya kuma yi alamun na ikon Yahweh a gaban mutanen.31Mutanen suka gaskanta. Lokacin da suka ji cewa, Yahweh ya lura da Isra'ilawa kuma da cewa ya ga ƙuncinsu, sai suka sunkuyar da kansu suka kuma yi masa sujada.

5

1Bayan waɗannan abubuwan sun faru, sai Musa da Haruna suka je wurin Fir'auna suka kuma ce, "Ga abin da Yahweh, Allah na Isra'ila, yace: 'Ka bar mutane na su tafi, domin suyi ma ni biki a cikin jeji.'"2Fir'auna yace, "Wane ne Yahweh? Don me zan saurari muryarsa har da zan bar Isra'ila ya tafi? Ban san Yahweh ba; don haka, ba zan bar Isra'ila ya tafi ba."

3Suka ce, "Allah na Ibraniyawa ya gamu da mu. Ka bar mu mu yi tafiyar kwana uku cikin jeji mu kuma yi hadaya ga Yahweh Allahnmu domin kada ya kawo mana farmaki da annoba ko takobi."4Amma sarkin Masar yace ma su, 'Musa da Haruna, don me kuke ɗauke mutanen nan daga aikinsu? Ku koma ga aikinku."5Ya kuma ce, "Gashi yanzu akwai mutane Ibraniyawa dayawa a cikin ƙasarmu, kuma kuna sasu su daina aikinsu."
6A wannan ranar, Fir'auna ya bada umarni ga shugabannin aikin tilas da masu jagorar mutanen. Ya ce,7Ba kamar dã ba, ba za ku bada tattaka ga mutanen ba domin yin tubula. Bari su tafi su tarawa kansu budu.8Duk da haka, za ka buƙaci tubula daga garesu dai dai kamar yadda ka buƙata a dã. Kada ku karɓi abin da ya gaza yadda aka sãba, domin ƙyuya gare su. Shi yasa suke kira da cewar, 'Bari mu je mu yi hadaya ga Allahnmu.'9Ku ƙara wa mazajen aiki don su duƙufa cikinsa har da ba za su saurari maganganun yaudara ba."
10Sai shugabannin aikin tilas da masu jagorar mutanen suka fita suka yi magana da mutane. Suka ka ce, "Ga abin da Fir'auna yace: 'Ba zan ƙara baku wani budu ba.11Ku da kanku dole ku je ku kuma samo budu duk inda ake samunsa, amma aikin ku ba zai ragu ba.'"
12Don haka sai mutanen suka barbazu a ko'ina cikin ƙasar Masar domin su tãra yayi don budu.13Sai 'yan gandu suka ci gaba da tsananta masu suna cewa, "Ku gama aikin ku, kamar yadda dã ake baku tattaka."14Shugabannin aikin tilas na Fir'auna suka dinga bugun masu jagorar Isra'ilawa, waɗanda aka sanya bisa sauran ma'aikata. Shugabannin aikin tilas suka dinga tambayarsu, "Don me yasa baku yi dukkan ãdadin tubula da ake buƙata ba, ko na jiya da kuma na yau, kamar yadda kuka sãba a baya?"
15Sai masu jagora na Isra'ilawa suka shiga wurin Fir'auna da kuka gare shi. Suka ce, "Meyasa kake yi da bayinka haka?16Babu wata tattakar da ake ba bayin ka kuma, duk da haka suna ce mana, 'Ku yi tubula!' Mu ma, bayin ka, yanzu bugun mu ake yi, duk da haka laifin mutanen ka ne."17Amma Fira'auna yace, "Kuna da ƙyuya! Kuna da ƙyuya! Kun ce, 'Ka barmu mu je mu yi hadaya ga Yahweh.'18Saboda haka yanzu ku koma ga aiki. Ba za a ba ku tattaka ba, amma dole ne ku cika ãdadin tubulan ku."
19Sai masu jagorar Isra'ilawa suka ga cewa suna cikin matsala lokacin da aka ce da su, "Ba za ku rage tubula na kowace rana ba."20Sai suka sami Musa da Haruna, a wannan lokaci suna tsaye a wajen fãdar, sa'ad da suke fitowa daga wurin Fir'auna.21Suka cewa Musa da Haruna, 'Bari Yahweh ya dube ku ya kuma hore ku, domin kunsa mun zama abin kyama a gaban Fir'auna da kuma bayinsa. Kun sanya takobi a hannunsu don su kashe mu."
22Sai Musa ya komo ga Yahweh ya kuma ce, "Ubangiji, meyasa ka kawo wahala ga mutanenka? Meyasa ka aiko ni tun da farko?23Tun lokacin da na iso wurin Fir'auna domin in yi magana da shi a sunanka, ya jawo wa mutanen nan wahala, kuma baka ƙubutar da mutanenka ba sam-sam."

6

1Daga nan Yahweh ya cewa Musa, "Yanzu ne za ka ga abin da zan yi wa Fir'auna. Za ka ga wannan, gama zai barsu su tafi sabili da hannuna mai ƙarfi. Sabili da hannuna mai ƙarfi, zai kore su daga ƙasarsa."

2Allah ya yi magana da Musa ya kuma ce masa, "Ni ne Yahweh.3Na bayyana ga Ibrahim, ga Ishaku, ga Yakubu kuma a matsayin Allah Mai Iko Dukka; amma da sunana, Yahweh, basu san Ni ba.4Na kuma kafa alƙawari na da su, domin in ba su ƙasar Kan'ana, ƙasar da suka zauna a matsayin baƙi, ƙasar da suka yi yawo a ciki.5Bugu da ƙari, na ga ƙuncin 'ya'yan Isra'ila waɗanda Masarawa suka bautar, kuma na tuna da alƙawarina.
6Saboda haka, ka gaya wa Isra'ilawa, 'Ni ne Yahweh. Zan fito da ku daga bautar Masarawa, kuma zan fishe su daga ƙarƙashin ikon su. Zan kuɓutar da ku ta wurin nuna ikona, tare da manyan ayyukan hukunci.7Zan ɗauke ku a gare ni a matsayin mutane na, zan kuma zama Allahnku. Za ku sani Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya fito da ku daga bautar Masarawa.
8Zan kawo ku cikin ƙasar da na rantse in ba Ibrahim, da Ishaku, da kuma Yakubu. Zan bada ita gareku abin mallaka. Ni ne Yahweh."'9Da Musa ya faɗi wannan ga Isra'ilawa, sai suka ƙi su saurare shi saboda karayar zucinsu sabili da bautarsu mai zafi.
10Sai Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,11"Tafi ka faɗi wa Fir'auna, sarkin Masar, ya bar mutanen Isra'ila su tafi daga ƙasarsa."12Sai Musa ya cewa Yahweh, "To idan har Isra'ilawa ba su saurare ni ba, don me Fir'auna zai saurare ni, tunda ban ƙware a magana ba?"13Yahweh ya yi magana da Musa da kuma Haruna. Ya ba su umarni domin Isra'ilawa domin kuma Fir'auna, sarkin Masar, su fito da Isra'ilawa daga ƙasar Masar.
14Waɗannan su ne shugabannin gidajen kakanninsu: 'Ya'yan Ruben, ɗan fari na Isra'ila, su ne Hanok, da Fallu, da Hezron, da kuma Karmi. Waɗannan su ne kakannin kabilar Ruben.15'Ya'yan Simiyon su ne Yemuwel, da Yamin, da Ohad, da Yakin, da Zohar, da kuma Shawul - ɗan wata mace Bakan'aniya. Waɗannan su ne kakannin kabilar Simiyon.
16Ga jerin sunayen 'ya'yan Lebi, tare da zuriyarsu. Sune Gashon, da Kohat, da kuma Merari. Lebi ya yi rayuwa har shekaru 137.17'Ya'yan Gashon su ne Libni da Shimei.18'Ya'yan Kohat su ne Amram, da Izhar, da Hebron, da kuma Uzziyel. Kohat ya yi rayuwa har ya kai shekaru 133.19'Ya'yan Merari su ne Mahli da Mushi. Waɗannan suka zama kakannin kabilar Lebiyawa, tare da zuriyarsu.
20Amram ya auri Yokebeb, 'yar'uwar mahaifinsa. Ta haifar masa Haruna da Musa. Amram ya yi rayuwa har tsawon shekaru 137 sai kuma ya mutu.21'Ya'yan Izhar su ne Korah, da Nefeg, da Zikri.22'Ya'yan Uzziyel su ne Mishyel, da Elzafan, da kuma Sitri.
23Haruna ya auri Elisheba, ɗiyar Amminadab, 'yar uwar Nahshon. Ta haifar masa Nadab da Abihu, da Eliyeza da kuma Itamar.24'Ya'yan Kora su ne Assir, da Elkana, da kuma Abiyasaf. Waɗannan su ne kakannin kabilar Korahawa.25Eliyeza, ɗan Haruna, ya auri ɗaya daga cikin 'ya'ya matan Futiyel. Ta haifa masa Finehas. Waɗannan su ne shugabannin gidajen ubanni a cikin Lebiyawa, tare da zuriyarsu.
26Waɗannan mutanen biyu su ne Haruna da Musa a gare su ne Yahweh yace, "Ku fito da 'ya'yan Isra'ilawa daga ƙasar Masar, bisa ga ƙungiyoyinsu na mayaƙa."27Sai Haruna da Musa suka yi magana da Fir'auna, sarkin Masar, da ya barsu su fito da Isra'ilawa daga Masar. Waɗannan dai Musa da Harunan ne.
28Da Yahweh ya yi magana da Musa a cikin ƙasar Masar,29ya ce masa, "Ni ne Yahweh. Ka ce wa Fir'auna, sarkin Masar, dukkan abin da zan faɗa maka."30Amma Musa ya cewa Yahweh, "Ban ƙware ba wurin magana, don haka ta yaya Fir'auna zai saurare ni?"

7

1Yahweh ya cewa Musa, "Duba, Na maishe ka kamar wani allah ga Fir'auna. Haruna ɗan'uwanka zai zama annabi dominka.2Za ka faɗi dukkan abin da na dokace ka ka faɗa. Haruna ɗan'uwanka zai yi magana da Fir'auna don ya bar mutanen su tafi daga ƙasarsa.

3Amma zan taurare zuciyar Fir'auna, kuma zan bayyana alamu masu yawa na iko na, abubuwa masu ban mamaki, cikin ƙasar Masar.4Amma Fir'auna ba zai saurare ku ba, saboda haka zan saukar da hannuna bisa Masar in kuma kawo ƙungiyoyin mayaƙana, mutanena, zuriyar Isra'ila, daga cikin ƙasar Masar da manyan ayyuka na shara'antawa.5Masarawa zasu sani Ni ne Yahweh sa'ad da na miƙa hannuna bisa Masar na kuma fito da Isra'ilawa daga cikin su."
6Sai Musa da Haruna suka aikata haka; suka yi dai-dai kamar yadda Yahweh ya dokace su.7Musa yana da shekara tamanin, Haruna kuma yana da shekara tamanin da uku a lokacin da suka yi magana da Fir'auna.
8Yahweh ya cewa Musa da Haruna,9"Idan Fir'auna yace maku, 'Ku yi abin al'ajibi,' sai ka ce wa Haruna, 'Ka ɗauki sandarka ka kuma jefa ta ƙasa a gaban Fir'auna, domin ta zama maciji.'"10Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir'auna, sai kuma suka yi kamar yadda Yahweh ya umarce su. Haruna ya jefar da sandarsa ƙasa a gaban Fir'auna da bayinsa, sai ta zama maciji.
11Sai Fir'auna shima ya kira masu hikimarsa da masu duba. Sai su ma suka yi haka ta wurin sihiri.12Kowanne mutum ya jefar da sandarsa ƙasa, sai sandunan suka zama macizai. Amma sai macijin Haruna ya haɗiye macizansu.13Amma zuciyar Fir'auna ta taurare, bai kuwa saurara ba, kamar yadda Yahweh ya faɗa tun dã.
14Yahweh ya cewa Musa, "zuciyar Fir'auna ta yi tauri, kuma ya ƙi ya bar mutanen su tafi.15Ka tafi wurin Fir'auna da safe lokacin da ya fita wurin ruwan. Ka tsaya daga bakin kogin don ka tarye shi, ka kuma ɗauki sandarka a hannunka sandar da ta zama maciji.
16Ka ce masa, 'Yahweh, Allah na Ibraniyawa, ya aike ni gare ka in ce maka, "Ka bar mutanena su tafi, don su yi mani sujada cikin jeji. Har yanzu baka saurara ba."17Yahweh ya faɗi wannan: "Ta haka zaka sani Ni ne Yahweh. Zan bugi ruwa na Kogin Nilu da sandar dake a hannuna, sai kuma ruwan ya zama jini.18Kifayen da suke a cikin kogin za su mutu, kuma kogin zai yi ɗoyi. Masarawa ba za su iya shan ruwa daga kogin ba.'""
19Sai Yahweh yace da Musa, "Ka ce wa Haruna, 'Ka ɗauki sandarka ka miƙa ta zuwa ga ruwayen Masar, da kuma zuwa ga kogunansu, da rafufukansu, da kududdufansu, da kuma dukkan tafkunansu, domin ruwayensu sun zama jini. Ka yi wannan domin a sami jini cikin dukkan ƙasar Masar, har ma da randunan itace da na duwatsu.'"
20Sai Musa da Haruna suka yi kamar yadda Yahweh ya umarta. Haruna ya miƙa sandar ya kuma bugi ruwan kogin, a gaban Fir'auna da bayinsa. Sai dukkan ruwaye na kogunan suka zama jini.21Kifayen kogin suka mutu, sai kogin ya fara ɗoyi. Masarawa ba su iya shan ruwa daga kogin ba, kuma sai jinin ya bazu ko'ina a cikin ƙasar Masar.22Amma masu sihiri na Masar suka yi haka dai-dai da dabonsu. Amma zuciyar Fir'auna an taurare, sai kuma ya ƙi ya saurari Musa da Haruna, kamar yadda Yahweh ya faɗi zai faru.
23Sai Fir'auna ya juya ya koma gidansa. Bai ma ba da hankalinsa ga wannan ba.24Dukkan Masarawa suka haƙa rami a gefen kogin don su sami ruwa su sha, amma ba su iya shan ruwan kogin da kansa ba.25Kwana bakwai suka wuce bayan da Yahweh ya kai farmaƙi ga kogin.

8

1Sai Yahweh ya yi magana da Musa, "Ka tafi wurin Fir'auna ka kuma ce masa, 'Yahweh ya faɗi wannan: "Ka bar mutanena su tafi domin suyi mani sujada.2Idan ka ƙi ka barsu su tafi, zan azabtar da dukkan ƙasarka da ƙwaɗi.3Kogunan za su cika da kwaɗi. Za su fito su shiga gidajenku, da ƙuryar ɗakinku, da kan gadonku. Za su shiga cikin gidajen bayinku. Za su kai ga mutanenka, cikin murhunka, da kuma cikin makwaɓan ƙullunka.4Kwãɗin za su hau kanka, da mutanenka, da kuma dukkan bayinka.""'

5Yahweh ya cewa Musa, "Ka ce wa Haruna, 'Miƙa hannun ka tare da sandarka bisa kogunan, da rafufuka, da kuma kududdufai, ka kawo kwãɗi bisa ƙasar Masar."'6Sai Haruna ya miƙa hannunsa bisa ruwayen Masar, sai kwãɗin suka zo suka rufe dukkan ƙasar Masar.7Amma bokayen suka aikata irin haka da dabonsu; suka kawo kwãɗi bisa ƙasar Masar.
8Sai Fir'auna ya kirawo Musa da Haruna ya kuma ce, "Ku yi addu'a ga Yahweh don ya kawar da kwãɗin daga gare ni da mutanena. Sa'an nan zan bar mutanen su tafi, domin su yi masa hadaya."9Musa ya cewa Fir'auna, "Kana iya samun zarafin gaya mani in yi maka addu'a, da bayinka, da kuma mutanenka, don a kawar da kwãɗin daga gare ku da gidajenku su kuma tsaya a cikin kogin kawai."
10Fir'auna yace, "Gobe." Musa yace, "Bari shi zama yadda ka faɗa, don ka san cewa babu wani kamar Yahweh, Allahnmu.11Kwãɗin za su bar ka, da gidajenka, da bayinka, da kuma mutanenka. Za su tsaya cikin kogi ne kawai."12Sai Musa da Haruna su ka fito daga gaban Fir'auna. Sai Musa ya yi kuka ga Yahweh game da kwãɗin da ya kawo bisa Fir'auna.
13Yahweh ya aikata kamar yadda Musa ya roƙa: Sai kwãɗin suka mutu cikin gidajen, daga shirayi, da filaye.14Sai mutanen suka tara su tuli-tuli, sai kuma ƙasar ta yi ɗoyi.15Amma da Fir'auna ya ga cewa akwai sauƙi, sai ya taurare zuciyarsa bai kuma saurari Musa da Haruna ba, kamar yadda Yahweh yace zai yi.
16Yahweh ya cewa Musa, "Ka ce da Haruna, 'Ka miƙa sandarka ka bugi ƙurar ƙasa, don ta zama kwarkwata cikin dukkan ƙasar Masar."'17Suka aikata haka: Haruna ya miƙa hannunsa da sandarsa. Ya bugi ƙura a ƙasa. Sai kwarkwata masu yawa suka zo bisa mutum da dabba. Dukkan ƙurar ƙasa ta zama kwarkwata cikin dukkan ƙasar Masar.
18Sai bokayen su ma suka gwada da sihirinsu domin su fito da kwarkwata, amma ba su iya yin haka ba. Aka sami kwarkwata a bisa mutane da kuma dabbobi.19Sai bokayen suka ce wa Fir'auna, "Wannan yatsan Allah ne." Amma zuciyar Fir'auna ta taurare, don haka bai saurare su ba. Dai-dai ne ga yadda Yahweh ya faɗi cewa Fir'auna zai yi.
20Yahweh ya cewa Musa, "Ka tashi da sauri da safe ka kuma tsaya a gaban Fir'auna yayin da ya fito zuwa kogi. Ka ce da shi, 'Yahweh ya faɗi wannan: "Ka bar mutanena su tafi don suyi mani sujada.21Amma idan baka bar su sun tafi ba, zan aiko da cin-cirindon ƙudaje gareka, zuwa ga bayinka, da kuma mutanenka, da kuma cikin gidajenka. Gidajen Masarawa za su cika da cin-cirindon ƙudaje, har ma da ƙasar da suke tsayawa za ta cika da ƙudaje.
22Amma a wannan ranar zan bambanta ƙasar Goshen, ƙasar da mutanena suke zama, don kada a sami wani cin-cirindon ƙudaje a nan. Wannan zai faru domin ka san cewa Ni ne Yahweh da nake tsakiyar wannan ƙasa.23Zan bambanta tsakanin mutanena da mutanenka. Wannan alama ce ta ikona zai faru gobe.""'24Yahweh ya yi haka, sai kuma cin-cirindon ƙudaje mai kauri suka aukawa gidan Fir'auna da kuma gidajen bayinsa. Cikin dukkan ƙasar Masar, ƙasar ta lalace ta dalilin cin-cirindon ƙudajen.
25Sa'an nan Fir'auna ya kira Musa da Haruna yace, "Ku tafi, ku yi hadaya ga Allahnku a cikin ƙasarmu."26Musa yace, "Bai yi dai-dai ba muyi haka, gama hadayar da muke yi ga Yahweh Allahnmu abar ƙyama ce ga Masarawa. Idan muka miƙa hadayar suna gani abin ƙyama ga Masarawa, ba zasu jejjefemu ba?27Ba haka ba, tafiyar kwana uku ce cikin jeji da ya kamata muyi, domin muyi hadaya ga Yahweh Allahnmu, kamar yadda ya umurce mu."
28Fir'auna yace, "Zan bar ku don ku tafi ku yiwa Allahnku hadaya cikin jeji. Sai dai kada ku tafi da nisa sosai. Ku yi mani addu'a.29Musa yace, "Da zarar na fita daga gare ka, zan yi roƙo ga Yahweh domin cin-cirindon ƙudaje su bar ka, Fir'auna, da bayinka da kuma mutanenka gobe. Amma kada ka ƙara yin yaudara ta wurin ƙin barin mutanenmu su tafi su yiwa Yahweh hadaya."
30Sai Musa ya fita daga gaban Fir'auna ya kuma yi roƙo ga Yahweh.31Yahweh ya yi yadda Musa ya roƙa; ya kuma janye cin-cirindon ƙudaje daga Fir'auna, da bayinsa, da mutanensa. Babu wanda ya rage32Amma Fir'auna ya taurare zuciyarsa wannan lokaci kuma, ya kuma ƙi barin mutanen su tafi.

9

1Sa'an nan Yahweh yace da Musa, "Jeka wurin Fir'auna ka ce masa, 'Yahweh, Allah na Ibraniyawa, ya faɗi wannan: "Bar mutanena su tafi domin suyi mani sujada."2Amma idan baka yarda ka bar su ba, idan ka hana su,3daganan hannun Yahweh zai kasance bisa garken shanunka cikin filaye da kuma bisa dawakai, da jakuna, da raƙuma, garkunan dabbobi, da garkunan tumaki da awaki, kuma zai yi sanadiyar cuta mai banrazana.4Yahweh zai bambanta garken Isra'ilawa da ta Masarawa kuma babu dabbar dake ta Isra'ilawa da za ta mutu.

5Yahweh ya tsayar da lokaci; ya riga yace, "Gobe ne zan aikata wannan abin cikin ƙasar.""'6Yahweh ya yi wannan washegari: Dukkan garkunan shanun Masar suka mutu, amma babu dabbar da ke ta Isra'ila da ta mutu, ko dabba ɗaya.7Fir'auna ya yi bincike, kuma, duba, ko da ɗaya na dabbar Isra'ilawa bata mutu ba. Amma zuciyarsa ta taurare, don haka bai yadda mutanen su tafi ba.
8Sai Yahweh ya cewa Musa da Haruna, "Ku ɗebo toka daga murhu. Kai, Musa, dole ka watsa tokar sama cikin iska yayin da Fir'auna na gani.9Za su zama ƙura mai laushi bisa dukkan ƙasar Masar. Za su yi sanadiyar gyambuna da kuma marurai su addabi mutane da dabbobi cikin dukkan ƙasar Masar."10Sai Musa da Haruna suka ɗebo toka daga murhu suka kuma tsaya a gaban Fir'auna. Sai Musa ya watsar da tokar cikin iska. Tokar ta yi sanadiyar gyambuna da marurai da suka addabi mutane da dabbobi.
11Bokayen ba su iya tsayayya da Musa ba sabili da gyambunan, domin gyambunan sun kama su da sauran Masarawa.12Yahweh ya taurare zuciyar Fir'auna, don haka Fir'auna bai saurari Musa da Haruna ba. Wannan kamar yadda Yahweh ya riga ya gaya wa Musa ne cewa Fir'auna zai yi.
13Sai Yahweh yace wa Musa, "Ka tashi da sassafe, ka tsaya a gaban Fir'auna, ka kuma ce masa, 'Yahweh, Allah na Ibraniyawa, ya faɗi wannan: "Ka bar mutanena su tafi domin suyi mani sujada.14Gama a wannan karon zan aiko da dukkan annobaina a kanka, a bisa bayinka da mutanenka. Zan aikata wannan domin ka san cewa babu wani mai kama da ni cikin dukkan duniya.
15Ko a yanzu da na miƙa hannuna in kai maka farmaki da mutanenka da cuta, kuma da yanzu an kawar da kai daga ƙasar.16Amma sabili da wannan dalili ne na bar ka ka tsira: Domin in nuna maka ikona, domin a shaida sunana a cikin dukkan duniya.17Har yanzu kana ɗaukaka kanka gãba da mutanena da har yanzu baka barsu su tafi ba.
18Ka saurara! Gobe warhaka zan kawo ruwa da ƙanƙara mai ƙarfi, irin wadda ba a taɓa gani ba a cikin ƙasar Masar ba tun lokacin da aka kafa ta zuwa yau.19Yanzu dai, ku aika mazaje su dawo da garken ku da dukkan abin da kuke da shi a cikin gonaki zuwa ga mafaka. Kowanne mutum da dabba dake a gona da ba a shigo da su gida ba - ƙanƙarar zata faɗo masu, za su kuma mutu.""'
20Sa'an nan wasu daga cikin bayin Fir'auna waɗanda suka gaskanta da saƙon Yahweh suka yi hanzari suka dawo da bayinsu da kuma garkensu cikin gidaje.21Amma waɗanda ba su ɗauki maganar Yahweh da wani mahimmanci ba suka bar bayinsu da garken su cikin gonaki.
22Sai Yahweh yace wa Musa, "Miƙa hannunka zuwa sararin sama don a yi ƙanƙara cikin dukkan ƙasar Masar, bisa mutane, bisa dabbobi, da kuma dukkan itatuwan cikin gonaki a dukkan ƙasar Masar."23Sai Musa ya miƙa sandarsa zuwa sararin sama, sai Yahweh ya aiko da aradu, ƙanƙara, da walkiya a ƙasar. Ya kuma kwararo ruwan ƙanƙara a bisa ƙasar Masar.24Saboda haka aka yi ƙanƙara da walƙiya gauraye da ƙanƙarar, mai tsananin gaske, irin da ba a taɓa yi ba cikin dukkan ƙasar Masar tun lokacin da ta zama al'umma.
25A dukkan ƙasar Masar kuwa, ƙankaran ta bugi kowanne abu cikin gonaki, da mutane da kuma dabbobi. Ta bugi kowacce shuka dake a gonaki ta kuma karya kowanne itace.26A ƙasar Goshen ne kaɗai, inda Isra'ilawa ke zama, babu ƙanƙara.
27Daga nan sai Fir'auna ya aika da mutane su kawo Musa da Haruna. Ya ce masu, "Na yi zunubi dai yanzu. Yahweh mai adalci ne, ni kuwa da mutanena mugaye ne.28Ku yi addu'a ga Yahweh, domin waɗannan tsawa mai ƙarfi da kuma ƙanƙara sun yi yawa. Zan barku ku tafi, ba kuma zaku zauna nan ba."
29Musa yace masa, "Da zarar na fita daga birnin, zan buɗe hannuwana ga Yahweh. Tsawar aradun zata tsaya, kuma babu sauran ƙanƙara. Ta haka zaka sani cewa duniyar ta Yahweh ce.30Amma game da kai da bayinka, Na san da cewa har yanzu baka rigaya ka girmama Yahweh Allah ba da gaske."
31Yanzu dai da hatsi da kuma riɗi an lallatar da su, gama riɗi ta yi ido, hatsi kuma tana fidda kai.32Amma alkama da gero ba a ji masu rauni ba domin ba su yi girma ba tukuna.33Bayan da Musa ya bar Fir'auna da kuma birnin, ya miƙa hannuwansa ga Yahweh; tsawa da ƙanƙara suka tsaya, sai kuma ruwan sama bai sake saukowa ba.
34Sa'ad da Fir'auna ya ga cewa ruwan sama ya tsaya, da ƙanƙarar, da tsawar aradun sun tsaya, sai ya sake yin zunubi ya taurare zuciyarsa, duk da bayinsa.35Zuciyar Fir'auna ta taurare, don haka bai bar mutanen Isra'ila su tafi ba. Yadda Yahweh ya riga ya faɗa wa Musa cewa Fir'auna zai aikata.

10

1Yahweh ya cewa Musa, "Ka tafi wurin Fir'auna, gama na taurare zuciyarsa da zuciyar bayinsa. Na yi haka ne domin in nuna waɗannan alamun ikon ƙarfina a cikin su.2Na kuma yi haka ne domin ku gaya wa 'ya'yanku da jikokinku abubuwan dana yi, yadda na fusata bisa Masar, da kuma yadda na nuna alamu daban-daban na ƙarfin ikona a tsakaninsu. Da haka zaku sani Ni ne Yahweh."

3Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir'auna suka kuma ce masa, "Yahweh, Allah na Ibraniyawa, ya faɗi wannan: 'Har yaushe zaka ƙi ka ƙasƙantar da kanka a gabana? Ka bar mutanena su tafi domin suyi mani sujada.4Amma idan ka ƙi ka bar mutanena su tafi, ka saurara, gobe zan kawo fãri cikin ƙasarka.
5Za su rufe fuskar ƙasa har babu wanda zai iya ganin ƙasa. Za su chinye kowanne abin da ya tsira daga ƙanƙara. Za su kuma cinye kowanne itacen da ya tsiro domin ka cikin gonaki.6Za su cika gidajenka, da na bayinka, da na dukkan Masarawa - abu ne wanda mahaifinka da kakanka basu taɓa gani ba, abin da ba a taɓa gani ba tun daga ranar da suke cikin duniya har wa yau.'" Daga nan Musa ya fita ya kuma bar Fir'auna.
7Sai bayin Fir'auna suka ce masa, "Har yaushe wannan mutum zai zama mana bala'i? Ka bar Isra'ilawan su tafi domin su yi wa Yahweh Allahnsu sujada. Ko ba ka fahimci cewa an hallakar da Masar ba?"8Aka kawo Musa da Haruna kuma a gaban Fir'auna, sai yace masu, "Ku tafi ku yiwa Yahweh Allahnku sujada. Amma waɗanne mutane ne za su tafi?"
9Musa yace, "Za mu tafi tare da ƙanananmu da kuma tsofofinmu, tare da 'ya'yanmu maza da 'ya'ya mata. Zamu tafi da tumakanmu da garkenmu, gama dole ne muyi buki ga Yahweh."10Fir'auna yace masu, "Bari Yahweh lallai ya kasance tare da ku, idan har na barku ku tafi tare da 'yan ƙanananku. Duba, kana da wata mugunta a cikin zuciya.11Ba haka ba! Ku tafi, mazaje kawai na cikinku, ku yiwa Yahweh sujada, gama abin da kuke so kenan." Sa'an nan aka kori Musa da Haruna daga fuskar Fir'auna.
12Sai Yahweh ya cewa Musa, "Ka miƙa hannunka bisa ƙasar Masar zuwa ga fãrin, domin su abko wa ƙasar Masar su kuma cinye dashe-dashen cikin ta, dukkan sauran abubuwan da ƙanƙara ta rage."13Musa ya miƙa sandarsa bisa Masar, Yahweh kuwa ya aiko da iskar gabas bisa ƙasar dukkan wannan rana da dare. Sa'ad da safiya ta yi, iskar gabas ta riga ta kawo fãrin.
14Fãrin suka shiga dukkan ƙasar Masar suka kuma cutar da dukkan sassanta. Ba a taɓa yin irin wannan cin-cirindon fãri cikin ƙasar ba, ba kuma za a sake mai kamannin haka ba.15Suka rufe fuskar dukkan ƙasa har wuri ya yi duhu. Suka cinye dukkan dashe-dashe da ke cikin ƙasa da dukkan 'ya'yan itatuwan da ƙanƙara ta rage. A cikin dukkan ƙasar Masar, babu koren tsiro mai rai da ta ragu, ko wani itace ko dashe a cikin gonaki.
16Sa'an nan Fir'auna ya kirawo Musa da Haruna ya kuma ce, "Na yi zunubi ga Yahweh Allahnku, da gare ku kuma.17Yanzu dai, ku gafarta zunubi na wannan kãron, kuyi addu'a ga Yahweh Allahnku don ya ɗauke wannan mutuwa daga gare ni."18Don haka Musa ya fita daga gaban Fir'auna ya yi addu'a ga Yahweh.
19Yahweh ya kawo babbar iskar yamma mai ƙarfi da ta kwashe fãrin ta kora su cikin Jan Teku; babu fãrar da ta rage cikin dukkan lardunan Masar.20Amma Yahweh ya taurare zuciyar Fir'auna, kuma Fir'auna bai bar Isra'ilawa su tafi ba.
21Sai Yahweh ya cewa Musa, "Ka miƙa hannunka zuwa sararin sama, don a yi duhu bisa ƙasar Masar, duhun da za a iya taɓawa."22Sai Musa ya miƙa hannunsa zuwa sama, sai aka yi wani gaggarumin duhu bisa dukkan ƙasar Masar har na kwana uku. Babu wanda ya iya ganin wani;23Babu wanda ya bar gidansa har kwana uku. Duk da haka, dukkan Isra'ilawa suna da haske a wurin da suke zaune.
24Sai Fir'auna ya aika aka kawo Musa sai yace, "Ku tafi ku yi wa Yahweh sujada. Har da iyalanku na iya tafiya tare da ku, amma garkunan ku na tumaki dole ku bar su nan."25Amma Musa yace, "To dole ka ba mu dabbobin da zamu yi hadaya ga Yahweh Allahnmu.26Garkunan mu dole mu tafi da su; babu ko ƙofaton su da zai rage a baya, gama dole ne mu tafi da su domin yin sujada ga Yahweh Allahnmu. Gama ba mu san da mene ne za mu yi sujada ga Yahweh ba, sai mun isa can."
27Amma sai Yahweh ya taurare zuciyar Fir'auna, har da ba zai bar su su tafi ba.28Fir'auna ya cewa Musa, "Ka fita daga gare ni! Kayi hankali da abu ɗaya, cewa kada ka ƙara gani na, gama duk ranar da ka ga fuskata, za ka mutu."29Sai Musa yace masa, "Kai da kanka ka faɗa. Ba zan ƙara ganin fuskarka ba."

11

1Daga nan Yahweh ya cewa Musa, "Akwai sauran annoba guda ɗaya da zan kawo bisa Fir'auna da Masar. Bayan wannan, zai barku ku tafi daga nan. Sa'ad da a ƙarshe ya barku kuka tafi, zai kore ku gaba ɗaya.2Ka umarci mutanen cewa kowanne mutum da kowacce mace su roƙi maƙwabcinsa ko maƙwabciyarta kayayyakin azurfa da kayayyakin zinariya."3Yanzu dai Yahweh ya sa Masarawa suyi ɗokin farantawa Isra'ilawa rai. Bugu da ƙari, mutumin nan Musa ya birge sosai a gaban barorin Fir'auna da mutanen Masar.

4Musa yace, "Yahweh ya faɗi wannan: 'Wajen tsakar dare zan ratsa cikin dukkan Masar.5Dukkan 'ya'yan fãri cikin ƙasar Masar za su mutu, daga ɗan fãrin Fir'auna, wanda ke zaune bisa kursiyinsa, zuwa ɗan fãrin baiwa wanda ke bayan dutsen niƙa tana niƙa, da dukkan 'ya'yan fãrin dabbobi.
6Daga nan za a yi babban makoki cikin dukkan ƙasar Masar, irin wanda ba a taɓa yi ba kuma ba za a ƙara yi ba.7Amma babu ko kare da zai yi haushi ga ko ɗaya daga cikin mutanen Isra'ila, ko ga mutum ko dabba. Ta wannan hanya za ku sani cewa ina nuna bambanci tsakanin Masarawa da Isra'ilawa.'8Dukkan waɗannan bayin naka, Fir'auna, za su sauko zuwa gare ni su rusuna mani. Za su ce, 'Ka tafi, kai da dukkan mutanen da suka biyo ka!' Bayan wannan zan fita." Daga nan ya fita daga wurin Fir'auna da babban fushi.
9Yahweh ya cewa Musa, "Fir'auna ba zai saurare ka ba. Wannan ya zama haka ne domin in aiwatar da abubuwan ban mamaki masu yawa a cikin ƙasar Masar."10Musa da Haruna suka yi dukkan waɗannan al'ajibai a gaban Fir'auna. Amma Yahweh ya kangarar da zuciyar Fir'auna, Fir'auna kuma bai bar mutanen Isra'ila suka fita daga ƙasarsa ba.

12

1Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna a cikin ƙasar Masar. Ya ce,2"Game da ku, wannan wata zai zama farawar watanni, watan farko na shekara a gare ku.

3Ka faɗa wa taron Isra'ila, 'A ranar goma ga wannan watan dole ne kowannen su ya ɗauki ɗan rago ko ɗan akuya domin kansu, kowanne iyali na yin wannan, ɗan rago domin kowanne gida.4Idan gidan ya yi ƙanƙanta sosai domin ɗan rago, mutumin da makwabcinsa zasu ɗauki naman ɗan rago ko ɗan akuya wanda zai isa domin adadin mutanen. Ya kasance ya isa domin kowanne mutum ya ci, saboda haka dole su ɗauki isasshen nama domin dukkan su su ci.
5‌Ɗan ragonku ko ɗan akuyan dole ya zama marar aibi, ɗan shekara ɗaya m. Kuna iya ɗaukar ɗaya daga cikin tumaki ko awaki.6Tilas ku ajiye ta har sai ranar sha huɗu ga wata. Daga nan dukkan taron Isra'ila tilas su yanka waɗannan dabbobi da hasken asuba.7Tilas ku ɗiba daga cikin jinin ku kuma sanya a dokin ƙofa gefe biyu da saman ginshiƙan ƙofofin gidajen inda zaku ci naman.8Tilas ku ci naman a wannan daren, bayan an gasa da farko a bisa wuta. A ci shi da gurasa da akayi ba da gami ba, tare da ganye mai ɗaci.
9Kada ku ci shi ɗanye ko dafaffe cikin ruwa. A maimako, ku gasa shi bisa wuta tare da kansa, kafafunsa da kayan cikinsa.10Tilas ba za ku bar wani daga cikinsa ba ya rage har safiya. Tilas ku ƙone duk abin da ya rage har safiya.11Ga yadda tilas zaku ci shi: tare da ɗamararku a ɗaure, takalmanku bisa tafin ƙafarku, da sandarku a hannunku. Tilas ku ci shi da hanzari. ‌Ƙetarewa ne na Yahweh.
12Yahweh ya faɗi wannan: zan ratsa ta cikin ƙasar Masar a wannan dare zan kuma kai hari ga dukkan 'ya'yan fãri na mutum da na dabba a cikin ƙasar Masar. Zan kawo horaswa ga dukkan allolin Masar. Ni ne Yahweh.13Jinin zai zama alama ne bisa gidajenku domin zuwa na a gare ku. Idan naga jinin, Zan ƙetare ku sa'ad da na kai hari ga ƙasar Masar.14Wannan annoba ba za ta zo bisan ku ba ta kuma hallaka ku. Wannan rana zata zama abar tunawa domin ku, wadda tilas ku kiyaye a matsayin bikin Yahweh. A koyaushe zai kasance shari'a a gare ku, cikin dukkan tsararrakin mutanenku, cewa tilas ku kiyaye wannan rana.
15Zaku ci gurasa ba tare da gami ba a lokacin kwanakin bakwai. A rana ta farko zaku cire gami daga gidajenku. Duk wanda yaci gurasa mai gami daga ranar farko zuwa rana ta bakwai, wannan taliki tilas a datse shi daga Isra'ila.16A rana ta farko za ayi taro da za a keɓe a gare ni, a rana ta bakwai kuma za a sake yin wani irin wannan taron. Babu wani aikin da za ayi a cikin waɗannan kwanaki, sai dai girki domin kowa ya ci. Wannan ne kaɗai aikin da tilas ya zama mai yiwuwa a gare ku.
17Tilas ku kiyaye wannan biki na gurasa marar gami saboda a wannan rana ce na fito da mutanenku, ƙungiya, ƙungiya na mayaƙa, daga cikin ƙasar Masar. Saboda haka tilas ku kiyaye wannan rana cikin dukkan tsararrakin mutanenku. Wannan a koyaushe zai zama shari'a a gare ku.18Tilas ku ci gurasa marar gami tun daga hasken asuba na ranar sha huɗu ga watan farko na shekara, har zuwa hasken asuba na ranar ashirin da ɗaya ga watan.
19A lokacin waɗannan kwanaki bakwai, tilas kada a sami wani gami cikin gidajenku. Duk wanda ya ci gurasa da aka yi da gami tilas a datse shi daga cikin gundumar Isra'ila, koda wannan taliki baƙo ne ko kuma wanda aka haifa a cikin ƙasar.20Tilas ba zaku ci wani abin da akayi da gami ba. Duk inda kuka zauna, tilas ku ci gurasa da akayi ba tare da gami ba."'
21Daga nan Musa ya yi sammace ga dukkan dattawan Isra'ila ya kuma ce masu, "Kuje ku zaɓi 'yan raguna ko 'yan awaki waɗanda za su isa ku ciyad da iyalanku sai ku kuma yanka su a matsayin ɗan ragon ‌Ƙetarewa.22Daga nan sai ku ɗauki curin soso ku tsoma cikin jinin da zai kasance cikin kwano. Sai ku shafa jinin a bisa ginshiƙin ƙofa da dokin ƙofofi biyu. Kada waninku ya fita daga ƙofar gidansa har sai da safe.
23Domin Yahweh zai ratsa ta ciki ya kai hari ga Masarawa. Idan yaga jinin a bisa ginshiƙin ƙofar da dokin ƙofa biyun, zai ƙetare ƙofarku kuma ba zai bada izini ga mai lalatarwa ba ya shigo cikin gidajenku ya kawo maku hari.
24Tilas ku kiyaye wannan al'amari. Wannan a koyaushe zai zama shari'a domin ku da zuriyarku.25Idan kuka shiga ƙasar da Yahweh zai baku, kamar yadda ya yi alƙawari zai yi, tilas ku kiyaye wannan aikin sujada.
26Idan 'ya'yanku suka tambaye ku, 'Mene ne ma'anar wannan aikin sujada?'27daganan tilas ku ce, 'hadayar ‌Ƙetarewa ce ta Yahweh, saboda Yahweh ya ƙetare gidajen Isra'ilawa a Masar sa'ad da ya kai hari ga Masarawa. Ya 'yantar da gidajenmu."' Daga nan mutanen suka rusuna suka kuma yi sujada ga Yahweh.28Isra'ilawa suka tafi suka yi dai-dai yadda Yahweh ya umarci Musa da Haruna.
29Ya kuwa faru a tsakar dare Yahweh ya kai hari ga dukkan 'ya'yan fãri dake cikin ƙasar Masar, daga ɗan fãrin Fir'auna, wanda ya zauna bisa kursiyi, har ya zuwa ɗan fãrin talikin dake cikin kurkuku da dukkan 'ya'yan fãrin dabbobi.30Fir'auna ya tashi da dare - shi, dukkan bayinsa, da dukkan masarawa. Akwai makoki mai ƙara a Masar, domin babu wani gida inda ba wanda ba a rasa wani da ya mutu ba.
31Fir'auna ya yi sammace ga Musa da Haruna da dare ya kuma ce, "Ku tashi, ku fita daga cikin mutanena, ku da Isra'ilawa. Ku tafi, kuyi sujada ga Yahweh, kamar yadda kuka ce kuna so kuyi.32Ku ɗauki garken tumakinku dana awakinku da garken shanunku, kamar yadda kuka ce, ku kuma tafi, sai ku kuma albarkace ni."33Masarawa suna cikin babban hanzari su fitar dasu daga ƙasar, gama sun ce, "Dukkanmu zamu mutu."
34Sai mutanen suka ɗauki ƙullinsu ba tare da sun ƙara wani gami ba. Kwanonin markaɗensu sun riga sun ɗaure cikin kayansu da bisa kafaɗunsu.35Yanzu mutanen Isra'ila sun yi yadda Musa yace masu. Suka roƙi Masarawa domin kayayyakin azurfa, da kayayyakin zinariya, da sutura.36Yahweh yasa Masarawa ɗokin farantawa Isra'ilawa rai. Sai masarawa suka basu komai game da abin da suka roƙa. Ta wannan hanyar, Isra'ilawa suka washe Masarawa.
37Isra'ilawa suka yi tafiya daga Remasis zuwa Sukkot. Lissafinsu kimanin mazaje 600,000, baya ga ƙarin mataye da yara.38Gaurayen taron waɗanda ba Isra'ilawa ba ma suka tafi tare da su, tare da garkunan tumaki da awaki da na shanu, babban lissafin dabbobi.39Suka gasa gurasa marar gami daga cikin ƙullin da suka kawo daga Masar. Ya zama marar gami ne saboda an kore su daga Masar ba zasu kuma yi jinkirin shirya abinci ba.40Isra'ilawa sun yi zama a cikin Masar har shekaru 430.
41A ƙarshen shekaru 430, a dai-dai wannan rana, dukkan ƙungiyoyin mayaƙan Yahweh suka fita daga ƙasar Masar.42Wannan dare ne na tsayawa a faɗake, domin Yahweh ya fito da su daga ƙasar Masar. Wannan daren Yahweh ne da za a kiyaye ga dukkan Isra'ilawa cikin dukkan tsararrakin mutanensu.
43Yahweh ya cewa Musa da Haruna, "Wannan ne ka'ida domin ‌Ƙetarewa: babu wani bare da mai yiwuwa yaci daga cikin sa.44Duk da haka, kowanne bawan Ba-isra'ile, da aka sawo da kuɗi, yana iya ci bayan kun yi masa kaciya.
45Bare da bayin haya tilas ba za su ci wani daga cikn abincin ba.46Tilas a ci abincin cikin gida ɗaya. Tilas ba za ku ɗauki wani daga cikin abincin ba ku fita da shi waje, tilas kuma ba za ku karya wani ƙashi ba daga cikin sa.
47Dukkan gundumar Isra'ila tilas su kiyaye wannan biki.48Idan bare yana zaune tare daku kuma yana so ya kiyaye ‌Ƙ‌etarewar ga Yahweh, dukkan danginsa maza tilas a yi masu kaciya. Daga nan zai yiwu su zo su kuma kiyaye shi. Zai zama kamar mutanen da aka haifa cikin ƙasar, Duk da haka, babu wani taliki marar kaciya da mai yiwuwa ya ci wani abu daga cikin abincin.
49Wannan irin dokar za a zartar ga haifaffen garin da kuma bare dake zaune cikin ku.50Sai dukkan Isra'ilawa suka yi dai-dai yadda Yahweh ya umarci Musa da Haruna.51Sai ya kasance a dai-dai wannan rana ce Yahweh ya fito da Isra'ila daga ƙasar Masar a ƙungiyoyin mayaƙansu.

13

1Yahweh ya yi magana da Musa ya kuma ce,2"Ka keɓe mani dukkan 'ya'yan fãri, kowanne ɗan fãri namiji daga cikin Isra'ilawa, duk da na mutane da dabbobi. 'Ya'yan fãrin nawa ne."

3Musa ya cewa mutanen, "Ku tuna da wannan rana, ranar da kuka fito daga Masar, daga gidan bauta, domin ta hannun Yahweh mai ƙarfi ya fito daku daga nan wurin. Babu wata gurasa mai gami da zai yiwu a ci.4Za ku fita daga Masar a wannan ranar, a cikin watan Abib.5Sa'ad da Yahweh ya kawo ku cikin ƙasar Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Amoriyawa, da Hibbiyawa, da kuma Yebusiyawa, ƙasar da ya rantse wa kakanninku zai baku, ƙasar dake malala da madara da zuma - daganan tilas ku kiyaye wannan aikin sujada a cikin wannan watan.
6Gama kwanaki bakwai tilas za ku ci gurasa marar gami; a ranar kwana na bakwai za ayi bikin girmama Yahweh.7Gurasa marar gami tilas za a ci cikin dukkan kwanakin bakwai; babu wata gurasa mai gami da zai yiwu a gani a cikin ku. Babu wani gami da zai yiwu a gani tare daku a cikin kowanne kan iyakokinku.
8A wannan rana zaku cewa 'ya'yanku, 'Wannan saboda abin da Yahweh ya yi domina ne sa'ad da na fito daga Masar.'9Wannan zai zama abin tunawa domin ka a bisa hannu, abin tunawa kuma a bisa goshi. Wannan saboda shari'ar Yahweh ta kasance a bakinka, domin tare da hannu mai ƙarfi Yahweh ya fito da kai daga Masar.10Saboda haka tilas ka kiyaye wannan shari'a a lokacin da aka zaɓa daga shekara zuwa shekara.
11Sa'ad da Yahweh ya kawo ku cikin ƙasar Kan'aniyawa, kamar yadda ya rantse maku da kakanninku zai yi, kuma sa'ad da ya bayar da ƙasar a gare ku,12tilas ku keɓe ga Yahweh kowanne yaro ɗan fãri da ɗan farko na dabbobinku. Mazajen dukka za su zama na Yahweh.13Kowanne ɗan fãrin jaki tilas ku saye shi da ɗan rago. Idan baku saye shi ba, daga nan tilas ku karya wuyansa. Amma kowanne ɗan fãri namiji daga cikin dukkan 'ya'yanku maza - tilas ku sake sayen su.
14Idan ɗan ka yayi maka tambaya daga bisani, 'Mene ne ma'anar wannan?' Daga nan sai ka gaya ma shi, 'Ta wurin hannun Yahweh mai ƙarfi ne aka fito damu daga Masar, daga gidan bauta.15Sa'ad da Fir'auna da taurin kai ya ƙi ya bar mu mu tafi, Yahweh ya kashe dukkan 'ya'yan fãri na ƙasar Masar, duk da 'ya'yan fãrin mutane da 'ya'yan fãrin dabbobi. Shi ya sa nake hadaya ga Yahweh na ɗan fãri namiji na kowacce dabba, shi yasa kuma nake sake sayen 'ya'yan fãri na mazaje.'16Wannan zaya zama abin tunawa a hannunku, abin tunawa kuma a bisa goshinku, domin ta hannu mai ƙarfi Yahweh ya fito damu daga Masar."
17Sa'ad da Fir'auna ya bar mutanen su tafi, Allah bai bida su ta hanyar ƙasar Filistiyawa ba, koda yake wannan ƙasar tana kurkusa. Domin Allah yace, "Watakila mutanen za su canza ra'ayinsu sa'ad da suka fuskanci yaƙi daganan kuma su koma Masar."18Sai Allah ya bi da mutanen su kewaya ta cikin jeji zuwa Tekun Iwa. Isra'ilawa suka fita daga ƙasar Masar shirye domin yaƙi.
19Musa ya ɗauki ƙasusuwan Yosef tare da shi, domin Yosef yasa Isra'ilawa suka yi rantsuwa ya kuma ce, "Babu shakka Allah zai ceto ku, kuma tilas ku ɗauke ƙasusuwana tare daku."20Isra'ilawa suka yi tafiya daga Sukkot suka kuma yi sansani a Itam a bisa gaɓar jeji.21Yahweh ya shiga gabansu da rana ta inuwar girgije domin ya bida su ta hanyar da zasu bi. Da dare ya tafi ta inuwar wuta domin ya basu haske. Ta wannan hanyar suna iya tafiya da rana da kuma dare.22Yahweh bai ɗauke kuma daga gaban mutanen da rana inuwar girgije ba da dare kuma inuwar wuta ba.

14

1Daga nan Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,2"Ka gaya wa Isra'ilawa cewa su juya su kuma yi sansani kafin Fi Hahirot, tsakanin Magdol da teku, kafin Ba'al Zifon. Za ku yi sansani a gefen teku akasi da Fi Hahirot.3Fir'auna zai ce game da Isra'ilawa, 'Su na yawo a cikin ƙasar. Jeji ya rufe bisan su.'

4Zan taurare zuciyar Fir'auna, kuma zai runtume su. Zan sami girmamawa saboda Fir'auna da dukkan mayaƙansa. Masarawa zasu sani cewa Ni ne Yahweh." Sai Isra'ilawa suka yi sansani kamar yadda aka umarce su.5Sa'ad da aka gaya wa sarkin Masar cewa Isra'ilawa sun tsere, sai ra'ayin Fir'auna da bayinsa suka juya gãba da mutanen. Suka ce, "Me muka yi? Mun saki Isra'ila daga bauta ma na?"
6Daga nan sai Fir'auna ya shiryo karusansa ya kuma ɗauki mayaƙansa tare da shi.7Ya ɗauki zaɓaɓɓun karusai ɗari shidda da dukkan sauran karusan Masar, da shugabanni a bisa dukkansu.8Yahweh ya taurare zuciyar Fir'auna, sarkin Masar, sarkin kuma ya runtumi Isra'ilawa. Yanzu dai Isra'ilawa sun yi tafiyarsu cikin nasara.9Amma Masarawa suka runtume su, tare da dukkan dawakansa da karusai, mahayan dawakansa, da mayaƙansa. Suka sha kan Isra'ilawa da suka yi sansani a gefen teku a gefen Fi Hahirot, kafin Ba'al Zifon.
10Sa'ad da Fir'auna ya iso kusa, Isra'ilawa suka duba sama suka kuma yi mamaki. Masarawa suna tattaki bayan su, suka kuma firgita. Isra'ilawa suka yi kuka ga Yahweh.11Suka ce wa Musa, "Saboda babu kaburbura ne a Masar, shi yasa ka ɗauko mu domin mu mutu a jeji? Meyasa ka yi haka da mu, ka fito da mu daga Masar?12Ba wannan muka gaya maka ba a Masar? Muka ce maka, 'Ka ƙyale mu, domin mu yiwa Masarawa aiki.' Ya gwammace mana muyi aiki domin su maimakon mu mutu cikin jeji."
13Musa ya cewa mutanen, "Kada kuji tsoro. Ku tsaya cik ku kuma ga ceton da Yahweh zai wadata domin ku a yau. Domin ba zaku sake ganin Masarawan da kuka gani ba a yau.14Yahweh zai yi yaƙi domin ku, kuma tsayawa kawai za kuyi cik."
15Daga nan Yahweh ya cewa Musa, "Meyasa kai, Musa, ka ke ci gaba da kira a gare ni? Ka gaya wa Isra'ilawa su tafi gaba.16Ka ɗaga sandarka, ka miƙa hannunka bisa tekun ka kuma raba ta biyu, saboda mutanen Isra'ila su bi ta tekun bisa busasshiyar ƙasa.17Ka sani cewa zan taurare zukatan Masarawa saboda su biyo bayansu. Zan sami daraja saboda Fir'auna da dukkan mayaƙansa, karusansa, da mahaya dawakansa.18Daga nan Masarawa zasu sani cewa Ni ne Yahweh sa'ad da Na samo daraja saboda Fir'auna, karusansa, da mahaya dawakansa."
19Mala'ikan Allah, wanda ya tafi gaban Isra'ilawa, ya matsa ya kuma je bayansu. Inuwar girgijen ta matsa daga gabansu ta kuma koma ta tsaya bayansu.20Girgijen ya zo tsakanin sansanin Masar da sansanin Isra'ila. Girgije mai duhu ne ga Masarawa, amma ya haska daren domin Isra'ilawa, sai gefe ɗaya basu zo kusa da ɗayan ba dukkan dare.
21Musa ya miƙar da hannunsa bisa tekun. Yahweh ya maida tekun baya da babbar iskar gabas dukkan wannan dare ya kuma maida tekun zuwa busasshiyar ƙasa. Ta haka ruwayen suka rabu.22Isra'ilawa suka tafi ta cikin teku bisa busasshiyar ƙasa. Ruwayen suka yi katanga domin su a hannun dama da hannun hagu.
23/ Masarawa suka runtume su. Suka tafi bayansu cikin tsakiyar teku - dukkan dawakan Fir'auna, da karusai, da mahaya dawakai.24Amma a sa'o'in farkon safiya, Yahweh ya duba ƙasa bisa mayaƙan Masarawa ta wurin umudin wuta da girgije. Ya sanya firgita tsakanin Masarawa.25Keken karusansu suka cije, mahayan dawakan suka yi tuƙi da wahala. Sai masarawa suka ce, "Bari mu tsere daga Isra'ila, gama Yahweh yana yaƙi domin su gãba da mu."
26Yahweh ya cewa Musa, "Ka miƙar da hannunka bisa tekun domin ruwayen su dawo bisa Masarawa, karusansu, da mahaya dawakansu."27Sai Musa ya miƙar da hannunsa bisa tekun, kuma ya koma yadda ya ke da safiya ta bayyana. Masarawa suka tsere cikin teku, Yahweh kuma ya kora Masarawa zuwa cikin tsakiyarsa.28Ruwayen suka dawo suka rufe karusan Fir'auna, mahayan dawakai, da dukkan mayaƙansa dasu ka bi karusan zuwa cikin teku. Babu wanda ya tsira.
29Duk da haka, Isra'ilawa suka yi tafiya bisa busasshiyar ƙasa cikin tsakiyar teku. Ruwayen suka zama katanga domin su a hannun damansu da hagunsu.30Sai Yahweh ya ceto Isra'ila a wannan rana daga hannun Masarawa, Isra'ila kuma suka ga matattun Masarawa bisa gaɓar teku.31Sa'ad da Isra'ila suka ga babban iko da Yahweh ya yi amfani da shi gãba da Masarawa, mutanen suka girmama Yahweh, suka kuma amince da Yahweh da kuma bawansa Musa.

15

1Daga nan Musa da mutanen Isra'ila suka raira wannan waƙa ga Yahweh. Suka raira, "Zan raira ga Yahweh, gama ya yi ɗaukakakkiyar nasara; doki da mahayinsa ya watsar cikin teku.

2Yahweh ne ƙarfina da waƙata, ya kuma zama mai cetona. Wannan ne Allahna, kuma zan yabe shi, Allah na mahaifina, zan kuma ɗaukaka shi.3Yahweh mayaƙi ne; Yahweh ne sunansa.
4Ya watsar da karusan Fir'auna da mayaƙansa cikin teku. Zaɓaɓɓun hafsoshin Fir'auna sun nutse cikin Tekun Iwa.5Zurfafa sun rufe su; sun tafi ƙasa cikin zurfafa kamar dutse.
6Hannunka na dama, Yahweh, ɗaukakakke ne cikin iko; hannunka na dama, Yahweh, ya rugurguza maƙiyi.7Cikin babban girma ka kayar da waɗanda suka taso gãba da kai. Ka aika da hasalarka; ta cinye su kamar haki.8Da hucin kafofin hancinka ruwaye suka jera; ruwayen dake malala suka tsaya tsaye suka yi tsibi; ruwa mai zurfi ya daskare a cikin zuciyar teku.
9Maƙiyi yace, 'Zan runtuma, zan sha kai, zan rarraba ganima; marmarina zai ƙoshi a kansu; zan zaro takobina; hannuna zai hallakar dasu.'10Amma ka busa da iskarka, teku kuma ya rufe su; suka nutse kamar baƙin ƙarfe cikin manyan ruwaye.11Wane ne kamar ka, Yahweh, a tsakanin alloli? Wane ne kamar ka, girma cikin tsarki, daraja cikin yabo, mai aikata al'ajibai?
12Ka miƙa hannun damanka, ƙasa kuma ta haɗiye su.13A cikin alƙawarin amincinka ka bida mutanen ka ceto su. A cikin ƙarfinka ka bida su zuwa wuri mai tsarki inda kake zaune.
14Mutane zasu ji, zasu kuma yi rawar jiki; fargaba zai afko wa mazaunan Filistiya.15Daga nan shugabannin Idom zasu ji tsoro; sojojin Mowab zasu girgiza; dukkan mazaunan Kan'ana zasu narke.
16Tsoro da fargaba zai fãɗo masu. Saboda ikon damtsenka, zasu tsaya cik kamar dutse har sai mutanenka sun wuce, Yahweh - har sai mutanen da ka ceto sun wuce.
17Za ka kawo su ka dasa su bisa tsaunin gãdonka, wurin da, Yahweh, ka yi domin ka zauna a ciki, wuri mai tsarki, Ubangijinmu, wanda hannuwanka suka gina.18Yahwah zai yi mulki har abada abadin."
19Gama dawakan Fir'auna suka tafi tare da karusansa da mahaya dawakansa cikin teku. Yahweh ya maido da ruwayen teku bisansu. Amma Isra'ilawa suka yi tafiya bisa busasshiyar ƙasa a tsakiyar teku.20Miriyam annabiya, 'yar'uwar Haruna, ta ɗauki kacau-kacau, dukkan mataye kuma suka fita da kacau-kacau, suna rawa tare da ita.21Miriyam ta raira masu waƙa: "Ku raira ga Yahweh, domin ya yi ɗaukakakkiyar nasara. Doki da mahayinsa ya jefar cikin teku."
22Daga nan Musa ya bida Isra'ila gaba daga Tekun Iwa. Suka tafi zuwa cikin jejin Shur. Suka yi tafiya kwana uku cikin jeji basu kuma sami ruwa ba.23Daga nan suka iso Mara, amma basu iya shan ruwan wurin nan ba saboda yana da ɗaci. Sai suka kira sunan wannan wuri Mara.
24Sai mutanen suka yi gunaguni ga Musa suka kuma ce, "Me zamu sha?"25Musa ya yi kuka ga Yahweh, sai Yahweh ya nuna masa wani itace. Musa ya jefa shi cikin ruwan, ruwan kuma ya zama da daɗin sha. A wannan wurin ne Yahweh ya basu shari'a mai tsauri, a wannan wurin ne kuma ya gwada su.26Ya ce, "Idan a hankali kuka saurari muryar Yahweh Allahnku, kuka kuma yi abin dake dai-dai a idanunsa, idan kuma kuka kasa kunne ga umarninsa kuka kuma yi biyayya da dukkan shari'unsa - ba zan sanya maku ko ɗaya daga cikin cututtukan dana sanya wa Masarawa ba, gama Ni ne Yahweh dake warkar da ku."
27Daga nan mutanen suka iso Elim, inda akwai maɓuɓɓugan ruwa sha biyu da itatuwan dabino saba'in. Suka yi sansani a nan bakin ruwa.

16

1Mutanen suka kama hanya daga Elim, kuma dukkan taron jama'ar Isra'ila suka iso jejin Sin, wanda ke tsakanin Elim da Sinai, a ranar sha biyar ga watan biyu bayan barowarsu daga ƙasar Masar.2Dukkan taron jama'ar Isra'ila suka yi gunaguni gãba da Musa da Haruna a cikin jejin.3Isra'ilawa suka ce masu, "Da ma kawai mun mutu ta hannun Yahweh a ƙasar Masar sa'ad da muke zama gefen tukwanen nama muke kuma cin gurasa mu ƙoshi. Domin ka fito da mu cikin wannan jeji ka kashe dukkan taron jama"armu da yunwa."

4Daga nan Yahweh ya cewa Musa, "Zan yi ruwan gurasa daga sama domin ku. Mutanen zasu fita su tattaro ta yini ɗaya kowacce rana saboda in gwada su in gani ko zasu yi ko kuwa ba zasu yi tafiya cikin shari'a ta ba.5Za ya kasance a rana ta shida, zasu tattaro riɓi biyu na yawan yadda suke tattarawa kowacce rana a baya, sai kuma su dafa abin da suka ɗebo."
6Daga nan Musa da Haruna suka cewa dukkan mutanen Isra'ila, "Da maraice zaku sani cewa Yahweh ne ya fito da ku daga ƙasar Masar.7Da safe zaku ga ɗaukakar Yahweh, domin ya ji gunaguninku gãba da shi. Mu su wane ne da zaku yi gunaguni gãba da mu?"8Musa ya sake cewa, "Zaku san wannan sa'ad da Yahweh ya baku nama da maraice da gurasa da safe ku ƙoshi - domin ya ji gunagunan da kuka furta gãba da shi. Su wane ne Haruna da ni? Gunagunanku ba gãba damu ba ne; gãba da Yahweh ne."
9Musa ya cewa Haruna, "Ka cewa dukkan taron jama'ar mutanen Isra'ila, 'Ku zo kusa a gaban Yahweh, domin ya ji gunagunanku."'10Sai ya kasance, yayin da Haruna yake magana da dukkan taron jama'ar mutanen Isra'ila, sai suka kalli zuwa jeji, kuma, duba, ɗaukakar Yahweh ta bayyana a girgije.11Daga nan Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,12"Na ji gunagunan mutanen Isra'ila. Ka yi magana dasu ka ce, 'Da maraice zaku ci nama, da safe kuma zaku cika da gurasa. Daga nan zaku sani cewa Ni ne Yahweh Allahnku."'
13Sai ya kasance da maraice makwarwai suka taso suka rufe sansanin. Da safe raɓa ta kwanta kewaye da sansanin.14Da raɓar ta tafi, a nan birbishin jejin sai ga wasu falle-falle kamar dusar ƙanƙara a ƙasa.15Sa'ad da mutanen Isra'ila suka gan ta, suka ce da juna, "Mene ne wannan?" Ba su san ko mene ne ba. Musa yace masu, "Gurasar da Yahweh ya baku ce ku ci.
16Wannan ne umarnin da Yahweh ya bayar: 'Tilas ku tattaro, kowannen ku, adadin da kuke buƙata ku ci, awon kowanne taliki bisa ga lissafin mutanenku. Ga yadda zaku tattara ta: Ku tattara isasshe domin ci ga kowanne taliki dake zaune a rumfarku."'17Mutanen Isra'ila suka yi haka. Wasu suka tãra da yawa, wasu suka tãra kaɗan.18Sa'ad da suka auna da awon gwangwani, waɗanda suka tãra da yawa basu rage komai ba, waɗanda kuma suka tãra kaɗan basu rasa komai ba. Kowanne taliki ya tãra dai-dai da biyan buƙatarsu.
19Daga nan Musa yace masu, "Dole ba wanda zai bar komai daga cikin ta har safiya."20Duk da haka, basu saurari Musa ba. Waɗansu suka rage daga cikin ta har safiya, sai ta haifar da tsutsotsi ta kuma yi wãri. Daga nan Musa ya fusata da su.21Suka tattara ta safiya bayan safiya. Kowanne taliki ya tãra isassar wanda zai ci domin wannan ranar. Sa'ad da rana ta yi zafi, ta narke.
22Sai ya kasance a rana ta shida kowannensu ya tãra riɓi biyu na gurasar, gwangwani biyu domin kowanne taliki. Dukkan shugabannin jama'ar suka zo suka faɗi wa Musa.23Ya ce masu, "Wannan ne abin da Yahweh yace: 'Gobe hutun nadama ne, Asabar mai tsarki cikin girmama Yahweh. Ku gasa abin da kuke so ku gasa, ku kuma dafa abin da kuke so ku dafa. Duk abin da ya rage, sai ku ajiye shi gefe domin kanku har sai da safe."'
24Sai suka ajiye ta gefe har sai da safe, kamar yadda Musa ya bada umarni. Ba ta zama da wãri ba, ko kuma a sami wata tsutsa a cikinta.25Musa yace, "Ku ci wannan abin cin yau, domin yau rana ce wadda aka keɓe a matsayin Asabaci na girmama Yahweh. Yau ba zaku same ta ba a gonaki.
26Zaku tattara ta cikin kwanaki shida, amma rana ta bakwai Asabaci ce. A ranar Asabar babu manna."27Sai ya kasance a rana ta bakwai waɗansu mutane suka fita su tattaro manna, amma ba su sami komai ba.
28Daga nan Yahweh ya cewa Musa, "Har yaushe zaku ƙi kiyaye umarnai na da shari'u na?29Duba, Yahweh ya baku Asabaci. Don haka a rana ta shida yana baku gurasa domin kwanaki biyu. Kowannen ku tilas ya tsaya a wurinsa; tilas babu wanda zai fita daga wurin shi a rana ta bakwai."30Sai mutanen suka huta a rana ta bakwai.
31Mutanen Isra'ila suka kira wannan abinci "Manna." Ita fara ce kamar tsabar riɗi, ɗanɗanon ta kuma kamar wainar da aka yi da zuma.32Musa yace, "Wannan ne Yahweh ya umarta: 'A ajiye gwangwanin manna cikin dukkan tsararrakin mutanenku saboda zuriyarku su ga gurasar dana ciyar da ku a jeji, bayan da na fito daku daga ƙasar Masar."'
33Musa ya cewa Haruna, "Ka ɗauki tukunya ka sa gwangwani ɗaya na manna a cikin ta. Ka adana ta gaban Yahweh domin a ajiye ta cikin dukkan tsararrakin mutanen."34Kamar yadda Yahweh ya umarci Musa, Haruna ya ɓoye ta bayan alƙawarin dokoki a cikin akwatin alƙawari.35Mutanen Isra'ila suka ci manna shekaru arba'in har sai da suka zo ƙasar dake da mazauna. Ita suka ci har sai da suka zo kan iyakokin ƙasar Kan'ana.36Yanzu dai gwangwanin kashi ɗaya ne cikin goma na mudu.

17

1‌Ɗaukacin taron jama'ar Isra'ilawa suka yi tafiya daga jejin Sin, biye da umarnan Yahweh. Suka yi sansani a Refidim, amma babu ruwa domin mutane su sha.2Sai mutanen suka ba Musa laifi saboda halin da suke ciki suka kuma ce, "Ka ba mu ruwa mu sha." Musa yace, "Meyasa kuke faɗa da ni? Meyasa kuke gwada Yahweh?"3Mutanen suna jin ƙishi sosai, suka kuma yi gunaguni gãba da Musa. Suka ce, "Meyasa ka fito da mu daga Masar? Don ka kashe mu da 'ya'yanmu da kuma dabbobinmu da ƙishi?"

4Daga nan Musa ya yi kuka ga Yahweh, "Me zanyi da waɗannan mutanen? Sun kusa shirya jifa na."5Yahweh ya cewa Musa, "Ka tafi gaba da mutanen, ka tafi kuma tare da wasu dattawan Isra'ila. Ka ɗauki tare da kai sandar daka buga kogi, ka kuma tafi.6Zan tsaya a gabanka can a dutsen Horeb, zaka kuma bugi n. Ruwa zai fito daga cikin sa domin mutanen su sha." Daga nan Musa ya yi haka a gaban dattawan Isra'ila.7Ya kira wannan wuri Massa da Meriba saboda gunagunin Isra'ilawa, saboda kuma sun gwada Ubangiji ta wurin cewa, "Yahweh yana cikinmu ko a'a?"
8Daga nan mayaƙan mutanen Amalekawa suka fita suka kuma kai hari ga Isra'ila a Refidim.9Sai Musa ya cewa Yoshuwa, "Ka zaɓi wasu mutane ka fita. Ka yi faɗa da Amalekawa. Gobe zan tsaya bisa tudu tare da sandar Allah a hannuna."10Sai Yoshuwa ya yi faɗa da Amalekawa kamar yadda Musa ya umarta, yayin da Musa, Haruna, da Hor suka hau saman tudu.
11Yayin da Musa ke riƙe da hannayensa sama, Isra'ila suna nasara; idan ya sauke hannayensa su huta, sai Amalekawa su fãra yin nasara.12Sa'ad da hannayen Musa suka zama da nauyi, Haruna da Hor suka ɗauki dutse suka sanya ƙasansa domin ya zauna a kai. A dai-dai wannan lokaci, Haruna da Hor suka riƙe hannayensa sama, mutum ɗaya a gefensa ɗaya, mutum ɗaya kuma a ɗayan gefensa. Haka aka riƙe hannayen Musa a tallafe har faɗuwar rana.13Haka Yoshuwa ya kayar da mutanen Amalekawa da takobi.
14Yahweh ya cewa Musa, "Ka rubuta wannan cikin littafi ka kuma karanta shi cikin kunnuwan Yoshuwa, saboda da zan share tunawa da Amalekawa kakaf daga ƙarƙashin sammai."15Daga nan Musa ya gina bagadi ya kira shi "Yahweh ne tuta ta."16Ya ce, "Gama an ɗaga hannu sama zu wa kursiyin Yahweh - cewa Yahweh zai ja dagar yaƙi da Amalekawa daga tsara zuwa tsara."

18

1Yetro, firist na Midiyan, surukin Musa, ya ji dukkan abin da Allah ya yi domin Musa domin kuma Isra'ila mutanensa. Ya ji cewa Yahweh ya fito da Isra'ila daga Masar.2Yetro, surukin Musa, ya ɗauki Ziffora, matar Musa, bayan da ya tura ta gida,3da 'ya'yanta maza biyu; sunan ɗan ɗaya Gashom, domin Musa yace, "Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa."4Sunan ɗayan Eliyeza, domin Musa yace, "Allah na kakannina ne taimako na. Ya cece ni daga takobin Fir'auna."

5Yetro, surukin Musa, ya zo tare da 'ya'yan Musa da matarsa a wurin Musa a cikin jeji inda ya yi sansani a tsaunin Allah.6Ya cewa Musa, "Ni, surukinka Yetro, ina zuwa tare da matarka da 'ya'yanta maza biyu."
7Musa ya tafi domin ya tarbi surukinsa, ya rusuna ƙasa, ya kuma sumbace shi. Suka tambayi lafiyar juna daganan kuma suka tafi cikin rumfa.8Musa ya gaya wa surukinsa dukkan abin da Yahweh ya yi wa Fir'auna da Masarawa saboda Isra'ila, game da dukkan wahalhalun da suka afko masu a kan hanya, da yadda Yahweh ya cece su.
9Yetro ya yi farinciki game da dukkan nagartar da Yahweh ya yi wa Isra'ila, yadda ya cece su daga hannun Masarawa.10Yetro yace, "Bari a yabi Yahweh, domin ya cece ka daga hannun Masarawa daga kuma hannun Fir'auna, ya kuma kuɓutar da mutanen daga hannun Masarawa.11Yanzu na sani cewa Yahweh babba ne fiye da dukkan alloli, saboda sa'ad da Masarawa suka wulaƙanta Isra'ilawa da gadara, Allah ya ceci mutanensa."
12Yetro, surukin Musa, ya kawo baikon ƙonawa da hadayu ga Allah. Haruna da dukkan dattawan Isra'ila suka zo su ci abinci a gaban Allah tare da surukin Musa.
13Washegari Musa ya zauna domin yi wa mutane hukunci. Mutane suka tsaitsaya kewaye da shi daga safe har yamma.14Sa'ad da surukin Musa yaga dukkan abin da ya yi domin mutanen, ya ce, "Mene ne haka kake yi tare da mutanen?" Meyasa kake zaunawa kai kaɗai kuma dukkan mutanen ke tsayawa kewaye da kai daga safe har yamma?"
15Musa ya cewa surukinsa, "Mutanen suna zuwa wurina ne su tambayi bishewar Allah.16Sa'ad da suka sami saɓani, suna zuwa wurina. Ina ɗaukar matsayi tsakanin taliki ɗaya da wani, kuma ina koyar da su farillan Allah da shari'unsa."
17Surukin Musa yace masa, "Abin da kake yi bai da kyau sosai.18Tabbas zaka gajiyar da kanka, kai da mutanen dake tare da kai. Wannan ƙangi ya yi maka nauyi sosai. Ba zaka iya yin shi ba kai kaɗai.19Ka saurare ni. Zan baka shawara, kuma Allah zai kasance tare da kai, saboda kai ne a madadin mutane ga Allah, kuma kai ke kawo rikice-rikicensu gare shi.20Dole ka koya masu farillansa da shari'unsa. Dole ka nuna masu hanyar da zasu yi tafiya da kuma aikin da zasu yi.
21Gaba da haka, dole ka zaɓi mutane tsayayyu daga cikin mutanen, mutane masu girmama Allah, mutane masu gaskiya masu ƙin ƙazamar riba. Dole ka sanya su bisa mutane su zama shugabannin dubbai, da ɗarurruka, da hamsin-hamsin, da goma-goma.22Za su yi hukunci tsakanin mutane a dukkan al'amuran yau da kullum, amma al'amura masu wuya sai su kawo maka. Game da dukkan ƙananan al'amura kuwa, zasu hukunta waɗannan da kansu. ta wannan hanyar zai yi maka sauƙi, za su kuma ɗauki nauyin tare da kai.23Idan ka yi wannan, idan kuma Allah ya umarce ka kayi haka, daganan zaka iya jurewa, kuma dukkan mutanen zasu iya tafiya gida a barace."
24Sai Musa ya saurari maganganun surukinsa ya kuma yi dukkan abin da ya ce.25Musa ya zaɓi tsayayyun mutane daga dukkan Isra'ila ya kuma maida su shugabannin mutanen, shugabanni masu lura da dubbai, da ɗarurruka, da hamsin-hamsin, da goma-goma.26Suka hukunta mutane a al'amura masu sauƙi, al'amura masu wuya kuma suka kawo wa Musa, amma su da kansu suka hukunta dukkan ƙananan al'amura.27Daga nan Musa ya bar surukinsa ya tafi, Yetro kuma ya koma cikin ƙasarsa.

19

1A cikin wata na uku bayan da mutanen Isra'ila suka fito daga ƙasar Masar, a wannan ranar, suka zo jejin Sinai.2Bayan da suka bar Refidim suka kuma zo jejin Sinai, suka yi sansani a jejin a gaban tsaunin.

3Musa ya hau zuwa wurin Allah. Yahweh ya kira shi daga tsaunin ya kuma ce, "Tilas ka gaya wa gidan Yakubu, mutanen Israi'la;4Kunga yadda na yiwa Masarawa, yadda na ɗauko ku bisa fikafikan gaggafa na kuma kawo ku a gare ni.5To yanzu, idan da biyayya kuka saurari muryata kuka kuma kiyaye alƙawarina, daganan zaku zama mallakata ta musamman daga cikin dukkan mutane, domin dukkan duniya tawa ce.6Zaku zama masarautar firistoci da al'umma mai tsarki domina. Waɗannan maganganun ne tilas ka faɗe su ga mutanen Isra'ila."
7Daga nan Musa ya zo ya sammaci shugabannin mutanen. Ya faɗi a gabansu dukkan waɗannan maganganun da Yahweh ya umarce shi.8Dukkan mutanen suka amsa tare suka ce, "Za muyi dukkan abin da Yahweh yace." Daga nan Musa ya zo ya kawo rahoton maganganun mutanen ga Yahweh.9Yahweh ya cewa Musa, "Zan zo gare ka cikin girgije mai kauri saboda mutanen su iya ji sa'ad da zan yi magana tare da kai, su kuma gaskata da kai har abada." Daga nan Musa ya faɗi maganganun mutanen ga Yahweh.
10Yahweh ya cewa Musa, "Ka tafi wurin mutanen. Yau da gobe Tilas ka keɓe su a gare ni. ka kuma sanya su su wanke tufafinsu.11Ku shirya domin rana ta uku, gama a rana ta uku Yahweh zai sauko bisa Tsaunin Sinai.
12Tilas ka sanya kan iyakoki domin mutanen a dukkan kewayen tsaunin. Ka ce masu, 'Ku kula da cewa baku hau zuwa tsaunin ba koku taɓa kan iyakarsa. Duk wanda ya taɓa tsaunin tabbas za a kashe shi.'13Kada hannun wani ya taɓa irin wannan taliki. A maimako, babu shakka tilas za a jefe shi ko a harbe shi. Ko mutum ne ko dabba tilas a kashe shi. Sa'ad da aka busa ƙaho mai dogon amo, suna iya zuwa gindin tsaunin."
14Daga nan Musa ya tafi ya gangara daga tsaunin zuwa ga mutanen. Ya keɓe mutanen ga Yahweh suka kuma wanke tufafinsu.15Ya cewa mutanen, "Ku shirya a rana ta uku; kada ku kusanci matayenku."
16A rana ta uku, sa'ad da safiya ta yi, aka yi cida da wurge-wurgen walƙiya da girgije mai kauri a bisa tsaunin, da ƙarar kaho mai ƙarfi sosai. Dukkan mutanen dake cikin sansanin suka yi rawar jiki.17Musa ya fito da mutanen daga cikin sansanin su gamu da Allah, suka kuma tsaya a gindin tsaunin.18Tsaunin Sinai kuwa an lulluɓe shi ɗungum da hayaƙi saboda Yahweh ya sauko bisa kansa cikin wuta da hayaƙi. Hayaƙin kuwa ya yi sama kamar hayaƙin tanderu, tsaunin kuma gabaɗaya ya yi mummunar girgiza.
19Da ƙarar ƙahon ta ci gaba da ƙaruwa bisa ƙaruwa, Musa ya yi magana, Allah kuma ya amsa masa da murya.20Yahweh ya sauko bisa Tsaunin Sinai, bisa ƙololuwar tsaunin, ya kuma sammaci Musa zuwa sama. Sai Musa ya haye sama.21Yahweh ya cewa Musa, "Ka gangara ka dokaci mutanen da kada su faso gareni su kalla, ko dayawa daga cikin su su hallaka.22Bari firistocin suma dake kusantata su keɓe kansu - su shirya kansu domin zuwa na - saboda kada in kai masu hari."
23Musa ya cewa Yahweh, "Mutanen ba zasu iya zuwa har Tsaunin Sinai ba, domin ka dokace mu: 'Ku sanya kan iyakoki kewaye da tsaunin ku kuma keɓe shi ga Yahweh."'24Yahweh yace masa, "Tafi, ka gangara daga tsaunin, ka kuma kawo Haruna tare da kai, amma kada ka bar firistocin da mutanen su faso shingen su hawo zuwa gare ni, ko in kai masu hari."25Sai Musa ya gangara zuwa ga mutanen ya yi magana da su.

20

1Allah ya furta dukkan waɗannan maganganu,2"Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya fito daku daga ƙasar Masar, daga gidan bauta.3Tilas ne ba zaku yi wasu alloli ba baya ga ni.

4Ba zaku yi wa kanku sassaƙaƙƙen siffa ba ko kamannin wani abu dake can cikin sama, ko a ƙarƙashin ƙasa, ko a cikin ruwaye.5Dole ne ba zaku rusuna masu ba koku yi masu sujada, gama Ni, Yahweh Allahnku, Allah ne mai kishi. Ina horon muguntar kakanni ta wurin sauko da horo bisa zuriyarsu, har zuwa tsararraki na uku da na huɗu na waɗanda ke ƙi na.6Amma ina nu na alƙawarin aminci ga dubban waɗanda ke ƙaunata suke kuma kiyaye dokokina.
7Dole ne ba zaku ɗauki sunan Yahweh Allahnku ba, a wofi, domin ba zan riƙe shi marar laifi ba duk wanda ya ɗauki sunana a wofi.
8Ku tuna da ranar Asabaci, ku keɓe ta domina.9Dole kuyi aiki tuƙuru ku kuma yi dukkan aikinku a ranaku shida.10Amma rana ta bakwai Asabaci ce ga Yahweh Allahnku. A wannan rana baza kuyi wani aiki ba, koku, ko 'ya'yanku maza, ko 'ya'yanku mata, ko bayinku maza, ko bayinku mata, ko garken shanunku, ko baƙon da yake cikin ƙofofinku.11Domin a cikin ranaku shida Yahweh ya yi sammai da duniya, da teku, da dukkan abin dake cikin su, sai kuma ya huta a rana ta bakwai. Saboda haka Yahweh ya albarkaci ranar Asabaci ya kuma keɓe ta.
12Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, saboda ka rayu na dogon lokaci a cikin ƙasar da Yahweh Allahnka yake baka.13Tilas ba zaka kashe kowa ba.14Tilas ba zaka yi zina ba.
15Tilas ne ba zaka yi sata ba daga wani.16Tilas ne ba zaka bada shaidar ƙarya ba gãba da maƙwabcinka.17Tilas ne ba zaka yi ƙyashin gidan maƙwabcinka ba; tilas ne ba zaka yi ƙyashin matar maƙwabcinka ba, bawansa namiji, baiwarsa mace, sansa, jakinsa, ko dukkan wani abu dake na maƙwabcinka."
18Dukkan mutanen suka ga cidar da walƙiyar, suka kuma ji muryar ƙahon, suka kuma ga tsaunin na hayaƙi. Sa'ad da mutanen suka ga haka, suka firgice suka kuma tsaya daga nesa.19Suka cewa Musa, "Ka yi magana da mu, zamu kuma saurara; amma kada ka bari Allah ya yi magana da mu, ko kuwa za mu mutu."20Musa ya cewa Mutanen, "Kada kuji tsoro, domin Allah ya zo ya gwada ku saboda girmamawarsa ya kasance cikin ku, saboda kuma kada kuyi zunubi."21Sai mutanen suka tsaya nesa, Musa kuma ya kusanci duhun mai kauri inda Allah ya ke.
22Yahweh ya cewa Musa, "Wannan ne tilas ka gayawa Isra'ilawa: 'Ku da kanku kunga cewa nayi magana da ku daga sama.23Kada ku yiwa kanku wasu alloli tare da ni, allolin azurfa ko allolin zinariya.
24Tilas ku gina mani bagadin ƙasa, dole kuma ku yi hadayar baye-baye na ƙonawa a kansa, baye-baye na zumunta, tumaki, da shanu. A cikin dukkan inda nasa a girmama sunana, zan zo gare ku in albarkace ku.25Idan kuka yi mani bagadin dutse, ba zaku gina shi ba da dutsen da aka yanko, domin idan kuka yi amfani da kayan aikinku a kansa, kun riga kun gurɓata shi.26Tilas ne ba za ku hau bisa bagadina ta matakala ba, saboda kada tsirancinku ya bayyana."'

21

1To waɗannan su ne sharuɗan da zaka sa a gabansu:

2Idan ka sayi bawa Ba'ibrane, zai yi bauta shekara shida, a ta bakwai zai tafi 'yantacce ba tare da ya biya kome ba.3Idan shi kaɗai ya zo, sai ya tafi shi kaɗai, idan kuma ya zo da mata, zata zama 'yantarta ta tafi tare da shi.4Idan ubangijinsa ne ya yi masa aure, da matar da 'ya'yanta zasu zama na ubangijinsa, shi kuwa zai zama 'yantacce ya tafi shi kaɗai.
5Amma idan bawan da kansa ya ce, "Ina ƙaunar ubangijina da matata da 'ya'yana; ba zan zama 'yantacce in tafi ba,"6Dole ubangijinsa ya kawo shi wurin Yahweh, dole ubangijinsa zai kawo shi ƙofa ko bakin ƙofa, kuma dole ubangijinsa zai huda kunnensa da allura. Daga nan zai zama bawa har iyakar rayuwarsa.
7Idan mutum ya sayar da ɗiyarsa mace ta zama baiwa, ba zata tafi haka nan kamar yadda bayi maza suke yi ba.8Idan ba ta gamshi ubangijinta wanda ya ajiye ta domin kansa ba, to dole ne a fanshe ta. Ba zai sayar da ita ga waɗan su baƙin mutane ba. Ba shi da wannan damar saboda ya yaudare ta.
9Idan ubangijinta ya bada ita ga ɗansa ta zama matarsa, sai ya ɗauke ta kamar ɗiyarsa.10Idan ya ɗauko wata matar, kada ya hana ta abinci ko tufafi ko kuwa 'yancinta na aure.11Amma idan bai ba ta waɗannan abubuwa uku ba, to sai ta tafi a matsayin 'yantarta, ba tare da ta biya wasu kuɗi ba.
12Ko wane ne ya doki wani mutum har ya mutu, shima sai a kashe shi.13Idan mutumin bada manufa ya yi ba, amma ya yi da kuskure ne, zan tanada wurin da zai gudu.14Idan wani mutum ya kaiwa maƙwabcinsa hari, ya yaudare shi har ya kashe shi, zaka ɗauke shi, koda yana kan bagadin Yahweh, domin a kashe shi.
15Dukkan wanda ya doki mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole za a kashe shi.16Dukkan wanda ya yi garkuwa da mutum - ko wanda ya yi garkuwa da mutumin ya sayar da shi, ko kuwa an same shi a hannun mai garkuwar - dole ne a kashe mai yin garkuwar.17Dukkan wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa dole za a kashe shi.
18Idan mutane suka yi faɗa, ɗaya ya bugi ɗayan da dutse ko ya naushe shi, kuma mutumin bai mutu ba, amma ya kwanta saboda dukan da ya yi masa;19idan mutumin ya samu ya tashi, har yana tafiya yana dogara sanda, shi wanda ya doke shi zai biya shi diyyar lokacin da ya ɓata; dole mutumin ya biya kuɗin jinyar sa har ya warke. Amma mutumin bai tserewa laifin kisan kai ba.
20Idan mutum ya doki bawansa ko baiwarsa da sanda, har bawan ya mutu sanadiyar wannan duka, dole ne za a hori mutumin. Duk da haka,21idan bawan ya rayu kwana ɗaya ko biyu, ba za a hori mutumin ba, saboda ya sha wuyar rashin bawansa.
22Idan mutane suka yi faɗa suka yi wa mace mai ciki rauni, har ta yi ɓari amma ba wani rauni a jikinta, mai laifin zai biya tara yadda mijinta ya bukata, dole ya biya abin da alƙali ya ce ya biya.23Amma idan akwai rauni mai muni, sai a bada rai maimakon rai,24ido maimakon ido, haƙori maimakon haƙiri, hannu naimakon hannu, ƙafa maimakon ƙafa,25ƙuna maimakon ƙuna, rauni maimakon rauni, ƙujewa maimakon ƙujewa.
26Idan mutum ya bugi bawansa ko baiwarsa a ido har idon ya mutu, bawan zai zama 'yantacce ya tafi maimakon idonsa ko idonta.27Idan ya buge wa bawansa ko baiwarsa haƙori har ya cire, bawan ko baiwar zai zama 'yantacce ya tafi maimakon haƙorinsa ko haƙorinta.
28Idan să ya soki mutum namiji ko mace har ya mutu, dole za a jejjefe san, kuma ba za a ci namansa ba; amma mai san zai zama baratacce.29Amma idan san ya kan soki mutane dama, kuma an yi wa mai san gargaɗi bai kuwa ɗaure san ba, idan san ya soki wani mutum ko wata mace har ga mutuwa, za a jejjefe san, mai san ɗin shima za a kashe shi.30Idan kuwa an ce a biya diyya domin ransa, to, dukkan abin da aka bukata a biya haka zai biya.
31Idan san ya soki ɗan wani ko ɗiyar wani, mai san zai yi kamar yadda wannan ka'ida ta bukaci ya yi.32Idan san ya soki bawan wani mutum na miji ko mace, mai san zai biya azurfa talatin, san kuma za a jejjefe shi.
33Idan mutum ya buɗe rami ko ya gina rami bai rufe shi ba, idan să ko jaki ya faɗa cikin sa,34wanda ya yi ramin zai biya diyya. Dole zai biya mai dabbar kuɗi, matacciyar dabbar kuma za ta zama asararsa.
35Idan san wani ya yi wa san wani rauni har ya mutu, za a sayar da san mai rai sai su raba kuɗin, su kuma raba san wanda ya mutu.36Amma idan dama san ya saba yin haka, kuma an yiwa mai san gargaɗi amma bai ɗaure sansa ba, zai biya să maimakon să matacciyar dabbar kuma za ta zama ta sa.

22

1Idan mutum ya saci bijimi ko tinkiya, ya kashe ko ya sayar, zai biya da bijimai biyar a kan bijimi ɗaya, ko tinkiya huɗu a kan tinkiya ɗaya.2Idan aka kama ɓarawo yana fasa gida, aka buge shi har ya mutu, ba za a kama kowa da laifin kisan kai a kansa ba.3Amma idan rana ta fito kamin ya fasa ya shiga, za a kama wanda ya kashe shi da laifin kisan kai. Dole ɓarawo ya biya diyya. Idan kuwa ba shi da komi, sai a sayar da shi saboda satar sa.4Idan an sami dabbar da ya sata a wurin sa, ko bijimi ne ko jaki ko tinkiya, dole ya biya riɓi biyu na abin da ya sata.

5Idan mutum yana kiwo, ya bar dabbarsa ta kwance ta yi kiwo a gonar wani, dole ya biya diyya daga gonarsa mafi kyau ko daga garkarsa mafi kyau.
6Idan wuta ta ƙwace ta shiga cikin ƙayoyi har ta tarar da hatsi, ko an girbe ko kuwa yana tsaye har ta cinye gonar, dole wanda ya kunna wutar ya biya diyya.
7Idan mutum ya ba maƙwabcinsa ajiyar kuɗi ko kaya, sai aka sace abin a gidansa, idan aka kama ɓarawon dole zai biya diyyar abin da ya sata riɓi biyu.8Amma idan ba a kama ɓarawon ba, sai mai gidan ya zo wurin alƙali a gani ko ya ɗauki wani abu cikin kayan maƙwabcinsa.9Gama kowacce jayayya game da wani abu, ko bijimi ko jaki ko tinkiya ko kayan sawa, ko kowanne abin da ya ɓace wani ya ce, "Wannan nawa ne," dole a zo wurin alƙali da masu jayayyar. Wanda a ka samu da laifi zai biya maƙwabcinsa diyya riɓi biyu.
10Idan mutum ya ba maƙwabcinsa ajiyar jaki ko bijimi ko tinkiya ko kowacce irin dabba, sai ta mutu ko aka ji mata rauni ko aka ɗauke ta ba wanda ya gan ta,11dole su biyun suyi rantsuwa domin a gane wani bai ɗauki kayan maƙwabcinsa ba. Sai mai abin ya yarda da haka kuma ɗayan ba zai biya diyya ba.12Amma idan sacewa aka yi, sai mutumin ya biya diyya ga mai shi.13Idan kuma an yayyaga dabbar ne, sai mutumin ya kawo dabbar shaida. Ba zai biya dabbar da aka yayyaga ba.
14Idan mutum ya yi aron dabba a wurin maƙwabcinsa, sai aka yi wa dabbar rauni ko ta mutu ba a wurin mai ita ba, dole ɗaya mutumin ya biya diyya.15Amma idan dabbar tana wurin mai ita, ɗaya mutumin ba zai biya ba; idan hayar dabbar aka yi sai a biya kuɗin hayar.
16Idan mutum ya ruɗi budurwa wadda ba a yi riƙon ta ba, har ya kwana da ita, dole yasa ta zama matarsa ta wurin biyan dukiya yadda aka bukaci ya biya.17Idan mahaifinta ya ƙi ba shi ita, to dole ya biya dukiya dai-dai da ta budurwa.
18Dole ne ba zaka bar mayya ta rayu ba.19Dukkan wanda ya kwana da dabba dole za a kashe shi.
20Dukkan wanda ya yi hadaya ga wani allah in ba Yahweh ba dole za a hallaka shi.21Dole ne ba zaku yi wa baƙo laifi ba ko kuwa ku ƙware shi, domin dă ku baƙi ne a Masar.
22Kada ka wulaƙanta gwauruwa ko maraya.23Idan ka ƙware su, suka yi kira gare ni, babu shakka zan ji kiran su.24Fushina zai yi, ƙuna kuma zan kashe ka da kaifin takobi; matanka zasu zama gwauraye, 'ya'yanka kuma su zama marayu.
25Idan ka bada rancen kuɗi cikin mutanena matalauta, kada ka zama kamar mai bada kuɗi da ruwa, ba zaka sa riba ba.26Idan ka karɓi rigar maƙwabcinka da alƙawari, dole ka dawo masa da ita kafin rana ta faɗi,27gama ita kaɗai ce abin rufarsa; ita ce rigar da zai sa jikinsa. Da me zai rufa? Sa'ad da ya kira gare ni, zan ji kiransa gama ni mai tausayi ne.
28Kada ka yi mani saɓo, Allah, ko ka zagi mai mulkin mutanenka.
29Kada ku hana baye-baye daga amfanin gonarku ko ruwan inabinku. Dole ku bani nunar fari ta 'ya'yanku.30Dole kuma ku yi haka da bijimanku da tumakinku. Gama kwana bakwai za su yi da iyayensu, a rana ta takwas za ku bada su gare ni.31Za ku zama mutane keɓaɓɓu gare ni. Kada ku ci kowanne abin da naman daji ya kashe a gona. Sai dai, ku jefa wa karnuka shi.

23

1Kada ku ba da shaidar ƙarya game da wani. Kada ku haɗa kai da mai mugunta ku zama maƙaryatan shaidu.2Kada ku bi rububi domin ku yi mugunta, ko ku goyi bayan rububi ku yi shaida domin ku ɓata adalci.3Kada ku nuna wa matalauci fifiko idan a na yi ma sa shari'a ko kaɗan.

4Idan ka gamu da bijimin maƙiyinka ko jakinsa ya ɓace, dole ka dawo masa da shi.5Idan ka ga jakin wanda yake ƙin ka ya faɗi, kaya ya danne shi, kada ka bar shi shi kaɗai. Dole ka taimake shi ka tada jakinsa.
6Kada ka yar da adalci gefe sa'ad da ake yi wa matalaucinka shari'a.7Kada ka haɗa kai da waɗan su ku yi zargi a kan ƙarya, kada ku kashe marar laifi ko mai adalci, gama ba zan 'yantar da mai mugunta ba.8Kada ku karɓi toshi ko kaɗan, gama toshi ya kan sa masu gani su makance, ya hana maganar masu aminci aiki.9Kada ku cuci baƙo, da yake ka san rayuwar baƙo, gama da kuma baƙi ne a Masar.
10Shekaru shida za ka shuka iri a gonakinka ka sami amfaninsa.11Amma a shekara ta bakwai za ka bar ta ba za ka noma ba, domin matalauta na cikin ku su ci abinci. Abin da suka rage namun daji za su ci. Haka kuma za ku yi da gonakinku da garkunan inabinku.
12Cikin kwanaki shida za ku yi aiki, amma a rana ta bakwai dole za ku huta. Ku yi haka domin bijimanku da jakinku su huta, domin 'ya'yan bayinka da kowanne baƙo ya huta ya wartsake.13Ku yi lura da dukkan abin da na gaya maka. Kada ku ambaci sunayen waɗansu alloli, ko ku bari a ji sunayensu daga bakinku.
14Dole ku je ku yi mani biki sau uku a kowacce shekara.15Za ku yi bikin gurasa marar gami. Kamar yadda na umurce ku, za ku ci gurasa marar gami kwana bakwai. A wannan lokaci, za ku zo gabana a watan Abib, wanda aka tsaida domin yin haka. A cikin wannan wata ne kuka fito daga Masar. Amma kada ku zo gabana hannu wofi.
16Dole za ku yi Bikin Kaka, na nunar fari na irin da kuka shuka a gonakinku. Kuma dole ku yi Bikin Tattarawa a ƙarshen shekara, sa'ad da kuka tattara amfanin gonakinku gida.17Dole mazajenku dukka su zo gaban Ubangiji Yahweh sau uku a shekara
18Dole ba za ku miƙa mani jinin hadayunku da gurasa wadda take da gami ba. Kitsen hadayun idodina ba zai wuce dukkan dare ya kai safiya ba.19Dole ku kawo zaɓaɓɓar nunar fari na gonakinku gidana, gidan Yahweh Allahnka. Ba za ka dafa 'yar burguma mai shan nonon uwarta ba.
20Zan aiko da mala'ika ya yi maku jagora a kan hanya, ya kawo ku wurin da na shirya.21Ku saurare shi ku yi masa biyayya. Kada ku cakune shi domin ba zai gafarta laifofinku ba. Sunana yana kansa.22Idan kuka yi biyayya da muryarsa kuka yi dukkan abin da na faɗa maku, zan zama maƙiyi ga maƙiyanku in tayar wa masu tayar maku.
23Mala'ikana zai shiga gabanku ya kawo ku wurin Amoriyawa da Hittiyawa da Firizziyawa da Kan'aniyawa da Hibiyawa da Yebusiyawa. Zan hallaka su.24Kada ku rusuna wa allolinsu, ku yi masu sujada, ko ku yi kamar yadda suke yi. Maimakon haka, dole ku kaɓantar da su dukka, ku ragargaza ginshiƙan duwatsunsu rugu--rugu.25Dole Yahweh Allahnku za ku yiwa sujada, kuma zai albarkaci gurasarku da ruwanku. Zan kawar da ciwo daga cikin ku.
26Ba matar da za ta zama bakarariya ko ta yi ɓarin jariri a ƙasarku. Zan baku tsawancin kwana.27Zan sa tsoro a cikin waɗanda kuke shiga ƙasarsu. Zan kashe dukkan mutanen da kuka gamu da su. Zan sa dukkan maƙiyanku su juya maku baya a wurin yaƙi.28Zan aiko da zirnaƙo ya kori Hibiyawa da Kan'aniyawa da Hittiyawa daga gabanku.29Ba zan kore su a cikin shekara ɗaya ba domin kada ƙasar ta zama ba kowa, kada namun daji su yi maku yawa ƙwarai.
30Maimakon haka zan kore su da kaɗan-kaɗan har ku yi yawa ku gaji ƙasar.31Zan sa iyakokinku daga Tekun Iwa zuwa Tekun Filistiyawa, kuma daga jejin Kogin Yuferatis. Zan baku nasara a kan dukkan mazunan ƙasar. Za ku kore su daga gabanku.32Kada ku yi amana da su koda allolinsu.33Kada su zauna a ƙasarku, domin kada su sa ku yi zunubi a gare ni. Idan kuka yi sujada ga allolinsu, babu shakka zai zama tarko a gare ku."'

24

1Sa'an nan Yahweh yace da Musa, "Ku hawo wuri na-kai, da Haruna, da Nadab, da Abihu, da dattawa saba'in na Isra'ila, ku yi mani sujada daga nesa.2Musa kaɗai ne zai zo kusa da ni. Sauran ba zasu zo kusa ba, mutanen ba zasu hawo tare da shi ba."

3Musa ya je ya faɗa wa mutanen Isra'ila dukkan maganganun Yahweh da farillai. Dukkan mutanen suka amsa da murya ɗaya suka ce, "Za mu yi dukkan abin da Yahweh yace,"4Sa'an nan Musa ya rubuta dukkan maganganun Yahweh. Tun da sassafe, Musa ya gina bagadi a kusa da tsaunin ya shirya duwatsu goma sha biyu, domin duwatsun goma sha biyu su zama a madadin kabilu goma sha biyu na Isra'ila.
5Ya aiki waɗansu samarin Isra'ila su miƙa baye-baye na ƙonawa da hadaya ta baye-bayen zumunta na bijimai ga Yahweh.6Musa ya ɗauki rabin jinin ya sa cikin darurruka; ya yayyafa sauran rabin a bisa bagadin.
7Ya ɗauki littafin Alƙawarin ya karanta shi da murya ga mutanen. Suka ce, "Za mu yi dukkan abin da Yahweh ya faɗi. Za mu zama masu biyayya."8Sa'an nan Musa ya ɗauki jinin ya yayyafa shi a kan mutanen. Ya ce, "Wannan shi ne jinin alƙawarin da Yahweh ya yi daku sa'ad da ya baku alƙawari da dukkan waɗannan maganganun."
9Sa'an nan Musa da Haruna da Nadab da Abihu, da dattawa saba'in na Isra'ila suka hau bisa tsaunin.10Suka ga Yahweh na Isra'ila. A ƙarƙashin ƙafafunsa a kwai wani dakali wanda aka yi kamar da n safire, yana sheƙi kamar sararin sama.11Yahweh bai ɗora hannu don fushi a kan dattawan Isra'ila ba. Suka ga Yahweh, suka ci suka sha.
12Yahweh yace da Musa, "Ka hawo wurina a kan tsaunin ka tsaya a can. Zan baka alluna na dutse da doka da dokokin da na rubuta, domin ka koya masu."13Sai Musa ya shirya, shi da mataimakinsa Yoshuwa suka hau tsaunin Yahweh.
14Musa yace da dattawan, "Ku tsaya nan ku jira har sai mun dawo wurin ku. Haruna da Hor suna tare da ku. Idan wani yana da damuwa, ya je wurin su."15To sai Musa ya hau tsaunin, girgije ya rufe tsaunin.
16Darajar Yahweh ta sauko a kan Tsaunin Sinai, girgije ya rufe shi har kwana shida. A rana ta bakwai ya kira Musa daga cikin girgijen.17Baiyanuwar darajar Yahweh ta yi kama da wuta mai ci a idanun Isra'ilawa a kan tsaunin.18Musa ya shiga cikin girgijen ya hau kan tsaunin. Yana can kan tsaunin har kwana arba'in da yini arba'in.

25

1Yahweh yace da Musa,2"Ka ce da Isra'ilawa, duk mutumin da ya ji yana da niyya a zuciyarsa ya kawo mani baiko. Sai ka karɓi waɗannan baye-baye domi na.

3Ga baye-bayen da za ka karɓa daga wurin su: zinariya, da azurfa, da tagulla;4da shuɗi, da shunayya, da jăn kaya; da leshe mai kyau; da gashin awaki;5da fatar rago da aka yiwa jan rini da fatar ragon ruwa; da itacen ƙirya;6da mai domin fitilu na haikali; da kayan yaji saboda mai na shafewa da turare mai ƙanshi da duwatsun7oniks da sauran duwatsu masu daraja da za a manna a alkyabba da ɗamara ta ƙirji.
8Sai su yi mani haikali domin in zauna a cikin su.9Sai ka yi dai-dai yadda zan nuna maka tsarinsa da dukkan kayayyakinsa.
10Za su yi akwati na itacen ƙirya. Ratarsa za ta zama kamu biyu da rabi; faɗinsa zai zama kamu ɗaya da rabi; tsayinsa zai zama kamu ɗaya da rabi.11Sai ka shafe shi da zinariya tsantsa ciki da waje, dole ka kewaye shi da rawanin zinariya a bisansa.
12Sai ka yi ƙawanyu huɗu na zubi da zinariya domin sa, kasa su a ƙafafu huɗu na akwatin, da ƙawanyoyi biyu a ɗaya gefen.13Sai ka yi sanduna na itacen ƙirya ka shafe su da zinariya.14Sai kasa sandunan a cikin ƙawanyoyi na gefen akwatin alƙawarin, yadda za a iya ɗaukar sa.
15Za a bar sandunan jikin akwatin; kada a cire su.16Sai ka sa ka'idodi na alƙawarin da zan baka a cikin akwatin.17Sai ka yi marfi na zinariya tsantsa. Ratarsa za ta zama kamu biyu da rabi, faɗinsa kuma kamu ɗaya da rabi.18Sai ka yi sifofi biyu na kerubim da gogaggiyar zinariya saboda gefe biyu na marfin kafara.
19Ka yi kerub ɗaya saboda gefe ɗaya na marfin kafara, ɗaya kerub ɗin kuma saboda ɗaya gefen. Za ka yi su dai-dai kamar abu ɗaya da marfin kafara.20Fukafukan kerubobin su miƙe tsaye su yi sama su yiwa marfin kafara inuwa. Kerubobin su dubi juna su kalli tsakiyar marfin kafara.21Sai ka sa marfin kafara a kan akwatin, kuma kasa ka'idodi na alƙawari da zan ba ka a ciki.
22A wurin akwatin ne zan sadu da kai. Zan yi magana da kai a inda nake a bisa marfin kafara. Zai zama daga tsakanin kerubobin biyu a bisa akwatin na shaida zan yi magana da kai game da dukkan ka'idodi da zan baka domin Isra'lawa.
23Sai ka yi teburi na itacen ƙirya. Ratarsa za ta zama kamu biyu; faɗinsa kamu ɗaya, tsayinsa zai zama kamu ɗaya da rabi.24Sai ka shafe shi da zinariya tsantsa ka yi masa ado da dajiya ta zinariya a sama kewaye da shi.
25Sai kayi dajiya ta kewaye shi mai faɗin tafin hannu ɗaya, ka kuma yiwa bakinsa ado da bugaggen zinariya.26Sai ka yi masa ƙawanyoyi na zinariya guda huɗu ka liƙa ƙawanyoyin a kusurwoyinsa huɗu, inda ƙafafun nan huɗu suke.27Sai ka liƙa ƙawanyoyin a wuri domin sandunan, yadda za a iya ɗaukar teburin.
28Sai ka yi sandunan da itacen ƙirya ka shafe su da zinariya domin a iya ɗaukar teburin tare da su.29Sai ka yi tasoshinsa da cokulansa da butocinsa da akusoshinsa domin zuba baye-baye na sha. Sai ka yi su da zinariya zalla.30Za ka riƙa ɗora gurasa ta kasancewa a bisa teburin a gabana.
31Sai ka yi wurin ɗora fitila da gogaggiyar zinariya. Wurin ɗora fitilar za kayi da wurin zamansa. Kofinansa da leɓunansa da furanninsa za kayi su tare kamar abu ɗaya.32Rassa shida za su fito daga gefunansa-rassa uku daga gefe ɗaya, rassa uku kuma na wurin ɗora fitilar su zarce a ɗaya gefen.
33Reshe na farko zai zama da kofuna uku kamar an yi su da lingaɓin itacen almond, da baki mai kamar ganye da fure, kofuna uku kuma an yi su kamar lingaɓin itacen almond a ɗaya reshen, da baki kamar ganye da fure. Dukkan su shida za su zama dai-dai da juna, su zarce daga abin ɗora fitilar.34A kan abin ɗora fitilar kansa, a tsakiyarsa, zai kasance da kofuna huɗu masu kama da lingaɓin itacen almond, da kamannin ganye da furanni.
35Tagwayen rassa biyu na farko za su zama da baki kamar ganye-an yi su tare kamar abu ɗaya, tagwayen rassa na biyu kuma an yi su da kamar ganye abu ɗaya tare. Haka kuma tagwayen rassa na uku za a yi su da kamannin ganye sai ka ce abu ɗaya. Haka dukkan rassan shida za su zama su zarce wurin ɗora fitilar.36Bakunansu masu kama da ganye za su zama abu ɗaya, an yi shi da bugaggiyen aikin curin zinariya tsantsa.
37Za ka yi abin ɗora fitilar da fitulunsa guda bakwai, kasa fitilun a bisansa domin su bada haske daga wurinsa.38Hantsukan da tasoshin a yi su da zinariya tsantsa.39A yi amfani da awo ɗaya na zinariya a yi wurin ɗora fitilar da kayayyakinsa.40Ka tabbata ka yi su kamar yadda aka nuna maka a kan tsaunin.

26

1Rumfar taruwa kuma za ka yi ta da labule goma da aka yi su da lilin mai kyau da shuɗi da shunayya da jan ulu mai zanen cerubim. Wanda gwanin mai aikin hannu ya yi.2Tsawon kowanne labule zai zama kamu ashirin da takwas, faɗi kuma kamu huɗu. Labulen dukkan su su kasance girmansu ɗaya.3Labule biyar su zama haɗe da juna, sauran biyar kuma su zama haɗe da juna.

4Kashi ɗaya na labulen za ka yi masa abin ratayewa na shuɗi daga ƙarshensa. Kashi na biyu ma haka za ka yi masu daga ƙarshe.5Kashi na farko za ka yi masu wurin ratayewa hamsin, kashi na biyu ma za ka yi masu wurin ratayewa hamsin. Ka yi haka domin wurin ratayewar labulen su dubi junansu.6Sai ka yi kayan adon labule na zinariya guda hamsin ka haɗa labulen tare da juna domin rumfar sujadar ta zama a haɗe.
7Za ka yi labule na gashin awaki domin rumfa ta bisan rumfar sujada. Za ka yi labule guda goma sha ɗaya.8Tsawon kowanne labule zai zama kamu talatin, faɗin kowanne labule kuma kamu huɗu. Labulen nan goma sha ɗaya girmansu ya zama ɗaya.9Labule biyar sai ka haɗa su da juna sauran shida kuma ka haɗa su da juna. Sai ka gwama labule na shida wanda yake a gaban rumfar.
10Sai ka yi maratayi hamsin a gefen labule jeri na farko, maratayi hamsin kuma a gefen labulen da ya haɗa jeri na biyu.11Sai ka yi abin maƙalawa hamsin na tagulla ka sa su a maratayin. Sa'an nan ka haɗa rumfar tare ta zama abu ɗaya.
12Rabin labulen da ya rage, wato wanda ya zarce ya ragu daga labulen rumfar, sai ka bar shi yana lilo a bayan rumfar sujada.13Zai zama kamu ɗaya na labulen a gefe ɗaya, kamu ɗaya kuma na labulen a ɗaya gafen-wato abin da ya ragu na labulen rumfar a bar shi ya na lilo a gefen rumfar sujada a sashi ɗaya domin ya rufe ta.14Sai ka yi wa rumfar sujadar abin rufewa da fatun rago waɗanda a ka jeme mai rinin jă, wani marfin kuma na fata mai kyau ka sa ya rufe wannan.
15Sai ka yi wa rumfar sujadar diraku na itacen ƙirya a kafa su a tsaye.16Ratar kowacce dirka zai zama kamu goma, faɗin ta kuma kamu ɗaya da rabi.17Sai a yi wa dirakun turaka biyu na katako domin su haɗa su da juna. Haka za ka yi dukkan dirakun rumfar sujada.18Sa'ad da ka yi dirakun rumfar sujadar, sai ka yi guda ashirin saboda sashi na kudu.
19Sai ka yi darurruka arba'in na azurfa a ƙarƙashin dirakun nan ashirin. Darurruka biyu za su zama matashin dirka ta farko, darurruka biyu kuma za su zama matashin dirakun guda biyu.20Sashi na biyu na rumfar sujada, wato daga arewa, za ka yi masa diraku ashirin21da darurrukansu guda arba'in na azurfa. Dirka ta farko za ta kasance da darurruka biyu, biyu kuma a ta gaba, har a gama su dukka.
22Bayan rumfar sujada kuma daga sashin yamma, sai ka yi ma sa diraku shida.23Sai ka yi diraku biyu saboda kusurwar rumfar sujada ta baya.24Waɗannan dirakun ba za a haɗa su daga ƙasa ba, amma daga sama za a haɗa su da ƙawanya ɗaya. Haka kusurwoyi biyu na baya za su zama.25Za su zama diraku takwas, tare da darurrukansu na azurfa. Za a sami darurruka goma sha shida, darurruka biyu a ƙarƙashin dirka ta farko, darurruka biyu kuma a ta gaba, har a gama.
26Dole ka shirya katakai da zasu gitta da itacen ƙirya-biyar saboda sashi ɗaya na dirakun rumfar sujada,27katakai biyar na gittawa kuma saboda ɗaya sashin na dirakun rumfar sujada, katakai biyar na gittawa kuma saboda dirakun sashin rumfar sujada na baya wajan yamma.28Katakon da yake tsakiyar dirakun, zai kai daga wannan ƙarshe zuwa wancan ƙarshen.
29Sai ka shafe dirakun da zinariya. Za kuma ka yi zobbansu da zinariya, domin su riƙe katakan da aka gitta, na gittawar ma za ka shafe su da zinariya.30Dole ka tsara rumfar sujada ta wurin bin yadda aka nuna maka a kan tsaunin.
31Sai ka kayi labule na shuɗi, da shunayya, da jan ulu, da leshe mai kyau da zanen kerubim, wanda ƙwararren mai aikin hannu zai yi.32Sai dole ka rataye shi a kan ginshiƙai na itacen ƙirya shafaffu da zinariya. Waɗannan ginshiƙai za a yi ma su ƙugiyoyi na zinariya a kan darurruka huɗu na azurfa.33Sai kuma dole ka sa labulen a wurin ratayewarsa, sai kuma ka kawo akwatin a ciki. Labulen zai raba tsakanin wuri mai tsarki da wuri mafi tsarki.
34Sai kasa marfi na kafara a bisa akwatin shaida, wanda yake a cikin wuri mafi tsarki. Sai kasa teburin a waje daga labulen.35Sai kasa wurin ɗora fitilar ya dubi teburin daga sashin kudu na rumfar sujada. Teburin ya kasance daga sashin arewa.
36Sai kuma dole ka yi maratayi a ƙofar shiga rumfar. Sai kuma dole ka yi shi da shuɗi, da shunayya, da jan ƙyalle, da leshe mai kyau, murɗaɗɗe wanda mai iya zane a kan tufa ya yi.37Wurin ratayewar za ka yi masa ginshiƙai biyar na ƙirya shafaffu da zinariya. Ƙugiyoyinsu su zama na zinariya, ka yi darurruka biyar na zubi da tagulla.

27

1Sai ka yi bagadi na itacen ƙirya, ratarsa kamu biyar faɗinsa ma kamu biyar. Bagadin zai kasance kamu dai-dai kowanne gefe da tsawonsa kamu uku.2Za ka sa kusurwoyinsa su zarce da kamannin ƙahonin bijimi. Bagadin da ƙahonin za su zama tare kamar abu ɗaya, zaka shafe su da tagulla.

3Za ka yi kayan aiki domin bagadin: wato tukunya saboda zuba toka da kuma cebur da darori da cokulan tsamo nama da kasake na tuya. Dukkan waɗannan kayan aikin za kayi su da tagulla.4Za ka yiwa bagadin makari na tagulla da răgă. Za ka yi zobba na tagulla guda huɗu domin kowacce kusurwa.
5Za ka sa makarin ƙasa da bagadin, ya kai rabin sa daga ƙasa.6Za ka yiwa bagadin sanduna na itacen ƙirya, ka shafe su da tagulla.
7Sandunan za ka sa su shiga cikin zobban, a sassa biyu na bagadin, domin a iya ɗaukar sa.8Za kayi bagadin ba kome a cikinsa, da katakai. Za kayi shi kamar yadda a ka nuna maka a kan tsaunin.
9Za ka yi wa rumfar sujada haraba. Za a yi wuraren rataye-rataye a harabar a sashin kudu, ragayu na leshe mai kyau saƙaƙƙe mai ratar kamu ɗari.10Za ka yi diraku ashirin domin ragayun, da darori ashirin na tagulla. Za a yi ƙugiyoyi liƙe da dirakun da sanduna na azurfa.
11Haka kuma a sashin arewa, za ka yi ragayu guda ɗari tare da diraku ashirin da darori ashirin na tagulla da ƙugiyoyi liƙe da dirakun da sandunan azurfa.12A sashin yamma na harabar za ka yi labule kamu hamsin. Za ka yi diraku goma da darori goma.13Haraba za ta zama kamu hamsin daga sashin gabas.
14Ragayoyi na wurin shiga ratarsa za su zama kamu hamsin. Za su zama da diraku uku da darori uku.15Ɗaya sashin ma zai zama da ragayu kamu goma sha biyar. Da dirakunsu uku da darorinsu uku.16Ƙofar shigowa harabar za ta zama da labule mai ratar kamu ashirin. Za a yi labulen da shuɗi da shunaiya da jăn ƙyalle da saƙaƙƙen leshe mai kyau, wanda ƙwararren mai aikin hannu ya yi. Zai zama da diraku huɗu da darori huɗu.
17Dukkan dirakun harabar za su zama da sandunan azurfa da ƙugiyoyin azurfa da darorin tagulla.18Ratar harabar za ta zama kamu ɗari, da faɗin kamu hamsin da tsawon kamu biyar da ragaya ta saƙaƙƙen leshe mai kyau da darori na tagulla.19Dukkan kayan aikin rumfar sujada, da abubuwan kamawar na harabar za a yi su da tagulla.
20Za ka umurci mutanen Isra'ila su kawo man zaitun, mai tsabta, domin fitilun su yi ta ci ba fasawa.21A rumfa ta taruwa, bayan labulen rumfar sujada inda akwatin shaida ya ke, Haruna da 'ya'yansa za su sa fitilun suyi ta ci tun daga yamma har zuwa safiya a gaban Yahweh. Mutanen Isra'ila za su lura da wannan ka'idar a dukkan zamanu.

28

1Ka kira Haruna ɗan'uwanka da 'ya'yansa maza- wato, Nadab, da Abihu, da Eliyeza, da Itama - daga cikin Isra'ilawa domin su yi mani hidima a matsayin firistoci.2Ka yi wa Haruna, ɗan'uwanka rigunan keɓaɓɓu gare ni. Waɗannan riguna za su zama domin ya fita da kyau da kwarjini.3Ka yi magana da mutane masu hikima a zuciya, waɗanda na cika su da ruhun hikima, domin su yi wa Haruna riguna a keɓe shi domin ya yi mani hidima a matsayin firist.

4Rigunan da za suyi su ne, ɗamara ta sawa a ƙirji da alkyabba, da taguwa, da riga mai aiki, da rawani, da ɗamara. Za su yi waɗannan tufafi keɓaɓɓu gare ni. Za su zama saboda Haruna ɗan'uwanka da 'ya'yansa domin su yi mani hidima a matsayin firistoci.5Ma su aikin hannu za su yi amfani da leshe mai kyau mai launin zinariya, da shuɗi, da shunayya, da jã.
6Sai su yi alkyabba da launin zinari, da shuɗi, da shunayya, da jan ulu, da leshe mai kyau mai aiki. gwani ne zai yi aikin.7A kusurwoyi biyu za ta kasance da ƙyallayen da za'a sa a kafaɗa.8A yi mata saƙa mai kyau ɗamarar ta zama kamar alkyabbar; kuma a yi su tare da falmarar, ayi su da leshe mai kyau mai aiki da launin zinari da shuɗi da shunaiya da ja.9Ka ɗauki duwatsu biyu na oniks ka rubuta sunayen 'ya'yan Isra'ila goma sha biyu.
10Sunaye shida a kan dutsen ɗaya, sauran shidan kuma a kan ɗaya dutsen, bisa ga yadda aka haife su.11Mai iya rubutu a kan dutse ne zai yi rubutun kamar yadda ake rubuta hatimi, ka rubuta sunayen 'ya'yan Isra'ila goma sha biyu a kan duwatsun guda biyu. Ka ɗora duwatsun a kan kasko na zinariya.12Za ka ɗora duwatsun biyu a ƙyallen kafaɗa na falmara, su zama duwatsun tuna wa Yahweh da 'ya'yan Isra'ila. Haruna zai ɗauki sunayensu a gaban Yahweh bisa kafaɗunsa biyu su zama abin tunawa a gare shi.
13Sai kayi kasake na zinariya14za kayi sarƙoƙi biyu na zinariya kamar tsarkiyoyi, ka liƙa sarƙoƙin a jikin kasaken.
15Za ka yi ƙyalle na ƙirji domin yin shawara, ka sami gwani ya tsara shi kamar alkyabba. A yi shi na zinariya, da shuɗi, da shunayya, da jan ulu, da linin mai kyau.16Ya zama murabi'i. Ƙyallen na ƙirji za ka sa shi riɓi biyu. Ratarsa za ta zama taki ɗaya faɗinsa ma taki ɗaya.
17Ka yi jere huɗu na duwatsu masu daraja a jikinsa. Dole jeri na farko a sa rubi, da tofez, da kuma ganet..18A jeri na biyu kuma dole a sa emerald, da saffiya, da lu'u-lu'u.19Jeri na uku kuma dole kasa yasint, da agat, da kuma ametis.20Jeri na huɗu za ka sa beril da oniks, da yasfa. A sa su a kan kasaken zinariya.
21Za a jera duwatsun bisa ga sunayen 'ya'yan Isra'ila goma sha biyu, bi da bi a jere. A zana su kamar yadda a ke yin hatimi da zobe, kowanne suna ya zama a madadin kabilu goma sha biyu.22Ƙyalle na ƙirjin ya zama sarƙa kamar tsarkiya, saƙaƙƙe na zinariya tsantsa.23Za ka yi wa ƙyallen zobba biyu liƙe da juna a kusurwoyinsa biyu.24Ka liƙa sarƙoƙin nan biyu a jikin ƙyalle na ƙirji.
25Za ka liƙa ƙarshen sarƙoƙin nan biyu a jikin kasaken. Sa'an nan ka liƙa su a jikin ƙyallen kafaɗa na falmara a gaba.26Za ka yi zobba na zinariya guda biyu, ka sa su a ɗaya gefe na ƙyallen na ƙirjin, a ƙarshen kalmasa ta ciki kusa da haɓar.
27Dole zaka yi waɗansu zobba na zinariya guda biyu, ka liƙa su jikin ƙyalle na kafaɗar falmara daga ƙasa, a bisa ɗamarar nan ta kyakkawan leshe na falmarar.28Su haɗa ƙyallen nan na ƙirji da zobban falmarar nan masu launin shuɗi, domin su haɗu saƙaƙƙiyar ɗamarar nan ta falmarar. Domin kada ƙyallen na ƙirji ya zama a ware da falmarar.
29Sa'ad da Haruna yake shiga cikin wuri mai tsarki, zai ɗauki sunayen mutanen Isra'ila a bisa zuciyarsa cikin ƙyallen nan na ƙirji domin ɗaukar shawara, za ayi ta yin haka domin ya zama abin tunawa a gaban Yahweh.30Zaka sa Urim da Tummim a cikin ƙyalle na ƙirjin domin ɗaukar shawara, domin su zama a bisa zuciyar Haruna sa'ad da yake shiga gaban Yahweh. Ta haka Haruna zai riƙa ɗaukar abin ɗaukar shawara domin mutanen Isra'ila bisa zuciyaarsa a gaban Yahweh.
31Rigar wato falmara zaka yi ta duka da shuɗi.32Za a yi mata wurin sa kai a tsakiya. Dole ayi wa wurin sa kai ɗin saƙa domin kada ya yage. Dole a sami mai saƙa ya yi aikin.
33Za ka yi wa haɓar rigar, ado na 'yan tutoci da shuɗi, da shunayya, da jan ulu ya kewaye dukka.34Ka yi ƙararrawa ta zinariya ta zagaya dukka a tsakanin tutocin. A sa ƙararrawa ta zinariya da tuta, sai kuma ƙararrawa ta zinariya sai kuma tuta - da sauransu - kewaye tufar dukkan ta.35Haruna zai sa wannan tufar sa'ad da zai yi hidima, domin a iya jin ƙararta sa'ad da yake shiga wuri mai tsarki gaban Yahweh da sa'ad da yake fita. Wannan domin kada ya mutu ne.
36Dole ka yi faranti na zinariya ka yi zane a kan sa, kamar zanen hatimi, "Tsarki ga Yahweh."37Za ka liƙa wannan farantin da shuɗiyar iggiya a jikin rawanin.38Haruna zai sa shi a kansa; zai ɗauki laifi da ake yi game da baye-baye masu tsarki na Isra'ilawa waɗanda aka keɓe domin Yahweh. Dole rawanin ya kasance a kansa domin Yahweh ya karɓi baye- bayensu.
39Dole ka yi alkyabba da linin mai kyau, da rawani na linin mai kyau. Kuma zaka sa mai zane ya yi masa ado.
40Zaka yi riguna saboda 'ya'yan Haruna, da ɗammaru, da abin ɗaurawa a kansu saboda daraja da kwarjini.41Dole ka suturta Haruna ɗan'uwanka, da 'ya'yansa. Dole ka shafe su, ka naɗa su, ka keɓe su domi na, domin su yi mani hidima a matsayin firistoci.
42Dole ka yi masu wuyan wanduna na sawa a ciki domin su rufe tsiraicin jikinsu, ya rufe su daga kwankwaso zuwa cinya.43Haruna da 'ya'yansa za su riƙa sa waɗannan tufafi sa'ad da suke shiga wurin taruwa da sa'ad da suke fuskantar bagadi su yi hidima a wuri mai tsarki. Dole su yi haka domin kada su zama da kuskure in ba haka ba za su mutu. Wannan zaunanniyar doka ce domin Haruna da zuriyarsa a bayansa.

29

1Ga abin da za ka yi domin ka keɓe su yadda za su iya yi mani hidima a matsayin firistoci. Ka ɗauki ɗan bijimi da raguna biyu marasa cikas da,2gurasa marar gami, da waina marar gami gauraye da mai. Ka kuma ɗauki wainar alkama marar gami ka shafe da mai. wadda aka yi da kyakkyawar alkama. Wadda ake ci da zuma.

3Dole ka sa su a cikin kwando ɗaya, ka kawo su a cikin kwandon, ka miƙa su tare da bijimin da ragunan nan biyu.4Dole ne ka miƙa Haruna da 'ya'yansa a ƙofar shiga rumfar ta taruwa. Za ka yi wa Haruna da 'ya'yansa wanka da ruwa.
5Dole ka ɗauki rigunan da alkyabba ka sa wa Haruna da maratayin falmara da falmara da ƙyalle na ƙirjin da ɗamara ta leshe mai kyau tare da falmara ka yafa masa.6Ka naɗa rawanin a kansa da kambi na tsarki a bisa rawanin.7Sa'an nan ka ɗauki mai na shafewa ka zuba a kansa, da haka za ka shafe shi.
8Dole ka kawo 'ya'yansa su ma ka sa masu alkyabbobi.9Za ka sa wa Haruna da 'ya'yansa ɗammaru da ƙyalle na ado a kansu. Aikin firist zai zama nasu kullum bisa ga doka. Ta haka za ka tsarkake Haruna da 'ya'yansa domin su yi mani hidima.
10Dole dukkan ku za ku kawo bijimin a wurin rumfa ta taruwa, Haruna da 'ya'yansa za su sa hannayensu a kan bijimin.11Zaka yanka bijimin a ƙofar rumfar ta taruwa a gaban Yahweh.
12Dole ka ɗauki jinin bijimin da yatsarka ka sa a kan ƙahon bagadin, sai ka ɗauki sauran jinin ka zubar da shi a dakalin bagadin.13Dole ka ɗauki kitse na marfin ciki da wanda ya lulluɓe hantar da ƙodojin biyu da kitsen da yake kansu; ka ƙona a kan bagadin.14Amma naman bijimin da fatarsa da sauran abin da ya rage jikinsa, dole ka ƙone su a waje. Za ya zama baiko na zunubi.
15Dole ka kuma ɗauki rago ɗaya, Haruna da 'ya'yansa su ɗora hannuwansu a kansa.16Dole ka yanka ragon, ka yayyafa jininsa a kowanne sashi na bagadin.17Dole ka yanka ragon gunduwa--gunduwa da ƙafafunsa, ka sa 'yancikinsa tare da gunduwoyin tare da kansa,18a bisa bagadin. Sa'an nan ka ƙone ragon dukkan sa. Zai zama baiko na ƙonawa ga Yahweh, baiko mai daɗin ƙanshi wanda aka yi domin Yahweh.
19Sa'an nan dole ka ɗauki ɗaya ragon, Haruna da 'ya'yansa su ɗora hannuwansu a kansa.20Sa'an nan dole ka yanka ragon ka ɗauki jininsa. Ka sa shi a bisa kunnen Haruna na dama, da bisa kan kunnuwan 'ya'yansa na dama, da kan babban yatsansu na dama, da babban yatsan kowannen su na dama na ƙafa. Sa'an nan ka yayyafa jinin a jikin bagadin a kowanne sashe.
21Dole ka ɗauka daga jinin da yake kan bagadi da mai na shafewa, ka yayyafa a kan Haruna da tufafinsa, da kuma kan 'ya'yansa da tufafinsu. Sa'an nan Haruna zai zama keɓaɓɓe domi na, da kuma tufafinsa da 'ya'yansa da tufafinsu tare da shi.
22Dole ka ɗauki kitsen ragon da kitsen bindin da kitsen da ya rufe kayan cikin da wanda ya lulluɓe hantar, da ƙodojin biyu da kitsen dake kansu, da cinyar dama-wannan ragon na keɓewar firistoci ne a gare ni.23Ka ɗauki dunƙule ɗaya na gurasa da wainar da aka yi da mai, guda ɗaya da wainar alkama ɗaya daga cikin kwandon wadda bata da gami wadda ke gaban Yahweh.
24Dole ka sa waɗannan a cikin hannuwan Haruna da hannuwan 'ya'yansa ka ɗaga su a gabana domin baiko na ɗagawa a gaban Yahweh.25Sa'an nan dole ka ɗauke abincin daga hannuwansu ka ƙone shi a kan bagadin tare da baiko na ƙonawa. Zai kawo ƙanshi mai daɗi a gare ni; zai zama baikon da aka yi mani da wuta.
26Dole ka ɗauki haƙarƙarin ragon da aka yanka saboda keɓe Haruna ka ɗaga shi ka karkaɗa shi sama domin ya zama baiko na ɗagawa ga Yahweh, shi ne kuma zai zama rabonka.27Dole ka keɓe ƙirjin da aka karkaɗa a sama domi na, cinyar da firistoci suka kawo gudummuwa-ƙrjin da aka karkaɗa da cinyar da aka kawo gudummuwa saboda Haruna da 'ya'yansa.28Wannan zai zama zaunanniyar ka'ida saboda Haruna da 'ya'yansa. Zai zama gudummuwar da mutanen Isra'ila suka ba Yahweh baye-baye na salama.
29Za a ajiye tufafin Haruna masu tsarki saboda 'ya'yansa a bayansa. Za a shafe su a cikin waɗannan tufafi a keɓe su gare ni a cikin su.30Firist ɗin da ya gaje shi daga cikin 'ya'yansa, wanda ya zo rumfa ta taruwa domin ya yi mani hidima a wuri mai tsarki, zai sa waɗannan tufafi har kwanaki bakwai.
31Dole ka ɗauki ragon na rantsar da firistoci ka dafa namansa a cikin wuri mai tsarki.32Haruna da 'ya'yansa ne za su ci naman ragon da gurasar dake cikin kwando a ƙofar shiga rumfa ta taruwa.33Dole su ci naman da gurasar da aka bayar domin a yi masu kafara a kuma naɗa su, domin a keɓe su domina. Ba wanda zai ci wannan abincin, saboda zai zama abin da aka tsarkake saboda ni.34Idan naman keɓewar da aka bayar ko gurasar sun rage har sun kai safiya, za ka ƙone shi. Ba za a ci shi ba saboda an riga an keɓe shi saboda ni.
35Haka za ka yi, ka bi umarnin dana baka, ka yi wa "ya'yan Haruna haka. Ka shirya su har kwana bakwai.36Kowacce rana zaka miƙa bijimi domin baiko na zunubi damin kafara. Dole ka tsarkake bagadin ta wurin yin kafara domin sa, zaka shafe shi domin ya zama a keɓe domi na.37Dole ka yi kwana bakwai kana yin hadaya saboda bagadin kana keɓe shi saboda Yahweh. Sa'an nan bagadin zai zama keɓaɓɓe saboda ni. Dukkan abin da ya taɓa bagadin zai zama keɓaɓɓe na Yahweh.
38Dole ka riƙa miƙa ɗan rago bana ɗaya kowacce rana.39Dole ka miƙa ɗan rago ɗaya da safe, ɗaya ɗan ragon kuma ka miƙa shi da yamma.
40Tare da ɗan rago na fari, za a miƙa mudu biyu na garin alkama mai laushi wanda aka kwaɓa da man zaitun kwalba biyu, da ruwan inabi shi ma kwalba biyu baiko na sha.
41Rago na biyu tilas ka miƙa shi da faɗuwar rana. Dole ka sa gari kamar yadda ka sa da safe, haka kuma baiko na sha. Waɗannan za su zama da ƙamshi mai daɗi a gare ni; za su zama baiko da aka yi mani da wuta.42Waɗannan za su zama baiko na ƙonawa a cikin dukkan tsararrakinku, a ƙofar shiga rumfa ta taruwa a gaban Yahweh, inda zan sadu da kai in yi magana da kai a can.
43A nan ne zan sadu da Isra'ilawa; darajata za ta keɓe rumfar. Zan keɓe rumfar ta taruwa da bagadin domin su nawa ne ni kaɗai.44Zan kuma keɓe Haruna da 'ya'yansa domin su yi mani hidima a matsayin firistoci.
45Zan zauna a cikin Isra'ilawa zan zama Allahnsu.46Za su sani Ni ne Yahweh, Allahnsu wanda ya fito da su daga Masar domin in zauna a cikin su. Ni ne Yahweh Allahnsu.

30

1Tilas ka yi bagadi na ƙona turare. Tilas ka yi shi da itacen ƙirya.2Ratarsa za ta zama kamu ɗaya, faɗinsa kamu ɗaya. Tilas ka yi shi murabbi'i, tsawonsa kamu biyu. Tilas ka yi shi tare da ƙahonninsa.

3Tilas ka shafe bagadin da zinariya tsantsa-bisansa, da sassansa, da ƙahoninsa. Tilas ka kewaye gefensa da zinariya.4Tilas ka yi zobba biyu na zinariya liƙe da shi a kusa da shi daga ƙasa suna duban sa a sassa biyu. Zobban za su zama wurin zura sandunan riƙewa da za a iya ɗaukar bagadin.
5Tilas ka yi sandunan da itacen ƙirya, ka shafe su da zinariya.6Tilas ka sa bagadin turaren a gaban labulen dake kusa da akwatin shaida. Zai zauna a gaban marfin kafara na zunubi a bisa akwatin shaida, inda zan sadu da kai.
7Tilas Haruna ya ƙona turare mai ƙamshi kowacce safiya. Zai ƙona shi sa'ad da yake gyara fitilun,8da yamma kuma Haruna zai kunna fitilun domin turaren ya riƙa ƙonewa koyaushe a gaban Yahweh, a dukkan tsararraki.9Amma kada ka miƙa wani turaren a kan bagadin turaren, ko wani baiko na ƙonawa ko baiko na hatsi. Kada ka zuba wani baiko na sha a kansa.
10Tilas Haruna ya yi hadaya ta zunubi a kan ƙahonninsa sau ɗaya a shekara. Da jinin baikon na zunubi zai yi hadaya ta zunubi sau ɗaya a shekara a dukkan tsararrakinku. Keɓaɓɓe ne sarai saboda Yahweh."
11Sa'an nan Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,12"Sa'ad da ka ƙidaya Isra'ilawa, kowanne mutum zai kawo abin fansa domin ransa ga Yahweh. Sa'ad da ka ƙidaya su dole ne ka yi haka. Domin kada annoba ta auko a cikin su sa'ad da kake ƙidaya su.13Dukkan wanda aka ƙidaya cikin yin ƙidayar zai biya rabin awo na azurfa, bisa ga kuɗin da ake amfani da su a wuri mai tsarki (awon dai-dai yake da abin da ake auna nauyin ƙaramin abu). Wannan rabin awo baiko ne domin Yahweh.14Dukkan wanda aka ƙidaya, daga shekara ashirin zuwa gaba, dole ya bada wannan baikon gare ni.
15Lokacin da mutane suke bada wannan baiko domin fansar rayukansu, masu arziki ma ba zasu bada fiye da rabin awon nan ba, matalauta kuma ba zasu bada abin da bai kai rabin awon nan ba.16Dole ka karɓi wannan kuɗin fansa daga Isra'ilawa ka sa su cikin aikin rumfa ta taruwa. Dole ya zama abin tunawa ga Isra'ilawa a gare ni, su miƙa abin kafara domin rayukansu.
17Sa'an nan Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,18"Zaka yi babban bangaji na tagulla da wurin zamansa na tagulla, bangajin wanke-wanke. Tilas ka sa shi tsakanin rumfa ta taruwa da bagadi, ka zuba ruwa a cikin sa.
19Haruna da 'ya'ansa za su wanke hannuwansa da ƙafafunsu da ruwan dake cikin sa.20Sa'ad da suke shiga rumfa ta taruwa da sa'ad da suke zuwa kusa da bagadi su yi mani hidima ta ƙona baiko, dole su wanke da ruwa domin kada su mutu.21Dole su wanke hannuwansu da ƙafafunsu domin kada su mutu. Dole wannan ta zama dawwamammar doka ga Haruna da zuriyarsa a dukkan tsararrakin mutanensa.
22Sa'an nan Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,23"Ka ɗauki waɗannan kayan yaji masu kyau: da murr mai zubowa na awo ɗari biyar, da sinamon mai ƙanshi mai daɗi na awo 250, da kayan yaji mai ƙanshi na awo 250,24da kayan yaji mai ƙanshi na kasiya na awo ɗari biyar, wanda aka auna bisa ga ma'aunin wuri mai tsarki, da kwalba ɗaya ta man zaitun.25Dole da waɗannan kayan haɗi za ka sa maiyin turare ya yi mai na shafewa mai tsarki. Zai zama man tsarki na shafewa, ajjiyayye saboda ni.
26Dole da wannan mai na shafewa za ka shafe rumfa ta taruwa da akwati na shaida,27sai kuma teburin da kayan aikinsa da abin ɗora fitilar da kayanta da sanduƙin turare,28sai kuma bagadin ƙona baye--baye da dukkan kayansa da bangajin da wurin ɗora shi.
29Tilas ka keɓe su saboda ni su zama masu tsarki domi na. Dukkan abin da ya taɓa su zai zama mai tsarki.30Tilas ka keɓe Haruna da 'ya'yansa domin su yi mani hidima a matsayin firistoci.31Dole kace da Isra'ilawa, 'Wannan mai na shafewa ne da aka keɓe domin Yahweh a dukkan tsararrakin mutanenku.
32Dole mutane ba za su shafa shi a jikinsu ba, kuma ba za ka yi wani mai da kamar yadda ka yi shi ba, saboda keɓaɓɓe ne saboda Yahweh. Dole ka lura da shi ta wannan hanya.33Dukkan wanda ya yi turare irin sa, ko ya shafa wa wani shi, za a datse shi daga cikin mutanensa."'
34Yahweh yace da Musa, "Ka ɗauki kayan yaji - wato su-stakte da onika da galbanum-kayan yaji masu ƙanshi tare da lubban tsantsa, ka auna su dai-dai wa daida.35Ka yi su kamar turaren yadda maiyin turare ya haɗa, gyararre da gishiri, mai tsafta keɓaɓɓe.36Ka yi masa haɗi mai kyau ka niƙa. Ka ɗiba cikinsa ka sa a shaida, wanda yake a cikin rumfa ta taruwa, inda zan sadu da kai. Ka ɗauke shi da tsarki sosai a gare ni.
37Wannan turaren da zaka yi, ba zaka yi wani irin sa domin kanka ba. Zai zama mai tsarki sosai a gare ka.38Dukkan wanda ya yi turare irin sa ya yi anfani da shi za a datse shi daga cikin mutanensa."

31

1Sai Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,2"Duba, na kira sunan Bezalel ɗan Uri ɗan Hour, daga kabilar Yahuda.

3Na kuma cika Bezalel da Ruhuna, ya ba shi hikima, basira da ilimi, da dukkan kayayyakin ayyukan hannuwa,4don ya yi fasalin abubuwa da aikin zinariya da azurfa da tagulla;5ya kuma yanka da jera duwatsu da sassaƙa itace -- ya yi kowanne irin aikin fasahar hannu.
6Tare da shi, na zaɓi Oholiyab ɗan Ahisamak, daga kabilar Dan. Na sa fasaha a zukatan dukkan masu hikima don su yi dukkan abin dana umarce ka. Wannan ya haɗa da7rumfar taruwa, da akwatin shaida, da abin tuba da yake kan akwatin, da dukkan kayayyakin dake cikin rumfar-8teburi da kayayyakinsa da tsantsa alkuki tare da dukkan kayayyakinsa, da turaren bagadi da9bagadin hadayar konawa da dukkan kayayyakinsa da babbar kwatarniya tare da mazaunin ta.
10Wannan ya haɗa da ƙyakkyawan - sakakkun riguna - tsarkakkun tufafin domin Haruna firist da 'ya'yansa maza, na ajiye su domin na, saboda su yi aikin firistoci.11Wannan ya haɗa da man shafewa da turare domin wuri mai tsarki. Waɗannan masu sana'ar hannu dole ne su yi dukkan waɗannan abubuwa kamar yadda na umarce ku."
12Sai Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,13"Faɗa wa Isra'ilawa: 'Dole ku kiyaye ranakun Asabar na Yahweh, domin dukkan waɗannan za su zama alama tsakanin shi da ku acikin dukkan zuriyar mutanenku har abada don ku sani shi ne Yahweh, wanda ya keɓe ku domin kansa.14Saboda haka dole ku kiyaye Asabar, don ku lura da ita da tsarki, ya keɓe ta dominsa. Duk wanda ya tozarta ta babu shakka kashe shi za a yi. Duk wanda ya yi aiki ranar Asabar, wannan mutum babu shakka za a yanke shi daga mutanensa.15Ku yi aiki a kwana shida kaɗai, amma a rana ta bakwai ranar Asabar ce ku huta, tsattsarka ga Yahweh. Duk wanda ya yi aiki a ranar Asabar babu shakka za a kashe shi.
16Saboda haka Isra'ilawa dole su kiyaye Asabar. Dole su kiyaye ta a dukkan tsararrakin mutanensu za ta zama dawwamammar doka.17Asabar za ta zama a kullum alama tsakanin Yahweh da Isra'ilawa, gama a cikin kwana shida Yahweh ya yi sama da ƙasa, a rana ta bakwai kuma ya huta da yin komai.'"
18Sa'ad da Allah ya gama magana da Musa a kan Tsaunin Sinai, ya ba shi alluna biyu na alƙawarin ka'idodi, da aka yi da dutse, rubutattu da hannunsa.

32

1Da mutanen suka ga Musa ya yi jinkirin dawowa daga tsaunin, sai suka taru kewaye da Haruna, suka ce masa, "Zo, ka yi mana gunki da zai wuce gaban mu. Domin wannan Musa, mutum wanda ya fito damu daga ƙasar Masar, bamu san abin da ya faru da shi ba."2Sai Haruna yace masu, "Ku tuttuɓe zobbanku na zinariya waɗanda suke a kunnuwan matayenku da kunnuwan 'ya'yanku maza da mata ku kawo su gare ni."

3Dukkan jama'a suka tuttuɓe zobban da suke a kunnuwansu, suka kawo su wurin Haruna.4Ya karɓi zinariyar daga wurinsu, ya narkar da su, ya mai da shi siffa ta ɗan maraki. Sai mutanen suka ce, "Isra'ila, wannan shi ne allahnku wanda ya fito da ku daga ƙasar Masar."
5Sa'ad da Haruna ya ga wannan, ya gina bagadi a gaban siffar marakin ya yi shela; ya ce, "Gobe akwai bikin girmama Yahweh."6Mutane suka tashi da asussuba kashegari suka miƙa hadayu na konawa da bayarwar zumunta. Sai suka zauna suka ci suka sha, sa'an nan suka tashi suna shagalin shashanci.
7Sai Yahweh ya yi magana da Musa, "Tafi da sauri, gama mutanenka, waɗanda ka fito da su daga ƙasar Masar, sun ƙazantar da kansu.8Sun yi saurin ƙyale hanyar dana umarce su. Sun yi wa kansu ɗan maraki suna yi masa sujada, suna miƙa masa hadaya. Sun kuma ce, Isra'ila, wannan shi ne allahnka wanda ya fito daku daga ƙasar Masar.'"
9Sai Yahweh ya faɗa wa Musa, "Na ga wannan jama'ar. Duba, mutanen nan suna da taurinkai.10Yanzu dai, kada ka yi ƙoƙarin hana ni. Fushina ya yi ƙuna a kansu, saboda haka zan hallaka su. Sai in yi wata babbar al'umma daga gare ka."11Amma Musa ya yi ƙoƙarin roƙon Yahweh Allahnsa. Ya ce, "Yahweh, me ya sa ka husata da mutanenka, waɗanda ka fito da su daga ƙasar Masar da ƙarfin iko da babban hannu?
12Me ya sa za ka sa Masarawa su ce, 'Ya sa su sun fito da mugun nufi, don ya kashe su cikin duwatsu ya kuma shafe su daga fuskar duniya?' Ka janye daga zafin fushinka, ka ji tausayi daga wannan hukunci a kan mutanenka.13Ka tuna da Ibrahim da Ishaku da Isra'ila, bayinka, waɗanda kai da kanka ka rantse ka ce, 'Zan riɓaɓɓanya zuriyarka kamar taurarin sammai, in kuma ba zuriyarku dukkan wannan ƙasa wanda na yi maganar ta. Za ku gaje ta har abada.'"14Sai Yahweh ya huce ya janye daga hukuncinsa da ya ce zai sa masifa a kan mutanensa.
15Musa kuwa ya juyo ya sauko daga kan tsaunin, yana ɗauke da allunan biyu na shaidar ka'idodi a hannunsa. Allunan rubutattu ne ciki da waje, gaba da baya.16Allunan kuma aikin Allah ne, rubutun kuwa na Allah ne, da ya zana a kan allunan.
17Sa'ad da Yoshuwa ya ji hayaniyar mutane kamar suna ihu, ya cewa Musa, "Akwai hargowar yaƙi a zangon."18Amma Musa yace, "Ai ba amon nasara ba ce, ba kuma amon mutanen da aka ci nasara a kansu bane, amma hayaniyar waƙa nake ji."
19Sa'ad da Musa ya kusato zangon ya ga siffar ɗan maraki mutane kuma na ta rawa. Ya harzuka da haushi. Ya watsar da allunan da suke hannunwansa suka farfashe a gindin tsaunin.20Ya ɗauki siffar ɗan marakin da mutane suka yi, ya kone ta, ya nike ta zama gari, ya barbada a cikin ruwa. Sa'an nan ya sa mutanen Isra'ila su sha ta.
21Musa ya cewa Haruna, "Me waɗannan mutane suka yi maka, da ka jawo babban zunubi a kansu?"22Haruna yace, "Kada ka bar fushinka ya yi ƙuna, ya shugabana. Ka san waɗannan mutane, yadda suke a kan yin mugunta.23Sun ce da ni, 'Ka yi mana allah wanda zai wuce gabanmu. Gama Musa, mutumin da ya fito da mu daga ƙasar Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba.'24Ni kuwa nace da su, 'Duk wanda yake da zinariya, bari ya tuɓe ya kawo ta.' Suka ba ni zinariya ni kuwa na zuba su cikin wuta, daganan wannan maraki ya fito."
25Musa ya ga mutanen sun gagara (gama Haruna ya barsu sun fi karfin a shawo kansu, suna sa abokan gãbarsu su yi masu ba'a).26Sai Musa ya tsaya a ƙofar zango ya ce, "Duk wanda yake wajen Yahweh, ya zo wurina." Dukkan Lebiyawa suka tattaru a wurinsa.27Ya ce masu, "Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: 'Bari kowanne mutum ya rataya takobinsa a gefensa da bayansa ya tafi ya dawo daga ƙofa zuwa ƙofa cikin zango kowa kuma ya kashe ɗan'uwansa, ya kashe abokinsa da kuma makwabcinsa.'"
28Lebiyawa kuwa suka yi yadda Musa ya umarta. A ranan nan mutane dubu uku suka mutu.29Musa ya cewa Lebiyawa, "Ku bada kanku cikin aikin Yahweh yau, gama kowannenku ya yi gãba da ɗansa da ɗan'uwansa, saboda Yahweh ya iya baku albarka yau."
30Washegari Musa ya cewa mutanen, "Kun aikata babban zunubi. Yanzu zan tafi wurin Yahweh. Watakila zan iya yin kafara domin zunubanku."31Musa ya koma wurin Yahweh yace, "Aiya, waɗannan mutane sun aikata zunubi mai girma, sun yi wa kansu gunkin zinariya.32Amma yanzu, idan ka yarda ka gafarta zunubansu; amma idan ba za ka yi ba, ka shafe sunana daga cikin litafin daka rubuta."
33Yahweh ya cewa Musa, "Duk wanda ya yi mani zunubi, shi ne kuwa zan shafe sunansa daga cikin littafina.34Saboda haka yanzu ka tafi, ka bida mutanen zuwa wurin da zan faɗa maka. Duba, mala'ikana zai wuce gabanka. Amma a ranar da zan hukuntasu, zan hukuntasu saboda zunubinsu."35Yahweh ya aika da annoba ga mutanen domin sun yi ɗan marakin, da Haruna ya yi.

33

1Sai Yahweh ya yi magana da Musa. "Tafi, daganan, kai da mutane waɗanda ka fito da su daga ƙasar Masar. Tafi zuwa ƙasar dana rantse wa Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, da na ce, 'Zan bada ita ga zuriyarku.'2Zan kuma aiki mala'ika a gabanka, zan kori Kan'aniyawa, da Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Hibiyawa, da Yebusiyawa.3Tafi zuwa ƙasar, wanda ke fitar da madara da zuma, amma ba zan tafi tare da ku ba, gama ku mutane ne masu taurinkai. Don zan iya hallaka ku a hanya."

4Sa'ad da mutane suka ji waɗannan maganganu masu tada hankali, suka damu suka yi nadama babu wanda ya sa kayan ado.5Yahweh yace da Musa, "Faɗa wa Isra'ilawa, 'Ku mutane ne masu taurin kai. Idan na tafi tare daku ɗan lokaci kaɗan, zan hallaka ku. Domin haka yanzu, ku tuɓe kayan adonku don zan iya yin abin dana shawarta da ku.'"6Saboda haka Isra'ilawa ba su sa kayan ado daga Tsaunin Horeb ba har zuwa gaba.
7Musa ya ɗauki rumfar ya kafa ta a bayan zango. Ya kuma kira ta da suna rumfar taro. Duk wanda yake neman Yahweh da kowanne abu sai ya tafi rumfar taruwa, wajen zangon.8Duk sa'ad da Musa ya fita daga zango, dukkan mutane nan za su tashi tsaye a ƙofar rumfarsu su kalli Musa har sai ya shiga ciki.9Duk sa'ad da Musa ya shiga rumfa, al'amudin girgije yakan sauko ya tsaya bisa ƙofar rumfar, Yahweh kuwa ya yi magana da Musa.
10Duk lokacin da dukkan mutane suka ga al'amudin girgijen nan na tsaye a kofar rumfar, sai su tashi su yi sujada, kowanne mutum a ƙofar rumfarsa.11Yahweh kuwa zai yi magana da Musa fuska da fuska, kamar mutum ne ke magana da abokinsa. Musa kuwa zai koma cikin zango, amma baransa Yoshuwa ɗan Num, saurayin mutum, zai tsaya a rumfar.
12Musa ya cewa Yahweh, "Duba, ka faɗa mani cewa, 'Ka fita da mutanen nan a tafiyarsu,' amma ba ka bar ni in san wanda za ka aika tare da ni ba. Ka ce, 'Na san ka ta wurin sunanka, ka kuma sami tagomashi a idanuwana.'13Yanzu idan har na sami tagomashi a idanunka, ka nuna mani hanyoyinka domin in san ka in kuma cigaba da samun tagomashi a idanunka. Ka tuna wannan al'umma mutanenka ne."
14Yahweh kuwa ya amsa, "Zan tafi tare da kai, zan kuma baka hutawa."15Musa yace da shi, "Idan ba za ka tafi tare da mu ba, kada ma ka ɗaga mu daga nan.16Domin in ba ta haka ba, ƙaƙa za a sani na sami tagomashi a idanunka, ni da mutanenka? Ba sai ka tafi tare da mu ba, domin ni da mutanenka a ga bambanci daga dukkan sauran jama'ar da suke fuskar duniya?"
17Yahweh ya cewa Musa, "Zan kuma yi wannan abu yadda ka roƙa, gama ka sami tagomashi a idanuna, na kuma san ka da suna."18Musa kuwa ya ce, "Idan ka yarda ka nuna mani darajarka."
19Yahweh yace, "Zan sa dukkan ɗaukakata ta wuce a gabanka, zan kuma yi alheri ga wanda na yi wa alheri, zan kuma nuna jinkai ga wanda na yi wa jinkai.20Amma Yahweh yace, "Ba za ka iya ganin fuskata ba, gama babu wanda zai gan ni ya rayu."
21Yahweh yace, "Duba, a nan ga wani wuri kusa da ni; inda za ka tsaya bisa wannan dutsen.22Sa'ad da ɗaukakata take wucewa, zan sa ka a tsaguwar dutsen, in rufe ka da hunnuna har sai na wuce.23Sa'an nan zan ɗauke hannuna, za ka ga bayana, amma ba za ka ga fuskata ba."

34

1Yahweh ya cewa Musa, "Ka datse allunan biyu na dutse kamar allunan farkon. Zan rubuta kalmomin a kan waɗannan allunan yadda suke cikin allunan farkon, allunan da ka farfasa.2Ka yi shiri da safe, ka zo kan Tsaunin Sinai, ka gabatar da kanka gare ni a kan saman tsaunin.

3Babu wani da zai zo tare da kai. Kada ka bari a ga wani a ko'ina a kan tsaunin. Kada a bar garken tumaki ko awaki, su yi kiwo a gaban tsaunin."4Sai Musa ya sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, ya tashi da sassafe, ya hau kan Tsaunin Sinai, kamar yadda Yahweh ya umarce shi. Musa ya rike allunan na dutse a hannunsa.
5Yahweh kuwa ya sauko cikin girgije ya tsaya tare da Musa a can, ya yi shelar sunansa "Yahweh." Yahweh ya wuce ta gabansa ya yi shelar Yahweh,6Yahweh, Allah mai jinkai, mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan kauna, mai gaskiya,7mai kiyaye alƙawarin aminci ga dubban tsarraraki, mai gafarta mugunta da laifuffuka da zunubai. Gama ba zai kuɓutar da mai mugunta ba. Zai hukunta 'ya'ya da jikoki har tsara ta uku da tsara ta hudu saboda zunubin iyaye."
8Musa ya hanzarta ya sukunyar da kansa ƙasa ya yi sujada.9Sai ya ce, "Idan na sami tagomashi a idanunka, Ubangijina, ina roƙonka ka tafi tare da mu, gama waɗannan mutanen suna da taurinkai. Gafarta mana laifinmu da zunubinmu, ka ɗauke mu abin gãdonka."
10Yahweh yace, "Duba na kusan yin alƙawari. Gaban dukkan mutanenka, zan aikata al'ajabi irin wanda ba a taba yi ba a cikin dukkan duniya ko a cikin wata al'umma. Dukkan mutanen dake cikinku za su ga aikina, gama abin bantsoro nake yi da ku.11Ku kiyaye abin dana umarce ku yau. Na kusa korar maku Amoriyawa da Kan'aniyawa da Hittiyawa da Ferizziyawa da Hibiyawa da Yebusiyawa.
12Ku lura da kada ku yi alƙawari tare da mazaunan ƙasar inda za ku tafi, ko su zama tarko a cikinku.13A maimakon haka dole ku rurrushe bagadansu, ku farfashe al'amudansu na dutse, ku sassare gumakansu.14Gama ba za ku yi wa wani allah sujada ba, domin Yahweh, wanda sunansa mai Kishi, Allah mai kishi ne.
15Saboda haka kuyi hankali kada ku ƙulla alƙawari tare da mazaunan ƙasar, domin sun karuwantar da kansu ga allolinsu, kuma suka miƙa hadaya ga allolinsu. Sa'an nan wani daga cikinsu zai gayyace ku kuma za ku ci daga cikin hadayarsa,16sa'an nan kuma za ku ɗauka daga cikin 'ya'yansa mata domin "ya'yanku maza, 'ya'yansa mata za su karuwantar da kansu ga allolinsu, za su kuma sanya 'ya'yanku maza su karuwantar da kansu ga allolinsu.17Kada ku yi wa kanku alloli na zuɓi.
18Dole ku kiyaye Bukin Abinci Marar Gami. Kamar yadda na umarce ku, ba za ku ci gurasa marar gami ba har kwana bakwai a kan lokacin da aka sa a watan Abib, gama a watan Abib kuka fito daga cikin Masar.
19Dukkan ɗan farin nawa ne, koda ɗan farin mutum ne ko na dabba, dukkan 'ya'yan farin dabbobinku, wato na saniya da tunkiya.20Za ku fanshi ɗan farin jaki da ɗan rago, amma idan kuwa ba za ku fanshi ɗan rago ba, sai ku karya wuyansa. Dole za ku fanshi kowanne ɗan fari 'ya'ya mazanku. Kada wani ya zo gabana da hannu wofi.
21Za ku iya yin aiki kwana shida, amma a kan rana ta bakwai dole sai ku huta. Koda lokacin noma ne da lokacin girbi dole ku huta.22Dole ku kuma kiyaye Bukin Makwanni tare da amfanin fari na alkama da kuka cire, kuma dole ku kiyaye bukin Tattarawa a karshen shekara.
23Sau uku a cikin shekara dukkan mazajenku dole su hallara a gaban Ubangiji Yahweh, Allah na Isra'ila.24Gama zan kori al'ummai daga gabanku, in faɗaɗa kan iyakokinku. Babu wani da zai yi ƙyashin ƙasarku kamar na su a lokatan da kuka tafi ku bayyana a gaban Yahweh Allahnku sau uku a shekara.
25Ba za ku miƙa jinin hadayata tare da wani abu mai gami ba, ko wani nama daga hadaya ta Bikin Ƙetarewa wanda za a bari har zuwa safiya.26Dole ku kawo mai kyau ta nunar farin amfanin gonakinku a cikin gidana. Kada ku yarda ku dafa ɗan akuya da yake shan nonon uwarsa."
27Yahweh ya cewa Musa, "Rubuta waɗannan maganganu, gama dai-dai suke da maganganu alƙawarin da ni na ɗauka da Isra'ila."28Musa kuwa yana tare da Yahweh yini arba'in da dare arba'in; bai ci kowanne abinci ba ko ya sha ruwa ba. Ya rubuta maganganun alƙawarin a kan allunan, Dokoki Goma.
29Lokacin da Musa ya sauko daga Tsaunin Sinai tare da alluna biyu na alƙawarin a hannunsa, bai sani ba, fuskarsa tana annuri lokacin da yake magana tare da Allah.30Sa'ad da Haruna da Isra'ilawa suka ga fatar fuskar Musa tana annuri, sai suka ji tsoro suka ka sa zuwa kusa da shi.31Amma Musa ya yi magana da Haruna da dukkan shugabannin jama'a su zo gare shi. Musa kuwa ya yi magana da su.
32Bayan wannan, dukkan mutanen Isra'ila suka zo wurin Musa, ya faɗa masu dukkan umarnin da Yahweh ya ba shi a Tsaunin Sinai.33Sa'ad da Musa ya gama magana tare da su, sai ya sa mayafi ya rufe fuskarsa.
34Duk lokacin da Musa ya je gaban Yahweh ya yi magana da shi, sai ya cire lullubin, har sai ya fito. Idan ya fito, zai faɗawa Isra'ilawa abin da aka umarce shi ya faɗa.35Da Isra'ilawa suka ga fuskar Musa tana haske, sai ya lullube fuskarsa kuma har sai ya koma don ya yi magana tare da Yahweh.

35

1Musa ya tattara dukkan jama'ar Isra'ilawa ya ce da su, "Waɗannan su ne abubuwan da Yahweh ya umarce ku da yi.2A rana ta shida za ku yi aiki, amma dominku, rana ta bakwai za ku maida ita rana mai tsarki, ranar Asabar ce ku huta sosai, mai tsarki ta Yahweh. Duk wanda ya yi wani aiki a ranar lalai zai mutu.3Ba za a hura wuta a kowanne gida ba a ranar Asabar."

4Musa kuwa ya yi magana da dukkan jama'ar Isra'ilawa, cewa, "Wannan shine abin da Yahweh ya umarta.5Ku karɓi baiko domin Yahweh, dukkan ku wanda ya yi niyya a zuciya. Ku kawo baikon ga Yahweh--zinariya da azurfa da tagulla6da zane shudi da shunayya da mulufi da lallausan zaren lilin da gashin awaki da7fatun raguna da aka rina suka zama ja da fatun awaki da itacen kirya8da man fitila da kayan yaji domin man keɓewa da turaren konawa9da duwatsu masu tamani da duwatsun da za a mammanne a alkyabba da kyallen makalawa a kirji."
10Kowanne mutum da yake da fasaha a cikinku ya zo ya yi wani abu ga Yahweh ya umarta-11rumfar sujada da rumfarta, da murfinta da maratayai da katakanta da sandunanta da dirkokinta da kwasfanta12da kuma akwati da sandunansa, da marfin kafara, da labule domin rufewa.
13Suka kawo tebur da sandunansa da dukkan kayayyakinsa, kuma da gurasa ta kasancewa,14da alkuki don haske, tare da kayayyakinsa da fitilunansa da man fitilu15da bagadin turaren ƙonawa da sandunansa da man keɓewa mai ƙanshi da turaren ƙonawa da labulen ƙofar rumfa ta sujada16bagadin baye-baye na ƙonawa da ragarsa ta tagulla da sandunansa da kuma kayayyakinsa da babban daro da gammonsa.
17Suka kawo labulen domin harabar tare da dirkokinsa da kwasfansu da labulen don ƙofar harabar18da kuma turakun maratayin rumfar da turakun farfajiyar tare da igiyoyinsu.19Suka kawo saƙaƙƙun tufafi na yin aiki a wuri mai tsarki da tsarkakkun tufafi domin Haruna firist da tufafin 'ya'yansa maza na aikin firistoci."
20Sai dukkan kabilun Isra'ila suka tashi daga gaban Musa.21Kowanne zuciyarsa ta kada shi da wanda ruhunsa ya iza shi ya yi niyya kawo wa Yahweh baiko domin yin rumfa ta sujada, da dai dukkan ayyuka cikinta da kuma tsarkakkun tufafi.22Suka zo, maza da mata, dukkan waɗanda suke da niyya a zuciya. Suka kawo kayayyakin ƙawanya wato su 'yan kunne da ƙawane da mundaye da kayayyakin dukkan zinariya iri iri. Dukkansu suka bada baikon zinariya kamar su baye-bayen kaɗawa ga Yahweh.
23Kowanne mutum da yake da shuɗi ko shunayya ko mulufi ko lallausan lilin ko gashin awaki ko fatun raguna da aka rina suka zama ja ko fatun awaki ya kawo su.24Kowanne ne wanda ya iya yin baikon azurfa da tagulla ga Yahweh, da kowanne wanda aka same shi yana da itacen ƙirya wanda zai zama da amfani a cikin aikin ya kawo shi.
25Kowace mace mai fasaha da ta kaɗa zare da hannuwanta ta kawo zaren da ta kaɗa na shuɗi da shunayya da mulufi da lallausan lilin.26Dukkan mataye waɗanda zukatansu suka iza su, suka kaɗa zare da gashin awaki.
27Shugabanai suka kawo duwatsu masu daraja da za a jera a kan alkyabba da kyallen makalawa a kirji;28suka kuma kawo kayan yaji da mai don fitilu da mai domin keɓewa da turare mai kanshi don ƙonawa.29Sai Isra'ilawa suka kawo bayarwar yardar rai ga Yahweh; kowanne mutum da mace waɗanda zuciyarsu ta iza su da niyya suka kawo kayayyaki domin dukkan aikin da Yahweh ya umarta ta wurin Musa aka yi shi.
30Musa ya cewa Isra'ilawa, "Duba Yahweh ya kira Bezalel ɗan Uri ɗan Hur da sunansa, daga kabilar Yahuda.31Ya cika Bezalel da Ruhunsa, domin ya ba shi hikima da basira da sani da ilimi, don ya iya dukkan kowanne irin aiki,32ya ƙirƙiro zane-zane da aikin zinariya da azurfa da tagulla33da kuma wajen sassaƙar duwatsu na jerawa da sassaƙar itace-ya yi dukkan kowanne irin zane-zane na gwaninta.
34Ya sa masa a cikin zuciyarsa ya koyar, shi da Oholiyab dan Ahisamak, daga kabilar Dan.35Ya cika su da fasaha ta yin kowanne irin aiki, da aiki kamar na sassaƙa dana zane-zane dana yin ɗinke-ɗinke da shuɗi da shunayya da mulufi da lallausan lilin dana yin saƙa. Sun iya yin kowanne irin aiki da yin zane-zane.

36

1Bezalel da Oholiyab da kowanne mutum mai fasaha waɗanda Yahweh ya ba su fasaha da basira na sanin yin kowanne irin aikin wuri mai tsarki bisa ga dukkan yadda Yahweh ya umarta."

2Musa ya kirawo Bezalel da Oholiyab da kowanne mutum mai fasaha wanda Yahweh ya ba shi fasaha a zuciya da dai dukkan wanda zuciyarsa ta iza shi ya zo ya yi aikin.3Su kuwa sun karɓa daga wurin Musa dukkan baye-bayen da Isra'ilawa suka kawo domin aikin wuri mai tsarki. Duk da haka mutane suna kawo baye-bayen yardar ransu kowacce safiya ga Musa.4Sai dukkan mutane masu fasaha suke yin aiki a wuri mai tsarki suka zo daga aikin da suke ta yi.
5Masu aikin hannu suka faɗa wa Musa, "Mutane suna ta kawo wa fiye da abin da ake buƙata domin aikin da Yahweh ya umarta a yi."6Sai Musa ya umarce su kada wani a cikin zango ya sake kawo baiko don aikin wuri mai tsarki.7Saboda haka mutane suka dena bada waɗannan kyaututtuka. Sun bada fiye da kayayyakin da ake buƙata domin yin dukkan aikin.
8Sai dukkan gwanayen mutane a cikin ma'aikatan suka yi rumfa da labule goman da aka yi daga lallausan zanen lilin da shudi da shunayya da mulufi da kuma zanen kerubim. Wannan shine aikin Bezalel, mai babbar fasahar sassaƙa.9Tsawon kowanne labule kamu ashirin da takwas, faɗinsa kuma kamu hudu ne. Dukkan labule girmansu ɗaya ne.10Bezalel ya haɗa labule biyar ga kowanne ɗayan, sa'an nan kuma ɗayan labule biyar ya kuma haɗa kowanne da ɗan'uwansa.
11Ya sa maratayai shuɗi a gefen karshen labule na layin, ya sake yin haka har sau biyu.12Ya sake sa hantuna hamsin a karbun labule na fari, haka kuma ya sa na biyun. Saboda haka dukkan maratayan suna daura da juna.13Ya kuma yi maɗauri hamsin na zinariya, ya harhaɗa labulen da juna da maɗauran saboda rumfar sujadar ta zama ɗaya.
14Bezalel ya yi labulai da gashin awaki domin a rufe rumfar; ya yi waɗannan labulai goma sha ɗaya.15Tsawon kowanne labule kamu talatin, faɗinsa kuma kamu huɗu ne. Kowanne ɗaya daga cikin labule goma sha ɗayan girmansu ɗaya ne.16Ya harhaɗa labule biyar wuri ɗaya, labule shida kuma ya harhaɗa su wuri ɗaya da juna.17Sai ya yi hantuna hamsin ya sa a gefe na bisa na labule na farin, haka kuma ya sa maratayai hamsin a gefen sama na labule na biyu.
18Bezalel ya yi hamsin maɗaurai da tagulla waɗanda zai harhaɗa maratayan da su domin rumfar ta zama ɗaya.19Ya yi wa rumfar marufi da fatun raguna da aka rina ja, ya kuma sake yin wani abin rufewa na fata mai kyau ya hau sama da shi.
20Bezalel ya yi katakan rumfar da itacen ƙirya.21Tsawon kowanne katako kamu goma ne, kaurinsa kuwa kamu ɗaya da rabi ne.22Kowanne katako an feƙe bakinsa biyu domin a harhaɗa su tare. Ya yi wannan domin dukkan katakan rumfar.23Ya yi katakan rumfar ne ta wannan hanya: ya kafa katakai ashirin domin gefen kudu.
24Bezalel ya yi kwasfa arba'in da azurfa su shiga ƙarƙashin katakai ashirin. Akwai kuma katako da yana da kwasfa biyu don bakinsa biyu da aka feƙe.25Gama na biyun yana wajen arewa da rumfar, ya kafa katakai ashirin,26kwasfa arba'insu na azurfa. Akwai katako da yake da kwasfa biyu a ƙarƙashin katakon gaba.
27Domin bayan rumfar a gefen yamma, Bezalel ya yi tsaikoki shida.28Ya yi kuma katakai biyu don kusurwar baya ta rumfar.
29Waɗannan katakai an raba su tun daga ƙasa, amma an haɗa su a sama a ƙawanya ta fari. Haka ya yi da su kusurwoyin nan biyu.30Akwai katakai takwas da kwasfansu na azurfa guda goma sha shida dukkansu, kowanne katako yana ƙarƙashin na fari, katakai biyu kuma suna ƙarƙashin kwasfa ta gaba.
31Bezalel ya yi sanduna na itacen ƙirya-sanduna biyar domin katakan gefe ɗaya na rumfar,32sanduna biyar kuwa don katakan ɗaya gefen na rumfar, biyar kuma domin katakan da yake bayan rumfar wajen yamma.33Ya sa sandan da yake a tsakiya ya wuce daga ƙarshe zuwa ƙarshe. Ya dalaye katakan da zinariya.34Ya yi masu ƙawanne na zinariya, don su yi aikin riƙe sarƙafa sandunan, ya kuma dalaye sandunan da zinariya.
35Bezalel ya yi labule da shuɗi, da shunayya da mulufi da lallausan zaren lilin, ya kuma yi wa labulen zanen kerubim na aikin gwaninta.36Ya yi wa labulen dirkoki huɗu da itacen ƙirya, sai ya dalaye su da zinariya. Ya kuma yi masu maratayai da zinariya don dirkokin kwasfa huɗu da azurfa.
37Ya yi wa ƙofar rumfar labule da shuɗi da shunayya da mulufi da lallausan zaren lilin ya yi wa labulen ado sosai.38Ya kuma haɗa labulen da dirkokinsa biyar. Ya dalaye kawunansu da maɗauransu da zinariya. Kwasfansu guda biyar an dalaye su da tagulla.

37

1Bezalel ya yi akwati da itacen ƙirya, tsawonsa kamu biyu da rabi, faɗinsa kamu ɗaya da rabi, tsayinsa kamu ɗaya da rabi.2Ya dalaye shi da zinariya tsantsa ciki da waje, ya kuma yi masa dajiya da zinariya kewaye har sama.3Ya sa ƙawanya huɗu ta zinariya domin kafafunsa huɗu, kawanne biyu a gefensa ɗaya, biyu kuma a ɗaya gefen.

4Ya yi sandunan da itacen ƙirya ya kuma dalaye su da zinariya.5Ya zura sandunan cikin ƙawayun da suke a gefen akwatin don ɗaukarsa.6Ya yi murfin kafara da zinariya tsantsa. Tsawonsa kamu biyu da rabi faɗinsa kuma kamu ɗaya da rabi.
7Bezalel ya ƙera siffofin kerubobin biyu da zinariya domin ƙarshen kafara biyu.8Kerub ɗaya don ƙarshen kafara, ɗaya kerub kuma domin ƙarshen gefen. An yi su kamar guntu ɗaya ne na murfin.9Kerubobin suka buɗe fikafikansu sama, suka inuwanta murfin da fikakansu. Kerubobin suna fuskantar juna, suna kallon tsakiyar murfin kafara.
10Bezalel ya yi tebur da itacen ƙirya. Tsawonsa kamu biyu, faɗinsa kamu ɗaya ne, tsayinsa kamu ɗaya da rabi.11Ya dalaye shi da zinariya tsantsa, ya kuma yi masa dajiya da zinariya tsantsa a kewayan samansa.12Ya yi masa dajiya mai faɗin tafin hannu kewaye da shi, ya kuma yi wata dajiya da zinariya a kewaye da ita.13Ya yi ƙawanye huɗu na zinariya, ya kuma manna kowanne a kursuwoyi huɗu na ƙafafunsa.
14Kowannensu na kusa da dajiyar inda za a zura sanduna na ɗaukar teburin.15Ya yi sanduna da itacen ƙirya, ya kuma dalaye su da zinariya domin ɗaukar teburin.16Ya yi kayan da za a ɗora a kan teburin-kwanonin da cokula da kwanonin tuya da butoci waɗanda za ayi baye-baye da su. Ya yi su da zinariya tsantsa.
17Ya yi alkuki da zinariya tsantsa. Ya yi alkuki a gindinsa da gorar jikinsa, ƙoƙunan da mahaɗansa da furanninsa dukkansu a haɗe aka yi da ita.18Akwai rassa guda shida daga cikin kowanne gefen-rassa uku daga cikin ɗaya gefen, sa'an nan rassa uku na alkukin daga wancan gefen.19Reshe na fari ya yi da ƙoƙuna uku an yi su kamar tohon almond tare da mahaɗai da furanni da kofuna guda uku wanda aka yi kamar almond ya yi fure a kan reshe da mahaɗan furannin. Tana kamar dukkan rassa shidan daga wajen alkuki.
20A bisa alkukinsa, a tsakiyar ƙyauran, akwai kofuna guda huɗu da aka yi su kamar tohon almond da mahaɗai da furanni.21Akwai mahaɗi a ƙarƙashin kowanne reshe biyu biyu-an yi su kamar ɗaya da ita, a ƙarƙashin rassa na biyu biyu-haka nan kuma an yi kamar guda ɗaya a haɗe. Ta wannan hanyar akwai mahaɗi a ƙarƙashin rassa na uku, an yi da maɗauri ɗaya. Haka aka yi don dukkan rassa shida daga cikin alkukin.22Ganyensu da rassan an yi dukka a maɗauri ɗaya, da ƙerarriyar zinariya tsantsa aka yi kome.
23Bezalel ya yi alkuki da fitilunsa bakwai da hantsuka da farantansa da zinariya tsantsa.24Ya yi alkuki da kayayyakinsa tare da talanti ɗaya da zinariya tsantsa.
25Bezalel ya yi bagadin ƙona turare. Ya yi ta da itacen ƙirya. Tsawonsa kamu ɗaya, faɗinsa kamu ɗaya, murabba'i tsayinsa kuma kamu biyu. Ƙahoninsa an yi su kamar ɗaya ne da shi.26Ya dalaye bagadin da zinariya tsantsa-bisansa da gefensa da ƙahoninsa. Ya kuma kewaye shi da dajiya ta zinariya.
27Ya yi masa ƙawanne biyu wanda za a haɗa su da ita a ƙarƙashin dajiya daura da juna. Kowannen su yana riƙe da sandunan da za a ɗauki bagadin.28Ya kuma yi sanduna na itacen ƙirya, ya kuma dalayesu da zinariya.29Ya yi tsattsarkan mai na keɓewa da kuma tsantsa turare mai ƙanshi yadda mai yin turare ya kan yi.

38

1Bezalel ya yi bagadin ƙona baye-baye da itacen ƙirya. Tsawonsa kamu biyar faɗinsa kamu biyar - murabba'i ne nan - tsayinsa kuwa kamu uku ne.2Ya yi masa zankaye a kusurwoyinsa huɗu siffar kamar ƙahonnin takarkari. An yi ƙahonnin su haɗe tare da bagadin, ya dalaye shi da tagulla.3Ya yi dukkan kayayyakin domin bagadin-tukwane da cokula da daruna da cokula masu yatsotsi da farantan wuta. Ya kuma yi dukkan kayayyakin da tagulla.

4Ya yi raga domin bagadin, an yi aikin ne da tagulla aka sa a ƙarƙashin kanta, yasa ta daga ƙasa zuwa sama.5Ya sa ƙawanyoyi huɗu domin kusurwoyi huɗu na ragar tagulla don zura sandunan.
6Bezalel ya yi sanduna da itacen kirya ya kuma dalaye su da tagulla.7Sai ya zura sandunan cikin ƙawanne na gefen bagadin, don ɗaukar shi. Ya yi bagadin da itace sa'an nan ya raba cikinsa.
8Bezalel ya yi daron wanka da tagulla da gammonsa na tagulla. Ya yi gammuna daga madubai na mata masu yin aiki a ƙofar rumfar taro.
9Ya kuma yi haraba. Ya yi labulenta na gefen kudun harabar da lallausan zaren lilin, tsawonsu kamu ɗari ne.10Labulai suna da dirkokinsu ashirin, tare da tagulla a ƙarƙashin kwasfan ashirin. Akwai maratayan dirkoki, da maɗaurai da aka yi da azurfa.
11Kamar yadda yake gefen arewa, akwai labule kamu ɗari da sanduna masu kamu ashirin na tagulla, maɗauran sanduna ƙarafuna na azurfa.12Labule na gefen yamma kamu hamsin ne, dirkokinsa kuwa guda goma ne. Maɗaurai da dirkokin ƙarafuna na azurfa ne.
13Tsawon harabar kamu hamsin ne wajen gabas.14Labulai na gefe ɗaya na ƙofar kamu goma sha biyar ne. Suna da dirkoki guda uku tare da kwasfan dirkoki uku.15A gefen ƙofar farfajiyar akwai labule masu tsawo kamu goma sha biyar da dirkoki uku da kuma kwasfan uku.16Dukkan labulai da suke kewaye da harabar an yi su da lallausan zaren lilin.
17An yi kwasfan dirkoki da tagulla. Maratayan dirkoki da maɗauransu an yi su ne da azufa. Dukkan dirkokin farfajiyoyin an dalaye su da azurfa, kuma marufan dirkokin suma an yi su da azurfa. Dukkan harabar dirkokan an dalaye su da azurfa.18Labulan ƙofar harabar kamu ashirin tsayinsa. Labulen an yi su da shudi da na shunayya da na mulufi da na lallausan zaren lilin.19Tsawonsa kamu ashirin, tsayinsa kamu biyar dai-dai da labulen haraba. An yi dirkokin labulen guda huɗu da kwasfan dirkoki na azurfa. An dalaye kawunansu da maɗauransu da azurfa.20Dukkan turakun rumfa da harabar an yi su da tagulla,
21Wannan shi ne lissafin abubuwan da aka yi na rumfa, rumfar alƙawarin ka'idodi, kamar yadda aka yi bisa ga yadda Musa ya yi umarni. Wannan aikin Lebiyawa ne a ƙarƙashin jagorancin Itamar ɗan Haruna firist.22Bezalel ɗan Uri ɗan Hur daga kabilar Yahuda, an yi dukkan abin da Yahweh ya umarci Musa.23Oholiyab ɗan Ahisamak daga kabilar Dan, wanda ya yi aiki tare da Bezalel gwani ne, cikakken ma'aikacin zane-zane da ɗinki na shuɗi, da na shunayya da na mulufi da na lallausan zaren lilin.
24Dukkan zinariya da aka yi aikace-aikacen da ita don wannan aiki, a cikin dukka aikin wanda ya haɗa da wuri mai tsarki - zinariya daga baikon bankwana - talanti ashirin da tara ne da awo 730 bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi.25Azurfar da aka samu ta wurin taron mutane awonsa talanti ɗari ne da awo 1,775, bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi,26ko kowanne mutum da aka ƙidaya ya bada rabin awo. Wannan adadin abin da aka samu bisa kowanne mutum wanda aka ƙidaya ta ƙasa, waɗanda sun kai 603,550 daga shekara ashirin zuwa gaba manya da tsoffafi na dukkan maza.
27An yi amfani da azurfa talanti ɗari domin yin kwasfa don wuri mai tsarki da labule-an yi kwasfa ɗari da talanti ɗaya don kowanne kwasfa.28Sauran 1,775 na awon azurfa, Bezalel yayi maratayan dirkokin, ya dalaye saman maratayan dirkoki ya kuma yi da ƙarafuna dominsu.29Tagulla daga abin da aka bayar kuwa talati saba'in da awo 2,400.
30Tare da wannan ya yi kwasfa domin ƙofar rumfar taruwa, da tagullar bagadi, da tagulla aka yi ragarsa, da dukkan kayayyakin bagadin,31Kwasfa domin harabar, da kwasfa don ƙofar harabar, da dukkan turakun don rumfar sujada da na dukkan turakun harabar.

39

1Tare da shuɗi da shunayya da mulufi, suka ɗinka tufafi masu kyau domin aiki a wuri mai tsarki. Sun yi wa Haruna tsarkakun tufafi domin wuri mai tsarki, kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.

2Bezalel ya yi falmarar da zinariya, da shuɗi da shunayya da mulufi da lallausan lilin.3Suka buga zinariya falle-falle, suka yanyanka ta zare-zare don su yi aikin saƙa da ita tare da zane na shuɗi da shunayya da mulufi da kuma na lallausan lilin, aikin gwani mai fasaha ne.
4Suka yi aikin kafaɗu domin falmara, sa'an nan suka haɗa su a gefenta biyu na sama.5An yi anfani da ɗamarar falmarar ta saƙa mai kyau; da irin kayan da aka saƙa falmara ne aka saƙa su da zinariya da shuɗi da shunayya da mulufi da zane lallausan lilin, kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.
6Sun gyaggyarta duwatsu masu daraja aka jera su a tsaiko, aka zana sunayen 'ya'yan Isra'ila goma sha biyu.7Bezalel ya sa a kan kafaɗun falmarar don su zama duwatsun tunawa da Isra'ila, kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.
8Ya kuma yi ƙyallen maƙalawa a ƙirji, an yi amfani da gwaninta kamar yadda aka yi wa falmarar. Ya yi ta da zinariya da shuɗi da shunayya da mulufi da lallausan lilin.9Tana nan murabba'i. An yi ƙyallen maƙalawa a kirji riɓi biyu. tsawonsa da faɗinsa kamu ɗaya ne.
10Suka sa jeri huɗu na duwatsu masu daraja a bisansa. Jeri na fari aka sa yakutu da tofaz da ganat.11A jeri na biyu aka sa emeral da saffir da lu'u-lu'u.12A jeri na uku aka sa yakinta da idon mage da ametis.13A jeri na huɗu aka sa beril da onis da yasfa. Duwatsun an yi masu maɗauki da zinariya.
14An jera duwatsun bisa sunayen 'ya'yan Isra'ila goma sha biyu, kowanne bisa ga yadda sunansa yake. Suna kamar yadda a kan yi hatimin zoɓe, kowanne suna ya tsaya domin ɗaya daga cikin kabilu goma sha biyu.15A kan kirjin sai suka yi tukakkun sarƙoƙi kamar igiyoyin amara da aikinsa zinariya tsantsa.16Sai suka yi tsaiko biyu na zinariya da ƙawanyu biyu na zinariya, suka sa ƙawanen nan biyu a gefe biyu na ƙyallen maƙalawa a ƙirji.
17Suka kuma zura sarkokin nan biyu na zinariya a kowannen biyu na ƙyallen maƙalawa a ƙirji.18Sai suka maƙala waɗancan a bakin sarƙoƙin biyu. Sa'an nan suka rataya su a kafaɗun falmarar daga gaba.
19Suka yi ƙawanne biyu na zinariya, suka sa su a gefe biyu na kyallen maƙalawa a ƙirji daga ciki kusa da falmaran.20Suka yi waɗansu ƙawanne biyu na zinariya, suka maƙala su kusa a gaban kafaɗu biyu na falmarar kusa da mahaɗin a bisa abin damarar falmarar.
21Sai suka ɗaure ƙawanyun kyallen maƙalawa a ƙirji a ƙawanyun falmarar da shuɗiyar igiya saboda kyallen maƙalawa a ƙirji ya kwanta lif a bisa kan abin damarar. An yi wannan don kada falmarar ya kwance daga ƙirjin falmarar. Wannan ya faru ne kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.
22Bezalel ya saka taguwa ta falmaran da shuɗi ga baki ɗaya, aikin masaƙi ne.23An yi wa taguwar wuya wurin sa kai a tsakiya. An yi wa wayan saƙa saboda kada ta yage.24A ƙasan taguwar, sai suka yi fasalin 'ya'yan rumman da shuɗi, shunayya, da mulufi da lallausan lilin.
25Suka yi kararrawa da zinariya tsantsa, suka sa su a tsakankanin rumman dukka kewaye a ƙasa da bakin igiyar, tsakanin rumman --26an sa ƙararrawa da rumman, ƙararrawar da rumman -- a bakin igiya domin Haruna ya yi hidima a ciki. Wannan bisa ga yadda Yahweh ya umarci Musa.
27Suka saƙa janfofi da lallausan zaren lilin saboda Haruna da 'ya'yansa.28Suka kuma yi rawani da lallausan lilin, da huluna da mukura da lallausan lilin, da mukurai da lallausan lilin.29Sun kuma yi abin damara da lallausan lilin mai launin shuɗi da shunayya da mulufi, an yi mata dinkin ado. Wannan an yi shi kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.
30Suka yi allo tsattsarka da zinariya tsantsa suka zana rubutu a kan ta, irin na hatimi a kanta, "Mai Tsarki ga Yahweh."31Suka ɗaura shi da shuɗiyar igiya a gaban rawanin. Wannan an yi shi yadda Yahweh ya umarci Musa.
32Haka kuma aka yi aikin rumfar sujada, da rumfar taruwa, kuma an gama ta. Mutanen Isra'ila suka yi shi dukka. Suka bi dukkan umarnin da Yahweh ya ba Musa.33Suka kawo wa Musa rumfar sujada - rumfar da dukkan kayayyakinta, maratayanta da katakanta da sandunanta da dirkokinta da kwasfanta34da murfi na jan fatun raguna da na awaki da labulen rufewa35da akwatin alƙawari da sandunansa da murfin kafara.
36Suka kawo tebur da dukkan kayayyakinsa da gurasar ajiyewa37da alkuki na zinariya tsantsa da fitilunsa, tare da kayayyakinsa da mai domin fitilu38da bagadin zinariya da mai na keɓewa da turare mai ƙanshi da labulen ƙofar rumfar sujada39da bagadin tagulla da ragarsa ta tagulla da sandunansa da kayayyakinsa da daro da gammonsa.
40Suka kawo labulen harabar da dirakunta da kwasfanta da labulen ƙofarta da igiyoyinta da turakunta da dukkan kayayyaki don aiki a rumfar sujada da rumfar taruwa.41Suka kawo tufafin ado na aiki a wuri mai tsarki da tsarkakan tufafin domin Haruna firist da tufafin 'ya'yansa maza, domin su yi aiki a matsayin firistoci.
42Mutanen Isra'ila suka yi dukkan wannan aiki yadda Yahweh ya umarci Musa.43Musa ya duba dukkan aikin, duba, sun yi shi dai-dai. Yadda Yahweh ya umarta, ta wannan hanya suka yi shi. Sai Musa ya sa masu albarka.

40

1Sai Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,2"A kan rana ta fari a wata na fari a sabuwar shekara dole ka kafa rumfar sujada, rumfar taruwa.

3Ka sa akwatin alƙawari a cikin ta sa'an nan ka kare akwatin da labule.4Ka shigar da tebur, ka shirya shi yadda ya kamata da kayayyakinsa dai-dai. Ka kuma shigar da alkukin da fitilu a bisansa.
5Ka ajiye bagadi na zinariya na ƙona turare a gaban akwatin alƙawari, sa'an nan ka rataya labulen ƙofar rumfar sujada.6Ka ajiye bagadi na yin baikon ƙonawa a gaban ƙofar rumfar taruwa.7Ka kuma ajiye daro tsakanin rumfar taruwa da bagadin sa'an nan ka zuba ruwa a cikin shi.
8Ka yi harabar ka kewaye ta, sa'an nan ka rataya labulen ƙofar harabar.9Ka ɗauki man keɓewa, ka shafa wa rumfar sujada da kome dake cikinta. Ka tsarkake ta da dukkan kayayyakinta gare ni, ta kuma zama tsarkakkiya.10Ka shafe bagadin domin ƙona hadaya da dukkan kayayyakinsa. Za ka tsarkake bagadin a gare ni, zai zama mafi tsarki gare ni.11Ka shafa wa daron tagulla da mazauninsa man keɓewa a gare ni.
12Ka kawo Haruna da 'ya'yansa maza a ƙofar rumfar taruwa, kuma dole ka yi masu wanka da ruwa.13Sa'an nan ka sa wa Haruna tufafi masu tsarki ka shafa masa man domin ka tsarkake shi ya yi mani aikin firist.
14Ka kawo 'ya'yansa maza, ka kuma sa masu taguwoyi.15Sa'an nan ka shafe su da mai kamar yadda ka shafe mahaifinsu saboda su yi mani aiki a matsayin firistoci. Shafe su da man zai sa su zama firistoci din-din din cikin dukkan tsararrakin mutanen su.16Wannan shine abin da Musa ya yi; ya bi dukkan umarnin da Yahweh ya ba shi. Ya yi dukkan waɗannan abubuwa.
17Sai aka kafa rumfar sujadar a kan rana ta fari a wata na fari a sheka ta biyu.18Musa ya kafa rumfar sujadar, ya kafa kwasfanta, ya jera katakanta, ya sa mata sandunanta, ya kakkafa dirkokinta.19Sa'an nan ya baza shinfiɗa a bisa rumfar sujadar ya sanya rumfa a bisan ta, kamar yadda Yahweh ya umarce shi.20Sai ya ɗauki dokokin alƙawaran ka'idodi ya sa a cikin akwatin. Ya kuma zura sandunan a ƙawanen akwatin, sa'an nan ya sa murfin kafara a bisansa.
21Ya kawo akwatin a cikin rumfar sujada. Sa'an nan ya sa labulen domin kare akwatin alƙawari yadda Yahweh ya umarce shi.22Ya sa teburin cikin rumfar taruwa, a wajen gefen arewa na rumfar sujada, a wajen labulen.23Sai ya jera gurasa a kan teburin a gaban Yahweh, yadda Yahweh ya umarce shi.
24Ya kuma sa alkukin a cikin rumfar taruwa, daura da gaban tebur, a wajen kudu na rumfar sujada.25Ya kunna fitilu a gaban Yahweh, yadda Yahweh ya umarce shi.
26Sai ya sa zinariyar turaren bagadi a cikin rumfar taruwa a gaban labule.27Ya ƙona turare a kanta, yadda Yahweh ya umarce shi.
28Ya sa labule a ƙofar rumfar sujada.29Ya kuwa sa bagadi domin ƙona hadaya a ƙofar rumfar sujada da rumfar taruwa. Ya kuma miƙa hadaya ta ƙonawa da hadayar gari, yadda Yahweh ya umarce shi.30Ya sa daro a tsakanin rumfar taruwa da rumfar sujada, ya kuma sa ruwa a cikinta domin wankewa.
31Musa da Haruna da 'ya'yansa maza su kan wanke hannuwansu da ƙafafuwansu daga daron,32sa'ad da suke shiga cikin rumfar taruwa, da sa'ad da su kan tafi bisa bagadi, yadda Yahweh ya umarci Musa.33Musa kuwa ya yi haraba kewaye da rumfar sujada da bagadin. Ya sa labulen ƙofar harabar. Ta wannan hanya, Musa ya gama aikin.
34Sa'ad da girgije ya rufe rumfar taruwar, sai ɗaukakar Yahweh ta cika rumfar sujada.35Musa kuwa bai iya shiga rumfar taruwa ba gama girgijen yana zaune a bisanta, kuma saboda ɗaukakar Yahweh ta cika rumfar sujadar.
36Duk lokacin da aka ɗauke girgijen daga kan rumfar sujadar, mutanen Isra'ila su kan kama hanya domin tafiya.37Amma idan girgijen bai tashi daga rumfar sujadar ba, mutanen ba za su iya tafiya ba. Za su tsaya har ranar da ya tashi.38Gama girgijen Yahweh yana bisa kan rumfar sujada da rana, haka nan wutarsa ta na bisan shi da dare, wannan ya sa dukkan mutanen Isra'ila suka yi tafiyarsu ko'ina.

Littafin lebitikus

1

1Yahweh ya kira Musa ya yi masa magana daga cikin rumfar taruwa, ya ce,2"Ka yi wa mutanen Isra'ila magana ka gaya masu cewa, 'Sa'ad da waninku ya kawo baiko ga Yahweh, sai ya kawo baikon dabbar daga cikin dabbobinsa, daga garken shanu ko kuma na tumaki.

3Idan baikonsa baiko ne na ƙonawa daga garken shanu, dole ya miƙa namiji marar lahani. Zai miƙa shi a ƙofar rumfar taruwa, domin ya zama karɓaɓɓe a gaban Yahweh.4Zai ɗibiya hannunsa a kan baiko na ƙonawar, sa'an nan za a karɓa daga gare shi a yi masa kaffara domin shi kansa.
5Dole ne ya yanka bijimin a gaban Yahweh. 'ya'yan Haruna maza, firistoci, zasu miƙa jinin su yayyafa shi a kan bagadi wanda ya ke a bakin ƙofar rumfar taruwa.6Sa'an nan dole ya feɗe baikon ƙonawar ya kuma yanyanka shi gunduwa-gunduwa.
7Sa'an nan 'ya'ya maza na Haruna firist zasu kunna wuta a kan bagadin su sa itace domin iza wutar.8'Ya'yan Haruna maza, firistoci zasu jera gunduwa-gunduwar nan, za su sa kan da fari sa'an nan kitsen a jere haka a kan itacen da ke bisa wutar da ke kan bagadi.9Amma kayan cikinsa da ƙafafuwansa dole ya wanke su da ruwa. Sa'an nan firist zai ƙona dukka a kan bagadi a matsayin baiko na ƙonawa. Zai ba da ƙamshi mai daɗi a gare ni; zai zama baikon da aka yi mani da wuta.
10Idan baikonsa domin baiko na ƙonawa ne daga cikin garke, ɗaya daga cikin tumaki ko ɗaya daga cikin awaki, dole ya miƙa namiji marar lahani.11Dole ya yanka shi a arewacin bagadin a gaban Yahweh. 'Ya'yan Haruna maza, firistoci, zasu yayyafa jinin a kowanne gefen bagadin.
12Sa'an nan dole zai yanka shi gunduwa-gunduwa, tare da kansa, da kuma kitsensa, firist zai jera su dai-dai akan itace da ke kan wuta, wadda take kan bagadi, amma kayan ciki da ƙafafun dole ya wanke su da ruwa.13Sa'an nan firist zai miƙa dukka, ya ƙona shi a kan bagadin. baiko na ƙonawa ne, zai bada ƙamshi mai daɗi ga Yahweh; zai zama baikon da aka yi masa da wuta.
14Idan baikonsa ga Yahweh zai zama baiko na ƙonawa na tsuntsaye, to dole ya kawo baikon kurciya ko 'yar tantabara.15Dole firist ya kawo shi ga bagadi, ya murɗe kansa, ya ƙona shi a kan bagadin. Sa'an nan dole a tsiyaye jininsa a gefen bagadin.
16Dole ya cire ƙururunsa da abin da ke cikinsa, ya jefar da shi a gabashin bagadin a gefe, wurin da ake zuba toka.17Dole ya tsaga shi biyu ya buɗe shi daga fukafukansa, amma ba zai raba shi biyu ba. Sa'an nan firist zai ƙona shi a kan bagadin, a kan itacen da ke kan wuta. Zai zama baiko na ƙonawa, kuma zai bada ƙamshi mai daɗi ga Yahweh; zai zama baiko da aka yi masa da wuta.

2

1Sa'ad da wani ya kawo baikon hatsi ga Yahweh, dole ne baikonsa ya zama na gari mai laushi, kuma ya zuba mai a kai ya sa turare a kai.2Zai kai baikon ga 'ya'yan Haruna maza firistoci, a can firist zai ɗibi tafi guda na garin mai laushi tare da mai da turare da ke kansa. Sa'an nan firist zai ƙona baikon a kan bagadin baiko na tunawa kenan. Zai ba da ƙamshi mai daɗi ga Yahweh; zai zama baikon da aka yi masa da wuta.3Duk ragowar baiko na garin hatsi zai zama rabon Haruna da 'ya'yansa maza. Mafi tsarki ne sosai ga Yahweh domin daga baye-baye ne da aka yi wa Yahweh da wuta.

4Sa'ad da kuka miƙa baiko na garin hatsi da babu gami da aka toya a tanda, dole ya zama waina mai laushi da aka yi da lallausar gari cuɗe da mai, ko waina mai tauri da bata da gami, da aka yayyafa mata mai.5Idan baikonku na garin hatsi an toya shi a tandar ƙarfe ne, dole ya zama gari mai laushi marar gami cuɗaɗɗe da mai.
6Za ku yanyanka shi gunduwa-gunduwa a zuba mai a kai. Wannan shi ne baiko na hatsi.7Idan baikonku na garin hatsi an dafa a tukunyar tuya ne, dole a yi shi da gari mai laushi da mai.
8Dole ku kawo baiko na garin hatsi da aka yi su daga waɗannan abubuwa ga Yahweh, za a kuma miƙa su ga firist, wanda zai kawo su wurin bagadi.9Sa'an nan firist zai ɗauki wasu daga baiko na garin hatsin domin ya zama baikon madadi, zai kuma ƙona su a kan bagadin. Zai zama baikon da aka yi da wuta, zai bada ƙamshi mai daɗi ga Yahweh.10Ragowar baikon garin hatsi zai zama na Haruna da 'ya'yansa maza. Abu ne mafi tsarki ga Yahweh daga cikin baye-baye da aka yi ga Yahweh da wuta.
11Kada baiko na garin hatsi da za ku miƙa wa Yahweh ya zama da gami, gama ba za ku ƙona gami ba, ko zuma, a baikon da aka yi da wuta ga Yahweh.12Za ku miƙa su ga Yahweh a madadin baikon nunar fari, amma ba za a yi amfani da su don su bada ƙamshi mai daɗi a kan bagadi ba.13Dole kowanne baye-bayenku na garin hatsi a sa masa ɗanɗanon gishiri. Kada ku fasa sa gishiri na alƙawari na Allahnku a cikin baikonku na garin hatsi. Cikin dukkan baye-bayenku dole ku miƙa gishiri.
14Idan kuka miƙa baikon hatsin nunar fari ga Yahweh, ku miƙa sabon hatsi wanda aka gasa da wuta sa'an nan aka ɓarza,15Sai ku sa mai da turare a kai. Wannan shi ne baiko na garin hatsi.16Sa'an nan firist zai ƙona wasu daga cikin ɓarzajjen hatsin da mai da turare sun zama baiko na madadi. Wannan baiko ne da aka yi da wuta ga Yahweh.

3

1Idan wani ya miƙa hadayarsa wanda baiko ne na zumunta na dabba daga garken shanu, ko namiji ko mace, dole ya miƙa dabbar da ba ta da lahani a gaban Yahweh.2Zai ɗibiya hannusa a kan baikonsa ya yanka ta a ƙofar rumfar taruwa. Sa'an nan 'ya'yan Haruna maza firistoci zasu yayyafa jinin kewaye da bagadin.

3Mutumin zai miƙa hadayar baiko na zumunta da wuta ga Yahweh.‌ Ƙitsen da ya rufe ko kuma da ke haɗe da kayan ciki,4da ƙodoji biyu, da ƙitsen da ya ke kansu a wajen kwiɓi, da na taiɓar hanta, tare da ƙodoji - zai cire dukkan waɗannan.5'Ya'yan Haruna maza zasu ƙona wannan a kan bagadi tare da baiko na ƙonawa, wanda ya ke a kan itacen da ya ke kan wuta. Wannan zai bada ƙamshi mai daɗi ga Yahweh; zai zama baikon da aka yi masa da wuta.
6Idan hadayar mutumin baikon zumunta ne ga Yahweh daga cikin garken tumaki; namiji ko mace, dole ya miƙa hadaya marar lahani.7Idan ya miƙa ɗan rago domin hadaya, to dole ya miƙa shi a gaban Yahweh.8Zai ɗibiya hannunsa a kan hadayar ya yanka shi a gaban rumfar taruwa. Sa'an nan 'ya'yan Haruna maza zasu yayyafa jinin kewaye da bagadin.
9Mutumin zai miƙa hadayar baye-bayen zumunta domin baiko da aka yi da wuta ga Yahweh. Kitsen, dukkan kitse na wajen wutsiya da aka yanke kusa da ƙashin baya, da kitsen da ya rufe kayan ciki da dukkan kitsen da ke kusa da kayan ciki,10da kuma ƙodojin biyu da kitsen da ke tare da su, wanda ke kusa da kwiɓi, da na taiɓar hanta, tare da ƙodoji - zai cire duk waɗannan.11Sa'an nan firist zai ƙona su dukka a kan bagadi ya zama baiko na ƙonawa na abinci ga Yahweh.
12Idan baikon mutumin akuya ce, to zai miƙa ta a gaban Yahweh.13Dole ya ɗibiya hannunsa a kan akuyar ya yanka ta a gaban rumfar taruwa. Sa'an nan 'ya'yan Haruna maza za su yayyafa jinin kewaye da bagadi.14Mutumin zai miƙa hadayarsa da ya yi da wuta ga Yahweh. Zai cire kitsen da ya rufe kayan ciki, da kuma dukkan kitsen da ke kusa da kayan cikin.
15Zai kuma cire ƙodojin biyu da kitsen da ke tare da su, wanda ke wajen kwiɓi, da wajen taiɓar hanta tare da ƙodoji.16Firist zai ƙona dukkan waɗannan a kan bagadi ya zama baiko na ƙonawa na abinci, da zai bada ƙamshi mai daɗi. Duk kitsen ya zama na Yahweh.17Zai zama madawwamin farilla ga dukkan tsararrakin jama'arku a ko'ina da kowanne wuri da kuka maida shi mazauninku, cewa ba za ku ci kitse ba ko jini.'"

4

1Yahweh ya yi wa Musa magana, ya ce,2"Ka gaya wa mutanen Isra'ila, 'Lokacin da wani ya yi zunubi ba da niyyar yin zunubi ba, ya yi wani abu daga cikin abubuwan da Yahweh ya dokata kada a yi, idan ya yi abin da aka hana, ga abin da dole za a yi.3Idan babban firist ne ya yi zunubin har ya kawo laifi a kan jama'a, domin zunubinsa da ya aikata sai ya miƙa ɗan maraƙi marar lahani ga Yahweh baiko don zunubi kenan.

4Dole ya kawo bijimin ƙofar rumfar taruwa a gaban Yahweh, ya ɗibiya hannunsa a kansa, ya yanka shi a gaban Yahweh.5Keɓaɓɓen firist zai ɗiba daga jinin bijimin ya kai rumfar taruwa.
6Firist zai tsom‌a ɗan yatsansa cikin jinin ya yayyafa shi sau bakwai a gaban Yahweh, a gaban labulen wuri mafi tsarki.7Sa'an nan firist zai sa daga jinin a ƙahonnin bagadin na turare mai ƙamshi a gaban Yahweh, wanda ya ke cikin rumfar taruwa, zai kuma zuba dukkan sauran jinin bijimin a gindin bagadi domin baye-baye na ƙonawa, wanda ya ke a ƙofar rumfar taruwa.
8Zai yaɗe dukkan kitsen bijimin baiko don zunubi; kitsen da ya rufe kayan ciki, da dukkan kitsen da ke manne da kayan ciki,9da ƙodojin biyu da kitsen da ke bisansu, wanda ke wajen kwiɓi, da taiɓar hanta, tare da ƙodoji - zai yanke duk wannan.10Zai yanke shi dukka, kamar yadda ya yanke shi daga bijimi na hadayar baye-baye ta salama. Sa'an nan firist zai ƙona waɗannan ɓangare akan bagadin baye-bayen ƙonawa.
11Fatar bijimin da duk sauran naman, da kan da ƙafafunsa da kayan cikinsa da kashinsa,12da dukkan sauran sashen bijimin - zai ɗauki dukkan waɗannan ya kai bayan sansani wurin da aka tsarkake domina, inda ake zuba toka; zasu ƙona waɗannan a bisa itace. Dole su ƙona waɗannan ragowar bijimin inda suke zubar da toka.
13Idan dukkan taron Isra'ila suka yi zunubin da ba na ganganci ba, kuma taron ba su san sun yi zunubi ba idan suka yi wani abu daga cikin abubuwan da Yahweh ya umarta kada su yi, idan sunyi laifin,14sa'annan, yayin da zunubin da suka aikata ya zama sananne, dole taron su miƙa ɗan bijimi baiko wato baiko don zunubi a kuma kawo shi gaban rumfar taruwa.15Dattawan taro zasu ɗibiya hannuwansu a bisa kan bijimin a gaban Yahweh, za a yanka bijimin a gaban Yahweh.
16Keɓaɓɓen firist zai kawo daga jinin bijimin zuwa rumfar taruwa,17firist kuma zai tsoma yatsansa cikin jinin ya yayyafa shi sau bakwai a gaban Yahweh, a gaban labule.
18Zai sa daga jinin a ƙahonnin bagadin da ke gaban Yahweh, wanda ya ke cikin rumfar taruwa, zai kuma zuba jinin dukka a gindin bagadin baye-baye na ƙonawa, wanda ya ke a kofar rumfar taruwa.19Zai ɗebe dukkan ƙitsen daga gare shi ya ƙona a kan bagadi.
20Wannan shi ne abin da zai yi dole da bijimin. Kamar yadda ya yi da bijimin baiko don zunubi, haka kuma zai yi da wannan bijimin, firist kuma zai yi kaffara domin mutane, za a kuma gafarta masu.21Zai ɗauki bijimin ya kai shi bayan zango ya ƙona kamar yadda ya ƙona bijimi na farko. Wannan shi ne baiko don zunubi saboda taron.
22Sa'ad da shugaba ya yi zunubi ba dagangan ba, har ya yi ɗaya daga cikin dukkan abubuwan da Yahweh Allahnsa ya umarta ka da a yi, kuma ya yi laifin,23sai aka sanar da shi a kan zunubin da ya aikata, dole ya kawo hadayarsa ta akuya, bunsuru marar lahani.
24Zai ɗibiya hannunsa a kan bunsurun ya yanka shi inda aka yanka baiko na ƙonawa a gaban Yahweh. Wannan shi ne baiko domin zunubi.25Firist zai tsoma ɗan yatsansa cikin jinin baiko domin zununbi ya sa shi a ƙahonnin bagadin domin baye-baye na ƙonawa, sai ya kuma zuba jinin a gindin bagadin baiko na ƙonawa.
26Zai ƙona dukkan kitsen a kan bagadi, dai-dai kamar na kitsen hadayar baye-baye na salama. Firist zai yi kafara domin shugaban game da zunubinsa, za a kuwa gafarta wa shugaban nan.
27Idan wani talaka ya yi zunubi ba dagangan ba, sai ya yi wani abu daga cikin abubuwan da Yahweh ya umarta kada a yi, idan ya gane laifinsa,28sa'an nan za a bayyana masa zunubinsa, sai ya kawo akuya domin hadayarsa, ta mace marar lahani, domin zunubin da ya aikata.
29Zai ɗibiya hannunsa a kan baiko domin zunubi ya kashe baikon don zunubin a wurin yin baiko na ƙonawa.30Firist zai lakuto daga jinin a yatsansa ya sa a ƙahonnin bagadi domin baye-baye na ƙonawa. Zai zuba dukkan sauran jinin a gindin bagadin.
31Zai yaɗe dukkan kitsen, dai-dai kamar yadda ya yaɗe kitsen da ke kan hadayar baye-baye na salama. Firist zai ƙona su a kan bagadi domin ya bada ƙamshi mai daɗi ga Yahweh. Firist zai yi kaffara domin mutumin, za a kuwa gafarta masa.
32Idan mutumin ya kawo ɗan rago domin hadayarsa ta baiko domin zunubi, zai kawo mace marar lahani.33Zai ɗibiya hannunsa a kan baiko domin zunubi sai kuma a yanka ta saboda baiko domin zunubi a inda aka yanka baiko na ƙonawa.
34Firist zai ɗiba daga jinin baiko domin zunubi a ɗan yatsansa yasa su a kan ƙahonnin bagadi domin baye-baye na ƙonawa, zai zuba dukkan jinin a gindin bagadi.35Zai yaɗe dukkan kitsen, kamar yadda aka yaɗe kitsen ɗan rago daga hadayar baye-bayen salama, firist zai ƙona shi a kan bagadi a bisa baye-bayen Yahweh da aka yi da wuta. Firist zai yi kaffara saboda shi domin zunubin da ya aikata, za a kuwa gafarta wa mutumin.

5

1Idan wani ya yi zunubi domin bai bada shaida ba sa'ad da ya ga wani abu game da abin da yakamata ya yi shaida, ko ya gani, ko kuwa yaji akan abin, za a kama shi da laifi.2Ko wani ya taɓa wani abin da Allah ya haramta shi marar tsarki, ko mushen haramtacciyar dabbar jeji ko ta gida da ta mutu, ko dabba mai rarrafe, ko da mutumin bai yi niyyar taɓa ta ba, ya ƙazamtu, ya kuma zama da laifi.

3Ko kuma idan ya taɓa ƙazamtar wani mutum, ko ma mene ne ƙazamtar, idan har bai sani ba, zai zama da laifi bayan an sanar da shi.4Ko kuma wani ya yi rantsuwa da garaje da bakinsa zai yi mugunta, ko ya yi nagari, ko mene ne mutum ya rantse da garaje, ko ma dai da rashin saninsa, idan an sanar da shi, zai zama da laifi a cikin abubuwan nan.
5Idan wani yana da laifi ko da guda ɗaya ne daga cikin waɗannan abubuwa, dole ya furta kowanne zunubi da ya aikata.6Dole ya kawo wa Yahweh baiko na laifi domin zunubin da ya aikata, dabba mace daga cikin garke ko ɗan rago ko akuya, domin baiko na zunubi, firist kuma zai yi kaffara dominsa game da zunubinsa.
7Idan ba zai iya sayan ɗan rago ba, sai ya kawo baikonsa na laifi domin zunubinsa kurciyoyi biyu ko 'yan tantabarai biyu ga Yahweh, ɗaya domin baiko na laifi ɗaya kuma domin baiko na ƙonawa.8Dole ya kawo su ga firist, wanda zai miƙa ɗaya domin baiko domin zunubi da fari - zai murɗe kan daga wuya amma ba zai cire shi ɗungum daga jikinsa ba.9Sa'an nan zai yayyafa kaɗan daga cikin jinin baikon domin zunubi a gefen bagadi, sauran jinin zai tsiyayar a gindin bagadi. Wannan shi ne baiko domin zunubi.
10Sa'an nan dole ya miƙa tsuntsu na biyu domin baiko na ƙonawa, kamar yadda aka bayyana a cikin farillai, sai firist kuma ya yi masa kaffara domin zunubin da ya aikata, za a kuwa gafarta wa mutumin.
11In kuwa ba zai iya sayan kurciyoyi biyu ko 'yan tantabarai biyu ba, sai dole ya kawo hadaya domin zunubinsa tiya biyu na gari mai laushi saboda baiko domin zunubi. Ba zai sa mai ko turare a kai ba, saboda baiko ne domin zunubi.
12Dole ne ya kawo shi ga firist, firist kuma zai ɗiba dai-dai tafin hannu ya zama baiko domin tunawa Sa'an nan zai ƙona shi a kan bagadi, a bisa baye-baye da aka yi da wuta domin Yahweh. Wannan baiko domin zunubi kenan.13Firist zai yi kaffara domin kowanne zunubin da mutumin ya aikata, za a kuwa gafarta wa mutumin nan. Duk ragowa daga baikon zai zama rabon firist, kamar dai baiko na hatsi.'"
14Sa'an nan Yahweh ya yi wa Musa magana, cewa,15"Idan wani ya yi zunubi ya aikata rashin aminci game da abubuwan da ke na Yahweh, amma ba dagangan ba, to dole ya kawo baiko domin laifi ga Yahweh. Wannan baiko dole ya zamana rago marar lahani daga garken tumaki; za a lisafta tamaninsa da ma'aunin azurfar - ma'auni na masujada - domin baiko na laifi.16Dole ya gamshi Yahweh domin abin da ya yi marar kyau game da abu mai tsarki, dole kuma ya ƙara kashi ɗaya cikin biyar a kai domin ya ba firist. Sa'an nan firist zai yi masa kafara da ragon baiko na laifi, za a kuwa gafarta wa mutumin nan.
17Idan wani ya yi zunubi har ya yi wani abin da Yahweh ya bada doka kada a yi, idan ma bai ankara da yinsa ba, duk da haka ya yi laifi dole ne ya amsa laifinsa.18Dole ya kawo rago marar lahani daga cikin garke, dai-dai tamanin kuɗinsa a yanzu, domin baiko domin laifi ga firist. Sa'an nan firist zai yi masa kaffara game da zunubin da ya aikata, wanda ya yi da rashin sani, za a kuwa gafarta masa.19Baiko ne domin laifi, kuma hakika yana da laifi a gaban Yahweh."

6

1Yahweh ya yi wa Musa magana, cewa,2"Idan wani ya yi abin rashin aminci gãba da Yahweh ta wurin yaudarar makwabcinsa game da wani abin da aka bashi riƙon amana, ko game da wani abin da aka sace, ko dai ya yi ta zaluntar makwabcinsa,3ko ya tsinci abin da makwabcinsa ya ɓatar ya yi musu a kansa, ya kuma rantse a kan ƙaryar, ko duk dai cikin abubuwa makamantan haka da mutane ke zunubi,4idan ya zamana ya yi zunubi, har aka same shi mai laifi ne, dole ne ya mayar da abin da ya karɓe da ƙwace ko ta hanyar zalunci, ko ta ajiyar da aka bashi riƙon amana ko ta abin da ya ɓace ya kuma tsinta.

5Bugu da ƙari, a cikin kowanne al'amari da ya rantse a kan karya, dole ya mayar cif yadda ya ke ya kuma ƙara kashi ɗaya cikin biyar na tamanin abin da ya biya dukka ga mai ita a ranar da aka kama shi da laifi.6Sa'an nan zai kawo wa Yahweh baiko na laifinsa, rãgo marar lahani daga cikin garke wanda tamaninsa haka ya ke a kasuwa, domin baiko na laifi ga firist.7Firist zai yi masa kaffara a gaban Yahweh, za a kuma gafarta masa game da duk wani laifi da ya yi."
8Sa'an nan Yahweh ya yi wa Musa magana, cewa,9"Ka dokaci Haruna da 'ya'yansa maza, cewa, 'Wannan ita ce dokar baiko na ƙonawa: Dole baiko na ƙonawa ya kasance a kan garwashin wutar bagadi dukkan dare har safiya, kuma wutar bagadin za a dinga izata tayi ta ci.
10Firist zai sanya rigunansa na lilin, zai kuma sa ƙananan kaya 'yan ciki na lilin. Zai kwashe tokar da ta rage bayan wuta ta cinye baiko na ƙonawa da ke kan bagadi, zai kuma sa tokar a gefen bagadin.11Zai tuɓe rigunansa ya sa wasu rigunan domin ya kai tokar bayan zango a wuri mai tsabta.
12Wutar da ke kan bagadi za a dinga iza ta. Ba za a barta ta mutu ba, firist zai yi ta ƙona itace a kanta kowacce safiya. Zai shirya baiko na ƙonawa yadda ya kamata a bisansa, a kansa zai ƙona kitsen baye-baye na salama.13Dole a sa wuta ta yi ta ci a kan bagadin ba fasawa. Kada a bari ta mutu.
14Wannan ita ce shari'a ta baiko na hatsi. 'Ya'yan Haruna maza zasu miƙa shi a gaban Yahweh a gaban bagadi.15Firist zai ɗibi tafin hannu na lallausar gari daga cikin baiko na garin hatsi da na mai da kuma turare wanda ya ke a kan baiko na garin hatsi, zai ƙona shi a kan bagadin domin ya bada ƙamshi mai daɗi domin baiko na madadi.
16Haruna da 'ya'yansa maza zasu ci duk abin da ya rage daga baikon. Dole a ci shi ba gami a wuri mai tsarki. Za su ci shi a harabar rumfar taruwa.17Ba za a toya shi da gami ba. Na ba su wannan kason ya zama nasu rabon daga nawa baye-baye da aka yi mani da wuta. Abu ne mafi tsarki, kamar baiko domin zunubi da baiko domin laifi.18Domin dukkan lokatai masu zuwa dukkan tsararrakin mutanenku, kowanne ɗa namiji daga zuriyar Haruna zai iya cin rabonsa, daga baye-baye ga Yahweh da aka yi da wuta. Duk wanda ya taɓa su zai tsarkaka.'"
19Sai Yahweh ya sake yin magana da Musa, cewa,20"Wannan shi ne baikon Haruna da 'ya'yansa maza, wanda zasu miƙa wa Yahweh a ranar da aka keɓe kowanne ɗa: kashi ɗaya cikin goma na garwar lallausar gari domin baiko na hatsi koyaushe, rabinsa da safe rabi kuma da maraice.
21Za a yi shi da mai a kaskon tuya. Sa'ad da aka jiƙa shi, za ku kawo shi ciki. A toye curi-curi za ku miƙa baiko na garin hatsi domin ya bada ƙamshi mai daɗi ga Yahweh.22‌Ɗan babban firist wanda zai gaji babban firist daga cikin 'ya'yansa zai miƙa shi. Kamar yadda aka umarta har abada, za a ƙona shi dukka ga Yahweh.23Kowanne baiko na garin hatsi na firist za a ƙona shi ƙurmus. Ba za a ci shi ba."
24Yahweh ya sake yin magana da Musa, cewa,25"Ka yi wa Haruna da 'ya'yansa maza magana, cewa, "Wannan ita ce dokar baiko domin zunubi: Dole a kashe baiko domin zunubi inda aka kashe baiko na ƙonawa a gaban Yahweh. Abu ne mafi tsarki.26Firist da ya miƙa shi don zunubi zai ci shi. Dole a ci shi a wuri mai tsarki a harabar rumfar taruwa.
27Duk abin da ya taɓa naman zai zama da tsarki, kuma idan aka yayyafa jinin akan wata riga, dole ku wanke ta, wannan shashen da ya ɗiga a kai, a wuri mai tsarki.28Amma tukunyar yunɓun da aka dafata a ciki dole a fashe ta. Idan an dafa ne a tukunyar ƙarfe, dole ne a kankare ta a ɗauraye ta cikin ruwa mai tsabta.
29Kowanne ɗa namiji daga cikin firistoci zai iya ci daga ciki domin mafi tsarki ne.30Amma kowanne baiko domin zunubi wanda aka kawo jininsa a rumfar taruwa domin a yi kaffara a wuri mai tsarki ba za a ci shi ba. Dole ne a ƙona shi.

7

1Wannan ita ce dokar baiko domin laifi. Mafi tsarki ne.2Dole a kashe baiko domin laifi a mayankarsa, dole kuma su yayyafa jininsa a kowanne gefen bagadi.3Dukkan kitsen da ke cikinsa za a miƙa shi: kitsen wutsiya, da kitsen da ke a kan kayan ciki,4da ƙodojin biyu da kitsen da ke bisan su, wanda ke kusa da kwiɓi, da wanda ya rufe hanta, tare da ƙodoji - duk wannan dole a cire su.

5Dole firist ya ƙona waɗannan sassa a kan bagadin shi ne baikon da aka yi da wuta ga Yahweh. Wannan shi ne baiko domin laifi.6Kowanne namiji daga cikin fistoci zai iya ci daga wannan baikon. Dole ne a ci shi a wuri mai tsarki domin mafi tsarki ne.
7Baiko domin zunubi kamar baiko domin laifi ya ke. Doka guda ce domin su biyun. Za su zama na firist wanda ya ke yin kaffara da su.8Firist wanda ya miƙa wa wani baikonsa na ƙonawa zai iya ɗaukar wa kansa fatar wannan baikon.
9Kowanne baiko na garin hatsi da aka toya a cikin tanda, da kowanne makamancin baiko da aka dafa a tukunya ko a kaskon tuya zai zama na firist da ya miƙa baikon.10Kowanne baiko na garin hatsi, ko busasshe ko kwaɓaɓɓe da mai, za su zama rabon dukkan zuriyar Haruna dai-dai wa dai-da.
11Wannan ita ce shari'ar hadayar baye-baye na salama wadda mutane za su miƙa ga Yahweh.12Idan wani ya miƙa shi domin ya yi godiya, to dole ya miƙa shi da hadayar waina da aka yi ba a sa gami ba, amma kwãɓe da mai, waina da aka yi ba gami, amma an shafa masu mai, waina da aka yi ta da lallausar gari da aka kwaɓa da mai.
13Kuma domin dalilin miƙa godiya, dole ya miƙa baikonsa na salama tare da wainar gurasa da aka yita da gami.14Zai miƙa guda ɗaya na kowanne irin waɗannan hadayu ya zama baikon da aka miƙa ga Yahweh. Zai zama rabon firist wanda ya yayyafa jinin baye-baye na salama a kan bagadi.
15Mutumin da ke miƙa baiko na salama domin nuna godiya dole ya ci naman baikonsa a ranar yin hadayar. Kada ya bar ragowar har kashegari da safe.16Amma idan hadayar baikonsa domin wa'adi ne, ko kuma domin bayarwar yardar rai, dole a ci naman a ranar da ya miƙa hadayar, amma duk abin da ya rage a ciki za a iya cinsa kashegari.
17Amma, kowanne ragowar naman hadaya a rana ta uku dole a ƙone shi.18Idan aka ci naman hadayar wani na baikon salama a rana ta uku, ba za a karɓa ba, ba kuma za a lisafta shi ga mai miƙa wa ba. Zai zama abin ƙyama, kuma mutumin da ya ci shi zai ɗauki laifin zunubinsa.
19Duk naman da ya taɓa abin da ba tsarki ba za a ci shi ba. Dole a ƙona shi. Game da sauran naman, duk wanda ya ke da tsarki zai iya cin shi.20Amma fa, mutum marar tsarki wanda ya ci wani nama daga hadayar baiko na salama wanda ya ke na Yahweh ne- wannan mutum dole a datse shi daga mutanensa.
21Idan wani mutum ya taɓa wani abu marar tsarki - ko ƙazamtar mutum ne, ko na ƙazamin dabba, ko na wani abu marar tsarki na ban ƙyama, sa'an nan kuma ya ci daga naman hadayar baiko na salama wanda ya ke na Yahweh ne, wannan mutumin dole a datse shi daga mutanensa.'"
22Sai Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,23"Yi magana da mutanen Isra'ila ka ce, 'Ba za ku ci kitsen sã ko na tunkiya ko na akuya ba.24Kitsen dabba mushe da ba a yi hadaya da ita ba, ko kitsen dabbar da namomin jeji suka yayyaga, za a iya yin amfani da su domin wani abu, amma kada ku kuskura ku ci su.
25Ko wane ne ya ci kitsen dabbar da mutane zasu iya miƙa ta hadaya ta ƙonawa ga Yahweh, wannan mutumin dole a datse shi daga mutanensa.26Ba za ku ci jini ba daɗai a gidajenku, ko daga tsuntsu ya ke ko dabba.27Duk wanda ya ci jini, dole a datse wannan mutum daga mutanensa.'"
28Sai Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,29"Ka yi magana da mutanen Isra'ila ka ce, 'Wanda duk ya ke miƙa hadayar baiko na salama ga Yahweh dole ya kawo wani sashen hadayar ga Yahweh.30Baiko domin Yahweh da za a yi da wuta, mai ita ne zai kawo da hannunsa. Dole ya kawo kitsen tare da ƙirjin, saboda a kaɗa ƙirjin ya zama baiko don kaɗawa a gaban Yahweh.
31Dole ne firist ya ƙona kitsen a kan bagadi, amma ƙirjin zai zama na Haruna da zuriyarsa.32Dole a bada cinyar ƙafar dama ga firist a matsayin baikon da aka miƙa daga cikin hadayarku ta baye-baye na salama.
33Firist, ɗaya daga cikin dangin Haruna, wanda ya miƙa jinin baye-baye na salama da kitsen - shi zai ɗauki cinyar ƙafar dama rabonsa kenan na baikon.34Gama na ɗauka daga mutanen Isra'ila, ƙirjin baiko na kaɗawa, da cinya su zama bayarwarsu, an rigaya an ba Haruna firist da 'ya'yansa maza waɗannan su zama rabonsu koyaushe.
35Wannan ne rabon Haruna da zuriyarsa daga baye-bayen da aka yi wa Yahweh da wuta, a ranar da Musa ya miƙa su su yi wa Yahweh hidima a cikin aikin firist.36Wannan rabon ne da Yahweh ya umarta a ba su daga mutanen Isra'ila, a ranar da ya keɓe firistoci. Kullum zai zama rabonsu har dukkan tsararraki.
37Wannan shi ne shari'ar baiko na ƙonawa, da baiko na hatsi, da baiko domin zunubi, da baiko domin laifi, da baiko na keɓewa, da na hadayar baye-baye na salama,38wanda Yahweh ya ba da umarnai ga Musa a kan Tsaunin Sinai a ranar da ya umarci mutanen Isra'ila su miƙa hadayunsu ga Yahweh a jejin Sinai.'"

8

1Yahweh ya yi magana da Musa, cewa'2"Ka ɗauki Haruna da 'ya'yansa maza tare da shi, da riguna, da man ƙeɓewa, da bijimi domin baiko na zunubi, da raguna biyu, da kwandon waina marar gami.3Ka tara dukkan taron a ƙofar rumfar taruwa."

4Sai Musa ya yi yadda Yahweh ya umarce shi, dukkan taron suka tattaru a ƙofar rumfar taruwa.5Sai Musa ya cewa taron, "Ga abin da Yahweh ya umarta a yi."
6Musa ya kawo Haruna da 'ya'yansa maza ya wanke su da ruwa.7Ya sa wa Haruna riga 'yarciki ya ɗaura masa ɗamara a ƙugunsa, ya sa masa taguwa ya kuma sa masa falmara, sa'an nan ya ɗaura masa falmarar da wata ƙasaitacciyar ɗamara mai kyan ɗinki ya zagaya ƙugunsa da ita ya ɗaure.
8Ya sa masa ƙyallen ƙirji, a kan ƙyallen kuma ya sa Urim da Tumim.9Ya naɗa masa rawani a kansa, a kan rawanin, a goshi, ya kafa masa tasar zinariya, kambi mai tsarki, kamar yadda Yahweh ya umarce shi.
10Musa ya ɗauki man ƙeɓewa, ya keɓe rumfar da dukkan abin da ke cikinta ya keɓe su ga Yahweh.11Ya yayyafa man a kan bagadi sau bakwai, ya shafe bagadin da dukkan kayan aikinta, da daron wanki da maɗorinta, saboda a keɓe su domin Yahweh.
12Ya zuba wasu man keɓewa akan Haruna ya shafe shi don a keɓe shi.13Musa ya kawo 'ya'yan Haruna maza ya suturta su da su riguna 'yanciki. Ya ɗaura masu ɗamara kewaye da ƙugunsu ya ɗaura masu rawanin ƙyallen lilin a kawunansu, kamar yadda Yahweh ya umarce shi.
14Musa ya kawo bijimin na baiko domin zunubi, sai Haruna da 'ya'yansa maza suka ɗibiya hannuwansu a kan bijimin da suka kawo saboda baiko domin zunubi.15Ya yanka shi, sai ya ɗauki jinin ya sa a kan ƙahonnin bagadin da ɗan yatsansa, ya tsarkake bagadin, ya zuba jinin a ƙarƙashin bagadin, ya keɓe shi ga Yahweh domin ya yi kaffara domin shi.
16Ya ɗauki dukkan kitsen da ke kan kayan ciki, da wanda ya rufe hanta, da ƙodojin biyu da kitsensu, sai Musa ya ƙona su dukka a kan bagadi.17Amma bijimin, da fatarsa, da namansa, da kashinsa ya ƙona su a bayan sansani, kamar yadda Yahweh ya umarce shi.
18Musa ya miƙa rãgon domin baiko na ƙonawa, kuma Haruna da 'ya'yansa maza suka ɗibiya hannuwansu a kan rãgon.19Ya yanka shi ya yayyafa jininsa a kowanne gefen bagadin.
20Ya yanka rãgon gunduwa gunduwa ya ƙona kan da yankakkun naman da kuma kitsen.21Ya wanke kayan cikin da ƙafafun da ruwa, ya kuma ƙona rãgon ɗungum a kan bagadi. Baiko ne na ƙonawa mai bada ƙamshi mai daɗi, baiko ne da aka yi da wuta ga Yahweh kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.
22Sa'an nan Musa ya miƙa ɗaya ragon, ragon tsarkakewa, Haruna da 'ya'yansa maza suka ɗibiya hannuwansu a kan rãgon.23Sai Haruna ya yanka shi, Musa kuma ya ɗiba daga jinin ya sa su a leɓatun kunnen dama na Haruna, da bisa babban yatsansa na hannun damansa da bisa babban yatsan ƙafarsa ta dama.24Ya kawo 'ya'yan Haruna maza, ya sa daga jinin a kan leɓatun kunnuwansu na dama, da kan manyan yatsan hannuwansu na dama, da kan manyan yatsansu na ƙafafun dama. Sa'an nan Musa ya yayyafa jinin a kowanne gefen bagadin.
25Ya ɗauki kitsen, kitsen wutsiya, dukkan kitsen da ke bisa kayan ciki, da wanda ya rufe hanta, da ƙodojin biyu da kitsensu, da cinyar dama.26Daga cikin kwandon gurasa da bata da gami da ke gaban Yahweh, ya ɗauki curi guda na marar gami, da curi guda na gurasa da aka shafe ta da mai, da waina guda, sai ya ɗibiya su bisa kitsen da kuma kan cinyar dama.27Ya sa su dukka a hannuwan Haruna da kuma hannuwan 'ya'yansa maza kuma ya kaɗa su a gaban Yahweh domin baiko na kaɗawa.
28Sa'an nan Musa ya karɓe su daga hannunsu ya ƙona su a kan bagadi domin baiko na ƙonawa. Baiko ne na keɓewa ya kuma bada ƙamshi mai daɗi. Baiko ne da aka yi da wuta ga Yahweh.29Musa ya ɗauki ƙirjin ya kaɗa su don su zama baikon kaɗawa ga Yahweh. Wannan shi ne rabon Musa daga rãgon domin naɗa firist, kamar yadda Yahweh ya umarce shi.
30Musa ya ɗiba daga man keɓewa da jinin da ke kan bagadi; ya yayyafa su a kan Haruna, da kan rigunansa, da kan 'ya'yansa maza, da kan rigunan 'ya'yansa maza tare da shi. Da haka ne ya keɓe Haruna da rigunansa, da 'ya'yansa maza da rigunansu ga Yahweh.
31Sai Musa ya cewa Haruna da 'ya'yansa maza, "Ku dafa naman a ƙofar shiga rumfar taruwa, ku ci a can da gurasar da ke cikin kwandon tsarkakewa, kamar yadda na umarta, cewa, 'Haruna da 'ya'yansa maza za su ci shi.'32Duk abin da ya rage daga naman da gurasar dole a ƙona.33Ba za ku fita daga ƙofar rumfar taruwa ba har kwana bakwai, sai kwanakin naɗinku sun cika. Domin Yahweh zai tsarkake ku kwana bakwai.
34Mene ne aka rigaya aka yi yau - Yahweh ya umarta a yi domin a yi maku kaffara.35Za ku zauna dare da rana har kwana bakwai a ƙofar rumfar taruwa, ku yi biyayya da umarnin Yahweh, domin kada ku mutu, domin wannan ne aka umarce ni.36Sai Haruna da 'ya'yansa maza suka yi dukkan abubuwan da Yahweh ya umarce su ta wurin Musa.

9

1A rana ta takwas Musa ya kira Haruna da 'ya'yansa maza da dattawan Isra'ila.2Ya cewa Haruna, "Ka ɗauki ɗan maraƙi daga garke domin baiko na zunubi, da rago marar lahani domin baiko na ƙonawa, ka miƙa su a gaban Yahweh.

3Dole ka yi wa mutanen Isra'ila magana ka ce, 'Ku ɗauki bunsuru domin baikon zunubi da kuma ɗan maraƙi da ɗan rãgo, dukka biyun bana ɗaya kuma marasa lahani, domin baiko na ƙonawa;4kuma ka ɗauki sã da rãgo domin baiko na salama a yi hadaya ga Yahweh, da baiko na garin hatsi cuɗaɗɗe da mai, domin yau Yahweh zai bayyana a gare ku.'"5Sai suka kawo dukkan abin da Yahweh ya umarta zuwa rumfar taruwa, sai dukkan taron Isra'ila suka matso suka tsaya a gaban Yahweh.
6Sai Musa ya ce, "Wannan shi ne Yahweh ya umarce ku kuyi domin ɗaukakarsa ta bayyana a gare ku,"7Musa ya cewa Haruna, "Ka matso kusa da bagadi ka miƙa baikonka domin zunubi da na ƙonawa, ka yi wa kanka kaffara domin mutane kuma, ka kuma miƙa hadaya domin mutane domin a yi masu kaffara kamar yadda Yahweh ya umarta."
8Sai Haruna ya tafi kusa da bagadi ya yanka ɗan maraƙin domin baikon zunubi wanda domin kansa ne.9'Ya'yan Haruna suka miƙa masa jinin, sai ya tsoma yatsansa cikinsa ya sa a ƙahonnin bagadin; sa'an nan ya zuba jinin a gindin bagadin.
10Amma, ya ƙona kitsen, da ƙodojin da wanda ya rufe hanta a kan bagadi domin baikon zunubi, kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.11Da naman da fatar ya ƙona su a bayan sansani.
12Haruna ya yanka baiko na ƙonawa, 'ya'yansa maza suka bashi jinin, wanda ya warwatsa a kowanne gefen bagadi.13Sa'an nan suka miƙa masa baiko na ƙonawa, gunduwa-gunduwa, tare da kan, sai ya ƙona su a kan bagadi.14Ya wanke kayan cikin da ƙafafuwan ya ƙona su a kan baiko na ƙonawa a kan bagadi.
15Haruna ya miƙa hadayar mutanen - bunsuru, sai ya ɗauke shi domin hadayar zunubansu ya yanka shi; ya miƙa hadayar ne domin zunubi, kamar yadda ya yi da bunsuru na fari.16Ya miƙa baiko na ƙonawa ya miƙa kamar yadda Yahweh ya umarta.17Ya miƙa baiko na garin hatsi; ya cika tafin hannunsa da ita ya ƙona ta a kan bagadi, tare da baikon ƙonawa na safe.
18Ya kuma yanka san da rãgon, hadaya domin baiko na salama, saboda mutanen. 'Ya'yan Haruna maza suka ba shi jinin, wanda ya yayyafa a kowanne gefen bagadi.19Amma, suka yanke kitsen bijimin da na rãgon, da kitsen wutsiyar, da kitsen da ya rufe kayan ciki, da ƙodoji, da wanda ya rufe hanta.
20Suka ɗauki sassan da aka yanka suka ɗibiyasu a kan ƙirjin, sa'an nan Haruna ya ƙona kitsen a kan bagadi,21Haruna ya kaɗa ƙirjin da cinyar ƙafar dama domin baiko na kaɗawa a gaban Yahweh, kamar yadda Musa ya umarta.
22Sa'an nan Haruna ya ɗaga hannuwansa yana fuskantar mutane ya albarkace su; sai ya dawo daga miƙa baiko na zunubi, baiko na ƙonawa, da baiko na salama.23Musa da Haruna suka shiga rumfar taruwa, suka sake fitowa kuma suka albarkaci mutanen, sai ɗaukakar Yahweh ta bayyana ga dukkan mutane.24Wuta ta fito daga Yahweh ta cinye baikon ƙonawar da kitsen da ke kan bagadin. Da dai dukkan mutane suka ga haka, sai suka yi ihu suka kwanta fuskokinsu a ƙasa.

10

1Sai Nadab, da Abihu 'ya'yan Haruna maza, kowannensu ya ɗauki farantinsa ya sa wuta a ciki, da kuma turare. Sa'an nan suka miƙa haramtacciyar wuta a gaban Yahweh, wanda bai dokace su su miƙa ba.2Saboda haka wuta ta fito daga gaban Yahweh ta hallaka su, suka kuwa mutu a gaban Yahweh.

3Sai Musa ya cewa Haruna, "Wannan shi ne Yahweh ya ke magana a kai sa'ad da ya ce, "Zan bayyana tsarkina ga waɗanda suka matso gare ni. Za a ɗaukaka ni a gaban dukkan mutane.'" Haruna bai ce komai ba.4Musa ya kira Mishayel da Elzafan, 'ya'ya maza na Uziyel kawun Haruna, ya ce masu, "Ku zo nan ku ɗauki 'yan'uwanku daga cikin sansani daga gaban rumfar taruwa."
5Sai suka matso kusa suka ɗauke su, suna saye da rigunansu na firistoci, zuwa bayan sansani, kamar yadda Musa ya umarta.6Sai Musa ya ce da Haruna da Eliyazar da kuma Itamar 'ya'yansa maza, "Kada ku bar gashin kanku da tsawo, kada kuma ku kekketa tufafinku, domin kada ku mutu, kuma domin kada Yahweh ya yi fushi da dukkan taro. Amma ku bari 'yan'uwanku wato dukkan gidan Isra'ila, su yi makoki domin waɗanda wutar Yahweh ta babbake.7Ba za ku fita daga ƙofar rumfar taruwa ba, ko kuwa ku mutu, gama man shafewa na Yahweh yana kanku." Sai suka aikata bisa ga umarnin Musa.
8Yahweh ya yi magana da Haruna, cewa,9"Kada ka sha ruwan inabi ko barasa, da kai, da 'ya'yanka maza da ke tare da kai, yayin da kuka shiga rumfar taruwa, domin kada ku mutu. Wannan zai zama tsayayyar ka'ida dukkan tsararrakin mutanenku,10domin a faiyace mai tsarki da marar tsarki, tsakanin ƙazamtacce da tsarkakke,11domin ka koyar da mutanen Isra'ila dukkan farillan da Yahweh ya umarta ta wurin Musa."
12Musa ya yi magana da Haruna da Eliyazar da kuma Itamar, 'ya'yansa maza da suka rage, "‌Ku ɗauki baiko na hatsi da ya ragu daga baye-bayen Yahweh da aka yi da wuta, ku ci bada gami ba kusa da bagadi, gama mafi tsarki ne.13Dole ka ci shi a wuri mai tsarki, domin rabonku ne da kuma rabon 'ya'yanku maza baye-bayen da aka yi wa Yahweh da wuta, gama wannan ne aka umarce ni in faɗa maku.
14Ƙirjin da aka kaɗa da cinyar da aka miƙa wa Yahweh, dole ku ci a wuri mai tsabta karɓaɓɓe ga Yahweh. Da kai da 'ya'yanka maza da 'ya'yanka mata tare da kai za ku ci waɗannan rabon, gama an bada su domin su zama rabonka da na 'ya'yanka maza daga cikin hadayu na baye-baye na zumunta na mutanen Isra'ila.15Cinyar da aka miƙa da ƙirjin da aka kaɗa, dole ne su kawosu da baye-baye na kitse da aka yi da wuta, domin a kaɗa su a gaban Yahweh. Za su zama naka da na 'ya'yanka maza rabonku ne har abada, kamar yadda Yahweh ya umarta."
16Sa'an nan Musa ya tambaya game da bunsurun baiko na zunubi, sai ya ga an ƙone shi kurmus. Saboda haka ya yi fushi da Eliyazar da Itamar, sauran 'ya'ya maza na Haruna; ya ce,17"Me ya sa ba ku ci baiko na zunubi a harabar rumfar sujada ba, tunda shike mafi tsarki ne, kuma tun da Yahweh ya bada shi gare ku domin a ɗauke laifin taro, domin a yi masu kaffara a gabansa?18Duba, ba a kawo jininsa cikin rumfar sujada ba, yakamata lallai da kun ci shi a harabar rumfar sujada, kamar yadda na umarta."
19Sai Haruna ya amsa wa Musa, "Duba, yau sun miƙa baikonsu na zunubi da baiko ta ƙonawa a gaban Yahweh, kuma ga wannan abu ya faru da ni yau. In da na ci baiko na zunubi yau, da zai zama da kyau kenan a idon Yahweh?"20Da Musa ya ji wannan, sai ya gamsu.

11

1Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna, cewa,2"Ka yi wa mutanen Isra'ila magana, ka ce, 'Waɗannan su ne masu rai da za ku ci daga cikin dukkan dabbobin da ke a duniya.

3Za ku ci kowacce dabba da ke da rababben kofato tana kuma tuƙa.4Amma fa, wasu dabbobin suna tuƙa, ko kuma suna da rababbun kofatai, ba za ku ci su ba, dabbobi kamar su raƙumi, domin yana tuƙa, amma ba shi da rababben kofato. Saboda haka raƙumi marar tsarki ne a gare ku.
5Haka ma rema, domin tana tuƙa amma ba ta da rababben kofato, ita ma marar tsabta ce a gare ku.6Zomo yana tuƙa, amma ba shi da rababben kofato, saboda haka marar tsabta ne a gare ku.7Alade, koda shike yana da rababben kofato, ba ya tuƙa, marar tsabta ne a gare ku.8Ba za ku ci namansu ba, ko ku taɓa gawawakinsu. Marasa tsabta ne a gare ku.
9Dabbobin da ke zaune cikin ruwa da za ku ci su ne duk waɗanda ke da ƙege ko kamɓori, ko a cikin teku ko cikin koguna.10Amma duk rayayyun hallitu da ba su da ƙege ko kamɓori a cikin teku da koguna, har da ma dukkan masu yawo a ruwa da dukkan hallitu da ke cikin ruwa - dole za su zama abin ƙyama a gare ku.
11Tun da ya zama dole ku ƙyamace su, ba za ku ci daga namansu ba; kuma, dole ku ƙyamaci gawawakinsu.12Dukkan abin da ba shi da ƙege ko kamɓori a cikin ruwa dole ku ƙyamace su.
13Ga tsuntsayen da za ku ji ƙyama kuma ba za ku ci su ba su ne: gaggafa, da ungulu,14da shirwa, da kowacce irin mikiya,15da kowanne irin hankaka,16jimina, da mujiyar dare, da shaho, da kowacce irin shirwa.
17Za ku kuma ƙyamaci mujiya, da babba da ƙarama, da zalɓe,18da kazar ruwa, da kwasakwasa, da ungulu,19da shamuwa, da jinjimi, da burtu, da jemage.
20Dukkan ƙwari masu fukafukai da ke tafiya a kan ƙafa huɗu abin ƙyama ne a gare ku.21Amma za ku iya cin ƙwari masu tashi suna kuma tafiya a kan ƙafafu huɗu idan ƙafafunsu suna da mahaɗi don tsalle a ƙasa.22Za ku iya cin kowacce irin fara, da gara mai fukafukai da gyare, ko fara.23Amma duk ƙwari masu tashi masu ƙafa huɗu abin ƙyama ne a gare ku.
24Za ku ƙazantu har faɗuwar rana ta wurin waɗannan dabbobi idan kun taɓa mushen ɗaya daga cikinsu.25Duk wanda ya ɗauki ɗaya daga cikin gawawakinsu dole ya wanke tufafinsa ya ƙazantu har ya zuwa faɗuwar rana.
26Duk dabbar da ke da rababben kofato kuma bata tuƙa zai zama ƙazantacce a gare ku. Duk wanda ya taɓa ta zai ƙazantu.27Duk abin da ke tafiya a kan daginsa a cikin dukkan dabbobi da suke tafiya a kan ƙafafu huɗu, ƙazantattu ne a gare ku. Duk wanda ya taɓa mushensu zai ƙazantu zuwa maraice.28Duk wanda ya ɗauki gawarsa dole ya wanke tufafinsa ya ƙazantu har ya zuwa maraice. Waɗannan dabbobi za su zama ƙazantattu a gare ku.
29Cikin dabbobi masu rarrafe a ƙasa, waɗannan dabbobi za su zama ƙazantattu a gare ku: da murɗiya, da ɓera, da kowanne irin babban ƙadangare,30da tsaka, guza, da ƙadangare, da damo da hawainiya..
31A cikin dukkan dabbobi masu rarrafe, waɗannan ne dabbobin da za su zama ƙazantattu a gare ku. Duk wanda ya taɓa mushensu zai ƙazantu har maraice.32Idan waninsu ya mutu ya kuma faɗi a kan wani abu, wannan abin ya ƙazantu, ko an yi shi da itace, ƙyalle, fata, ko tsumma, Ko mene ne shi kuma ko mene ne ake amfani da shi, dole a sa shi cikin ruwa; zai zama ƙazamtacce har maraice. Sa'an nan zai zama tsarkakakke.33Duk tukunyar yumɓun da ƙazantacciyar dabbar ta faɗa ciki, duk abin da ke cikin tukunyar ya ƙazanta, dole ku fasa tukunyar.
34Duk abinci da za a iya ci amma yana da ruwa a bisansa wannan tukunya ba ta da tsabta. Duk abin sha da ya ke cikin tukunyar ya ƙazantu.35Duk abin da mushe ya faɗi a kansa ya ƙazantu; ko tanderu ne ko ƙaramin murhu ne, dole a farfasa su mitsi-mitsi. Ba su da tsarki kuma dole su kasance marasa tsarki a gare ku,
36Maɓuɓɓugar ruwa ko daron ɗibar ruwa zai zama da tsabta; amma duk wanda ya taɓa mushensu ya ƙazantu.37Idan wani shashen mushen ya faɗa kan iri domin shuka, waɗannan irin yana da tsabta.38Amma idan an zuba ruwa akan wannan iri, kuma wani sashe na mushen ya faɗi a kansa, za ya zama ƙazantattu a gare ku.
39Idan dabbar da ya kamata ku ci ta mutu, sai shi wanda ya taɓa gawar ya ƙazantu har sai maraice.40Duk wanda ya ci wannan mushen dole ya wanke tufafinsa ya ƙazantu har faɗuwar rana. Wanda duk ya ɗauki wannan gawa zai wanke tufafinsa ya ƙazantu har maraice.
41Kowacce dabba da ke rarrafe a ƙasa za ku ƙyamace ta; ba za ku ci su ba.42Duk abin da ke jan ciki, da duk abin da ke tafiya akan ƙafafu huɗu, ko mai ƙafafu da yawa - dukkan dabbobi masu rarrafe a ƙasa, ba za ku ci waɗannan ba, domin abin da za a ji ƙyama ne.
43Ba za ku ƙazantar da kanku da kowacce hallita mai rai wanda ya ke jan ciki ba; ba za ku ƙazantar da kanku da su ba, har da za ku zama marasa tsarki da su.44Gama ni ne Yahweh Allahnku. Za ku ƙeɓe kanku da tsarki, saboda haka, kuma ku zama da tsarki, domin ni mai tsarki ne. Ba za ku ƙazantar da kanku da kowacce irin dabbar da ke tafiya a fuskar ƙasa ba.45Domin ni ne Yahweh, wanda ya fitar daku daga ƙasar Masar, domin in zama Allahnku. Saboda haka dole ne ku zama da tsarki, gama ni mai tsarki ne,
46Wannan ita ce dokar da ta shafi dabbobi, da tsuntsaye, da dukkan rayayyun hallitu da ke yawo cikin ruwaye, da kowacce hallita da ke rarrafe a fuskar ƙasa,47waɗanda za a sa bambanci tsakanin marasa tsarki da masu tsarki, da tsakanin abubuwa masu rai da za a iya ci, da abubuwa masu rai da ba za a ci su ba.'"

12

1Yahweh ya cewa Musa,2"Ka yi wa mutanen Isra'ila magana, cewa, "Idan mace ta yi ciki ta haifi ɗa namiji, za ta ƙazantu har kwana bakwai, kamar yadda ta ƙazantu a kwanakin watan hailarta.3A rana ta takwas dole a yi wa ɗan yaron kaciya.

4Sa'an nan tsarkakewar uwar daga zubar jini zai ci gaba har kwana talatin da uku. Ba zata taɓa wani abu mai tsarki ba ko ta shiga harabar haikali har sai kwanakin tsarkakewarta sun cika.5Amma idan ta haifi 'ya mace, za ta ƙazantu sati biyu, kamar yadda take kwanakin hailarta. Sa'an nan kwanakin tsarkakewar uwar zai ci gaba har kwana sittin da shida.
6Lokacin da kwanakin tsarkakewarta suka cika, domin ɗa na miji ko mace, dole ta kawo ɗan tunkiya bana ɗaya, domin baiko na ƙonawa, da ɗan kurciya ko tattabara domin baiko na zunubi, zuwa ƙofar rumfar taruwa, zuwa ga firist.
7Sa'an nan zai miƙa shi a gaban Yahweh ya yi kaffara domin ta, sa'an nan za ta tsarkaka daga zubar jininta. Wannan ita ce doka game da matar da ta haifi ɗa ko ɗiya.8Idan ba ta iya ba da tunkiya ba, to sai ta ɗauko kurciyoyi biyu ko 'yan tantabarai biyu, ɗaya domin baikon ƙonawa, ɗayan domin baiko na zunubi, sa'an nan firist zai yi kaffara domin ta; sa'an nan za ta tsarkaka.'"

13

1Yahweh ya yi magana da Musa da kuma Haruna, ya ce,2"Sa'ad da wani yana da kumburi ko ɓamɓaroki ko tabo mai haske a fatar jikinsa, har ya kamu da cuta kuma akwai cutar fata a jikinsa, dole a kawo shi ga Haruna babban firist, ko ga ɗaya daga cikin 'ya'yansa maza firistoci.

3Firist zai dudduba cutar a fatar jikinsa. Idan gashin da ke cikin cutar ya zama fari, kuma idan an ga cutar ta yi zurfi fiye da fatar jiki, to cuta ce mai yaɗuwa. Bayan da firist ya dudduba shi, dole ya furta shi marar tsarki.4Idan tabon mai haske a jikinsa fari ne, kuma ba aga cutar ta yi zurfin data zarce fatar jikin ba, kuma idan gashin da ke cikin cutar bai rikiɗa fari ba, to dole firist ya ware wannan mai cutar shi kaɗai har kwana bakwai.
5A rana ta bakwai, dole firist ya duba shi idan a ganinsa cutar ba ta ƙara muni ba, in kuma ba ta bazu a cikin fatar ba. Idan ba ta bazu ba, sai dole firist ya ƙara tsare shi wasu kwanaki bakwai kuma.6Firist zai sake bincike shi a rana ta bakwai ya ga ko cutar ta yi sauƙi, bata kuma ƙara bazuwa a fatar ba. Idan bata bazu ba, sai firist ya furta shi tsarkakakke.‌ Ƙuraje ne. Dole ya wanke tufafinsa, sai ya tsarkaka.
7Amma idan ɓamɓaroki ya yaɗu a cikin fatar bayan ya nuna kansa ga firist domin tsarkakewarsa, sai dole ya sake nuna kansa ga firist kuma.8firist zai sake duba shi ya ga ko ɓamɓarokin ya ƙara yaɗuwa a fatar jikin. Idan ya yaɗu, dole firist ya furta shi marar tsarki. Cutar fata ce mai bazuwa.
9Idan cutar fata mai yaɗuwa tana jikin wani, dole a kawo shi wurin firist.10Firist zai duba shi ya ga ko akwai farin kumburi a fatar jikinsa, idan gashin ya rikiɗa ya zama fari, ko kuma akwai buɗaɗɗen ƙurji a kumburin.11Idan akwai, to lallai akwai riƙaƙƙiyar cutar fata mai yaɗuwa, dole firist ya furta shi marar tsarki. Ba zai ware shi ba kaɗai, gama ya rigaya ya ƙazantu.
12Idan cutar ta bazu barkatai a cikin fata kuma ta mamaye duk fatar jikin mutumin daga kansa har zuwa kafafunsa, bisa ga ganin firist,13sai dole firist ya dudduba shi domin ya ga ko cutar ta rufe dukkan jikinsa. Idan kuwa haka ne, sai firist dole ya furta cewa mutumin nan mai cutar tsarkakke ne. Idan ta rikiɗa ta zama fari, to tsarkakakke ne.14Amma idan akwai buɗaɗɗen ƙurji a kansa, to ya ƙazantu.
15Dole firist ya duba miƙin jikin ya furta cewa ya ƙazantu domin miƙin fatar ƙazantacce ne. Cuta ce mai yaɗuwa.16Amma idan miƙin fatar ya koma kuma ya zama fari, dole mutumin ya tafi wurin firist.17Firist zai dudduba shi ya ga ko fatar ta koma fari. Idan ya koma, sai firist ya furta wannan mutum tsarkakke ne.
18Idan mutum yana da maruru a fatar jikinsa amma ya warke,19kuma a tabon marurun nan sai ga wani farin kumburi ko fata mai ƙyalli, ja da fari, to fa dole a nuna wa firist.20Firist zai dudduba ya ga ko ya shiga cikin fata sosai, kuma idan gashin wurin ya rikiɗa ya zama fari. Idan haka ne, dole firist ya furta shi marar tsarki. Cuta ce ta fata mai saurin yaɗuwa, idan ya girma a inda kumburin ya ke.
21Amma idan firist ya dudduba ya ga ba farin gashi a ciki, kuma zurfin bai zarce fata ba amma ya dushe, dole firist ya ware shi da bam har kwana bakwai.22Idan ta bazu ta mamaye fatar, dole firist ya furta shi marar tsarki. Cuta ce mai yaɗuwa.23Amma idan fata mai haske ta kassance wuri guda bai bazu ba, to tabon maruru ne, dole kuma firist ya furta shi tsarkakakke.
24Idan fata tana da ƙuna kuma wani buɗaɗɗen ƙurji ya fito a wurin da launi jaja-jaja fari-fari ko farin ɗigo,25sai firist ya dudduba shi ya ga ko gashin wurin ya zama fari, in kuma zurfinsa ya wuce fata. Idan haka ne, to cuta ce mai yaɗuwa. Ya ɓullo ne akan tabo, dole ne firist ya furta shi marar tsarki. Cuta ce mai yaɗuwa.
26Amma idan firist ya dudduba shi ya ga babu farin gashi a wurin, kuma bai zarce fata ba amma ya dushe, sai dole firist ya ware shi shi kaɗai har kwana bakwai.27Sa'an nan ɗole firist ya dudduba shi a rana ta bakwai. Idan ya yaɗu ya mamaye fatar, dole firist ya furta shi marar tsarki. Cuta ce mai yaɗuwa.28Idan cutar ta tsaya wuri guda ba ta yaɗu cikin fatar ba amma ta dushe, to kumburi ne daga ƙuna, dole firist ya furta shi tsarkakakke, saboda ba wani abu ba ne, sai dai tabo ne daga ƙuna.
29Idan namiji ko mace na da cuta mai yaɗuwa a kã ko a haɓa,30sai dole firist ya dudduba mutumin saboda cutar da ke yaɗuwa domin a ga ko ta zarce fatar jikin, idan aka ga gashi ruwan ɗorowa, kuma siriri a cikinsa. Idan akwai shi, to dole firist ya furta shi marar tsarki.‌ Ƙaiƙai ne. Cuta ce mai yaɗuwa a kã ko a haɓa,
31Idan firist ya dudduba cuta mai ƙaiƙayi ya ga babu ita ƙarƙashin fata, kuma ba baƙin gashi a ciki, to sai firist ya ware mutumin nan mai cutar ƙaiƙayi shi kaɗai har kwana bakwai.
32A rana ta bakwai firist zai duba cutar ya ga ko ta bazu. Idan babu gashi mai kalar ruwan ɗorowa, kuma idan cutar ba ta zarce zurfin fata ba, sai dole a yi masa aski,33amma ba za a aske wajen cutar ba, kuma dole firist ya ware mutumin nan mai cutar ƙaiƙayi shi kaɗai kimamin wasu kwana bakwai.
34A rana ta bakwai firist zai dudduba cutar ya ga ko ta dena bazuwa a cikin fatar, Idan an ga bata zarce zurfin fata ba, sai dole firist ya furta shi tsarkakakke. Dole mutumin ya wanke tufafinsa, sa'an nan za ya zama tsarkakakke,
35Amma idan cutar ƙaiƙayin ta bazu da yawa a cikin fatar bayan firist ya ce ya tsarkaka,36sai dole firist ya sake dudduba shi kuma. Idan cutar ta bazu a cikin fatar, firist bai buƙatar ya nemi gashi mai launin rawaya. Mutumin ya kazantu.37Amma idan a ganin firist cutar ƙaiƙayi ta dena bazuwa kuma baƙin gashi ya toho a wurin, to cutar ta warke. Ya zama tsarkakakke, dole firist ya furta shi tsarkakakke.
38Idan namiji ko mace na da farin tabbuna a fata,39sai dole firist ya dudduba mutumin ya ga ko tabbunan ba farare sosai ba ne, wannan ƙuraje ne kawai da suka farfashe a cikin fatar. Shi tsarkakakke ne.
40Idan gashin namiji ya zube daga kansa, yana da saiƙo, amma yana da tsarki.41Idan gashinsa suka zube daga gaban kansa, idan goshinsa na da saiƙo, shi tsarkakakke ne.
42Amma idan akwai wani ƙurji jaja-jaja fari-fari akan saiƙonsa ko goshinsa, wannan cuta ce mai yaɗuwa da ta faso.43Saboda haka dole firist ya dudduba shi ya ga ko kumburin cutar inda take a kan saiƙo ko goshinsa ya yi jaja-jaja fari-fari, da kuma kamannin cuta mai yaɗuwa ce a cikin fata.44Idan ita ce, to yana da cuta mai yaɗuwa kuma ba shi da tsarki. Tabbas kuma dole ne firist ya furta shi marar tsarki saboda cutarsa da ke a kansa.
45Mutumin da ke da cuta mai yaɗuwa dole ya sa yagaggun tufafi, ya bar gashin kai ba gyara, dole kuma ya rufe fuskarsa har hanci yana kira da ƙarfi, 'Marar tsarki, marar tsarki.'46Dukkan kwanakin da ya ke da wannan cuta mai yaɗuwa zai kasance marar tsarki. Domin ya ƙazantu da cuta mai yaɗuwa, dole ya zauna shi kaɗai. Dole ya zauna a bayan sansani.
47Rigar data ƙazantu da kuturta ko ta ulu ce ko rigar lilin ce,48abin da aka saƙa ko aka ɗinka daga ulu ko lilin, ko fata, ko mene ne dai da aka yi shi daga fata -49idan akwai wani kore-kore ko jaja-jajar ƙazanta a taguwar, fatar, da saƙa ko ɗinkakken yadi, ko mene ne dai da aka yi daga fata, to wannan kuturta ce data yaɗu; dole a nuna wa firist.
50Dole firist ya dudduba kayan don kuturta; dole ne ya kulle duk abin da ke da kuturta har kwana bakwai.51Zai sake duba kuturtar nan a rana ta bakwai. Idan ta bazu a tufar da aka saƙa ko aka ɗinka daga ulu ko yadin lilin ko fata ko wani abu da aka yi amfani da fata, to wannan kuturta ce mai cutarwa, wannan abu ya ƙazantu.52Dole ya ƙona wannan tufar, ko sakakkiya ko ɗinkakkiyar abin da aka yi da ulu ko yadin lilin, ko fata, ko wani abin da aka yi daga fata, dukkan abin da aka sami kuturta mai cutarwa a ciki, gama zai iya kaiwa ga cuta, Dole a ƙona wannan abin ƙurmus.
53Idan firist ya dudduba abin ya ga kuturta amma bata bazu cikin tufa ba ko cikin abin da aka ɗinka da yadi ko aka saƙa da ulu ko lilin, ko kayayyakin da aka yi su da fata,54sa'an nan zai umarce su su wanke kayan da aka sami kuturta a ciki, dole kuma zai kulle shi wasu kwana bakwai kuma.55Sa'an nan firist zai duba abin bayan an wanke wannan kayan mai kuturta. Idan kuturtar bata sauya launin ba, koda shike bata bazu ba, ƙazamtacce ne. Dole a ƙona wannan abin, ko ma a ina kuturtar ta ƙazamtar da shi.
56Idan firist ya duba wannan abin, idan kuturtar ta dushe bayan an wanke ta, dole ya yage wannan ƙazantaccen wuri daga tufar ko fatar, ko daga saƙaƙƙe ko ɗinkakken yadi.57Idan kuturta ta sake bayyana a taguwar ko a cikin saƙaƙƙe ko ɗinkakken yadi, ko wani abin da aka yi da fata, bazuwa take yi. Dole ku ƙona duk wani abin da ke da kuturta.58Riga ko wani abin da aka saƙa ko aka ɗinka daga ulu ko yadin lilin, ko fata, ko wani abin da aka yi da fata - idan kun wanke abin kuma kuturtar ta fita, sai kuma dole ku wanke wannan abin karo na biyu, sa'an nan zai zama da tsarki.
59Wannan ita ce shari'a game da kuturta a tufar ulu ko lilin, ko kowanne abin da aka saƙa ko ɗinka daga ulu ko yadin lilin, ko fata ko ko mene ne da aka yi shi da fata, domin ku furta shi mai tsarki ko marar tsarki."

14

1Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,2"Wannan ce shari'a domin mutum mai cuta a ranar tsarkakewarsa. Dole ne a kawo shi ga firist.

3Firist zai fita daga cikin zango domin ya dudduba mutumin ya ga ko cutar mai yaɗuwa a fata ta warke.4Sa'an nan firist zai bada doka cewa wanda za a tsarkake ya ɗauki tsuntsaye biyu masu rai, masu tsabta, da itacen sida. da jan zare, da ɗaɗɗoya.5Firist zai umarce shi ya kashe ɗaya daga cikin tsuntsayen a kan ruwa mai tsabta da ke cikin tukunyar yumɓu.
6Firist zai ɗauki tsuntsun mai rai da itacen sida, da jan zare da ɗaɗɗoyar, yatsoma dukkan waɗannan abubuwa, har ma da tsuntsun nan mai rai, a cikin jinin tsuntsun da aka kashe a kan ruwa mai tsabta.7Sa'an nan firist zai yayyafa wannan ruwa sau bakwai a kan mutumin da za a tsarkake daga cutar, sa'an nan firist zai furta cewa ya tsarkaka. Sa'an nan firist zai saki tsuntsun mai rai ya yi tafiyarsa jeji.
8Mutumin da ake tsarkakewa zai wanke tufafinsa, ya aske dukkan gashinsa, ya yi wanka da ruwa, sa'an nan zai tsarkaka. Bayan wannan dole ya dawo cikin zango. amma ba zai zauna a cikin rumfarsa ba sai bayan kwana bakwai.9A rana ta bakwai dole ya yanke dukkan gashin kansa, kuma dole ya aske gemunsa da girar idonsa. Dole ya aske dukkan gashinsa, kuma dole ya wanke tufafinsa ya yi wanka da ruwa; sa'an nan zai zama da tsarki.
10A rana ta takwas dole ya ɗauki 'yan raguna biyu marasa lahani, da 'yar tunkiya bana ɗaya marar lahani, da kashi uku bisa goma na mudun lallausar gari cuɗaɗɗe da mai domin baiko ta hatsi, da moɗar mai ɗaya.11Firist da ya tsarkake shi zai tsaida wanda za a tsarkake, tare da waɗannan abubuwa, a gaban Yahweh a ƙofar rumfar taruwa.
12Firist zai ɗauki ɗaya daga cikin 'yan ragunan ya miƙa shi baiko domin laifi, tare da moɗar mai; zai kaɗa su domin baiko na kaɗawa a gaban Yahweh.13Dole ya yanka ɗan ragon a inda suke yanka baye-baye na zunubi da baye-baye na ƙonawa, a harabar haikali, domin baiko na zunubi rabon firist ne, haka ma baiko na laifi, domin mafi tsarki ne.
14Firist zai ɗauki kaɗan daga cikin jinin baikon domin laifi ya sa shi a leɓatun kunnen dama na mutumin da za a tsarkake, da kan babban yatsan hannun damansa, da kan babban yatsan ƙafarsa ta dama.15Sa'an nan firist zai ɗauki mai daga moɗar ya zuba shi a tafin hannun hagunsa,16ya tsoma yatsansa na dama a cikin man da ke tafin hannunsa na hagu, ya yayyafa daga man da yatsansa sau bakwai a gaban Yahweh.
17Firist zai sa ragowar man a hannunsa a kan leɓatun kunnen dama na mutumin da za a tsarkake, da a kan babban yatsan hannunsa na dama, da a kan babban yatsan ƙafarsa ta dama. Dole ya sa wannan mai a kan jinin baiko domin laifi.18Game da sauran man da ke hannun firist, zai sa shi a kan mutumin da za a tsarkake, firist kuma zai yi kaffara dominsa a gaban Yahweh.
19Sa'an nan firist zai miƙa baiko na zunubi ya yi kaffara domin wanda za a tsarkake saboda rashin tsarkinsa, bayan wannan zai yanka baiko na ƙonawa.20Sa'an nan firist zai miƙa baiko na ƙonawa da kuma baiko na hatsi a kan bagadi. Firist zai yi kaffara domin wannan mutumin, sa'an nan zai zama da tsarki.
21Amma, idan mutumin matalauci ne har ba zai iya ba da waɗannan hadayu ba, to sai ya ɗauki ɗan rago ɗaya domin baiko na laifi saboda a kaɗa shi, a yi kaffara dominsa, da awon garwa na gari mai laushi da aka kwaɓa da mai domin baiko na hatsi, da mai a moɗa,22tare da kurciyoyi biyu ko 'yan tantabaru biyu, iyakar dai abin da ya iya samu; tsuntsu ɗaya zai zama na baikon zunubi ɗayan kuma baiko na ƙonawa.23A rana ta takwas dole ya kawo su domin tsarkakewarsa ga firist, zuwa ƙofar shiga rumfar taruwa, a gaban Yahweh.
24Firist zai ɗauki ragon domin baiko, zai ɗauke shi tare da moɗar man zaitun, sai ya ɗaga su sama sosai sa'ad da ya ke miƙa wa Yahweh.25Zai yanka ɗan ragon baiko domin laifi, zai ɗauki ɗan jinin baiko domin laifi ya sa su a leɓatun kunnen dama na wanda za a tsarkake, da kan babban yatsan hannun dama, da kan babban yatsan ƙafar damansa.
26Sa'an nan firist zai zuba daga cikin man a tafin hannunsa na hagu,27kuma ya yayyafa da ɗan yatsansa na dama daga cikin man da ke tafin hannunsa na hagu sau bakwai a gaban Yahweh.
28Firist zai sa daga man da ke tafin hannunsa a kan leɓatun kunnen dama na wanda za a tsarkake, da kan babban yatsan hannun damansa, da kuma kan babban yatsan ƙafar damansa, a nan wuraren da ya sa jinin baiko domin laifi.29Zai sa sauran man da ke hannunsa a kan wanda za a tsarkake, domin a yi kaffara dominsa a gaban Yahweh.
30Dole ya miƙa ɗaya daga cikin 'yan kurciyoyin ko 'yan tantabarai, gwargwadon abin da mutumin ya iya samowa -31ɗaya domin baikon zunubi ɗaya kuma domin baiko na ƙonawa, tare kuma da baiko na garin hatsi. Sai firist ya yi kaffara domin wanda za a tsarkake a gaban Yahweh.32Wannan ita ce doka domin mutumin da ke da cutar fata mai yaɗuwa, wanda ya gaza bayarwa bisa ga ka'idodin baye-baye domin tsarkakewarsa."
33Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna, cewa,34"Sa'ad da kuka shiga cikin ƙasar Kan'ana wanda na ba ku ta zama mallakarku, idan na sa kuturta mai yaɗuwa a cikin gida cikin ƙasar mallakarku,35sai dole mai wannan gida ya tafi ya faɗa wa firist. Dole ne ya ce, 'Ni a gani na akwai wani abu kamar kuturta a cikin gidana.'
36Sa'an nan firist zai umarta a fitar da komai daga cikin gidan kafin ya shiga ya duba ya tabbatar akwai kuturtar, domin kada a ƙazamtar da dukkan abin da ke gidan. Bayan wannan firist zai shiga ya duba cikin gidan.37Dole ya dudduba kuturtar ya ga ko tana bangayen gidan, ya duba ko yana da kore-koren launi ko jaja-jaja cikin zurfin bangayen.38Idan akwai kuturta a gidan, sai firist ya fita daga gidan ya rufe ƙofar gidan har kwana bakwai.
39Sa'an nan firist zai sake dawowa a rana ta bakwai ya dudduba shi domin ya ga ko kuturtar ta bazu a bangayen gidan.40Idan ta bazu, sai firist ya umarta a cire duwatsun da aka tarar da kuturta a jefar da su a wuri marar tsabta a bayan birni.
41Zai sa a kankare dukkan bangayen cikin gidan, dole kuma a kwashe dukkan ƙazamtattun kayayyakin da aka kankare a kai su can bayan birni a zuba su a wuri marar tsabta.42Dole su ɗauki wasu duwatsu su cike gurbin waɗancan duwatsun da aka cire, dole kuma su yi amfani da sabuwar ƙasa su yaɓe gidan.
43Idan kuturta ta sake ɓullowa cikin gidan da aka ciccire duwatsun bangayen aka kakankare su aka kuma yi sabon shafe,44sai dole firist ya shiga ciki ya dudduba gidan ya ga ko kuturtar ta bazu a cikin gidan. Idan ta bazu, to kuturtar mai cutarwa ce, gidan kuma ya ƙazantu.
45Dole ne a rushe gidan nan. Da duwatsun, da katakan, da dukkan shafen cikin gidan dole a kwashe su daga cikin birni zuwa wuri marar tsabta.46Bugu da ƙari, duk wanda ya shiga cikin gidan a lokacin da aka kulle gidan zai zama marar tsarki har maraice.47Duk wanda ya kwana a cikin gidan dole ya wanke tufafinsa, kuma duk wanda ya ci a cikin gidan dole ya wanke tufafinsa.
48Idan firist ya shiga domin ya dudduba ya ga ko kuturtar ta yaɗu a cikin gidan bayan an yi wa gidan yaɓe, sa'an nan, idan kuturtar ta tafi, sai ya furta wannan gida tsarkakakke.
49Sai dole firist ya ɗauki tsuntsayen biyu domin tsarkake gidan, da itacen sida, da shuɗin zare, da ɗaɗɗoya.50Sai ya kashe ɗaya tsuntsun a bisa ruwa mai tsabta cikin tukunyar yumɓu.51Zai ɗauki itacen sida, da ɗaɗɗoyar, da shuɗin zaren da kuma tsuntsun mai rai, ya tsoma su cikin jinin ɗaya tsuntsun da aka kashe, cikin ruwan nan mai tsabta, ya yayyafa gidan sau bakwai.
52Zai tsarkake gidan da jinin tsuntsun da ruwan nan mai kyau, tare da tsuntsun nan mai rai, da itacen sida, da ɗaɗɗoya, da kuma jan zare.53Amma zai bar tsuntsun mai rai ya fita daga cikin birni ya tafi jeji. Ta haka ne dole zai yi kaffara domin gidan, zai kuma zama da tsarki.
54Wannan ita ce shari'a domin dukkan irin cutar fata mai yaɗuwa, da abubuwan da ke sa irin wannan cuta, ko ƙaiƙayi,55da kuma kuturta a cikin tufafi da cikin gida,56da kumburi, da ƙuraje, da kuma tabo,57domin a tabbatar da lokacin da makamantan haka ba tsarki ko da tsarki. Wannan ita ce shari'a a kan cututtukan fatar jiki mai yaɗuwa da kuma kuturta.

15

1Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna, cewa,2"Ka yi magana da mutanen Isra'ila, ka ce masu, "Yayin da kowanne mutum ya ke da ruwan da ke fitowa daga cikin jikinsa, ya zama ƙazantacce.3Ƙazantarsa sakamakon wannan cutar ruwan ce. Ko jikinsa yana zubar da ruwan ko ya tsaya, kazantacce ne.

4Kowanne gadon da ya kwanta akai zai ƙazantu, duk abin da ya zauna akansa kuma zai ƙazantu.5Duk wanda ya taɓa gadonsa dole ya wanke tufafinsa kuma ya yi wanka cikin ruwa, kuma ya ƙazantu har yamma.
6Duk wanda ya zauna akan kowanne abin da da mutum mai cutar zubar ruwan nan ya zauna akai, wannan mutum dole ya wanke tufafinsa ya kuma yi wanka cikin ruwa, kuma zai zama marar tsabta har yamma.7Duk wanda ya taɓa jikin mai cutar zubar ruwa dole ya wanke tufafinsa kuma ya yi wanka cikin ruwa, ya ƙazantu har yamma.
8Idan mutumin nan mai cutar zubar ruwa ya tofa miyau a bisa wani mai tsabta, daga nan wannan mutumin dole ya wanke tufafinsa ya yi wanka cikin ruwa, kuma ya ƙazantu har yamma tayi.9Kowanne sirdi da mai zubar ruwan ya hau kai zai zama ƙazantacce.
10Duk wanda ya taɓa kowanne abin da ke ƙarƙashin mutumin zai ƙazantu har yamma, kuma wanda ya ɗauki waɗannan abubuwan dole ya wanke tufafinsa ya yi wanka cikin ruwa; ya ƙazantu har yamma ta yi.11Duk wanda mai cutar zubar ruwan ya taɓa ba tare da ya ɗauraye hannuwansa da farko cikin ruwa ba, mutumin da aka taɓa dole ya wanke tufafinsa ya yiwa kansa wanke cikin ruwa, kuma zai zama marar tsabta har yamma ta yi.12Kowacce tukunyar yumɓun da mai irin wannan zubar ruwan ya taɓa dole a fasata, kuma kowanne akushin itace dole a ɗauraye shi cikin ruwa.
13Sa'ad da shi mai zubar ya tsarkaka daga zubar tasa, daga nan sai ya ƙirgawa kansa kwana bakwai domin tsarkakewarsa; daga nan dole ya wanke tufafinsa ya kuma yi wanka cikin ruwa mai gudu. Daga nan zai tsarkaka.14A rana ta takwas dole ya ɗauki "yan kurciyoyi biyu ko 'yan tantabarai guda biyu ya zo gaban Yahweh a ƙofar shiga rumfar taruwa; a can dole ya bada tsuntsayen ga firist.15Dole firist ɗin ya miƙa su, ɗaya a matsayin hadayar zunubi ɗaya a matsayin ƙonanniyar hadaya, kuma dole firist ya yi kaffara domin sa a gaban Yahweh domin zubarsa.
16Idan kowanne mutum yana da fitaccen maniyyi, daga nan dole ya wanke dukkan jikinsa cikin ruwa; zai zama marar tsabta har yamma.17Kowacce riga ko tufar fata inda akwai maniyyin dole a wanke ta da ruwa; zata zama marar tsarki har yamma.18Idan mace da miji suka kwanta tare kuma akayi canjin maniyyi zuwa gare ta, dole dukkansu su yi wanka cikin ruwa; zasu zama marasa tsarki har yamma.
19Idan mace tana haila, rashin tsarkinta zai ci gaba har kwana bakwai, kuma duk wanda ya taɓata zai ƙazantu har yamma ta yi.20Kowanne abin data kwanta akai lokacin al'adarta zai zama marar tsarki; kowanne abin data zauna akansa kuma zai zama marar tsarki.
21Duk wanda ya taɓa gadonta dole ya wanke tufafinsa kuma ya wanke kansa cikin ruwa; wannan mutumin zai zama marar tsarki har yamma.22Duk wanda ya taɓa kowanne abin data zauna a kansa dole ya wanke tufafinsa ya kuma yi wanka cikin ruwa; wannan mutumin zai ƙazantu har yamma.23Ko akan gado ko akan kowanne abin da ta zauna akai, idan ya taɓa shi, wannan mutumin zai zama marar tsarki har yamma.
24Idan kowanne mutum ya kwana da ita, kuma idan zubar rashin tsarkinta ya taɓa shi, zai zama marar tsarki har kwana bakwai. Kowanne gadon da ta kwanta kai zai zama marar tsarki.
25Idan mace tana zubar jini kwanaki da yawa wanda ba cikin kwanakin hailarta bane, ko idan tana zuba fiye da kwanakin hailarta, lokacin dukkan kwanakin zubar rashin tsarkinta, zata zama kamar tana cikin kwanakin hailarta. Marar tsarki ce.26Kowanne gadon data kwanta akai dukkan kwanakin zubar jininta zai zama a gareta kamar gadon data kwanta akai lokacin hailarta, kuma duk abin data zauna akai zai ƙazantu, kamar rashin tsarkin ta na haila.27Duk wanda ya taɓa kowanne ɗaya daga cikin waɗannan abubuwan zai zama marar tsarki; dole ya wanke tufafinsa ya kuma wanke kansa cikin ruwa, kuma ya zama marar tsarki har yamma tayi.
28Amma idan ta tsarkaka daga zubar jininta, daga nan sai ta lisafta wa kanta kwanaki bakwai, bayan wannan ta tsarkaka.29A rana ta takwas za ta ɗauki 'yan'kurciyoyi guda biyu ko 'yan' tantabarai guda biyu za ta kawo su wurin firist a ƙofar rumfa ta taruwa.30Firist zai miƙa tsuntsu ɗaya a matsayin hadaya ta zunubi, ɗayan kuma domin ƙonanniyar hadaya, kuma zai yi kaffara domin ta a gaban Yahweh domin zubar jininta.
31Ta haka za ku keɓe mutanen Isra'ila daga ƙazantarsu, domin kada su mutu ta wurin ƙazantarsu, ta wurin ɓata rumfar sujadata, in da nake zama a tsakiyar su.
32Waɗannan su ne ka'idodi domin duk wanda ya ke zubar ruwa, domin kowanne mutum da maniyinsa ya fita daga gare shi ya sa shi ya zama marar tsarki,33ga kowacce mace da ke haila, da duk wanda ya ke zubar ruwa, ko namiji ko mace, da kuma duk wanda ya kwana da matar da ta ƙazanta.'"

16

1Yahweh ya yi magana da Musa -- wannan bayan mutuwar 'ya'yan Haruna guda biyu, lokacin da suka kusato Yahweh kuma suka mutu.2Yahweh ya ce da Musa. "Ka yi magana da Haruna ɗan'uwanka ka ce masa kada kowanne lokaci ya riƙa shiga wuri mai tsarki cikin labule, a gaban mazaunin jinƙai wanda ke bisa kan akwatin al̀ƙawari. Idan ya yi haka, zai mutu, saboda ina bayyana cikin girgije a bisa mazaunin jinƙai.

3Don haka ga yadda Haruna zai shiga wuri mafi tsarki. Dole ya shiga da ɗan bijimi domin hadaya ta zunubi, da rago domin hadaya ta ƙonawa.4Dole ya sanya riga mai tsarki, kuma dole ya sa riga 'yarciki a jikinsa, kuma dole ya sa ɗamarar linin da rawanin linin. Waɗannan su ne riguna masu tsarki. Dole ya wanke jikinsa cikin ruwa daga nan ya shirya kansa da waɗannan rigunan.5Dole ya karɓi bunsura biyu daga taron jama'ar Isra'ila a matsayin baikon zunubi da rago ɗaya domin ƙonanniyar hadaya.
6Daga nan dole Haruna ya miƙa bijimi domin baikon zunubi, wanda ya ke domin kansa, zai yi kaffara domin kansa da iyalinsa.7Daga nan dole ya ɗauki bunsura biyun ya ajiye su gaban Yahweh a ƙofar shiga rumfar taruwa.
8Daga nan dole Haruna ya jefa ƙuri'a domin bunsuran biyu, ɗaya domin Yahweh, ɗaya a matsayin refataccen bunsuru.9Daga nan dole Haruna ya miƙa bunsurun da ƙuri'a ta faɗa wa ga Yahweh, kuma ya miƙa bunsurun a matsayin baikon zunubi.10Amma bunsurun da ƙuri'a ta faɗa wa a matsayin refataccen bunsuru dole a kawo shi da rai gaban Yahweh, domin kaffara ta wurin aikar da shi a matsayin refataccen bunsuru cikin jeji.
11Daga nan dole Haruna ya miƙa bijimi domin baikon zunubi, wanda zai zama domin kansa. Dole ya yi kafara domin kansa da kuma domin iyalinsa, dole ya yanka bijimi a matsayin baikon zunubi domin kansa.
12Dole Haruna ya ɗauki kasko cike da garwashin wuta daga bisa bagadi gaban Yahweh, hannuwansa kuma cike da gyararren garin turare mai ƙanshi, ya kuma kawo waɗannan abubuwan cikin labule.13A can dole ya ɗibiya turare akan wuta gaban Yahweh domin hayaƙi daga turaren ya rufe marfin kaffara a bisa dokokin alƙawarin. Dole ya yi haka domin kada ya mutu.
14Daga nan dole ya ɗauki jinin bijimi ya yayyafa shi da yatsansa a gaban marfin kaffara. Dole ya yayyafa sauran jinin da yatsansa sau bakwai gaban mazaunin jinƙai.
15Sa'an nan dole ya yanka bunsuru domin hadayar zunubi wanda ya ke domin jama'a ya kawo jininsa cikin labule. A can dole ya yi da jinin kamar yadda ya yi da jinin bijimin: Dole ya yayyafa shi a bisa murfin kafara da kuma gaban murfin kafara.16Dole ya yi kafara domin wuri mai tsarki saboda ƙazantar ayyukan mutanen Isra'ila, da kuma domin tayarwarsu da dukkan zunubansu. Dole kuma ya yi haka kuma domin rumfar taruwa, inda Yahweh ke zama cikinsu, a gaban ƙazantattun ayyukansu.
17Ba wanda zai kasance a rumfar taruwa sa'ad da Haruna ya shiga domin ya yi kaffara cikin wuri mafi tsarki, har lokacin da ya fito ya kuma gama yin kaffara domin kansa da kuma iyalinsa, da kuma dukkan taron Isra'ila.18Dole ya fita zuwa bagadin da ke gaban Yahweh domin ya yi kaffara domin sa, kuma dole ya ɗibi jinin bijimi da jinin akuyar ya sa shi a bisan ƙahonnin bagadi ko'ina kewaye.19Dole ya yayyafa daga cikin jinin a kai da yatsansa sau bakwai ya tsabtace shi ya keɓe shi ga Yahweh, nesa daga ƙazantar ayyukan mutanen Isra'ila.
20Sa'ad da ya gama yin kaffara domin wuri mafi tsarki, rumfar taruwa, da bagadi, dole ya miƙa bunsurun mai rai.21Dole Haruna ya ɗibiya hannayensa a kan bunsurun mai ran ya furta dukkan muguntar mutanen Isra'ila, dukkan tayarwarsu, da dukkan zunubansu. Daga nan dole ya sa zunubansu a kan bunsurun ya sallami bunsurun ta wurin kulawar mutumin da ya shirya ya jagoranci bunsurun zuwa cikin jeji.22Dole bunsurun ya ɗaukarwa kansa dukkan muguntar mutane zuwa wurin da ba kowa. A can cikin jeji, mutumin zai saki bunsurun ya tafi hakanan.
23Daga nan dole Haruna ya koma cikin rumfar taruwa ya tuɓe rigunansa na linin waɗanda ya sa kafin ya shiga wuri mafi tsarki, kuma dole ya bar rigunan can.24Dole ya wanke jikinsa a cikin ruwa cikin wuri mai tsarki, ya sa tufafinsa da ya saba; daga nan dole ya fito ya miƙa baikonsa na ƙonawa da baikon ƙonawa domin jama'a, ta haka zai yi kaffara domin kansa kuma domin jama'a.
25Dole ya ƙone kitsen baikon zunubi a bisa kan bagadi.26Mutumin da ya bar refataccen bunsuru ya tafi dole ya wanke tufafinsa ya kuma yi wanka cikin ruwa; bayan haka, zai iya dawowa cikin sansani.
27Bijimi domin baikon zunubi da bunsurun domin baikon zunubi, wanda aka kawo jininsu domin kaffara cikin wuri mai tsarki, dole a ɗauke su waje bayan sansani. A can dole su ƙone fatarsu, namansu, da kashinsu.28Mutumin da ya ƙone waɗannan sassan dole ya wanke tufafinsa ya wanke jikinsa cikin ruwa; bayan haka, zai iya dawowa cikin sansani.
29Zai zama farilla a gare ku kullum a cikin wata na bakwai, a bisa rana ta goma, dole ku ƙasƙantar da kanku kada ku yi aiki, ko wanda aka haifa ɗan gari ko bãƙo wanda ya ke zama a cikinku.30Saboda a ranar nan za ayi kaffara domin ku, a tsarkake ku daga dukkan zunubanku domin ku tsarkaka a gaban Yahweh.31Assabat ta musamman ta hutawa domin ku, dole kuma ku ƙasƙantar da kanku kada ku yi wani aiki. Wannan zai zama farilla a gare ku kullum.
32Babban firist, wanda za a zuba masa mai a keɓe shi ya zama babban firist a madadin mahaifinsa, dole ya yi wannan kaffarar ya sa tufafin linin, wato, tufafi masu tsarki.33Zai yi kaffara domin wuri mafi tsarki; dole ya yi kaffara domin rumfar taruwa da kuma domin bagadi, kuma dole ya yi kaffara domin firistoci kuma domin dukkan taron jama'a.
34Wannan zai zama farilla a gare ku koyaushe, a yi kaffara domin mutanen Isra'ila saboda dukkan zunubansu, sau ɗaya a cikin shekara." An yi haka kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.

17

1Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,2"Ka yi magana da Haruna da 'ya'yansa, da dukkan mutanen Isra'ila. Ka faɗa masu abin da Yahweh ya umarta:3'Duk mutumin da ke daga gidan Isra'ila wanda ya kashe sã, rago ko akuya a cikin sansani, ko wanda ya kashe shi a bayan sansani, domin ya miƙa shi hadaya -4idan bai kawo shi a ƙofar rumfar taruwa ya miƙa shi hadaya ga Yahweh a gaban mazaunin sa ba, wannan mutum ya zama da laifin zubar da jini. Ya zubar da jini, wannan mutum dole a datse shi daga cikin jama'arsa.

5Dalilin wannan dokar shi ne domin mutanen Isra'ila su kawo hadayunsu ga Yahweh a ƙofar rumfar taruwa, wurin firist domin hadaya a matsayin baikon zumunta ga Yahweh, maimakon baikon hadayun da suke miƙawa a fili.6Firist zai yayyafa jinin a bisa bagadin Yahweh a ƙofar rumfar taruwa, zai ƙona kitsen domin ya bada ƙanshi mai daɗi domin Yahweh.
7Nan gaba mutanen ba za su ƙara miƙa hadayunsu ga gumakan bunsuru ba, domin sun aikata kamar karuwai. Wannan zai zama farilla ta din-din din a gare su ga dukkan tsararsu.'
8Dole ka ce masu, 'Kowanne mutumin Isra'ila, ko kowanne baƙon da ke zaune a cikinsu, wanda ya miƙa baikon ƙonawa ko hadaya9kuma bai kawo ta a ƙofar rumfar taruwa domin a miƙa ta ga Yahweh ba, wannan mutumin dole a fitar da shi daga jama'arsa.
10Idan wani mutumin gidan Isra'ila, ko wani baƙon da ke zaune a cikin su ya sha kowanne irin jini, zan sa fuskata gãba da wannan mutum da ya sha jini kuma zan datse shi daga cikin jama'arsa.11Gama ran dabba yana cikin jininsa. Na bada jininsa gare ku domin ku yi kaffara a bisa bagadi domin rayukanku, saboda jini ne ke yin kaffara, gama jini ke yin kaffara domin rai.
12Domin wannan na ce da mutanen Isra'ila ba wani a cikinku da zai ci jini, ko kowanne bãƙo da ke zaune a cikinku ya ci jini.13Kowanne mutumin Isra'ila, ko baƙin da ke zaune a cikinsu, wanda ya yi farauta ya kashe dabba ko tsuntsun da za a iya ci, dole wannan mutumin ya zubar da jinin sa'an nan ya rufe jinin da ƙasa.
14Gama ran dukkan halitta yana cikin jininta. Shi ya sa na ce da mutanen Isra'ila, "Ba za ku ci jinin kowacce halitta ba, gama ran kowacce halitta yana cikin jininta. Duk wanda ya ci ya zama dole a datse shi."
15Kowanne mutumin da ya ci dabbar data mutu ko wadda namomin jeji suka yayyaga, ko mutumin nan haifaffen gida ne ko baƙon da ke zama a cikinku, dole ya wanke tufafinsa ya kuma yi wanka cikin ruwa, zai zama ƙazantacce har yamma. Sa'an nan zai tsarkaka.16Amma idan bai wanke tufafinsa ba ko ya wanke jikinsa ba, daga nan dole ya ɗauki alhakin laifinsa.'"

18

1Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,2"Ka yi magana da mutanen Isra'ila ka ce masu, 'Ni ne Yahweh Allahnku.3Ba za ku yi abubuwan da mutane ke yi a Masar ba, in da kuka taɓa zama. Ba za ku yi abubuwan da mutane ke yi a Kan'ana ba, ƙasar da nake kai ku. Kada ku bi al'adunsu.

4Shari'una su ne za ku yi dole, dokokina kuma su ne za ku kiyaye dole, domin ku yi tafiya cikinsu, saboda ni ne Yahweh Allahnku.5Don haka dole ku kiyaye umarnaina da shari'una. Idan mutum ya yi biyayya da su, zai rayu saboda su. Ni ne Yahweh.
6Ba wanda zai kwanta da kowanne dangi na kusa domin ya buɗe tsiraicinsa. Ni ne Yahweh.7Kada ka ƙasƙantar da mahaifinka ta wurin kwanciya da mahaifiyarka. Ita mahaifiyarka ce! Kada ka ƙasƙantar da ita.8Kada ka kwana da kowacce matar mahaifinka; kada ka ƙasƙantar da mahaifinka kamar haka.
9Kada ka kwana da kowacce 'yar'uwarka, ko ita ɗiyar mahaifinka ce ko ɗiyar mahaifiyarka, ko a gidan ku ta girma ko a wani gida na nesa da kai. Kada ka kwana da 'yan'uwanka mata.10Kada ka kwana da ɗiyar ɗanka ko ɗiyar 'yarka. Wannan zai zama abin kunya gare ka.11Kada ka kwana da ɗiyar matar mahaifinka, wadda mahaifinka ya haifa. Ita 'yar'uwarka ce, kuma kada ka kwana da ita.
12Kada ka kwana da 'yar'uwar mahaifinka, Ita 'yar'uwar mahaifinka ce ta kusa.13Kada ka kwana da 'yar'uwar mahaifiyarka. Ita 'yar'uwar mahaifiyarka ce ta kusa.14Kada ka ƙasƙantar da ɗan'uwan mahaifinka ta wurin kwana da matarsa. Kada ka yi kusa da ita akan wannan dalili; ita bãbarka ce.
15Kada ka kwana da matar ɗanka. Ita matar ɗanka ce; kada ka kwana da ita.16Kada ka kwana da matar ɗan'uwanka; kada ka ƙasƙantar da shi ta wurin yin haka.
17Kada ka kwana da mace da ɗiyarta kuma, ko ɗiyar ɗanta ko ɗiyar 'yarta. Su danginta ne na kusa, kwana da su zai zama mugunta.18Ba zaka auri 'yar'uwar matarka a matsayin kishiyarta ba kuma ka kwana da ita yayin da matarka ta farko na da rai.
19Kada ka kwana da mace a lokacin hailarta. Ba ta da tsarki a wannan lokacin.20Kada ka kwana da matar maƙwabcinka kuma ka ƙazantar da kanka da ita ta wannan hanya.
21Kada ka bada ko ɗaya daga cikin 'ya'yanka a sa su cikin wuta, domin ka miƙa su hadaya ga Molek, saboda ba za ka tozarta sunan Allahnka ba. Ni ne Yahweh.
22Kada ka kwana da wasu maza kamar yadda ake yi da mace. Wannan zai zama mugunta.23Kada ka kwana da kowacce dabba ka kuma ƙazantar da kanka da ita. Ba wata mace da zata kwana da kowacce dabba. Wannan zai zama keta doka.
24Kada ka ƙazantar da kanka ta kowanne irin waɗannan hanyoyi, gama ta cikin irin waɗannam hanyoyi ne al'ummai suka ƙazantu, al'umman da na kora daga gaban ku.25ƙasar ta ƙazantu, na hukunta zunubansu, ƙasar ta amayar da mazaunanta.
26Domin haka, ku, dole ku kiyaye dokokina da umarnaina, kuma ba za ku aikata ko ɗaya daga cikin waɗannan abubuwan banƙyama ba, ko haifaffen Ba - Isra'ile ko bãƙon da ke zaune a cikinku.27Gama wannan ita ce muguntar da mutanen cikin ƙasar da suka rigaye ku suka aikata, waɗanda suka zauna nan kafin ku, yanzu kuma ƙasar ta ƙazantu.28Don haka sai ku yi hankali don kada ƙasar ta amayar da ku bayan da kun ƙazantar da ita, kamar yadda ta amayar da mutanen da suka rigaye ku.
29Duk wanda ya aikata kowanne ɗaya daga cikin abubuwan banƙyamar nan, mutanen da suka yi waɗannan za a datse su daga cikin jama'arsu.30Don haka dole ku kiyaye dokata kada ku aikata ko ɗaya daga cikin waɗannan al'adun mãsu banƙyama waɗanda aka aikata a nan a gaban ku, domin kada ku ƙazantar da kanku ta wurin su. Ni ne Yahweh Allahnku.'"

19

1Yahweh ya yi magana da Musa cewa,2"Ka yi magana ga dukkan taron jama'ar Isra'ila ka ce masu, "Dole ku zama da tsarki, gama ni Yahweh Allahnku mai tsarki ne.3Kowanne dole ya girmama mahaifiyarsa da mahaifinsa, kuma dole ku kiyaye assabataina. Ni ne Yahweh Allahnku.4Kada ku juya ga gumakai marasa amfani, ko ku yi wa kanku alloli na ƙarfe. Ni ne Yahweh Allahnku.

5Sa'ad da ka miƙa hadaya ta zumuntar baye-baye ga Yahweh, dole ka miƙa ta yadda za a karɓe ka.6Dole a cinye ta a ranar da aka miƙa ta, ko kuma washegari. Idan wani abu ya rage har rana ta uku, dole a ƙone shi da wuta.7Idan anci ta ko kaɗan a kan rana ta uku, naman ya zama marar tsarki; ba za a karɓe ta ba,8kuma duk wanda ya ci dole ya ɗauki alhakin laifinsa saboda ya ƙazantar da abin da ke mai tsarki na Yahweh, wannan mutum dole a datse shi daga jama'arsa.
9Sa'ad da kuka girbe amfanin ƙasarku, ba za ku girbe kusurwowin gonarku dukka ba, ba kuma za ku tattara dukkan amfanin girbin ku ba.10Ba za ku tattara kowanne inabi daga garkar inabin ba, ko ku tattara inabin da ya faɗi a ƙasa cikin garkar. Dole ku bar su domin matalauta kuma domin bãƙi. Ni ne Yahweh Allahnku.
11Kada ku yi sata. Kada ku yaudari juna.12Kada ku rantse da sunana kan ƙarya kuma ku tozarta sunan Allahnku. Ni ne Yahweh.
13Kada ka zalunci makwabcinka ko ka yi masa fashi. Haƙin bawan da aka yi hayarsa kada ya kwana wurinka har safiya.14Kada ka la'anta kurma ko ka sa abin tuntuɓe gaban makaho. Maimakon haka, dole ku ji tsoron Allah. Ni ne Yahweh.
15Kada ka aikata rashin gaskiya cikin shari'a. Kada ka nuna tãra ga wani saboda shi talaka ne, kuma kada ka nuna tãra ga wani saboda muhimmancinsa. Maimakon haka, ka shari'anta makwabcinka bisa ga adalci.16Kada ka yi tafiyar yawon ɓatanci a cikin mutanenka, amma ka nemi kare ran makwabcinka. Ni ne Yahweh.
17Kada ka ƙi ɗan'uwanka a zuciyarka. Dole ka tsauta wa maƙwabcinka akan gaskiya domin kada zunubinsa ya shafe ka.18Kada ka ɗaukar wa kanka fansa ko ka riƙe shi da ƙiyayya gãba da wani cikin mutanenka, amma maimakon haka sai ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka. Ni ne Yahweh.
19Dole ku kiyaye dokokina. Kada ku bar dabbobinku su yi barbara da wasu irin dabbobi dabam. Kada ku cuɗa iri biyu lokacin da kuke shuka a gonarku. Kada ku sa tufafin da aka yi da ke da haɗe-haɗe iri biyu tare.
20Duk wanda ya kwana da yarinyar da take baiwa wadda aka alƙawarta wa miji, amma ba a fanshe ta ba ko 'yanta ta ba, dole a hukunta su. Ba za a kashe su ba saboda ba a 'yanta ta ba.21Sai mutumin ya kawo baikon laifinsa ga Yahweh a ƙofar shiga rumfar taruwa - rago domin hadayar laifi.22Daga nan firist zai yi kaffara domin sa da rago domin baikon laifi a gaban Yahweh, domin zunubin da ya aikata. Daga nan za a gaffarta masa zunubin da ya yi.
23Sa'ad da kuka zo cikin ƙasar kuma kuka dasa ko waɗanne irin itatuwa domin abinci, sai ku maida 'ya'yan itatuwansu haramtattu gare ku har shekaru uku. Ba za ku ci su ba.24Amma a cikin shekara ta huɗu dukkan amfaninsu za su zama mãsu tsarki, baikon yabo ga Yahweh.25A cikin shekara ta biyar za ku iya cin amfanin, domin kun jira saboda itatuwan su ƙara ba da 'ya'ya da yawa. Ni ne Yahweh Allahnku.
26Kada ku ci kowanne irin nama tare da jininsa a cikinsa. Kada ku tuntuɓi ruhohi game da abin da zai faru nan gaba, kada ku nemi ku mulki waɗansu ta wurin manyan ikoki ko duba.27Ba za ku aske gashin kanku a kewaye ko ku aske ƙarshen gemunku ba.28Kada ku yanke jikinku domin matattu ko ku yi tsaga a jikinku. Ni ne Yahweh.
29Kada ka kunyatar da ɗiyarka ta wurin sa ta karuwanci, ko ƙasar ta faɗa cikin karuwanci ƙasar kuma ta cika da mugunta.30Dole ku kiyaye Assabataina ku girmama mazaunina mai tsarki. Ni ne Yahweh.
31Kada ku juya wurin waɗanda suke magana da matattu ko da ruhohi, kada ku neme su, domin za su ƙazantar da ku. Ni ne Yahweh Allahnku.
32Dole ku tashi tsaye gaban wanda ya ke da furfura kuma ku gimama kasancewar dattijo. Dole ku ji tsoron Allah. Ni ne Yahweh.
33Idan bãƙo na zaune a wurinku cikin ƙasarku, kada ku cutar da shi.34Bãƙon da ke zaune tare da ku dole ya zama kamar haifaffen Ba-Isra'ile wanda ya ke zama a cikin ku, kuma dole ka ƙaunace shi kamar kanka, saboda dã ku bãƙi ne a cikin ƙasar Masar. Ni ne Yahweh Allahnku.
35Kada ku yi awo da ma'aunin ƙarya lokacin auna tsawo, nauyi ko yawa.36Dole ku yi amfani da ma'auni, madaidaici, kwanon gaskiya kofi na gaskiya. Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya fitar da ku daga ƙasar Masar.37Dole ku kiyaye dukkan farillaina da dokokina, kuma ku aikata su. Ni ne Yahweh.'"

20

1Yahweh ya yi magana da Musa cewa,2"Ka faɗa wa mutanen Isra'ila 'Duk wanda ke daga cikin jama'ar Isra'ila, ko bãƙon da ke zaune a cikin Isra'ila ya miƙa ɗaya daga cikin 'ya'yansa ga gunkin nan Molek, dole a kashe shi. Dole mutanen cikin ƙasar su jejjefe shi da duwatsu.

3Zan kuma sa fuskata gãba da wannan mutumin in kuma datse shi daga cikin mutanensa domin ya miƙa ɗansa ga Molek, domin ya ƙazantar da wurina mai tsarki ya kuma muzanta sunana mai tsarki.4Idan jama'ar ƙasar suka kulle idanunsu ga wannan mutumin a lokacin da ya ke miƙa ɗaya daga cikin 'ya'yansa ga Molek, Idan suka ƙi kashe shi,5Sa'an nan Ni da kaina zan sa fuskata gãba da wannan mutumin da danginsa, zan kuma datse shi da kuma dukkan wanda ya shiga karuwanci domin ya aikata karuwaci tare da Molek.
6Mutum wanda ya juya ga wa‌ɗ‌anda suke magana da matattu, ko ga waɗanda ke magana da ruhohi don ya yi karuwanci tare da su, Zan sa fuskata gãba da wannan mutumin; Zan datse shi daga cikin mutanen sa.7Don haka ku tsarkake kanku ku kuma zama da tsarki, domin Ni ne Yahweh Allahnku.
8Dole ku kiyaye umarnaina ku kuma aikata su. Ni ne Yahweh wanda ya ke‌ɓe ku a matsayin tsarkaka.9Duk wanda ya la'anta mahaifinsa ko mahaifiyarsa dole a kashe shi. Ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, to ya yi laifi kenan ya kuma cancanci mutuwa.
10Mutumin da ya yi zina da matar wani, wato, dukkan wanda ya yi zina da matar maƙwabcinsa - mazinacin da mazinaciyar dole ne a kashe su.11Idan mutum ya kwana da matar mahaifinsa, ya buɗe tsiraicin mahaifinsa. Da ɗan da matar mahaifinsa dole a kashe su. Alhakin jininsu na kansu.12Idan mutum ya kwana da matar ɗansa, dukkan su dole ne a kashe su, sun aikata abin ƙyama. Masu laifi ne sun kuma cancanci mutuwa.
13Idan mutum ya kwana da namiji, yadda ake yi da mace, dukkansu sun aikata mummunan abin ƙyama. Hakika tilas ne a kashe su. Masu laifi ne sun kuma cancanci mutuwa.14Idan mutum ya auri mace ya kuma auri mahaifiyarta, wannan mugunta ce. Dole ne a ƙone su, shi da matar dukka, domin ya zama babu mugunta a tsakiyarku.
15Idan mutum ya kwana da dabba, dole ne a kashe shi, dole kuma ku kashe dabbar.16Idan mace ta kusanci kowacce dabba domin ta kwana da ita, dole ku kashe macen da dabbar. wajibi ne ku kashe su. masu laifi ne sun kuma cancanci mutuwa.
17Idan mutum ya kwana da 'yar'uwarsa, ɗiyar mahaifinsa ko ɗiyar mahaifiyarsa, ya kuma buɗe tsiraicinta, ita kuma ta ga tsiraicinsa, abin kunya ne. Dole a datse su daga gaban jama'arsu, saboda ya kwana da ƴar'uwarsa. Dole ya ɗauki alhakin sa.18Idan mutum ya kwana da mace a lokacin jinin al'adarta har ya kwana da ita, har ya buɗe jinin da ke gudanowa daga jikinta, maɓulɓular jininta. Da mutumin da matar dole a datse su daga cikin jama'arsu.
19Ba za ka kwana da 'yar'uwar mahaifiyarka ba, ko kuma da 'yar'uwar mahaifinka, domin zaka ‌ƙas‌ƙantar da danginka na kusa. Wajibi ne ka ɗauki alhakinka.20Idan mutum ya kwana da bãbarsa, ya ƙasƙantar da kawunsa. Za su ɗ‌auki hakkin zunubinsu, za su kuma mutu babu 'ya'ya.21Idan mutum ya auri matar ɗan'uwansa sa'ad da ɗan'uwansa ke da rai, wannan ƙasƙanci ne. Ya ƙasƙantar da ‌ɗan'uwansa, kuma zan ɗauke wa 'ya'yansu duk wata mallaka da suka gada daga iyayensu.
22Saboda haka wajibi ne ku kiyaye dukka farillaina da dukkan dokokina; Dole ku yi biyayya da su domin kada ƙasar da Na ke kai ku domin ku zauna a ciki ta amayar da ku daga cikinta.23Ba za ku yi tafiya cikin al'adun al'umman da nake kora daga gabanku ba, domin sun aikata duk waɗannan abubuwan, kuma na ƙyamace su.
24Na faɗa maku, "Za ku gãji ƙasarsu; Zan ba ku ita ku mallaketa, ƙasa mai ɓulɓulo da madara da zuma. Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya keɓe ku daga sauran mutane.25Dole ne ku bambanta tsakanin dabbobi masu tsarki da marasa tsarki, da kuma tsakanin tsuntsaye marasa tsarki da masu tsarki. Wajibi ne ku ƙaurace wa ƙazantar da kanku da dabbobi ko tsuntsaye ko da kowacce irin halitta mai rarraffe akan ƙasa, wanda Na keɓe su a matsayin ƙazamtattu daga gare ku.
26Dole ne ku zama da tsarki, gama Ni, Yahweh, Mai Tsarki ne, kuma Na keɓe ku daga sauran mutane, saboda ku nawa ne.
27Mutum ko matar da ke yin magana da matacce ko suke yin magana da ruhohi dole ne a kashe su. Dole jama'a su jejjefe su da duwatsu. masu laifi ne sun kuma cancanci mutuwa.'"

21

1Yahweh ya cewa Musa: "Ka yi magana da firistoci, 'ya'ya maza na Haruna, ka ce masu, 'Kada a sami wani a cikinku da zai ƙazantar da kansa da gawar wanda ya mutu daga cikin mutanensa,2sai dai idan shi dangi ne na kusa - mahaifiyarsa, mahaifinsa, ɗansa, 'yarsa, ɗan'uwansa,3ko 'yar'uwarsa budurwa wadda ya ke rike da ita, tunda ya ke bata da miji - saboda ita yana iya ƙazantar da kansa.

4Amma kada ya ƙazantar da kansa saboda wa‌ɗansu dangi ta haka ya kuma ‌ɓata kansa.5Firistoci ba za su aske kansu ko su aske gefen gemun su, ko su yanka jikkunnansu ba.6Dole su zama tsarkaka ga Allahnsu, kada kuma su ƙasƙantar da sunan Allahnsu, gama firistoci ke mi‌ƙa hadayun Yahweh na abinci, gurasa ta Allahnsu. Don haka wajibi ne firistoci su zama da tsarki.
7Ba za su auri kowacce mace wadda take karuwa ba da wadda aka ɓata, Kuma ba za su auri mace wadda mijinta ya sake ta ba, domin su keɓaɓɓu ne ga Allahnsu.8Za ku keɓe shi, domin shi ne mai miƙa gurasa ga Allahnku. Dole ya zama da tsarki gare ku, domin Ni, Yahweh wanda ya tsarkake ku, Mai Tsarki ne.9Duk wata ɗiya ta firist da ta ƙazantar da kanta ta wurin zama karuwa ta ƙasƙantar da mahaifinta. Dole a ƙone ta.
10Wanda ya ke shi ne babban firist daga cikin "yan'uwansa, wanda aka zuba mai na keɓewa a kansa, wanda kuma aka tsarkake domin ya sa rigar babban firist, ba zai kwance gashin kansa ko ya keta tufafinsa ba.11Ba zai je wurin da akwai gawa ba ya kuma ƙazantar da kansa, ko da mataccen mahaifinsa ne ko mahaifiyarsa ce.12Babban firist ba zai bar harabar haikali ko ya ƙazantar da haikalin Allahnsa ba, domin an keɓe shi a matsayin babban firist ta wurin man keɓewa na Allahnsa. Ni ne Yahweh.
13Wajibi ne babban firist ya auri budurwa a matsayin matarsa.14Ba zai auri gwauruwa, ko sakakkiyar mace, ko mace wadda take karuwa ba. Ba zai auri irin waɗannan matan ba. Zai iya auren budurwa daga cikn jama'arsa,15domin kada ya ƙazantar da 'ya'yansa daga cikin jama'arsa, domin Ni ne Yahweh, wanda ya maishe shi tsarkakakke.'"
16Yahweh ya yi magana da Musa, ya ce,17"Ka yi magana da Haruna ka faɗa masa, 'Dukkan wanda aka samu da wata nakasar jiki cikin zuriyarka a dukkan tsararrakinsu, ba zai matso kusa domin ya miƙa abinci ga Allahnsa ba.
18Kowanne mutum da ke da nakasa a jiki kada ya kusanci Yahweh, irin wannan makahon ko mutumin da bai iya tafiya, shi da ya ke da nakasa a jiki ko fuskar,19mutumin da ke da nakasa a hannu ko a ƙafa,20mutumin da ke da ƙusumbi a bayansa ko shanyayye ko wãda, ko mutumin da ke da hãkiya a idanunsa, ko ya ke da cuta, gyambo, ƙurji, ko rauni a mazakutta.21Ba wani mutum daga cikin zuriyar Haruna firist mai nakasa a jikinsa da zai matso kusa domin ya miƙa baye-bayen da ake miƙawa da wuta ga Yahweh. Irin wannan mutumin mai naƙasa a jiki; kada ya zo kusa domin ya miƙa gurasar Allahnsa.
22Ya iya cin abincin Allahnsa, ko daga cikin mafi tsarki ko kuma daga cikin mai tsarki.23Duk da haka, Ba zai shiga daga cikin labulen ko ya zo kusa da bagadi ba, saboda yana da naƙasa a jikinsa, domin kada ya ƙazantar da tsattsarkan wurina, gama Ni ne Yahweh, wanda ya tsarkake su."'24Haka Musa ya fa‌ɗawa Haruna wa‌ɗ‌annan maganganu, ga 'ya'yansa, da kuma ga dukkan mutanen Isra'ila.

22

1Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,2"Ka yi magana da Haruna da 'ya'yansa maza, ka fa‌ɗa masu su kiyaye kansu daga kayayyaki masu tsarki na mutanen Isra'ila, waɗanda suka keɓe gare ni. Ba za su ƙasƙantar da sunana mai tsarki ba. Ni ne Yahweh.3Ka faɗa masu, 'Idan wani daga cikin zuriyarku cikin dukkan tsararrakinku ya kusanci kayayyaki masu tsarki da jama'ar Isra'ila suka keɓe ga Yahweh, a sa'ad da ya ke marar tsarki, wannan mutumin dole a datse shi daga gabana: Ni ne Yahweh.

4Kada wani daga cikin zuriyar Haruna wanda ke da cutar fata, ko mai miki da ke zubar da ruwa daga jikinsa, ya ci ko ɗaya daga wa‌ɗannan hadayun da aka miƙa ga Yahweh har sai ya tsarkaka. Dukkan wanda ya taɓa wani abu marar tsarki ta wurin taɓa gawa, ko ta wurin taɓa mutum mai zub da maniyyi,5ko kowacce dabba mai rarrafe data ƙazantar da shi, ko kowanne mutum ɗaya maida shi marar tsarki, ko dai kowacce irin ƙazanta ta zama-6daga nan firist wanda ya taɓa kowanne abu marar tsarki zai zama marar tsarki har maraice. Ba zai ci duk wani abu mai tsarki ba, har sai ya wanke jikinsa a cikin ruwa.
7Sa'ad da rana ta fa‌ɗi, zai zama tsarkakakke. Bayan rana ta faɗi ya iya ci daga cikin tsarkakakkun abubuwa, domin su abincinsa ne.8Ba zai ci duk abin da aka same shi matacce ba ko abin da naman jeji ya kashe, wanda ta wurin haka zai ƙazantar da kansa. Ni ne Yahweh.9Wajibi ne firistoci su bi umarnaina, domin kada su yi zunubi, su mutu domin muzanta ni. Ni ne Yahweh wanda ke tsarkake su.
10Kada wanda ba daga iyalin firist ya ke ba, duk da baƙon da ya sauka a gidan firist ko barorinsa, ya ci duk abin da ya ke tsatstsarka.11Amma idan firist ya sayi wani bawa da ku‌ɗinsa, wannan bawan na iya ci daga cikin abin da aka keɓe ga Yahweh. Iyalan gidan firist da kuma bayin da aka haifa a gidansa, za su iya cin waɗannan abubuwan tare da shi.
12Idan ɗiyar firist ta auri wani mutum wanda ba firist ba, ba za ta ci ko ‌ɗaya daga cikin baye-bayen gudunmuwa mai tsarki ba.13Amma idan ɗiyar firist ɗin gwauruwa ce, ko kuma sakakkiya, kuma idan bata da ɗa, kuma idan ta koma ta zauna a gidan mahaifinta kamar a lokacin ƙuruciyarta, za ta iya ci daga cikin abincin mahaifinta. Amma kada wani wanda ba daga cikin iyalin firist ya ke ba yaci abincin firist.
14Idan mutum yaci abinci mai tsarki ba da sani ba, dole ya biya firist abin da ya ci; wajibi ne ya ƙara kashi ɗaya bisa biyar akan abin ya kuma maida wa firist.15Mutanen Isra'ila ba za su ƙazantar da abubuwa masu tsarki waɗanda suka ‌ɗaga sama suka miƙa ga Yahweh ba.16Su jawowa kansu ɗaukar zunubin da zai sa su yi laifin cin abinci mai tsarki, gama Ni ne Yahweh wanda ya ke tsarkake su."
17Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,18"Ka yi magana da Haruna shi da 'ya'yansa maza, da dukkan mutanen Isra'ila. Ka fa‌ɗ‌a masu, 'Duk Ba-Israi'le, ko bãƙon da ke zaune cikin Isra'ila, lokacin da suka kawo hadaya- kodai ta cika wa'adi, ko ta bayarwar yadda rai, ko idan sun kawo hadayar ƙonawa ga Yahweh,19Idan za ta zama karɓaɓɓiya, dole su miƙa dabba namiji marar aibu daga cikin garken shanu, tumaki, ko awaki.
20Amma kada ku miƙa duk wani abu mai aibu. Ba zan karbe su a maimakon ku ba.21Kowanne mutum da ya miƙa hadaya ta salama daga cikin garke ko tumaki ga Yahweh don cika wa'adi, ko a matsayin bayarwar yardar rai, dole ta zama marar aibu kafin a kar‌ɓe ta. Kada a sami nakasa cikin dabbar.
22Ba zaku miƙa mani dabbobi makafi ba, ko guragu, ko naƙasassu, ko masu kirci, ko masu ƙuraje, ko tabbai. Ba za ku miƙa waɗannan ga Yahweh a matsayin hadaya ta ƙonawa a kan bagadi ba.23Zaku iya miƙa bayarwar yardar rai da sã, ko da ‌ɗ‌an rago da ke da naƙasa ko ƙanƙane, amma bayarwa irin wannan ba za ta karɓu domin cika wa'adi ba.
24Kada ku miƙa wa Yahweh kowacce dabbar da ke da ƙurji, gurzajje, yayyagagge, ko dandaƙaƙƙe ba. Ba za ku yi wannan a cikin ƙasarku ba.25Kada kubar baƘo ya miƙa maku gurasa ga Allahnku. Wa‌ɗannan dabbobin naƙasassu ne suna kuma da aibu a cikin su, ba za'a karɓe su a madadinku ba."
26Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,27"Sa'ad da aka haifi ɗan maraki, ko ɗan tunkiya ko ɗan akuya, dole ya zauna tare da mahaifiyarsa har kwana bakwai. A kwana na takwas, a iya karbar shi a matsayin hadayar ƙonawa da wuta ga Yahweh.
28Ba za ku kashe saniya ko tunkiya tare da ƙananunsu, dukka a rana ‌ɗ‌aya ba.29Duk sa'ad da kuke miƙa hadaya ta godiya ga Yahweh, dole ku miƙa ta ta karɓaɓɓiyar hanya.30Dole ku cinye naman hadayar a ranar da aka miƙa ta. Ba za ku rage komai daga ciki zuwa safiya ba. Ni ne Yahweh.
31Dole ne ku kiyaye dokokina ku kuma aikatasu dukka. Ni ne Yahweh.32Kada ku ƙasƙantar da sunana mai tsarki. Dole ne a san ni a matsayin mai tsarki ta wurin jama'ar Isra'ila. Ni ne Yahweh mai tsarkake ku,33wanda ya fishsheku daga ƙasar Masar domin in zama Allahnku: Ni ne Yahweh.

23

1Yahweh ya fa‌ɗa wa Musa:2"Ka yi magana da mutanen Isra'ila, kace masu, 'wa‌ɗannan su ne ƙayyadaddun bukukuwanku ga Yahweh, wa‌ɗ‌anda dole ku shaida su a matsayin tattaruwa mai tsarki; su ne bukukuwana na yau da kullum.

3Za ku iya yin aiki kwanaki shida, amma rana ta bakwai asabar ce ta cikakken hutu, tattaruwa mai tsarki. Ba za ku yi wani aiki ba domin asabar ce ta Yahweh a cikin dukkan wuraren da kuke zaune.
4Wa‌ɗannan su ne ƙayyadaddun bukukuwa na Yahweh, tattaruwa mai tsarki da dole ku sanar a ƙayyadaddu lokuttansu:5A wata na farko, a rana ta goma sha hu‌ɗ‌u ga wata washegari, ranar bukin ƙetarewa ne na Yahweh.6A rana ta goma sha biyar ga wannan watan ranar za ta zama ranar bukin gurasa marar gami ga Yahweh. Dole za ku ci gurasa marar gami har tsawon kwana bakwai.
7A rana ta farko za ku keɓe kanku domin ku taru wuri ‌ɗaya; ba za ku yi kowanne irin aiki da kuka saba yi ba.8Za ku miƙa bayarwar abinci ga Yahweh har kwana bakwai. Kwana na bakwai tattaruwa ce keɓaɓɓiya ga Yahweh, kuma a wannan rana wajibi ne ba za ku yi kowanne aiki da kuka saba yi ba.
9Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,10"Ka yi magana da mutanen Isra'ila ka ce masu, 'Lokacin da kuka shiga cikin ƙasar da zan ba ku, Sa'ad da kuka yi girbi, wajibi ne ku kawo dami na nunar fari na hatsin ga firist.11Shi zai ‌ɗ‌aga damin hatsin a gaban Yahweh ya kuma miƙa shi gare shi, domin a karɓe shi a maimakon ku. A kwana ‌ɗaya bayan assabacin firist zai ‌ɗaga abin ya kuma gabatar da shi gare ni.
12A ranar da kuka ɗaga damin hatsin kuka kuma miƙa shi gare ni, wajibi ne ku miƙa ɗan rago mai shekara ɗaya kuma marar naƙasa hadaya ta ƙonawa ga Yahweh.13Hadaya ta gari wajibi ne ta zama kashi biyu bisa goma na lallausan gari da aka gauraya da mai, bayarwar da aka yi da wuta ga Yahweh. Domin ta bada ƙamshi mai da‌ɗi, kuma tare da ita hadaya ta abin sha, awo hu‌ɗ‌u na ruwan inabi.14Ba za ku ci gurasa, ko gasashshen nama, ko ‌ɗanyen hatsi ba, har sai ranar da kuka kawo sadakar ga Allahnku ta kewayo. Wannan farilla haka zata zama din-din din cikin dukkan tsararrakin jama'arku, a cikin dukkan wurin da kuke zaune.
15Tun daga kwana ‌ɗaya bayan ranar asabaci-Wannan ce ranar da ku ka kawo damin hatsi a matsayin sadaka ta ‌ɗagawa - ku ƙirga makonni bakwai cikakku.16Dole ku ƙirga kwanaki hamsin, wanda zai kasance rana bayan asabar ta bakwai. Wajibi ne ku miƙa bayarwar sabon hatsi ga Yahweh.
17Dole ku ‌ɗibo curi biyu daga cikin gidajenku da aka yi da kashi biyu bisa goma na garwa. Wajibi ne a yi su da lallausan gari da aka yi da gami; zasu zama bayarwar nunar fari ta ɗagawa ga Yahweh.18Za ku miƙa gurasar tare da 'yan raguna bakwai masu shekara ‌ɗ‌aya marasa aibu, ‌ɗan maraƙi ɗaya, da raguna biyu. Dole su zama hadaya ta ƙonawa ga Yahweh, tare da hadayar garin da hadaya ta sha, bayarwar da aka yi da wuta mai kuma bada ƙanshi ga Yahweh.
19Za ku miƙa bunsuru ɗaya domin hadaya ta zunubi, ku kuma miƙa 'yan raguna biyu masu shekara ‌ɗaya hadaya, a matsayin hadaya ta zumunci.20Wjibi ne firist ya ka‌ɗa su tare da gurasar nunar fari a gaban Yahweh, ya kuma miƙa su gare shi a matsayin bayarwa tare da 'yan raguna biyu. Za su zama baye-baye masu tsarki na Yahweh domin firist.21Dole kayi shaida a wannan ranar. Za'a ha‌ɗa taro mai tsarki, kuma kada kuyi aikin da kuka saba yi. Wannan zai zama farilla na din-din din cikin dukkan tsararrakin jama'arku a cikin dukkan wuraren da kuke zaune.
22Lokacin da kuka girbe amfanin gonarku, baza ku girbe har ƙurewar gonakinku ba, ba kuma za ku yi kalar gonakinku ba. Dole ne ku rage wa matalauta da baƙi su. Ni ne Yahweh Allahnku'".
23Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,24"Ka yi magana da mutanen Isra'ila ka faɗi masu, 'A wata na bakwai, ranar farko ta wannan watan zata zama ranace ta cikakken hutu gare ku, ranar tunawa tare da busa sarewa, da kuma ranar taro mai tsarki.25Ba za ku yi wani aiki ba, kuma dole ne ku miƙa hadaya da wuta ga Yahweh."'
26Sai Yahweh ya yi magana da Musa, cewa27"Yanzu ranar goma ga wannan wata na bakwai ita ce Ranar Kaffara. Za ta kasance tattaruwa mai tsarki, kuma dole ku ƙasƙantar da kanku ku kuma miƙa baiko da wuta ga Yahweh.
28Ba za ku yi wani aiki a wannan rana ba gama Ranar Kaffara ce, ku yi kaffara domin kanku a gaban Yahweh Allahnku.29Dukkan wanda bai ƙasƙantar da kansa a wannan rana ba dole a datse shi daga cikin mutanensa.
30Dukkan wanda ya yi wani aiki a wannan rana, Ni, Yahweh, zan hallakar da shi daga cikin mutanensa.31Ba za ku yi kowanne irin aiki a wannan rana ba. Wannan zai zama farilla ta din-din din cikin dukkan tsararrakin mutanenku a dukkan wuraren da kuke zama.32Ranar nan zata zama Assabat ta cikakken hutu gare ku, kuma dole ku ƙasƙantar da kanku a rana ta tara ga watan da maraice. Daga maraice zuwa maraice za ku kiyaye Assabacinku."
33Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,34"Ka yi magana da mutanen Isra'ila, cewa, 'Rana ta goma sha biyar ga wata na bakwai zata zama ranar bukukuwan bukkoki ga Yahweh. Za ku kiyaye shi har kwanaki bakwai.
35Za ku yi tattaruwa mai tsarki a rana ta fari. Ba za ku yi aikin da kuka saba yi ba.36Tsawon kwana bakwai za ku miƙa hadaya ta wurin wuta ga Yahweh. A rana ta takwas za ku yi taro mai tsarki, kuma dole ne ku miƙa hadaya ta wuta ga Yahweh. Wannan babban taro ne, kuma ba za ku yi aikin da kuka saba yi ba.
37Waɗannan su ne ƙayyadaddun bukukuwa ga Yahweh, waɗanda zaku shaida a matsayin tattaruwa mai tsarki ku miƙa hadayu na wuta ga Yahweh, bayarwar ƙonawa da kuma bayarwar gari, hadaya da kuma bayarwar abin sha, kowacce a ranar ta.38Waɗannan bukukuwa ƙari ne ga Assabar ta Yahweh da kuma kyaututtukanku, dukkan alƙawuranku, da kuma dukkan baye-bayenku na yardar rai da kuka ba Yahweh.
39Dangane da bukukuwan bukkoki, a ranar goma sha biyar ga wata na bakwai, lokacin da kuka gama tattara albarkun ƙasar, Dole ku kiyaye wannan bukukuwa ga Yahweh har kwana bakwai. Ranar farko zata zama ta cikakken hutu, haka rana ta takwas ma zata kasance ranar cikakken hutu.
40A rana ta fari za ku ‌ɗauka daga cikin mafi kyau na 'ya'yan itatuwanku, rassan itatuwan dabino, da rassa masu ganyayyaki na itatuwa masu ƙarfi, d‌a ciyayi masu yaɗo daga rafuka, zaku yi murna a gaban Yahweh Allahnku har kwana bakwai.41Tsawon kwana bakwai a kowacce shekara, wajibi ne ku yi wannan buki ga Yahweh. Wannan zai zama farilla gare ku cikin dukkan tsararrakin mutanenku a dukkan wuraren da kuke zama. Dole ne ku yi bukin nan a wata na bakwai.
42Wajibi ne ku zauna cikin bukkoki har kwana bakwai. Dukkan haifaffen gidan Isra'ila dole ya zauna cikin ƙananan bukkoki tsawon kwana bakwai,43domin zuriyarku, daga tsara zuwa tsara, su koyi yadda nasa mutanen Isra'ila suka zauna a cikin irin waɗannan bukkokin lokacin da na jagorance su daga cikin ƙasar Masar. Ni ne Yahweh Allahnku."'44Ta haka fa, Musa ya sanar wa mutanen Isra'ila ƙayyadaddun bukukuwa ga Yahweh.

24

1Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,2"Ka umurci mutanen Isra'ila su kawo maka mai mai tsabta da aka tatso daga zaitun don a riƙa amfani dashi cikin fitilu, domin su yi ta bada haske ba yankewa.

3A wajen labulen a gaban akwatin alƙawari cikin rumfar taruwa, wajibi ne ga Haruna daga maraice zuwa safiya, ya sa fitila ta yi ta ci a gaban Yahweh. Wannan zai zama farillanku na din-din din cikin dukkan tsararrakin jama'arku.4Dole babban firist ya sa fitilu su yi ta ci a gaban Yahweh, fitilun za su kasance a kan ma‌ɗ‌orin da aka yi da zinariya tsantsa.
5Ka ‌ɗauki lallausan gari ka yi curin gurasa goma sha biyu dashi. Kowanne curi a yi shi da adadin kashi biyu bisa goma na garwa.6Sa'an nan wajibi ne ku jera su a layi biyu, shida a kan kowanne layi, a kan tebur na zinariya mai tsabta a gaban Yahweh.
7Wajibi ne ku sa turare mai tsabta a kan kowanne jerin gurasa a maimakon baiko. Wannan turaren za a ƙone shi domin Yahweh.8Kowacce Assabar babban firist ya ajiye gurasa a gaban Yahweh a maimakon mutanen Isra'ila, a matsayin alama ta alƙawari na har abada.9Wannan bayarwar zata zama domin Haruna da 'ya'yansa maza, kuma za su ci gurasar a wurin da ya ke mai tsarki, domin rabo ne daga baye-baye ga Yahweh da aka miƙa ta wuta."
10Ya zama fa ɗan wata mata Ba-isra'iliya, wanda mahaifinsa Ba-masare ne, ya tafi tare da mutanen Isra'ila. Wannan ɗan matar Ba-isra'iliya ya yi faɗa da mutumin Isra'ila a cikin zango.11Wannan ɗan matar Ba-isra'iliya ya zagi sunan Yahweh ya kuma la'anta Allah, domin haka jama'a suka kawo shi gaban Musa. Sunan mahaifiyarsa Shelomit, ɗiyar Dibri, daga kabilar Dan.12Suka tsare shi a kurkuku har sai sun ji abin da Yahweh da kansa zai furta nufinsa a kansu.
13Daga nan Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,14"Ka ɗauki mutumin da ya la'anta Allah bayan sansani. dukkan wanda ya ji shi dole su ɗibiya hannayensu a kansa, daga nan dukkan taron jama'a su jejjefe shi.
15Dole ka bayyanawa mutanen Isra'ila ka ce, "Duk wanda ya la'anci Allahnsa dole ya ɗauki alhakin laifinsa.16Shi wanda ya saɓi sunan Yahweh hakika dole a kashe shi. Dukkan taron jama'a dole su jejjefe shi da dutse, ko shi baƙo ne ko haifaffen Ba-Isra'ile. Duk wanda ya yi saɓon sunan Yahweh, dole a kashe shi.
17Duk wanda ya bugi wani mutum har ya mutu, lallai dole shi ma a kashe shi.18Idan wani ya bugi dabbar wani har ta mutu, dole ya mayar, rai maimakon rai.
19Idan wani ya yi wa maƙwabcinsa rauni, dole ayi masa yadda ya yi wa maƙwabcinsa:20tsaga maimakon tsaga, ido domin ido, haƙori domin haƙori. Kamar yadda ya jawo lahani ga mutum, to haka shi ma za'a yi masa.21Duk wanda ya kashe dabba dole ya biya, kuma duk wanda ya kashe mutum dole shi ma a kashe shi.
22Dole ku kasance da doka iri ɗaya domin baƙo da wanda ya ke haifaffen Ba-Isra'ile, gama Ni ne Yahweh Allahnku.'"23Sai Musa ya yi magana da mutanen Isra'ila, mutanen kuma suka fito da mutumin wajen sansani, wanda ya la'anta Yahweh. Suka jejjefe shi da duwatsu. Mutanen Isra'ila suka aiwatar da dokar Yahweh ta hannun Musa.

25

1Yahweh ya yi magana da Musa akan tsaunin Sinai, cewa,2"Ka yi magana da mutanen Isra'ila ka ce masu, "Sa'ad da kuka zo cikin ƙasa wadda na ba ku, daga nan dole ƙasar za ta kiyaye Assabat domin Yahweh.

3Dole ku shuka gonarku shekaru shida, shekaru shida kuma dole ku gyara gonarku ta inabi ku tattara amfaninta.4Amma a cikin shekara ta bakwai, dole a kula da Assabat mai saduda ta hutu, Assabat domin Yahweh. Ba za ku shuka gonar ba ko ku gyara gonar inabinku ba.
5Ba za ku shirya girbe duk abin da ya tsiro don kansa ba, kuma ba za ku shirya girbin inabin da ya tsiro a kuringar da baku gyara ba. Wannan za ta zama shekara mai saduda ta hutawa domin ƙasar.6Duk tsiron da ƙasar da baku aikata ba ta bayar lokacin Assabat na ƙasar zai zama abinci domin ku. Ko, 'ya'yanku maza, da bayinku mata, da bayin da aka yi hayarsu, da baƙi da ke zaune tare da ku za ku iya tattara abinci,7dabbobinku kuma da bisashenku za su iya cin amfanin da ƙasar ta bayar.
8Dole ku lisafta Assabat guda bakwai na shekaru, wato, bakwai sau shekaru bakwai, wato akwai Assabat bakwai na shekaru, jimilla duka shekaru arba'in da tara ke nan.9Sa'an nan za ku busa ƙaho da ƙarfi ko'ina a rana ta goma a watan bakwai. A ranar kaffara dole ku busa ƙaho ko'ina a cikin ƙasarku.
10Dole ku keɓe shekara ta hamsin ga Yahweh kuma ayi shelar 'yanci ko'ina a ƙasar ga dukkan mazaunanta. Zata zama ranar mayarwa domin ku, inda kowacce mallaka da bayi dole za su koma wurin iyalinsu.
11Shekara ta hamsin zata zama shekarar mayarwa a gare ku. Ba za ku shuka ko shirya girbi. Ko cin duk abin da ya tsiro da kansa ba, kuma ba za ku tattara inabi da ya tsiro a kuringai da baku gyara ba.12Gama Shekarar 'Yanci ce, wadda za ta zama mai tsarki domin ku. Dole kuci amfanin da ya tsiro don kansa a gonaki.
13Dole ku mayar wa da kowanne mutum mallakarsa a shekarar 'Yanci.14Idan ka sayar da gona ga maƙwabcinka ko ka sayi gona a wurin maƙwabcinka, kada ku cuci ko ku zalunci juna.
15Idan ka sayi gona daga maƙwabcinka, sai ka yi la'akari da shekaru da amfanin da za a girbe har zuwa shekarar gaba ta 'Yanci. Maƙwabcinka da ke sayar maka da gonar dole ya kula da wannan shi ma.16Yawan shekarun har zuwa shekarun 'Yanci zai ƙara tamanin ƙasar, gwargwadon ƙarancin shekarun za a rage tamanin ta, saboda yawan girbin da ƙasar zata bayar domin sabon mai gonar yana alaƙa da yawan shekaru kafin shekarar 'Yanci ta gaba.17Ba za ku cuci ko ku zalunci juna ba; maimakon haka dole ku girmama Allahnku, gama Ni ne Yahweh Allahnku.
18Domin wannan dole ku kiyaye umarnaina, ku kiyaye dokokina, kuma ku aiwatar da su. Daga nan za ku zauna cikin ƙasar lafiya.19ƙasa za ta bada amfaninta, kuma za ku ci ku ƙoshi kuma ku zauna can cikin tsaro.
20Za ku iya cewa, "Me zamu ci cikin shekara ta bakwai? Duba, ba dama mu shuka ko mu tattara amfaninmu ba."21Zan umarci albarkata ta zo bisanku a cikin shekara ta shida, kuma zata bada isasshen amfani har shekaru uku.22Za ku shuka cikin shekara ta takwas kuma ku ci gaba da cin abincin da kuka ajiye a shekarun baya. Har lokacin girbi na shekara ta tara ta zo, za ku ci daga tanajin ajiyar da kuka yi a shekarun baya.
23Ba za a sayar da ƙasa ga wani ya zama sabon mai ita ta din-din din ba, saboda ƙasa tawace. Dukkanku bãƙi ne masu zama na ɗan lokaci a ƙasa ta.24Dole ku kula da haƙin fansa domin dukkan ƙasar da kuka mallaka; dole ku bari a sake sayen ƙasar ga iyalin daga wanda ya saye ta.25Idan ɗan'uwanka Ba-Isra'ile ya zama talaka kuma akan wannan dalili ya sayar da wata mallaka tasa, daga nan danginsa na kusa zai iya zuwa ya fanshi mallakar da ya sayar maka.
26Idan mutum ba shi da ɗan'uwa da zai fãnshi mallakarsa, amma idan ya azurta har zai iya fãnsar ta,27daga nan zai iya lissafta shekaru tun lokacin da aka sayar da ƙasar sai ya biya sauran ga mutumin da ya sayar wa. Daga nan zai iya dawo wa ga mallakarsa.28Amma idan bai iya dawo da ƙasar domin kansa ba, daga nan ƙasar da ya sayar za ta kasance cikin mallakar shi wanda ya saye ta har zuwa lokacin shekarar 'Yanci. A shekarar 'Yanci, ƙasar zata koma ga mutumin da ya sayar da ita, ainihin mai ita kuma zai koma ga mallakarsa.
29Idan mutum ya sayar da gidansa a cikin birni mai ganuwa, daga nan zai iya ya fãnshar sa cikin dukkan shekara bayan ya sayar. Gama a cikin cikar shekara yana da 'yancin fãnsa.30Idan ba a fãnshi gidan kamin cikar shekara ba, daga nan gidan da ke cikin birni mai ganuwa zai zama mallaka ta din-din din ga wanda ya saya shi da zuriyarsa. Ba za a mayar da shi cikin shekara ta 'Yanci ba.
31Amma gidajen ƙauyukan da ba su da gãnuwa kewaye da su za a yi lissafinsu a matsayin filin ƙasa. Za a iya fãnsarsu kuma dole a dawo da su a shekarar 'Yanci.32Amma, gidajen da Lebiyawa suka mallaka cikin birane za su iya fãnsarsu a kowanne lokaci.
33Idan ɗaya daga cikin Lebiyawa bai fãnshi gidan da ya sayar ba, daga nan gidan da aka sayar a cikin birni a inda ya ke dole a dawo da shi cikin shekarar 'Yanci, gama gidajen biranen Lebiyawa mallakarsu ne a cikin mutanen Isra'ila.34Amma filayen da ke kewaye da biranen ba za a sayar da su ba saboda mallakar Lebiyawa ne na din-din din.
35Idan ɗan ƙasarku ya zama talaka, yadda ba zai iya biyan buƙatar kansa ba, daga nan dole ka taimake shi kamar yadda za ka taimaki bãƙo ko wani dabam da ke zaune kamar na waje a cikinku.36Kada ka caje shi da ruwa ko ka yi ƙoƙarin samun riba daga gare shi ta kowacce hanya, amma ka girmama Allahnka domin ɗan'uwanka ya ci gaba da zama tare da kai.37Kada ka bashi bashin kuɗi da ruwa, ko ka sayar masa abinci don samun riba.38Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya fito da ku daga ƙasar Masar, domin in baku ƙasar Kan'ana, kuma in zama Allahnku.
39Idan ɗan ƙasarku ya zama talaka har ya sayar da kansa gare ka, kada kasa shi ya yi aiki kamar bawa. Ka kula da shi kamar baran haya.40Dole ya zama kamar wanda ya ke zama da kai na ɗan lokaci. Zai yi hidima tare da kai har zuwa shekarar 'Yanci.41Daga nan zai tafi daga gare ka, shi da 'ya'yansa tare da shi, zai koma wurin iyalinsa da mallakar kakanninsa.
42Gama su bayina ne waɗanda na kawo daga ƙasar Masar. Ba za a sayar da su kamar bayi ba.43Kada ku mallake su da tsanani, amma dole ku girmama Allahnku.44Ga zancen bayinku maza da mata, waɗanda za ku samu daga al'umman da ke kewaye da ku, za ku iya sayen bayi daga gare su.
45Za ku iya sayen bayi daga bãƙin da ke zaune a wurin ku, wato, daga iyalin da ke tare da ku, 'ya'yan da aka haifa cikin ƙasarku. Sun zama mallakarku.46Za ku iya tanada wa 'ya'yanku irin waɗannan bayi su zama gãdo bayan ku, su riƙe su a matsayin mallaka, su kuma za su zama bayi har abada, amma baza ku yi mulkin 'yan'uwanku cikin mutanen Isra'ila da tsanani ba.
47Idan bãƙo ko wani da ke zama cikinku na ɗan lokaci ya azurta, ɗan'uwanku kuma Ba-Isra'ile ya talauce ya sayar da kansa ga bãƙon, ko ga wani cikin iyalin bãƙon,48bayan da an sayi Ba-Isra'ilenku, za a iya fãnsarsa. Wani daga cikin iyalinsa zai iya fãnsar sa.
49Zai iya zama kawun mutumin ko ɗan kawunsa, wanda ya fanshe shi, ko wani wanda ya ke kusa da iyalinsa. Ko, idan ya azurta, zai iya fãnsar kansa.50Dole ya yi ciniki da wanda ya saye shi; dole su lisafta shekarun daga shekarar da ya sayar da kansa ga wanda ya saye shi har zuwa shekarar 'Yanci. Farashin da aka fãnshe shi zai zama dai-dai da yawan wanda aka biya baran da akayi hayar sa, zai iya ci gaba da yin aiki har wasu shekaru ga wanda ya sawo shi.
51Idan har yanzu akwai sauran shekaru da yawa kafin shekarar 'Yanci, dole ya biya kuɗin domin fãnsarsa bisa ga adadin waɗannan shekaru.52Amma idan shekarun sun ragu kaɗan ga shekarar 'Yanci, daga nan dole ya yi ciniki tare da mai sayensa ya nuna yawan shekarun da suka ragu kafin shekarar 'Yanci, kuma dole ya biya domin fãnsarsa bisa ga yawan shekarun.
53Dole a kula da shi kamar mutumin da aka yi hayarsa shekara bayan shekara. Dole ku tabbatar ba a tsananta masa da tsanani ba.54Idan ba a fãnshe shi ta waɗannan hanyoyi ba, daga nan zai ci gaba da bauta har zuwa shekarar 'Yanci, shi da 'ya'yansa tare da shi.55A gare ni mutanen Isra'ila bayi ne. Bayi na ne waɗanda na fisshe su daga ƙăsar Masar. Ni ne Yahweh Allahnku.'"

26

1"Ba za ku yi gumakai ba, kuma ba za ku ɗaga sassaƙaƙƙiyar siffa ko keɓaɓɓen ginshiƙin dutse, kuma ba za ku kafa kowacce irin sassaƙaƙƙiyar siffa ta dutse a cikin ƙasarku da za ku durƙusa masa ba, gama ni ne Yahweh Allahnku.2Dole ku kiyaye assabataina ku girmama rumfar sujadata. Ni ne Yahweh.

3Idan kuka yi tafiya cikin umarnaina kuka kiyaye dokokina kuma kuka yi biyayya da su,4daga nan zan ba ku ruwan sama a lokacinsa; ƙasar kuwa zata bada amfaninta, itatuwan gonaki kuma za su bada 'ya'yansu.
5Za ku yi ta girbi har lokacin girbin 'ya'yan inabi, girbin inabi kuma zai ci gaba har lokacin shuka. Za ku ci abincinku ku ƙoshi kuma ku zauna lafiya inda kuka yi gida a cikin kasarku.6Zan bada salama cikin ƙasar; za ku kwanta ba abin da zai tsoratar da ku. Zan kawar da mugayen dabbobi daga ƙasar, takobi kuma ba zata ratsa ta ƙasarku ba.
7Za ku runtumi maƙiyanku, kuma za su faɗi a gaban ku ta wurin takobi.8Mutum biyar ɗinku za su runtumi ɗari, mutum ɗarinku kuma za su runtumi mutum dubu goma; maƙiyanku za su faɗi a gabanku ta wurin takobi.
9Zan dube ku da idon rahama in sa ku hayayyafa in riɓanɓanya ku; zan tabbatar da alƙawarina tare da ku.10Za ku ci abinci ku ajiye shi tsawon lokaci. Za ku fitar da abincin da kuka ajiye saboda kuna buƙatar ɗaki domin ku ajiye sabon hatsi.
11Zan kafa mazaunina a tsakiyar ku, ba kuwa zan ƙi ku ba.12Zan yi tafiya tare da ku in kuma zama Allahnku, kuma za ku zama mutanena.13Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar, domin kada ku zama bayinsu. Na karya sandunan karkiyarku na sa ku yi tafiya madaidaiciya.
14Amma idan ba za ku saurare ni ba, kuma ba za ku yi biyayya da dukkan dokokin nan ba,15idan kuma kuka yi watsi da dokokina kuma kuka ƙi umarnaina, domin kada ku yi biyayya da dukkan dokokina, amma kuka karya alƙawarina -
16- idan kuka yi waɗannan abubuwa, daga nan nima zan yi wannan a gare ku: Zan sa tsõro a kan ku, cututtuka da zazzaɓin da zai lalatar da idanunku rayuwa zata zama da wahala. Za ku shuka irinku a banza, amma maƙiyanku ne za su ci amfaninsu.17Zan sa fuskata gãba da ku, maƙiyanku za su fi ƙarfinku. Mutanen da suke ƙin ku za su mallake ku. Za ku yi gudu ko da wani bai kore ku ba.
18Idan bayan dukkan wannan baku saurare ni ba, daga nan zan ƙara hukunta ku da tsanani sau bakwai domin zunubanku.19Zan karya gimanku cikin ikonku. Zan sa sama da ke kanku ta zama kamar ƙarfe ƙasarku kuma kamar tagulla.‌20Ƙ‌arfinku zai zama ba amfani, saboda ƙasarku ba zata bada amfaninta ba, itatuwan ‌ƙasar kuma ba za su bada 'ya'yansu ba.
21Idan kuka yi tafiya gãba da ni ba ku saurare ni ba, Zan kawo nushi sau bakwai akan ku, bisa ga yawan zunubanku.22Zan aiko maku da mugayen namomin jeji gãba da ku, waɗanda za su sace 'ya'yanku, su hallaka dabbobinku, su sa ku zama kaɗan. Hanyoyin kuma za su zama ba masu gilmawa.
23Idan baya ga waɗannan duk da haka ba ku karɓi gyara na ba kuka ci gaba da tafiya cikin yin adawa da ni,24daga nan ni ma zan yi tafiya cikin yin adawa da ku, kuma Ni da kaina zan hukunta ku sau bakwai saboda zunubanku.
25Zan kawo takobi a kanku a kashe ku da ramuwa domin karya alƙawari. Za a tattara ku tare cikin biranenku, can zan aikar da cuta a wurin, za a miƙa ku cikin hannun maƙiyanku.26Idan na datse abincin da kuka tanada, mata goma za su dafa abinci a murhu ɗaya, kuma za su rarraba abincinku bisa ga ma'auni. Za ku ci amma ba za ku ƙoshi ba.
27Idan ba ku saurare ni ba duk da waɗannan abubuwan, amma kuka ci gaba da tafiya gãba da ni,28daga nan ni ma zanyi tafiya gãba da ku cikin fushi, kuma zan hukunta ku har sau bakwai sosai saboda zunubanku.
29Za ku ci naman 'ya'yanku maza; za ku ci naman 'ya'yanku mata.30Zan lalatar da wurarenku masu tsayi, in datse bagadan ƙona turarenku, in jefar da gawarwakinku akan gawarwakin gumakanku, kuma ni da kaina zan ji ƙyamar ku.
31Zan juyar da biranenku su zama kufai in lalatar da masujadanku. Ba zan ji daɗin ƙamshin baye-bayenku ba.32Zan lalatar da ƙasar. Maƙiyanku da ke zaune a ƙasar za su yi mamaki da irin lalatarwar.33Zan warwatsaku cikin ƙasashe, kuma zan zare takobina in fafareku. ‌Ƙ‌asarku za a yashe ta, biranenku kuma za su zama kangaye.
34Daga nan ƙasar zata ji daɗin hutunta muddin tana kwance yasasshiya kuma ku kuna ƙasashen maƙiyanku. A wannan lokaci, ƙasar zata huta zata ji daɗin hutunta.35Muddin ƙasar tana kwance kango, zata huta, zai zama hutun da bata samu ba tare da assabatunku, lokacin da kuka zauna cikinta.36Amma ga waɗansun ku da suka ragu cikin ƙasashen maƙiyanku, Zan aikar da tsoro cikin zukatansu yadda motsin kaɗawar ganye cikin guguwa ma zai razanar da ku, za ku sheƙa a guje kamar kuna gujewa takobi. Za ku faɗi, koda ba wanda ke korar ku.
37Za ku yi ta karo da juna kamar kuna gujewa daga takobi, kodashike ba mai korar ku. Ba za ku sami ikon tsayawa gaban maƙiyanku ba.38Za ku hallaka cikin al'ummai, ƙasar maƙiyanku kanta za ta haɗiye ku.39Waɗanda suka ragu a cikinku za su lalace cikin zunubansu, a can cikin ƙasashen maƙiyanku, saboda zunubin kakanninsu kuma za su lalace kamar su.
40Duk da haka idan suka furta zunubansu da zunubin kakanninsu, da cin amanar su da suka zama da rashin aminci a gare ni, da tayarwar da suka yi mani --41wanda ya sa ni na juya gãba da su na kawo su cikin ƙasar maƙiyansu - idan suka ƙasƙantar da zukatansu marasa kaciya, kuma suka karɓi hukunci domin zunubansu,42daga nan zan tuna da alƙawarina da Yakubu, alƙawarina da Ishaku, da kuma alƙawarina tare da Ibrahim; kuma, zan tuna da ƙasar.
43Za su yashe da ƙasar, za ta ji daɗin hutunta yayin da take kwance yasasshiya ba tare da su ba. Za su biya alhakin zunubansu saboda su da kansu sun yi watsi da umarnaina suka yi ƙyamar dokokina.
44Duk da haka bayan dukkan waɗannan, sa'ad da suke cikin ƙasar maƙiyansu, ba zan ƙi su ba, ko in ƙyamace su domin in hallaka su gaba ɗaya har in karya alƙawarina da su ba, Gama Ni ne Yahweh Allahnsu.45Amma saboda su zan tuna da alƙawarina tare da kakanninsu, waɗanda na fisshe su daga ƙasar Masar a idon al'ummai, domin in zama Allahnsu. Ni ne Yahweh."
46Waɗannan dokoki, umarnai da shari'u waɗanda Yahweh ya yi tsakaninsa da mutanen Isra'ila a Tsaunin Sinai ta hannun Musa.

27

1Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,2"Ka yi magana da mutanen Isra'ila ka ce masu, 'Idan wani ya yi alƙawari na musamman ga Yahweh, yi amfani da waɗannan tamanin.

3Darajar misalin abin da za ka biya domin maza daga shekara ashirin zuwa sittin dole ya zama awo hamsin na tagulla, bisa ga awo na wuri mai tsarki.4Ga mataye masu shekaru iri ɗaya darajar abin da za a biya dole ya zama awo talatin.
5Daga shekara biyar zuwa shekara ashirin darajar abin da za a biya domin maza dole ya zama awo ashirin, mataye kuma awo goma.6Daga wata ɗaya zuwa shekara biyar darajar abin da za a biya domin maza dole ya zama awo biyar na tagulla, ga mata awo uku na tagulla.
7Daga shekaru sittin zuwa sama ga maza tamanin abin da za a biya dole ya kai awo goma sha biyar, mata kuma awo goma.8Amma idan mutumin da ya yi wa'adi ba zai iya biyan tamanin ba, daga nan mutumin da aka bayar dole a kawo shi gaban firist, firist ɗin zai kimanta tamanin abin da mutumin da ya yi wa'adin zai iya biya bisa ga ƙarfinsa.
9Idan wani yana son miƙa hadayar dabba ga Yahweh, kuma idan Yahweh ya karɓe ta, daga nan wannan dabbar za a keɓe ta dominsa.10Kada mutumin ya musanya irin wannan dabbar, mai kyau da marar kyau ko marar kyau da mai kyau. Idan ya musanya ko canza dabbar da wata, daga nan dukkan su biyu da aka musanya da wadda aka musanyar za su zama masu tsarki.
11Duk da haka, idan abin da mutumin ya yi wa'adi zai ba Yahweh ta zama marar tsarki, don haka Yahweh ba zai karɓe ta ba, daga nan dole mutumin ya kai dabbar wurin firist.12Firist zai kimanta tamanin ta, bisa ga darajar dabbar. Duk yadda firist ya kimanta dabbar, haka darajarta zata zama.13Idan mai ita yana so ya fãnshe ta, sai ya yi ƙarin kashi biyar na farashin fãnsa.
14Idan mutum ya keɓe gidansa a matsayin kyauta mai tsarki ga Yahweh, daga nan sai firist ya kimanta tamaninsa ko da kyau ko ba kyau. Duk yadda firist ya kimanta darajarsa, haka zai zama.15Amma idan mai gidan wanda ya keɓe gidan yana so ya ƒãnshe shi, dole ya ƙara kashi ɗaya cikin biyar na tamanin farashin fansa, gidan kuwa zai zama nasa.
16Idan mutum ya keɓe wani sãshe na gonarsa, daga nan tamaninta zai zama kimanin dai-dai da yawan irin da ya kamata a shuka - tiyar bãli tamaninta zai zama a bakin shekel hamsin na azurfa.
17Idan ya keɓe gonarsa lokacin shekarar 'Yanci, haka tamaninta zai tsaya.18Amma idan ya keɓe gonarsa bayan shekarar 'Yanci dole firist ya lisafta yawan tamanin ƙasar bisa ga yawan shekarun da suka rage har zuwa shekarar 'Yanci, kuma dole a rage tamaninta.
19Idan shi mutumin da ya keɓe gonar yana so ya fãnshe ta, daga nan dole ya ƙara kashi biyar na tamanin, kuma sai ta zama ta sa.20Idan bai fãnshi gonar ba, ko idan ya rigaya ya sayar da gonar ga wani mutum, ba za ta fãnsu ba faufau.21Maimakon haka, idan gonar, an sake ta cikin shekarar 'Yanci, zata zama kyauta mai tsarki ga Yahweh, kamar gonar da aka bayar gaba ɗaya ga Yahweh. Zata zama mallakar firist.
22Idan mutum ya keɓe gonar da ya saya, amma wannan gonar bata cikin ƙasar gãdon iyalinsa,23daga nan firist zai kimanta tamaninta har zuwa shekarar 'Yanci, daga nan dole mutumin ya biya tamaninta a ranar a matsayin kyauta mai tsarki ga Yahweh.
24A cikin shekarar 'Yanci, sai gonar ta koma ga mutumin wanda daga wurinsa aka saye ta, ga ainihin mai gonar.25Dukkan kowanne tamani dole ya zama bisa ga nauyin awo na wuri mai tsarki. ‌Ƙaramin awo ashirin da ke matsayin awo ɗaya.
26Ba wanda zai keɓe ɗan fãri cikin dabbobi, da shike dama na Yahweh ne; ko sã ko tunkiya, na Yahweh ne.27Idan dabbar marar tsarki ce, daga nan mai ita zai iya fãnsar ta bisa ga tamanin, dole ya ƙara kashi biyar akan tamanin. Idan ba'a fãnshi dabbar ba, daga nan sai a sayar da ita bisa ga tamanin da aka sanya.
28Amma ba abin da mutum zai bayar ga Yahweh, daga dukkan abin da ya ke da shi, ko mutum ko dabba, ko ƙasar gãdonsa, da za a sayar ko a fãnsar. Duk abin da aka keɓe ya zama mai tsarki na Yahweh.29Ba za a biya kuɗin fãnsa ba ga mutumin da aka keɓe domin hallakarwa. Wannan mutumin dole a kashe shi.
30Dukkan zakkar ƙasa, ko ta hatsin da aka noma a ƙasa ko 'ya'yan itatuwa, na Yahweh ne. Mai tsarki ne ga Yahweh.31Idan mutum ya fãnshi kowanne abu na zakkarsa, dole ya ƙara ɗaya bisa biyar na tamaninta.
32Ga kowanne ɗaya bisa goma na makiyaya ko dabbobi, ko mene ne ya wuce ta ƙarƙashin sandar makiyaya, dole a keɓe ɗaya bisa goma ga Yahweh.33Kada makiyayin ya nemi mai kyau ko munanan dabbobi, kada ya musanya da wata. Idan har ya canja, daga nan dukkansu da wadda ya canja za su zama tsarkakku ga Yahweh. Ba za a fãnshe su ba.'"
34Waɗannan su ne dokokin da Yahweh ya bayar a tsaunin Sinai ga Musa domin mutanen Isra'ila.

Littafin lissafi

1

1Yahweh ya yi magana da Musa a runfar taruwa a cikin jejin Sinai. Wannan ya fãru ne a rana ta farko a wata na biyu a shekara ta biyu bayan da mutanen Isra'ila suka fito daga ƙasar Masar. Yahweh yace,2"Ka yi ƙidayar dukkan mutanen Isra'ila daga kowanne dangi, a cikin iyalan ubanninsu. Ka ƙidaya su bisa ga sunaye. Ka ƙidaya kowanne namiji, kowanne mutum3wanda ke shekaru ashirin ko fiye. Ka ƙidaya dukkan waɗanda ke iya faɗa a matsayin sojoji domin Isra'ila. Kai da Haruna tilas ku rubuta lissafin dukkan mazaje a rukunonin mayaƙansu.

4Mutum daga kowacce kabila, kan dangi, tilas ya yi hidima tare da ku a matsayin shugaban kabilarsa. Kowanne shugaba tilas ya shugabanci mazajen da zasu yi faɗa kabilarsa.5Waɗannan ne sunayen shugabannin waɗanda tilas su yi faɗa tare da ku: Daga kabilar Ruben, Elizur ɗan Shedeyur;6daga kabilar Simiyon, Shelumiyel ɗan Zurishaddai;
7daga kabilar Yahuda, Nashon ɗan Amminadab;8daga kabilar Issaka, Netanel ɗan Zuwar;9daga kabilar Zebulun, Eliyab ɗan Helon;
10daga kabilar Ifraim ɗan Yosef, Elishama ɗan Ammihud; daga kabilar Manasse, Gamaliyel ɗan Fedazur;11daga kabilar Benyamin, Abidan ɗan Gidiyoni;
12daga kabilar Dan, Ahiyeza ɗan Ammishaddai;13daga kabilar Asha, Fagiyel ɗan Okran;14daga kabilar Gad, Eliyasaf ɗan Duwel;15kuma daga kabilar Naftali, Ahira ɗan Enan."
16Waɗannan ne mazajen da aka zaɓa daga mutanen. Suka bida kabilun kakanninsu. Sune shugabannin kabilun a Isra'ila.
17Musa da Haruna suka ɗauki waɗannan mutane, waɗanda aka lissafa da sunayensu,18tare da waɗannan mutanen tattaro dukkan mutanen Isra'ila a rana ta farko na wata na biyu. Daga nan kowanne mutum ɗan shekaru ashirin da sama ya tantance asalinsa. Dole ya bada suna ga dangi da iyalan zuriyar daga kakanninsa.19Daga nan Musa ya rubuta lissafinsu a cikin jejin Sinai, kamar yadda Yahweh ya umarce shi ya yi.
20Daga zuriyar Ruben, haihuwar fãrin Isra'ila, an yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum kuma ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen dangin kakanninsu da iyalansu.21Suka ƙidaya mutane 46,500 daga kabilar Ruben.
22Daga zuriyar Simiyon kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum kuma ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen kabilun kakanninsu da iyalansu.23Suka ƙidaya mutane 59,300 daga kabilar Simiyon.
24Daga zuriyar Gad kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum kuma ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen dangin kakanninsu da iyalansu.25Suka ƙidaya mutane 45,650 daga kabilar Gad.
26Daga zuriyar Yahuda kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum kuma ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen dangin kakanninsu da iyalansu.27Suka ƙidaya mutane 74,600 daga kabilar Yahuda.
28Daga zuriyar Issaka kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen dangin kakanninsu da iyalansu.29Suka ƙidaya mutane 54,400 daga kabilar Issaka.
30Daga zuriyar Zebulun kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen dangin kakanninsu da iyalansu.31Suka ƙidaya mutane 57,400 daga kabilar Zebulun.
32Daga zuriyar Ifraim kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen dangin kakanninsu da iyalansu.33Suka ƙidaya mutane 40,500 daga kabilar Ifraim.
34Daga zuriyar Manasse kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen dangin kakanninsu da iyalansu.35Suka ƙidaya mutane 32,200 daga kabilar Manasse.
36Daga zuriyar Benyamin kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen kabilun kakanninsu da iyalansu.37Suka ƙidaya mutane 35,400 daga kabilar Benyamin.
38Daga zuriyar Dan kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen kabilun kakanninsu da iyalansu.39Suka ƙidaya mutane 62,700 daga kabilar Dan.
40Daga zuriyar Asha kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen kabilun kakanninsu da iyalansu.41Suka ƙidaya mutane 41,500 daga kabilar Asha.
42Daga zuriyar Naftali kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen kabilun kakanninsu da iyalansu.43Suka ƙidaya mutane 53,400 daga kabilar Naftali.
44Musa da Haruna suka ƙidaya dukkan waɗannan mutane, tare da mutanen sha biyu waɗanda ke shugabancin kabilun sha biyu na Isra'ila.45Haka dukkan mazajen Isra'ila daga 'yan shekaru ashirin zuwa sama, dukkan waɗanda ke iya faɗa a yaƙi, aka ƙidaya su a kowanne iyalansu.46Suka ƙidaya mutane 603,550.
47Amma mazajen da suka fito daga zuriyar Lebi ba a ƙidaya su ba,48saboda Yahweh ya cewa Musa,49"Tilas baza ka ƙidaya kabilar Lebi ba ko ka haɗa da su cikin jimillar mutanen Isra'ila.
50A maimakon haka, ka sa Lebiyawa lura da runfar alƙawarin dokoki, su kuma lura da dukkan kayayyakin adon runfar da kowanne abu dake cikinta. Tilas Lebiyawa su ɗauki runfar, kuma tilas su ɗauki kayayyakin adon runfar. Tilas su lura da runfar, su kuma yi wa kansu sansani kewaye da ita.
51Sa'ad da za a matsa da runfar zuwa wani wuri, tilas Lebiyawa su sauke ta. Sa'ad da za a kafa runfar, tilas Lebiyawa su kafa ta. Duk wani baƙo da ya zo kusa da runfar tilas a kashe shi.52Sa'ad da mutanen Isra'ila zasu kafa runfunansu, kowanne mutum tillas ya yi haka kusa da tutar da take ta ƙungiyar mayaƙansa.
53Duk da haka, Lebiyawa tilas su kafa runfunansu kewaye da runfar alƙawarin dokoki kada fushina ya sauko bisa mutanen Isra'ila. Tilas Lebiyawa su lura da runfar alƙawarin dokoki."54Mutanen Isra'ila suka yi dukkan waɗannan abubuwa. Suka yi kowanne abin da Yahweh ya umarta ta wurin Musa.

2

1Yahweh ya sake magana da Musa da Haruna. Ya ce,2"Kowanne Ba'isra'ile dole ya yi sansani wajen matsayinsa, tare da tutocin gidan ubanninsa. Za su yi sansani kewaye da rumfar taruwa ta kowanne gefe.

3Waɗanda za su yi sansani gabas da rumfar taruwa, inda rana ke fitowa, su ne sansanin Yahuda kuma suna sansani a ƙarƙashin matsayinsu. Nashon ɗan Amminadab shi ne shugaban mutanen Yahuda.4Lissafin mutanen Yahuda 74,600 ne.
5Kabilar Issaka tilas su yi sansani a gaba da Yahuda. Netanel ɗan Zuyar tilas ya shugabanci mayaƙan Issaka.6Lissafin bataliyar mutane 54,400 ne.
7Kabilar Zebulun tilas su yi sansani a gaba da Issaka. Eliyab ɗan Helon tilas ya shugabanci mayaƙan Zebulun.8Lissafin bataliyarsa 57,400 ne.
9Dukkan lissafin sansanin Yahuda 186,400 ne. Sune za su fãra tafiya.
10Gefen kudu zai zama sansanin Ruben a wajen matsayinsu. Shugaban sansanin Ruben shi ne Elizur ɗan Shedewur.11Lissafin dake bataliyarsa 46,500 ne.
12Simiyon zai yi sansani a gaba da Ruben. Shugaban mutanen Simiyon shi ne Shelumiyel ɗan Zurishaddai.13Lissafin bataliyarsa shi ne 59.300.
14Kabilar Gad su ne gaba. Shugaban mutanen Gad shi ne Eliyasaf ɗan Deuyel.15Lissafin bataliyarsa shi ne 45,650.
16Lissafin dukkan mutanen da aka bayar ga sansanin Ruben, bisa ga bataliyarsu, shi ne 151,450.
17Na gaba, rumfar sansanin tilas ta fita daga sansanin tare da Lebiyawa a tsakiyar dukkan sansanan. Tilas su fita daga sansanin bisa ga tsarin yadda suka shiga sansanin. Kowanne mutum tilas ya tsaya a wurinsa, gefen tutarsa.
18Rabe-raben zangon sansanin Ifraim a ƙarƙashin matsayinsu. Shugaban mutanen Ifraim shi ne Elishama ɗan Ammihud.19Lissafin bataliyarsa shi ne 40,500.
20Gaba dasu su ne Kabilar Manasse. Shugaban Manasse shi ne Gamaliyel ɗan Fedazur.21Lissafin bataliyarsa shi ne 32,200.
22Gaba da su zai kasance kabilar Benyamin. Shugaban Benyamin shi ne Abidan ɗan Gidiyoni.23Lissafin dake bataliyarsa 35,400 ne.
24Dukkan waɗanda aka lissafa a sansanin Ifraim 108,100 ne. Su ne na ukun fita.
25Daga arewa zai kasance bataliyoyin sansanin Dan. Shugaban mutanen Dan shi ne Ahiyeza ɗan Ammishaddai.26Lissafin dake bataliyarsa 62,700 ne.
27Mutanen kabilar Asha suka yi sansani gaba da Dan. Shugaban Asha shi ne Fagiyel ɗan Okran.28Lissafin bataliyarsa 41,500 ne.
29Kabilar Naftali su ne gaba. Shugaban Naftali shi ne Ahira ɗan Enan.30Lissafin dake bataliyarsa 53,400 ne.
31Dukkan waɗanda aka lissafa a sansanin tare da Dan 157,600 ne. Sune na ƙarshen fita daga sansanin, a ƙarƙashin tutarsu."
32Waɗannan ne Isra'ilawa, an lissafa su bisa ga iyalansu. Dukkan waɗanda aka ƙidaya a sansanansu, bisa ga bataliyoyinsu, 603,550 ne.33Amma Musa da Haruna ba su ƙidaya Lebiyawa ba a cikin mutanen Isra'ila. Wannan bisa ga yadda Yahweh ya umarci Musa ne.
34Mutanen Isra'ila suka yi kowanne abu da Yahweh ya umarci Musa. Suka yi sansani bisa ga tutocinsu. Suka fita daga sansanin bisa ga dangoginsu, bisa ga tsarin iyalan kakanninsu.

3

1Yanzu wannan ne tarihin zuriyar Haruna da Musa sa'ad da Yahweh ya yi magana da Musa a Tsaunin Sinai.2Sunayen 'ya'yan Haruna maza su ne Nadab haihuwar farko, da Abihu, Eliyeza, da Itama.

3Waɗannan ne sunayen 'ya'yan Haruna maza, firistoci waɗanda aka shafe aka kuma naɗa su yi hidima a matsayin firistoci.4Amma Nadab da Abihu sun fãɗi sun mutu a gaban Yahweh sa'ad da suka miƙa masa wuta marar karɓuwa a cikin jejin Sinai. Nadab da Abihu ba su da 'ya'ya, sai Eliyeza da Itama ne kawai suka yi hidima a matsayin firistoci tare da Haruna mahaifinsu.
5Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,6"Ka kawo kabilar Lebiyawa ka gabatar da su ga Haruna firist domin su taimake shi.
7Tilas su aiwatar da ayyuka a madadin Haruna da dukkan jama'a a gaban rumfar taruwa. Tilas su yi hidima a rumfar sujada.8Tilas su lura da dukkan kayan ado na cikin rumfar taruwa, kuma tilas su taimaki kabilun Isra'ila su aiwatar da hidimar rumfar sujada.
9Tilas ka bayar da Lebiyawa ga Haruna da 'ya'yansa maza. An bayar da su ɗungun su taimaka masa ya yi hidima ga mutanen Isra'ila.10Tilas ka naɗa Haruna da 'ya'yansa maza a matsayin firistoci, amma duk wani bãre da yazo kusa tilas a kashe shi."
11Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,12"Duba, na ɗauki Lebiyawa daga tsakanin mutanen Isra'ila. Na yi haka ne a maimakon ɗaukar kowanne haihuwar fãri namiji wanda aka haifa a cikin mutanen Isra'ila. Lebiyawa nawa ne.13Dukkan haihuwar fãri nawa ne. A ranar dana kai hari ga dukkan haihuwar fãri na ƙasar Masar, na keɓewa kaina dukkan haihuwar fãri cikin Isra'ila, mutane duk da dabbobi. Nawa ne su. Ni ne Yahweh."
14Yahweh ya yi magana da Musa a jejin Sinai. Ya ce,15"Ka ƙidaya zuriyar Lebi a kowanne iyali, cikin dangoginsu. Ka ƙidaya kowanne namiji daga wata ɗaya zuwa sama.16"Musa ya ƙidaya su, yana bin maganar Yahweh, kamar yadda dai aka umarce shi ya yi.
17Sunayen 'ya'yan Lebi maza su ne Gashon, Kohat, da Merari.18Dangin da suka fito daga 'ya'yan Gashon maza su ne Libni da Shimai.19Dangin da suka fito daga 'ya'yan Kohat maza su ne Amram, Izhar, Hebron, da Uzziyel.20Dangin da suka fito daga 'ya'yan Merari maza su ne Mahli da Mushi. Waɗannan ne dangogin Lebiyawa, aka rubuta dangi zuwa dangi.
21Dangin Libniyawa da Shimaiyawa sun fito daga Gashon. Waɗannan ne dangogin Gashonawa.22Dukkan mazaje daga wata ɗaya zuwa sama an ƙidaya su, jimilla 7,500.23Kabiluin Gashonawa tilas su yi sansani gefen yamma da rumfar sujada.
24Eliyasaf ɗan Layel tilas ya shugabanci kabilun zuriyar Gashonawa.25Iyalin Gashon tilas su lura da rumfar taruwa duk da rumfar sujada. Tilas su lura da rumfar, da abin rufewar ta, da labulen da ake amfani da shi a shiga rumfar taruwar.26Tilas su lura da masagalen labulen harabar, labulen dake ƙofar harabar - harabar dake kewaye da tsattsarkan wuri da bagadi. Tilas su lura da igiyoyin rumfar taruwa kuma domin kowanne abu dake cikinta.
27Waɗannan kabilun sun zo daga Kohat: kabilar Amramiyawa, dangin Izrahiyawa, kabilar Hebroniyawa, da kabilar Uzziyeliyawa. Waɗannan kabilar Kohatawa ne.28Mazaje 8,600 an ƙidaya su shekaru daga wata ɗaya zuwa sama su lura da abubuwan dake na Yahweh.29Dangogin Kohat tilas su yi sansani a gefen kudu da rumfar sujada.
30Elizafan ɗan Uzziyel tilas ya shugabanci dangogin Kohatawa.31Tilas su lura da akwatin, da teburin, da abin ajiyar fitila, da bagadai, da abubuwa masu tsarki da ake amfani da su wajen hidimarsu, labule, da dukkan aiki dake kewaye da shi.32Eliyeza ɗan Haruna firist tilas ya shugabanci mutanen dake shugabantar Lebiyawa. Tilas ya kula da mutanen dake lura da wuri mai tsarki.
33Dangogi biyu suka zo daga Merari: Dangin Mahliyawa da dangin Mushiyawa. Waɗannan dangogi sun zo daga Merari.34Mazaje 6,200 aka ƙidaya shekara daga wata ɗaya zuwa sama.35Zuriyel ɗan Abihayil tilas ya shugabanci dangogin Merari. Tilas su yi sansani a gefen arewa da rumfar sujada.
36Zuriyar Merari tilas su lura da katakan rumfar sujada, da sandunan gittawa, dana dirkoki, dana kafa harsashe, dukkan kaya masu ƙarfi, da duk wani abu da yake tattare dasu, duk da37ginshiƙai da dirkokin harabar dake kewaye da rumfar sujada, tare da kwasfofinsu, turkuna, da igiyoyin.
38Musa da Haruna da 'ya'yansu maza tilas su yi sansani a gefen gabas na rumfar sujada, a gaban rumfar taruwa, zuwa tasowar rana. Sune ke da nauyi domin cika ayyukan tsattsarkan wuri da ayyukan mutanen Isra'ila. Duk wani bãre da ya gabato tsattsarkan wuri tilas a kashe shi.39Musa da Haruna suka ƙidaya dukkan mazajen dake cikin dangogin Lebi masu shekaru daga wata ɗaya zuwa sama, kamar dai yadda Yahweh ya umarta. Suka ƙidaya maza dubu ashirin da biyu.
40Yahweh ya cewa Musa, "Ka ƙidaya dukkan mazaje haihuwar fãri na mutanen Isra'ila masu shekaru daga wata ɗaya zuwa sama. Ka lissafa sunayensu.41Tilas ka ɗauki Lebiyawa domina - Ni ne Yahweh - maimakon dukkan haihuwar fãri na mutanen Isra'ila, da dabbobin Lebiyawa maimakon haihuwar fãri na dabbobin zuriyar Isra'ila."
42Musa ya ƙidaya dukkan haihuwar fãri na mutanen Isra'ila yadda Yahweh ya umarce shi ya yi.43Ya ƙidaya sunan dukkan mazaje haihuwar fãri, shekara daga wata ɗaya zuwa sama. Ya ƙidaya maza 22,273.
44Yahweh, ya sake magana da Musa. Ya ce,45"Ka ɗauki Lebiyawa a maimakon dukkan haihuwar fãri daga cikin mutanen Isra'ila, ka kuma ɗauki dabbobin Lebiyawa a maimakon dabbobin mutanen. Lebiyawa nawa ne - Ni ne Yahweh.
46Tilas ne ka karɓi shekel biyar domin fansar kowanne ɗaya daga cikin 273 haihuwar fãri na mutanen Isra'ila da suka zarce lissafin Lebiyawa.47Tilas ka yi amfani da shekel na tsattsarkan wuri a matsayin adadin awo. Shekel na dai-dai da awo ashirin na gera.48Tilas ku bayar da kuɗin fansa da kuka biya ga Haruna da 'ya'yansa maza."
49Sai Musa ya karɓi biyan fansar daga wurin waɗanda suka zarce lissafin waɗanda Lebiyawa suka fansa.50Musa ya karɓi kuɗin daga haihuwar fari na mutanen Isra'ila ya karɓi shekel 1,365 an auna da shekel na tsattsarkan wuri. Musa ya bayar da kuɗin fansa ga Haruna da 'ya'yansa maza.51Musa ya yi kowanne abu da aka ce masa yayi ta maganar Yahweh kamar yadda Yahweh ya umarce shi.

4

1Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna. Ya ce,2"Ka yi ƙidayar mazaje zuriyar Kohat daga cikin Lebiyawa, bisa ga dangoginsu da iyalansu.3Ka ƙidaya dukkan mazan dake shekaru talatin zuwa hamsin. Waɗannan mutane tilas su shiga ayarin hidima a cikin rumfar taruwa.4Zuriyar Kohat tilas su lura da abubuwa mafi tsarki da aka keɓe domina a cikin rumfar taruwa.

5Sa'ad da sansanin ya shirya matsawa gaba, Haruna da 'ya'yansa maza tilas su shiga cikin rumfar, su sauke labulen da ya raba tsakanin wuri mafi tsarki da wuri mai tsarki su kuma rufe akwatin alƙawari da shi.6Tilas su rufe akwatin da fãtun saniyar teku. Tilas su baza shuɗiyar sutura a kai. Tilas su sãƙa dirkokin don su ɗauke shi.
7Za su baza shuɗiyar sutura bisa teburin gurasa da ke gabansa. A bisan sa tilas su sa kwanonin, da cokulan, da langunan, da kwalaben zubawa. Tilas koyaushe gurasa ta kasance a teburin.8Tilas su rufe ta da jar sutura kuma tare da fãtar saniyar teku. Tilas su sãƙa dirkoki na ɗaukar teburin.
9Tilas su ɗauki shuɗiyar sutura su rufe mazaunin fitilar, tare da fitilun, da mamurɗan, da tururrukan, da dukkan kwalaben mai domin fitilun.10Tilas su sanya mazaunin fitilar tare da kayayyakinsa a cikin abin rufewar da aka yi da fãtar saniyar teku, tilas su sanya shi cikin katakon ɗauka.11Tilas su baza sutura shuɗiya bisa bagadin zinariya. Tilas su rufe shi da abin rufewar da aka yi da fãtun saniyar teku, daga nan kuma a sãƙa dirkokin ɗauka.
12Tilas su ɗauki dukkan kayayyakin aikin wuri mai tsarki a kuma rufe su da shuɗiyar sutura. Tilas su rufe shi da fãtun saniyar teku a sanya kuma kayayyakin cikin katakon ɗauka.13Tilas su ɗebe toka daga bagadi su kuma shimfiɗa sutura shunayya bisa bagadin.14Tilas su sanya dukkan kayayyaki da suka yi amfani da su wurin aikin bagadi bisa katakon ɗauka. Waɗannan kayayyaki su ne kaskunan wuta, cokula masu yatsu, cebura, kwanuka, da dukkan sauran kayayyaki domin bagadi. Tilas su rufe bagadin da fãtun saniyar teku Daga nan kuma su sãƙa dirkokin ɗauka.
15Sa'ad da Haruna da 'ya'yansa maza suka kammala rufe wuri mai tsarki da dukkan kayayyakinsa, sa'ad da kuma sansani ya matsa gaba, Daga nan zuriyar Kohat tilas su zo su ɗauki wuri mai tsarki. Idan suka taɓa kayayyakin aikin masu tsarki, tilas su mutu. Wannan ne aikin zuriyar Kohat, su ɗauki kayayyakin ado na cikin rumfar taruwa.16Eliyeza ɗan Haruna firist zai shugabanci lura da mai domin haskakawa, turare mai daɗi, baikon hatsi da aka saba yi, da mai na shafewa. Zai shugabanci lura da rumfar sujadar gaba ɗaya da dukkan abin dake cikin ta, wuri mai tsarki da kayayyakinsa."
17Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna. Ya ce,18"Kada ku bari a cire kabilar dangogin Kohatawa daga cikin Lebiyawa.19Ku kãre su, domin su rayu kada kuma su mutu, ta wurin yin haka. Sa'ad da suka kusanci abubuwa mafi tsarki20tilas ba za su je su duba wuri mai tsarki ba ko dana ɗan taƙi, ko kuwa tilas su mutu. Haruna da 'ya'yansa maza tilas su shiga ciki, Daga nan kuma Haruna da 'ya'yansa maza tilas su sanya kowanne daga cikin Kohatawa ga aikinsa, ga aikinsa na musamman."
21Yahweh ya sake magana da Musa, ya ce,22"Ka yi ƙidayar zuriyar Gashon kuma, bisa ga iyalan kakanninsu bisa ga dangoginsu.23Ka ƙidaya waɗanda suke shekaru talatin zuwa shekaru hamsin. Ka ƙidaya dukkan waɗanda za su shiga ayarin su yi bauta a rumfar taruwa.
24Wannan ne aikin kabilun Gashonawa sa'ad da suka yi bauta da abin da suka ɗauka.25Tilas su ɗauki labulan rumfar sujada, da rumfar taruwa da abin rufe ta, abin rufe ta na fãtar saniyar teku, da labulan hanyar shiga rumfar taruwa.26Tilas su ɗauki labulan harabar, labule domin hanyar ƙofa ta ƙofar harabar, wadda ke kusa da rumfar sujada kusa kuma da bagadi, igiyoyinsu, da dukkan kayayyakin aiki domin hidimarsu. Duk abin da ya kamata a yi da waɗanan abubuwa, tilas su yi shi.
27Haruna da 'ya'yansa maza tilas su bida dukkan hidimar zuriyar Gashonawa, a cikin dukkan abin da suka ɗauko, a cikin kuma dukkan hidimarsu.28Tilas ka sanya su ga dukkan ayyukansu. Wannan ne hidimar dangogin zuriyar Gashonawa domin rumfar taruwa. Itama ɗan Haruna firist tilas ne ya bida su cikin hidimarsu.
29Tilas ka ƙidaya zuriya Merari bisa ga dangoginsu, ka kuma shirya su bisa ga iyalan kakanninsu,30daga shekaru talatin zuwa sama har shekaru hamsin. Ka ƙidaya dukkan waɗanda za su shiga ayari su kuma yi bauta a rumfar taruwa.
31Wannan ne hakkinsu da aikinsu a cikin dukkan hidima domin rumfar taruwa. Tilas su lura da katakan rumfar sujada, da sandunan gittawa, dirkoki, da mahaɗai,32tare da dirkokin filin harabar dake kewaye da rumfar sujada, mahaɗansu, turkuna, da igiyoyinsu, tare da dukkan kayayyakinsu. Ka lissafa bisa sunan kayayyakin da tilas su ɗauka.
33Wannan ne aikin kabilun zuriyar Merari, abin da za su yi domin rumfar taruwa, ƙarƙashin bishewar Itama ɗan Haruna firist."
34Musa da Haruna da shugabannin jama'a suka ƙidaya zuriyar Kohatawa bisa ga dangogin iyalan kakanninsu.35Suka ƙidaya su daga shekaru talatin zuwa sama har shekaru hamsin. Suka ƙidaya kowanne da zai shiga ayari ya yi bauta a rumfar taruwa.36Suka ƙidaya mazaje 2,750 bisa ga dangoginsu.
37Musa da Haruna suka ƙidaya dukkan mazaje a cikin dangogi da iyalan Kohatawa waɗanda suke bauta a rumfar taruwa. A cikin yin haka, sun yi biyayya da abin da Yahweh ya umarce su suyi ta wurin Musa.
38Aka ƙidaya zuriyar Gashon a cikin dangoginsu, ta wurin iyalan kakanninsu,39daga shekaru talatin zuwa shekaru hamsin, kowanne da zai shiga ayari ya yi bauta a rumfar taruwa.40Dukkan mazaje, da aka ƙidaya ta wurin dangogi da iyalan kakanninsu, lissafi 2,630 ne.
41Musa da Haruna suka ƙidaya dangogin zuriyar Gashon waɗanda za su yi bauta a cikin rumfar taruwa. A cikin yin haka, sun yi biyayya da abin da Yahweh ya umarce su suyi ta wurin Musa.
42Aka ƙidaya zuriyar Merari a cikin dangoginsu ta wurin iyalan kakanninsu,43daga shekaru talatin zuwa shekaru hamsin, kowanne da zai shiga ayari ya yi bauta a cikin rumfar taruwa.44Dukkan mazaje, da aka ƙidaya ta wurin dangoginsu da iyalan kakanninsu, lissafi 3,200 ne.
45Musa da Haruna suka ƙidaya dukkan waɗannan mazaje, zuriyar Merari. A cikin yin haka, sun yi biyayya da abin da Yahweh ya umarce su suyi ta wurin Musa.
46Sai Musa, Haruna, da shugabannin Isra'ila suka ƙidaya dukkan Lebiyawa ta wurin dangoginsu cikin iyalan kakanninsu47daga shekaru talatin zuwa shekaru hamsin. Suka ƙidaya kowanne da zai yi aiki a cikin rumfar sujada.48Suka ƙidaya mazaje 8,580.
49Ta umarnin Yahweh, Musa ya ƙidaya kowanne mutum, yana ajiyar ƙidayar kowanne bisa ga irin aikin da aka ba shi ya yi. Ya ƙidaya kowanne mutum bisa ga irin hakkin da aka ɗora masa ya ɗauka. A cikin yin haka, sun yi biyayya da abin da Yahweh ya umarce su su yi ta wurin Musa.

5

1Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,2"Ka umarci mutanen Isra'ila su kori kowanne mutum daga sansani wanda ke da cutar fãta da ake ɗauka, da kowanne dake da ƙurjin dake fitar da ruwa, da duk wanda ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa.3Ko namiji ko mace, tilas ka kore su daga sansanin. Tilas ne ba za su gurɓata sansanin ba, saboda ina zaune a cikin sa."4Mutanen Isra'ila suka yi haka. Suka kore su daga sansanin, kamar yadda Yahweh ya umarci Musa. Mutanen Isra'ila suka yi biyayya da Yahweh.

5Yahweh ya sa ke magana da Musa. Ya ce,6"Ka yi magana da mutanen Isra'ila. Sa'ad da wani mutum ko wata mata suka aikata zunubi irin wanda mutane ke aikatawa ga junansu, kuma ya yi rashin aminci a gare ni, wannan mutum ya yi laifi.7Daga nan tilas ya furta zunubin da ya yi. Tilas ya biya farashin laifinsa gaba ɗaya ya kuma ƙara akan farashin kashi ɗaya cikin biyar. Tilas ya bayar da wannan ga wanda ya yiwa laifin.
8Amma idan wanda aka yiwa laifin bai da ɗan'uwa na kusa da zai karɓi biyan, tilas ya biya farashin laifinsa gare ni ta wurin firist, tare da rago na yin kaffara domin sa.9Kowanne baiko na mutanen Isra'ila, abubuwan da aka keɓe aka kuma kawo ga firist ta wurin mutanen Isra'ila, zai zama nasa.10Baye-bayen kowanne taliki zai zama domin firist; idan wani ya bayar da wani abu ga firist, zai zama nasa."
11Bugu da ƙari, Yahweh yayi magana da Musa. Ya ce,12"Kayi magana da mutanen Isra'ila. Ka ce da su, 'Ga misali idan matar wani ta kauce hanya ta kuma yi zunubi gãba da mijinta.
13Misali a ce wani mutum ya kwana da ita. A wannan al'amari, ta ƙazantu. Ko da mijinta bai gani ba ko kuma ya san da hakan, kuma ko da ba wanda ya kama ta cikin aikata hakan kuma ba bu wanda zai bada shaida gãba da ita,14duk da haka. ruhun kishi zai sanarwa mijin cewa matarsa ta ƙazamtu. Ko da yake, ruhun kishi na ƙarya na iya sauko wa mutum alhali matarsa ba ta ƙazantu ba.
15A cikin irin waɗannan al'amura, tilas mutumin ya kawo matarsa ga firist. Tilas mutumin ya zo da baikon da ake buƙata a madadin ta, kashi goma na awon garin bali. Tilas ne kuma ba zai zuba mai a kai ba ko kuma ya zuba turaren ƙonawa a kai ba, saboda baikon hatsi ne na kishi, baikon hatsi domin tunawa, a matsayin abin tunawa da laifin.
16Tilas firist ya kawo ta kusa ya miƙa ta gaban Yahweh.17Tilas firist ya ɗauki gorar ruwa mai tsarki ya kuma ɗibi ƙurar ƙasan rumfar sujada. Tilas ya zuba ƙurar cikin ruwan.
18Firist zai sa matar gaban Yahweh kuma zai kwance gashin dake kan matar. Zai sanya cikin hannuwanta baikon hatsi na tunawa, wanda shi ne baikon hatsi na zato. Firist zai riƙe a hannunsa ruwa mai ɗaci da zai iya kawo la'ana.19Firist zai sanya matar ƙarƙashin rantsuwa ya kuma ce mata, 'Idan babu mutumin da yayi saduwar jima'i dake, idan kuma baki fita iskanci ba kika kuma aikata rashin tsarki, to zaki 'yantu daga wannan ruwa na ɗaci da zai iya kawo la'ana.
20Amma idan ke, mace ƙarƙashin mijinta, kin fita iskanci, idan kin ƙazantu, idan kuma wani mutum daban ya kwana da ke,21daga nan, (tilas firist ya sa matar ta ɗauki rantsuwar da za ta sauko mata da la'ana, daga nan kuma tilas ya ci gaba da magana da matar) 'Yahweh zai maida ke la'ana da za a nuna wa mutanenki ya kasance haka. Wannan zai kasance idan Yahweh ya sa cinyarki ta ruɓe kuma mararki ta kumbura.22Wannan ruwan da zai kawo la'ana zai shiga cikin cikinki ya sa mararki ta kumbura cinyoyinki kuma su ruɓe.' Matar kuma za ta maida amsa, 'I, bari haka ya kasance idan ina da laifi.'
23Firist tilas ne ya rubuta waɗannan la'anoni cikin naɗaɗɗen littafi, Daga nan kuma tilas ya wanke rubutattun la'anonin cikin ruwa mai ɗaci.
24Tilas firist ya sa matar ta sha ruwa mai ɗaci da zai kawo la'ana. Ruwan dake kawo la'ana zai shiga cikinta ya zama ɗaci.25Firist tilas ya ɗauke baikon hatsi na kishi daga hannun matar. Dole ya riƙe baikon hatsin a gaban Yahweh ya kuma kawo shi zuwa bagadi.26Firist tilas ya ɗibi tafin hannu na baikon hatsin a matsayin baikon madadi, ya kuma ƙonashi bisa bagadi. Daga nan tilas ya ba matar ruwa mai ɗaci ta sha.
27Sa'ad da ya ba ta ruwan ta sha, idan ta ƙazantu saboda ta aikata zunubi gãba da mijinta, to ruwan dake kawo la'ana zai shiga cikinta, ya kuma zama ɗaci. Mararta za ta kumbura kuma cinyarta ta ruɓe. Matar za ta zama la'ananna a cikin mutanenta.28Amma idan matar ba ta ƙazantu ba kuma da tsabtarta, to tilas ta 'yantu. Za ta iya haihuwar 'ya'ya.
29Wannan ce shari'ar kishi. Shari'a ce domin matar da ta fita iskanci daga wurin mijinta ta kuma ƙazantu.30Shari'a ce domin mutumin da ka tare da ruhun kishi sa'ad da yake kishin matarsa. Tilas ya kawo matar a gaban Yahweh, kuma firist tilas ya yi mata dukkan abin da shari'ar kishi ta tsara.
31Mutumin zai 'yantu daga laifi domin kawo matarsa da ya yi a gaban firist. Tilas ne matar ta ɗauki nauyin kowanne laifi da take da shi."

6

1Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,2"Ka yi magana da mutanen Isra'ila. Ka ce masu, 'Idan namiji ko mace ya keɓe kansa ga Yahweh tare da alƙawari na musamman na zama Nazari,3ba zai taɓa shan ruwan inabi da abin sha mai ƙarfi ba. Ba zai taɓa shan abin sha mai tsami da aka yi daga ruwan inabi ba ko daga abin sha mai ƙarfi. Ba zai taɓa shan abin da aka matso daga inabi ba ko ya ci sabobbin 'ya'yan inabi ko busassun 'ya'yan inabi ba.4A cikin dukkan kwanakin keɓewarsa gare ni, ba zai ci wani abin da aka yi da inabi ba, tare da dukkan abin da aka yi daga tsabar inabin zuwa fãtunsa.

5A cikin dukkan lokacin alƙawarinsa na keɓewa, ba za a yi amfani da aska ba a bisa kansa har sai kwanakin keɓewarsa ga Yahweh sun cika. Tilas a ware shi ga Yahweh. Tilas ya bar gashinsa ya yi tsawo a bisa kansa.
6A cikin dukkan lokacin da ya keɓe kansa ga Yahweh, tilas ne ba zai zo kusa da gawa ba.7Tilas ne ba zai mai da kansa marar tsarki ba ko da domin mahaifinsa, mahaifiyarsa, ɗan'uwansa, da 'yar uwarsa ba, idan suka mutu. Wannan kuwa saboda an keɓe shi ga Allah, kamar yadda kowa zai gani ta wurin dogon gashinsa.8A cikin dukkan lokacin keɓewarsa mai tsarki ne shi, ajiyayye domin Yahweh.
9Idan wani da gaske farat ɗaya ya mutu a gefensa, ya kuma ɓãta keɓaɓɓen kansa, Daga nan tilas ya aske kansa a ranar tsarkakewarsa - a rana ta bakwai tilas ya aske shi.
10A rana ta takwas tilas ya kawo kurciyoyi biyu ko tantabaru 'yan shila biyu ga firist a ƙofar shiga rumfar taruwa.11Firist kuma tilas ya miƙa tsuntsuwa ɗaya a matsayin baikon zunubi, ɗaya kuma a matsayin baikon ƙonawa. Waɗannan za su yi masa kafara saboda ya yi zunubi ta wurin kasancewa kusa da gawa. Tilas ya sake keɓe kansa kuma a wannan rana.
12Tilas ya kiyaye kansa ga Yahweh domin kwanakin keɓewarsa. Tilas ya kawo ɗan rago ɗan shekara ɗaya a matsayin baikon laifi. Kwanakin da ya yi kafin ya ƙazantar da kansa tilas ba za a lissafa su ba, domin keɓewarsa ta ƙazantu.
13Wannan ce shari'a game da Nazari domin sa'ad da lokacin keɓewarsa ya cika. Tilas a kawo shi ƙofar shiga rumfar taruwa.14Tilas ya gabatar da baikonsa ga Yahweh. Tilas ya miƙa a matsayin baikon ƙonawa ɗan rago ɗan shekara ɗaya kuma marar aibi. Tilas ya miƙa a matsayin baikon zunubi 'yar tunkiya 'yar shekara ɗaya kuma marar aibi. Tilas ya kawo rago a matsayin baikon zumunta wanda yake marar aibi.15Tilas ya kawo kwandon gurasa da aka yi ba tare da gami ba, dunƙule-dunƙule na gari mai laushi da aka gauraya da mai, waina marar gami da aka shafe da mai, tare da baikon hatsinsu da baye-baye na sha.
16Tilas ne firist ya gabatar da su a gaban Yahweh. Tilas ya miƙa baikon zunubinsa da baikon ƙonawa.17Tare da kwandon gurasa marar gami, tilas ya miƙa ragon a matsayin hadaya, baikon zumunta ga Yahweh. Firist kuma tilas ya gabatar da baikon hatsi da baikon abin sha.
18Nazirin tilas ya aske kansa don a nuna cewa an keɓe shi ga Allah a ƙofar shiga rumfar taruwa. Tilas ya ɗauki gashin dake daga kansa ya kuma sanya a cikin wutar dake ƙarƙashin hadayar baye-bayen zumunta.
19Tilas firist ya ɗauki dafaffiyar kafaɗar ragon, curin gurasa ɗaya marar gami daga cikin kwandon, da waina ɗaya marar gami. Tilas ya ɗora su cikin hannuwan Banazaren bayan ya aske kansa nuna keɓewa.20Tilas firist ya wurga su a matsayin baiko a gaban Yahweh, kaso mai tsarki domin firist, tare da ƙirgin da aka wurga da kuma cinyar da aka gabatar domin firist. Bayan haka, Banazaren zai iya shan ruwan inabi.
21Wannan ce shari'a domin Nazari wanda ya yi alƙawarin baikonsa ga Yahweh domin keɓewarsa. Kowanne abu kuma da zai iya bayarwa, tilas ya kiyaye ka'idodin alƙawarin da ya ɗauka, ya kiyaye alƙawarin da aka nuna ta wurin shari'a domin Banazare."'
22Yahweh ya sake magana da Musa. Ya ce,23"Ka yi magana da Haruna da 'ya'yansa maza. Cewa, 'Tilas ku albarkaci mutanen Isra'ila ta wannan hanya. Tilas ku ce masu,24"Bari Yahweh ya albarkace ku ya kuma kiyaye ku.
25Bari Yahweh ya sa fuskarsa ta haskaka a bisanku ya kuma yi maku alheri.26Bari Yahweh ya kalle ku da tagomashi ya kuma ba ku salama."'27Ta wannan hanya ce tilas za su bayar da sunana ga mutanen Isra'ila. Daga nan zan albarkace su.

7

1A ranar da Musa ya kammala rumfar sujadar, sai ya shafe ta ya kuma keɓe ta ga Yahweh, tare da dukkan kayan adonta. Ya yi haka kuma domin bagadin da dukkan kayayyakinsa. Ya shafesu ya kuma keɓe su ga Yahweh.2A wannan rana, shugabannin Isra'ila, shugabannin iyalan kakanninsu, suka miƙa hadayu. Waɗannan mutane ne ke shugabancin kabilun. Sun shugabanci lissafin mazajen a ƙidaya.3Suka kawo baye-bayensu gaban Yahweh. Suka kawo kekunan noma rufaffu guda shida da shanu sha biyu. Suka kawo kowanne keken noma ɗaya domin shugabanni biyu, kuma kowanne shugaba ya kawo sã ɗaya. Suka gabatar da waɗannan abubuwa a gaban rumfar sujada.

4Daga nan Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,5"Ka karɓi baye-bayen daga garesu ka kuma yi amfani da baye-bayen domin aikin rumfar taruwa. Ka bayar da baye-bayen ga Lebiyawa, ga kowannen su bisa ga yadda aikinsa ke buƙatarsu."
6Musa ya ɗauki kekunan noman da shanun, ya kuma bayar da su ga Lebiyawa.7Ya bayar da kekunan noma biyu da shanu huɗu ga zuriyar Gashon, saboda abin da aikinsu ke buƙata.8Ya bayar da kekunan noma huɗu da shanu takwas ga zuriyar Merari, cikin kulawar Itama ɗan Haruna firist. Ya yi wannan ne saboda abin da aikinsu ya ke buƙata.
9Amma bai ba da ko ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa ba ga zuriyar Kohat, saboda nasu zai kasance aikin dake da dangantaka da abubuwan dake na Yahweh wanda za su ɗauka bisa kafaɗunsu.
10Shugabannin suka miƙa kayayyakinsu domin keɓewar bagadi a ranar da Musa ya shafe bagadi. Shugabannin suka miƙa hadayunsu a gaban bagadin.11Yahweh ya cewa Musa, "Kowanne shugaba a ranarsa zai miƙa hadayarsa domin keɓewar bagadi."
12A rana ta farko, Nashon ɗan Amminadab, na kabilar Yahuda, ya miƙa tasa hadayar.13Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awo na rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai domin baikon hatsi.14Ya bayar da kwanon zinariya guda ɗaya mai nauyin awo goma cike da turaren ƙonawa.
15Ya bayar da bijimi ɗaya domin baiko na ƙonawa, rago ɗaya, da ɗan rago shekara ɗaya.16Ya bayar da bunsuru ɗaya domin baikon zunubi.17Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, da 'yan raguna biyar 'yan shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Nashon ɗan Amminadab.
18A rana ta biyu, Netanel ɗan Zuyar, shugaban Issaka, ya miƙa hadayarsa.19Ya miƙa a matsayin hadaya tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa ɗaya mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai domin baikon hatsi.
20Ya kuma bayar da kwanon zinariya guda ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.21Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, da ɗan rago shekara ɗaya.22Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.23Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, da 'yan raguna biyar dake shekara ɗaya, a matsayin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Netanel ɗan Zuyar.
24A rana ta ukku, Eliyab ɗan Helon, shugaban zuriyar Zebulun, ya miƙa hadayarsa.25Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130, da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai domin baikon hatsi.26Ya kuma bayar da kwanon zinariya ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.
27Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, da ɗan rago shekara ɗaya.28Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon sujada.29Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, da 'yan raguna biyar 'yan shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Eliyab ɗan Helon.
30A rana ta huɗu, Elizur ɗan Shedeyur, shugaban zuriyar Ruben, ya miƙa hadayarsa.31Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai domin baikon hatsi.32Ya kuma bayar da kwanon zinariya ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.
33Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, ɗan rago shekara ɗaya.34Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.35Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, da 'yan raguna biyar dake shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Elizur ɗan Shedeyur.
36A rana ta biyar, Shelumiyel ɗan Zurishaddai, shugaban zuriyar Simiyon, ya miƙa hadayarsa.37Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai domin baikon hatsi.38Ya kuma bayar da kwanon zinariya ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.
39Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, ɗan rago shekara ɗaya.40Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.41Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, da 'yan raguna biyar, a matsayi hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Shelumiyel ɗan Zurishaddai.
42A rana ta shida, Eliyasaf ɗan Deuyel, shugaban zuriyar Gad, ya miƙa hadayarsa.43Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai a matsayin baikon hatsi.44Ya kuma bayar da kwanon azurfa ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.
45Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, ɗan rago shekara ɗaya.46Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.47Ya bayar da shanu biyu, roga biyar, bunsuru biyar, da 'yan raguna biyar dake shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Eliyasaf ɗan Deuyel.
48A rana ta bakwai, Elishama ɗan Ammihud, shugaban zuriyar Ifraim, ya miƙa hadayarsa.49Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai a matsayin baikon hatsi.50Ya kuma bayar da kwanon zinariya ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.
51Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, da ɗan rago shekara ɗaya.52Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.53Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, da 'yan raguna biyar dake shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Elishama ɗan Ammihud.
54A rana ta takwas, Gamaliyel ɗan Fedazur, shugaban zuriyar Manasse, ya miƙa hadayarsa.55Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai domin baikon hatsi.56Ya kuma bayar da kwanon zinariya ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.
57Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, da ɗan rago shekara ɗaya.58Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.59Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, da 'yan raguna biyar dake shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Gamaliyel ɗan Fedazur.
60A rana ta tara, Abidan ɗan Gidiyoni, shugaban zuriyar Benyamin, ya miƙa hadayarsa.61Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai domin baikon hatsi.62Ya kuma bayar da kwanon zinariya ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.
63Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, da ɗan rago shekara ɗaya.64Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.65Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, 'yan raguna biyar dake shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Abidan ɗan Gidiyoni.
66A rana ta goma, Ahiyeza ɗan Ammishaddai, shugaban zuriyar Dan, ya miƙa hadayarsa.67Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai a matsayin baikon hatsi.68Ya kuma bayar da kwanon zinariya ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.
69Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, ɗan rago shekara ɗaya.70Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.71Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, 'yan raguna biyar dake shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Ahiyeza ɗan Ammishaddai.
72A rana ta sha ɗaya, Fagiyel ɗan Okran, shugaban zuriyar Asha, ya miƙa hadayarsa.73Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai a matsayin baikon hatsi.74Ya kuma bayar da kwanon zinariya ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.
75Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, da ɗan rago shekara ɗaya.76Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.77Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, 'yan raguna biyar dake shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Fagiyel ɗan Okran.
78A rana ta sha biyu, Ahira ɗan Enan, shugaban zuriyar Naftali, ya miƙa hadayarsa.79Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai domin baikon hatsi.80Ya kuma bayar da kwanon zinariya ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.
81Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, da ɗan rago shekara ɗaya.82Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.83Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, 'yan raguna biyar dake shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Ahira ɗan Enan.
84Shugabannin Isra'ila suka keɓe dukkan waɗannan a ranar da Musa ya shafe bagadi. Suka keɓe tirirrikan azurfa sha biyu, bangajin azurfa sha biyu, da kwanukan zinariya sha biyu.85Kowanne tire nauyin awo 130 kowanne bangaji kuma nauyin awo saba'in. Dukkan kayan azurfar nauyin su awo 2,400 ne, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada.86Kowanne kwanukan zinariya sha biyu, cike da turaren ƙonawa, nauyin awo goma bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan kwanukan zinariyar nauyin awo 120 ne.
87Suka keɓe dukkan dabbobi domin baye-baye na ƙonawa, bijimai sha biyu, rago sha biyu, 'yan raguna sha biyu 'yan shekara ɗaya. Suka bayar da baikon hatsinsu. Suka bayar da bunsuru sha biyu a matsayin baikon zunubi.88Daga dukkan garken dabbobinsu, suka bayar da bijimai ashirin da huɗu, rago sittin, bunsuru sittin, da 'yan raguna sittin 'yan shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan domin keɓewar bagadi ne bayan an shafe shi.
89Sa'ad da Musa ya shiga cikin rumfar taruwa domin ya yi magana tare da Yahweh, ya ji muryarsa ya na magana da shi. Yahweh ya yi magana da shi daga bisan marfin kafara dake a kan akwatin alƙawari., daga tsakanin kerubim biyu. Ya yi masa magana.

8

1Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,2"Ka yi magana da Haruna. Ka ce da shi, 'Fitilun nan guda bakwai su bada haske a gaban wurin ɗora fitilar idan ka kunna su."'

3Haruna kuwa ya yi haka. Ya kunna fitilun yadda za su ba da haske wajan gaban inda a ke ɗora fitilun, kamar yadda Yahweh ya ummarci Musa.4Haka a ka yi wurin ɗora fitilun yadda Yahweh ya nuna wa Musa. Ya zama bugaggiyar zinariya tun daga ƙasa har sama, da bugaggun koffuna kamar furanni.
5Yahweh, ya sake yin magana da Musa. Ya ce,6"Ka ɗebi Lebiyawa daga cikin mutanen Isra'ila ka tsarkake su.
7Ga yadda za ka tsarkake su: Ka yayyafa ruwan kafara a kansu. Ka sa su aske jikinsu dukka, su wanke tufafinsu ta haka za su tsarkake kansu.8Ka sa su sami ɗan bijimi da baikonsa na gari wanda a ka gauraya da mai. Su kuma sami wani ɗan bijimin domin baiko na zunubi.
9Ka kawo Lebiyawan gaban rumfa ta taruwa ka kuma tattara dukkan mutanen Isra'ila.10Sa'ad da ka kawo Lebiyawan gaban Yahweh, sai dukkan mutanen Isra'ila su ɗora hannuwansu a kan Lebiyawan.11Sai Haruna ya miƙa Lebiyawan a gaban Yahweh, kamar bayarwa ta ɗagawa daga mutanen Isra'ila domin su yi wa Yahweh hidima.
12Sai Lebiyawan su ɗora hannuwansu a bisa kawunan bajiman. Sai ka miƙa bijimi ɗaya baiko na zunubi, ɗaya bijimin kuma baiko na ƙonawa gare ni, sai a yi wa Lebiyawan kafara.13Sai ka gabatar da Lebiyawan ga Haruna da 'ya'yansa, ka ɗaga su kamar baiko na ɗagawa a gare ni.
14Ta haka za ka keɓe Lebiyawan daga cikin mutanen Isra'ila. Lebiyawan za su zama nawa.15Bayan wannan sai Lebiyawan su shiga su yi hidima a cikin rumfa ta taruwa. Dole ne ka tsarkake su. Dole kuma ka miƙa su kamar baikon na ɗagawa.
16Ka yi haka, saboda sun zama nawa ɗungum daga cikin mutanen Isra'ila. Su za su zama kamar kowanne ɗă namiji da aka fara haifuwa, ɗa na fari daga kowacce zuriya ta Isra'ila. Na ɗauki Lebiyawa domin kaina.17Kowanne ɗă na fari na mutanen Isra'ila nawa ne, na mutum dana dabba. A ranar dana ɗauke dukkan rayukan 'ya'yan fari cikin ƙasar Masar, na keɓe su gare ni.
18Na ɗauki Lebiyawa daga cikin mutanen Isra'ila a madadin dukkan 'ya'yan fari.19Na bayar da Lebiyawa kyauta ga Haruna da 'ya'yansa. Na ɗauke su daga cikin mutanen Isra'ila domin su yi aikin mutanen Isra'ila a cikin rumfa ta taruwa. Na bayar da su domin su yi kafara saboda mutanen Isra'ila domin kada annoba ta same su sa'ad da suka zo kusa da wuri mai tsarki."
20Musa da Haruna da dukkan taron mutanen Isra'ila suka yi haka da Lebiyawa. Suka yi dukkan abin da Yahweh ya ummurci Musa game da Lebiyawa. Mutanen Isra'ila suka yi haka da su.21Lebiyawan su ka tsarkake kansu suka wanke tufafinsu, Haruna ya gabatar da su kamar baiko na ɗagawa ga Yahweh kuma ya yi kafara domin su ya tsaftace su
22Bayan haka, sai Lebiyawan suka shiga domin su yi hidima a cikin rumfa ta taruwa a gaban Haruna da 'ya'yansa. Wannan ya zama kamar yadda Yahweh ya ummarci Musa game da Lebiyawa. Haka suka yi da dukkan Lebiyawa.
23Yahweh ya sake yin magana da Musa. Ya ce,24"Dukkan wannan saboda Lebiyawan da suka kai shekara ashirin da biyar ne zuwa gaba. Za su haɗu da sauran su yi hidima a cikin rumfa ta taruwa.
25Za su dena yin hidima sa'ad da suka kai shekara hamsin. A waɗannan shekarun ba za su ƙara yin hidima ba.26Za su iya taimakon 'yan'uwansu waɗanda suke ci gaba da yin hidima a rumfa ta taruwa, amma su ba za su ƙara yin hidima ba. Sai ka jagoranci Lebiyawa cikin dukkan waɗannan al'amura.

9

1Yahweh ya yi magana da Musa a cikin jejin Sinai, a cikin wata na biyu bayan sun fito daga ƙasar Masar. Ya ce,2"Sai mutanen Isra'ila su kiyaye idin Ƙetarewa a lokacin da aka ayyana cikin shekara.3A kan rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, da yamma, dole ne ku kiyaye idin Ƙetarewa a lokacin da aka ayyana shi a shekara. Ku kiyaye shi ku bi dukkan ka'idodi, ku yi biyayya da dukkan farillan da aka ayyana domin sa."

4Haka, Musa ya gaya wa mutanen Isra'ila ya wajaba su riƙa kiyaye Idin Ƙetarewa.5Haka suka kiyaye Idin Ƙetarewa a cikin wata na fari a kan rana ta goma sha huɗu ga watan, da yamma, a cikin jejin Sinai. Mutanen Isra'ila suka kiyaye dukkan abin da Yahweh ya ummarci Musa ya yi.
6Akwai waɗansu mutanen da suka zama ƙazamtattu ta wurin taɓa gawa. Ba su iya kiyaye Idin Ƙetarewar a wannan ranar ba.7Waɗannan mutane suka ce da Musa, "Mun ƙazamtu ta wurin taɓa gawar wani mutum. Meyasa hana aka mu miƙa hadaya ga Yahweh tare da sauran mutanen Isra'ila a lokacin da a ka ayyana na shekara?"8Musa yace da su, "Ku jira in ji umarnin da Yahweh zai bani saboda ku."
9Sai Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,10"Ka yi magana da mutanen Isra'ila. Cewa, 'Idan wani a cikin ku, ko zuriyarku ya ƙazamtu ta wurin taɓa gawa, yana cikin tafiya mai nisa, zai iya kiyaye Idin Ƙetarewa ga Yahweh.'
11A cikin wata na biyu a kan rana ta goma sha huɗu da yamma, za su iya cin abincin Idin Ƙetarewa. Za su ci ragon Idin Ƙetarewa da gurasa marar gami da ganyaye masu ɗăci.12Kada su rage shi har zuwa safiya, ko su karya ƙasusuwan. Dole ne su kiyaye dukkan ka'idodin da aka ayyan na Idin Ƙetarewar.
13Amma dukkan mutum mai tsarki kuma ba tafiya ya ke yi ba, amma bai yi Idin Ƙetarewar ba, wannan mutum za a datse shi daga cikin mutanensa saboda bai miƙa hadaya ga Yahweh yadda ake bukata a lokacin da aka ayyana a shekara ba. Wannan mutum zai ɗauki zunubinsa.14Idan akwai baƙo a cikin ku yana kiyaye Idin Ƙetarewa domin ya ba Yahweh girma, sai ya kiyaye dukkan abin da aka umarta, da ka'idodinsa, da dukkan dokokinsa. Dokoki ɗaya ne za su shafi wanda aka haifa a ƙasar da kuma baƙo."
15A ranar da aka kafa alfarwar, sai girgije ya sauka ya rufe ta, wato rumfar ta alƙawari. Da yamma girgijen yana bisan alfarwar. Ya zama kamar wuta har zuwa safiya.16Haka ya ci gaba. Da dare girgijen ya rufe alfarwar kamar wuta.17Duk lokacin da aka ɗauke girgijen daga bisa rumfar, sai mutanen Isra'ila su ci gaba da tafiyarsu. Dukkan sa'adda girgijen ya tsaya wuri ɗaya, sai mutanen su yi zango.
18Idan Yahweh ya bada ummurni, sai mutanen Isra'ila su tafi, idan ya bada ummurni sai su yi zango. Sa'ad da girgijen ya tsaya a bisan alfarwar, sai su tsaya a zangonsu.19Idan girgijen ya tsaya a bisan alfarwar kwanaki da yawa, sai mutanen Isra'ila su yi biyayya da ka'idodin Yahweh ba za su tafi ba.
20Wani lokaci girgijen yakan tsaya a bisa alfarwar har 'yan kwanaki. A wannan lokaci, sai su yi biyayya da umarnin Yahweh--sai su yi zango sai in ya bada umarni sai su tafi.21Wani lokacin sai girgijen ya kasance a bisa zangon tun daga yamma har safiya. Idan girgijen ya tashi da safe sai su tafi. Idan kuma ya ci gaba da tsayawa dare da rana, sai sa'ad da girgijen ya tashi za su tafi.
22Duk sa'ad da girgijen ya tsaya a bisa alfarwar kwana biyu ko wata ɗaya ko shekara, idan dai girgijen yana tsaye a nan, mutanen za su tsaya a zangonsu ba za su tafi ba. Amma duk lokacin da aka ɗauke girgijen sai su kama tafiyarsu.23Za su yi zango sa'adda Yahweh ya bada umarni, kuma su tafi bisa ga umarninsa. Sun yi biyayya da umarnin da Yahweh ya ba Musa.

10

1Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,2"Ka yi kakaki biyu na azurfa. Ka yi su da bugaggiyar azurfa. Ka yi amfani da ƙahonin domin ka kira ƙungiyoyin jama'a su zo su taru kuma domin ka kira ƙungiyoyin jama'a su zakuɗa da zangunansu.

3Fristoci su busa kakakin domin su kira dukkan ƙungiyoyin jama'a su taru a gaban rumfa ta taruwa.4Idan firistoci suka busa kakaki ɗaya, sai shugabanni da shugabannin iyalai na Isra; ila, su zo su taru.5Idan ka busa alama mai ƙara, sai zangon gabas su fara tafiyarsu.
6Idan ka busa alama mai ƙara ta biyu, sai zanguna na zangon kudu su fara tafiyarsu. Suma sai su busa alama mai ƙara domin su tafi.7Sa'anda jama'a suka taru wuri ɗaya sai ka busa ƙahonin, amma ba da ƙarfi ba.8'Ya'yan Haruna da firistoci ne za su busa kakakin. Wannan za ta zama ka'ida a gare ka dukkan zamanun mutanenka.
9Idan kuka tafi yaƙi cikin ƙasarku da maƙiyi wanda yake găba da ku, sai ku busa alama da kakakin. Ni, Yahweh Allahnku, zan tuna daku in cece ku daga maƙiyanku.
10Kuma, lokacin bukukuwa, da bukukuwanku na yau da kullum ko na farkon wata, sai ku busa kakaki saboda baye--bayenku na ƙonawa da hadayinku da baye--bayenku na zumunci. Waɗannan abubuwa za su sa in tuna da ku, Ni Allahnku. Ni ne Yahweh Allahnku."
11A cikin shekara ta biyu, a cikin wata na biyu, a rana ta ashirin ga watan, sai aka ɗauke girgijen daga bisa rumfar taruwa ta umarnin alƙawari.12Sai mutanen Isra'ila suka ci gaba da tafiyarsu daga jejin Sinai. Sai girgijen ya tsaya a jejin Faran.13Suka yi tafiyarsu ta fari, suna bin umarnin da Yahweh ya ba Musa.
14Sai zangon dake ƙarƙashin tutar zuriyar Yahuda suka fara tafiya, suka fara gusawa da sojojinsu. Nashon ɗan Amminadab ya jagoranci sojojin Yahuda.15Netanel ɗan Zuyar ya jagoranci sojojin zuriyar Issaka.16Eliyab ɗan Helon ya jagoranci sojojin zuriyar Zebulun.
17Zuriyar Geshon da Merari, waɗanda ke lura da alfarwa, suka ɗauki alfarwar suka tafi.18Na biye su ne sojojin dake ƙarƙashin tutar zangon Ruben suka shirya suka tafi. Elizur ɗan Shedur ya jagoranci sojojin Ruben.19Shenumiyel ɗan Zurishaddai ya jagoranci sojojin zuriyar Simeyon.20Eliyasaf ɗan Dewuyel ya jagoranci sojojin kabilar zuriyar Gad.
21Sai Kohatiyawa suka shirya fita. Suka ɗauki kayayyaki masu tsarki na wurin sujada. Waɗansu za su shirya alfarwa kafin Kohatiyawa su zo zango na gaba.22Sojoji na ƙarƙashin tutar zuriyar Ifraim su ne na gaba. Elishama ɗan Amihud ya jagoranci sojojin Ifraim.23Gamaliyel ɗan Fedazur ya jagoranci sojojin kabilar zuriyar Manasse.24Abidan ɗan Gidiyoni ya jagoranci sojojin kabilar zuriyar Banyami.
25Sojojin da suka yi zango a ƙarƙashin tutar zuriyar Dan su ne suka tashi daga ƙarshe. Ahiyezer ɗan Ammishaddai ya jagoranci sojojin Dan.26Fagiyel ɗan Okran ya jagoranci sojojin kabilar zuriyar Asha.27Ahira ɗan Inan ya jagoranci sojojin kabilar zuriyar Naftali.28Wannan shi ne yadda sojojin mutanen Isra'ila suka shirya suka fita tafiyarsu.
29Musa ya yi magana da Hobab ɗan Rewuyel mutumin Midiya. Rewuyel ne mahaifin matar Musa. Musa ya yi magana da Hobab ya ce, "Za mu tafi wurin da Yahweh ya bayyana. Yahweh yace, 'Zan baku shi.' Ka biyo mu zamu kyautata maka. Yahweh ya yi alƙawari zai kyautatawa Isra'ila."30Amma Hobab yace da Musa, "Ba zan bi ku ba. Zan tafi ƙasata wurin mutanena."
31Sai Musa ya amsa, "Idan ka yarda kada ka rabu da mu. Ka san yadda a ke yin zango a cikin jeji. Sai ka kula da mu.32Idan ka biyo mu, zamu kyautata ma ka kamar yadda Yahweh zai kyautata mana."
33Suka yi tafiya ta kwana uku daga tsaunin Yahweh. Akwatin alƙawari na Yahweh ya tafi a gabansu kwana uku domin ya samar masu wurin da za su huta.34Girgijen Yahweh yana bisansu da rana inda suke tafiya.
35Dukkan lokacin da akwatin alƙawari ya tashi, Sai Musa yace, "Yahweh, tashi ka watsar da maƙiyanka. Ka sa masu ƙin ka su gudu daga wurinka."36Duk sa'ad da akwatin alƙawari ya tsaya, sai Musa yace,"Yahweh ka dawo wurin Isra'ila masu yawa dubbai."

11

1Sai mutanen suka yi kuka game da matsalolinsu Yahweh kuwa yana ji. Yahweh ya ji ya yi fushi. Sai wuta ta fito daga wurin Yahweh ta kama a cikinsu har ta ƙone gefunan wasu bayan wani zangon.2Sai mutanen suka yi kira ga Musa, sai Musa ya yi addu'a ga Yahweh, sai wutar ta mutu.3Aka kira wannan wurin da suna Tabera, saboda wutar Yahweh ta yi ƙuna a wurin.

4Sai waɗansu baƙi suka fara sauka a zangon zuriyar Isra'ila. Suka so su ci abinci mai kyau. Daga nan mutanen Isra'ila suka fara kuka suka ce, "Wane ne zai ba mu nama mu ci?5Mun tuna da kifin da muka ci a Masar kyauta, da kukumba da kabewa da albasa da kankana da tafarnuwa.6Yanzu har ma bamu da marmari, saboda wannan mannar kaɗai muke iya gani."
7Manna dai tana kama da ƙwayar riɗi. Launinta kuma kamar ƙaro.8Mutanen suka zagaya suka ɗebo ta. Suka niƙa ta a dutse, suka daka ta a turmi, su ka dafa ta a tukwane, suka yi waina da ita. Sai ɗanɗanonta ya zama kamar na sabon man zaitun.
9Sa'ad da raɓa ta sauko a kan zangon da dare, manna kuma ta faɗo.10Musa ya ji mutanen suna ta kuka cikin iyalansu, kowanne mutum ya fito ƙofar rumfarsa. Sai Yahweh ya yi fushi ƙwarai, Musa kuwa yana ganin koken-koken nasu bai yi dai-dai ba.
11Musa yace da Yahweh, "Me yasa ka yiwa mutanenka mummunan abu haka? Me yasa baka yarda da ni ba? Ka sa na ɗauki nawaiyar mutanen nan dukka.12Ni na ɗauki cikin dukkan mutanen nan? Ni na haife su da zaka ce dani, 'Ka ɗauke su a ƙirjinka kamar yadda uba yake ɗaukar jariri?' Ni zan ɗauke su in kai su ƙasar da ka rantse wa kakaninsu cewa za ka ba su?
13A ina zan sami naman da zan ba dukkan mutanen nan? Suna ta kuka a gabana suna cewa, 'Ka bamu nama mu ci.'14Ba zan iya da mutanen nan ba ni kaɗai. Sun yi mani yawa.15Tun da haka kake yi da ni, gara ka kashe ni yanzu--Idan na sami tagomashi a idanunka -- kada ka bari in ga takaicina."
16Sai Yahweh yace da Musa, "Ka kawo dattawan Isra'ila guda saba'in a wurina. Ka tabbatar su dattawa ne kuma shugabannin jama'a. Ka kawo su rumfa ta taruwa su tsaya nan tare da kai.17Zan sauko in yi magana da su a can. Zan ɗauka daga Ruhun da yake a kanka in sashi a kansu. Za su ɗauki nawayar mutanen tare da kai. Ba za kayi ta fama da su kai kaɗai ba.
18Ka ce da mutanen, 'Ku tsarkake kanku, gama gobe za ku ci nama sosai, gama kun yi kuka kuma Yahweh ya ji. Kun ce, "Wane ne zai ba mu nama mu ci? Gama dã abincinmu ne a Masar." Yahweh zai ba ku nama, kuma za ku ci shi.19Ba wai zaku ci nama yini ɗaya ko biyu ko biyar ko goma ko ma ashirin ba,20amma zaku yi wata guda kuna cin nama har sai ya fito maku a ƙofar hancinku. Sai ya ginshe ku, gama kun ƙi Yahweh, wanda ke cikin ku. Kun yi kuka a gabansa. Kun ce, "Meyasa muka baro Masar""'
21Sa'an nan Musa yace, "Mutane 600,000 ne ke tare dani, kuma ka ce, 'Zan ba su nama su yi ta ci har wata guda ɗungum.'22Garkunan shanu dana tumaki za a yanka har ya ƙosar da su?"23Sai Yahweh yace da Musa, "Hannuna ya kasa ne? Yanzu zaka gani ko maganata gaskiya ce ko a'a."
24Musa ya fita ya faɗawa mutanen maganar Yahweh. Ya tattara dattawan su saba'in ya sa suka kewaye rumfar.25Yahweh ya zo cikin girgije ya yi magana da Musa. Yahweh ya ɗauka daga cikin Ruhun da yake kan Musa ya sa a kan dattawan su saba'in. Sa'ad da Ruhun ya sauko a kansu, sai suka yi anabci, amma a wannan lokacin ne kaɗai ba su ƙara yi ba kuma.
26Sai mutane biyu suka rage a zangon, su ne Eldad da Medad. Su ma Ruhun ya sauko a kansu. An rubuta sunayensu, amma basu fita sun je rumfa ta taruwa ba. Duk da haka, sun yi anabci a cikin zangon.27Wani saurayi ya ruga daga cikin zangon ya gaya wa Musa cewa, Ga Eldad da Medad suna yin anabci a cikin zango."
28Sai ɗaya daga cikin zaɓaɓɓun mutanensa Yoshuwa mataimakin Musa, ya ce da Musa, "Shugabana Musa, ka hana su."29Musa yace da shi, "Kana jin kishi saboda ni ne? So na ne dukkan mutanen Yahweh su zama annabawa ya kuma sawa dukkan su Ruhunsa!"30Daga nan sai Musa da dattawan Isra'ila suka koma cikin zango.
31Daga nan sai iska ta taso daga wurin Yahweh ta kawo makware daga teku. Suka faɗo kusa da zangon, misalin kusan tafiyar yini ɗaya a wannan sashi, haka kuma a ɗaya sashin. Makwaren suka kewaye zangon wajen kamu ɗaya daga bisa suka kere ƙasa.32Mutanen suka yi ta tara makware a wannan yini dukka da wannan daren dukka da kuma washe gari dukka. Kowanne mutum ya kama makware da yawan gaske. Suka raba makwaren cikin zangon dukka.
33Sa'anda naman ke tsakankanin haƙoransu, suna tauna shi, Sai Yahweh ya yi fushi da su. Ya sa wani ciwo mai zafi ya auko masu.34Aka kira sunan wannan wurin Kibrot Hattãba, saboda sun rufe mutanen da suka yi zarin cin nama.35Daga Kibrot Hattãba mutanen suka yi tafiya zuwa Hazerot, suka tsaya a can.

12

1Sai ya zama Miriyam da Haruna suka yi gunaguni a kan Musa saboda wata mace Bakushiya da ya aura.2Suka ce, "Kai kaɗai ne Yahweh ya yi magana da kai? Mu ma bai yi magana da mu ba ne?" Sai Yahweh ya ji abin da suka ce.3Musa kuwa mutum ne mai tawali'u, fiye da kowa a duniya.

4Nan take Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna da Miriyam: "Ku uku ɗin, ku fito, ku zo rumfa ta taruwa." Sai su uku ɗin suka fito suka je.5Sa'an nan Yahweh ya sauko ta cikin umudin girgije. Ya tsaya a ƙofar rumfa ta taruwa ya kira Haruna da Miriyam. Sai suka matso.
6Sai Yahweh yace, "Sa'ad da annabina ke tare da ku, zan bayyana kaina a wurinsa ta wurin ruya in yi magana da shi cikin mafarkai.7Bawana Musa ba haka yake ba. Shi mai aminci ne a cikin dukkan gidana.8Na kan yi magana da shi kai tsaye, ba a zaurance ko da ruya ba. Ya kan ga zatina. Me yasa ba ku ji tsoron yin gunaguni a kan bawana Musa ba?"
9Fushin Yahweh ya yi ƙuna a kansu, kana ya bar su.10Girgijen ya tashi daga bisa rumfar, nan da nan Miriyam ta zama kuturwa--ta yi fari kamar auduga. Da Haruna ya juya sai ya ga Miriyam ta zama kuturwa.
11Sai Haruna yace da Musa, "Ya shugabana, idan ka yarda kada ka riƙe mu a kan wannan abu. Mun yi magana cikin wawanci, kuma mun yi zunubi.12Idan ka yarda kada ka barta ta zama kamar jaririn da naman jikinsa ya lalace sa'ad da yake fitowa daga cikin mahaifar uwarsa."
13Sai Musa ya yi kira zuwa ga Yahweh. Ya ce, "Idan ka yarda ka warkar da ita, Ya Allah, idan ka yarda."14Sai Yahweh yace da Musa, "Idan ubanta ya tofa mata yau a fuska, za a ƙasƙantar da ita har kwana bakwai. Ka rufe ta a bayan zango har kwana bakwai. Bayan haka sai ka dawo da ita."15Haka aka rufe Miriyam har kwana bakwai a bayan zango. Mutanen ba su tafi ba sai da ta dawo zangon.
16Bayan haka, mutanen suka tafi daga Hazerot suka yi zango a cikin jejin Faran.

13

1Sa'an nan Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,2"Ka aiki waɗansu mutane su dubo ƙasar Kan'ana, wadda na ba mutanen Isra'ila. Ka aiki mutum ɗaya daga kowacce kabila ta ubanninsu. Kowanne ya zama shugaba ne a cikinsu."

3Musa ya aike su daga jejin Faran, domin su yi biyayya da ummarnin Yahweh. Dukkan su shugabanni ne a cikin mutanen Isra'ila.4Ga sunayensu: daga kabilar Ruben, Shammuya ɗan Zakkur;
5daga kabilar Simiyon kuma, Shafat ɗan Hori;6daga kabilar Yahuda, kuma Kaleb ɗan Yefunne;7daga kabilar Issakar kuma, Igal ɗan Yosef;8daga kabilar Ifraim kuma, Hosheya ɗan Nun;
9daga kabilar Benyamin kuma, Falti ɗan Rafu;10daga kabilar Zebulun kuma, Gaddiyel ɗan Sodi;11daga kabilar Yosef kuma, (wato daga kabilar Manasse), Gaddi ɗan Susi;12daga kabilar Dan kuma, Ammiyel ɗan Gemalli;
13daga kabilar Asha kuma, Shetur ɗan Mikayel;14daga kabilar Naftali kuma, Nãbi ɗan Bofsi;15daga kabilar Gad kuma, Gewuyel ɗan Maki.16Waɗannan su ne sunyen mazajen da Musa ya aika su dubo ƙasar. Musa ya kira Hosheya ɗan Nun da suna Yoshuwa.
17Musa ya aike su domin su dubo ƙasar Kan'ana. Ya ce da su, "Ku bi ta Negeb ku hau ta ƙasar kan tudu.18Ku dubo ƙasar ku ga yadda ta ke. Ku yi la'akari da irin mutanen da suke zauna a can, ko suna da ƙarfi ko kuwa raunana ne, kuma ko suna da yawa ko 'yan kaɗan ne.19Ku ga yadda ƙasar ta ke inda suke zaune. Ta na da kyau ko ba ta da kyau? Yaya biranen suke? Kamar zango--zango suke, ko kuwa ƙayatattun birane ne?20Ku gano yadda ƙasar ta ke, ko shuka za ta iya yin girma da kyau ko babu, ko akwai itatuwa ko babu. Ku yi ƙarfin hali ku kawo abin misali daga irin amfanin ƙasar." Lokacin kuwa na nunar fari na inabi ne.
21Sai mazajen suka je suka duba ƙasar tun daga jejin Zin zuwa Rehob, kusa da Lebo Hamat.22Suka hau ta Negeb suka ɓullo Hebron. Ahiman da Sheshayi da Talmai, waɗanda jinsinsu ya fito daga Anak, suna nan. Ya zama an gina Hebron shekaru bakwai kafin Zowan ta cikin Masar.
23Sa'ad da suka kawo kwarin Eshkol, suka yanki reshe da kurshen zaitun. Suka sagalo shi a jikin sanda tsakanin ƙungiyoyinsu biyu. Suka kawo rumman da ɓaure kuma.24Wannan wurin a ka kira da suna kwarin Eshkol, saboda kurshen zaitun da mutanen Isra'ila suka yanko daga can.
25Bayan kwana arba'in, suka dawo daga dubo ƙasar.26Suka dawo wurin Musa da Haruna da dukkan taron jama'ar Isra'ila a cikin jejin Faran a Kadesh. Suka kawo masu labari tare da dukkan jama'a, suka nuna masu irin amfanin ƙasar.
27Suka ce da Musa, "Mun kai ƙasar daka aike mu. Gaskiya ne tana zubo da madara da zuma. Ga irin amfanin wurin.28Duk da haka, mutanen da suka yi gidajensu a can ƙarfafa ne. Biranen ƙayatattu ne manya ne kuma. Mun kuma ga kabilar Anak a can.29Amelekawa na zaune a Negeb. Hitiyawa da Yebusawa da Amoriyawa na da gidajensu a ƙasar kan tudu. Kan'aniyawa na zama a bakin teku kusa da Kogin Yodan."
30Kaleb ya sa mutanen suka yi shiru a gaban Musa yace, '"Bari mu je mu karɓe ƙasar, gama ba shakka za mu iya cin nasara da ita."31Amma mazajen da suka je tare da shi suka ce, "Ba za mu iya kai wa mutanen nan hari ba domin sun fi mu ƙarfi."
32Sai suka kai rahoton karya gwiwa ga mutanen Israila game da ƙasar da suka je suka dubo. Suka ce, "Ƙasar da muka je muka dubo cinye mazauna ƙasar su ke yi. Dukkan mazajen da muka gano a can dogaye ne ƙwarai.33Mun gano jarumawa a can, zuriyar Anak, waɗanda dama jarumawa ne. Idan a ka kwatanta mu da su, mu kamar fara mu ke, haka kuma suka gan mu."

14

1A wannan daren al'ummar dukka ta yi kuka da ƙarfi.2Dukkan mutanen suka ba Musa da Haruna laifi. Dukkan al'ummar suka ce da su, "Da ma mun mutu a ƙasar Masar, ko nan cikin jeji!3Meyasa Yahweh ya kawo mu wannan ƙasar mu mutu ta wurin takobi? Matayenmu da ƙanananmu za su cutu. Ba zai fi kyau a gare mu mu koma Masar ba?"

4Suka cewa junansu, "Bari mu zaɓi wani shugaba, mu koma Masar."5Sai Musa da Haruna suka kwanta a gaban taron mutanen Isra'ila da fuskokinsu a ƙasa.
6Yoshuwa ɗan Nun da Kaleb ɗan Yefunne, waɗanda ke cikin waɗanda aka aika dubo ƙasar, suka tsage tufafinsu.7Suka yi magana da al'ummar mutanen Isra'ila. Suka ce, "Ƙasar da muka ratsa muka dubo muka wuce, ƙasa ce mai kyau ƙwarai.8Idan Yahweh ya ji daɗin mu, zai kai mu cikin wannan ƙasa ya ba mu ita. Ƙasar tana zubowa da madara da zuma.
9Amma kada ku bijire wa Yahweh, kuma kada ku ji tsoron mutanen ƙasar, gama su gurasa ne a gare mu. Tsaronsu zai rabu da su, saboda Yahweh na tare da mu. Kada ku ji tsoron su."10Sai dukkan taron suka ce a jejjefe su da duwatsu. Amma sai ga darajar Yahweh ta bayyana ga dukkan mutanen Isra'ila a rumfar taruwa.
11Yahweh yace da Musa, "Har yaushe waɗannan mutane za su rena ni? Har yaushe za su kasa gaskatawa dani, su rena dukkan alamu da ikon dana yi a cikin su?12Zan sa annoba ta auko masu, ba za su zama gãdona ba kuma, in sa kabilarka ta zama babbar al'ummar da za ta fi su girma."
13Musa yace da Yahweh, "Idan ka yi haka Masarawa za su ji labari, saboda ka kuɓutar da waɗannan mutane da ikonka daga wurinsu.14Za su gaya wa mazaunan wannan ƙasar. Sun ji labarinka, Yahweh, kana tare da waɗannan mutane ne saboda ana ganin ka fuska da fuska. Girgijenka yana tsayawa a bisa mutanenka. Kana tafiya a gabansu da umudin girgije da rana da dare kuwa da umudi na wuta.
15Yanzu idan ka kashe mutanen nan kamar mutum ɗaya, sa'an nan al'umman da suka ji labarin jaruntakarka zasu ce,16'Saboda Yahweh ya kăsă kai mutanen nan ƙasar da ya rantse zai ba su, sai ya kashe su a cikin jeji.'
17Ina roƙon ka, ka yi amfani da ikonka mai girma. Gama ka ce,18'Yahweh mai jinkirin fushi ne kuma mai yalwar jinƙai. Yakan gafarta mugunta da laifofi. Ba zai yafe mugunta ba sa'ad da ya kawo horon zunubin kakanni a kan zuriyarsu, har zuwa zuriya ta uku da ta huɗu.'19Ka yafe, zunubin mutanen nan, ina roƙon ka, saboda alƙawarin jinƙanka mai girma, kamar yadda kake ta gafarta wa mutanen nan tun daga cikin Masar har zuwa yanzu."
20Sai Yahweh yace, "Na yafe masu saboda roƙonka,21amma gaskiya, kamar yadda nake a raye, dukkan duniya zata cika da ɗaukakata,22dukkan mutanen nan da suka ga ɗaukakata da alamu na ikon da na yi a cikin Masar da cikin jeji--har yanzu suna jarabta ta sau goma kenan ba su saurari muryata ba.
23Babu shakka ba za su ga wannan ƙasar da nayi wa ubanninsu alƙawari ba. Waɗannan da suka rena ni ba ko ɗaya a cikin su da zai gan ta,24sai bawana Kaleb kaɗai, saboda da ruhunsa daban yake. Ya bini da gaske; zan kai shi ƙasar da ya je ya dubo. Zuriyarsa zasu gaje ta.25(To Amelikawa da Kan'aniyawa suna zaune a cikin kwari.) Gobe ka juya ka tafi jejin ka bi ta Teku na Iwa."
26Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna. Ya ce,27"Har yaushe zan jure da muguntar mutanen nan da suke ta ganin laifina? Na ji gunagunin mutanen Isra'ila game da ni.
28Ka ce da su, 'Yahweh yace, 'kamar yadda nike a raye, 'kamar yadda kuka yi magana ina ji, ga abin da zan yi ma ku:29Dukkan ku da kuka yi gunaguni a kaina zaku mutu a cikin jeji, ku da aka ƙirga cikin lissafi, dukkan ma su shekara ashirin zuwa gaba.30Babu shakka ba zaku shiga ƙasar dana yi alƙawari zan yi maku gida ba. Sai dai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
31Amma ƙanananku da kuka ce abin zai shafe su, su zan kai cikin ƙasar. Za su ji yadda ƙasar da kuka ƙi ta ke!32Ku kuwa jikkunanku za su faɗi su mutu a cikin jeji.33'Ya'yanku za su zama makiyaya a cikin jeji har shekara arba'in. Dole ne za su sha sakamakon aikinku na bijirewa a cikin jeji har sai gawarwakinku sun ƙare.
34Kamar yadda kuka yi kwana arba'in kuna dubo ƙasar, Haka zaku yi shekara arba'in kuna ɗaukar alhakin zunubanku-- kowanne kwana ɗaya a matsayin shekara ɗaya, zaku gane abin da zai faru da ku idan na yi găba da ku.35Ni, Yahweh ne na faɗa. Babu shakka haka zan yi wa wannan al'umma mai mugunta da suka haɗa kai gãba dani. Za a datse su gaba ɗaya, a nan za su mutu."
36Haka mazajen da Musa ya aika su gewayo ƙasar, waɗanda suka dawo suka kawo rahoton da ya sa dukkan taron jama'a suka yi gunaguni a kan Musa game da ƙasar--37Waɗan nan mazaje da suka kawo rahoto marar daɗi aka hallaka su da annoba daga wurin Yahweh suka mutu.38A cikin mazajen da suka gewaya ƙasar, Yoshuwa ɗan Nun da Kaleb ɗan Yefunne ne kaɗai suka rage da rai.
39Sa'ad da Musa ya bada wannan rahota ga mutanen Isra'ila dukka, sai suka yi baƙinciki ƙwarai.40Suka fita tun da sassafe suka hau bisa kan tsauni suka ce, "Dubã, ga mu nan, kuma za mu tafi wurin da Yahweh ya yi alƙawari, gama mun yi zunubi."
41Amma Musa yace, "Meyasa kuke wulakanta ummarnin Yahweh? Ba za ku yi nasara ba.42Kada ku tafi, saboda Yahweh ba ya tare da ku, domin ya kare ku, don kada abokan gãbarku su yi nasara a kanku ba.43Su Amelekawa da Kan'aniyawa suna can, kun zo ku mutu da kaifin takobi saboda kun dena bin Yahweh. Saboda haka ba zai kasance tare da ku ba."
44Amma sai suka yi taurin kai suka tafi ƙasar kan tudu; amma kuma, ko Musa ko akwatin alƙawarin Yahweh ba wanda ya bar zangon.45Sai Amelekawa suka sauko, Kan'aniyawa ma suka sauko daga tuddai. Suka kai hari a kan Isra'ilawa suka kuma ci nasara a kansu har zuwa Horma.

15

1Sai Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,2"Kayi magana da mutanen Isra'ila ka ce dasu, 'Sa'ad da kuka shiga ƙasar da zaku zauna, wadda Yahweh zai ba ku,3sai ku shirya baiko da wuta domin Yahweh, ko baiko na ƙonawa ko hadaya domin a cika alƙawarin baiko na yardar rai, ko baiko na idodinku, domin ku kawowa Yahweh baiko na ƙamshi mai daɗi daga garkenku ko daga dangwalinku.

4Dole ku kawo wa Yahweh baiko na ƙonawa da baiko na gari da hadaya ta sha ta gari mai kyau wanda aka gauraya da mai kwalba bakwai.5Kuma za ku haɗa baiko na ƙonawar ko hadayar da ruwan inabi saboda sha domin kowanne ɗan rago.
6Idan rago ne ake miƙawa, sai kuma a shirya baiko na gari awo uku wanda aka gauraya da mai kwalba biyar.7Domin baiko na sha kuwa sai a bada ruwan inabi kwalba biyar. Zai bada ƙanshi mai daɗi ga Yahweh.
8Idan kuka shiya bijimi domin baiko na ƙonawa ko hadaya domin ku cika alƙawari, ko baiko na zumunci ga Yahweh,9sai ku miƙa bijimin tare da baiko na hatsi, gari mai kyau awo uku wanda aka gauraya da mai kwalba biyu.10Dole kuma ku ba da baiko na ruwan inabi kwalba biyu, baikon da aka yi da wuta, da zai bada ƙanshi mai daɗi ga Yahweh.
11Haka za ayi wa kowanne bijimi da kowanne rago da kowanne ɗan rago da 'yan awaki.12Kowacce hadaya za ku shirya ku miƙa haka za ku yi ta kamar yadda aka bayyana a nan.13Dukkan 'yan ƙasa da aka haifa a Isra'ila haka za su yi waɗannan abubuwa, sa'adda wani ya kawo baikon da za ayi da wuta, domin ya kawo ƙanshin da zai gamshi Yahweh.
14Idan baƙo na zaune wurinku, ko duk wanda zai zauna a cikin ku a dukkan zamanin mutanenku, dole ne ya yi baikon da za ayi da wuta domin ya bada ƙanshi mai daɗi ga Yahweh. Dole ne shi ma ya yi kamar yadda kuke yi.15Dokar da ta shafi taron jama'arku ita ce za ta shafi baƙon da yake zaune a wurinku, wannan zaunanniyar doka ce gare ku dukkan zamanin jama'arku. Kamar yadda kuke haka ma wanda ya zo wurin ku zai zama. Dole ne ya yi kamar yadda kuke yi a gaban Yahweh.16Doka da ka'idar da ta shafe ku ita ce kuma za ta shafi baƙon da yake tare da ku.'"
17Yahweh ya sake yin magana da Musa. Ya ce,18"Ka yi magana da mutanen Isra'ila ka ce da su, 'Idan kuka zo ƙasar da zan kai ku,19idan kuka ci abincin da aka yi a ƙasar, sai ku yi baiko ku miƙa shi gare ni.
20Cikin abin da za ku fara ɓarzawa sai ku yi dunƙule da shi ku ɗaga shi kamar baiko na ɗagawa a masussuka. Ga yadda za ku ɗaga shi.21Daga abin da kuka ɓarza da fari sai ku yi bayarwa ta ɗagawa a dukkan zamanin mutanenku.
22Wani lokaci za ku yi zunubi ba tare da saninku ba, idan ba ku yi biyayya da dukkan umarnin dana gaya wa Musa ba--23dukkan abin dana umarce ku ta wurin Musa tun daga ranar dana fara baku umarni har zuwa zamanin mutanenku dukka.24A lamarin zunubin da aka yi ba tare da niyya ba kuma jama'a ba su sani ba, sai dukkan jama'a kowa ya yi baiko na ƙonawa da bijimi domin ya bada shessheƙi na ƙanshi mai daɗi ga Yahweh. Tare da wannan sai a yi baiko na hatsi dana sha, kamar yadda aka umarta a ka'idodi, da baiko na ɗan akuya ɗaya domin baiko na zunubi.
25Sai firist ya yi kafara domin dukkan taron jama'ar Isra'ila. Za a gafarta masu saboda zunubin kuskure ne. Sun kawo hadayarsu, baikon da aka yi da wuta zuwa gare ni. Sun kawo baiko na zunubi gare ni gama kuskure ne.26Sa'an nan za a gafartawa dukkan taron jama'ar Isra'ila, da dukkan baƙin da suke zaune tare da su, saboda dukkan taron jama'ar sun yi zunubin ba tare da sanin su ba,
27Idan wani mutum ya yi zunubi cikin rashin sani, sai ya miƙa baiko na ɗan akuya bana ɗaya saboda zunubinsa.28Sai firist ya yi kafara a gaban Yahweh saboda mutumin da ya yi zunubi ba tare da saninsa ba. Idan aka yi kafara za a gafarta wa wannan mutum.29Sai ku kasance da doka iri ɗaya ga duk wanda ya yi wani abu ba tare da saninsa ba. Doka ɗaya da ta shafi ɗan ƙasa da aka haifa a Isar'ila ita ce kuma za ta shafi baƙin dake zaune a cikin su.
30Amma idan mutum ya yi ba dai--dai ba cikin sanin sa, ko ɗan ƙasa ne ko baƙo, ya yi mani zunubi. Wannan mutum za a datse shi daga cikin mutanensa.31Saboda ya rena maganata ya karya dokokina, wannan mutum za a datse shi sarai. Zunubinsa zai zauna a kansa.
32Sa'ad da mutanen Isra'ila ke a cikin jeji, sai suka tarar da wani mutum na tattara itace ranar Asabaci.33Waɗanda suka tarar da shi suka kawo shi wurin Musa da Haruna da dukkan taron jama'ar Isra'ila.34Sai suka sa shi a cikin kurkuku saboda ba a yanke abin da za a yi masa ba.
35Sa'an nan Yahweh yace da Musa, "Sai a kashe wannan mutum. A kai shi bayan zango, dukkan jama'a su jejjefe shi da duwatsu.36Haka dukkan jama'ar suka kawo shi bayan zango suka jejjefe shi da duwatsu har ya mutu kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.
37Yahweh ya sake yin magana da Musa. Ya ce,38"Kayi magana da 'ya'yan Isra'ila ka umarce su da su yi tutoci su maƙala a kafaɗun rigunansu, su maƙala su a kowacce kafaɗa da shuɗin zare. Za su yi haka a dukkan zamanin mutanensu.39Idan kuka dube su za su zama abin tunawa da dukkan dokokina na musamman a gare ku. Ku ɗauke su a wurinku domin kada ku dubi zuciyarku da idanunku ku yi karuwanci da su.
40Ku yi wannan domin ku tuna ku yi biyayya da dukkan dokokina, kuma domin ku zama da tsarki, keɓaɓɓu domina Allahnku.41Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya fito da ku daga ƙasar Masar, ya zama Allahnku. Ni ne Yahweh Allahnku."

16

1Ana nan sai Korah ɗan Izhar ɗan Kohat ɗan Lawi, tare da Datan da Abiram 'ya'yan Eliyab da On ɗan Felet, zuriyar Ruben, suka taru da waɗansu mutane.2Suka tayar wa Musa, tare da waɗansu daga cikin mutanen Isra'ila, su ɗari biyu da hamsin shugabannin jama'a sanannu sosai a cikin jama'a.3Suka tattaro kansu domin su fuskanci Musa da Haruna. Suka ce da su, "Fankamarku ta yi yawa! Dukkan mutanen keɓaɓɓu ne, kowanne ɗayan su, kuma Yahweh na tare da su. Meyasa kuke ɗaukaka kanku fiye da sauran mutanen Yahweh?"

4Sa'ad da Musa ya ji haka, sai ya kwanta da fuskarsa ƙasa.5Ya yi magana da Korah da dukkan waɗanda ke tare da shi, "Gobe da safe Yahweh zai nuna wanda ke nasa, da wanda ya keɓe domin kansa. Zai kawo wannan mutum kusa da shi. Zai kawo wanda ya zaɓa kusa da shi.
6Korah, kai da ƙungiyarka ga abin da za ku yi.7Gobe ku ɗauki turare ku sa wuta a gaban Yahweh. Wanda Yahweh ya zaɓa, zai zama keɓaɓɓe na Yahweh. Fankamarku ta yi yawa, ku 'ya'yan Lebi."
8Musa ya ƙara cewa da Korah, "Ka saurara, kai zuriyar Lebi:9ƙaramin abu ne a wurin ka da Allah na Isra'ila ya keɓe ka daga cikin mutanen Isra'ila, ya kawo ka kusa da shi, domin ka yi aiki cikin alfarwar Yahweh, kuma ka tsaya a gaban jama'a ka yi masu hidima?10Ya kawo ku kusa da dukkan 'ya'uwanka, zuriyar Lebi, tare da kai, kuma kana nema ka zama firist!11Wannan ne yasa kai da ƙungiyarka kuka taru ku yiwa Yahweh tayarwa. Meyasa kake gunaguni a kan Haruna, wanda ya yi biyayya da Yahweh?"
12Sai Musa ya kira Datan da Abiram, 'ya'yan Eliyab, amma suka ce, "Ba za mu hawo ba.13Ƙaramin abu kayi daka fito da mu daga ƙasa mai zubo da madara da zuma, ka kashe mu a cikin jeji? Yanzu kana so ka maida kanka mai mulki a kan mu!14Bugu da ƙari, baka kai mu ƙasar dake zubowa da madara da zuma ba, ko ka bamu gonaki da lambuna su zama gadonmu. Yanzu kana so ka makantar da mu da alƙawuran wofi? Ba zamu zo wurin ka ba."
15Musa ya yi fushi ƙwarai ya ce da Yahweh, "Kada ka karɓi baikonsu. Ban ɗauki ko jaki ɗaya daga wurin su ba, kuma ban ji wa ko ɗaya a cikin su ba.16Sa'an nan Musa yace da Korah, "Gobe kai da mutanenka za ku je gaban Yahweh--kai da su, da Haruna.17Kowannen ku ya ɗauki tasa ya sa turare a ciki. Kuma dole kowanne mutum ya kawo tasarsa gaban Yahweh, tasoshi ɗari biyu da hamsin. Kai da Haruna kuma kowa ya kawo tasarsa,"
18Sai kowanne mutum ya ɗauki tasarsa, yasa wuta a ciki, yasa turare a cikin ta, suka tsaitsaya a ƙofar rumfa ta taruwa tare da Musa da Haruna.19Sai Korah kuma ya tattara dukkan mutanen da suke tayarwa Musa da Haruna a ƙofar rumfa ta taruwa, sai ɗaukakar Yahweh ta bayyana ga dukkan jama'a.
20Sa'an nan Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna:21"Ku ware kanku daga cikin wannan taron domin in hallaka su yanzun nan."22Musa da Haruna suka kwanta da fuskokinsu a ƙasa suka ce, "Ya Allah, Allah na ruhohin dukkan mutane, idan mutum ɗaya ya yi zunubi, ka yi fushi da dukkan mutane?"
23Yahweh ya amsa wa Musa. Ya ce,24"Ka faɗawa taron jama'ar. Ka ce, 'Ku gudu daga rumfar Kora da Datan da Abiram."'
25Sai Musa ya tashi ya je wurin Datan da Abiram; dattawan Isra'ila suka bi shi.26Ya yi magana da taron ya ce, "Sai ku gudu daga rumfunan waɗannan mugayen mutane kada ku taɓa kome nasu."Idan ba haka ba zunubinsu zai cinye ku dukka."27Haka jama'ar dake cikin rumfunan su Korah da Datan da Abiram suka rabu da su. Datan da Abiram suka fito suka tsaya a ƙofar rumfunansu, tare da matansu da 'ya'yansu da ƙananansu.
28Sa'an nan Musa yace, "Ta wurin wannan za ku sani Yahweh ne ya aiko ni in yi dukkan waɗannan ayyuka, gama ba domin kaina nake yin su ba.29Idan mutanen nan suka yi mutuwa irin ta kowanne mutum, kamar yadda abu yakan sami kowanne mutum, ba Yahweh ne ya aiko ni ba.30Amma idan Yahweh ya halitto wani sabon abu, idan ƙasa ta buɗe bakinta ta haɗiye su, tare da dukkan abin da suke da shi, suka tafi cikin lahira da rai, sa'an nan za ku gane waɗannan mutane sun rena Yahweh."
31Da dai Musa ya gama faɗin wannan magana, ƙasa ta buɗe a ƙarƙashin waɗannan mutane.32Ƙasa ta buɗe bakinta ta haɗiye su, da iyalinsu da dukkan jama'ar dake na Korah, tare da dukkan abin da suka mallaka.
33Haka su da dukkan abin da suka mallaka suka tafi lahira da ransu. Ƙasa ta rufe a kan su, suka lalace daga wurin taron jama'a.34Dukkan mutanen Isra'ila dake kewaye da su suka gudu daga biranensu. Suka yi kururuwa, watakila mu ma ƙasa za ta haɗiye mu!"35Sa'an nan wuta ta walƙato daga wurin Yahweh ta haɗiye mutane 250 da suka miƙa turare.
36Yahweh ya ƙara yin magana da Musa ya ce,37Ka yi magana da Eliyeza ɗan Haruna firist bari ya ɗauke tasoshin daga cikin wuta, gama tasoshin keɓaɓɓu ne a gare ni. Sa'an nan ya barbaza garwashin daga nesa.38Ɗauke tasoshin waɗanda suka rasa rayukansu saboda zunubinsu. A bubbuge su su zama marfin bagadinsu. Waɗancan mutanen sun miƙa su a gabana, don haka sun zama keɓaɓɓu a gare ni. Za su zama alamar kasancewata ga mutanen Isra'ila."
39Sai Eliyeza firist ya ɗauki tasoshi na tagulla da mutanen da suka ƙone suka yi amfani da su, aka bubbuga su, suka zama marfin bagadin,40domin su zama abin tunawa ga mutanen Isra'ila, domin ya zama ba wani baƙo wanda ba a cikin kabilar Haruna yake ba da zai zo ya ƙona turure a gaban Yahweh, domin kada su zama kamar Korah da ƙungiyarsa--kamar yadda Yahweh ya bada umarni ta wurin Musa.
41Amma da safiya ta yi sai dukkan taron jama'ar suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna. Suka ce, "Kun kashe mutanen Yahweh."42Sai ya zama, sa'ad da mutanen suka taru gãba da Musa da Haruna, da suka duba wajen rumfa ta taruwa, duba sai gashi girgije ya rufe ta. Darajar Yahweh ta bayyana,43sai Musa da Haruna suka zo gaban rumfar ta taruwa.
44Sa'an nan Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,45"Ka gudu daga gaban wannan taron domin in hallaka su yanzu--yanzu." Sai Musa da Haruna suka kwanta da fuskokinsu a ƙasa.46Musa yace da Haruna, "Ka ɗauki tasa, ka sa wuta a ciki ba a kan bagadin ba, ka sa turare a cikin ta, ka kai ta wurin taron jama'ar, da sauri ka yi kafara saboda su, saboda fushi na zuwa daga wurin Yahweh. Annobar ta fara."
47Sai Haruna ya yi kamar yadda Musa ya ummurce shi. Ya ruga cikin tsakiyar taron jama'ar. Annobar ta fara bazuwa a cikin mutanen, sai ya sa turaren a ciki ya yi kafara saboda mutanen.48Haruna ya tsaya a tsakanin matattu da masu rai; ta haka annobar ta tsaya.
49Waɗanda annobar ta kashe sun kai 14,700, ban da waɗanda suka mutu cikin lamarin Korah.50Haruna ya dawo wurin Musa a ƙofar rumfa ta taruwa, sai annobar ta ƙare.

17

1Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,2"Faɗa wa mutanen Isra'ila, su ɗauki sanduna daga gare su, kowanne ɗaya domin kabilar kakanni, sanduna goma sha biyu. Rubuta sunan kowanne mutum a kan sandarsa.

3Ka rubuta sunan Haruna a kan sandan Lebi. A kan kowacce sanda domin shugaban kabilar kowanne kakanninsa.4Ka ajiye sandunan a cikin alfarwar taro a gaban ka'idodi alƙawari, wurin da nakan sadu da kai.5Zai zamana sandan mutumin dana zaɓa za ta yi toho. Zan sa ƙorafe-ƙorafe daga mutanen Isra'ila ya tsaya, waɗanda suke magana a kanka."
6Sai Musa ya yi magana da mutanen Isra'ila. Dukkan shugabannin kabilu suka ba shi sandunan, sanda ɗaya daga kowanne shugaba, da aka zaɓa daga dukkan kabilun kakanin, sanduna goma sha biyu dukka. Sandan Haruna na cikinsu.7Sai Musa ya ajiye sandunan a gaban Yahweh cikin alfarwar ka'idodin alƙawari.
8Kashegari Musa ya tafi cikin alfarwar ka'dodin alƙawari, sai ga shi, sandar Haruna ta kabilar Lebiyawa ta yi toho. Ta tuko tayi toho ta bada 'ya'yan almon nunannu!9Musa kuwa ya fito da dukkan sandunan a gaban Yahweh zuwa ga dukkan mutanen Isra'ila, sai kowanne mutum ya ɗauki sandansa.
10Yahweh yace da Musa, "Sa sandan Haruna a gaban ka'idodin alƙawari. Ka ajiye ta alama ce a kan mutane waɗanda ke tawaye saboda ka kawo ƙarshen gunaguni a kaina, ko kuwa za su mutu.11Musa kuwa ya yi kamar yadda Yahweh ya umarce shi.
12Mutanen Isra'ila suka yi magana da Musa suka ce, "Za mu mutu a nan. Dukkan mu zamu lalace! Duk wanda ya zo nan, kowa ya kusanci alfarwar Yahweh, zai mutu.13Mu dukka za mu lalace?"

18

1Yahweh yace da Haruna, "Kai, da 'ya'yanka, da kabilar kakanninka za ku ɗauki hakkin dukkan zunubai da za ayi game da alfarwar sujada. Amma kai da 'ya'yanka ne kaɗai za ku ɗauki hakkin dukkan zunuban da ya shafi kowanne firist.2Kuma sauran 'yan'uwan kabilar Lebi, kakanninka, ka kawo su tare da kai saboda su kasance tare da kai don su taimake ka da 'ya'yanka aiki a gaban alfarwa ta ka'idodin alƙawari.

3Su yi maka dukkan ayyukan alfarwa. Amma ba za su zo su kusanci kowanne abu dake a wuri mai tsarki, ko wani abu da ya shafi bagaɗi ba, ko su da kai dukka ku mutu.4Su haɗu da kai, don su lura da alfarwar taruwa, domin dukkan aikace-aikace na alfarwar. Kada wani baƙo ya zo kusa da ku.5Ku ɗauki nauyin ayyukan wuri mai tsarki da kuma bagaɗi saboda kada fushina ya zo a kan mutanen Isra'ila kuma.
6Duba, ni da kaina na zaɓi 'yan 'uwan Lebiyawa daga cikin zuriyar Isra'ila. Kyauta suke a gare ku, an bani su don su yi aikin lura da alfarwar taro.7Amma da kai da 'ya'yanka za ku yi aikin firist da duk abin da ya shafi bagaɗi da dukkan aiki na bayan labule. Kune da kanku za ku yi waɗannan aikace-aikace. Ina baku aikin firist a matsayin kyauta. Duk wani baƙo wanda ya matso zai mutu."
8Sai Yahweh ya cewa Haruna, "Duba, na baka aikin, kula da baikon ɗagawa a gare ni, da dukkan baye -baye masu tsarki da mutanen Isra'ila suka bani. Na bada dukkan baye-bayen a gare ka da 'ya'yanka maza har abada.9Wannan zai zama rabonka daga abubuwa masu tsarkin gaske da za a ajiye daga wuta. Daga kowanne baiko nasu--kowacce bayarwar hatsi, da kowacce bayarwa don zunubi da bayarwar laifi--za su ajiye su gare ka da 'ya'yanka.
10Waɗannan baye-baye suna da tsarki sosai, kowanne namiji ya ci shi, domin suna da tsarki a gare ka.11Waɗannan su ne baye-bayen da za su zama naka: sun zama da tsarki daga dukkan bayarwar ɗagawa daga mutanen Isra'ila. Na bada su a gare ka da 'ya'yanka maza da 'ya'yanka mata, a matsayin naka har abada. Duk wanda yake da tsarki a iyalinka zai iya cin kowanne daga waɗannan baye-bayen.
12Dukkan mai mai kyau, dukkan sabon ruwan inabi da hatsi da nunar fari masu kyau da mutane suka bada gare ni--dukkan waɗannan abubuwa na bada su a gare ka.13Nunan fari na dukkan amfanin gonarsu, wanda suke kawo wa gare ni, za su zama naka. Duk wanda yake da tsarki a iyalinka zai iya cin waɗannan abubuwa.
14Iyakar abin da aka keɓe a Isra'ila zai zama naka.15Dukkan abin da aka haifa, dukkan nunar fari wadda jama'a suka bayar ga Yahweh, mutum ko dabba, zai zama naka. Duk da haka, mutane dole su fanshi kowanne haihuwar fari na mutum, su kuma fanshi ɗan fari na dabba namiji da ba shi da tsarki.16Waɗanda mutane za su fansa dole sai sun kai wata ɗaya da haihuwa. Sa'an nan mutane zasu iya fansar su, gama kuɗinsu shekel biyar ne bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi na shekel, wanda ya ke dai dai da awo ashirin na gerah.
17Amma haihuwar fari ta saniya, ko ta tunkiya ko ta akuya--ba za ka fanshi waɗannan dabbobi ba; keɓaɓɓu ne a gare ni. Sai ka yayyafa jininsu a kan bagaɗi, ka ƙona kitsensu a matsayin baiko na ƙonawa, abin ƙanshi mai gamsarwa ga Yahweh.18Namansu zai zama naka. Kamar ƙirjin da aka ɗaga da cinyar dama, namansu zai zama naka.
19Dukkan baye--baye masu tsarki da mutanen Isra'ila suka bayar ga Yahweh, na bada su gare ka da 'ya'yanka maza da 'ya'yanka mata tare da kai, yadda za ku ci gaba da samun rabo ke nan. Wannan alƙawarin gishiri mara ƙarewa ne, alƙawarin yana nan har abada, a gaban Yahweh domin ka da zuriyarka.20Yahweh yace da Haruna, "Ba za ka sami gãdo a cikin ƙasar mutane ba, ko ka sami rabon kaya a cikin mutane. Ni ne rabonka da gãdonka a cikin mutanen Isra'ila.
21Duba, ga zuriyar Lebi, na ba su dukkan zakar Isra'ila a matsayin gãdonsu saboda hidimar da suke yi a cikin rumfa ta taruwa.22Daga yanzu mutanen Isra'ila za su zo kusa da rumfa ta taruwa, ko su ɗauki alhakin wannan zunubi, su mutu.
23Lebiyawa ne za su yi aikin da ya shafi rumfa ta taruwa. Za su ɗauki alhakin kowane zunubi dangane da shi. Wannan zai zama doka ta din-din-din a dukkan zamanan mutanenka. A cikin mutanen Isra'ila ba za su sami gãdo ba.24Gama zakkar mutanen Isra'ila, wadda za su miƙa a matsayin gudummuwarsu gare ni-- waɗannan ne na bayar ga Lebiyawa a matsayin gãdonsu. Wannan shi yasa na ce da su, 'Baza su sami gãdo ba a cikin mutanen Isra'ila.'"
25Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,26"Dole ka yi magana da Lebiyawa ka ce da su, 'Sa'ad da suka karɓi kashi goma daga mutanen Isra'ila wanda na basu gãdo, sai ku bada gudummuwa daga cikin ta ga Yahweh, kashi goma na zakkar.27dole ku ɗauke ta kamar kashi goma na hatsinsu ne daga masussuka ko kuma kamar amfani daga wurin matsewar inabinku.
28Haka kuma dole ku miƙa gudummuwa ga Yahweh daga dukkan zakkar da kuke karɓa daga wurin mutanen Isra'ila. Daga ciki dole za ku bayar da gudummuwa ga Haruna firist.29Daga dukkan kyaututtukan da kuke karɓa, dole ku bada kowacce gudummuwa ga Yahweh. Dole ku yi wannan daga dukkan abu mafi kyau mafi tsarki da aka ba ku.'
30Saboda haka dole ka ce da su, 'Sa'ad da kuka bada mafi kyau daga ciki, sai ya zama na Lebiyawa kamar amfanin da ya fito daga masussuka da wurin matsewar inabi.31Za ku iya cin sauran kyaututtukanku a kowanne wuri, ku da iyalinku, gama ladanku ke nan saboda aikin da kuke yi a rumfa ta taruwa.32Ba kuwa za ta zama maku sanadin laifi ba ta wurin cinta da shanta, in dai har kuka bada ga Yahweh mafi kyau daga cikin abin da ku ka karɓa. Amma ba za ku ɓata tsarkakakken baye-bayen na mutanen Isra'ila ba, ko ku mutu.'"

19

1Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna.2Ya ce, "Wannan ita ce ka'ida, da doka wadda nake umartar ku: Ka faɗawa mutanen Isra'ila dole su kawo maka jar karsana marar lahani ko wadda ba ta da wani aibi, wadda ba a taɓa aza mata karkiya ba.

3Sai ka ba Eliyeza firist karsanar. Dole ya kawo ta a wajen zango, kuma dole wani zai yanka ta a gabansa.4Dole Eliyeza, firist, ya ɗibi jininta da yatsansa ya yayyafa sau bakwai a gaban rumfa ta taruwa.5Dole sai wani firist ya ƙone karsanar a idonsa. Dole zai ƙone fatarta da namanta da jinin tare da ƙashinta.6Dole firist ya ɗauki itacen al'ul da abin tsaftacewa da mulufi ya jefa su dukka a cikin tsakiyar wutar da take ƙone karsanar.
7Sa'an nan dole ya wanke tufafinsa ya yi wanka a cikin ruwa. Sa'an nan zai zo ya shiga zangon, a wurin zai zama da ƙazamta har zuwa maraice.8Shi kuwa wanda ya ƙone karsanar zai wanke tufafinsa a cikin ruwa, ya yi wanka a cikin ruwa. Zai zama da ƙazamta har zuwa maraice.
9Mutumin dake da tsarki shi zai tara tokar karsanar, ya sa ta wajen sansani a wuri mai tsabta. Za a adana tokar saboda jama'a mutanen Isra'ila. Za su riƙa zubawa a ruwa don tsarkakewar zunubi, tun da yake tokar daga bayarwar zunubi ce.10Shi kuwa wanda ya tara tokar karsanar sai ya wanke tufafinsa. Zai zama ƙazantacce har maraice. Wannan doka ce ta har abada domin mutanen Isra'ila da baƙin dake zama tare da su."
11Duk wanda ya taɓa jikin gawar mutum zai ƙazantu har kwana bakwai.12Wannan mutum zai tsarkake kansa a rana ta uku da rana ta bakwai. Sa'an nan zai tsarkaka. Amma in a rana ta uku bai tsarkake kansa ba, ba zai zama da tsarki ba a rana ta bakwai.13Duk wanda ya taɓa jikin gawar mutum wanda ya mutu, bai tsarkake kansa ba--wannan mutum zai kazantar da alfarwar Yahweh. Wannan mutum za a yanke shi daga cikin Isra'ila domin ba a yayyafa masa ruwan tsarkakewa ba. Zai kasance ƙazantacce; ƙazancewarsa za ta kasance a kansa.
14Wannan ita ce doka a kan wanda ya rasu a cikin alfarwa. Duk wanda ya shiga alfarwar da wanda ke cikin alfarwar za su ƙazantu har kwana bakwai.15Kowanne buɗaɗɗen akwati da ba a rufe ba, zai ƙazantu.16Hakanan ma duk wanda ke wajen alfarwar ya taɓa jikin mamacin wanda aka kashe da takobi, ko kowacce gawa, ko ƙashin mutum, ko kabari--wannan mutumin zai ƙazantu har kwana bakwai.
17A yi wannan domin mutumin da ya ƙazantu: A ɗibi toka daga cikin bayarwar ƙonawa a haɗa su a cikin tulu tare da sabon ruwa.18Duk wanda ke da tsarki zai ɗauki abin tsaftacewar ya tsoma a ruwan, ya yayyafa wa alfarwar da dukkan kayayyakin dake cikin alfarwar, da mutanen dake a wurin, da wanda ya taɓa ƙashin ko wanda aka kashe ko wanda ya mutu, ko kabari.19A kan rana ta uku da ta bakwai kuma wanda yake da tsarki zai yayyafa wa mutum marar tsarkin ruwa. A rana ta bakwai mutum mara tsarki zai tsarkake kansa. Zai wanke tufafinsa, ya yi wanka a ruwa. Da maraice kuwa zai tsarkaka.
20Amma duk wanda ya kasance da rashin tsarki, wanda ya ƙi ya tsarkake kansa--wannan mutum za a datse shi daga jama'a, domin ya ƙazantar da wuri mai tsarki na Yahweh. Kuma ba a yayyafa masa ruwan da ake yayyafa wa marasa tsarki ba.21Wannan zai zama doka a gare su a kan abubuwa kamar haka. Wanda ya yayyafa ruwan don tsarkakewa, zai wanke tufafinsa, wanda kuma ya taɓa ruwan don tsarkakewa zai zama marar tasrki har maraice.22Duk abin da mutumin da ba shi da tsarki ya taɓa, zai ƙazantu. Duk wanda kuma ya taɓa abu marar tsarki, zai ƙazantu har maraice."

20

1Sai mutanen Isra'ila da dukkan taron jama'a suka zo jejin Zin a wata na fari, suka sauka a Kadesh. A nan ne Miriyam ta rasu, a nan kuma aka bizne ta.

2Babu ruwa domin jama'a, sai suka taru suka tayar wa Musa da Haruna.3Mutane kuwa suka yi wa Musa gunaguni. Suka ce, "Zai fi kyau idan da mun mutu yadda 'yan'uwanmu Israilawa suka mutu a gaban Yahweh!
4Donme ka fito da taron jama'ar Yahweh a cikin wannan jeji mu mutu a nan, mu da dabobbinmu?5Donme kuma ka sa muka fito daga Masar ka kawo mu a wannan mugun wuri? A nan babu hatsi, ko ɓaure ko inabi ko rumman ko ruwan da za a sha."
6Sai Musa da Haruna suka tafi daga gaban taron. Suka shiga alfarwar taro, suka faɗi rub da ciki. A wurin ɗaukakar Yahweh ta bayyana a gare su.
7Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,8"ɗauki sandarka ka tara jama'a, kai da Haruna ɗan'uwanka. Yi magana da dutse a gaban idanunsu, ya bada ruwan dake cikinsa. Za ka sa ruwa ya ɓuɓɓugo daga dutsen domin su, ka bada ruwan ga jama'ar da garkunansu su sha."9Musa ya ɗauki sandar daga gaban Yahweh, kamar yadda Yahweh ya umarce shi ya yi.
10Sai Musa da Haruna suka tara dukkan jama'ar, a gaban dutsen. Musa yace da su, "Ku saurara yanzu, ku 'yan tawaye. Za mu fito da ruwa daga cikin dutsen nan domin ku?11Musa kuwa ya ɗaga hannu, ya bugi dutsen sau biyu da sandarsa, sai ruwa mai yawa ya yi ta kwararowa. Jama'a kuwa suka sha, dabobbi ma suka sha.
12Sai Yahweh yace da Musa da Haruna, "Tun da yake baku gaskata ni ba, baku kuwa ɗaukaka ni akan ni mai tsarki bane a idon mutanen Isra'ila, to, baza ku kai wannan taron a cikin ƙasar dana ba su ba."13Wannan wuri ne aka kira shi ruwan Meriba domin mutanen Isra'ila suka yi wa Yahweh gunaguni a wurin, inda shi kuma ya nuna masu shi kansa mai tsarki ne.
14Musa ya aika da manzanni daga Kadesh zuwa ga sarkin Idom: Yan'uwanka Israila sun faɗi wannan: "Ka san dukkan wahalun da suka same mu.15Ka san yadda kakanninmu suka tafi can Masar, suka zauna a Masar da daɗewa. Masarawa suka wahalshe mu, mu da kakanninmu.16Sa'ad da muka yi kira ga Yahweh, ya ji muryarmu, ya aiko da mala'ikansa, ya fishe mu daga Masar. Duba, muna nan a Kadesh, birni dake kan iyakar ƙasarka.
17Ina roƙonka ka yardar mana mu ratsa ƙasarka. Za mu bi ta cikinta mu wuce gona, ko gonar inabi, ba za mu sha ruwa daga cikin rijiyarka ba. Za mu bi ta gwadaben sarki. Ba za mu kauce dama ko hagu ba, har mu wuce ƙasarka."
18Amma sarkin Idom ya amsa masa, "Ba za ku ratsa ta nan ba. Idan kuwa kuka yi, zan fita tare da takobi, za mu ci ku da yaƙi."19Sai mutanen Isra'ila suka ce da shi, "Za mu bi gwadabe ne kawai. Idan kuwa mu da dabobbinmu mun sha ruwanku, za mu biya. Mu dai, a yardar mana mu wuce a ƙafafunmu, ba tare da yin wani abu ba kuma."
20Amma sarkin Idom ya sake amsa masu da cewa, "Ba mu yarda ba. "Sai sarkin Idom ya fito gãba da Isra'ila da runduna mai yawa.21Sarkin Idom ya ƙi ya bar Isra'ila su ratsa a kan iyakarsu. Domin wannan, Isra'ila suka juya daga ƙasar Idom.
22Sai mutane suka kama tafiya daga Kadesh. Mutanen Isra'ila da dukkan jama'a suka zo Tsaunin Hor.23Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna a Tsaunin Hor, a iyakar Idom. Ya ce,24"Dole ne Haruna ya tarar da mutanensa, don ba zai shiga ƙasar dana ba mutanen Isra'ila ba. Wannan domin ku biyun kun yi mani tawaye a kan maganata a kan ruwan Meriba.
25Ka ɗauki Haruna da Eliyeza ɗansa, ka zo da su bisa Tsaunin Hor.26Ka ɗauki rigar firistanci ta Haruna, ka sawa ɗansa Eliyeza. Haruna zai mutu, za a tara shi ga mutanensa a can.
27Musa kuwa ya yi yadda Yahweh ya umarta. Suka hau bisa Tsaunin Hor a idon dukkan jama'a.28Musa ya ɗauki rigar Haruna ta firist ya sawa Eliyeza ɗansa. Haruna kuwa ya rasu a bisa tsaunin. Sa'an nan Musa da Eliyeza suka sauko ƙasa.29Sa'ad da dukkan jama'a suka ga Haruna ya rasu, sai dukkan jama'a suka yi kuka da makoki domin Haruna har kwana talatin.

21

1Sa'ad da sarkin Kan'ana na Arad wanda ke zaune a Negeb, ya ji Isra'ila na zuwa ta hanyar Atarim, sai ya yi faɗa da Isra'ila ya ɗauki waɗansu a matsayin kamammun yaƙi.2Isra'ila suka yi wa'adi ga Yahweh cewa, "Idan zaka ba mu nasara a kan waɗannan mutane, sai mun hallakar da su da biranensu."3Yahweh ya saurari muryar Isra'ila, ya kuma ba su nasara a kan Kan'aniyawa. Suka hallaka su da biranensu. Shiyasa ake kiran wurin Horma.

4Suka yi tafiya daga Tsaunin Hor ta hanya zuwa Tekun Iwa a kewayen ƙasar Idom. Sai mutane suka kusan fitar da zuciya a hanya.5Mutane suka yi gunaguni da Allah da Musa: "Meyasa kuka fitar da mu daga Masar don mu mutu a cikin jeji? Babu abinci, babu ruwa kuma bamu son irin wannan abinci mai gundura."
6Sai Yahweh ya aika da macizai masu zafin dafi a cikin mutane. Suka kuwa sassari mutane, har mutane da yawa suka mutu.7Mutane suka zo wurin Musa suka ce, "Mun yi zunubi gama mun yi wa Yahweh gunaguni, mun kuma yi maka. Ka roƙi Yahweh domin ya ɗauke macizan daga gare mu." Musa kuwa ya yi addu'a saboda mutanen.
8Yahweh ya cewa Musa, "Ka yi maciji ka sa shi a sanda, zai zamana duk wanda macijin ya sare shi idan ya dubi macijin tagulla zai tsira."9Musa kuwa ya yi maciji na tagulla ya sarƙafa shi a bisa dirka. Idan kuwa maciji ya sari mutum, in dai ya dubi macijin tagulla sai ya tsira.
10Sai mutanen Isra'ila suka kama hanya suka yi zango a Obot.11Sun yi tafiya daga Obot, suka yi zango a Iye Abarim a cikin jeji suna fuskantar Mowab wajen gabas.
12Daga can suka tashi suka sauka a Kwarin Zered.13Daga can kuma suka tashi suka sauka hayin Kogin Arnon, wanda ke cikin jeji wanda ya nausa zuwa iyakar Amoriyawa. Kogin Arnon shi ne kan iyakar Mowab, tsakanin Mowab da Amoriyawa.
14Saboda haka aka faɗa a littafin Yaƙoƙi na Yahweh,"--"Waheb ta cikin yankin Sufa da kwaruruka na kogin Arnon,15da gangaren kwaruruka wanda ya nausa zuwa garin Ar, ya kuma dangana da kan iyakar Mowab."
16Daga can suka ci gaba da tafiya zuwa Biyer, rijiya wadda Yahweh yace da Musa, "Ka tattara mutane wuri ɗaya domi na, zan kuwa ba su ruwa."
17Sai Isra'ila suka raira waka: "Ƙorama ki, ɓuɓɓugo yadda ya kamata! Rera waƙa a game da ita,18a game da rijiyar da shugabanninmu suka gina, rijiyar da mutanenmu masu daraja suka gina, da sandan sarauta da kuma sandunansu." Daga cikin jeji suka tafi har zuwa Mattana.
19Daga Mattana suka tafi Nahaliyel, daga can kuma suka tafi Bamot,20daga Bamot kuma suka tafi kwarin dake a ƙasar Mowab wajen ƙwanƙolin Dutsen Fisga wanda ke duban hamada.
21Sai Israila suka aiki manzanni zuwa wurin Sihon sarkin Amoriyawa suna cewa,22"Ka yarda mana mu ratsa ta ƙasarka. Ba za mu ratsa ta cikin gonaki ko cikin gonakin inabi ba, ba kuwa za mu sha ruwan rijiyarka ba, gwadaben sarki za mu bi sosai har mu fita daga iyakarka."23Amma sarkin Sihon bai yarda wa Isra'ila su ratsa ta kan iyakarsa ba. Maimakon haka, sai ya tattara dukkan sojojinsa don su kaiwa Isra'ila hari a cikin jeji. Ya zo Yahaz, wurin da ya yi yaƙi da Isra'ila.
24Sojojin Isra'ila suka faɗa su da karkashewa da kaifin takobi suka karɓe ƙasar daga Arnon zuwa kogin Yabbok, har ma zuwa ƙasar mutanen Ammonawa. To sai aka ƙayata iyakar mutanen Amonawa.25Isra'ila kuwa su ka ci dukkan biranen Amoriyawa da dukkan waɗanda su ke zama da su, ya haɗa da Heshbon da dukkan kauyukanta.26Heshbon ita ce birnin Sihon sarkin Amoriyawa wanda ya yi yaƙi da sarkin Mowab a dã. Sihon ya ƙwace dukkan ƙasarsa daga yakinsa zuwa Kogin Arnon.
27Don haka shi ya sa waɗanda suka yi magana suke misali cewa, "Ku zo Heshbon. Bari birnin Sihon a sake gina shi, ya kuma tabbata.28Wuta daga Heshbon, hasken wuta daga birnin Sihon ya lanƙwame Ar ta Mowab, da mazaunan tuddan wuraren Arnon.
29Kaitonki, Mowab! Kin lalace, mutanen Kemosh. Ya sa 'ya'yansa maza na gudu, an kama 'ya'yansa mata sun zama 'yan kurkukun Sihon sarkin Amoriyawa.30Amma yanzu an ci nasarar Sihon. Heshbon ta lalata dukkan hanya zuwa Dibon. Mun ci nasararsu a dukkan hanya zuwa Nofa, wadda ta kai kusa da Medeba."
31Sai Isra'ila suka fara zama a ƙasar Amoriyawa.32Musa ya aika mutane su leko asirin Yazar. Suka tafi suka ci ƙauyukanta, suka kori Amoriyawa daga cikinta waɗanda ke a can.
33Sa'an nan suka juya suka tafi su haura ta hanyar Bashan. Og sarkin Bashan ya fita gãba da su, shi da dukkan sojojinsa su yi yaƙi da su a Edirai.34Sai Yahweh yace da Musa, "Kada ka ji tsoronsa, gama na baka nasara a kansa, da dukkan sojojinsa da ƙasarsa. Ka yi masa yadda ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, waɗanda suka zauna a Heshbon."35Haka fa suka kashe shi da 'ya'yansa maza da dukkan sojojinsa, har babu wani a mutanensa da ya rage a raye. Sai suka mallaki ƙasarsa.

22

1Mutanen Isra'ila suka kama tafiya har suka yi zango a filayen Mowab kusa da Yeriko, a ɗaya gefen a Kogin Yodan daga birnin.

2Balak ɗan Ziffor ya ga dukkan abin da Isra'ila suka yi wa Amoriyawa.3Mowab sun firgita kwarai saboda mutanen, domin suna da yawa. Mowab sun ji tsoron mutanen Isra'ila kwarai.4Sarkin Mowab ya cewa dattawan Midiyanawa, "Wannan taro zai cinye dukkan abin da ke kewaye da mu, kamar yadda sã ya kan cinye ciyawar saura" Yanzu Balak ɗan Zippor wanda ke sarkin Mowab a wancan lokacin.
5Ya aika da manzanni zuwa wurin Balaam dan Beyor, a Fetor wadda ke kusa da Kogin Yuferatis, a cikin ƙasar al'ummar mutanensa. Ya kira shi ya ce, "Duba, mutane sun zo nan daga Masar. Sun rufe fuskar duniya, ga shi suna zaune kusa da ni.6Ina roƙonka ka zo, ka la'anta mutanen nan domi na, gama suna da ƙarfi sosai fiye da ni. Ko ya yiwu in ci su, in kore su daga ƙasar. Na sani duk wanda ka sawa albarka zai albarkatu, wanda kuwa ka la'anta zai zama la'ananne."
7Sai dattawan Mowab da dattawan Midiyanawa suka tafi, suka ɗauki ladar duba tsibbu. Suka tafi wurin Balaam suka faɗa masa saƙon Balak.8Balaam yace da su, "Ku kwana a nan. Ni kuwa zan baku abin da Yahweh ya faɗa mani." Shugabannin Mowab suka tsaya suka kwana tare da Balaam.
9Allah kuwa ya zo wurin Balaam yace,10"Su wane ne mutanen dake tare da kai? Balaam ya amsa wa Allah, Balak ɗan Zippor, sarkin Mowab, ya aiko su gare ni. Ya ce,11'Duba, mutanen da suka zo daga Masar suka cika fuskar ƙasata. Yanzu zo ka la'anta su domi na. Watakila zan iya faɗa da su, har in kore su.'"
12Allah ya amsa wa Balaam, "Ba za ka tafi tare da mutanen ba, ba kuwa za ka la'anta mutanen Isra'ila ba domin masu albarka ne."13Balaam ya tashi da safe ya yi magana da shugabannin Balak, "Ku koma ƙasarku gama Yahweh ya hana ni in tafi tare da ku."14Shugabannin Mowab suka koma wurin Balak. Suka ce, "Balaam ya ƙi ya taho tare da mu."
15Sai Balak ya sake aiken shugabannin, kuma masu yawa masu daraja fiye dana fari.16Suka zo wurin Balaam suka ce da shi, "Balak ɗan Zippor ya faɗi wannan, 'Idan ka yarda kada ka bar wani ya hana ka zuwa gare ni,17gama zan biya ka sosai, za a ɗaukaka ka ƙwarai, kome kuwa ka faɗa mani in yi, zan yi. Ka zo ka la'anta wannan jama'a domi na.'"
18Balaam ya amsa, yacewa mutanen Balak, "Ko da a ce Balak zai bani fadarsa cike da azurfa da zinariya, ba zan yi wani abu ko kaɗan saɓanin umarnin Yahweh, Allahna ba, ba zan ƙara wani abu ko in rage ba sai dai abin da ya faɗa mani.19Amma yanzu, ina rokonku ku kwana a nan, har in san abin da Yahweh zai sake faɗa mani."20Allah ya zo wurin Balaam da dare, ya ce masa, "Tun da mutanen nan sun zo kiran ka ne, sai ka tashi, ka tafi tare da su, amma abin dana umarce ka kaɗai za ka yi."
21Balaam ya tashi da safe, ya yi wa jakarsa shimfiɗa, ya tafi tare da shugabannin Mowab.22Amma saboda ya tafi, fushin Allah ya yi zafi. Mala'ikan Yahweh ya tsaya a hanya kamar wani ya tarye Balaam, wanda ya ke bisa jakarsa. Barorin Balaam biyu na tare da shi.23Jakar kuwa ta ga mala'ikan Yahweh na tsaye kan hanya da takobi zare a hannunsa. Sai jakar ta kauce daga hanya ta shiga saura. Balaam ya bugi jakar don ta juyo a kan hanyar.
24Sai mala'ikan Yahweh ya tsaya a inda hanyar ta yi matsatsi a tsakanin bangayen gonakin inabi, bango a gefen damarsa da bango gefen hagunsa.25Jakar ta ga mala'ikan Yahweh kuma. Sai ta matsa a jikin bango, ta goge ƙafar Balaam ga bangon. Balaam ya sake bugunta.
26Mala'ikan Yahweh kuma ya sha kanta ya tsaya a ƙuntataccen wuri inda ba wurin juyawa zuwa dama ko hagu.27Jakar ta ga mala'ikan Yahweh, sai ta kwanta a ƙafafun Balaam. Sai Balaam ya husata ya bugi jakar da sandarsa.
28Sa'an nan Yahweh ya buɗe bakin jakar har ta yi magana. Ta ce da Balaam, "Me nayi maka da ka buge ni har sau uku?"29Balaam ya amsa wa jakar, "Domin kin shashantar da ni. Dama a ce ina da takobi a hannuna, da na kashe ki."30Jakar ta ce wa Balaam, "Ba ni ce jakarka ba wadda kake ta hawa dukkan lokacin rayuwarka har zuwa wannan ranar ba? Na taɓa yi maka haka? Balaam ya ce, "A'a."
31Sa'an nan Yahweh ya buɗe idanun Balaam, ya ga mala'ikan Yahweh na tsaye a hanya da takobi zare a hanunsa. Balaam ya sunkuyar da kansa, ya faɗi rubda ciki.32Mala'ikan Yahweh yace da shi, "Meyasa ka bugi jakarka har sau uku? Duba, na fito ne kamar wani abokin gãba don ayyukanka a wuri na mugunta ne.33Jakar ta gan ni, ta kauce mani har sau uku. Da a ce bata kauce mani ba, lallai da na kashe ka, in bar ta da rai."
34Balaam ya cewa mala'ikan Yahweh, "Na yi zunubi. Ban san ka tsaya gãba da ni a hanya ba. To yanzu, idan ka ga mugun abu ne, sai in koma."35Amma mala'ikan Yahweh ya cewa Balaam, "Tafi tare da mutanen. Amma abin da na faɗa maka shi kaɗai zaka faɗa." Sai Balaam ya tafi tare da shugabannin Balak.
36Sa'ad da Balak ya ji Balaam ya zo, ya fita ya tarye shi a birnin Mowab a Arnon, wadda ke kan iyaka.37Balak yace wa Balaam, "Ashe, ban aika a kirawo ka ba? Meyasa baka zo wurina ba? Ko ban isa in ɗaukaka ka ba ne?"
38Sai Balaam ya amsa wa Balak yace, "Ga shi, na zo gare ka. Ina da wani ikon yin wata magana ne? Zan iya faɗin maganar da Allah ya sa a bakina ne kawai."39Balaam ya tafi tare da Balak, suka je Kiriyat Huzot.40Sai Balak ya yi hadaya da sã da tunkiya ya aika wa Balaam da shugabannin da ke tare da shi.
41Washegari, Balak ya ɗauki Balaam ya kai shi kan tudu wurin Ba'al. Daga wurin Balaam ya ga wasu daga mutanen Isra'ilawa a zangonsu.

23

1Balaam ya cewa Balak, "Ka gina mani bagadai guda bakwai a nan, ka shirya bijimai bakwai da raguna bakwai."2Balak ya yi yadda Balaam ya bukace shi ya yi. Sai Balak da Balaam suka miƙa bijimi da rago a kan dukkan bagadan.3Balaam yace da Balak, "Tsaya kusa da bayarwar ƙonawa, ni kuwa zan tafi can. Watakila Yahweh zai sadu da ni. Duk abin da ya bayyana mani zan faɗa maka." Ya kuwa tafi wani fako a kan tudu wurin da ba itatuwa.

4A lokacin da yake a kan tudu, Allah ya sadu da shi, Balaam yace da shi, "Na riga na shirya bagadai bakwai, na kuwa miƙa bijimai guda da rago guda a kan kowanne bagadi."5Yahweh ya sa magana a bakin Balaam yace, "Koma wurin Balak, ka yi magana da shi."6Sai ya koma wurin Balak, wanda ke tsaye kusa da hadayar ƙonawarsa, da dukkan shugabannin Mowab tare da shi.
7Balaam kuwa ya fara maganarsa ta annabci ya ce, "Balak ya kawo ni daga Aram, sarkin Mowab daga duwatsun gabas. 'Zo, la'anta Yakubu domi na,' ya ce, 'Zo, ka tsine wa Isra'ila.'8Ƙaƙa zan iya la'anta waɗanda Allah bai la'antar ba? Ƙaƙa zan iya tsine wa waɗanda Yahweh bai tsine wa ba?
9Gama daga kan duwatsu na gan shi, daga bisa kan tuddai na hange shi. Duba, akwai mutane waɗanda ke zama su kaɗai, ba su ɗauki kansu a bakin kome ba a cikin jama'a.
10Wa zai iya ƙidaya ƙurar Yakubu ko ya iya yin lissafin ɗaya bisa hudu na Isra'ila? Ka sa in mutu mutuwar adalin mutum, ka sa in mutu cikin salama kamar irin mutuwarsa."
11Balak ya cewa Balaam, "Me kenan ka yi mani? Na kawo ka ka la'anta abokan gãbana amma ga shi sai albarka kake sa masu."12Balaam ya amsa ya ce, "Ba zan yi hankali da abin da zan ce abin da Yahweh ya sa a bakina ba?
13Balak yace da shi, "Idan ka yarda zo tare da ni zuwa wani wuri inda za ka gan su. Za ka gansu a kurkusa, ba dukkansu ba. A can sai ka la'anta su domi na."14Ya kuwa ɗauki Balaam a cikin filin Zofim, a bisa Dutsen Fisga, ya gina bagadai bakwai. Ya miƙa bijimi da rago a kan kowanne bagadi.15Sai Balaam yace da Balak, "Tsaya nan kusa da hadayarka ta ƙonawa, ni kuwa in tafi in sadu da Yahweh a can.
16Yahweh kuwa ya sadu da Balaam, ya sa masa magana a bakinsa. Ya ce, "Koma wurin Balak ka faɗa masa maganata."17Balaam ya koma wurinsa, ga shi a tsaye kusa da bayarwarsa ta ƙonawa, shugabannin Mowab na tare da shi. Balak yace da shi, "Me Yahweh ya ce?"18Balaam ya fara annabcinsa. Ya ce, "Tashi, Balak, ka ji. Ka saurare ni, ya ɗan Ziffor.
19Allah ba mutum ba ne, da zai yi ƙarya, ko kuwa mutum ne, da zai canza tunaninsa. Ya yi wani alƙawarin da bai cika shi ba? Ko ya ce zai yi wani abu kuma bai yi shi ba?20Duba, an umarce ni in sa albarka. Allah ya bada albarka, ba zan iya janye ta ba.
21Ya ga babu mugunta a Yakubu ko wahala a Isra'ila. Yahweh Allahnsu na tare da su, suna sowa domin sarkinsu na cikinsu.22Allah ne ya fishe su daga Masar da ƙarfi kamar kutunkun ɓauna.
23Babu wata maitar da zata cuci Yakubu, ba sihirin da zai cuci Isra'ila. Maimakon haka dole ace da, Yakubu da Isra'ila, 'Duba abin da Allah ya yi!'
24Duba, mutane sun tashi kamar ƙaƙƙarfan zaki, yadda zai fito ya hallakar. Ba ya kwantawa har sai ya cinye ganimarsa, ya lashe jinin abin da ya kashe."
25Sai Balak ya cewa Balaam, "Kada ka la'anta su ko ka albarka ce su dukka."26Amma Balaam ya amsa ya ce da Balak, "Ban faɗa maka ba, zan faɗi dukkan abin da Yahweh ya ce da ni shi zan ce?"27Balak ya amsa wa Balaam, "Ka zo yanzu, zan ɗauke ka zuwa wani wuri. Watakila Allah zai yarda ka la'anta su a can domi na."
28Balak kuwa ya kai Balaam a ƙwanƙolin Dutsen Feyor, wanda ke fuskantar hamada.29Balaam yace da Balak, "Gina mani bagadai bakwai a nan ka shirya bijimai bakwai da raguna bakwai."30Balak ya yi yadda Balaam ya ce ya yi; ya miƙa hadayar bijimi da rago a kan kowanne bagadi.

24

1Da Balaam ya ga Yahweh ya ji daɗin da aka sawa Isra'ila albarka, bai tafi ba, kamar waɗancan lokutan, don ya yi aiki da tsafi. Maimakon haka, sai ya duba wajen jeji.

2Ya tada idanunsa, ya ga Isra'ila sun yi zango, kowa a cikin kabilarsu, Ruhun Allah ya sauko masa.3Ya karɓi wannan annabci, ya ce, "Balaam ɗan Beyor ne ke magana, mutumin da idanuwansa a buɗe suke.
4Ya faɗa, an ji maganar Allah. Ya ga wahayi daga wurin Maɗaukaki. A gaban wanda ke durƙushe tare da idanuwansa a buɗe.5Yaya kyan alfarwarka, Yakubu, a wurin da ka zauna, Isra'ila!
6Kamar kwarurruka suka bazo, kamar gonaki a gefen kogi, kamar itatuwan aloyes da Yahweh ya dasa, kamar itatuwan al'ul a gefen ruwaye.
7Ruwa na malalowa daga bokatansu, iri ya jiƙu sosai. Sarkinsu zai fi Agag girma, za a ɗaukaka mulkinsu.
8Allah ne ya fisshe su daga Masar da iko kamar kutunkun ɓauna. Zai cinye al'ummai waɗanda suka yi faɗa gãba da shi. Zai kakkarya ƙasusuwansu gutsu gutsu. Zai harbe su da kibiyoyinsa.
9Zai laɓe a ƙasa kamar zaki, kamar zakanya. Ba bu wanda zai dame shi? Bari duk wanda ya albarka ce shi ya yi albarka; duk wanda ya la'anta shi ya zama la'ananne."
10Balak ya husata da Balaam, ya tafa hannunsa a cikin fushi. Balak yace da Balaam, "Na kirawo ka ka la'anta maƙiyana, amma ga shi har sau uku kana sa masu albarka.11Yanzu sai ka tafi gidanka. Na ce zan ɗaukaka ka, amma ga shi Yahweh ya hana ka samun wani lada."
12Sai Balaam ya amsa wa Balak, "Na faɗa wa manzanninka waɗanda ka aiko gare ni.13Idan Balak ya ba ni fadarsa cike da azurfa da zinariya, ba zan iya in zarce maganar Yahweh ba, da wani mugun abu ko mai kyau ne, kai kowanne irin abu ne zan so in yi. Zan faɗi abin da Yahweh ya faɗa mani shi zan ce.' Ban faɗa masu haka ba?14Saboda haka yanzu, ga shi, zan koma ga mutanena. Amma da farko bari in gargaɗe ka abin da waɗannan mutane za su yiwa mutanenka a ranaku masu zuwa."
15Balaam ya fara wannan annabci. Ya ce, "Balaam ɗan Beyor ya faɗa, mutumin da idanunsa ke buɗe.16Wannan shi ne annabcin wanda yake jin magana daga Allah, wanda ke da ilimi daga wurin Maɗaukaki, wanda ke da wahayi daga Mai Iko Dukka, A gaban wanda yake durƙurshe tare da idannunsa a buɗe.
17Na gan shi, amma baya nan yanzu. Ina hangensa, amma baya kusa. Tauraro zai fito daga cikin Yakubu, kendir zai fito daga cikin Isra'ila. Za ya ragargaje shugabannin Mowab ya hallaka dukkan zuriyar Shitu.
18Sai Idom ta zama mallakar Isra'ila, Seyir kuma za ta zama mallakarsu, abokan gãbar Isra'ila, waɗanda Isra'ila zasu ci da ƙarfi.19Daga cikin Yakubu sarki zai zo wanda zai yi mulki, zai hallaka waɗanda suka ragu a birninsu."
20Sai Balaam ya dubi Amalek ya fara annabcinsa. Ya ce, "Amalek mafi girma ne cikin al'ummai, amma ƙarshensa zai kasance hallaka."
21Sai Balaam ya duba zuwa wajen Kan'aniyawa, ya fara annabcinsa. Ya ce, "Wurin da kuke zama mai ƙarko ne, gidajenku kuma na cikin duwatsu.22Duk da haka ku Kan'aniyawa za a lalatar da ku da wuta idan Asiriyawa suka ɗauke ku bayi."
23Sai Balaam ya fara annabcinsa na ƙarshe. Ya ce, "Kaito! Wa zai rayu sa'ad da Allah ya yi wannan24Jiragen ruwa kuwa za su zo daga gaɓar tekun Kittim; za su faɗawa Asiriya, zasu ci Eber, amma kuma, ƙarshensu hallaka ce."
25Sai Balaam ya tashi ya tafi. Ya koma gidansa, Balak ma yayi tafiyarsa.

25

1Isra'ila ta zauna a Shittim, maza suka fara yin karuwancinsu da matan Mowab,2domin Mowabawa sun gayyaci mutane zuwa wajen hadayar allolinsu. Saboda haka mutane suka ci suka durƙusa wa allolin Mowabawa.3Mutanen Isra'ila suka shiga bautawa gumakun Ba'al na Feyor, Yahweh ya yi fushi da Isra'ila.

4Yahweh yace da Musa, "Kashe dukkan shugabannin mutanen, ka rataye su a gabana a nuna su a fili, don in huce daga fushi da nake yi da Isra'ila."5Musa kuwa ya cewa shugabanin Isra'ila, "Kowannen ku dole ya kashe mutanensa waɗanda suka shiga bautar gumakun Ba'al Feyor."
6Sai ɗaya daga cikin mutanen Isra'ila ya zo, ya kawo mace Bamidiyaniya cikin iyalinsa. Wannan ya faru ne a idannun Musa da dukkan jama'ar mutanen Isra'ila, a sa'ad da suke kuka a ƙofar alfarwar taro.7Finehas ɗan Eliyeza ɗan Haruna firist, ya gani, sai ya tashi daga cikin jama'a, ya ɗauki mãshi a hannunsa.
8Ya bi Ba'isra'ilen cikin alfarwa, ya soke dukkansu biyu, Ba'isra'ilen da macen. Da haka aka tsaida annobar da Allah ya aiko wa mutanen Isra'ila.9Waɗanda suka mutu saboda annobar sun kai jimilar mutane dubu ashirin da hudu.
10Yahweh ya faɗa wa Musa ya ce,11"Finehas ɗan Eliyeza ɗan Haruna firist, ya kawar da fushina daga mutanen Isra'ila gama yayi kishi irin nawa a cikinsu. Saboda haka ba zan hallakar da mutanen Isra'ila da fushina ba.
12Saboda haka ne, 'Yahweh ya faɗa, "Duba, ina ba Finehas alƙawarin salamata.13Dominsa da zuriyarsa zasu bi shi, alƙawarin da ba zai taɓa ƙarewa ba daga firistoci gama yana da kishi domin, Allahnsa. Ya kuwa yi kafara domin mutanen Isra'ila.'"'
14Yanzu sunan Ba'isra'ilen da aka kashe tare da Bamidiyar, Zimri ɗan Salu, shugaban zuriyar iyalin Simiyonawa.15Sunan Bamidiyar wanda aka kashe, ita ce Kozbi 'ɗiyar Zur, wanda yake shi ne shugaban wata kabila na iyalin Midiyan.
16Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,17"Ku fãɗa wa Midiyanawa abokan gãbarku, ku hallaka su,18gama sun yi maku kamar abokan gãbanku da makircinsu. Sun kai ku cikin mugun abu a kan Feyor da na Kozbi 'yar'uwarsu, ɗiyar shugaban Midiyan, wadda aka kashe a ranar da aka yi annoba a Feyor."

26

1Ya zamana bayan annobar sai Yahweh ya yi magana da Musa da Eliyeza ɗan Haruna firist. Ya ce,2"Ku ƙidaya dukkan taron mutanen Isra'ila, daga mai shekaru ashirin zuwa gaba, bisa ga zuriyar kakanninsu, da dukkan waɗanda za su iya zuwa yaƙi domin Isra'ila."

3Musa da Eliyeza firist suka yi masu magana a filayen Mowab daura da Yodan a Yeriko, suka ce,4"A ƙidaya mutane daga mai shekaru ashirin zuwa gaba kamar yadda Yahweh ya umarci Musa da mutanen Isra'ila, waɗanda suka fito daga ƙasar Masar."
5Ruben shi ne ɗan fari na Isra'ila. Daga ɗansa Hanok kabilar Hanokiyawa ta zo. Daga Fallu kabilar Falluniyawa ta zo.6Daga Hesruna har zuwa kabilar Hezaroniyawa. Daga Karmi har zuwa kabilar Karmiyawa.7Waɗannan su ne kabilun Ruben, waɗannan yawansu ya kai jimilar mutane 43,730.
8Eliyab shi ne ɗan Fallu.9'Ya'yan Eliyab su ne Nemuwel da Datan da Abiram. Waɗannan su ne Datan da Abiram waɗanda suka bi Korah a lokacin da suka yi wa Musa da Haruna ƙalubale, suka kuma yi tawaye ga Yahweh.
10Ƙasa kuwa ta buɗe bakinta ta haɗiye su tare da Kora da dukkan mabiyansa suka mutu. A wancan lokaci, wuta kuma ta cinye mutane 250, waɗanda suka zama abin faɗakarwa.11Amma iyalin Kora ba su mutu ba.
12Kabilar zuriyar Simiyon su ne waɗannan: Ta wurin Nemuwel, aka sami kabilar Nemuwelawa, ta wurin Yamin, kabilar Yaminawa, ta wurin Yakin, kabilar Yakinawa,13ta wurin Zera, kabilar Zerawa, ta wurin Shawul, kabilar Shawulawa.14Waɗannan su ne kabilun zuriyar Simiyon, waɗanda aka ƙidaya jimilar mutane 22,200.
15Kabilar zuriyar Gad su ne waɗannan: Ta wurin Zifon, aka sami kabilar Zifonawa, ta wurin Haggi, kabilar Haggiyawa, ta wurin Shuni, kabilar Shuniyawa16ta wurin Ozni, kabilar Oziniyawa, ta wurin Eri, kabilar Eritiyawa,17ta wurin Arod kabilar Arodiyawa, ta wurin Areli, aka sami kabilar Areliyawa.18Waɗannan su ne kabilar zuriyar Gad sun kai jimilar mutane 40,500.
19'Ya'yan Yahuda su ne Er da Onan, amma waɗannan mutane sun rasu a ƙasar Kan'ana.20Sauran kabilar zuriyar Yahuda su ne: ta wurin Shela, kabilar Shelatawa, ta wurin Feresa, kabilar Feresawa, da ta wurin Zera, kabilar Zerawa.21Zuriyar Ferez su ne: Ta wurin Hezron, kabilar Hezronawa, ta wurin Hamul, kabilar Hamulawa.22Waɗannan su ne zuriyar kabilar Yahuda sun kai jimilar mutane 76,500.
23Kabilar zuriyar Issaka su ne: Ta wurin Tola, kabilar Tolawa, ta wurin Fuwa, kabilar Fuwayawa,24ta wurin Yashub, kabilar Yashubawa, ta wurin Shimron, kabilar Shimronawa.25Waɗannan su ne kabilun Issaka, waɗanda sun kai jimilar mutane 64,300.
26Zuriyar kabilar Zebulun su ne waɗannan: Ta wurin Sered, kabilar Seredawa, ta wurin Elon, kabilar Elonawa, ta wurin Yaleyel, kabilar Yaleyawa.27Waɗannan su ne kabilun Zebulun, sun kai jimilar mutane 60,500.
28Zuriyar kabilar Yosef su ne Manasse da Ifraim.29Zuriyar Manasse su ne waɗannan: ta wurin Makir, kabilar Makiriyawa (Makir shi ne mahaifin Giliyad), ta wurin Giliyad, kabilar Gilidiyawa.
30Zuriyar Giliyad su ne waɗannan: Ta wurin Leza, kabilar Lezawa, ta wurin Helek, kabilar Helekawa,31ta wurin Asriyel, kabilar Asrilawa,32ta wurin Shekem, kabilar Shekemawa, ta wurin Shemida, kabilar Shemidawa, ta wurin Hefer, kabilar Heferawa.
33Zelofehad ɗan Hefer ba shi da 'ya'ya maza, amma sai 'ya'ya mata kaɗai. Sunayen 'ya'yansa mata su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka daTirza.34Waɗannan su ne kabilar Manasse, sun kai jimilar mutane 52,700.
35Zuriyar kabilar Ifraim su ne waɗannan: Ta wurin Shutela, kabilar Shutelawa, ta wurin Beker, kabilar Bekerawa, ta wurin Tahat, kabilar Tahatawa.36Zuriyar Shutela su ne, ta wurin Eran, kabilar Eraniyawa.37Waɗannan su ne zuriyar kabilar Ifraim, sun kai jimilar mutane 32,500. Waɗannan su ne zuriyar Yosef an lissafta kowanne bisa ga kabilunsu.
38Zuriyar kabilar Benyamin su ne waɗannan: Ta wurin Bela, kabilar Belayawa, ta wurin Ashbel, kabilar Ashbelawa, ta wurin Ahiram, kabilar Ahiramawa,39ta wurin Shefufam, kabilar Shefufamawa, ta wurin Hufam, kabilar Hufamawa.40'Ya'yan Bela maza su ne Ard da Na'aman. Daga Ard aka sami kabilar Ardawa, daga Na'aman aka sami kabilar Na'amawa.41Waɗannan su ne zuriyar Benyamin. Yawan mutane 45,600 ne.
42Zuriyar kabilar Dan su ne, ta wurin Shuham, aka sami kabilar Shuhamawa. Waɗannan su ne zuriyar kabilun Dan.43Dukkan kabilun Shuhamawa sun kai yawan mutane 64,400.
44Zuriyar kabilar Asha su ne waɗannan: Ta wurin Imna, kabilar Imnawa, ta wurin Ishbi, kabilar Ishabawa, ta wurin Beriya, kabilar Beriyawa.45Zuriyar Beriya su ne waɗannan: Ta wurin Hebar, kabilar Hebarawa, ta wurin Malkiyel, kabilar Malkiyawa.46Sunan 'yar Asha Sera.47Waɗannan su ne zuriyar kabilun Asha, sun kai jimilar mutane 53,400.
48Zuriyar kabilar Naftali su ne waɗannan: Ta wurin Yazeyel, kabilar Yazelawa, ta wurin Guni, kabilar Guniyawa,49ta wurin Yezer, kabilar Yezerawa, ta wurin Shilem, kabilar Shilemawa.50Waɗannan su ne zuriyar kabilun Naftali sun kai jimilar mutane 45,400.
51Wannan shi ne cikakken lissafin maza a cikin mutanen Isra'ila: 601,730.
52Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,53"Dole a raba ƙasar ga waɗannan mutane gãdo bisa ga yawan sunayensu.
54Za ka ba babbar kabila babban rabon gãdo, ka ba karamar kabila karamin rabon gãdo. Kowacce kabila za a ba ta gãdo bisa ga yawan mutanenta da aka lissafta.55Amma za a rarraba ƙasar ta wurin kuri'a. Za su gaji ƙasar yadda aka raba a tsakanin kabilun kakanninsu.56Za a rarraba gãdo tsakanin manya da ƙananan kabilai ta hanyar kuri'a."
57Kabilar Lebiyawa da aka ƙidaya bisa kabila kabila, su ne waɗannan: Ta wurin Gershon, kabilar Gershawa, ta wurin Kohat, kabilar Kohatiyawa, ta wurin Merari, kabilar Merariyawa.58Kabilar Lebi su ne waɗannan: kabilar Lebiyawa da kabilar Hebroniyawa da kabilar Maliyawa da kabilar Mushiyawa da kabilar Koriyawa. Kohat shi ne kakan Amram.59Sunan matar Amram ita ce Yokabed, zuriyar Lebi, wanda ya haifi Lebiyawa a Masar. Ta haifa wa Amram 'ya'yansu, su ne Haruna da Musa da Miriyam 'yar uwarsu.
60Haruna ya haifi Nadab da Abihu, Eliyeza da Itamar.61Nadab da Abihu sun rasu saboda sun miƙa hadaya da haramtacciyar wuta a gaban Yahweh.62Mazan da aka ƙidaya daga cikinsu sun kai dubu ashirin da uku, dukkansu maza daga wata ɗaya zuwa sama. Amma ba a ƙidaya su ba cikin zuriyar Isra'ila domin ba a ba su gãdo a cikin mutanen Isra'ila ba.
63Waɗannan su ne waɗanda Musa da Eliyeza firist suka ƙidaya. Suka ƙidaya mutanen Isra'ila a kwarin Mowab Yodan a Yeriko.64Gama a cikin waɗannan babu mutum wanda Musa da Haruna firist ba su ƙidaya ba a zuriyar Isra'ila da aka ƙidaya a jeji Sinai.
65Gama Yahweh ya ce da dukkan waɗannan mutane lalle za su mutu a jeji. Ba wani mutumin da ya ragu daga cikinsu, sai dai Kalibu ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.

27

1Sai Musa ya zo wurin 'ya'ya mata na Zelofehad ɗan Hefer ɗan Giliyad ɗan Makir ɗan Manasse, kabilar Manasse ɗan Yosef. Waɗannan su ne sunayen 'ya'yansa mata: Mala, Nowa, Hogla, Milka da kuma Tirza.

2Suka tsaya a gaban Musa da Eliyeza firist, da shugabanni, da dukkan jama'a a ƙofar shiga rumfar taro. Suka ce,3"Mahaifinmu ya rasu a cikin jeji. Ba ya cikin waɗanda suka tayar wa Yahweh a ƙungiyar Kora. Ya mutu saboda alhakin zunubinsa, ga shi ba shi da 'ya'ya maza.
4Donme za a cire sunan mahaifinmu daga cikin kabilar iyalinsa saboda ba shi da ɗa? Ka ba mu gãdo tare da 'yan'uwan mahaifinmu"5Musa ya kai maganarsu a gaban Yahweh.
6Yahweh ya yi magana da Musa, ya ce,7"Ya'ya mata na Zelofehad suna magana dai dai. Ka ba su ƙasa a matsayin gãdo a cikin 'yan'uwansu, za ka tabbatar sun sami gãdon mahaifinsu.8Ka yi magana da mutanen Isra'ila, ka ce, 'Idan mutum ya rasu, ba shi da ɗa, sai ka sa gãdon mahaifinsa ya koma kan 'yarsa.
9Idan ba shi da 'ya, sai ka bada gãdon ga 'yan'uwansa.10Idan kuma ba shi da 'yan'uwa maza, sai ka bada gãdonsa ga 'yan'uwan mahaifinsa maza.11Idan kuwa ba shi da 'yan'uwa maza, sai ka bada gãdonsa ga 'yan'uwansa na kusa a kabilarsa, zai ɗauke ta don kansa. Wannan ita ce doka da aka tabbatar da ka'ida saboda mutanen Isra'ila, kamar yadda Yahweh ya umarce ni.'"
12Yahweh yace da Musa, "Tafi bisa duwatsun Abarim, ka dubi ƙasa wadda na ba mutanen Isra'ila.13Bayan daka ganta, kai ma, za a tara ka ga mutanenka, kamar Haruna ɗan'uwanka.14Wannan zai kasance domin ku biyun kun yi tawaye akan umarnina cikin jejin Zin. A can, lokacin da ruwa ke kwararowa daga dutse, a cikin fushi baku girmama ni kamar mai tsarki a gaban idannun dukkan jama'a ba." Waɗannan su ne ruwayen Meriba dana Kadesh a jejin Zin.
15Sai Musa ya yi magana da Yahweh, ya ce,16"Bari kai, Yahweh, Allah na ruhohin dukkan 'yan adam, ya naɗa mutum bisa kan jama'a,17mutum wanda zai tafi, ya dawo a gabansu, ya shugabance su ya fita, ya dawo, saboda jama'arka ba kamar tumakin da ba makiyayi suke ba."
18Yahweh yace da Musa, "Ka ɗauki Yoshuwa ɗan Nun, mutum wanda Ruhuna yake raye a cikinsa, ka sa hannunka a kansa.19Sa shi a gaban Eliyeza firist da gaban dukkan jama'a, ka umarce shi a gaban idanunsu ya shugabance su.
20Ka danka masa ikonka a kansa, don dukkan jama'ar mutanen Isa'ila su yi masa biyayya.21Zai wuce gaban Eliyeza firist ya nemi nufina domin sa, ta wurin yanke shawarar Urim. Zai zama bisa ga umarninsa da mutane za su tafi waje su kuma komo ciki, shi da dukkan mutanen Isra'ila tare da shi, da kuma dukkan jama'a."
22Sai Musa ya yi kamar yadda Yahweh ya umarce shi. Ya ɗauki Yoshuwa ya sa shi a gaban Ele'yazar firist da dukkan jama'a.23Ya ɗibiya hannuwansa a kansa, ya umarce shi ya yi shugabanci, kamar yadda Yahweh ya umarce shi ya yi.

28

1Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,2"Ka umarci mutanen Isra'ila, ka ce da su, 'Za ku miƙa hadaya gare ni a ayyanannun lokatai, ta abincin baye-baye na ta wurin wuta mai daɗin ƙanshi domi na.'

3Ka kuma ce da su, 'Wannan bayarwa da za a yi da wuta, za ku bayar ga Yahweh--ɗan tunkiya shekara ɗaya wanda babu lahani a gare shi, guda biyu kowacce rana, matsayin bayarwar ƙonawa.4Dan tunkiya ɗaya za ku bayar da safe, ɗaya kuma da maraice.5Za ku bayar da mudun lallausan garin filawa matsayin bayarwar hatsi, kwaɓaɓɓe da man zaitun mafi kyau har rubu'in moɗa.
6Wannan zata zama ta bayarwar ƙonawa da za ku riƙa yi yadda an umarta a Tsaunin Sinai baiko mai daɗin ƙanshi, da aka yi da wuta ga Yahweh.7Bayarwar sha zata zama ɗaya bisa huɗu na moɗa don ɗaya ɗan rago. Za a kwarara a wuri mai tsarki baiko na sha mai ƙarfi ga Yahweh.8Ɗaya ɗan ragon kuma za a miƙa da maraice tare da baiko na gari kamar baiko na safe. Dole ne kuma a miƙa wani na sha tare da shi, baikon ƙonawa da wuta, mai daɗin ƙamshi ga Yahweh.
9A ranar Asabaci kuwa za a miƙa 'ya'yan raguna biyu kowanne bana ɗaya marasa lahani, da mudu biyu na lallausan gari a matsayin baiko, kwaɓaɓɓe da mai, da baiko na sha tare da shi.10Wannan shi ne baikon ƙonawa domin kowacce Asabaci, a kan kowanne baiko na ƙonawa da baiko na sha tare da shi.
11A farkon kowanne wata, za a miƙa baikon ƙonawa ga Yahweh. Za a miƙa 'yan bijimai biyu, da rago ɗaya da kuma 'yan raguna bakwai bana ɗaya ɗaya, marasa lahani.12Za a kuma miƙa kwaɓaɓɓen gari kashi uku bisa ɗaya na garwa da man zaitun don kowanne bijimi, da gari kashi biyu bisa goma na garwa don rago ɗaya.13Za a kuma miƙa humushin lallausan gari za a haɗa shi da mai kamar baikon hatsi don kowanne rago. Wannan zai zama baikon ƙonawa, domin ya bayar da ƙamshi mai daɗi, baiko da aka yi da wuta ga Yahweh.
14Baiko na sha na mutane dole ya zama rabin moɗa na ruwan inabi don bijimi, da ɗaya bisa uku na moɗa don rago da ɗaya bisa huɗu na moɗa don ɗan rago. Wannan shi ne baiko na ƙonawa a kowanne wata a dukkan watannin shekara.15Dole kuma a miƙa bunsuru ɗaya a matsayin baiko na zunubi ga Yahweh. Wannan zai zama ƙarin baiko na ƙonawa da baiko na sha da za a riƙa yi da su.
16A cikin wata na farko, a rana ta goma sha huɗu ga watan, idin Ƙetarewa ga Yahweh.17A kan rana ta goma sha biyar ga wannan watan kuwa za a yi idi. Gama kwanaki bakwai na cin abinci mara gami ne.18A rana ta fari, za ku yi tsarkakakken taron girmama Yahweh. Ba za ku yi aikin da kuka saba yi a ranar ba.
19Duk da haka, dole ku miƙa baiko da aka yi da wuta, a baiko na ƙonawa ga Yahweh. Dole ku miƙa 'yan bijimai biyu da rago ɗaya, da 'yan tumaki bakwai bana ɗaya ɗaya marasa lahani.20Tare da bijimi, za ku miƙa lallausan gari kashi uku na garwa wanda aka kwaɓa da mai tare da rago, kashi biyu bisa uku.21Tare da kowanne 'yan raguna bakwai, za ku miƙa lallausan gari haɗe da mai,22da ɗan akuya ɗaya a matsayin baikon zunubin ƙafara domin kanku.
23Dole ku miƙa waɗannan a kan bayarwar ƙonawa da kuke miƙawa kowacce safiya.24Kamar yadda aka nuna a nan, za ku miƙa waɗannan hadayu kullum, saboda ranaku bakwai na Idin ‌Ƙetarewa, za ku yi baikon abincin da aka yi da wuta mai daɗin kamshi ga Yahweh. Za a miƙa a kan bayarwar ƙonawa da kuke yi da baiko na sha.25A rana ta bakwai za ku yi tsattsarkan taro na girmama Yahweh, ba za ku yi aikin da kuka saba yi ba a ranar.
26Haka nan a ranar nunar fari, da kuke miƙa baikon sabon hatsi ga Yahweh a Bikin Makonni, za ku yi tsattsarkan taro na girmama Yahweh, ba za ku yi aikin da kun saba yi ba a ranar.27Dole ne ku miƙa baikon ƙonawa mai dadin ƙamshi ga Yahweh. Dole ne ku miƙa 'yan bijimai biyu da rago ɗaya da 'yan tumakai maza guda bakwai bana ɗaya ɗaya.28Kuma ku miƙa baikon gari tare da su: gari haɗe da mai, gari kashi uku bisa uku da aka haɗa da mai domin kowanne bijimi da kashi biyu don rago ɗaya.
29Ku miƙa kashi goma na garwa da aka haɗa da mai don kowanne 'yan raguna bakwai,30da ɗan akuya na ƙafara domin kanku.31Idan kuka miƙa waɗannan dabobbin marasa lahani, tare da baye bayenku na sha, wannan zai zama a kan baye-bayen ƙonawa, da hatsi da kuke bayarwa tare su.'"

29

1A cikin wata na bakwai, a rana ta farko ta watan, za ku yi taro mai tsarki na girmama Yahweh. Tilas ba za ku yi wani aikin da aka saba a koda yaushe ba a wannan rana. Dole ne ta zama ranar da za ku busa ƙahonni.

2Za ku miƙa ƙonannen baiko domin abin daɗi da ƙamshi ga Yahweh. Dole ku miƙa ɗan bijimi, rago ɗaya, da 'yan raguna bakwai masu shekara ɗaya, mara aibi.
3Dole ne ku miƙa su tare da baikonsu na hatsi, gari mai laushi cuɗaɗɗe da mai, uku cikin goma na efa domin bijimi, biyu cikin goma domin ragon,4ɗaya cikin goma kuma domin kowanne cikin raguna bakwai.5Dole ne ku miƙa bunsuru ɗaya domin baiko na zunubi don a yi maku kafara.
6A miƙa waɗannan baye-baye a cikin wata na bakwai a bisa kan sauran dukkan baye-bayen da za ku bayar a ranar farko ta kowanne wata: ƙonannen baiko na musamman da kuma baiko na hatsi a haɗa da shi. Waɗannan dole za a miƙa su zama ƙãri bisa ga ƙonannen baikon da aka sãba, baiko hatsin, da kuma baye-bayensa na sha. Sa'ad da kuka miƙa waɗannan baye-bayen, za ku yi biyayya da abin da aka umurtar don ya bãda ƙamshi mai daɗi, baiko na wurin wuta ga Yahweh.
7A rana ta goma ga watan bakwai za ku yi taro mai tsarki don girmama Yahweh. Dole ku ƙasƙantar da kanku ba za ku yi wani aiki ba.8Dole ku miƙa baiko na ƙonawa mai bãda ƙamshi mai daɗi ga Yahweh. Dole ku miƙa ɗan bijimi ɗaya, da ɗan rago ɗaya, da kuma 'yan raguna 'yan shekara ɗaya guda bakwai.
9Dole ku miƙa tare da su baiko na hatsi, gãri mai laushi gauraye da mai,10uku cikin goma na efa domin bijimi, biyu cikin uku domin tunkiya guda ɗaya, da kuma kashi goma na efa domin dukkan raguna bakwai ɗin.11Dole ku miƙa ɗan akuya ɗaya don baikon na zunubi. Wannan zai zama ƙãri bisa baikon zunubi na kaffara, da baye-bayensu na sha.
12A rana ta sha biyar ga watan bakwai za ku yi taro mai tsarki don girmama Yahweh. Ba za ku taɓa yin wani aiki yadda kuka sãba a kodayaushe a wannan rana ba, kuma za ku yi buki gare shi kwana bakwai.13Dole ku miƙa baiko na ƙonawa, hadaya da aka miƙa ta wurin wuta domin abin ƙamshi da daɗi ga Yahweh. Dole ku miƙa 'yan bijimi guda sha uku, tumaki guda biyu, da kuma tumakai guda sha huɗu 'yan shekara ɗaya. Kowanen su ya zama mara aibi.
14Dole ne ku miƙa tare da su baiko na hatsi, niƙaƙƙen gari harɗe da mai, kashi uku na efa don kowanne rago na raguna sha ukun, kashi biyu domin kowanne rago na raguna biyun,15da kashi ɗaya na efa domin dukkan tumaki guda sha huɗun.16Dole ku miƙa baiko na zunubi namijin akuya ɗaya ƙãri bisa ƙonannun baiko na kodayaushe, baikon hatsin, tare da shi kuma da baikon abin sha.
17A rana ta biyu na taruwa, dole ne ku miƙa 'yan raguna guda sha biyu, tumaki biyu, da awakai maza goma sha huɗu 'yan shekara ɗaya, kowanne mara aibi.18Dole ku miƙa su tare da baikon hatsi da baye-baye na shã domin ragunan, domin tumakin, domin kuma awakan, kuna miƙa baye-baye masu yawa kamar yadda aka umarce ku.19Dole ne ku miƙa baiko na zunubi ɗan rago ɗaya ƙãri bisa baiko na ƙonawa a kodayaushe yaushe, da kuma baye-bayensu na shã.
20A rana ta uku na taruwan, dole ne ku miƙa raguna shaɗaya, tumaki biyu, da bunsurai sha huɗu 'yan shekara ɗaya, kowanne mara aibi.21Dole ne ku miƙa su tare da baiko na hatsi da baye-baye na abin shã domin ragunan, domin su tumakin, da kuma don su awakan, kuna miƙa baye-baye masu yawa kamar yadda aka umarce ku.22Dole ne ku miƙa namijin tunkiya ɗaya baiko na zunubi ƙãri bisa baiko na ƙonawa na kodayaushe, baikon hatsinta, da kuma baye-bayensu.
23A rana ta huɗu ta taruwa, dole ne ku miƙa raguna guda goma, tumaki guda biyu, da mazajen awakai 'yan shekara ɗaya guda shahuɗu, kowannensu marasa aibi.24Dole ne ku yi tare da su baiko na hatsi da baye-baye na shã domin ragunan, domin tumakin, da kuma domin awakan, kuna miƙa baye-baye masu yawa kamar yadda aka umarce ku.25Dole ne ku miƙa bunsuru ɗaya baiko na zunubi ƙãri bisa baiko na ƙonawa na kodayaushe, baiko na hatsinsa, da baye-bayensu na shã.
26A rana ta biyar ta taruwa, dole ne ku miƙa raguna guda tãra, tumaki biyu, da bunsurai 'yan shekara ɗaya guda sha huɗu, marasa aibi.27Dole ne ku miƙa su tare da baiko na hatsi da kuma baye-baye na shã domin ragunan, domin tumakin, domin kuma awakan, ana miƙa baye-baye masu yawa kamar yadda aka umurta.28Dole ne ku miƙa namijin tunkiya ɗaya na baikon domin zunubi ƙari bisa ƙonannen baiko na kodayaushe, baikon hatsin, da baye-baye na shãnsu.
29A rana ta shida ta taruwar, dole ne ku miƙa raguna takwas, tumaki biyu, da mazajen awakai guda sha huɗu 'yan shekara ɗaya, marasa aibi.30dole ne ku miƙa su tare da baiko na hatsi da kuma baye-baye na shã domin ragunan, domin tumakan, domin kuma awakan, kuna miƙa baye-baye masu yawa kamar yadda aka umurce ku.31dole ne ku miƙa bunsuru guda ɗaya baiko na zunubi, baikon hatsi, da baye-bayensu na shã.
32A rana ta bakwai na taruwa, dole ne ku miƙa raguna guda bakwai, tumakai biyu, da kuma bunsurai guda sha huɗu 'yan shekara ɗaya, marasa aibi.33Dole ne ku miƙa tare da su baiko na hatsi da baye-baye na shã domin ragunan, domin tumakan, domin kuma awakan, kuna miƙa baye-baye masu yawa kamar yadda aka umurce ku.34Dole ne ku miƙa namijin akuya domin baiko na zunubi don ƙari bisa ga baiko na ƙonawa kamar na kodayaushe, domin baiko na hatsin, da kuma baye-bayensu na shã.
35A rana ta takwas zaku sake yin wani taron mai tsarki. Kar ku kuskura ku yi wani aiki kamar yadda kuka saba a wannan rana.36Dole ne ku miƙa hadaya na ƙonawa, baiko da aka yi da wuta domin a miƙa abin ƙamshi mai daɗi ga Yahweh. Za ku miƙa ɗan bijimi guda ɗaya, akuya ɗaya, da kuma 'yan raguna guda bakwai masu shekara ɗaya, kowanne mara aibi.
37Dole ne ku miƙa baikon hatsinsu da kuma baikon abin sha domin bijimi, domin ɗan akuya, kuma domin 'yan raguna, kuna miƙa baye-baye kamar yadda aka umurta.38Dole ne ku miƙa bunsuru guda ɗaya baiko na zunubi ƙari bisa ƙonannen baikon da aka sãba kodayaushe, baikon hatsinsu, da kuma baye-bayensu na shã.
39Waɗannan su ne dole ku miƙa ga Yahweh a tsayayyun bukukuwanku. Waɗannan za su zama ƙãri ne bisa alƙawaranku da kuma baye-bayenku na yardan rai. Dole ne ku miƙa waɗannan a matsayin baye-bayenku na ƙonawa, baye-baye na hatsi, baye-baye na shã, da baye-baye na zumunci."40Sai Musa ya gaya wa mutanen Isra'ila dukkan abin da Yahweh ya umurce shi ya faɗa.

30

1Musa ya yi magana da shugabannin ƙabilun mutanen Isra'ila. Ya ce, "Ga abin da Yahweh ya umarta.2Idan wani ya yi wa'adi ga Yahweh, ko ya yi rantsuwa don ya riƙe kansa ga alƙawari, kada ya karya maganarsa. Dole ya cika alƙawarinsa ya aikata duk abin da ya fito daga bakinsa.

3Idan 'yar matashiya mace mai zama cikin gidan mahaifinta ta yi wa'adi ga Yahweh ta ɗaure kanta ga alƙawari,4idan mahaifinta ya ji wa'adin da kuma alƙawarin da ta daukar wa kanta, kuma idan bai ce komai ba domin ya hana ta ba, to dukka wa'adodinta za su tsaya. Kowanne alƙawarin da ta ɗaukar wa kanta zai tsaya.
5Amma idan mahaifinta ya ji game da wa'adinta da alƙawarinta, idan kuma bai ce da ita komai ba, to dukkan wa'adodinta da alƙawaranta da ta ɗaukar wa kanta za su tsaya.
6Amma, idan mahaifinta ya ji dukkan wa'adodin da ta yi da kuma alƙawura masu tsarki da ta ɗaukar wa kanta, idan kuma ya sọke abin da ta yi a wannan ranar, to ba za su tsaya ba. Yahweh zai gafarta mata domin mahaifinta ya sọke abin da ta yi.7Idan ta auri mutum yayin da ta ke ƙarƙashin waɗannan wa'adodin, ko kuma idan ta furta alƙawarai cikin garaje da ta ɗaukar wa kanta nawaya, wannan nawayar tilas ta tsaya.
8Amma idan mijinta ya hana ta a ranar da ya ji game da zancen, sa'an nan ya hana alƙawarin da ta ɗauka, maganar gangancin da ta yi ta fita daga leɓunanta da ta ɗaure kanta. Yahweh zai sãke ta.
9Amma game da gwauruwa ko sakakkiyar mace, dukkan abin da ta ɗaure kanta da shi zai tsaya a kanta.10Idan mace ta ɗauki alƙawari a cikin gidan mijinta ko ta yi wa kanta hani ta wurin yin rantsuwa,11sai kuma maigidanta ya ji game da wannan, amma bai ce mata komai ba, to sai dukkan abin da ta alƙawarta su tsaya.
12Amma idan maigidanta ya hana su a wannan ranar da ya ji game da su, to duk abin da ya fito daga leɓunanta game da wa'adodinta ko alƙawaranta baza su tsaya ba. Mijinta ya hana su. Yahweh zai sãke ta.
13Kowanne wa'adi ko rantsuwar da mace ta yi da suka ɗaure ta har ta hana wa kanta wani abu maigidanta na iya tabbatarwa ko ya hana.14Amma idan bai ce mata komai a ranar ba, to ya tabbatar da dukkan wa'adodi da zaunannun alƙawarai wadanda ta ɗauka. Ta haka ya tabbatas da su domin bai ce da ita komi ba a ranar da ya ji game da su.
15Idan mijinta yayi ƙoƙarin hana alƙawarin da matarsa ta ɗauka da daɗewa bayan ya ji shi, don haka zai ɗauki laifinta."16Waɗannan su ne farillan da Yahweh ya umarci Musa da ya sanar - da farillai game da abin dake tsakanin mutum da matarsa da kuma tsakanin mahaifi da ɗiyarsa a matashiyarta sa'ad da take tare da iyalin mahaifinta.

31

1Yahweh ya yi magana da Musa ya kuma ce,2"Ka ɗauki fansa a bisa Midiniyawa kan abin da suka yi wa Isra'ilawa. Bayan ka yi wannan, za ka mutu a kuma tara ka ga mutanenka."

3Sai Musa ya yi magana da mutanen. Ya ce, "Ku shirya wasu daga cikin mazajenku don yaƙi gãba da Midiyan, ku kuma yi ramako na Yahweh a bisanta.4Kowacce kabila cikin dukkan Isra'ila dole ta aika da sojoji dubu zuwa yaƙi."5Saboda haka cikin dubban mazajen Isra'ila, aka aika da dubu ɗaya daga kowacce kabila, mazaje dubu sha biyu shiryayyu don yaƙi.
6Sai Musa ya aika da su zuwa yaƙi, daga kowacce kabila dubu ɗaya, tare da Finehas ɗan Eliyeza firist, da kuma wasu kayayyaki daga cikin wuri mai tsarki da kuma su ƙahonni dake a hannunsa don busawa ta alamar yaƙi.7Suka yi yaƙi da Midiya, kamar yadda Yahweh ya bada umarni ga Musa. Suka karkashe kowanne mutum.8Suka kashe sarakunan Midiyan tare da sauran matattunsu: Ebi, da Rekem, da Zur, da Hur, da kuma Reba, sarakuna guda biyar na Midiyan. Suka kuma kashe Bala'am ɗan Beyor, da takobi.
9Rundunar Isra'ila suka kwashe bayi matayen Midiyan, da yaransu, da dukkan shanunsu, da garkunansu, da dukkan dukiyarsu. Suka kwashe su ganima.10Suka ƙone dukkan biranensu inda suke zama da dukkan sansaninsu.
11Suka kwashe dukkan ganimar da kuma 'yan sarƙoƙi, da mutane da dabbobi.12Suka dawo da 'yan sarƙoƙin, da ganimar, da abubuwan da aka ƙwace wurin Musa, ga Eliyeza firist, zuwa kuma ga jama'ar Isra'ila. Suka kawo su zuwa cikin sansani cikin kwarurukan Mowab, wanda ke bakin Yodan kurkusa da Yeriko.
13Musa, da Eliyeza firist, da dukkan shugabannin jama'a suka fito domin su tarye su a wajen sansani.14Amma Musa ya yi haushi da shugabannin rundunar, kwamandojin na dubbai da kuma na ɗari ɗari, waɗanda suka dawo daga yaƙi.15Musa yace masu, "Kun bar dukkan matayen su rayu ko?
16Duba, waɗannan mataye sun jawo wa mutanen Isra'ila, ta wurin shawarar Bala'am, su aikata zunubi ga Yahweh ga zancen Feyor, yayinda annoba ta bazu cikin mutanen Yahweh.17Yanzu fa, sai ku kashe kowanne namiji cikin dukkan ƙananan, ku kuma kashe kowacce macen da ta taɓa kwana da namiji.
18Amma ku ɗaukar wa kanku dukkan 'yan matan da ba su taɓa kwana da namiji ba.19Dole ku yi sansani can a wajen sansani na Isra'ila har na kwana bakwai. Dukkan ku da kuka kashe wani da kuma ko kuka taɓa duk wani matacce -dole ku tsarkake kanku a rana ta uku a rana ta bakwai kuma- ku da bayinku.20Dole ku tsarkake kowacce tufa da kowanne abin da aka yi da fatar dabba da gashin akuya, da kuma kowanne abin da aka yi da itace."
21Sai Eliyeza yace da sojoji waɗanda suka tafi yaƙi, "Wannan shi ne umarnin shari'a da Yahweh ya bayar ga Musa:22Zinariyar, da azurfa, da jangaci, da tama, da kuza, da dalma,23da kuma kowanne abin da ya jimre ma wuta, sai ka saka shi ta wurin wuta, za shi kuma yi tsabta. Dole daga nan ka tsarkake waɗannan abubuwa da ruwan tsarkakewa. Duk abin da ba za shi shiga ta wuta ba sai ka tsarkake da ruwa.24Dole ku wanke tufafinku a rana ta bakwai, daga nan zaku zama da tsabta. Daga nan kuna iya shigowa cikin sansanin Isra'ila."
25Sai Yahweh ya yi magana da Musa ya kuma ce,26"Ka ƙirga dukkan abin ganimar da aka kawo, da mutane da dabbobi. Kai, da Eliyeza firist, da kuma shugabanni na gidajen ubanni na mutane27za a raba ganimar gida biyu. Ka raba a tsakanin sojojin da suka tafi yaƙi da kuma dukkan sauran mutanen.
28Sa'an nan za ka sa a karɓi haraji domina daga wurin sojojin da suka tafi yaƙi. Wannan harajin dole ya zama ɗaya daga cikin kowanne ɗari biyar, ko na mutane, ko na dabbobi, ko na jakuna, ko na awakai, ko tumakai.29Ka ɗauki wannan haraji daga rabinsu ka kuma bada su ga Eliyeza firist abin baikon da za a miƙa gare ni.
30Haka kuma daga rabin mutanen Isra'ila, sai ka karɓi ɗaya daga cikin kowanne hamsin - daga wurin mutane, ko shanu, ko jakai, ko awakai, da kuma tumaki. Ka miƙa su ga Lebiyawa ma su lura da mazamnina.31Sai Musa da Eliyeza firist suka yi kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.
32To yanzu dai ganimar da ta rage daga cikin abin da sojojin suka ɗauka su ne tumaki 675,000,33shanu dubu saba'in da biyu,34jakuna dubu sittin da ɗaya,35da kuma 'yan mata dubu talatin da biyu waɗanda ba su taɓa kwana da wani namiji ba.
36Rabin da aka ajiye domin sojoji tumaki 337,000 ne.37Tumaki waɗanda suke na Yahweh kuma 675 ne.38Shanu dubu talatin da shida ne waɗanda harajin Yahweh saba'in da biyu ne.
39Jakunan 30,500 ne, waɗanda daga ciki na Yahweh sittin da ɗaya ne.40Mutum dubu sittin ne daga ciki kuwa na harajin Yahweh talatin da biyu ne.41Sai Musa ya ɗauki harajin da za a miƙa ta baiko ga Yahweh. Ya bayar ga Eliyeza firist, kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.
42Game da rabi na mutanen Isra'ila waɗanda Musa ya karɓa daga sojojin da suka tafi yaƙi -43rabi na mutane kuwa, tumaki 337,500 ne,44shanu dubu sittin ne,45jakai 30,500 ne,46mata kuma dubu sha shida.
47Daga cikin rabi na mutanen Isra'ila, Musa ya ɗauki ɗaya daga kowanne hamsin, da na mutane da kuma dabbobi. Ya bayar da su ga Lebiyawa waɗanda ke lura da mazaunin Yahweh, kamar yadda Yahweh ya umarce shi ya yi.
48Sai shugabannin runduna, da na dubu dubu da kuma na bisa ɗari ɗari, suka zo wurin Musa.49Suka ce masa, "Bayinka sun lisafta sojojin dake a ƙarƙashinsu, kuma babu mutum ɗaya da ya ɓace.
50Mun kawo baiko na Yahweh, abin da kowanne mutum ya samu, kayayyakin ado na zinariya, ƙarafu na ƙafa da na hannu, zoben hannu, da zoben kunne, da kayan ado na wuya, domin a yi kafara domin mu kanmu a gaban Yahweh."51Sai Musa da Eliyeza firist suka karɓa daga garesu zinariyar da dukkan kayayyaki na aikin gwaninta.
52Dukkan baiko na zinariya da suka miƙa ga Yahweh - baye-baye daga shugabanni na dubbai daga kuma shugabanni na ɗari ɗari - an auna shekel 16,750.53Kowanne soja ya ɗauki ganima, kowanne mutum domin kansa.54Musa da Eliyeza firist suka karɓi zinariyar daga shugabanni na dubbai da na ɗari ɗari. Suka kai zuwa cikin alfarwa ta taruwa domin tunawa ta mutanen Isra'ila ga Yahweh.

32

1A wannan lokacin zuriyar Ruben da ta Gad suna da garkunan shanu masu yawan gaske. Da suka lura cewa ƙasar Yaza da Giliyad, ƙasa ce mai kyaun gaske domin kiwon shanu.2Saboda haka zuriyar Gad da ta Ruben suka zo suka yiwa Musa magana, ga Eliyeza firist, ga kuma shugabannin jama'a. Suka ce,3"Ga lissafin wuraren da muka yi bincike: Atarot, Dibon, Yaza, Nimra, da Heshbon, Eliyele, Sebam, Nebo, da kuma Beyon.

4Waɗannan su ne ƙasashen da Yahweh ya yaƙa a gaban shugabannin Isra'ila, kuma suna da kyau domin kiwon shanu. Mu, bayinka muna da shanu masu yawa."5Suka ce, "Idan mun sami tagomashi a wurinka, bari a bamu wannan ƙasa, mu bayinka, abin mallaka. Kada a ƙetare Yodan da mu."
6Sai Musa ya amsa wa zuriyar Gad da ta Ruben, "To 'yan'uwanku sun tafi yaƙi, ku kuma kwa zauna a nan?7Don me kuke karya zuciyar mutanen Isra'ila daga shiga cikin ƙasar alƙawarin da Yahweh ya ba su?
8Haka ubanninku suka yi sa'ad da na aike su daga Kadesh Barniya su yi duban ƙasa.9Suka tafi zuwa kwarin Eshkol. Suka ga ƙasar amma suka karya zukatan mutanen Isra'ila har da ba su yarda su shiga ƙasar da Yahweh ya basu ba.
10Fushin Yahweh ya yi ƙuna a wannan rana. Ya kuma yi rantsuwa ya ce,11'Hakika babu wani daga cikin mazajen da suka fito daga cikin Masar, daga mai shekara ashirin da fiye da haka, da zai ga ƙasa wadda na yiwa Ibrahim, da Yakubu, da Ishaku alƙawari, domin basu bi ni da dukkan yadda ya kamata ba, sai dai12Kaleb ɗan Yefunne Bakeniziye, da kuma Yoshuwa ɗan Nun. Kaleb da Yoshuwa kaɗai suka bi ni yadda ya kamata.'
13Fushin Yahweh kuma ya yi ƙuna a bisa Isra'ila. Ya sa suka yi watangaririya a cikin jeji na tsawon shekaru arba'in har sai da wannan tsãra ta waɗanda suka aikata wannan mugunta a fuskarsa suka hallaka.14Duba, kun tashi a cikin mazaunin ubanninku, haka kuma kuke mazaje masu zunubi, domin ku daɗa fushin Allah mai ƙuna gãba da Isra'ila.15Idan kuka juya daga binsa, shi kuma zai ƙara barinsu a cikin jeji, ku kuma da kun gama hallaka dukkan mutanen nan."
16Sai suka zo wurin Musa suka kuma ce, "Ka barmu mu gina ganuwa ta shimge a nan domin dabbobinmu da kuma birane domin iyalanmu.17Duk da haka, mu da kanmu za mu shirya mu ɗauki makamai mu tafi tare da rundunar Isra'ila har sai mun tafi da su zuwa wurarensu. Amma iyalanmu za su zauna a birane masu ganuwa saboda sauran mutanen dake zama cikin ƙasar.
18Ba zamu dawo ba har sai dukkan mutanen Isra'ila kowa ya karɓi gãdonsa.19Ba zamu ci gãdon ƙasan tare da su a ƙetaren Yodan ba, domin gãdonmu na a nan yamma da Yodan."
20Sai Musa ya amsa masu, "Idan kuka yi abin da kuka faɗa, idan kuka ɗauki makamai don ku wuce gaban Yahweh don yaƙi,21don haka kowanne mutum daga cikin mayaƙanku za shi ƙetare Yodan a gaban Yahweh, har sai ya kori maƙiyansa daga gabansa,22ƙasar kuma a ci mulkinta a gabansa. Sa'an nan daga baya ku komo. Za ku zama marasa laifi a gaban Yahweh da kuma wurin Isra'ila. Wannan ƙasa za ta zama abin mallaka a gaban Yahweh.
23Amma idan ba ku yi haka ba, duba, da ko za ku yi wa Yahweh zunubi. Ku kuma san da cewa lallai za a bayyana zunubinku a fili.24Ku gina birane domin iyalanku, shimgayen kuwa domin dabbobinku; sai ku yi abin da kuka faɗi."25Sai zuriyar Gad da na Ruben suka yi magana da Musa suka kuma ce, "Bayinka za su yi kamar yadda kai, shugabanmu, ka umarta.
26Da ƙanananmu, da matayenmu, da garkunan tumakinmu, da dukkan shanunmu za su zauna can cikin biranen Giliyad.27Amma, mu, bayinka, za mu ƙetare a gaban Yahweh zuwa ga yaƙi, kowanne mutum a shirye domin yaƙi, yadda kai, ubangidanmu, ka faɗi."
28Don haka sai Musa ya yi umarni game da su zuwa ga Eliyeza firist, zuwa ga Yoshuwa ɗan Nun, da kuma zuwa ga shugabanni na ubannin kabilun mutanen Isra'ila.29Musa yace masu, "Idan zuriyar Gad da na Ruben suka ƙetare Yodan tare da ku, kowanne mutum da ya yi shirin yaƙi a gaban Yahweh, idan kuwa aka sarayyar da ƙasar a gabanku, to, sai ku ba su ƙasar Giliyad abin mallaka.30Amma idan har basu ƙetare da ku da shirin yaƙi ba, don haka za su sami ta su mallakar tare da ku a cikin ƙasar Kan'ana."
31Sai zuriyar Gad da ta Ruben suka amsa suka ce, "Kamar yadda Yahweh ya faɗa mana, mu bayinka, wannan ita za mu yi.32Za mu ƙetare da shirin yaƙi a gaban Yahweh zuwa cikin ƙasar Kan'ana, amma namu gãdon mallakar za su zauna da mu a wannan sashe na Yodan."
33Don haka ga zuriyar Gad da na Ruben, da kuma ga rabin kabilar Manasse ɗan Yosef, Musa ya ba su masarautar Sihon, sarkin Amoriyawa, da na Og, sarkin Bashan. Ya ba su ƙasar, ya kuma raba masu dukkan biranenta da iyakokinta, da biranen dake kewaye da su.
34Sai zuriyar Gad suka sãke gina Dibon, Atarot, Arowa,35da Atrot Shofan, Yaza, Yogbeha,36Bet Nimra, da Bet Haran birane masu ganuwa da shimgaye domin tumaki.
37Zuriyar Ruben kuma suka gina Heshbon, da Eleyale, da Kiriyatayim,38da Nebo, da Ba'al Meyon - daga baya aka canza sunayensu, da kuma Sibma. Suka bada wasu sunaye ga biranen da suka sãke ginawa.39Zuriyar Makir ɗan Manasse ya tashi ya tafi Giliyad, ya kuma ɗauke ta daga Amoriyawa waɗanda ke cikinta.
40Sai Musa ya bãda Gilyad ga Makir ɗan Manasse, mutanen sa kuma suka zauna nan.41Yayir ɗan Manasse ya tashi ya tafi ya ci garuruwanta, ya kuma kira su da suna Habbot Yayir.42Noba ya tafi ya kuma cinye Kenat da kauyukanta, ya kuma kirata da suna Noba, bisa ga sunansa.

33

1Waɗannan su ne zangon mutanen Isra'ila bayan da suka bar ƙasar Masar da runduna bayan runduna a ƙarƙashin shugabancin Musa da Haruna.2Musa ya rubuta duk inda suka baro da inda suke kaiwa, yadda Yahweh ya umarta. Ga yadda zangon suka kasance, tashi bayan tashi.

3Suka yi tafiya daga Ramesis cikin wata na farko, da suka taso a rana ta sha biyar ga wata na farko. Da safe bayan Bikin ‌Ƙetarewa, sai mutanen Isra'ila suka fito a fili, dukkan Masarawa na gani.4Wannan ya faru ne sa'ad da Masarawa ke binne dukkan 'ya'yan farinsu matattu, waɗanda Yahweh ya kashe a cikinsu, gama ya kawo hukunci a bisa allolinsu.
5Sai mutanen Isra'ila suka tashi daga Ramesis suka kuma yi zango a Sukkot.6Suka tashi daga Sukkot suka yi zango a Etam, a gacin jejin.7Suka tashi daga Etam suka juya baya zuwa Fi Hahirot, wadda take kallon Ba'al Zefon, inda suka yi zango fuska da fuskar Migdol.
8Sai suka shirya tashi domi tafiya daga gaban Fi Hahirot suka kuma wuce ta tsakiyar teku zuwa cikin jeji. Sun yi tafiyar kwana uku zuwa cikin jejin Etam suka kuma yi zango a Mara.9Suka shirya tafiya daga Mara suka kuma isa Elim. A Elim inda akwai maɓulɓulan ruwa da kuma itatuwan dabino. A nan ne suka kafa zango.10Sai suka tashi daga Elim suka kafa zango a bakin Tekun Iwa.
11Sai suka tashi daga bakin Tekun Iwa suka yi zango a cikin jejin Sin.12Suka tashi daga jejin Sin suka yi zango a Dofka.13Suka tashi daga Dofka suka kuma yi zango a Alush.14Suka tashi daga Alush suka yi zango a Refidim, inda ba a sami ruwan da mutane zasu sha ba.
15Suka tashi daga Rafidim suka yi zango a cikin jejin Sinai.16Suka tashi daga jejin Sinai suka kuma yi zango a Kibrot Hattaba.17Suka tashi daga Kibrot Hattaba suka yi zango a Hazerot.18Suka tashi daga Hazerot suka kuma yi zango a Ritma.
19Suka tashi daga Ritma suka kuma yi zango a Rimmon Ferez.20Su ka tashi daga Rimmon Ferez suka kuma yi zango a Libna.21Suka tashi daga Libna suka kuma yi zango a Rissa.22Suka tashi daga Rissa suka kuma yi zango a Kehelata.
23Suka tashi daga Kehelata suka kuma yi zango a Tsaunin Shefa.24Suka tashi daga Tsaunin Shafa suka yi zango a Harada.25Suka tashi daga Harada suka kuma yi zango a Makhelot.26Suka tashi daga Makhelot suka yi zango a Tahat.
27Suka tashi daga Tahat suka kuma yi zango a Tera.28Suka tashi daga Tera suka kuma yi zango a Mitka.29Suka tashi daga Mitka suka kuma yi zango a Hashmona.30Suka tashi daga Hashmona suka kuma yi zango a Moserot.
31Suka tashi daga Moserot suka kuma yi zango a Bene Ya'akan.32Suka tashi daga Bene Ya'akan suka kuma yi zango a Hor Haggidgad.33Suka tashi daga Hor Haggidgad suka kuma yi zango a Yotbata.34Suka tashi daga Yotbata suka kuma yi zango a Abrona.
35Suka tashi daga Abrona suka kuma yi zango a Ezion Geba.36Suka tashi daga Ezion Geba suka kuma yi zango a cikin jejin Zin a Kadesh.37Suka tashi daga Kadesh suka kuma yi zango a Tsaunin Hor, a bakin iyakar ƙasar Idom.
38Sai Haruna firist ya haura bisa Tsaunin Hor ga umarnin Yahweh ya kuma mutu can a cikin shekara ta arba'in bayan da mutanen Isra'ila suka fito daga ƙasar Masar, a cikin wata na biyar, a rana ta farko ga watan.39Haruna na da shekaru 123 lokacin da ya mutu a Tsaunin Hor.
40Sarkin Arad, Bakan'ane, wanda ke zama cikin kudancin jeji a ƙasar Kan'ana, ya ji game da isowar mutanen Isra'ila.
41Suka tashi daga Tsaunin Hor suka kuma yi zango a Zalmona.42Suka tashi daga Zalmona suka kuma yi zango a Funon.43Suka tashi daga Funon suka kuma yi zango a Obot.
44Suka tashi daga Obot suka kuma yi zango a Iye Abarim, a bakin iyakar Mowab.45Suka tashi daga Iye Abarim suka kuma yi zango a Dibon Gad.46Suka tashi daga Dibon Gad suka kuma yi zango a Almon Diblatayim.
47Suka tashi daga Almon Diblatayim suka kuma yi zango a cikin duwatsu na Abarim, fuska da Nebo.48Suka tashi daga duwatsun na Abarim suka kuma yi zango a cikin kwarrurukan Mowab a bakin Yordnn a Yeriko.49Suka yi zango a bakin Yodan, daga Bet Yeshimot zuwa Abel Shittim cikin filayen Mowab.
50Yahweh ya yi magana da Musa a cikin filayen Mowab a bakin Yodan a Yeriko ya kuma ce,51"Ka yi magana da 'ya'yan Isra'ila ka kuma ce masu, 'Yayin da kuka ƙetare Yodan zuwa cikin ƙasar Kan'ana,52dole ne ku kori dukkan mazauna ƙasar daga gareku. Dole ku hallakar da dukkan sassaƙaƙƙun siffofinsu. Dole ku hallakar da siffofinsu na zubi ku kuma farfasa dukkan tuddan wurarensu.
53Dole ku mallaki ƙasar ku kuma zauna cikinta, domi na baku ƙasar abin mallaka.54Dole ne ku yi gãdon ƙasar yanki-yanki, bisa ga kowacce kabila. Dole ne ku bada yanki mai girma zuwa kabilar da tafi kowacce kabila, ga kabila mafi ƙanƙata kuwa ƙaramin yankin ƙasar. Duk sa'ad da yankin ya fãɗa ga kowacce kabila, wannan ƙasa zata zama tata. Za ku gãji ƙasar bisa ga kabilar ubanninku.
55Amma idan baku kori mazaunan ƙasar a gaban ku ba, sa'an nan mutanen da kuka bari su tsaya, za su zama maku kamar wani abu cikin idanunku da kuma ƙaya a kwiɓinku. Za su wahalshe da rayukanku cikin ƙasar da kuka zauna.56Sa'an nan zai zama kuma duk abin da na yi niyyar yi wa waɗannan mutanen, zan yi maku shi."'

34

1Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,2"Ka umarci mutanen Isra'ila ka kuma ce ma su, 'Sa'ad da kuka shiga cikin ƙasar Kan'ana, ƙasar da zata zama taku, ƙasar Kan'ana da iyakokinta,3iyakarku daga yamma zata kai har cikin jejin Zin kusa da iyakar Idom. Gabashin ƙarshe na yamma za shi zama kan layin da ya kai ƙarshe a yammancin ƙarshe na Tekun Gishiri.

4Iyakarku zata juya zuwa yamma daga dutsen Akrabbim ta wuce ta jejin Zin. Daga nan, zata tashi zuwa gabas da Kadesh Baniya har ta kai Harza Adda zuwa ga Azmon.5Daga nan, iyakar zata juya daga Azmon zuwa wajen rafin Masar ta kuma bi zuwa teku.
6Iyaka ta Kudu za ta zama kan iyakar Babban Teku. Wannan zai zama iyaka gareku ta yammanci.
7Iyakarku ta Arewa zata tashi daga kan layin da zaku sa alama daga Babban Teku zuwa Tsaunin Hor,8daga Tsaunin Hor zuwa Lebo Hamat, daga nan zuwa Zedad.9Daga nan iyakar zata ci gaba zuwa Zifuron ta tsaya a Hazar Enan. Wannan zata zama iyakarku ta arewa.
10Zaku saka alama mai nuna iyakarku ta gabas daga Hazar Enan kudu da Shefam.11Daga nan iyaka ta gabas za ta kai daga Shefam zuwa Ribla, gabas da Ain. Iyakar za ta gangaro ta wajen gabas gefen Teku na Kinneret.12Iyakar kuma za ta gangaro zuwa ga Kogin Yodan zuwa ga Tekun Gishiri ta kuma gangaro zuwa iyaka ta gabashin Tekun Gishiri. Wannan za ta zama ƙasarku, da dukkan iyakokinta dake zagaye da ita.
13Sai Musa ya umarci mutanen Isra'ila ya ce, "Wannan ce ƙasar da zaku yi gãdonta ta wurin rabo, wanda Yahweh ya umarta a bayar ga sauran kabilu tãre da kuma rabin kabilar.14Kabila ta zuriyar Ruben, bisa ga rabon gãdo ga ubannin kabilunsu, da kuma kabila ta zuriyar Gad, bisa ga rabon gãdo ga ubannin kabilunsu, da kuma rabin kabilar Manasse dukkansu suka karɓi tasu ƙasar.15Kabilun biyu da kuma rabin kabilar suka karɓi tasu gãdon na ƙasar a ƙetaren Yodan a sashen Gabashin Yeriko, wajen fitar rana."
16Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,17"Ga sunayen mazajen da zasu raba maku ƙasar domin gãdonku: Eliyeza firist da kuma Yoshuwa ɗan Nun.18Za ku zaɓi shugaba daga kowanne kabila don ya raba ƙasar domin zuriyarsu.
19Ga sunayen mazajen: Daga kabilar Yahuda, Kaleb ɗan Yefunne.20Daga kabilar zuriyar Simiyon, Shemuwel ɗan Ammihud.
21Daga kabilar Benyamin, Elidad ɗan Kislon.22Daga kabila ta zuriyar Dan aka sami shugaba, Bukki ɗan Yogli.23Daga cikin zuriyar Yosef, daga kabila ta zuriyar Manasse shugaba, Hanniyel ɗan Efod.
24Daga kabila ta zuriyar Ifraim aka sami shugaba, Kemuwel ɗan Shiftan.25Daga kabila ta zuriyar Zebulun aka sami shugaba, Elizafan ɗan Farnak.26Daga kabila ta zuriyar Issaka aka sami shugaba, Faltiyel ɗan Azzan.
27Daga kabila ta zuriyar Asha aka sami shugaba, Ahihu ɗan Shelomi.28Daga kabila ta zuriyar Naftali aka sami shugaba, Fedahel ɗan Ammihud."29Yahweh ya umarci waɗannan mutanen su raba ƙasar Kan'ana su kuma raba wa kowanne kabila na Isra'ila gãdonsu.

35

1Yahweh ya yi magana da Musa a kwarin Mowab kusa da Yodan a Yeriko ya kuma ce,2"Ka umarci jama'ar Isra'ila su baiwa Lebiyawa kaɗan daga gãdonsu na ƙasar. Zasu basu birane su zauna ciki da kuma wuraren kiwo zagaye da waɗannan birane.

3Su Lebiyawan zasu sami waɗannan biranen su zauna a ciki. Wuraren kiwon za su zama domin garkunansu na shanu, da na tumaki, da na dukkan dabbobinsu.4Wuraren kiwon zagaye da birnin da zaku baiwa Lebiyawan zai tashi daga bangon birnin kãmu dubu ɗaya a kowanne sashi.
5Dole ka auna kãmu dubu biyu daga wajen birnin a sashen gabas, kãmu dubu biyu zuwa sashen kudu, kãmu dubu biyu zuwa sashen yamma, kãmu dubu biyu kuma zuwa ga sashen arewa. Wannan za shi zama wuraren kiwo domin biranensu. Biranen zasu kasance a tsakiya.
6Birane shida da zaku ba Lebiyawa zasu zama biranen mafaka. Zaku ku yi tanadin waɗannan wurare domin duk wanda ya kashe wani na iya guduwa can. Haka kuma za ku yi tanadin wasu birane arba'in da takwas.7Biranen da zaku bai wa Lebiyawa gaba ɗaya zai zama arba'in da takwas. Dole ku basu tare da wuraren kiwonsu.
8Manyan kabilu na jama'ar Isra'ila, kabilar da take da yawan ƙasa, zata tanada birane fiye da kowa. 'Yar ƙaramar kabila kuwa zata tanadi birane kaɗan. Kowacce kabila zata tanada wa Lebiyawa dai-dai bisa ga gãdon da ta karɓa.
9Sai Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,10"Ka yi magana da 'ya'yan Isra'ila ka ce masu, 'Idan kuka ƙetare Yodan zuwa ƙasar Kan'ana,11sa'an nan zaku zaɓi birane su zama biranen mafaka dominku, wurin da idan mutum ya kashe wani ba da gangan ba, yana iya guduwa can.
12Waɗannan biranen zasu zama mafakarku daga mai ramako, domin kada a kashe mai kisa ba tare da ya gurfana gaban shari'a a gaban jama'ar ba.13Za ku zaɓi birane shida a matsayin birnin mafaka.
14Dole ku shirya birane uku a ƙetaren Yodan, uku kuma a cikin ƙasar Kan'ana. Za su zama birane na mafaka.15Domin jama'ar Isra'ila, domin baƙi, domin kowanne mai zama tare da ku, waɗannan birane shida zasu zama maku mafaka ga duk wanda ya kashe wani ba da gangan ba yana iya gudu can.
16Amma idan mutumin mai kisan ya bugi wani da ƙarfe, idan kuma mutumin ya mutu, to mutumin tabbas mai kisan kai ne. Lallai dole a kashe shi.17Idan wani mutum ya bugi wani da dutse cikin hannunsa dake iya kashe wani, idan kuma mutumin ya mutu, to tabbas wannan mutumin mai kisan kai ne. Lallai dole a kashe shi.18Idan mutum mai kisa ya bugi wani mutum da makami na sanda dake iya kashe wani mutumin, idan kuma mutumin ya mutu, to tabbas wannan mutumin mai kisan kai ne. Lallai dole a kashe shi.
19Mai ramakon jini zai kashe mai kisan. Idan ya same shi, mai ramakon jini sai ya kashe shi.20Idan ya bugi wani da ƙiyayya ko ya wurga masa wani abu, yayin da yake ɓuya domin ya yi masa kwanto, har mutumin ya mutu,21ko idan ya buge shi ƙasa da ƙiyayya da hannunsa har mutumin ya mutu, to mai kisan da ya buge shi dole za a kashe shi. Shi mai kisan kai ne. Mai ramakon jini na iya kashe mai kisan kan idan ya gãmu da shi.
22Amma idan mutumin mai kisan ya bugi wani nan da nan ba tare da ya shirya ƙiyayya ko ya wurga wani abin da ya buge shi ba tare da ya yi niyar yin hakan ba23ko ya wurga dutsen dake iya kashe shi ba tare da ya gan shi ba, don haka mai kisan bai zama maƙiyin sa ba; ba ƙoƙarin cutar da mutumin ya yi ba. Amma ga abin da za a yi idan mutumin ya mutu har wa yau.
24Idan haka ne, jama'ar zasu yi shari'a tsakanin mai kisan da mai ramakon jinin da waɗannan sharuɗa.25Jama'ar zasu kuɓutar da mai kisan daga ikon mai ramakon jinin. Su jama'ar zasu komo da mai kisan kan zuwa birnin ramakon wanda asali ya guje daga gare shi. Za ya zauna a wurin har sai bayan mutuwar babban firist, wanda aka shafe da mai mai-tsarki.
26Amma idan mai kisan ya fita daga iyakar birnin mafakan da ya gudu zuwa gare ta,27idan kuma mai ramakon jini ya gamu da shi a wajen iyakar birninsa na mafaka, idan kuma ya kashe mutumin mai kisan, mai ramakon jini ba zai zama mai laifi game da kisan kai ba.28Dalili kuwa shi ne mutumin mai kisan kai da bai fito daga cikin birnin mafaka ba har sai babban firist ya mutu. Bayan mutuwar babban firist, mai kisan kan na iya komawa ƙasarsa inda gãdonsa yake.
29Waɗannan dokokin zasu zama maku farillai dominku cikin dukkan tsararrakin mutanenku a dukkan inda kuka zauna.30Duk wanda ya kashe wani, za a kashe mai kisan, kamar yadda aka yi shaida daga shaidu. Amma shaidar mutum ɗaya baza ta iya sa a kashe mutum ba.
31Haka kuma, ba zaku karbi ɗiyya domin ran mai kisa wanda aka iske shi da laifin kisa ba. Dole a kashe shi.32Ba zaku karbi ɗiyya domin wanda ya gudu zuwa birnin mafaka ba. Da haka ba zaku yardar ma sa ya zauna bisa gãdonsa ba har sai babban firist ya mutu.
33Kada ku ƙazantar da wannan ƙasar da kuke zama a cikinta ta yin haka, gama jinin da aka zubar ta hanyar kisa na ƙazantar da ƙasa. Babu kafarar da za a iya yi domin ƙasar yayin da aka zubar da jini bisanta, sai dai da jinin shi wanda ya zubas da jinin.34Don haka baza ku ƙazantar da ƙasar da kuke zama cikinta ba domni ina zama cikinta. Ni, Yahweh, ina zaune cikin mutanen Isra'ila."'

36

1Sa'an nan shugabanni na gidajen kakannin iyalai na zuriyar Giliyad ɗan Makir (wanda shi ne ɗan Manasse), waɗanda suke daga zuriyar Yusufu, suka iso suka yi magana da Musa da a gaban shugabanni waɗanda ke kan gaba daga gidajen kakanni na mutanen Isra'ila.2Suka ce, "Yahweh ya umarce ka, ubangidanmu, ka bada rabon ƙasa bisa ga ƙuri'a ga mutanen Isra'ila. Yahweh ya umarce ka da ka bada rabon Zelofehad ɗan'uwanmu ga 'ya'yansa mata.

3Amma idan 'ya'yansa mata suka yi aure zuwa wata ƙabilar mutanen Isra'ila, sai gãdonsu na ƙasa a cire daga gãdon dake na ubanninmu. Za a ƙara bisa gãdon dake na ƙabilar da dã suka shiga. Don haka, za a cire daga namu gãdon.4Don haka, idan shekarar Yubili na mutanen Isra'ila ta zo, sai a harɗa gãdonsu da gãdon kabilar da suka yi aure. Ta haka, za a cire gãdonsu daga gãdon kabilar kakanninmu."
5Sai Musa ya ba da umarni ga mutanen Isra'ila, bisa ga maganar Yahweh. Ya ce, "Abin da kabilar zuriyar Yosef suka ce dai-dai ne.6Wannan ne abin da Yahweh ya faɗa game da 'ya'ya mata na Zelofehad. Ya ce, 'Bari su auri duk wanda ya yi masu dai-dai, amma dole ne su yi aure daga cikin zuriyar iyalin mahaifinsu.'
7Kada a canza gãdon wata kabilar mutanen Isra'ila zuwa ga wata kabilar. Duk mutumin Isra'ila dole ya ci gaba da zama da nasa gãdo na kabilar ubanninsa.
8Kowacce ɗiya ta mutanen Isra'ila wadda take da gãdo cikin kabilarta za ta auri wani daga zuriyar mahaifinta. Wannan zai zama haka domin dukkan mutanen Isra'ila su ajiye abin gãdonsu daga ubanninsu.9Babu gãdon da za a ɗauka daga kabila ɗaya zuwa wata kabilar. Kowacce kabila ta mutanen Isra'ila za ta riƙe nata abin gãdon.
10Sai 'ya'ya ɗiyan Zelofehad suka aikata kamar yadda Yahweh ya umarce Musa.11Mahal, Tirza, Hogla, Milka, da Nowa, 'ya'ya mata na Zelofehad, suka auri zuriyar Manasse.12Suka yi aure cikin dangin iyalin Manasse ɗan Yosef. Ta haka, gãdonsu ta kasance tare da kabilar da mahaifinsu ya fito.
13Waɗannan su ne umarnai da shari'un da Yahweh ya bai wa mutanen Isra'ila ta bakin Musa a cikin kwarurukan Mowab a bakin Yodan a Yeriko.

Littafin maimaitawar shari'a

1

1Waɗannan ne maganganun da Musa ya gaya wa dukkan Isra'ila a ƙetaren Yodan a cikin jeji, a sararin kwarin Kogin Yodan daura da Suf, tsakanin Faran, da Tofel, da Laban, da Hazerot, da kuma Di Zahab.2Tafiyar kwana sha ɗaya ce daga Horeb ta hanyar Dutsen Seyir zuwa Kadesh Barniya.

3Ya kasance a shekara ta arba'in, a wata na sha ɗaya, a kan ranar farko na watan, Musa ya yi magana da mutanen Isra'ila, yana gaya masu dukkan abin da Yahweh ya umarce shi game da su.4Wannan kuwa bayan da Yahweh ya kai hari ga Sihon sarkin Amoriyawa ne, wanda ke zama a Heshbon, da Og sarkin Bashan, wanda ke zama a Ashtarot a Edrayi.
5A ƙetaren Yodan, ƙasar Mowab, Musa ya fara sanar da waɗannan umarnai, cewa,6"Yahweh Allahnmu ya yi magana da mu a Horeb, cewa, 'Dogon zaman da kuka yi a wannan ƙasar tudu ya isa.
7Ku juya ku kama tafiyarku, ku kuma tafi ƙasar tudu ta Amoriyawa da dukkan wurare kusa da sararin kwarin Kogin Yodan, a cikin ƙasar tudu, a cikin ƙasar kwari, a cikin Negeb, da bakin teku - ƙasar Kan'aniyawa, da cikin Lebanon har ya zuwa babban kogi, wato Yufiretis.8Duba, na sanya ƙasar a gaban ku; ku tafi ciki ku kuma mallaki ƙasar da Yahweh ya rantse wa ubanninku - ga Ibrahim, ga Ishaku, ga kuma Yakubu - ya basu da kuma zuriyarsu a bayansu.'
9Na yi magana da ku a wancan lokacin, cewa, 'Bazan iya ɗaukarku da kaina ni kaɗai ba.10Yahweh Allahnku ya riɓanɓanya ku, kuma, duba, a yau kun riɓanɓanyu kamar taurarin sama.11Bari Yahweh, Allahn ubanninku, ya maida ku fiye da yadda kuke sau dubu, ya kuma albarkace ku, kamar yadda ya yi maku alƙawari!
12Amma ta yaya ni da kaina ni kaɗai zan ɗauki nawayoyinku, karkiyoyinku, da saɓananku?13Ku ɗauki mutane masu hikima, mutane masu fahimta, da mutane masu kyakkyawar shaida daga kowacce kabila, zan kuma sanya su shugabanni a bisan ku.'14Kuka amsa mani kuka ce, ' Abin da ka faɗa ya yi mana kyau mu yi.'
15Sai na ɗauki shugabanni daga cikin kabilunku, mutane masu hikima, mutane kuma masu kyakkyawar shaida, na kuma mai da su shugabanni a bisan ku, hafsoshin dubbai, hafsoshin ɗaruruwa, hafsoshin hamsin-hamsin, hafsoshin goma-goma, da ofisoshi, kabila bayan kabila.16Na umarci alƙalanku a wancan lokaci, cewa, 'Ku saurari saɓanai tsakanin 'yan'uwanku, ku kuma yi hukuncin adalci tsakanin mutum da ɗan'uwansa, da bãre wanda ya ke tare da shi.
17Ba zaku nuna sonkai ga kowa ba a cikin saɓani; zaku saurari ƙarami da babba bai ɗaya. Ba zaku ji tsoron fuskar mutum ba, domin hukuncin na Allah ne. Saɓanin da yafi ƙarfinku, zaku kawo a gare ni, zan kuma saurare shi.'18Na umarce ku a wancan lokaci dukkan abubuwan da zaku yi.
19Muka yi tafiyarmu daga Horeb muka kuma tafi ta cikin dukkan babban jeji da ban razana da kuka gani, a kan hanyarmu ta zuwa ƙasar tudu ta Amoriyawa, kamar yadda Yahweh Allahnmu ya umarce mu; kuma muka zo Kadesh Barniya.
20Na ce maku, 'Kun zo ƙasar tudu ta Amoriyawa, wadda Yahweh Allahnmu ya ke bamu.21Duba, Yahweh Allahnku ya sanya ƙasar a gaban ku; ku tafi, ku mallaketa, kamar yadda Yahweh, Allah na ubanninku, ya faɗi maku; kada ku ji tsoro, ko ku karaya.'
22Kowannenku ya zo gare ni ya kuma ce, 'Bari mu aika da mutane gaba da mu, saboda suyi binciken ƙasar domin mu, su kuma kawo mana magana game da hanyar da zamu bi mu kai hari, game kuma da biranen da zamu je.'23Shawarar ta gamshe ni sosai; na ɗauki mutanenku sha biyu, mutum ɗaya domin kowacce kabila.24Suka juya suka tafi zuwa cikin ƙasar tudu, suka isa kwarin Eshkol, suka kuma yawace shi.
25Suka ɗauko daga cikin amfanin ƙasar a cikin hannuwansu, suka kuma kawo mana. Suka kuma kawo mana magana suka kuma ce, '‌Ƙasa ce mai kyau da Yahweh Allahnmu ya ke bamu.'
26Duk da haka kuka ƙi kai hari, amma kuka yi tawaye gãba da dokar Yahweh Allahnku.27Kuka yi gunaguni a rumfunanku kuka kuma ce, "Saboda Yahweh ya ƙi mu ne ya fito da mu daga ƙasar Masar, ya bayar da mu cikin hannun Amoriyawa su hallaka mu.28Ina zamu iya zuwa yanzu? 'Yan'uwanmu sun sa zuciyarmu ta narke, cewa, 'Waɗannan mutane masu girma ne da tsayi fiye da mu; biranensu kuma manya ne kuma da garu har cikin sammai; bugu da ƙari, munga 'ya'ya maza na Anakim a wurin."'
29Daganan nace maku, 'Kada ku firgita, ko ku ji tsoronsu.30Yahweh Allahnku, wanda ya ke tafiya a gaban ku, zai yi yaƙi domin ku, kamar dukkan abin da ya yi domin ku a Masar, a gaban idanunku,31da kuma a cikin jeji, inda kuka ga yadda Yahweh Allahnku ya ɗauke ku, kamar yadda mutum ke ɗaukar ɗansa, dukkan inda kuka tafi har sai da kuka zo wannan wuri.'
32Amma duk da wannan magana baku gaskata da Yahweh Allahnku ba,33wanda ya tafi a gaban ku a bisa hanya don ya sami wuri domin kuyi sansani, cikin wuta da dare cikin kuma girgije da rana.
34Yahweh ya ji ƙarar maganganunku ya kuma yi fushi; ya yi rantsuwa ya ce,35'Tabbas babu ko ɗaya daga cikin waɗannan mutane na wannan muguwar tsara da zai ga ƙasa mai kyau da na rantse zan ba kakanninku,36sai Kaleb ɗan Yefunne; zai gan ta. A gare shi zan bayar da ƙasar da ya taka akai, ga 'ya'yansa kuma, saboda ya bi Yahweh ɗungum.'
37Sa'an nan Yahweh ya fusata da ni saboda ku, cewa, 'Kai ma baza ka je cikin wurin ba;38Yoshuwa ɗan Nun, wanda ke tsayawa a gaban ka, shi zai je cikin wurin; ka ƙarfafa shi, domin zai bida Isra'ila su gãje ta.
39Haka kuma, ƙananan yaranku, waɗanda kuka ce zasu hallaka, waɗanda a yau basu da sanin nagarta ko mugunta - zasu je cikin wurin. A gare su zan bayar da ita, kuma zasu mallake ta.40Amma game da ku, ku juya ku kama tafiyarku zuwa cikin jeji ta gefen hanyar zuwa Tekun Iwa.'
41Daganan kuka amsa kuka ce mani, 'Mun yi zunubi gãba da Yahweh; zamu tafi mu yi yaƙi, kuma zamu bi dukkan abin da Yahweh Allahnmu ya umarce mu mu yi.' kowanne mutum a cikin ku ya sanya makaman yaƙinsa, kuma kuka shirya ku kai hari ga ƙasar tudu.42Yahweh ya ce mani, 'Ka ce masu, "Kada ku kai hari kuma kada ku yi yaƙi, gama bazan kasance tare da ku ba, kuma zaku sha kaye daga maƙiyanku.'
43Na yi magana da ku ta wannan hanya, amma baku saurara ba. Kuka yi tawaye gãba da dokar Yahweh; kuka kangare kuma kuka kai hari ga ƙasar tudu.44Amma Amoriyawa, waɗanda ke zaune a ƙasar tudu, suka fito gãba da ku kuma suka kore ku kamar zuma, suka kuma mãke ku ƙasa a Seyir, har nesa zuwa Horma.
45Kuka dawo kuma kuka yi kuka a gaban Yahweh; amma Yahweh bai saurari muryarku ba, ko kuma ya kula da ku ba.46Sai kuka dakata a Kadesh na kwanaki da yawa, dukkan kwanakin da kuka dakata a can.

2

1Daga nan muka juya muka ɗauki tafiyarmu ta hanyar cikin jeji ta wajen Tekun Iwa, kamar yadda Yahweh ya yi magana da ni; muka tafi kewaye da Dutsen Seyir na kwanaki da yawa.2Yahweh ya yi magana da ni, cewa,3'Tafiyarku kewaye da wannan dutse ya isa; ku juya arewa.

4Ka umarci mutanen, cewa, "Zaku bi ta cikin kan iyakar 'yan'uwanku, zuriyar Isuwa, waɗanda ke zaune a Seyir; zasu ji tsoronku. Saboda haka ku kiyaye5kada ku yi yaƙi da su, domin ba zan baku ko ɗaya daga cikin ƙasarsu ba, a'a, bama wadda ta isa tafin ƙafarku ya taka ba; gama na bayar da Dutsen Seyir ga Isuwa a matsayin mallaka.
6Za ku sayi abinci daga gare su da kuɗi, domin ku ci; zaku kuma sayi ruwa daga gare su da kuɗi, domin ku sha.7Gama Yahweh ya albarkace ku a cikin dukkan aikin hannunku; ya san tafiyarku cikin wannan babban jeji. Cikin waɗannan shekaru arba'in Yahweh Allahnku yana tare daku, kuma baku rasa komai ba."'
8Sai muka ratsa ta wurin 'yan'uwanmu, zuriyar Isuwa da ke zaune a Seyir, nesa da hanyar Araba, daga Elat daga kuma Eziyon Gebar. Daganan muka juya muka kuma ratsa ta jejin Mowab.
9Yahweh ya ce mani, 'Kada ku matsawa Mowab, kada kuma ku yi faɗa da su a yaƙi. Domin ba zan bayar da ƙasarsa ba a gare ku domin mallakar ku, saboda na bayar da Ar ga zuriyar Lutu, domin mallakar su,'
10(Emiyawa suka yi zama a wurin a dã, mutane manya, masu yawa, masu tsayi kuma kamar Anakimawa;11su kuma waɗannan ana ɗaukar su 'yan Refayim, kamar Anakimawa; amma Mowabawa suna kiransu Emiyawa.
12Horitawa su kuma sun yi zama a Seyir a dã, amma zuriyar Isuwa suka gaje su. Suka hallakar da su a gabansu suka kuma zauna a wurin su, kamar yadda Isra'ila ya yi da ƙasar mallakarsa wadda Yahweh ya basu.)
13Yanzu ku tashi ku tafi tsallaken kwarin Zered.' Sai muka tafi tsallaken rafin Zered.14Yanzu daga kwanakin da muka zo daga Kadesh Barniya har muka ketare rafin Zered, shekaru talatin da takwas ne. A wannan lokacin ne dukkan tsarar mazajen da suka isa yaƙi aka kawar da su daga mutanen, kamar yadda Yahweh ya rantse masu.15Haka nan kuma, hannun Yahweh ya yi gãba da wannan tsara domin a lalatar da su daga mutanen har sai da suka ƙare.
16Sai ya kasance, sa'ad da dukkan mazajen da suka isa yaƙi suka mutu suka kuma ƙare daga cikin mutanen,17sai Yahweh ya yi magana da ni, cewa,18'A yau ne zaku ƙetare Ar, kan iyakar Mowab.19Sa'ad da kuka zo kusa daura da mutanen Ammon, kada ku matsa masu ko ku yi yaƙi da su; gama ba zan baku ko ɗaya daga cikin ƙasar mutanen Ammon ba a matsayin mallaka; saboda na bayar da ita ga zuriyar Lutu a matsayin mallaka."'
20(Wannan ita ma an ɗauke ta ƙasar Refayim. Refayim ne suka yi zama a wurin a dã - amma Ammoniyawa suna kiransu Zamzumiyawa -21mutane manya, masu yawa, masu tsayi kuma kamar Anakimawa. Amma Yahweh ya hallakar da su a gaban Ammoniyawa, suka kuma gaje su suka zauna a wurin su.22Wannan kuma Yahweh ya yi domin mutanen Isuwa, waɗanda ke zaune a Seyir, da ya hallakar da Horinawa a gabansu, zuriyar Isuwa kuma suka gaje su suka zauna a wurin su har ya zuwa yau.
23Amma game da Abibiyawa waɗanda ke zaune a ƙauyuka har nesa zuwa Gaza, Kaftorimawa, waɗanda suka zo daga Kafto, suka hallakar da su suka zauna a wurin su.)
24Yanzu ku tashi, ku kama tafiyarku, ku kuma ratsa ta kwarin Arnon; duba, Na bayar cikin hannunku Sihon Ba'amoriye, sarkin Heshbon, da ƙasarsa. Ku fara mallakarta, ku kuma yi faɗa da shi a yaƙi.25A yau zan fara sanya tsoronku da fargabanku a bisa mutanen da ke dukkan ƙarƙashin sama; zasu ji labari game da ku zasu kuma yi rawar jiki su kuma kasance cikin ƙunci sabili da ku.'
26Na aika da manzanni daga jejin Kedemot ga Sihon, sarkin Heshbon, da maganar salama, cewa,27Bari in ratsa ta cikin ƙasarka; zan bi ta kan titi; bazan juya ko zuwa hannun dama ba ko zuwa na hagu.
28Za ka sayar mani da abinci domin kuɗi, saboda in ci; ka bani ruwa domin kuɗi, saboda in sha; ka dai bar ni kawai in ratsa ta ciki bisa sawaye na;29kamar zuriyar Isuwa da ke zaune a Seyir, da Mowabawa da ke zaune a Ar; har sai na ketare Yodan zuwa cikin ƙasar da Yahweh Allahnmu ya ke bamu.'
30Amma Sihon, sarkin Heshbon, ba zai barmu mu ratsa ta wurinsa ba; domin Yahweh Allahnku ya taurare tunaninsa ya kuma sa zuciyarsa ta kafe, domin ya kayar da shi ta wurin ƙarfinku, wanda yanzu ya yi shi a yau.31Yahweh ya ce mani, 'Duba, Na fara miƙa Sihon da ƙasarsa a gaban ku; ku fara mallakar ta, domin ya zama kun gaji ƙasarsa.'
32Daganan Sihon ya fito gãba da mu, shi da dukkan mutanensa, su yi faɗa a Yahaz.33Yahweh Allahnmu ya bayar da shi a gare mu muka kuma kayar da shi da 'ya'yansa maza da dukkan mutanensa.
34Muka ɗauki dukkan biranensa a wancan lokaci muka kuma hallakar da kowanne birni ɗungum - maza da mata da ƙanana; bamu bar mai tsira ba.35Garken dabbobi ne kawai muka ɗauka a matsayin ganima domin mu, tare da ganimar biranen da muka ɗauka.
36Daga Arowa, wadda ke gefen kwarin Arnon, daga kuma birnin da ke cikin kwarin, dukkan hanya har Giliyad, babu birnin da ya fi ƙarfin mu. Yahweh Allahnmu ya bayar da su cikin hannuwanmu.37‌Ƙasar zuriyar Ammon ce kawai baku je ba, har ma dukkan gefen kogin Yabbok, da biranen ƙasar tudu - kowanne wurin da Yahweh Allahnmu ya hana mu zuwa.

3

1Daga nan muka juya muka tafi hanyar Bashan. Og, sarkin Bashan, yazo kuma ya kawo mana hari, shi da dukkan mutanensa, ya yi faɗa a Edrai.2Yahweh ya ce mani, "Kada ka ji tsoronsa; gama na baka nasara a kansa kuma na sanya dukkan mutanensa da ƙasarsa a ƙarƙashin mulkinka. Zaka yi masa yadda kayi wa Sihon, sarkin Amoriyawa, wanda ya zauna a Heshbon.'

3Sai Yahweh Allahnmu ya bamu nasara a bisa Og sarkin Bashan, dukkan mutanensa kuma aka sanya su ƙarƙashin mulkinmu. Muka fyaɗe su har ba ko ɗaya daga cikin mutanensa da ya rage.4Muka ɗauki dukkan biranensa a wancan lokaci. Babu ko ɗaya daga cikin biranen nan sittin da bamu karɓe ba daga gare su - dukkan lardin Argob, masarautar Og a Bashan.
5Dukkan waɗannan birane tsararru ne da dogayen ganuwoyi, ƙofofi, da ƙarafuna; waɗannan kuwa baya ga ƙauyuka marasa ganuwa masu yawan gaske.6Muka hallakar da su ɗungum, kamar yadda muka yi da Sihon sarkin Heshbon, muka hallakar da kowanne birni ɗungum - maza da mata da ƙanana.7Amma dukkan garken dabbobin da ganimar biranen, muka ɗauka a matsayin ganima domin mu.
8A wannan lokacin muka ɗauke ƙasar daga hannun sarakunan Amoriyawa biyu, waɗanda ke ƙetaren Yodan, daga kwarin Arnon zuwa dutsen Hamon9(Sidoniyawa na kiran dutsen Hamon Siriyon, Amoriyawa kuma na kiran sa Senir)10da dukkan biranen sarari, dukkan Giliyad, da dukkan Bashan, har ya zuwa Saleka da Edrai, biranen masarautar Og a Bashan."
11(Game da ragowar Refayim, Og sarkin Bashan ne kaɗai ya rage. Duba! gadonsa gadon ƙarfe ne. Ba yana a Rabba ba, inda zuriyar Ammon suka zauna? tsawonsa kamu tara ne fãɗinsa kuma kamu huɗu, bisa ga yadda mutane ke gwaji.)
12Wannan ƙasa muka ɗauka mallaka a wannan lokaci - daga Arowa, wato ta gefen kwarin Arnon, da rabin ƙasar tudu ta Giliyad, da biranenta - Na bayar ga Rubenawa ga kuma Gadanawa.13Sauran Giliyad da dukkan Bashan, masarautar Og, Na bayar ga rabin kabilar Manasse. (Dukkan lardin Argob, da dukkan Bashan. Wannan gundumar ce ake kira ƙasar Refayim.
14Yayir, wata zuriyar Manasse, suka ɗauki dukkan lardin Argob zuwa kan iyakar Geshurawa da Ma'akatawa. Ya kira lardin, wato Bashan, da sunansa, Habbot Yayir, har ya zuwa yau.)
15Na bayar da Giliyad ga Makir.16Ga Rubenawa ga kuma Gadawa na bayar da gunduma daga Giliyad zuwa kwarin Arnon - tsakiyar kwarin shi ne kan iyakar gundumar - zuwa kuma kogin Yabbok, wanda ke kan iyaka tare da zuriyar Ammon.
17Wasu kan iyakokinta kuma su ne sararin kwarin Kogin Yodan, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) zuwa gangarowar Dutsen Fisga maso gabas.
18Na dokace ku a wancan lokaci, cewa, 'Yahweh Allahnku ya baku wannan ƙasa ku mallake ta; ku, dukkan ku mazajen yaƙi, zaku ƙetare shirye da makamai a gaban 'yan'uwanku, mutanen Isra'ila.
19Amma matayenku, da ƙanananku, da garken dabbobinku (nasan kuna da garken dabbobi masu yawa), zasu tsaya a biranen da na baku,20har sai Yahweh ya bayar da hutawa ga 'yan'uwanku, kamar yadda ya yi a gare ku, har su ma sai sun mallaki ƙasar da Yahweh Allahnku ke bayarwa a gare su a ƙetaren Yodan; daganan za ku dawo, kowanne mutum a cikinku, ga kaddararku da na bayar a gare ku.'
21Na dokaci Yoshuwa a wancan lokacin, cewa, 'Idanunka sun ga dukkan abin da Yahweh Allahnka ya yi ga waɗannan sarakuna biyu; Yahweh zai yi irin haka ga dukkan masarautun da za ku je a ƙetare.22Ba za ku ji tsoronsu ba, gama Yahweh Allahnku shi ne zai yi yaƙi dominku.'
23Na yi roƙo da naciya ga Yahweh a wancan lokaci, cewa,24'Ya Ubangiji Yahweh, ka fãra nuna wa bawanka girmanka da ƙarfin hannunka; gama wanne allah ne a sama ko a duniya da zai yi irin ayyukan da ka aiwatar, kuma dai-dai irin manyan ayyukan?25Ka barni in ƙetare, na roƙe ka, in kuma kalli ƙasar mai kyau da ke ƙetaren Yodan, wannan ƙasar tudu mai kyau, da kuma Lebanon.'
26Amma Yahweh ya yi fushi da ni saboda ku; bai saurare ni ba. Yahweh ya ce mani, 'Bari wannan ya ishe ka - kada ka ƙara yi mani magana game da wannan al'amari:27ka hau zuwa ƙwalƙolin Fisga ka kuma ɗaga idanunka zuwa yamma, zuwa arewa, zuwa kudu, da zuwa gabas; ka duba da idanunka, domin ba zaka je ƙetaren Yodan ba.
28A maimakon haka, ka umarci Yoshuwa ya ƙarfafa ka kuma ƙarfafashi, gama zai shiga gaban waɗannan mutane ya ƙetare, zai kuma sa su gãji ƙasar da za ka gani.'29Sai muka tsaya a kwari daura da Bet Feyo.

4

1Yanzu, Isra'ila, ku saurari shari'o'i da dokoki da nake gab da koya maku, ku aikata su; saboda ku rayu ku kuma shiga ku kuma mallaki ƙasar da Yahweh, Allah na ubanninku, ya ke baku.2Ba zaku ƙara bisa ga maganganun dana umarce ku ba, ko kuma ku rage su, saboda ku kiyaye dokokin Yahweh Allahnku wanda na ke gab da umartar ku.

3Idanunku sun ga abin da Yahweh ya yi saboda Ba'al Feyo; domin dukkan mutanen da suka bi Ba'al na Feyo; Yahweh Allahnku ya lalatar da su a tsakaninku.4Amma ku da kuka manne wa Yahweh Allahnku kuna raye a yau, kowannen ku.
5Duba, na koya maku shari'u da dokoki, kamar yadda Yahweh Allahna ya umarce ni, cewa kuyi haka a tsakiyar ƙasa inda kuke tafiya ciki domin ku mallake ta.6Saboda haka ku kiyaye su ku kuma aikata su; domin wannan shi ne hikimarku da fahimtarku a idanun mutanen da zasu ji dukkan waɗannan farillai su kuma ce, 'Tabbas wannan babbar al'umma mutane ne masu hikima da fahimta.'
7Gama wacce al'umma ce da suke da allah da ke kusa da su sosai, kamar yadda Yahweh Allahnmu ya ke a duk sa'ad da muka yi kira a gare shi?8Wacce babbar al'umma ce da ke nan da take da shari'u da dokoki masu adalci sosai kamar dukkan shari'a da nake shiryawa a gaban ku a yau?
9Kawai dai ku lura ku kuma jagoranci kanku a hankali, domin kada ku manta da abin da idanunku suka gani, saboda kada su bar zukatanku domin dukkan kwanakin rayuwarku. A maimakon haka, ku sanar da su ga 'ya'yanku da 'ya'yan 'ya'yanku.10A ranar da kuka tsaya a gaban Yahweh Allahnku a Horeb, sa'ad da Yahweh ya ce mani, 'Ka tattara mani mutanen, zan kuma sa su su ji maganganuna, domin su koyi jin tsorona dukkan kwanakin da suke raye a duniya, domin kuma su koyawa 'ya'yansu.'
11Kuka zo kusa kuka tsaya a gindin dutsen. Dutsen na ƙonewa da wuta har tsakiyar sama, tare da duhu, girgije, da duhu mai kauri.12Yahweh ya yi magana daku daga cikin tsakiyar wuta; kuka ji muryar tare da maganganunta, amma baku ga wata siffa ba; murya kaɗai kuka ji.
13Ya furta maku alƙawarinsa da ya umarceku ku aikata, Dokoki goma. Ya rubuta su a allunan duwatsu biyu.14Yahweh ya dokace ni a wannan lokaci da in koya maku farillai da shari'u, saboda ku aikata su a cikin ƙasar da kuke ƙetarawa ku ɗauki mallaka.
15Saboda haka ku yi hankali da kanku - domin baku ga wata siffa ba a ranar da Yahweh ya yi magana daku a Horeb daga tsakiyar wuta -16domin kada ku lalata kanku ta wurin yin sassaƙaƙƙen siffa bisa ga siffar wani abu, a cikin kamannin namiji ko mace,17a cikin kamannin kowacce irin dabba a duniya, kamannin kowanne irin tsuntsu mai fukafukai da ke shawagi a sammai,18kamannin kowanne irin abu da ke rarrafe a bisa ƙasa, ko kamannin kowanne irin kifi da ke cikin ruwa a ƙarƙashin duniya.
19Ba zaku ɗaga idanunku zuwa sammai ba ku dubi rana, wata, ko taurari ba - dukkan rundunar sammai - kuma ku janye zuwa yi masu sujada ku kuma girmama su - waɗannan abubuwa waɗanda Yahweh Allahnku ya bada kaso ga dukkan mutanen ƙarƙashin sararin sama baki ɗaya.20Amma Yahweh ya ɗauko ku ya kawo ku kuma daga tanderun ƙarfe, daga Masar, ku zama a gare shi mutanen gãdonsa, kamar yadda kuke a yau.
21Yahweh yaji haushina saboda ku; ya yi rantsuwa cewa bazan ƙetare Yodan ba, da cewa kada in tafi cikin wannan ƙasa mai kyau, ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke bayarwa a gare ku a matsayin gãdo.22A maimako, tilas in mutu a wannan ƙasa; tilas ba zan tafi ƙetaren Yodan ba; amma ku zaku ƙetare ku kuma mallaki ƙasar mai kyau.
23Ku lura da kanku, domin kada ku manta da alƙawarin Yahweh Allahnku, wanda ya yi tare daku, ku kuma yi wa kanku sassaƙaƙƙen siffa a cikin siffar wani abu wanda Yahweh Allahnku ya hanaku ku yi.24Gama Yahweh Allahnku wuta ne mai lanƙwamewa, Allah ne mai kishi.
25Sa'ad da kuka haifi 'ya'ya da 'ya'yan 'ya'ya, sa'ad da kuma kuka kasance a ƙasar na dogon lokaci, idan kuma kuka lalata kanku kuka kuma yi wa kanku sassaƙaƙƙen siffa bisa ga siffar kowanne abu, kuka kuma aikata abin da ke na mugunta a idanun Yahweh Allahnku, domin ku tunzura shi zuwa fushi -26na kira sama da duniya suyi shaida gãba da ku a yau cewa ba da daɗewa ba zaku lalace daga ƙasar da kuke ƙetare Yodan domin ku mallaka; ba zaku tsawonta kwanakinku ba a cikin ta, amma ɗungum zaku rushe.
27Yahweh zai warwatsa ku cikin mutane, kuma zaku zama 'yan kaɗan a cikin al'ummai, inda Yahweh zai aika da ku.28A can zaku yi bautar wasu alloli, ayyukan hannuwan mutane, katako da dutse, waɗanda basu gani, ji, ci, ko sunsunawa.
29Amma daga can zaku biɗi Yahweh Allahnku, kuma zaku same shi, sa'ad da kuka neme shi da dukkan zuciyarku da dukkan ranku.
30Sa'ad da kuke cikin ƙunci, sa'ad da kuma dukkan waɗannan abubuwa suka zo kanku, cikin waɗannan kwanakin ƙarshe zaku dawo ga Yahweh Allahnku kuma ku saurari muryarsa.31Gama Yahweh Allahnku Allah ne cike da jinƙai; ba zai gaza maku ba ko ya rusa ku, ko kuwa ya manta da alƙawarin ubanninku wanda ya rantse masu.
32Ku yi tambaya yanzu game da kwanakin da suka wuce, waɗanda suke kafin lokacinku, tun ranar da Allah ya halitta mutum a duniya, ku yi tambaya daga ƙarshen sama zuwa ɗaya ƙarshen sama, ko an taɓa yin wani abu babba kamar wannan, ko an taɓa jin wani abu kamar wannan?33Ko an taɓa yin wasu mutane da suka ji muryar Allah na magana daga cikin wuta, kamar yadda kuka ji, kuka kuma rayu?
34Ko kuwa Allah ya taɓa ɗaukar wani mataki yaje ya ɗaukarwa kansa al'umma daga cikin wata al'ummar, ta wurin gwaje-gwaje, ta wurin alamu, da ta wurin al'ajibai, da ta wurin yaƙi, da ta wurin hannu mai ƙarfi, da ta wurin miƙaƙƙen damtse, da ta wurin babbar razana, kamar dukkan abin da Yahweh Allahnku ya yi domin ku a Masar a gaban idanunku?
35A gare ku aka nuna waɗannan abubuwa, saboda ku sani cewa Yahweh shi ne Allah, kuma da cewa babu wani baya gare shi.36Daga sama ya sa kuka ji muryarsa, saboda ya umarce ku; a duniya ya sa kuka ga babbar wutarsa; kuka ji maganganunsa daga cikin tsakiyar wutar.
37Saboda yana ƙaunar ubanninku, ya zaɓi zuriyarsu bayansu, ya kuma fito daku daga Masar tare da bayyanuwarsa, tare da babban ikonsa;38domin ya kore daga gabanku al'ummai da suka fi ku girma da ƙarfi, saboda ya kawo ku ciki, saboda ya baku ƙasarsu a matsayin gãdo, kamar a yau.
39Saboda haka ku sani a yau, ku kuma ajiye shi a zukatanku, cewa Yahweh shi ne Allah a sama can da duniya a ƙarƙashi; babu wani kuma.40Zaku kiyaye farillansa da dokokinsa waɗanda ya dokace ku a yau, domin lafiya ta tafi tare da ku da 'ya'yanku a bayanku, saboda kuma ku tsawonta kwanakinku a cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku har abada."
41Daganan Musa ya zaɓi birane uku daga sashen gabas da Yodan,42saboda wani yana iya gudu zuwa ɗaya daga cikinsu idan ya kashe wani taliki cikin kuskure, wanda ba maƙiyinsa bane a dã. Ta wurin tserewa zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane, zai iya tsira.43Su ne: Bezar a jeji, ƙasar sarari, domin Rubenawa; Ramot a Giliyad, domin Gadawa; da Golan a Bashan, domin Manasawa.
44Wannan ita ce shari'ar da Musa yasa a gaban mutanen Isra'ila;45waɗannan ne dokokin alƙawari, shari'u, da sauran dokoki daya faɗi ga mutanen Isra'ila sa'ad da suka fito daga Masar,46sa'ad da suke a gabas da Yodan, a kwari daura da Bet Feyo, a ƙasar Sihon, sarkin Amoriyawa, wanda ya zauna a Heshbon, wanda Musa da mutanen Isra'ila suka kayar sa'ad da suka fito daga Masar.
47Suka ɗauki ƙasarsa a matsayin mallaka, da ƙasar Og sarkin Bashan - waɗannan, sarakuna biyu na Amoriyawa, waɗanda ke ƙetaren Yodan zuwa gabas.48Wannan gunduma ta tafi daga Arowa, a gaɓas Kwarin Arnon, zuwa Dutsen Sihiyona (ko Dutsen Hamon),49ya kuma haɗa da dukkan sararin kwarin Kogin Yodan, maso gabas a ƙetaren Yodan, zuwa Tekun Araba, zuwa gangaren Dutsen Fisga.

5

1Musa ya yi kira ga dukkan Isra'ila ya ce masu, "Ku saurara, Isra'ila, ga farillai da dokoki da zan faɗa cikin kunnuwanku a yau, domin ku koye su ku kuma kiyaye su.2Yahweh Allahnmu ya yi alƙawari tare da mu a Horeb.3Yahweh bai yi wannan alƙawari tare da kakanninmu ba, amma tare da mu, dukkan mu da muke a raye a nan a yau.

4Yahweh ya yi magana daku fuska da fuska a dutse daga tsakiyar wuta5(na tsaya tsakanin Yahweh daku a wancan lokaci, in bayyana maku maganarsa; domin kuna jin tsoro saboda wutar, kuma baku hau zuwa tsaunin ba). Yahweh ya ce,6'Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya fito daku daga ƙasar Masar, daga gidan bauta.
7Ba za ku yi wasu alloli ba a gabana.8Ba za kuyi wa kanku sassaƙaƙƙen siffa ba ko kamannin wani irin abu da ke sama can, ko da ke a duniya a ƙasa, ko da ke a cikin ruwa a ƙarƙashi.
9Ba zaku russuna masu ba ko ku bauta masu, domin Ni, Yahweh Allahnku, ni Allah ne mai kishi. Ina hukunta muguntar kakanni ta wurin sauko da hukunci bisa 'ya'yan, har zuwa tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suka ƙi ni,10da nuna alƙawarin aminci ga dubbai, ga waɗanda ke ƙaunata da kiyaye dokokina.
11Ba zaku ɗauki sunan Yahweh Allahnku ba a banza, gama Yahweh ba zai riƙe shi marar laifi ba shi wanda ya ɗauki sunansa a banza.
12Ka lura da ranar Asabaci ka kiyaye ta da tsarki, kamar yadda Yahweh Allahnka ya dokace ka.13Gama cikin kwana shida zaka yi aikin ƙarfi kayi kuma dukkan ayyuka;14amma rana ta bakwai Asabaci ce ga Yahweh Allahnka. A cikin ta ba za ka yi wani aiki ba - ban da kai, ko ɗanka, ko ɗiyarka, ko bawanka, ko baiwarka, ko san ka, ko jakinka, ko wani daga cikin garken dabbobinka, ko wani baƙo daga cikin ƙofofinka. Wannan kuwa haka ne domin bawanka da baiwarka su huta kamar yadda za ka huta.
15Za ka tuna da cewa kaima bawa ne a ƙasar Masar, kuma Yahweh Allahnka ya fito da kai daga can da hannu mai ƙarfi da miƙaƙƙen damtse. Saboda haka Yahweh Allahnka ya dokace ka da ka kiyaye ranar Asabaci.
16Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kamar yadda Yahweh Allahnka ya dokace ka kayi, domin ka zauna na dogon lokaci a cikin ƙasar da Yahweh Allahnka ya ke baka, domin kuma ya kasance lafiya tare da kai.
17Ba za kayi kisa ba.18Ba zaka aikata zina ba.19Ba zaka yi sata ba.20Ba zaka bada shaidar zur ba gãba da maƙwabcinka.
21Ba zaka yi ƙyashin matar maƙwabcinka ba, ba zaka yi ƙyashin gidan maƙwabcinka ba, ko gonarsa, ko bawansa, ko baiwarsa, ko sansa, ko jakinsa, ko wani abu da ke na maƙwabcinka.'
22Waɗannan maganganu Yahweh ya faɗi da babbar murya ga dukkan taronku a bisa dutse daga tsakiyar wuta, daga gizagizai, daga kuma duhu mai kauri; baiyi ƙarin wasu maganganu ba. Ya rubuta su bisa allunan dutse ya kuma bani su.
23Sai ya kasance, da kuka ji muryar daga tsakiyar duhu, yayin da dutsen ke ƙonewa, sai kuka zo kusa da ni - dukkan dattawanku da shugabannin kabilunku.24Kuka ce, 'Duba, Yahweh Allahnmu ya nuna mana ɗaukakarsa da girmansa, kuma mun ji muryarsa daga tsakiyar wuta; mun gani a yau cewa sa'ad da Yahweh ya yi magana da mutane, za su iya rayuwa.
25Amma me yasa zamu mutu? gama wannan babbar wuta zata cinye mu; idan muka ƙara jin muryar Yahweh Allahnmu, zamu mutu.26Gama banda mu wane ne a cikin nama da jini, ya taɓa jin muryar Allah mai rai daga tsakiyar wuta ya kuma rayu, kamar yadda muka yi?27Game da kai, ka tafi ka saurari dukkan abin da Yahweh Allahnmu ya ce; ka maimaita mana dukkan abin da Yahweh Allahnmu ya ce maka; zamu saurara kuma mu yi biyayya.'
28Yahweh yaji maganganunku sa'ad da kuka yi zance da ni. Ya ce mani, 'Na ji maganganun waɗannan mutane, abin da suka ce maka. Abin da suka ce mai kyau ne.29Oh, ace ma akwai irin wannan zuciyar a cikinsu, cewa zasu girmama ni kuma koyaushe zasu kiyaye dokokina, domin ya tafi lafiya tare da su tare kuma da 'ya'yansu har abada!30Ka je kace masu, "Ku koma rumfunanku."
31Amma game da kai, ka tsaya nan gefe na, zan kuma gaya maka dukkan dokokin, farillai, da shari'u da zaka koya masu, saboda su kiyaye su a cikin ƙasar da zan ba su su mallaka.'
32Saboda haka, zaku kiyaye, abin da Yahweh Allahnku ya dokace ku; ba zaku kauce ba zuwa hannun dama ko hagu.33Zaku yi tafiya cikin dukkan hanyoyi da Yahweh Allahnku ya dokace ku, domin ku rayu, domin kuma ya tafi lafiya tare da ku, ku kuma tsawonta kwanakinku a cikin ƙasar da zaku mallaka.

6

1Yanzu waɗannan ne dokoki, da farillai, da kuma shari'un da Yahweh Allahnku ya dokace ni in koya maku, domin ku kiyaye su a cikin ƙasar da kuke tafiya ƙetaren Yodan ku mallaka;2saboda ku iya girmama Yahweh Allahnku, saboda ku kiyaye dukkan farillansa da dokokinsa waɗanda nake dokatarku a yau - ku, da 'ya'yanku, da 'ya'yan 'ya'yanku, dukkan kwanakin rayuwarku, saboda kwanakinku su yi tsawo.

3Saboda haka ku saurare su, Isra'ila, ku kuma kiyaye su, saboda ya tafi lafiya tare daku, saboda ku yi babbar ruɓanɓanya, a cikin ƙasar da ke malalowa da madara da zuma, kamar yadda Yahweh, Allah na ubanninku, ya yi maku alƙawari zai yi.
4Ku saurara, Isra'ila:5Yahweh Allahnmu ɗaya ne. Zaku ƙaunaci Yahweh Allahnku tare da dukkan zuciyarku, tare da dukkan ranku, tare kuma da dukkan ƙarfinku.
6Maganganun da nake umartarku a yau za su kasance a zukatanku;7da ƙwazo kuma zaku koyar da su ga 'ya'yanku; zaku yi magana game da su sa'ad da kuke zaune cikin gida, sa'ad da kuke tafiya akan hanya, sa'ad da kuke kwance, da sa'ad da kuka tashi.
8Za ku ɗaura su a matsayin alama a bisa hannunku, zasu kuma zama kamar 'yan goshi a tsakanin idanunku.9Zaku rubuta su a ginshiƙan gidajenku da ƙofofinku.
10Sa'ad da Yahweh Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da ya yi rantsuwa ga ubanninku, ga Ibrahim, ga Ishaku, ga kuma Yakubu, cewa zai baku, da birane manya-manya kyawawa da baku gina ba,11da gidaje cike da dukkan abubuwa iri-iri masu kyau da baku yi ba, tankunan ruwa da baku gina ba, garkunan inabi da itatuwan zaitun da baku dasa ba, zaku ci ku ƙoshi -12daganan ku lura saboda kada ku manta da Yahweh, wanda ya fito da ku daga ƙasar Masar, daga gidan ƙunci.
13Zaku girmama Yahweh Allahnku; shi ne zaku yi wa sujada, kuma zaku yi rantsuwa da sunansa.14Ba zaku bi waɗansu alloli ba, allolin mutanen da suke kewaye daku kakaf -15domin Yahweh Allahnku da ke tsakiyarku Allah ne mai kishi - idan kuka yi, fushin Yahweh Allahnku zai kunnu gãba daku kuma zai hallakar daku daga fuskar duniya.
16Ba zaku gwada Yahweh Allahnku ba kamar yadda kuka gwada shi a Massa.17Zaku yi ƙwazo ku kiyaye dokokin Yahweh Allahnku, dokokinsa natsastsu, da farillansa, waɗanda ya dokace ku.
18Zaku yi abin da ke dai-dai mai kyau kuma a idanun Yahweh, saboda ya kasance lafiya a gare ku, ku kuma iya zuwa ku mallaki ƙasa mai kyau da Yahweh ya rantse wa ubanninku,19ya kori dukkan maƙiyanku daga gare ku, kamar yadda Yahweh ya faɗa.
20Sa'ad da ɗanku ya tambaye ku a lokaci mai zuwa, cewa, 'Waɗanne ne dokokin alƙawari da farillai da sauran dokoki da Yahweh Allahnmu ya umarce ku?21daganan zaku cewa ɗanku, 'Mu bayin Fir'auna ne a Masar; Yahweh ya fito da mu daga Masar da hannu mai ƙarfi,22ya kuma aiwatar da alamu, da al'ajibai, manya masu tsanani, a bisa Masar, a bisa Fir'auna, a kuma bisa dukkan gidansa, a gaban idanunmu;23ya kuma fito da mu daga wurin, saboda ya kawo mu ciki, ya ba mu ƙasar da ya rantse wa ubanninmu.
24Yahweh ya dokace mu da a koyaushe mu kiyaye waɗannan farillai, mu ji tsoron Yahweh Allahnmu domin kyaunmu, domin ya iya kiyaye mu a raye, kamar yadda muke a yau.25Idan muka kiyaye dukkan waɗannan dokoki a gaban Yahweh Allahnmu, kamar yadda ya dokace mu, wannan ne zai zama adalcinmu.'

7

1Lokacin da Yahweh Allahnku ya kawo ku zuwa ƙasar da kuke shiga domin ku mallake ta, za ya kori al'ummai masu yawa - su Hittiyawa, da Girgashawa da Amoriyawa da Kan'aniyawa, da Feriziyawa, da Hibiyawa da kuma Yebusawa - al'ummai guda bakwai masu girma da ƙarfi fiye da ku.

2Yahweh Allahnku ne ya miƙa su cikin hannunku lokacin da kuka ci su da yaƙi, haka nan kuma dole ne ku hallaka su dukka. Ba zaku ɗauki alƙawari da su ba, kada kuma ku nuna masu jinƙai.3Kada kuma ku shirya aurayya da su. Ba zaku miƙa 'ya'yanku mata aure ga 'ya'yansu maza ba, kuma ba zaku ɗauko 'ya'yansu mata domin 'ya'yanku maza ba.
4Gama zasu juyar da hankalin 'ya'yanku maza daga bina, domin su yi sujada ga wasu alloli. Da haka fushin Yahweh za shi yi ƙuna gãba daku, kuma za ya hallaka ku da sauri.5Ga yadda zaku yi da su: Zaku rushe har ƙasa bagadansu, ku farfashe umudansu, ku datse Asherim da mazamninta, ku kuma ƙone sassaƙaƙƙun siffofinsu.
6Gama ku al'umma ce da aka keɓe ga Yahweh Allahnku. Ya zaɓe ku ku zama mutane domin ya mallaka, gaba da dukkan sauran mutanen da ke fuskar duniya.
7Yahweh bai ɗora ƙaunarsa bisanku ko ya zaɓe ku domin kun fi sauran mutane yawa bane - gama kun zama ƙalilan cikin dukkan mutane -8amma domin ya ƙaunace ku, kuma yana kiyaye alƙawarinsa da ya yi wa ubanninku. Wannan shi ne dalilin da yasa Yahweh ya fito daku da hannu mai girma ya kuma fanshe ku daga gidan bauta, daga hannun Fir'auna, sarkin Masar.
9Saboda haka ku san cewa Yahweh Allahnku - shi ne Allah, Allah mai aminci, mai cika alƙawari da kuma aminci ga dubban tsararraki da waɗanda suke ƙaunarsa suna kuma kiyaye dokokinsa,10amma yana saka wa waɗanda suka ƙi shi a fuskarsu, domin ya hallaka su; ba za ya tausaya wa duk wanda ya ƙi shi ba; zai yi masa sakamako yana ji yana gani.11Don haka zaku kiyaye dokoki, da farillai, da kuma umarnai dana dokace ku yau, domin ku aikata su.
12Idan kuka saurari waɗannan umarnai, kuka kiyaye ku kuma aikata su, za shi zama kuma Yahweh Allahnku za ya kiyaye ku da alƙawari da kuma amincin da ya rantse wa ubanninku.13Za ya ƙaunace ku, ya albarkace ku, ya kuma riɓanɓanya ku; za ya kuma albarkaci 'ya'yan jikinku da kuma na ƙasarku, hatsinku, da sabuwar inabinku, da kuma mai da ke naku, da ƙaruwar garkunanku da 'ya'yan garkunanku, a cikin ƙasan da ya rantse wa ubanninku zai baku.
14Zaku yi albarka fiye da dukkan sauran mutane; ba za a samu bakararre ko bakararriya cikinku ba ko a cikin garkunanku.15Yahweh zai ɗauke dukkan ciwo daga gare ku; babu ko ɗaya daga cikin mugayen cututtuka na Masarawa da kuka sani da zai sa a bisanku, amma zai sa su bisa dukkan waɗanda suka ƙi ku.
16Zaku hallaka dukkan mutanen da Yahweh Allahnku za ya bada su cikin hannunku, kuma idanunku ba zasu tausaya masu ba. Kada ku yi sujada ga allolinsu, gama wannan tarko ne a gare ku.
17Idan kun ce cikin zuciyarku, 'Waɗannan al'ummai sun sha ƙarfinmu da yawa; yaya zan ci ƙarfinsu in kore su?' -18kada ka ji tsoronsu; ka tuna da abin da Yahweh ya yi ma Fir'auna da dukkan Masarawa;19anobai masu girma da idanuwanka suka gani, alamu, da al'ajibai, hannu mai ƙarfi, da kuma miƙaƙƙiyar hannu wadda Yahweh Allahnku ya fito daku. Yahweh zai yi haka kuma ga dukkan mutanen da kuke tsoron su.
20Bayan wannan kuma, Yahweh Allahnku zai aika zirnaƙo a cikinsu, har sai duk waɗanda suka rage da waɗanda suka ɓoye kansu daga gare ku sun hallaka daga fuskarku.21Ba zaku razana ta dalilinsu ba, gama Yahweh Allahnku na cikinku, Allah mai girma mai ban razana.22Yahweh Allahnku zaya kori waɗannan al'ummai daga gabanku kaɗan-kaɗan. Ba zaku iya hallaka su dukka a lokaci ɗaya ba, don kada namomin jeji su yi yawa kewaye daku.
23Amma Yahweh Allahnku zaya baku nasara bisansu sa'ad da kuka gamu da su a dagar yaƙi; za ya rikitar da su matuƙa har sai sun lalace sarai.24Za ya sanya sarakunansu a ƙalƙashin ikonku, kuma zaku sa sunansu ya hallaka daga doron ƙasa. Babu wanda zaya iya tsayayya daku, har sai kun hallaka su sarai.
25Zaku ƙona sassaƙaƙƙun siffofin allolinsu - kada ku yi ƙyashin azurfa ko zinariyar da ta dalaye su ku kuma ɗauke ta domin amfaninku, don in kun yi haka, zai zama tarko gare ku - gama abin kyama ne ga Yahweh Allahnku.26Ba zaku kawo kowanne ƙazamtaccen abu cikin gidanku ba har da zaku yi masa sujada. Amma zaku yi matuƙar ƙyama ku kuma tsane su, gama keɓaɓɓe ne domin hallakarwa.

8

1Dole ku kiyaye dukkan dokokin da nake baku yau, domin ku rayu ku kuma riɓaɓɓanya, ku kuma fita ku mallaki ƙasar da Yahweh ya rantse ga ubanninku.2Zaku tuna da dukkan hanyoyin da Yahweh Allahnku ya bi daku waɗannan shekaru arba'in cikin jeji, domin ya ɗauke girman kai daga gare ku, domin ya gwada ku ya kuma san mene ne ke cikin zuciyarku, ko zaku kiyaye dokokinsa ko a'a.

3Ya ɗauke girman kanku, ya sa kun ji yunwa, ya kuma ciyar daku da manna, wadda ba ku taɓa sani ba wadda kuma ubanninku ba u sani ba. Ya yi haka ne domin ya koya maku da cewa bada gurasa kaɗai mutane ke rayuwa ba; sai dai, ta kowacce abin da ke fitowa daga bakin Yahweh mutane ke rayuwa.
4Tufafinku basu koɗe su kuma faɗi daga jikinku ba, kuma sawayenku basu kumbura cikin shekarun nan arba'in ba.5Zaku yi tunani cikin zuciyarku, ta yaya, kamar yadda mutum ke horon ɗansa, haka Yahweh Allahnku ya ke horonku.6Zaku kiyaye dokokin Yahweh Allahnku, domin ku yi tafiya cikin tafarkunsa ku kuma girmama shi.
7Gama Yahweh Allahnku yana kawo ku zuwa cikin ƙasa mai kyau, ƙasa mai rafuffuka, da ɓulɓulai da zurfafa da masu gangarowa daga tuddai, suna gudu zuwa cikin kwarurrukai da tuddai;8ƙasa mai alkama da bali, na inabi, itacen ɓaure, dana rumana; ƙasar da akwai man zaitun da kuma zuma.
9́‌‌Ƙ‌asa ce inda zaku ci gurasa babu rashi, kuma inda zaku tafi ba da rashin komai ba; ƙasa wadda duwatsunta tama ce, kuma daga cikin tsaunukanta kana iya haƙa jan ƙarfe.10Zaku ci ku kuma ƙoshi, ku kuma albarkaci Yahweh Allahnku domin ƙasa mai kyau da ya baku.
11Ku kula kada ku manta da Yahweh Allahnku, kuma kada kuyi banza da dokokinsa, farillansa, da umurnansa da nake dokace ku yau,12in ba haka ba, lokacin da kuka ci kuka kuma ƙoshi, kuka kuma gina gidaje kuka kuma zauna cikinsu, zuciyarku za ta yi kumburi.
13Ku kula sa'ad da garkunanku na shanu dana tumaki suka ƙaru kuma lokacin da azurfanku da zinariyarku suka ƙaru, da dukkan mallakarku suka yawaita,14sai zuciyarku ta kumbura har ku manta da Yahweh Allahnku, wanda ya fito daku daga ƙasar Masar, daga gidan bauta.
15Kada ku manta da shi wanda ya bishe ku ta cikin jeji babba da mai ban-razana, tare da macizai masu masifa da kunamai da ƙasa mai ƙishi inda babu ruwa, wanda ya fito maku da ruwa daga dutse fa.16Ya ciyas da ku cikin jeji da manna abin da ubanninku basu taɓa sanin ta ba, domin ya ɗauke fahariya daga gare ku ya kuma gwada ku, domin ya yi maku alheri a ƙarshe,17amma zaku ce a zuciyarku, 'Ai ƙarfina ne da ikon hannuna ne suka bani wannan dukkan dukiyar.'
18Amma zaku tuna da Yahweh Allahnku, domin shi ne ke baku iko don ku wadata; domin ya kafa alƙawarinsa da ya yi wa ubanninku, kamar yadda ya ke a yau.19Haka za shi zama, idan zaku manta da Yahweh Allahnku ku kuma bi wasu alloli, kuyi masu sujada, ku kuma girmamasu, nayi shaida gãba daku yau da cewa zaku hallaka.20Kamar al'ummai da Yahweh ke sasu hallaka a gaban ku, haka kuma zaku hallaka, domin kun ƙi ku saurari muryar Yahweh Allahnku.

9

1Ku saurara, Isra'ila; kuna gab da ƙetare Yodan yau, ku shiga ciki ku kaɓantar da al'ummai waɗanda suka fi ku girma da kuma ƙarfi, da kuma birane ƙarfafa da ganuwa na tsaro da ke kaiwa har sama,2mutane masu girma da tsawo, 'ya'yan Anakim, waɗanda kuka sani, kuma waɗanda kuka ji mutane ke cewa game da su, 'Waye zai iya tsayayya da 'ya'yan Anak?'

3Saboda haka yau ku sani cewa Yahweh Allahnku shi ne wanda ya ke tafiya a gabanku kamar wuta mai cinyewa; zaya hallakar da su, kuma zaya ci ƙarfinsu a gabanku; da haka zaku kore su ku kuma sasu hallaka da sauri, kamar yadda Yahweh ya gaya maku.
4Kada ku faɗi a zuciyarku, bayan da Yahweh Allahnku ya ture su waje a gabanku, 'Saboda adalcina ne Yahweh ya kawo ni ciki domin in mallaki wannan ƙasa; gama sabili da muguntar waɗannan al'ummai ne yasa Yahweh ya ke korarsu a gabanku.
5Ba saboda adalcinku ko dai-daituwa ta zuciyarku ne yasa zaku shiga ku mallaki ƙasarsu ba, amma saboda muguntar waɗannan al'ummai ne yasa Allahnku ke koran su waje daga gabanku, kuma domin ya cika maganarsa da ya rantse wa ubanninku, ga Ibarahim, da Ishaku, da kuma Yakubu.
6Don haka ku san cewa, Yahweh Allahnku ba yana baku wannan ƙasa mai kyau domin ku mallake ta don adalcin ku bane, gama ku mutane ne masu taurin zuciya.
7Ku tuna kada kuma ku manta yadda kuka tozarta Yahweh Allahnku ga fushi a cikin jeji; daga ranar da kuka baro ƙasar Masar har kuka iso wannan ƙasa, kun yi ta tayarwa gãba da Yahweh.8Haka ma a Horeb kuka tozarta Yahweh ga fushi, har Yahweh ya yi fushin da har zai iya hallaka ku.
9Da na tafi kan dutsen domin in karɓo allunan dutse, alluna na alƙawarin da Yahweh ya yi da ku, na zauna a dutsen har kwanaki arba'in da dare arba'in; ban ci gurasa ba ban kuma sha ruwa ba.10Yahweh ya ba ni allunan dutse guda biyu da ya yi rubutu da yatsansa; a cikinsu kuma aka rubuta dukkan maganganun da Yahweh ya shaida maku a kan dutse daga cikin tsakiyar wuta a ranan taro.
11Haka ya zama a ƙarshen waɗannan yini arba'in da dare arba'in da Yahweh ya bani allunan duwatsu guda biyu, alluna na alƙawari.12Yahweh ya ce da ni, 'Tashi, sauka ƙasa da sauri daga nan, gama mutanen ka, waɗanda ka fito da su daga Masar, sun ƙazamtar da kansu. Sun yi hamzari daga juyawa daga tafarkin dana dokace su. Sun yi ma kansu sassaƙaƙƙen siffa.'
13Gaba da wannan, Yahweh ya yi mani magana ya ce, 'Na ga waɗannan mutanen; mutane ne masu taurin zuciya.14Ka bar ni, don in hallaka su in shafe sunansu daga ƙarƙashin sama, sai kuma in maishe ka al'umma mafi ƙarfi da girma fiye da su.'
15Sai na juya na kuma sauko daga dutsen, dutsen kuma na ci da wuta. Allunan alƙawari guda biyu a cikin hannuwana.16Sai na duba, ai kuwa, kun rigaya kun saɓa wa Yahweh Allahnku. Kun yi wa kanku siffar gumaka. Kun juya da sauri daga tafarkin da Yahweh ya dokace ku.
17Sai na ɗauko alluna biyun na jefar da su daga hannuwana. Na karya su a idanunku.18Sai na sake kwantawa da fuska a ƙasa a gaban Yahweh yini arba'in da dare arba'in; ban ci ko burodi ko in sha ruwa ba, saboda zunubinku da kuka yi, na aikata abin da ke na mugunta a gaban Yahweh, domin ku tozarta shi ga fushi.
19Gama na ji tsoron fushi da rashin jin daɗi mai zafi irin wadda Yahweh ya yi gãba daku da ya isa har ya hallaka ku. Amma Yahweh ya saurare ni a wannan lokaci kuma.20Yahweh ya yi matuƙar fushi da Haruna har da zai hallaka shi; Na yi ma Haruna addu'a shi ma a wannan sa'a.
21Na ɗauki zunubinku, siffar ɗan maraƙin da kuka yi, na ƙone shi, na tattake shi, na kuma niƙa su gaba ɗaya, har ya zama kamar ƙura. Na zubas da ƙurar cikin rafin da ke gangarowa daga dutsen.
22A Tabera, a Massa, da kuma Kibrot Hatta'aba, kuka cakuni Yahweh ya fusata.23Lokacin da Yahweh ya aike ku daga Kadesh Barniya ya kuma ce, 'Ku haura ku mallaki ƙasar dana rigaya na baku,' sai kuka yi tawaye da dokokin Yahweh Allahnku, baku kuma gaskanta da shi ba koku saurari muryarsa ba.24Kun daɗe kuna tayaswa gãba da Yahweh tun daga ranar dana sanku.
25Sai na faɗi da fuskata ƙasa a gaban Yahweh a waɗannan yini arba'in da dare arba'in, domin ya ce zai hallaka ku.26Na yi addu'a ga Yahweh na kuma ce, 'Ya Ubangiji Yahweh, kada ka hallakar da mutanenka ko abin gãdon ka daka fanshe su ta wurin girmanka, waɗanda ka fitar daga Masar da hannu mai iko.
27Ka tuna da bayinka Ibrahim, da Ishaku, da kuma Yakubu; kada ka kula da taurin kan waɗannan mutane, ba kuma ga muguntarsu ba, ko ga zunubinsu ba,28domin kada ƙasar daka fito da mu su ce, "Domin Yahweh bai iya ya kai su zuwa cikin ƙasar da ya yi alƙawari garesu ba, kuma domin ya ƙisu, sai ya fito da su zuwa jeji domin ya kashe su a nan."29Duk da haka su mutanenka ne da kuma abin gãdonka, wanda ka fito da su da girman ƙarfinka da kuma ta wurin bayyana aikakkiyar ikonka.'

10

1A wannan lokaci Yahweh ya ce da ni, 'Kayi sassakan alluna guda biyu kamar na farko, sai ka hauro wurina kan dutsen, kayi akwatin alƙawari na itace.2Zan yi rubutu a cikin allunan maganganun da suke cikin alluna na farkon daka farfasa, zaka kuma sanya su cikin akwatin.'

3Sai na yi akwatin alƙawari daga itacen maje, sai na sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farkon, sai kuma na haura zuwa saman dutse, riƙe da allunan biyu a hannuna.4ya yi rubutu a bisa allunan, kamar rubutu na farko, Dokoki Goma wanda Yahweh ya yi maku magana a kan dutse daga cikin tsakiyar wuta a ranar taruwa; sai Yahweh ya miƙa mani su.
5Sai na juyo na sauko daga dutsen, na kuma sanya allunan cikin akwatin alƙawarin dana yi; a nan suke, kamar yadda Yahweh ya umarce ni."
6(Jama'ar Isra'la suka yi tafiya daga Birot Bene Ya'akan zuwa Mosera. A nan ne Haruna ya rasu, a nan kuma aka binne shi; Eleyaza, ɗansa, ya yi hidima na firist a matsayinsa.7Daga can suka yi tafiya zuwa Gudgoda, daga Gudgoda kuma zuwa Yotbata, ƙasa mai rafuffuka na ruwa.
8A wannan lokaci sai Yahweh ya zaɓi ƙabilar Lebi don su ɗauki akwatin alƙawari na Yahweh, domin su tsaya a gaban Yahweh su yi masa hidima, su kuma albarkaci mutane a cikin sunansa, kamar yau.9Don haka Lebi ba shi da rabo ko gãdon ƙasa tare da 'yan'uwansa; Yahweh ne gãdonsa, kamar yadda Yahweh Allahnka ya yi masa magana.)
10"Na zauna a kan dutsen kamar yadda nayi da farko, yini arba'in dare arba'in. Yahweh ya saurare ni wannan lokaci kuma; Yahweh ba shi da niyyar hallaka ku.11Yahweh ya ce mani, 'Ka tashi, ka sha gaban mutanen domin ka shugabance su a kan hanyarsu; za su shiga ciki su kuma mallaki ƙasar dana rantse wa ubanninsu in ba su.'
12Yanzu, Isra'ila, mene ne Yahweh Allahnka ke buƙata daga gare ka, sai dai ka ji tsoron Yahweh Allahnka, kayi tafiya cikin dukkan tafarkunsa, ka ƙaunace shi, ka kuma yi sujada ga Yahweh Allahnka da dukkan zuciyarka da kuma dukkan ranka,13don ka kiyaye dokokin Yahweh, da farillansa, waɗanda nake umartan ka yau domin lafiyarka?
14Duba, sama da kuma sama ta sammai na Yahweh Allahnka ne, duniyan, da dukkan abin da ke cikinta.15Yahweh ne kawai ya ji daɗin ubanninku da har ya ƙaunace su, ya kuma zaɓe ku, zuriyarsu, a bayansu, fiye da kowanne sauran mutane, kamar yadda ya ke yi yau.
16Don haka kuyi wa loɓan zuciyarku kachiya, kuma kada ku ƙara taurin kai kuma.17Gama Yahweh Allahnku, shi ne Allahn alloli da kuma Ubangijin iyayengiji, Allah Alƙadiru, mai girma mai bantsoro, wanda baya nuna sonkai baya kuma karɓan toshi.
18Yana aikata adalci domin marayu da gwamraye, kuma yana nuna ƙauna ga wanda ke baƙo ta yadda ya ke ba shi abinci da tufafi.19Saboda haka ka ƙaunaci wanda ya ke baƙo; gama ku da kanku dã baƙi ne a ƙasar Masar.
20Zaka ji tsoron Yahweh Allahnku; shi ne zaka yi masa sujada. Gare shi dole zaka manne, kuma da sunansa zaka yi rantsuwa.21Shi ne yabonka, kuma shi ne Allahnka, wanda ya aikata domin ka waɗannan al'amura masu girma da kuma ban-tsoro, waɗanda idanunku suka gani.
22Ubanninku suka tafi cikin Masar su mutum saba'in ne; yanzu Yahweh Allahnka ya maishe ka dayawa kamar taurarin sammai.

11

1Saboda haka zaka kaunaci Yahweh Allahnka ka kuma kiyaye umarnansa, da farillansa, da shari'unsa, da dokokinsa koyaushe.

2Ku yi la'akari da cewa ba da 'ya'yan ku nake magana ba, waɗanda basu sani ko suka ga hukuncin Yahweh Allahnku, da girmansa, hannunsa mai iko, ko miƙaƙƙiyar zira'assa,3da alamomi da kuma ayyukan da ya yi cikin Masar ga Fir'auna, sarkin Masar, ga kuma dukkan ƙasarsa.
4Ba su kuma ga abin da ya yi wa rundunar Masarawa ba, ko ya yi wa karusansu, yadda ya sa ruwayen Jan Teku suka haɗiye su yayin da suke bin bayansu, da kuma yadda Yahweh ya hallakar da su har wa yau,5ko abin da ya yi maku cikin jeji har kuka zo wannan wuri.
6Ba su ga abin da Yahweh ya yi wa Datan da Abiram, 'ya'yan Eliyab ɗan Ruben ba, yadda ƙasa ta buɗe bakinta ta haɗiye su dukka, da danginsu, da rumfarsu, da kowanne abu mai rai da ya biyo su, a tsakiyar dukkan Isra'ila.7Amma idanunku sun ga dukkan manyan ayyukan Yahweh da ya aiwatar.
8Don haka ku kiyaye dukkan dokokin da nake baku yau, domin ku yi ƙarfi, ku kuma shiga ku mallaki ƙasa inda kuke shigowa don ku mallake ta,9don kuma kwanakinku ya daɗe cikin ƙasar da Yahweh ya rantse wa ubanninku domin ya basu da kuma zuriyarsu, ƙasa mai zubowa da madara da zuma.
10Gama ƙasar, inda kuke shiga don ku mallake ta, ba kamar ƙasar Masar ba ne, inda kuka fito, wurin da kuka yi shukin irinku kuka kuma yi ban-ruwa da kafafunku, kamar lambun baƙulai;11amma ƙasar, da zaku shiga don ku mallake ta, ƙasa ce mai tuddai da kwaruruka, suna kuma shanye ruwan sama na sammai,12ƙasa wacce Yahweh Allahnku ke kula da ita; idanun Yahweh Allahnku na bisan ta koyaushe, daga farkon shekara har zuwa ƙarshen shekara.
13Zai faru haka, idan kuka saurara da aniya ga dokokina da nake dokace ku yau, cewa ku ƙaunaci Yahweh Allahnku ku kuma bauta masa da dukkan zuciyarku da kuma dukkan ranku,14sa'an nan zan bada ruwan sama na ƙasarku a kan lokaci, ruwa na farko dana ƙarshe, domin ku tara hatsinku, da sabuwar inabinku, da kuma manku.15Zan bada ciyawa cikin filayenku domin garkunanku, kuma zaku ci ku kuma ƙoshi.
16Ku lura da kanku don kada a ruɗar da zuciyarku, har da zaku kauce ku yi sujada ga wasu alloli ku kuma russuna masu;17har fushin Yahweh shi yi ƙuna gãba daku; kuma har kada ya kulle sammai da baza a yi ruwan sama ba, kuma ƙasa ta ƙi bada amfaninta, da kuma har ku hallaka da gaggawa daga cikin ƙasa mai kyau da Yahweh ya ke baku.
18Saboda haka ku ajiye waɗannan maganganuna a cikin zuciyarku da ranku, ku ɗaura su kamar alama a hannunku, kuma bari su zama kamar layu a tsakiyar idanunku.19Zaku koyar da su ga 'ya'yanku ku kuma yi zancensu lokacin da kuka zauna a gidanku, sa'ad da kuke tafiya kan hanya, da lokacin da kuke kwance, da kuma sa'ad da kuka tashi.
20Zaku rubuta su kan kofofin gidanku da kuma bisa kofofin biranenku,21don kwanakinku dana 'ya'yanku shi riɓaɓɓanya cikin ƙasar da Yahweh ya rantse wa ubanninku ya ba su har iyakar tsawon yadda sammai ke bisa duniya.
22Domin idan kuka yi himma ga kiyaye dukkan waɗannan dokokin da nake dokatan ku, don ku aikata su, kuna ƙaunar Yahweh Allahnku, kuna tafiya cikin dukkan tafarkunsa, ku kuma manne masa,23sa'annan Yahweh zai kori dukkan waɗannan al'ummai a gabanku, kuma zaku washe al'umman da suka fi ku yawa da kuma ƙarfi.
24Duk inda tafin sawunku zasu taka zasu zama naku; daga jeji zuwa Lebanon, daga kogin, Kogin Yufiretis, zuwa gabashin teku zasu zama iyakarku.25Babu mutumin da za ya iya tsayayya da ku. Yahweh Allahnku zai sa tsoronku da kuma razanarku bisa dukkan ƙasan da kuka taka, kamar yadda ya gaya maku.
26Duba, na sa a gabanku yau albarka da kuma la'ana:27albarkan, idan kuka yi biyayya da dokokin Yahweh Allahnku dana dokace ku yau,28la'anar kuma, idan baku yi biyayya da dokokin Yahweh Allahnku ba, amma kuka juya daga hanyar dana dokace ku yau, don ku bi wasu allolin da baku sani ba.
29Zai zama kuma, sa'ad da Yahweh Allahnku ya kawo ku zuwa ƙasar da kuke shiga domin ku mallake ta, zaku aza albarka bisa Dutsen Gerizim, la'ana kuma a bisa Dutsen Ebal.30Ba a ƙetaren Yodan suke ba, ta faɗuwar rana kan hanya, cikin ƙasar Kan'aniyawa waɗanda suke zama cikin Araba, gaba da Gilgal, daura da itatuwa na More?
31Gama zaku ƙetare Yodan domin ku shiga ciki ku mallaki ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku, kuma za ku mallaketa ku kuma zauna cikinta.32Za ku kiyaye dukkan farillai da umarnan dana shirya a gabanku yau.

12

1Waɗannan su ne farillai da dokoki da zaku kiyaye cikin ƙasar da Yahweh, Allahn ubanninku, ke baku domin ku mallaka, dukkan kwanakin da zaku rayu a duniya.2Tabbas zaku lallata dukkan wuraren da al'umman da zaku kora suka bauta wa allolinsu, a bisa duwatsu masu tsawo, a bisa tsaunuka, da kuma ƙarƙashin kowanne koren itace.

3Dole ku rurrushe bagadansu, ku ragargaje ginshiƙansu na dutse, ku ƙone dogayen sandunansu na Ashera. Dole ku sassare sassaƙaƙƙun siffofin allolinsu ku hallaka sunayensu daga wurin nan.4Ba zaku yi sujada ga Yahweh Allahnku haka ba.
5Amma wurin da Yahweh Allahnku zai zaɓa daga cikin dukkan kabilunku ya sa sunansa, wannan zai zama wurin da zai zauna kuma wurin ne zaku tafi.6A can ne zaku kawo baye-bayenku na ƙonawa, hadayunku, zakkarku, da baye-bayenku da kuka bayar da hannunku, baye-bayenku na wa'adodi, da baye-bayenku na yaddar rai, da 'ya'yan fari na garkunanku na shanu dana tumaki.
7A can ne zaku ci a gaban Yahweh Allahnku ku yi murna akan kowanne abin da kuka sa hannunku a gare shi, ku da iyalanku, wurin da Yahweh Allahnku ya albarkace ku.
8Ba zaku yi dukkan abubuwan da muke yi anan ba yau; yanzu kowanne yana yin abin da yaga ya dace a gare shi;9gama baku zo wurin hutawa ba tukuna, ga abin gãdo da Yahweh Allahnku ya ke baku.
10Amma idan kuka haye Yodan kuka kuma zauna cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ke baku ita gãdo, kuma zai baku hutu daga dukkan maƙiyanku da ke kewaye da ku, domin ku zauna lafiya.11Daga nan zuwa wurin da Yahweh Allahnku ya zaɓa yasa sunansa ya zauna a wurin -- a can ne zaku kawo kowanne abin da na umarce ku: baye-bayenku na ƙonawa, da hadayunku, da zakkarku, da baye-bayen da kuka bayar da hannunku, da dukkan baye-bayen da kuka zaɓa domin wa'adodi da zaku yi wa'adi ga Yahweh.
12Zaku yi murna a gaban Yahweh Allahnku -- ku, da 'ya'yanku maza, da 'ya'yanku mata, da bayinku maza, da bayinku mata, da Lebiyawan da ke zama tare da ku, saboda ba shi da rabo ko gãdo a cikin ku.
13Ku kula da kanku kada ku miƙa baye-bayenku na ƙonawa a kowanne wurin da kuka gani;14amma a wurin da Yahweh zai zaɓa a cikin ɗaya daga cikin kabilunku zaku miƙa baye-bayenku na ƙonawa, kuma a can ne zaku yi kowanne abin da na dokace ku.
15Duk da haka, zaku iya yanka dabbobi ku kuma ci a ko'ina cikin biranenku, kamar yadda kuke so, kuna karɓan albarkar Yahweh Allahnku domin dukkan abin da ya baku; mutane marasa tsarki da masu tsarki dukkansu za su iya ci, dabbobi kamar gada da barewa.16Amma ba zaku ci jinin ba; zaku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
17Ba zaku ci waɗannan a garuruwanku ba daga zakkar hatsinku, sabon inabinku, man ku, ko 'ya'yan farin shanunku, ko tumakinku; ba zaku ci kowanne nama da kuka yi hadaya tare da kowanne wa'adodinku da kuka yi, ko kuma baye-bayenku na yaddar rai, ko baikon da kuka bayar da hannunku.
18Maimakon haka, sai ku ci su a gaban Yahweh Allahnku a wurin da Yahweh Allahnku ya zaɓa -- ku, da 'ya'yanku maza, da 'ya'yanku mata, da barorinku maza, da barorinku mata, da Balebi wanda ke zaune a garuruwanku; zaku yi murna a gaban Yahweh Allahnku game da kowanne abin da ya sa a hannunku.19Ku lura da kanku domin kada ku manta da Lebiyawa muddin kuna zaune a ƙasarku.
20Sa'ad da Yahweh Allahnku ya fãɗaɗa iyakokinku, kamar yadda ya alƙawarta maku, sa'annan kuka ce, 'Zan ci nama,' saboda ƙãwar cin nama, zaku iya cin nama, yadda ranku ya ke so.
21Idan wurin da Yahweh Allahnku ya zaɓa ya sa sunansa ya yi maku nisa sosai, daganan sai ku yanka wasu daga garken shanunku da tumaki da Yahweh ya baku, kamar yadda na umarce ku; zaku iya ci a garuruwanku, kamar yadda ranku ya ke so.22Kamar gada da barewa zaku ci, sai ku ci su, mutane marasa tsarki da masu tsarki za su iya ci su ma.
23Sai dai ku tabbata baku ci jinin ba, gama jinin shi ne ran; ba zaku ci rai da nama ba.24Kada ku ci shi, zaku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.25Ba zaku ci shi ba, domin kome ya tafi lafiya tare da ku, tare da 'ya'yanku a bayan ku, idan kuka yi abin da ke dai dai a gaban Yahweh.
26Amma abubuwan da ke na Yahweh da kuke da su da baye-bayen wa'adodinku -- zaku ɗauki waɗannan zuwa wurin da Yahweh ya zaɓa.27A can ne zaku miƙa baye-bayenku na ƙonawa, naman da jinin, akan bagadin Yahweh Allahnku; za a zubar da jinin hadayunku akan bagadin Yahweh Allahnku, kuma zaku ci naman.
28Ku lura kuma ku saurara ga dukkan kalmomin da na dokace ku da su, don ku sami zaman lafiya tare da 'ya'yanku a bayanku har abada, yayin da kuke yin abin da ke mai kyau da yin dai-dai a gaban idanun Yahweh Allahnku.
29Sa'ad da Yahweh Allahnku ya datse al'umman daga gabanku, sa'ad da kuka je kuka kore su, kuka mallake su, kuka zauna cikin ƙasarsu,30ku yi hankali da kanku kada ku faɗa cikin tarkon bin su, bayan da an hallaka su a gabanku -- kada ku faɗa cikin tarkon binciko allolinsu, cikin tambayar, 'Ta yaya waɗannan al'ummai suka yi wa allolinsu sujada? Zan yi kamar yadda suka yi.'
31Kada ku yi wa Yahweh Allahnku sujada ta irin wannan hanya, gama kowanne abin ƙyama ga Yahweh, abubuwan da ya ƙi -- sun yi waɗannan abubuwa tare da allolinsu; har sun ƙona 'ya'yansu maza da mata cikin wuta domin allolinsu.32Iyakar abin dana dokace ku, ku aikata shi, kada ku ƙara masa ko ku rage daga gare shi.

13

1Idan wani annabi ya tashi daga cikinku ko mai mafarkin mafarkai, kuma idan ya baku wata alama ko mu'ujiza,2kuma idan alamar ko mu'ujizar ta faru, wanda ya yi maku magana ya ce, 'Bari mu bi waɗansu allolin, da baku sani ba, kuma bari muyi masu sujada,'3kada ku saurari maganganun annabin nan, ko mai mafarkin mafarkan; gama Yahweh Allahnku yana gwada kune ya sani ko kuna ƙaunar Yahweh Allahnku da dukkan zuciyarku tare da dukkan ranku.

4Zaku bi Yahweh Allahnku, ku girmama shi, ku kiyaye dokokinsa, kuyi biyayya da muryarsa za kuyi masa sujada kuma ku manne masa.5Wannan annabin ko wannan mai mafarkin mafarkai za a kashe shi, saboda ya yi maganar tayarwa gãba da Yahweh Allahnku, wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar, da wanda ya fãnshe ku daga gidan bauta. Wannan annabi yana so ya karkatarda ku daga hanyar da Yahweh Allahnku ya dokace ku ku yi tafiya a kanta. Don haka sai ku kawar da mugunta daga cikinku.
6Idan ɗan'uwanka, ɗan mahaifiyarka, ko ɗanka, ko ɗiyarka, ko matar da ke ƙirjinka, ko abokinka wanda ke ƙaunar ranka, a asirce ya lallasheka ya ce, 'Bari muje mu bauta wa wasu allolin da baku sani ba, ko ku ko kakanninku --7kowanne allolin mutanen da ke kewaye daku, ko kusa daku, ko nesa can daku, daga wannan iyakar duniya zuwa ƙarshen waccan iyakar duniya,'
8Kada ku yarda da shi ko ku saurare shi, kada ku bari idonku ya ji tausayinsa, kada ku barshi koku ɓoye shi.9Maimakon haka, ku tabbata kun kashe shi; hannunku ne zai zama na farko wajen kisan sa, daga nan sai hannun dukkan jama'a.
10Zaku jejjefe shi da duwatsu har ya mutu, saboda ya yi ƙoƙarin janye ku daga Yahweh Allahnku, wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar, daga gidan bauta.11Dukkan Isra'ila zasu ji kuma suji tsoro, kuma ba zasu ci gaba da yin irin wannan mugun abu a cikin ku ba.
12Idan kuka ji wani ya ce wani abu game da ɗaya daga cikin biranenku, da Yahweh Allahnku ya baku ku zauna ciki:13Waɗansu mugaye sun fita daga cikinku har sun janye mazaunan birnin suka ce, 'Bari muje muyi sujada ga allolin da baku sani ba.'14Daganan sai ku yi nazarin shaidar, ku bincika, ku tabbatar da kyau. Idan kun gãne cewa gaskiya ne kun haƙiƙance cewa abin ƙyama irin wannan ya faru a cikinku, daganan sai ku ɗauki mataki.
15Ku tabbatar kun kai wa mazaunan birnin hari da kaifin takobi, ku hallaka shi da dukkan mutanen da ke zaune ciki, tare da dabbobinsa, da kaifin takobi gaba ɗaya.16Zaku tattara dukkan ganimar daga gare shi zuwa cikin tsakiyar tituna zaku ƙone birnin, da dukkan ganimar -- domin Yahweh Allahnku. Birnin zai zama tsibin kufai har abada; ba za a ƙara gina shi ba.
17Ba ɗaya daga cikin abubuwan da aka keɓe domin hallakarwa da zai liƙe cikin hannunku. Dole haka ya faru, domin Yahweh ya juya daga zafin fushinsa, ya nuna maku jinkai, ya ji tausayinku, yasa ku riɓanɓanya, kamar yadda ya rantse wa kakanninku.18Zai yi wannan saboda kuna sauraron muryar Yahweh Allahnku, kuna kiyaye dukkan dokokin dana dokace ku da su yau, kuna yin abin da ke dai-dai a gaban Yahweh Allahnku.

14

1Ku mutanen Yahweh Allahnku ne. Kada ku tsãge kanku, ko ku aske kowanne sashi na fuskarku domin matacce.2Gama ku al'umma ce keɓaɓɓiya ga Yahweh Allahnku, Yahweh kuma ya zaɓe ku ku zama mutane abin mallaka, fiye da dukkan al'umman da ke a fuskar duniya.

3Ba zaku ci kowanne abin da ke haram ba.4Waɗannan su ne dabbobin da zaku iya ci: saniya, da tunkiya, da akuya,5da mariri, da barewa, da mazo, da bunsurun daji, da makwarwa, da gada, da ragon dutse.
6Zaku iya cin kowacce dabbar da ke da rababben kofato, wato, wadda kofatonta sun rabu kashi biyu, kuma tana tuƙa.7Duk da haka, ba zaku ci waɗansu dabbobin da suke tuƙa kuma suke da rababben kofato ba misali: raƙumi, da zomo, da reman dutse; saboda suna tuƙa amma ba su da rababben kofato, marasa tsarki ne a gare ku.
8Alade ma ba shi da tsarki a gare ku saboda yana da rababben kofato amma ba ya yin tuƙa; haram ne a gare ku. Kada kuci naman alade, kada kuma ku taɓa mushensu.
9Daga irin waɗannan da suke cikin ruwa zaku iya ci: duk abin da ke da ƙege da ɓanɓaroki;10amma duk abin da ba shi da ƙege da ɓanɓaroki kada ku ci su; marasa tsarki ne a gare ku.
11Zaku iya cin dukkan tsarkakakkun tsuntsaye.12Amma waɗannan tsuntsayen da ba zaku ci ba: Mikiya, da Ungulu, da ƙwaƙwa,13da jar shirwa da baƙar shirwa, da kowanne irin shaho.
14Kada ku ci kowanne irin hankaka,15da jimina, da ƙururu, da harbiyar ruwa, kowanne irin shaho,16ƙaramar mujiya da babbar mujiya, da farar mujiya,17da zalben ruwa, da ungulu, da agwagwar daji.
18Ba zaku ci zalɓe ba, da kowanne irin jinjimi, bunburwa da jemage.19Dukkan abin da ke da fiffike da masu rarrafe marasa tsarki ne a gare ku; ba zaku ci su ba.20Zaku iya cin dukkan tsarkakakkun abubuwan da suke shawagi.
21Kada ku ci kowanne abin da ya mutu da kansa; za ku iya ba baƙon da ke cikin garuruwanku, domin ya ci; ko ku sayar da shi ga baƙo. Gama ku al'umma ce keɓaɓɓiya ga Yahweh Allahnku. Ba zaku dafa ɗan akuya cikin madarar uwarsa ba.
22Dole ku tabbata kun fitar da zakkar dukkan amfanin irin da kuka shuka, wanda ke tsirowa a gona kowacce shekara.23Dole ku ci a gaban Yahweh Allahnku, a wurin da zai zaɓa a matsayin wuri mai tsarki, zakkar hatsin ku, da sabon inabi, dana manku, da 'ya'yan farin shanunku dana dabbobinku; domin kullum ku koyi girmama Yahweh Allahnku.
24Idan tafiyar ta yi maku nisa kwarai da baza ku iya kai ta ba, saboda wurin da Yahweh Allahnku ya zaɓa a matsayin wurin sa mai tsarki ya yi maku nisa, daganan, idan Yahweh ya albarkace ku,25sai ku sayar da zakkar ku mai da ita kuɗi, sai ku ƙulle kuɗin cikin hannunku, ku tafi wurin da Yahweh Allahnku zai zaɓa.
26A can ne zaku kashe kuɗin akan duk abin da kuke marmari: domin sã, ko domin tunkiya, ko domin ruwan inabi, ko domin abin sha mai ƙarfi, ko domin duk abin da kuke so; zaku ci a can a gaban Yahweh Allahnku, kuma ku yi murna, kuda iyalin gidanku.27Balebi wanda ya ke cikin garuruwanku -- kada ku yashe shi, gama ba shi da rabo ko gãdo tare da ku.
28A ƙarshen kowacce shekara uku za ku kawo dukkan zakkar amfaninku cikin wannan shekarar, zaku ajiye ta cikin ƙofofinku;29Balebi kuma, saboda ba shi da rabo ba shi da gãdo tare daku, da baƙo, da maraya, da gwamruwa waɗanda ke cikin ƙofofinku, za su zo su ci su ƙoshi. Ku yi haka domin Yahweh Allahnku ya albarkace ku cikin dukkan aikin da hannuwanku ke yi.

15

1A ƙarshen kowacce shekara bakwai, dole ku yafe basussuwa.2Ga yadda za a yi yafiyar: Kowanne mai bin bashi zai yafe abin da ya rantawa maƙwabcinsa; ba zai neme shi daga wurin maƙwabcinsa ba ko ɗan'uwansa saboda an yi shelar yafe basussuwa ta Yahweh.3Zaka iya nema daga wurin baƙo; amma duk abin da ke naka ya ke tare da ɗan'uwanka ba za ka nemi a biya ka ba.

4Har yanzu, ba za a sami matalauci a cikinku ba (gama lallai Yahweh zai albarkace ku a cikin ƙasar da ya ke baku ita a matsayin gãdo ku mallaka),5muddin kuka saurari muryar Yahweh Allahnku, kuka kiyaye dukkan waɗannan dokoki da nake umartarku da su yau.6Gama Yahweh Allahnku zai albarkace ku, kamar yadda ya alƙawarta maku; zaku ba al'ummai da yawa rance, amma ba zaku ranta ba; zaku yi mulkin al'ummai da yawa, amma ba zasu yi mulkin ku ba.
7Idan akwai wani mutum matalauci a cikinku, ɗaya daga cikin 'yan'uwanku, a tsakanin kowacce ƙofofinku cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku, kada ku taurare zuciyarku koku rufe hannunku daga ɗan'uwanku matalauci;8amma lallai sai ku buɗe hannunku gare shi kuma ku ranta masa issashe domin biyan bukatarsa.
9Ku lura kada ku kasance da mugun tunani a cikin zuciyarku, kuna cewa, 'Ai shekara ta bakwai, shekarar yafewa, ta kusa,' domin kada ku zama da maƙo game da ɗan'uwanku ku kuma ƙi bashi kome; zai iya yin kuka ga Yahweh game daku, kuma ya zama zunubi a gare ku.10Lallai dole ku bashi, zuciyarku kuma ba zata da mu ba idan kuka bashi, saboda wannan Yahweh Allahnku zai albarkace ku cikin dukkan aikinku da kuma dukkan abin da kuka sanya cikin hannunku ku yi.
11Gama ba za a rasa matalauta a cikin ƙasar ba; saboda haka na dokace ku cewa, 'Dole ku zama da hannu sake ga ɗan'uwanku, ga mabuƙatanku, da kuma matalauci a cikin ƙasarku.'
12Idan aka sayar maku da ɗan'uwanku, Ba'ibrane ko mace ko namiji sai ya bauta maku shekara shida, daga nan a cikin shekara ta bakwai dole ku 'yantar da shi daga gare ku.13Idan kuka 'yantar da shi daga gare ku, ba zaku barshi ya tafi hannun wofi ba.14Dole ku bashi kyauta a yalwace daga cikin tumakinku, da masussukar hatsinku, da wurin matsewar inabinku. Kamar yadda Yahweh Allahnku ya albarkace ku, dole ku ba shi.
15Dole ku tuna cewa dã ku bayi ne a cikin ƙasar Masar, kuma Yahweh Allahnku ya fãnshe ku; don haka nake umartarku yau ku yi haka.16Idan kuma ya ce maku, 'Ba zan tafi daga gare ku ba,' saboda yana ƙaunarku da gidanku, kuma yana jin daɗin zama tare da ku,17daganan sai ku ɗauki bisilla ku huda kunnensa har dogaran ƙofa, zai zama bawanku har iyakar rayuwa. Haka kuma zaku yi da mace baiwa.
18Kada ya zama da damuwa a gare ku idan kuka 'yantar shi daga gare ku, saboda ya yi maku bauta shekaru shida darajar bautarsa ta ninka biyu da ta mutumin da aka yi hayarsa. Yahweh Allahnku zai albarkace ku cikin dukkan abin da kuke yi.
19Dukkan 'ya'yan farin a cikin garkunan shanunku dana tumaki dole ku keɓe su ga Yahweh Allahnku. Kada ku yi aiki da 'ya'yan farin shanunku, koku yi sausayar ɗan farin tumakinku.20Dole ku ci ɗan farin a gaban Yahweh Allahnku kowacce shekara a wurin da Yahweh ya zaɓa, ku da iyalinku.21Idan tana da wani cikas -- misali, gurguntaka, ko makanta ko tana da wani cikas ta kowanne iri -- kada ku miƙa ta hadaya ga Yahweh Allahnku.
22Zaku ci ta a garuruwanku; mutane marasa tsarki da masu tsarki su ma dole su ci, kamar mariri ko barewa.23Sai dai kada ku ci jinin; dole ku zubar da jinin a ƙasa kamar ruwa.

16

1Ku kiyaye watan Abib, kuma ku kiyaye Bukin Ƙetarewa ga Yahweh Allahnku, gama a watan Abib ne Yahweh Allahnku ya fito daku daga Masar da daddare.2Zaku miƙa hadayar Ƙetarewa ga Yahweh Allahnku tare da wasu garkunan tumakinku dana shanu a wurin da Yahweh zai zaɓa a matsayin wurinsa mai tsarki.

3Ba zaku ci abinci mai gami tare da ita ba; kwana bakwai zaku ci abinci mara gami tare da hadayar, abincin wahala ne; gama kun fito daga ƙasar Masar da gaggawa. Kuyi haka dukkan kwanakinku domin ku tuna da ranar da kuka fito daga ƙasar Masar.4Kada a ga gami a cikinku a dukkan iyakokinku a lokacin kwanaki bakwai; kada kowanne naman da kuka miƙa hadaya da yamma a rana ta fari ya kwana har safiya.
5Kada ku miƙa hadayar Ƙetarewa a kowanne garin da Yahweh ya ke baku.6Maimakon haka, ku miƙa ta a wurin da Yahweh Allahnku zai zaɓa a matsayin wurinsa mai tsarki. A can zaku miƙa hadayar Ƙetarewa da yamma da faɗuwar rana, a dai-dai lokacin da shekarar da kuka fito daga Masar.
7Dole ku gasa shi kuma ku ci shi a wurin da Yahweh Allahnku zai zaɓa; da safe zaku juya ku koma zuwa rumfunanku.8Kwana shida zaku yi kuna cin abinci mara gami; a rana ta bakwai sai kuyi muhimmin taro domin Yahweh Allahnku; a wannan ranar kada kuyi aiki.
9Zaku ƙirga mako bakwai domin kanku; daga lokacin da kuka fara sa lauje ga hatsinku da ke tsaye dole ku fara ƙirga makonni bakwai.10Dole ku kiyaye Bikin Makonni domin Yahweh Allahnku tare da bada gudunmuwa ta yaddar rai daga hannunku da zaku bayar, gwargwadon yadda Yahweh Allahnku ya albarkace ku.
11Zaku yi murna a gaban Yahweh Allahnku - ku, da 'ya'yanku maza, da 'ya'yanku mata, da barorinku maza, da barorinku mata, da Balebiyen da ke zaune a ƙofofin garinku, da baƙo, da marayu, da gwamruwa waɗanda ke tare da ku, a wurin da Yahweh Allahnku zai zaɓa domin wurinsa mai tsarki.12Ku tuna dã ku bayi ne a Masar; dole ku kiyaye kuma ku aikata waɗannan farillai.
13Dole ku kiyaye Bikin Bukkoki kwanaki bakwai bayan da kun gama tattara amfaninku daga masussukanku da wurin matsewar ruwan inabinku.14Zaku yi murna a lokaci bikin -- ku, da 'ya'yanku maza, da 'ya'yanku mata, da barorinku mata, da Balebiye, da baƙo, da maraya da gwamruwa waɗanda ke a garuruwanku.
15Kwana bakwai zaku kiyaye biki ga Yahweh Allahnku a wurin da Yahweh zai zaɓa, saboda Yahweh Allahnku zai albarkace ku a cikin dukkan aikin hannuwanku, kuma dole ku zama da cikakkiyar murna.
16Sau uku a shekara dole dukkan mazajenku su hallara a gaban Yahweh Allahnku a wurin da zai zaɓa: a lokacin Bikin Abinci Marar Gami, da lokacin Bikin Makonni, da kuma lokacin Bikin Bukkoki. Kada wani ya hallara gaban Yahweh hannu- wofi;17maimakon haka, kowanne mutum zai bayar gwargawdon abin da zai iya, domin ku san albarkar da Yahweh Allahnku ya bayar gare ku.
18Dole ku naɗa alƙalai da shugabannai a dukkan ƙofofin garuruwanku da Yahweh Allahnku ya ke baku; za a ɗauko su daga kowacce kabilarku, dole su shari'anta jama'a da shari'a ta adalci.19Kada ku ɗauke adalci da ƙarfi; kada ku nuna son kai koku karɓi cin hanci, gama cin hanci yana makantar da idanun mai hikima ya karkatar da maganganun adali.20Dole kubi adalci, bayan adalci kaɗai, domin ku rayu ku iya gãdon ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku.
21Kada ku sanya wa kanku Asherah, kowanne irin itace, kusa da bagadin Yahweh Allahnku da zaku yi domin kanku.22Kada kuma ku gina wa kanku al'amudin dutse, wanda Yahweh Allahnku ya ke ƙi.

17

1Kada ku miƙa wa Yahweh Allahnku hadaya ta sã ko tunkiya da ke da kowanne lahani ko duk abin da bashi da kyau, gama wannan zai zama abin ƙyama ga Yahweh Allahnku.

2Idan aka sami wani, a tsakanin kowaɗanne ƙofofin garinku da Yahweh Allahnku ya ke baku, kowanne mutum ko mace, wanda ya aikata abin da ke mugu a gaban Yahweh Allahnku yana karya alƙawarinsa,3duk wanda yaje ya yi sujada ga waɗansu alloli ya kuma russuna masu, ko rana, ko wata, ko kowacce rundunar sama - ba abin dana umarce ku ba -4idan aka faɗa maku game da wannan, ko kuka ji labarinsa, daganan dole kuyi bincike a hankali. Idan gaskiya ne kuma an tabbatar da anyi irin wannan abin ƙyamar a Isra'ila, wannan shi ne abin da zaku yi.
5Dole ku kawo wannan mutum ko macen, wanda ya aikata wannan mugun abu, ga ƙofofin garuruwanku, wannan mutumin ko macen, dole ku jejjefe shi da duwatsu har ya mutu.6Bisa ga shaidu biyu ko shaidu uku, za a kashe shi; amma ba za a kashe mutum bisa ga shaidar mutum ɗaya ba.7Hannun shaidun zasu fara jifansa ga mutuwa, daganan sauran dukkan jama'a; ta haka zaku kawar da mugunta daga cikinku.
8Idan wani abu ya taso da ya zama da wahala a gare ku ku shari'anta - watakila zancen kisankai ko haɗarin mutuwa, ta zancen 'yancin wani da ta wani, ko tambaya akan wani irin lahani da aka yi, ko dai wani al'amari, al'amura masu wahalarwa a cikin ƙofofin garinku -- daga nan dole ku tafi wurin da Yahweh Allahnku zai zaɓa a matsayin wurinsa mai tsarki.9Dole ku je wurin firist, zuriyar Lebi, da kuma wurin alƙali da zai yi hidima a lokacin; zaku nemi shawararsu, zasu baku mafita.
10Dole ku bi shari'ar da aka baku a wurin da Yahweh zai zaɓa a matsayin wurinsa mai tsarki. Dole ku lura ku yi dukkan abin da suka jagorance ku ga yi.11Kubi shari'ar da suka koya maku, ku kuma yi bisa ga shawarwarin da suka baku. Kada ku kauce daga abin da suka faɗa maku, zuwa hananun dama ko zuwa hannun hagu.
12Duk wanda ya yi isgilanci, ta wurin ƙin sauraron firist wanda ke tsaye ya bauta wa Yahweh Allahnku, ko ta ƙin sauraron alƙali - wannan mutum zai mutu; dole ku kawar da mugunta daga Isra'ila.13Dukkan mutane dole suji kuma suji tsoro, ba zasu ƙara yi isgilanci ba.
14Sa'ad da kuka zo ƙasar da Yahweh Allahnku ya ba ku, kuma idan kuka mallake ta kuka fara zama cikinta, sa'an nan kuka ce, 'Zan sanya sarki a bisa kaina, kamar dukkan al'umman da suke kewaye da ni,'15daga nan dole ku tabbatar kun naɗa wa kanku sarki wanda Yahweh Allahnku zai zaɓa. Dole ku naɗa wa kanku sarki wanda ke daga cikin 'yan'uwanku. kada ku sanya baƙo, wanda ba ɗan'uwanku ba, a bisa kanku.
16Amma kada ya ƙara wa kansa dawakai, kada ya sa mutane su koma Masar don su ƙaro masa dawakai, gama Yahweh ya ce maku, 'Kada ku ƙara komawa can.'17Kada ya ɗauki mata da yawa domin kansa, domin kada zuciyarsa ta karkace. Kada ya tattara wa kansa tulin kuɗin azurfa da zinariya.
18Sa'ada da ya zauna kan gadon sarautar mulkinsa, dole ya rubutawa kansa a cikin naɗaɗɗen kwafin littafi shari' an nan, daga shari'a da ke gaban firist, waɗanda suke Lebiyawa.19Naɗaɗɗen littafin zai kasance tare da shi, kuma dole ya karanta shi cikin dukkan kwanakin ransa, domin ya koyi girmama Yahweh Allahnsa, domin ya kiyaye dukkan kalmomin shari'ar da waɗannan farillai, ya kiyaye su.
20Dole ya yi haka domin kada zuciyarsa ta kumbura bisa kan 'yan'uwansa, domin kada ya kauce daga bin dokokin, zuwa dama ko hagu; domin ya sami dalilin daɗewa cikin mulkinsa, shi da 'ya'yansa, a cikin Isra'ila.

18

1Firistoci, da suke Lebiyawa, da dukkan kabilar Lebi, ba za su sami rabo ko gãdo tare da Isra'ila ba; dole su ci baye-bayen Yahweh da aka yi da wuta a matsayin gãdonsu.2Ba zasu sami gãdo tare da 'yan'uwansu ba; Yahweh shi ne gãdon su, kamar yadda ya faɗa masu.

3Wannan shi ne rabon da aka ba firistoci, aka basu daga mutanen da suka miƙa hadaya, ko ta sã ne ko tunkiya ce: kafaɗar, kumatu biyu, da kuma kayan ciki.4Sai nunan fari na hatsinku, da sabon ruwan inabi, da manku, da gashin tumakinku da kuka fara sausaya, dole ku ba shi.5Gama Yahweh Allahnku ya zaɓe shi da ga cikin kabilunku su tsaya su yi hidima a cikin sunan Yahweh, shi da 'ya'yansa har abada.
6Idan Balebiye ya fito daga kowanne garinku na dukkan Isra'ila daga inda ya ke zama, kuma ya yi marmari da dukkan ransa ya zo wurin da Yahweh ya zaɓa,7daganan dole ya yi hidima a cikin sunan Yahweh Allahnsa kamar yadda dukkan 'yan'uwansa Lebiyawa suke yi, waɗanda ke tsayawa a can a gaban Yahweh.8Dole su sami rabo iri ɗaya su ci, banda abin da ke zuwa daga abin da iyalinsa suka sayar na gãdo.
9Sa'ad da kuka zo cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku, kada kuyi kwaikwayon ayyukan banƙyama na waɗannan al'ummai.10Kada a sami wani a cikinku da zai miƙa ɗansa ko 'yarsa hadaya cikin wuta, duk wanda ke amfani da maita ko mai faɗin gaibu, ko mai sihiri, ko ya shiga maita,11duk mabiya, ko mai sha'ani da ruhohi ko mai surkulle, mai magana da ruhohin matattu.
12Gama duk mai yin waɗannan abubuwa abin ƙyama ne ga Yahweh; saboda waɗannan abubuwan ban ƙyama ne Yahweh Allahnku ya ke korarsu daga gaban ku.13Sai ku zama marasa aibu a gaban Yahweh Allahnku.14Gama waɗannan al'ummai da zaku kora suna sauraran masu aikata maita da masu duba; amma ku, Yahweh Allahnku bai yaddar maku ku yi haka ba.
15Yahweh Allahnku zai tayar maku da wani annabi daga cikinku, ɗaya daga cikin 'yan'uwanku, kama ta. Dole ku saurare shi.16Wannan shi ne abin da kuka roƙa a wurin Yahweh Allahnku a Horeb a ranar taron, cewa, 'Kada ka barmu mu ƙara jin muryar Yahweh Allahnmu, ko mu ƙara ganin wannan babbar wuta, don zamu mutu.'
17Yahweh ya ce mani, 'Abin da suka ce yana da kyau.18Zan tayar masu da wani annabi daga cikin 'yan'uwansu, kamar ka. Zan sa maganganuna cikin bakinsa, zai faɗa masu dukkan abin da na dokace shi.19Zai kasance kuwa duk wanda bai saurari maganganuna da zai faɗa a cikin sunana ba, Zan nemi haƙƙinta a gareshi.
20Amma annabin da ya faɗi maganar isgilanci cikin sunana, maganar da ban umarce shi ba ya faɗa, ko wanda ya yi magana cikin sunan waɗansu alloli, wannan annabin dole ya mutu.'21Wannan shi ne abin da zaku ce a cikin zuciyarku: 'Ta yaya zamu san saƙon da Yahweh bai faɗi ba?'
22Zaku gane saƙon da Yahweh ya faɗa idan annabi ya yi magana a cikin sunan Yahweh. Idan wannan abin bai zo ba, ko bai faru ba, daganan wannan shi ne abin da Yahweh bai faɗa ba kuma annabin ya faɗe shi ne cikin isgilanci, kada ku ji tsoronsa.

19

1Sa'ad da Yahweh Allahnku ya datse al'ummai, waɗannan waɗanda Yahweh Allahnku zai baku ƙasarsu, sa'ad da kuka zo bayansu kuka zauna a cikin garuruwansu da gidajensu,2sai ku zaɓi birane uku domin kanku a tsakiyar ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke ba ku ku mallaka.3Sai ku gina hanyoyi ku kuma raba iyakokin ƙasarku kashi uku, ƙasar da Yahweh Allahnku ke saku gãda, domin duk wanda ya kashe wani mutum sai ya gudu zuwa can.

4Wannan itace doka domin wanda ya kashe wani da wanda ya gudu can don ya tsira - duk wanda ya kashe maƙwabcinsa ba don ya yi niyya ba, kuma bai ƙi shi ba a dã.5Misali, idan mutum ya tafi cikin jeji tare da maƙwabcinsa domin su saro itace, sai ruwan gatarin ya kwaɓe daga ƙotar ya sari maƙwabcinsa ya kashe shi - daganan wannan mutumin dole ya gudu zuwa ɗaya daga biranen domin ya tsirar da ransa.
6Idan ba haka ba mai bin haƙƙin jini zai iya bin shi wanda ya ɗauki ran, cikin zafin fushinsa ya cim masa, idan nisan ya yi yawa sosai, ya cim masa ya kashe shi, koda shike mutumin nan bai cancanci mutuwa ba, tunda shike bai ƙi shi ba a dã.7Don haka na dokace ku ku keɓe wa kanku birane uku.
8Idan Yahweh Allahnku ya fãɗaɗa iyakokinku, kamar yadda ya alƙawarta wa kakanninku zai yi, ya baku dukkan ƙasar da ya alƙawarta ya ba kakanninku;9idan kuka kiyaye dukkan waɗannan dokoki kuka aikata su, waɗanda nake dokatarku da su yau - dokokin ku ƙaunaci Yahweh Allahnku kullum kuyi tafiya cikin hanyoyinsa, daganan sai ku ƙara birane uku domin kanku, akan waɗannan ukun kuma.10Kuyi haka domin kada a zubar da jinin mara laifi a cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku domin gãdo, domin kada alhakin jini ya kasance a kanku.
11Amma idan wani yana ƙin maƙwabcinsa, ya yi kwanto yana jiransa, ya tasar masa, ya yi masa rauni har ya mutu, idan ya gudu zuwa cikin ɗaya daga cikin biranen nan -12daganan dattawan garinsu dole su aika a kawo shi daga can, daganan su miƙa shi a hannun ɗan'uwan mai bin hakƙin jini domin a kashe shi.13Kada idannunku su tausaya masa; maimakon haka dole ku kawar da alhakin zubar da jini daga Isra'ila, domin ku sami zaman lafiya.
14Kada ku kawar da iyakar maƙwabcinka da kakanninku suka kafa tuntuni, a cikin gãdon da zaku gãda, a cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku ku mallaka.
15Shaidar mutum ɗaya ba zata isa a tabbatar da cewa mutum ya yi kowanne irin laifi ba, ko kowanne zunubi, a kan kowanne zunubin da ya yi; sai an ji a bakin shaidu biyu ko uku, kafin a tabbatar da kowanne abu.16Alal misali idan mashaidi marar adalci ya tashi gãba da kowanne mutum ya shaida sharri game da laifinsa.
17Daganan sai dukkansu mutanen, waɗanda rashin jituwar ta faru tsakaninsu, dole su tsaya gaban Yahweh, a gaban firistoci da alƙalai masu yin hidima akwanakin nan.18Dole alƙalan suyi bincike sosai; su duba, idan mai shaidar mai shaidar zur ne, ya yi shaidar ƙarya game da ɗan'uwansa,19daganan sai ku yi masa, kamar yadda ya so ayi wa ɗan'uwansa; kuma zaku kawar da mugunta daga cikinku tawurin yin haka.
20Daganan sauran da suka ragu zasu ji su ji tsoro, kuma daganan ba zasu ƙara aikata irin wannan mugunta a cikinku ba.21Kada idannunku su tausaya; rai maimakon rai, ido mai makon ido, haƙori mai makon haƙori, hannu mai makon hannu, ƙafa mai makon ƙafa.

20

1Sa'ad da kuka tafi yaƙi gãba da maƙiyanku, idan kunga dawakai, karusai, da mutanen da suka fi ku yawa, kada ku ji tsoronsu; Gama Yahweh Allahnku yana tare daku, shi wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar.

2Sa'ad da kuke gab da shiga cikin yaƙi, sai firist ya kusato ya yi magana da mutane.3Dole ya ce masu, 'Ku saurara, Isra'ila, zaku tafi yaƙi gãba da maƙiyanku. Kada ku bari zukatanku su karaya. Kada kuji tsoro ko ku firgita. Kada kuji tsoronsu.4Gama Yahweh Allahnku shi ne mai tafiya tare daku ya yi yaƙi domin ku gãba da maƙiyanku ya cece ku kuma.'
5Dole shugabanni suyi magana da mutane su ce, 'Ko akwai wani mutum wanda ya gina sabon gida da bai buɗe shi ba? Bari ya koma gidansa, domin kada ya mutu cikin yaƙi sa'an nan wani mutum dabam ya yi bikin buɗewarsa.
6Ko akwai wani daya dasa gonar inabi da bai ci amfaninta ba? Bari ya koma gida, domin kada ya mutu a cikin yaƙi wani mutum dabam yaci amfaninta.7Wanne mutum ne ya ke tashin mace amma bai aure ta ba tukuna? Bari ya koma gida domin kada ya mutu a cikin yaƙi sa'an nan wani mutum dabam ya aure ta.'
8Shugabannin zasu ci gaba da yiwa mutane magana su ce, 'Ko a kwai wani mutum a nan da ya ke jin tsoro ko mai karyayyar zuciya? Bari ya koma gidansa, domin kada zuciyar 'yan'uwansa su narke kamar yadda zuciyarsa ta narke.'9Sa'ad da shugabanni suka gama yin magana da mutane, dole su naɗa hafsoshi a kansu.
10Sa'ad da kuka kusanci wani birni don ku kai masa hari, ku ba mutanen birnin kyautar salama.11Idan suka karɓi kyautar ku har suka buɗe maku ƙofofinsu, dukkan mutanen da kuka sãmu a cikinsa dole suyi maku aikin gandu kuma su bauta maku.
12Amma idan ya ƙi yin salama daku, maimakon haka sai ya yi yaƙi daku, daganan sai ku kewaye shi da yaƙi,13idan kuma Yahweh Allahnku ya baku nasara ya sa su ƙarƙashin sarrafawar ku, dole ku kashe kowanne mutum a cikin garin.
14Amma mata da ƙanana, da dabbobi, da kowanne abin da ke cikin birnin, da dukkan ganimarsu, zaku ɗauka a matsayin ganima domin kanku. Zaku ci ganimar maƙiyanku, wadda Yahweh Allahnku ya baku.15Haka zaku aikata ga dukkan biranen da ke nesa daku sosai, biranen da ba biranen waɗannan al'ummai ba.
16A cikin biranen al'umman nan da Yahweh Allahnku ya ke baku a matsayin gãdo, kada ku bar kowanne abin da ke numfashi da rai.17Maimakon haka zaku hallakar da su ƙarƙaf: Su Hittiyawa, da Amoriyawa, da Kan'aniyawa, da Feriziyawa, da Hibiyawa, da Yebusiyawa, kamar yadda Yahweh Allahnku ya dokace ku.18Ku yi haka domin kada su koya maku ku aikata kowanne abin banƙyamarsu kamar yadda suka yi tare da allolinsu. Idan kuka yi, zaku yi zunubi ga Yahweh Allahnku.
19Sa'ad da kuka daɗe da kewaye birni, yayin da kuke yaƙi da shi domin ku ci shi, kada ku hallaka itatuwansa da gatari ta wurin saransu. Gama zaku iya ci daga gare su, don haka kada ku sare su ƙasa. Gama itacen gona mutum ne da zaku kewaye shi da yaƙi?20Itatuwan kaɗai da kuka sani ba itatuwan da ake ci ba, zaku iya hallakarwa ku sare su ƙasa; zaku gina kagara da su gãba da birnin da ke yaƙi daku, har sai ya faɗi.

21

1Idan aka iske an kashe wani a cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku ku mallaka, a kwance cikin gona, kuma ba a san wanda ya kai masa hari ba;2daganan sai dattawanku da alƙalanku su fita, dole su auna zuwa garuruwan da ke kewaye da shi wanda aka kashe.

3Daganan dattawan garin da ke kusa da gawar mataccen dole su ɗauki karsana daga garke, wadda ba a taɓa aiki da ita ba, kuma ba a taɓa sa mata karkiya ba.4Daganan dole su jagoranci karsanar zuwa kwari inda ruwa ke gudu, kwarin da ba a noma ko shuka ba, kuma a can cikin kwarin zasu karya wuyar karsanar.
5Sai firistoci, zuriyar Lebi, dole su zo gaba, domin Yahweh Allahnku ya zaɓe su su hidimta masa su kuma sa albarka a cikin sunan Yahweh su kuma dai-dai ta kowacce matsalar jayayya da cin mutunci ta wurin maganarsu.
6Dukkan dattawan birni da ya fi kusa da mutumin da aka kashe dole su wanke hannuwansu a kan karsanar wadda aka karya wuyanta a cikin kwari;7kuma dole su amsa ga matsalar su ce, 'Hannayenmu ba su zubar da wannan jinin ba, idanunmu kuma ba su ga wanda ya zubar da shi ba.
8Yahweh, ka gafarta, wa mutanenka Isra'ila, waɗanda ka fansa, kuma kada ka ɗora alhakin jinin mara laifin nan a tsakiyar mutanenka Isra'ila.' Daganan za a yafe masu zubar da jinin.9Ta haka zaku kawar da alhakin jinin mara laifi daga cikinku, sa'ad da kuka yi abin da ke dai-dai a idanun Yahweh.
10Sa'ad da kuka fita yaƙi gãba da maƙiyanku Yahweh Allahnku kuwa ya baku nasara yasa su ƙarƙashin sarrafawarku, kuka kuwa ɗauke su a matsayin bayi,11idan a cikin bayinka akwai kyakkyawar mace, wadda ka yi sha'awarta kuma kana so ka ɗauke ta domin ta zama matarka,12daganan sai ka kawo ta gidanka; za ta aske kanta ta kuma yanke farshenta.
13Daganan zata tuɓe tufafinta da take sawa sa'ad da aka ɗauko ta bauta zata kasance cikin gidanka tana makokin mahaifinta da mahaifiyarta wata guda cif. Bayan haka zaka iya kwana tare da ita ka zama mijinta, ita kuma ta zama matarka.14Idan ka ji baka jin daɗinta, daganan sai ka barta ta tafi wurin da ta ga dama. Amma kada ka yarda ka sayar da ita domin kuɗi, kada kuma ka wahalsheta kamar baiwa, saboda ka ƙasƙantar da ita.
15Idan mutum yana da mata biyu sai ya nuna yana son ɗayar kuma ya ƙi ɗayar, kuma dukkansu sun haifa masa 'ya'ya - dukka da wadda ya ke ƙauna da wadda ya ke ƙi - idan ɗan farin na wadda ya ke ƙi ce,16daganan a ranar da zai sa 'ya'yansa su gãji abin da ya mallaka, kada yasa ɗan matar da ya ke ƙauna ya zama ɗan fari gaban ɗan matar da ya ke ƙi, wanda shi ne ainihin ɗan farin.17Maimakon haka, dole ya amince da wanda ya ke ɗan farin, wato ɗan matar da ya ke ƙi, ta wurin bashi kaso biyu na dukkan abin da ya mallaka; gama wannan ɗan shi ne farkon ƙarfinsa; haƙin ɗan fari nasa ne.
18Idan mutum yana da gagararren ɗa kuma mai tayaswa wanda ba ya biyayya da maganar mahaifinsa ko maganar mahaifiyarsa, kuma wanda, koda shike sun kwaɓe shi, ba ya sauraron su;19daganan sai mahaifinsa da mahaifiyarsa su cafke shi su kawo shi waje wurin dattawansu na birni kuma zuwa ƙofar birninsa.
20Dole su ce da dattawan birnisa, 'Wannan ɗanmu ne gagararre ne kuma ɗan tayarwa; baya biyayya da maganar mu; shi mai zarin ci ne kuma mashayi.'21Daganan dukkan mutanen birni dole su jejjefeshi da duwatsu har ya mutu; ta haka zaku kawar da mugunta daga cikinku. Dukkan Isra'ila zasu ji suji tsoro.
22Idan mutum ya aikata zunubin da ya isa mutuwa kuma aka kashe shi, kuma aka rataye shi a bisa itace,23daganan kada abar jikinsa ya kwana dukkan dare a kan itace, amma, dole ku tabbatar kun bizne shi a ranar; gama duk wanda aka rataye shi la'ananne ne ga Allah. Ku yi biyayya da dokar nan domin kada ku ƙazantar da ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku a matsayin gãdo.

22

1Kada ku kalli sã ko tunkiyar ɗan'uwanku Ba-isra'ile yana ɓacewa ku ƙyale su; dole ku tabbatar kun dawo da su ga maishi.2Idan ɗan'uwanku mutumin Isra'ila ba ya kusa daku, ko idan baku sanshi ba, daganan dole ku kawo dabbar wurinku a gidanku, za ta kasance tare daku har lokacin da ya zo neman ta, daganan dole ku mayar masa da ita.

3Dole kuyi irin haka da jakinsa, dole kuyi haka ga rigarsa; dole kuyi haka da kowanne abin da ya ɓace na ɗan'uwanku Ba-isra'ile, duk abin da ya ɓata kuka tsinta; lallai ba zaku ɓoye kanku ba.4Ba zaku ga jaki ko san ɗan'uwanku Ba-isra'ile ya faɗi a hanya ku ƙyale su ba; dole ku tabbatar kun taimake shi tawurin sake ɗaga shi sama.
5Kada mace ta sanya abin da ya shafi suturar maza, kuma kada namiji ya sanya suturar mata; gama duk wanda ya yi waɗannan abubuwa abin ƙyama ne ga Yahweh Allahnku.
6Idan kuna tafiya a kan hanya sai kuka ga sheƙar tsuntsu, a kan kowanne itace, ko a ƙasa, da 'ya'yansa ko ƙwayaye a ciki, uwar kuma na kwance a kan 'ya'yan ko a kan ƙwayayen, kada ku kama uwar duk da 'ya'yan.7Ku tabbatar uwar ta tafi, amma zaku iya kwashe 'ya'yan domin kanku. Ku yi biyayya da dokar nan domin ku sami zaman lafiya ta haka kuma zaku tsawaita kwanakinku.
8Sa'ad da kuka gina sabon gida, daganan dole ku ja rawani a rufin domin kada ku jawo wa gidanku alhakin jini idan wani ya faɗi daga can.
9Kada ku shuka iri biyu a gonar inabinku, domin kada wuri mai tsarki ya karɓe dukkan amfaninku, irin da kuka shuka da kuma amfanin gonar inabinku.10Kada ku haɗa sa da jaki suyi huɗa tare.11Kada ku sanya rigar da aka saƙa da ulu garwaye da lilin.
12Dole kuyi wa kanku geza a kusurwoyi huɗu na suturar da kuke suturta kanku.
13Idan mutum ya ɗauki mace, ya kwana da ita, daga nan ya ƙi ta,14kuma yana zarginta da yin abubuwan kunya ya sanya mummunar shaida akan ta, ya ce, 'Na ɗauki wannan mace, amma sa'ad da na yi kusa da ita, Na iske babu shaidar budurci a cikinta.'
15Daganan sai mahaifinta da mahaifiyar yarinyar su kawo shaidar budurcinta gaban dattawa a ƙofar birni.
16Mahaifin yarinyar zai cewa dattawan, 'Na bada 'yata aure ga wannan mutum, amma ya ƙi ta.17Duba, ya zarge ta da abubuwan kunya har ya ce, 'Ban sami ɗiyarka da shaidar budurci ba.' Amma ga shaidar budurcin 'yata.' Daganan zasu shimfiɗa ƙyalle a gaban dattawan birni.
18Sai dattawan garin su kama wannan mutumin su hukunta shi;19kuma zasu yi masa tarar awo ɗari na azurfa, su bada su ga mahaifin yarinyar, saboda mutumin ya bada mummunar shaida ga budurwa a Isra'ila. Dole ta zama matarsa; ba shi da iko ya sallame ta dukkan kwanakin ransa.
20Amma idan wannan gaskiya ne, cewa ba a ga shaidar budurci a cikin yarinyar ba,21daganan dole su kawo yarinyar a ƙofar gidan mahaifinta, daganan mutanen garin dole su jejjefeta da duwatsu har ta mutu, saboda ta aikata abin kunya a cikin Isra'ila, ta aikata karuwanci a cikin gidan mahaifinta; ta haka za ku kawar da mugunta a cikinku.
22Idan aka iske mutum yana kwana da matar wani, dukkansu biyu dole su mutu, wato mutumin da ke kwana da matar da matar kanta; ta haka zaku kawar da mugunta daga cikinku.
23Idan akwai yarinyar da ke budurwa, da wani ke tashinta, sai wani mutum ya iske ta cikin gari ya kwana da ita,24ku ɗauki dukkansu biyun zuwa ƙofar birni, a jejjefe su su mutu. Dole ku jejjefe yarinyar da duwatsu, saboda bata yi kururuwa ba, koda shike tana cikin gari. Dole ku jejjefe mutumin, saboda ya ɓata matar maƙwabcinsa; kuma dole ku kawar da mugunta daga cikinku.
25Amma idan mutumin ya iske yarinyar a cikin gona, idan ya ɗauke ta da ƙarfi ya kwana da ita, daga nan mutumin kaɗai daya kwana da ita za a kashe.26Amma ga yarinyar ba za ayi mata kome ba; domin bata yi zunubin da ya cancanci mutuwa ba. Gama wannan matsalar na dai-dai da mutumin da ya fãɗa wa maƙwabcinsa ya kashe shi.27Gama ya same ta a cikin gona; ita wadda ake tashinta ta yi kururuwa, amma ba wanda zai cece ta.
28Idan mutum ya iske yarinya wadda take budurwa amma ba a tashinta, idan ya kama ta da ƙarfi ya kwana da ita, idan aka gane su,29shi mutumin da ya kwana da ita dole ya biya shekel hamsin na azurfa ga mahaifin yarinyar, kuma dole ta zama matarsa, saboda ya ƙasƙantar da ita. Ba zai sallame ta ba dukkan kwanakin ransa.
30Kada mutum ya ɗauki matar mahaifinsa a matsayin matarsa; kada kuma ya ɗauke 'yancin auren mahaifinsa.

23

1Ba mutumin da aka yi wa rauni ta wurin dandaƙa ko yanke gabansa da zai shiga taron jama'ar Yahweh.2Shegen ɗa ba zai shiga taron jama'ar Yahweh ba; har tsara ta goma ta zuriyarsa, ba mutum a cikinsu da zai kasance a taron jama'ar Yahweh.

3Ba'ammone ko Bamowabe ba zai zama cikakken mutum a taron jama'ar Yahweh ba; har tsara ta goma ta zuriyarsu, ba wani a cikinsu da zai shiga taron jama'ar Yahweh ba.4Saboda basu zo sun tarye ku da abinci da ruwa ba sa'ad da kuke kan hanyarku lokacin da kuka fito daga Masar, kuma suka yi hayar Bala'am ɗan Beyor daga Fetor cikin Aram Naharayim, ya la'anta ku.
5Amma Yahweh Allahnku bai saurari Bala'am ba; sai Yahweh Allahnku ya juyar da la'anar ta zama albarka dominku, saboda Yahweh Allahnku yana ƙaunarku.6Kada ku taɓa nemar musu zaman lafiya ko wadata, lokacin dukkan kwanakinku.
7Kada kuji ƙyamar Ba'idome, gama shi ɗan uwanku ne; kada ku ƙi Bamasare, domin kunyi baƙunci a cikin ƙasarsa.8Zuriyarsu tsara ta uku da aka haifa masu zasu iya shiga taron jama'ar Yahweh.
9Sa'ad da kuka fita domin ku kafa sansani gãba da maƙiyanku, daganan dole ku kiyaye kanku daga kowanne mugun abu.10Idan a cikinku akwai wani mutum daya ƙazantu saboda abin da ya faru da shi da dare, daganan dole ya fita daga cikin sansanin; kada ya komo cikin sansanin.11Sa'ad da yamma ta yi, dole ya yi wanka cikin ruwa; sa'ad da rana ta faɗi, sai ya dawo cikin sansani.
12Dole ku kasance da wani wuri kuma a bayan sansani in da zaku je;13kuma sai ku kasance da wani abu cikin kayanku da zaku yi gini da shi; sa'ad da kuka tsuguna domin kuyi bayan gari, dole kuyi gini da shi daganan sai ku mayar da ƙasar ku rufe bayan garin da kuka yi.14Gama Yahweh Allahnku yakan yi yawo cikin sansaninku ya baku nasara ya kuma bada maƙiyanku cikin hannunku. Domin haka dole sansaninku ya kasance da tsarki, domin kada ya ga abu mara tsarki a cikinku ya juya daga gare ku.
15Kada ku bada bawan da ya tsere daga ubangijinsa.16Ku bar shi ya zauna tare daku, a cikin kowanne garin da ya zaɓa. Kada ku tsananta masa.
17Kada a sami ko ɗaya daga cikin 'yan'matan Isra'ila, ko 'ya'yansu maza a cikin ƙungiyar karuwanci na addini.18Kada ku kawo kuɗin da aka samu ta wurin karuwanci ko kuɗin da aka samu tawurin yin luɗu a cikin haikalin Yahweh Allahnku domin cika kowanne wa'adi; gama dukkan wannan abin ƙyama ne ga Yahweh Allahnku.
19Kada ku bada bashi da ruwa ga danginku Ba-isra'ile - ribar kuɗi, ribar abinci, kona kowanne irin abu da akan bada shi da ruwa.20Ga wanda ya ke baƙo zaku iya bashi rance da ruwa, domin Yahweh Allahnku yasa maku albarka a kan dukkan abin da kuka sa hannunku ga yi, a cikin ƙasar da zaku shiga ku mallake ta.
21Sa'ad da kuka yi wa'adi ga Yahweh Allahnku, kada kuyi jinkirin cikawa, gama Yahweh Allahnku lallai zai neme shi gare ku; zai zama zunubi a gare ku idan baku cika shi ba.22Amma idan kuka nisanci yin wa'adi, ba zai zama zunubi gare ku ba.23Duk abin da ya fita daga cikin leɓunanku dole ku kula ku aikata; bisa ga yadda kuka alƙawarta ga Yahweh Allahnku, duk abin da kuka alƙawarta da yaddar ranku da bakinku.
24Sa'ad da kuka shiga cikin gonar inabin maƙwabcinku, zaku iya cin inabin 'ya'yan inabin yadda kuke so har ku ƙoshi, amma kada ku sa ko ɗaya a cikin kwandonku.25Sa'ad da kuka shiga cikin hatsin maƙwabcinku daya nuna, zaku iya tsinke kawunan hatsin da hannunku, amma kada ku sa lauje ku yanki hatsin maƙwabcinku da ya nuna.

24

1Idan namiji ya ɗauki mata ya aure ta, idan bata sami tagomashi a idanunsa ba saboda ya sami wani abin aibatarwa da ita, sai dole ya rubuta mata takardar saki, yasa a hannunta, ya sallame ta daga gidansa.2Sa'ad da ta fita daga gidansa, zata iya ta tafi ta zama matar wani.

3Idan mijinta na biyun ya ƙi ta ya kuma rubuta mata takardar saki, yasa mata a hannunta, ya kuma sallame ta daga gidansa; ko kuma mijinta na biyun ya rasu, wato mutumin daya ɗauke ta ta zama matarsa -4sai mijinta na dã, wannan na farko wanda ya fara sallamar ta, ba zai koma ya ɗauke ta ta zama matarsa kuma ba, bayan ta rigaya ta ƙazamtu; domin wannan zai zama abin ƙyama ga Yahweh. Ba zaku sa ƙasar ta zama da laifi ba, ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku abin gado.
5Lokacin da namiji ya ɗauki sabuwar mata, ba zai tafi yaƙi da sauran mayaƙa ba, ba za a kuma umarce shi ya tafi ya yi aikin ƙarfi da yaji ba; yana da 'yanci ya zauna a gida har shekara guda ya faranta wa matarsa da ya aura rai.
6Kada wani ya karɓi jinginar dutsen niƙa ko ɗan dutsen niƙa, domin wannan zai zama karɓar ran mutum ne jingina.
7Idan an kama wani ya saci ɗan'uwansa daga cikin mutanen Isra'ila, ya mai da shi kamar bawa ya saida shi, wannan ɓarawon dole ya mutu; haka zaku kawar da mugunta daga tsakaninku.
8Ku kula game da annobar kuturta, domin ku aikata dai-dai a kowace ka'ida da aka baku, wanda firistoci, da lebiyawa, suka koya maku; kamar yadda na umarce su, haka zaku yi.9Ku tuna da abin da Yahweh Allahnku ya yi wa Maryamu sa'ad da kuke fitowa daga Masar.
10Sa'ad da ka ranta wa makwabcinka wani irin abu, ba zaka shiga cikin gidansa ka ɗauko jinginar ba.11Zaka tsaya a waje, sa'an nan mutumin nan daka ba shi rance zai fito waje ya baka jinginar.
12Idan mutumin matalauci ne, kada jinginarsa ta kwana a hannunka.13Hakika dole zaka mayar masa da jinginarsa kafin faɗuwar rana, domin ya yi barci cikin mayafinsa yasa maka albarka; zai zama adalci dominka a gaban Yahweh Allahnka
14Ba zaka zalumci bawanka ɗan ƙwadago matalauci fakiri ba, ko shi ɗan'uwanka Ba'isra'ile, ko daga baƙi waɗanda ke cikin ƙasarku cikin ƙofofin biranenku;15Dole kowacce rana ka bashi albashinsa; kada rana ta faɗi baka cika wa'adin nan ba, domin matalauci ne zuciyarsa tana kan hakinsa. Kayi wannan domin kada ya yi kuka gãba da kai ga Yahweh, kuma domin kada ya zama zunubin daka aikata.
16Ba za a kashe iyaye saboda 'ya'yansu ba, haka ma 'ya'ya ba za a kashe su saboda iyayensu ba. Maimakon haka, dole ne kowa ya mutu domin nasa zunubin.
17Ba zaka fizgi adalci daya cancanta karfi da yaji daga baƙo ba, ko maraya, ko ka ɗauki mayafin gwauruwa don jingina.18Maimakon haka, zaku tuna ku bayi ne dã a Masar, kuma Yahweh Allahnku ya kuɓutar daku daga can. Saboda haka ina umartar ku kuyi biyayya da wannan doka.
19Sa'ad da kuka girbe amfaninku daga gonakinku, idan kuka manta da dami guda a gonar, kada ku koma domin ku ɗauko shi; dole zai zama domin baƙo, domin marayu, domin gwauruwa, saboda Yahweh Allahnku ya albarkace ku a cikin dukkan aikin hannuwanku.20Sa'ad da kuka kakkaɓe itacen zaitunku, kada ku koma ku rore rassansu, zai zama domin baƙo, da marayu da, kuma gwauruwa.
21Sa'ad da kuka tattara 'ya'yan inabin garkarku, ba zaku yi kalarta kuma ba. Abin da aka bari baya zai zama na baƙo, na marayu, dana gwauruwa.22Dole ne ku tuna dã ku bayi ne a cikin ƙasar Masar. Saboda haka ina umartarku kuyi biyayya da wannan doka.

25

1Idan akwai jayayya tsakanin mutane sai suka tafi kotu, sai al'ƙalai suka shari'anta su, zasu kuɓutar da mai adalci su hukunta mugun.2Idan mai laifi ya cancanci dukã, sai al'ƙali yasa shi ya kwanta ayi masa bulala a gabansa iya ƙididdigar bugun, daya dace da laifinsa.

3Al'ƙali zai iya yi masa bulala arba'in, amma ba zai zarce wannan lambar ba; gama idan ya zarce lambar nan ya bulale shi da abin da yafi haka yawa, to za a ƙasƙantar da ɗan'uwanku Ba'isra'ile a kan idanunku.
4Ba zaku sa wa san da ke casar hatsi takunkumi ba.
5Idan 'yan'uwa maza suna zaune tare sai ɗayan ya rasu, kuma bashi da ɗa, ba za a aurar da matar marigayin ba ga wani a waje wanda baya cikin iyalin. Maimakon haka, dole ɗan'uwan miji marigayi ya kwana da ita ya ɗauke ta ta zama matarsa, ya yi mata abin da ya kamaci ɗan'uwan miji ya yi mata.6Wannan ya zama haka domin ɗan farin da zata haifa zai ci gaba da sunan ɗan'uwa marigayi, domin kada sunansa ya ɓace a Isra'ila.
7Amma idan mutumin baya so ya ɗauki matar ɗan'uwansa, sai matar ɗan'uwan ta tafi ƙofa wurin dattawa ta ce, '‌Ɗan'uwan mijina yaƙi ya wanzar da sunan ɗan'uwansa a Isra'ila; ba zai yi abin da ya kamaci ɗan'uwan miji ya yi mani ba.'8Dole sai dattawan birnin su kira shi suyi masa magana. Amma idan yaƙi ya ce, 'bana so in ɗauke ta.'
9Dole matar ɗan'uwansa ta je wajensa a gaban dattawa, ta cire takalminsa daga ƙafarsa, ta tofa masa miyau a fuskarsa. Zata amsa masa ta ce, 'Wannan shi ne abin da ake yi wa wanda yaƙi gina gidan ɗan'uwansa.'10Za a kira sunansa a Isra'ila, 'Gidan wandan aka saluɓe takalminsa.'
11Idan mutane suka yi faɗa da junansu, sai matar ɗaya daga cikinsu ta zo ta kuɓutar da mijinta daga hannun wanda ya mare shi, idan ta miƙa hannuta ta kama gabansa,12sai dole a yanke hannunta; kada idonku ya ji tausayi.
13Ba zaku riƙe ma'aunan nauyi iri biyu a jakarku ba, da babba da ƙarami.14Ba zaku ajiye a cikin gidanku ma'aunai iri biyu ba, da babba da ƙarami.
15Sai ku kasance da ma'aunin nauyi da ya ke dai dai; mudu na adalci zaku kasance da shi, domin kwanakinku suyi tsawo a cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ke baku.16Domin duk masu yin irin abubuwan nan, duk waɗanda ke aikata rashin gaskiya, abin ƙyama ne ga Yahweh Allahnku.
17Ku tuna da abin da Amalek suka yi maku a hanya sa'ad da kuka fito daga Masar,18yadda suka gamu daku a hanya suka fãɗa wa na bayanku, dukkan marasa ƙarfi na bayanku, sa'ad da kuka some kuka gaji; bai girmama Allah ba.19Saboda haka, sa'ad da Yahweh Allahnku zai baku hutawa daga dukkan maƙiyanku da kewaye, a cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku ku mallaka abin gado, ba zaku manta cewa dole ku shafe tunawa da Amalek daga ƙarƙashin sama ba.

26

1Sa'ad da kuka zo ƙasar da Yahweh Allahnku ke ba ku abin gãdo, kuma lokacin da kuka mallaƙeta kuka zauna cikinta,2sai dole ku ɗauki nunan farinku na dukkan girbin ƙasar wanda kuka kawo cikin gida daga ƙasar da Yahweh Allahnku ke baku. Dole kusa shi a kwando ku je inda Yahweh Allahnku zai zaɓa a matsayin haikalinsa.

3Dole za ku je wajen firist wanda shi ne mai hidima a kwanakin nan kuce masa, 'Ina shaida yau ga Yahweh Allahnka cewa nazo ƙasar da Yahweh ya rantse wa kakanninmu zai bamu.'4Dole firist zai karɓi kwandon daga hannunsa ya ajiye shi a gaban bagadin Yahweh Allahnku.
5Dole ku faɗi haka a gaban Yahweh Allahnku, 'Kakana mayawacin Ba'aramiye ne. Ya gangara zuwa cikin Masar ya zauna a can, kuma mutanensa kima ne. A can ya yi girma, ya ƙasaita, kuma ya zama al'umma mai jama'a.
6Masarawa suka wulaƙanta mu ainun suka tsananta mana. Suka bautar da mu.7Muka yi kuka ga Yahweh, Allah na ubanninmu, ya kuma ji muryarmu, ya dubi azabarmu da wahalarmu, da zalumtarmu da aka yita yi.
8Yahweh ya fitar da mu daga Masar da hannu mai ƙarfi, da damtsensa miƙaƙƙe, da babbar razanarwa, da alamu da kuma al'ajibai;9ya kuma kawo mu nan wajen ya kuma bamu wannan ƙasar, ƙasa wacce take zuba da madara da zuma.
10Duba yanzu, na kawo maka nunan fari na girbin ƙasar da kai, Yahweh, ka bani.' Dole ka ajiye shi a gaban Yahweh Allahnka kayi sujada a gabansa;11kuma dole kayi farinciki cikin dukkan abubuwa nagari da Yahweh Allahnka ya yi dominka, da kuma gidanka - da kai. da kuma Lebiyawa, da baƙon da ke tsakiyarku.
12Bayan kun gama bada dukkan zakkarku ta girbi a shekara ta uku, wato, shekara ta zakka, dole ne kuba Lebiyawa, da baƙo, da maraya, da kuma gwauruwa, domin su ci a ƙofofin biranenku su kuma ƙoshi.13Dole ku ce a gaban Yahweh Allahnku, 'Na kawo waɗannan daga cikin gidana abubuwan da suke na Yahweh, na kuma ba Lebiyawa, da baƙo da maraya, da kuma gwauruwa, bisa ga dukkan umarnai waɗanda ka bani. Ban kuskure ko kaɗan ba daga umarnanka, ban kuma manta da su ba.
14Ban ci ko kaɗan daga cikinsu a cikin baƙin cikina ba, ban kuma aje su a wani wuri marar tsarki ba, ko in miƙa su don girmama matacce. Na saurari muryar Yahweh Allahna; Nayi biyayya da dukkan abin da ka umarce ni in yi.15Ka duba daga wuri mai tsarki inda kake zaune, daga sama, ka albarkaci mutanenka Isra'ila, da ƙasar daka bamu, kamar yadda ka rantse wa ubanninmu, ƙasa wadda take zuba da madara da zuma.'
16Yau, Yahweh Allahnku yana umartarku kuyi biyayya da ka'idodinsa da dokokinsa; saboda haka za ku kiyaye su zaku yi biyayya da su da dukkan zuciyarku da kuma dukkan ranku.17Kun furta yau cewa Yahweh shi ne Allahnku, zaku kuma yi tafiya a tafarkunsa ku kuma kiyaye ka'idodinsa, da umarnansa da dokokinsa, cewa kuma zaku kasa kunne da muryarsa.
18Yau Yahweh ya furta cewa ku mutane ne waɗanda mallakarsa ce, kamar yadda ya alƙawarta maku, cewa zaku yi biyayya da dukkan umarnansa,19zai fifita ku sama da dukkan sauran al'umman da ya yi, zaku kuma sami yabo, da suna, da daraja. Zaku zama mutanen da aka keɓe su ga Yahweh Allahnku, kamar yadda ya faɗi."

27

1Musa da dattawan Isra'ila suka umarci mutanen suka ce, "Ku kiyaye dukkan umarnan dana umarce ku yau.2A ranar da zaku tsallake Yodan zuwa ƙasar da Yahweh Allahnku ke baku, sai dole ku kafa manyan duwatsu ku shafe su da farar ƙasa.3Dole ne ku rubuta a kansu dukkan maganganun dokokin nan sa'ad da kuka rigaya kuka ƙetare; domin ku tafi cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ke baku, ƙasa mai zubar da madara da zuma, kamar yadda Yahweh, Allahn kakanninku ya yi maku alƙawari.

4Sa'ad da kuka ƙetare Yodan, ku kafa waɗannan duwatsu da nake umartanku yau, a kan Dutsen Ibal, ku shafe su da farar ƙasa.5A can zaku gina bagadi ga Yahweh Allahnku, bagadi na duwatsu; amma ba zaku yi amfani da alatu na ƙarfe ku sassaƙa duwatsun ba.
6Dole ku gina wa Yahweh Allahnku bagadin da ba a sassaƙa duwatsun ba. Dole ku miƙa baye-baye na ƙonawa a kansa ga Yahweh Allahnku,7zaku miƙa hadayar baye-baye na zumunci ku kuma ci a can; zaku yi farinciki a gaban Yahweh Allahnku.8Zaku rubuta dukkan waɗannan maganganu na wannan dokoki a kan duwatsu su fita a fili sosai."
9Musa da firistoci, da Lebiyawa, suka yi magana da dukkan Isra'ilawa suka ce,10"Kuyi shuru ku saurara, ya Isra'ila: Yau kun zama mutanen Yahweh Allahnku. Saboda haka dole kuyi biyayya da muryar Yahweh Allahnku ku kuma yi biyayya da umarnansa da dokokinsa waɗanda nake umartan ku yau."
11Musa ya umarci mutanen a ranan nan ya ce,12"Waɗannan kabilu dole su tsaya a kan Dutsen Gerizim su albarkaci mutane bayan kun ƙetare Yodan: Simiyon, da Lebi, da Yahuda, da Isakar, da Yosef, da kuma Benyamin.
13Waɗannan su ne kabilun da dole su tsaya a kan Dutsen Ibal su furta la'anu: Ruben, da Gad, da Ashar, da Zebulun, da Dan da kuma Naftali.14Lebiyawa zasu amsa su cewa dukkan mutanen Isra'ila da murya mai ƙafi:
15Bari mutumin ya zama la'ananne wanda ya siffanta ko ya yi zubin ƙarfe, abin ƙyama ga Yahweh, aikin hannun gwanin masassaƙi, wanda ya kafa shi a asirce.' Dole ne dukkan mutane su amsa su ce, 'Amin.'
16'Bari mutumin ya zama la'ananne wanda bai girmama mahaifinsa da mahaifiyarsa ba.' Daganan dole ne dukkan mutane su ce, 'Amin.'17'Bari mutumin ya zama la'ananne wanda ya cire shaidar iyakar makwabcinsa.' Daganan dole ne dukkan mutane su ce, 'Amin.'
18Bari mutumin ya zama la'ananne wanda yasa makaho ya saki hanya.' Sai dole mutanen su ce,; Amin.'19Bari mutumin ya zama la'ananne wandan karfi da yaji ya ƙwace adalci daga baƙo, maraya, ko gwauruwa.' Daganan dole ne dukkan mutane su ce. 'Amin.'
20'Bari mutumin nan ya zama la'ananne wanda ya kwana da matar mahaifinsa, domin ya karɓe hakkin mahaifinsa.' Daganan sai dukkan mutane su ce, 'Amin.'21'Bari mutumin nan ya zama la'ananne wanda ya kwana da kowacce irin dabba.' Daganan dole ne dukkan mutane su ce, 'Amin.'
22'Bari mutumin nan ya zama la'ananne wanda ya kwana da 'yar'uwarsa, ɗiyar mahaifinsa, ko ɗiyar mahaifiyarsa.' Daganan dukkan mutane dole su ce, 'Amin.'23'Bari mutumin nan da zai kwana da surukarsa ya zama la'ananne.' Daganan dukkan mutane dole su ce, 'Amin.'
24Bari mutumin nan ya zama la'ananne wanda ya kashe makwabcinsa a ɓoye.' Sai dole dukkan mutane su ce, 'Amin.'25'Bari mutumin nan ya zama la'ananne wanda zai karɓi toshiya domin ya kashe da mutum marar laifi.' Sai dole dukkan mutane su ce, 'Amin.'
26'Bari mutumin nan ya zama la'ananne wanda ba zai yi biyayya da shariɗun nan ba.' Sai dole dukkan mutane su ce, 'Amin.'

28

1Idan kuka saurari muryar Yahweh Allahnku da kirki domin ku kiyaye dukkan dokokin nan da nake umartan ku yau, Yahweh Allahnku zai fifita ku fiye da dukkan sauran al'umman duniya.2Dukkan waɗannan albarku zasu zo bisanku har ma suyi amabaliya, idan kuka saurari muryar Yahweh Allahnku.

3Zaku zama da albarka cikin birni, kuma zaku zama da albarka a jeji.4'Ya'yanku zasu zama da albarka, ƙasarku zata zama da albarka wajen bada amfani, da'ya'yan dabbobinku, shanunku zasu yi yabanya, haka ma 'ya'yan tumakinku.
5Kwandunanku zasu zama da albarka, haka ma wurin kwaɓar wainarku.6Zaku shiga da albarka, ku fita da albarka.
7Yahweh zai sa maƙiyanku da suka tashi gãba daku a buge su a gaban ku; zasu tasar maku ta gefe guda amma zasu gudu daga gaban ku ta hanyoyi bakwai.8Yahweh zai umarta albarka ta zo bisanku a cikin rumbunanku, kuma da cikin dukkan abin da kuka sa hannunku; zai albarkace ku a cikin ƙasar da ya ke ba ku.
9Yahweh zai kafa ku a matsayin mutanen daya keɓe domin kansa, kamar yadda ya rantse maku, idan kuka kiyaye umarnan Yahweh Allahnku, kuma kuka yi tafiya a hanyoyinsa.10Dukkan al'umman duniya zasu ga ana kiranku da sunan Yahweh, zasu kuwa ji tsoronku.
11Yahweh zai azurta ku ainun, da 'ya'yan jikinku, da 'ya'yan shanunku, da amfanin ƙasa, a ƙasar da ya rantse wa ubanninku zai baku.12Yahweh zai buɗe maku rumbunsa na sammai ya baku ruwa domin ƙasarku a dai-dai lokaci, ya kuma albarkaci dukkan aikin hannuwanku; zaku ranta wa al'ummai da yawa, amma ku ba zaku karɓi rance ba.
13Yahweh zai saku zama kai, ba wutsiya ba; zaku kasance kullum a bisa, ba a ƙasa ba, idan kun kasa kunne ga umarnan Yahweh Allahnku da nake umartanku yau., domin ku lura ku yi su,14kuma idan baku juya daga waɗannan maganganu da nake umartanku a yau, ga hannun dama ko hagu ba, har da zaku bi waɗansu alloli ku bauta masu.
15Amma idan baku saurari muryar Yahweh Allahnku, kuka kiyaye dukkan umarnansa da ka'idodinsa da nake umartan ku yau ba, to dukkan waɗannan la'anu zasu afka maku su mamayeku.
16La'anannu zaku zama cikin birni, la'anannu zaku zama a jeji.17La'ana za ta bi kwandonku da kuma makwabar wainarku.
18'Ya'yanku zasu zama la'anannu, amfanin gonakinku zasu zama la'anannu, da 'yan maruƙanku da 'ya'yan garken tumakinku.19La'anannu ne ku sa'ad da kuka shiga, la'anannu ne ku sa'ad da kuka fita.
20Yahweh zai aiko maku la'ana, ruɗewa, da kwaɓa a dukkan abin da kuka ɗibiya hannunku, har sai kun lalace har sai kun hallaka nan da nan sabili da miyagun ayyukanku ta yadda kuka yashe ni.21Yahweh zai sa annoba ta manne maku har sai ya hallaka ku daga ƙasar da kuke tafiya zuwa cikin ta ku mallaka.
22Yahweh zai buge ku da annobai masu yaɗuwa, zazzaɓi, da marurai, da fãri, da zafin rana, da iska mai ƙuna, da kuturta. Waɗannan zasu runtume ku har sai kun hallaka.
23Samaniyar da ke kanku zata zama tagulla, ƙasar kuma da ke ƙarƙashinku zata zama ƙarfe.24Yahweh zai maida ruwan saman ƙasarku gari da ƙura; daga sammai zasu sabko kanku, har sai kun hallaka.
25Yahweh zai sa a buge ku a gaban maƙiyanku; za ku fita ta hanya guda gãba da su zaku guje daga gabansu ta hanyoyi bakwai. Za a yi ta kora ku gaba da baya cikin dukkan mulkokin duniya.26Gawawakinku za su zama abinci ga dukkan tsuntsayen sama da dabbobin duniya; ba wanda zai tsorata su su gudu.
27Yahweh zai far maku da maruran Masar da gyambuna, da ƙusumbi, da ƙaiƙayi wanda ba za a iya warkar daku daga su ba.28Yahweh zai buge ku da ciwon hauka, da makamta, da rikicewar hankali.29Zaku yita lalubawa da tsakar rana kamar yadda makaho ya ke yi a duhu, ba zaku azurta ba a ayyukanku; kullum za ayi ta zalumtarku ana maku ƙwace, ba kuma wanda zai cece ku.
30Zaku yi tashin matã, amma wani namiji zai ƙwace ta ya yi mata fyaɗe. Zaku gina gida amma ba zaku zauna a ciki ba; zaku noma garkar inabi amma ba zaku ji daɗin 'ya'yansa ba.31Za a yanka san nomanku a kan idanunku; amma ba zaku ci namansa ba; za a karɓe jakinku ƙiri ƙiri ƙarfi da yaji ba za a kuma mayar maku ba. Za a bada tumakinku ga magabtanku, ba ko ɗaya da zaku samu ya taimaka maku.
32Za a bada 'ya'yanku maza da mata ga wasu mutane; idanunku zasu neme su dukkan rana, amma za su gaji da sa zuciya. Hannuwanku zasu yi rauni.
33Girbin ƙasarku da dukkan wahalarku - wata al'ummar da baku santa ba zata cinye su; kullum za a zalumce ku a murƙushe ku,34haka zaku haukace tawurin abin da ya zama dole ku ga ya faru.35Yahweh zai bugi gyiwowinku da ƙafafunku da marurai wanda ba za a iya warkar daku daga su ba, daga tafin kafafunku har ƙolƙolin kanku.
36Yahweh zai ɗauke ku da sarkin da zaku naɗa bisa kanku zuwa wata al'umma da baku santa ba, koku ko kakanninku; a can zaku yi sujada ga allolin itace da duwatsu.37Zaku zama ban tsoro, da karin magana, da gatse, cikin dukkan mutane inda Yahweh zai kora ku.
38Zaku kai hatsi da yawa gona, amma zaku sami amfanin hatsin kaɗan, gama fãri zasu cinye su.39Zaku dasa garkunan inabi ku kuma noma su, amma ko kaɗan ba zaku sha ruwansu ba, ba ma zaku girbi 'ya'yansu ba, gama tsutsotsi zasu cinye su.
40Zaku kasance da itatuwan zaitun a dukkan yankinku, amma ba zaku shafa ko ɗan man a jikinku ba, gama itatuwan zaitunku zasu zubar da 'ya'yansu.41Zaku haifi 'ya'ya maza da mata, amma ba zasu zama naku ba, gama zasu tafi bautar talala.
42Dukkan itatuwanku da amfanin ƙasarku - fãri za su mamayesu.43Baƙon da ke tsakiyarku zai yi ta ƙaruwa fiye daku gaba gaba; amma ku zaku yi ta komawa baya baya.44Zai ranta maku, amma ku ba za ku ranta masa ba; shi zai zama kai, ku kuwa zaku zama wutsiya.
45Dukkan waɗannan la'anu zasu afko kanku su bi ku su chafke ku har sai sun hallaka ku. Wannan zai faru domin ba ku saurari muryar Yahweh Allahnku ba, da zaku kiyaye umarnansa da farillansa daya umarce ku.46Waɗannan la'anu suna kanku a matsayin alamu da al'ajibai, da kuma kan zuriyarku har abada.
47Saboda baku yi sujada ga Yahweh Allahnku tare da murna da farin cikin zuciya lokacin yalwarku ba,48domin wannan fa, zaku bauta wa maƙiyan da Yahweh zai aiko gãba da ku; zaku bauta masu da yunwa, cikin ƙishirwa, cikin tsiraici, da cikin talauci. Zai ɗibiya maku karkiyar ƙarfe a wuyanku har sai ya hallaka ku.
49Yahweh zai aiko da wata al'umma gãba daku daga nesa, daga ƙarshen duniya, kamar yadda gaggafa takan fyauce abincinta, al'ummar da baku fahimci harshenta ba;50al'umma da fuskarta abin ban razana ne waɗanda bata ganin kwarjinin tsoffi ko ta nuna alfarma ga matashi.51Zasu cinye 'yan maruƙanku da amfanin ƙasarku har sai sun hallaka ku. Ba zasu bar maku hatsi ba, ko sabon ruwan inabi, ko mai, ko 'yan maruƙanku na shanu ko na tumaki, har sai sun saku ku lalace.
52Zasu yi maku kwanto a dukkan ƙofofin biranenku, har sai tsararrun ganuwowinku masu tsayi sun faɗi a koina a ƙasarku, garu waɗanda kuka dogara a gare su. Zasu kafa maku dãga a dukkan ƙofofin biranenku a dukkan iyakar ƙasar da Yahweh Allahnku ya baku.53Zaku ci 'ya'yan da kuka haifa, naman 'ya'yanku maza da na 'ya'ya mata, waɗanda Yahweh Allahnku ya baku, a cikin kwanto da wahalai waɗanda maƙiyanku zasu ɗibiya maku.
54Mutum mai taushin zuciya kuma mai kula da ke tare daku-zai ji kyashin ɗan'uwansa da matarsa da ya ke ƙauna, da dukkan yaransa da suka rage.55Ba zai ba ko ɗayansu naman 'ya'yan jikinsa da zai ci ba, domin ba abin da zai rage ya ci don kansa a cikin kwanto da wahalai da maƙiya suka ɗibiya maku a dukkan ƙofofin biranenku.
56Mace mai taushin zuciya mai kula da ke a cikinku, wanda ba za ta kuskura ta aje tafin sawunta a ƙasa saboda taushin zuciya da kyakkyawan hali - zata ji kyashin mijinta da take ƙauna, da ɗanta, da ɗiyarta,57da sabon jaririnta da ya fito ta tsakanin ƙafafunta, da 'ya'ya waɗanda zata haifa. Zata cinye su a ɓoye domin babu abinci, a cikin kwanto da wahalai waɗanda maƙiyanku zasu ɗibiya maku a ƙofofin biranenku.
58Idan ba ku kiyaye dukkan maganganun dokokin da aka rubuta cikin wannan littafi ba, domin ku girmama wannan suna mai ɗaukaka da banrazana, Yahweh Allahnku,59sai Yahweh ya tsananta annobarku, dana zuriyarku; za a yi maku manyan annobai, masu tsawon lokaci, cututuka masu azabtarwa, na dogon lokaci.
60Zai sake maido da dukkan cututukan Masar bisa kanku waɗanda kuka ji tsoronsu; zasu manne maku.61Kuma kowacce cuta da annoba da ba a rubuta a wannan littafin shari'a ba, su kuma Yahweh zai kawo bisa kanku har sai kun hallaka.62'Yan kaɗan zaku ragu, koda shike dã kuna kamar taurarin sammai a yawa, saboda baku saurari muryar Yahweh Allahnku ba.
63Kamar yadda dã Yahweh ya yi farinciki da yi maku kirki, ya riɓaɓɓanya ku, haka ma zai yi farinciki da saku ku lalace da kuma hallakar daku. Za a tumbuƙe ku daga ƙasar da kuke tafiya ku mallaka.64Yahweh zai warwatsar daku cikin dukkan al'ummai daga wannan bangon duniya zuwa wancan bangon duniya; a can za ku yi sujada ga allolin da baku taɓa sani ba, ko ku, ko kakanninku, allolin itace da dutse.
65Ba zaku sami sakewa wurin waɗannan al'umman ba, kuma babu hutawa ga tafin ƙafafunku; maimakon haka, Yahweh zai baku a can zuciya mai fargaba, idanu marasa gani, da rai mai makoki.66Ranku zai kasance cikin shakka a gabanku; zaku zauna cikin tsoro kowanne dare da rana baku da tabbas ko kaɗan a dukkan rayyuwarku.
67Da safe zaku ce, 'Ina ma maraice ne!' da maraice zaku ce, 'Ina ma safiya ce!' saboda da tsoro a zukatanku da abubuwan da dole idanunku su gani.68Yahweh zai dawo daku cikin Masar a jiragen ruwa, ta hanyar dana riga na faɗa maku, 'Ba zaku ƙara ganin Masar ba.' A can zaku miƙa kanku domin saye ga maƙiyanku bayi maza da mata, amma ba wanda zai saye ku."

29

1Waɗannan su ne maganganun da Yahweh ya umarta wa Musa ya faɗi wa 'ya'yan Isra'ila a ƙasar Mowab, maganganu da aka ƙara a kan alƙawarin da ya yi da su a Horeb.

2Musa ya kira dukkan Isra'ila ya ce masu, "Kun dai ga dukkan abin da Yahweh ya yi a kan idanunku a ƙasar Masar ga Fir'auna, da dukkan barorinsa da dukkan ƙasarsa -3manyan wahalai da idanunku suka gani, da alamu, da waɗannan dukkan al'ajibai.4Har wa yau Yahweh bai baku zuciya ta sani ba, idanu domin a gani, ko kunnuwa domin ji.
5Na bisheku a jeji shekaru arba'in, rigunanku basu tsufa a jikinku ba, takalmanku ma basu tsufa a ƙafafunku ba.6Baku ci waina ba, baku sha ruwan inabi ba, ko barasa mai sa maye, domin ku sani nine Yahweh Allahnku.
7Sa'ad da kuka zo wannan wurin, Sihon, sarkin Hesbon, da Og sarkin Bashan, suka fito suyi yaƙi gãba daku, muka buga su.8Muka karɓe ƙasarsu muka ba Rubenawa, da Gadawa, da rabin kabilar Manasa.9Saboda haka, ku kiyaye waɗannan maganganun alƙawari ku aikata su, domin ku azurta cikin dukkan abubuwan da zaku yi.
10Kuna tsaye yau, dukkanku, a gaban Yahweh Allahnku, da sarkinku, da kabilunku, da dattawanku, da shugabanninku-da dukkan mazajen Isra'ila,11da 'yan ƙanananku, da matanku, da baƙi waɗanda suke zaune a tsakiyarku cikin zangonku, da shi wanda ke saro maku itace da mai‌ ɗibar maku ruwa.
12Kuna nan domin ku ƙulla alƙawari da Yahweh Allahnku da rantsuwa da Yahweh Allahnku ya ke yi da ku yau,13domin ya maishe ku yau mutane na kansa, domin kuma ya zama Allahnku, kamar yadda ya yi maku magana, kamar kuma yadda ya rantse wa kakanninku, ga Ibrahim, ga Ishaku, ga kuma Yakubu.
14Domin bada ku kaɗai nake yin wannan alƙawari da rantsuwa ba -15da kowannenku da ke tsaye tare da mu yau a gaban Yahweh Allahnmu - amma da kuma waɗanda basa nan tare da mu a yau.16Kun sani mun zauna a ƙasar Masar, da yadda muka biyo ta tsakiyar al'ummai waɗanda kuka wuce.
17Kun ga allolinsu masu banƙyama da aka yi su da itace da dutse, azurfa da zinariya, da ke tsakiyar su.18Ku tabbata ba wani a cikinku, wani mutum, mata, iyali, ko kabila da zuciyarsa take juyawa daga Yahweh Allahnmu, ya tafi ya yi sujada ga allolin waɗancan al'umman. Ku tabbata ba wani tushe a cikinku mai ba da ɗaci da dafi.19Lokacin da mutumin nan yaji maganganun la'anan nan, zai albarkaci kansa ya ce a zuciyarsa, "Zan sami salama koda shike zan yi tafiya cikin taurin zuciyata.' Wannan zai haddasa hallaka mai adalci tare da mugu.
20Yahweh ba zai gafarta masa ba, fushin Yahweh da kishinsa zai auka wa mutumin nan, kuma dukkan la'anan da aka rubuta a littafin nan zasu bi ta kansa, Yahweh zai shafe sunansa daga ƙarƙashin sama.21Yahweh zai ware shi domin bala'i daga dukkan kabilun Isra'ila, domin kiyaye dukkan la'ana na alƙawari da aka rubuta cikin wannan littafin dokoki.
22Tsara mai zuwa, yaranku da zasu tashi a bayanku da baƙon da zai zo daga ƙasa mai nisa, zasu yi magana sa'ad da suka ga annobai a kan ƙasannan da cututukan da Yahweh yasa mata ciwo -23sa'ad da suka ga dukkan ƙasar ta zama wuta da ƙibiritu, inda ba shuki ko ya bada 'ya'ya, inda ba tsiro, kamar sa'ad da aka kaɓar da Soduma da Gomarata, Adma da Zeboyim, waɗanda Yahweh ya hallakar cikin fushinsa da hasalarsa. -24zasu ce tare da dukkan wasu al'ummai, 'Meyasa Yahweh ya yi wa ƙasar nan haka? Mene ne ma'anar zafin hasalar nan?'
25Sa'annan mutane zasu ce, 'Domin sun watsar da alƙawarin Yahweh, Allahn kakanninsu, da ya yi da su lokacin daya fitar da su daga ƙasar Masar,26kuma domin sun tafi sun bauta wa wasu alloli suka russuna masu, allolin da basu sani ba ba kuma shi ya basu ba.
27Saboda haka fushin Yahweh ya yi ƙuna akan wannan ƙasa, har ya kawo a kanta dukkan la'anar da aka rubuta a littafin nan.28Yahweh ya tumbuƙe su daga ƙasarsu cikin fushi, da hasala, da fushi mai ƙuna, ya kuma jefar da su cikin wata ƙasa, har wa yau.'
29Sanin abubuwan asiri na Yahweh Allahnmu ne kaɗai; amma abubuwan da aka bayyana su namu ne har abada mu da kuma zuriyarmu, domin mu aikata dukkan maganganun waɗannan dokoki.

30

1Sa'ad da dukkan waɗannan abubuwa suka zo kanku, albarku da la'ana dana sa a gabanku, kuma sa'ad da kuka tuna da su yayin da kuna cikin dukkan al'ummai inda Yahweh Allahnku ya kora ku,2sa'ad da kuma kuka koma ga Yahweh Allahnku kuka yi biyayya da muryarsa, kuna yin dukkan abin da na umarce ku yau - ku da 'ya'yanku, - da dukkan zuciyarku da kuma dukkan ranku,3sa'an nan Yahweh Allahnku zai komo daku daga bautar talala ya yi juyayinku; zai juya ya tattaroku daga cikin dukkan al'ummai da Yahweh Allahnku ya warwatsa ku.

4Idan korarrun mutanenku suna cikin manisantan wuraren ƙasa da sammai, daga can Yahweh Allahnku zai tattara ku, kuma daga can zai kawo ku.5Yahweh Allahnku zai kawo ku cikin ƙasar da kakanninku suka mallaka, kuma zaku sake mallakarta; zai yi maku alheri ya riɓaɓɓanya ku fiye da yadda ya yi da kakanninku.
6Yahweh Allahnku zai yi wa zuciyarku kaciya da ta zuriyarku, domin ku ƙaunaci Yahweh Allahnku da dukkan zuciyarku da dukkan ranku, domin ku rayu.7Yahweh Allahnku zai sa dukkan waɗannan la'ana a kan maƙiyanku da kan waɗanda suke ƙin ku, waɗanda suka tsananta maku.8Zaku juyo kuyi biyayya da muryar Yahweh, kuma zaku aikata dukkan umarnansa da nake umartar ku yau.
9Yahweh Allahnku zai yalwata dukkan aikin hannunku, da 'ya'yan jikinku, da 'yan maruƙanku, da amfanin gonakinku, domin wadata; gama Yahweh zai sake yin farin ciki a kanku ya azurta ku, kamar yadda ya yi farinciki da ubanninku.10Zai yi wannan idan kuka yi biyayya da muryar Yahweh Allahnku, kuka kiyaye umarnansa da sharuɗansa da ke rubuce cikin littafin dokokin nan, idan kuka juyo ga Yahweh Allahnku da dukkan zuciyarku da dukkan ranku.
11Domin wannan umarni da nake umartan ku yau baifi ƙarfin ku ba, kuma bai yi nisa har da ba zaku kama ba.12Ba a sama ya ke ba, har da zaku ce, 'Wa zai je can sama domin mu ya sauko mana da ita yasa mu iya jinta, domin mu yi ta?'
13Kuma ba a ƙarshen ruwaye ya ke ba, da zaku ce, 'Wa zai haye ruwaye domin mu ya kawo mana ita yasa mu mu jita, domin mu aikata ta?'14Amma maganar tana kurkusa da kai, a bakinka da kuma zuciyarka, domin ka aikata ta.
15Duba, yau nasa a gabanku rai da nagarta, mutuwa da mugunta.16Idan kun yi biyayya da dokokin Yahweh Allahnku, waɗanda nake umartanku yau ku ƙaunaci Yahweh Allahnku, ku yi tafiya a tafarkunsa, ku kuma kiyaye umarnansa, da ka'idodinsa da kuma farillansa, zaku rayu ku riɓaɓɓanya, kuma Yahweh Allahnku zai albarkace ku cikin ƙasar da kuke shigarta domin ku mallaka.
17Amma idan zuciyarku ta juya, baku saurara ba a maimako kuka janye kuka russuna wa waɗansu alloli kuka yi masu sujada,18to yau ina maku shela cewa ba shakka zaku lalace; ba zaku yi tsawon kwanaki ba cikin ƙasar da kuke ƙetare Yodan domin ku shiga cikinta ku mallaka.
19Na kira sama da ƙasa suyi shaida gãba daku yau, cewa na ajiye a gabanku rai da mutuwa, albarku da la'ana; saboda haka ku zaɓi rai domin ku rayu, daku da zuriyarku.20Kuyi wannan don ku ƙaunaci Yahweh Allahnku, kuyi biyayya da muryarsa, ku kuma manne masa. Gama shi ne ranku da tsawon kwanakinku; kuyi haka domin ku zauna cikin ƙasar da Yahweh ya rantse wa kakanninku, ga Ibrahim, ga Ishaku, ga Yakubu kuma, zai ba su."

31

1Musa ya tafi ya faɗa wa Isra'ila waɗannan maganganu.2Ya ce masu, "Yanzu ina da shekaru ɗari da ashirin bana iya shiga in fita; Yahweh ya ce mani, 'Ba zaka ƙetare wannan Yodan ba.'3Yahweh Allahnku, zai sha gabanku; Zai hallaka waɗannan al'ummai a gaban ku, zaku ƙwace mallakarsu. Yoshuwa, zai jagorance ku, kamar yadda Yahweh ya faɗi.

4Yahweh zai yi masu kamar yadda ya yi wa Sihon da kuma Og, sarakunan Amoriyawa, da kuma ƙasarsu, waɗanda ya hallakar.5Yahweh zai baku nasara a kansu sa'ad da zaku kara da su a yaƙi, zaku yi masu dukkan yadda na umarce ku.6Ku ƙarfafa kuyi ƙarfin hali, kada ku ji tsoro, kada kuma ku firgita domin su; gama Yahweh Allahnku, shi ne wanda ya ke tafiya tare daku; ba zai kunyatar daku ba ko ya yashe ku."
7Musa ya kira Yoshuwa a gaban dukkan Isra'ila ya ce masa, "Ka ƙarfafa kayi karfin hali, gama zaka tafi da mutanen nan cikin ƙasar da Yahweh ya rantse wa kakanninsu zai basu; zaka sasu su gaje ta.8Yahweh, shi ne wanda ya sha gabanku; zai kasance tare daku; ba zai kunyatar daku ba ba zai yashe ku ba; kada ku ji tsoro, kada ku karaya."
9Musa ya rubuta wannan doka yaba firistoci, 'ya'yan Lebi, waɗanda suke ɗaukar akwatin alƙawari na Yahweh; ya kuma ba dukkan dattawan Isra'ila.10Musa ya umarce su ya ce, "A ƙarshen kowacce shekara bakwai, lokacin da aka ƙayyade domin kashe basussuka, lokacin Idin Rumfuna,11lokacin da dukkan Isra'ila ke zuwa su bayyana a gaban Yahweh Allahnku a wurin da zai zaɓa domin haikalinsa, zaku karanta wannan doka a gaban dukkan Isra'ila a kunnuwansu.
12A tara mutane, da maza, da mata, da 'yan ƙanana, da baƙon da ya ke a cikin ƙofar birninku, domin su ji su koya, domin kuma su girmama Yahweh Allahnku su kiyaye dukkan maganganun wannan dokoki.13Kuyi wannan domin 'ya'yansu da ba su sani ba, su ji su koya su girmama Yahweh Allahnku, dukkan kwanakin da zaku kasance a ƙasar nan da kuke ƙetare Yodan domin ku mallaketa."
14Yahweh ya cewa Musa, "Duba rana tana zuwa, da dole ka mutu; ka kira Yoshuwa ku nuna kanku a rumfar taruwa, domin in ba shi umarni." Sai Musa da Yoshuwa suka tafi suka nuna kansu a rumfar taruwa.15Sai Yahweh ya bayyana a umudin girgije; umudin girgijen ya tsaya a bakin ƙofar rumfa.
16Yahweh ya cewa Musa, "Duba, zaka yi barci tare da ubanninka; waɗannan mutane zasu tashi suyi kamar karuwai su bi waɗansu baƙin alloli waɗanda ke a tsakaninsu a cikin ƙasar da zasu. Zasu yasheni su karya alƙawarin da nayi da su.
17Sa'annan, a ranar nan, fushina zai yi ƙuna a kansu zan kuwa yashe su. Zan ɓoye fuskata za a kuma hallaka su. Masifu da wahalai zasu auka masu zasu ce a ranan nan, 'Ba waɗannan masifu sun zo kanmu domin Allahnmu ba shi tare da mu ba?'18Hakika zan ɓoye fuskata daga gare su a ranar nan, saboda dukkan muguntar da zasu aikata, domin sun juya ga waɗansu alloli.
19Saboda haka yanzu fa, ka rubuta wannan waƙa domin kanku ka koya wa mutanen Isra'ila. Ka sa a bakinsu, domin wannan waƙa ta zama shaida gãba da mutanen Isra'ila.20Gama bayan na kawo su cikin wannan ƙasar dana rantse zan ba kakaninsu ƙasa mai zuba da madara da zuma, bayan sun ci sun ƙoshi sun yi ƙiba, zasu juya ga wasu alloli su kuma bauta masu su rena ni su karya alƙawarina.
21Sa'ad da mugayen abubuwa da wahalai suka zo kan mutanen nan wannan waƙa za ta faɗa a gabansu ita ce shaida (gama ba za a manta ta ba a bakunan tsararrakinsu). Gama na san shirye-shiryen da suke ƙuƙƙullawa yau, tun ma kafin in kawo su ƙasar dana alƙawarta masu."
22Sai Musa ya rubuta wannan waƙa a ranan nan ya kuma koya wa mutanen isra'ila.23Yahweh ya ba Yoshuwa ɗan Nun umarni ya ce, "Ka ƙarfafa kayi ƙarfin hali; gama zaka kawo mutanen Isra'ila cikin ƙasar dana rantse masu, zan kuma kasance tare da kai."
24Da Musa ya gama rubuta waɗannan maganganun shari'a a cikin littafi,25sai ya umarci Lebiyawa masu ɗaukar akwatin alƙawari na Yahweh, ya ce,26"Ku ɗauki wannan littafin sharia ku aje shi a gefen akwatin alƙawari na Yahweh Allahnku, domin ya kasance a can ya zama maku shaida gãba da ku.
27Gama na san tayarwarku da taurin kanku; duba, da raina ma ina tare daku yau, kuna tawaye gãba da Yahweh; ballantana bayan na mutu?28Ku tattaro mani dattawan kabilunku, da shugabanninku, domin in faɗi maganganun nan a kunnuwansu in kira sama da ƙasa suyi shaida gãba da su.29Gama na sani bayan rasuwata zaku ƙazamtar da kanku zaku kauce ku bar tafarkin dana umarce ku; Masifa zata auka maku cikin kwanaki masu zuwa. Wannan zai faru domin zaku yi abin mugunta a idon Yahweh, har da zaku cakune shi ya yi fushi ta wurin aikin hannuwanku."
30Musa ya maimaita maganganun wannan waƙa a kunnuwan dukkan taron Isra'ila har sai da suka ƙare.

32

1Ku saurara, ku sammai, bari in yi magana. Bari duniya ta saurari maganganun bakina.2Bari koyarwata ta zubo kamar ruwan sama, bari maganata ta zubo kamar raɓa, kamar yayyafi a kan ɗanyar ciyawa, kamar ɗiɗɗigar ruwa akan shuke-shuke.

3Domin zan yi shelar sunan Yahweh, kuma in faɗi girman Allanmu.4Dutse ne, aikinsa cikakke ne; gama duk hanyoyinsa na adalci ne. Shi Allah mai aminci ne, marar zunubi. Mai adalci ne nagari kuma.
5Sun aikata mugunta gãba da shi. Ba 'ya'yansa ba ne. Abin ƙasƙancinsu ne. Su kam kangararru ne karkatacciyar tsara.6Haka zaku rama wa Yahweh, ku wawayen mutane marasa tunani? Shi ba mahaifinku bane, wanda ya hallice ku? Shi ya yi ku ya kuma kafa ku.
7Ku tuna da kwanakai da lokatan dã, ku tuna da shekaru na zamanai da yawa da suka wuce. Ku tambayi mahaifinku zai nuna maku, dattawanku zasu kuma gaya maku.8Lokacin da Maɗaukaki yaba al'ummai gadonsu - sa'ad da ya raba 'yan adam, ya rabawa al'ummai wurin zamansu, kamar yadda ya san yawan allolinsu.
9Gama rabon Yahweh mutanensa ne; Yakubu shi ne rabon gadonsa.10Ya same shi a cikin hamada, a cikin ƙasa marar amfani, wurin kuka a jeji; ya kare shi ya lura da shi, ya tsare shi kamar kwayar idonsa.
11Kamar yadda gaggafa take tsare sheƙarta tana shawagi bisa 'ya'yanta, haka Yahweh ya buɗe fuka- fukansa ya ɗauke su, ya tafi da su a kan kafaɗarsa.12Yahweh kaɗai ya bishe su; babu baƙon allah tare da su.
13Ya sa shi ya hau manyan tuddai na ƙasar, ya ciyar da shi da 'ya'yan itatuwan saura; ya yi kiwonsu da zuma daga dutse, da mai daga dutsen daya tsage..
14Ya sha man shanu daga garke kuma ya sha madara daga garken tumaki, daga ƙibar 'yan tumaki, ragunan Bashan da awakai, da lallausar garin alkama - kuka sha ruwan inabi mai kumfa da aka yi da ruwan 'ya'yan itacen inabi.
15Amma Yeshurun ya yi ƙiba ya yi hauri - ka yi ƙiba, ka ma zarce da ƙiba, ka ci isasshe - sai ya yashe da Allahn da ya yi shi, yaƙi Dutsen cetonsa.16Suka sa Yahweh ya ji kyashi ta wurin baƙin allolinsu; da abubuwan ƙyamarsu suka sa shi fushi.
17Suka yi wa al'jannu hadaya, waɗanda ba Allah ba - allolin da basu sani ba, sabobbin alloli, gumakun da ubanninku basu ji tsoro ba.18Kuka yashe da Dutsen, daya zama maku mahaifi, kuka manta da Allahn daya haife ku.
19Yahweh ya ga haka ya kuma ƙi su, sabili da 'ya'yansa maza da 'ya'yansa mata sun tsokane shi.20"Zan ɓoye fuskata daga gare su," ya ce, "zan ga yadda ƙarshensu zai zama; gama kangararrun tsara ne, 'ya'ya marasa aminci.
21Suka sa ni kishi ta wurin abin da ba allah ba suka sa ni fushi da abubuwan wofinsu. Zan sa suji kyashi da waɗanda ba mutane ba; tawurin wautar al'umma zan sasu yi fushi.
22Gama fushina ya kunna wuta yana kuma ci zuwa zurfafan Lahira; yana hallaka duniya da girbinta; yana kunna wuta a harsashin duwatsu.
23Zan tara masihu a kan su; zan harba dukkan kibiyoyina a kansu;24Yunwa za ta ƙarasa su zasu hallaka da ƙuna mai zafi da hallakarwa mai ɗaci; zan aika a bisansu haƙoran namun jeji, da dafin abubuwan da ke rarrafe cikin ƙura.
25A waje takobi zai kawo rashi, a ɗakunan kwana razana zata yi haka. Zata hallaka matashi da budurwa, da jariri mai shan mama, da mutum mai furfura.26Na ce zan warwatsa su da nisa, in sa tunawa da su ya shuɗe daga 'yan adam.
27Da ba domin ina tsoron tsokanar maƙiyi ba, cewa maƙiya zasu zaci kuskure, kuma zasu ce, 'Hannunmu ya sami ɗaukaka,' dana aikata dukkan waɗannan abubuwa.
28Gama Isra'ila al'umma ce marar hikima, babu fahimta a cikinsu.29Ai ya, da suna da hikima, da sun fahimci wannan, da zasu yi la'akari da ƙaddararsu mai zuwa!
30Ta ya ya ɗaya zai kori dubu, biyu su sa dubu goma su tsere, sai ko Dutsensu ya sayar da su, Yahweh kuma ya sadakar da su?31Gama dutsen maƙiyanmu ba kamar Dutsenmu ba, kamar dai yadda maƙiyanmu suke cewa.
32Gama kuringar inabinsu ta zo ne daga kuringar Saduma, daga kuma jejin Gomarata; inabinsu inabin dafi ne; nonan masu ɗaci ne.
33Ruwan inabinsu dafin macizai ne, da mugun dafin kumurci.34Wannan shiri ban aje shi a ɓoye ba, a kunle cikin kayayyakina masu daraja ba?
35Ni ke bada sakamako, da ramako, a lokacin da kafafunsu suka zarme; gama ranar masifa domin su tayi kusa, abubuwan da zasu zo ta kansu zasu hanzarta su faru."
36Gama Yahweh zai yi wa mutanensa adalci, kuma zai ji tausayin bayinsa. Zai ga cewa ƙarfinsu ya ƙare, kuma ba wanda ya rage, ko bawa ko baratattun mutane.
37Sa'annan zai ce, "Ina allolinsu suke, duwatsu waɗanda suka dogara a gare su? -38allolin da suka ci kitsen hadayunsu suka sha ruwan inabin baye-bayensu na sha. Bari su tashi su taimaka maku; bari su zamar maku kariya.
39Duba yanzu da Ni, har Ni, Allah nake, kuma babu wani allah banda ni; Nakan kashe, in kuma rayar; na kan sa rauni, in warkar, kuma ba wani da zai iya cetonku daga ƙarfina.40Gama na kan tada hannuna zuwa sama in ce, "kamar yadda na dawwama har abada, zan aikata.
41Sa'ad da na wasa takobina mai walƙiya, kuma sa'ad da hannuna ya fara kawo adalci, zan yi sakayya akan maƙiyana, in kuma sãka wa duk waɗanda suka ƙi ni.
42Zan sa kibiyoyina su bugu da jini, takobina zai ci tsoka tare da jinin kasassu da kamammu, tun daga kan shugabannin maƙiyan.'"
43Ku yi farinciki, ya ku al'ummai, da mutanen Allah, gama zai yi sakayyar jinin bayinsa; zai bada sakamako a kan maƙiyansa, kuma zai yi kafara domin ƙasarsa, kuma domin mutanensa.
44Musa ya zo ya maimaita dukkan maganganun waƙar nan a kunnuwan mutane, shi, da Yoshuwa ɗan Nun.45Sai Musa ya gama maimaita dukkan waɗannan maganganun ga dukkan Isra'ila.
46Ya ce masu, "Ku sa zuciyarku akan maganganun da nayi maku kashedi yau, domin ku umarci 'ya'yanku su kiyaye su, dukkan maganganun shari'ar nan.47Gama wannan ba wani abu ne kurum dominku ba, sabili da ranku ne, kuma tawurin wannan abu zaku tsawaita kwanakin ku a ƙasar da kuke tafiya ku haye Yodan ku mallaka."
48A ranar nan Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,49"Ka hau cikin waɗannan duwatsen Abarim, ƙolƙolin Dutsen Nebo, wanda ke ƙasar Mowab, hannun riga da Yariko. Zaka duba ƙasar Kan'ana, wanda nake ba mutanen Isra'ila abin mallakarsu.
50Zaka mutu akan dutsen da zaka hau, za a tattara ka zuwa ga mutanenka, kamar yadda Haruna ɗan'uwanka Ba'isra'ile ya rasu akan Dutsen Hor aka tattara shi zuwa ga mutanensa.51Wannan zai faru domin ka yi rashin aminci a gare ni a tsakiyar mutanen Isra'ila a bakin ruwayen Meriba a Kadesh, a jejin Zin; domin baka ɗaukakani ba kuma baka girmama ni cikin mutanen Isra'ila ba.52Gama zaka hangi ƙasar a gabanka, amma ba zaka je can ba, cikin ƙasar da nake ba mutanen Isra'ila."

33

1Wannan ita ce albarkar da Musa mutumin Allah ya albarkaci mutanen Isra'ila da ita kafin rasuwarsa. Ya ce:2Yahweh ya taho daga Sinai, kuma ya taso daga Seyir a bisansu. Ya haskaka daga Dutsen Faran, yazo da dubun dubbai goma na tsarkaka. A cikin hannun damarsa akwai tarwatsun walƙiya.

3Hakika, yana ƙaunar mutane; dukkan tsarkakansa suna cikin hannunka, suna kuma russunawa a ƙafafunka; suna karɓar maganganunka.4Musa ya umarta mana ka'idodi, abin gãdo domin taro na Yakubu.
5A sa'annan akwai sarki a Yeshurun, lokacin da shugabannin mutane suka taru, dukkan kabilar Isra'ila suka taru.6Bari Ruben ya rayu kada ya mutu, amma bari mutanensa su zama ƙalilan.
7Wannan ce albarkar Yahuda, Musa ya ce: Ku saurara, Yahweh, ga muryar Yahuda, a sake dawo da shi ga mutanensa. Kuyi yaƙi dominsa; ku zama taimako gãba da maƙiyansa.
8Game da Lebi, Musa ya ce: Da Tumim ka da Yurim ka na aminanka ne, waɗanda ka gwada su a Massa, waɗanda kayi jayayya da su a ruwayen Meriba.
9Mutumin da ya ce game da mahaifinsa da mahaifiyarsa, "Ni ban gansu ba." Bai kuma shaidi 'yan'uwansa maza ba, hallau bai yi la'akari da 'ya'yansa na cikinsa ba. Gama ya tsare maganganunka ya kuma kiyaye alƙawarinka.
10Yana koya wa Yakubu dokokinka da Isra'ila shari'arka. Zai sa turare a gabanka da dukkan baye- baye na ƙonawa akan bagadinka.
11Kasa albarka, Yahweh, bisa mallakarsa, ka karɓi aikin hannunsa. Ka rushe kwankwasan waɗanda suka tashi gãba da shi, da mutanen da suka ƙi shi, domin kada su sake tashi kuma.
12Game da Benyamin, Musa ya ce: Shi wanda Yahweh ya ke ƙauna yana zaune lafiya a gefensa; Yahweh ya kãre shi dukkan rana, yana zaune tsakiyar hannuwan Yahweh.
13Game da Yosef, Musa ya ce: Bari Yahweh ya albarkaci ƙasarsa da abubuwa masu daraja na sama, tare da raɓa, kuma tare da zurfafa da ke kwance a ƙasa.
14Bari ƙasarsa ta zama da albarkar abubuwa masu daraja na girbi dana rana, da abubuwa masu daraja na watanni,15tare da kyawawan abubuwa daga duwatsun dã, da kuma abubuwa masu daraja daga dawwamammun tuddai.
16Bari a albarkaci ƙasarsa da abubuwa masu daraja na duniya duk da cikarta, tare kuma da fatan alheri ga wanda ya zauna cikin saura. Bari albarka ta sauka a kan Yosef, da a kan shi wanda ya zama sarki bisa 'yan'uwansa maza.
17‌Ɗan fari na bijimi, mai daraja ne shi, ƙahonninsa kamar ƙahonnin bijimin jeji ne. Da su zai tunkuɗe mutane, dukkansu, har ƙarshen duniya. Waɗannan su ne dubbai goma na Ifraimu; waɗannan su ne dubbai na Manasa.
18Game da Zebaluna, Musa ya ce: Kayi farinciki, Zebaluna, cikin fitarka, kai kuma, Isakar, a cikin rumfunarka.19Zasu kira mutane zuwa duwatsu. A can zasu miƙa hadayu na adalci. Domin zasu sha wadatar tekuna, daga kuma yãshin da ke a bakin teku.
20Game da Gad, Musa ya ce: Mai albarka ne wanda ya faɗaɗa Gad. Zai zauna a can kamar zakanya, zai kuma farke hannu ko ƙoƙon kai.
21Ya samar wa kansa sashe mafi kyau, domin akwai rabon ƙasa da aka keɓe domin shugaba. Yazo da shugabannin mutane. Ya aiwata adalcin Yahweh da dokokinsa da Isra'ila.
22Game da Dan, Musa ya ce: Dan ɗan zaki ne da ya yi tsalle waje daga Bashan.
23Game da Naftali, Musa ya ce: Naftali, ya ƙoshi da tagomashi, cike ya ke da alheran Yahweh, ya mallaki ƙasar daga yamma da kudu.
24Game da Ashiru, Musa ya ce: Mai albarka ne Ashiru fiye da sauran 'ya'ya maza; bari ya zama karɓaɓɓe ga 'ya'uwansa maza, bari ya tsoma ƙafarsa cikin man zaitun.25Bari ƙurfan birninka su zama na baƙin ƙarfe da tagulla; dukkan kwanakin ranka, haka ma tsaron lafiyarka.
26Babu ko ɗaya kamar Allah, Yeshurun - mai gaskiyan nan, mai hawa cikin sammai ya kawo maka taimako, kuma cikin darajarsa bisa gajimarai.
27Allah madawwami mafaka ne, a ƙarƙashi kuma dawwamammun hannuwa. Yakan kori maƙiya daga gaban ka, sai kuma ya ce, "Hallaka!"
28Isra'ila ta zauna lafiya. Maɓulɓular Yakubu tana tsare cikin ƙasar hatsi da sabon ruwan inabi; labudda, bari sammansa su zubo raɓa a kansa.
29Albarkunka da yawa, Isra'ila! Wane ne kamarka, mutane da Yahweh ya ceta, garkuwar taimakonka, da takobin ɗaukakarka? Magabtanku zasu zo gare ku da rawar jiki, zaku tattake masujadarsu.

34

1Musa ya haura daga filin Mowab zuwa Dutsen Nebo, zuwa ƙwolƙwolin Fizga, wacce take hannun riga da Yariko. A nan Yahweh ya nuna masa dukkan ƙasar Giliyad har ya zuwa Dan,2da dukkan Naftali, da ƙasar Ifraimu da ta Manasa, da dukkan ƙasar Yahuda, har ya zuwa tekun kudu,3da Nageb, da filin Kwarin Yariko, Birnin Itatuwan Dabino, har ya zuwa Zowar.

4Yahweh ya ce masa, "Wannan ita ce ƙasar dana rantse wa Ibrahim, da Ishaku, da kuma Yakubu, cewa, "Ni zan bada ita ga zuriyarku.' Na yardar maka ka ganta da idanunka, amma ba zaka je can ba."5Sai Musa bawan Yahweh, ya rasu a nan ƙasar Mowab, kamar yadda maganar Yahweh ta alƙawarta.6Yahweh ya bizne shi a cikin kwari cikin ƙasar Mowab mai hannun riga da Bet Feyor, amma ba wanda yasan inda kabarinsa ya ke har wa yau.
7Musa yana da shekara ɗari da ashirin sa'ad da ya rasu, idanunsa basu dushe ba ƙarfinsa kuma bai ragu ba.8Mutanen Isra'ila suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab har kwana arba'in, sai kwanakin makoki domin Musa suka ƙare.
9Yoshuwa ɗan Nun yana cike da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa. Mutanen Isra'ila suka saurare shi kuma suka yi abin da Yahweh ya umarci Musa.
10Ba wani annabi da ya taɓa tashi a Isra'ila kamar Musa, wanda Yahweh ya san shi fuska da fuska.11Ba a taɓa yin wani annabi kamarsa ba a cikin dukkan alamu da mu'ujizai waɗanda Yahweh ya aike shi ya yi a ƙasar Masar, wurin Fir'auna, da dukkan barorinsa, da dukkan ƙasarsa.12Ba a taɓa yin wani annabi kamarsa ba a dukkan manyan, ayyukan ban tsoro da Musa ya yi a idanun dukkan Isra'ila.

Littafin yoshuwa

1

1Ya zamana fa bayan mutuwar Musa bawan Yahweh, sai Yahweh ya yi magana da Yoshuwa ɗan Nun, babban mataimakin Musa, ya ce,2"Bawana Musa, ya rasu. Yanzu fa, ka tashi, ka haye wannan kogin Yodan, da kai da dukkan mutanen nan, zuwa cikin wannan ƙasa da zan ba su - ga mutanen Isra'ila.3Na rigaya na ba ku dukkan inda sawun ƙafafunku za su taka. Na baku ita, kamar yadda na yi wa Musa alƙawari.

4Daga jejin Lebanon, har zuwa babban kogin Yufaratas, dukkan ƙasar Hatiyawa, da Babban Teku, inda rana take faɗuwa, za ta zama ƙasarku.5Ba wanda zai iya tsayayya da kai dukkan kwanakin ranka. Zan kasance tare da kai kamar yadda na kasance da Musa. Bazan yasheka ba ko in bar ka.
6Ka dage ka yi ƙarfin hali. Za ka sa mutanen nan su gaji ƙasar da na alƙawarta wa kakanninsu zan ba su.7Ka dage ka yi ƙarfin hali sosai. Ka yi hankali ka yi biyayya da dukkan dokokin da bawana Musa ya umarce ka. Kada ka kauce masu zuwa dama ko hagu, domin ka yi nasara duk inda ka tafi.
8Kullum za ka riƙa yin magana a kan wannan littafin shari'a. Za ka riƙa binbini a kansa dare da rana domin ka yi biyayya da dukkan abin da aka rubuta a ciki. Sa'annan za ka zama da albarka da nasara.9Ba ni ne na urmace ka ba? Ka ƙarfafa ka yi ƙarfin hali! Kada ka ji tsoro. Kada ka karaya. Yahweh Allahnka ya na nan tare da kai duk inda ka tafi."
10Sai Yoshuwa ya umarci shugabannin jama'a,11"Ku tafi cikin sansanin ku dokaci mutanen, 'Ku shirya wa kanku guzuri. Cikin kwana uku za ku haye wannan Yodan ku mallaki wannan ƙasa da Yahweh Allahnku ya ke ba ku gãdo."'
12Ga Rubainawa, da Gadawa da rabin kabilar Manasse, Yoshuwa ya ce,13"Ku tuna da maganar da Musa bawan Yahweh, ya umarce ku sa'ad da ya ce, 'Yahweh Allahnku ya na ba ku hutawa, ya na kuma ba ku wannan ƙasa.'
14Matanku, da 'yan ƙanananku, da dabbobin ku za ku barsu a ƙasar da Musa ya ba ku, can ƙetaren Yodan. Amma jarumawanku za su tafi da 'yan 'uwanku su taimaka masu15har sai Yahweh ya ba 'yan 'uwanku hutawa kamar yadda ya baku. Haka su ma za su mallaki ƙasar da Yahweh Allahnku ke ba su. Sa'annan za ku dawo zuwa taku ƙasar ku gaje ta, ƙasar da Musa bawan Yahweh ya baku can ketaren Yodan inda rana take fitowa."
16Sa'annan su ka amsa wa Yoshuwa, su ka ce, "Za mu yi dukkan abin da ka umarce mu, kuma duk in da ka aike mu za mu je.17Za mu yi maka biyayya kamar yadda muka yi wa Musa biyayya. Allahnka Yahweh dai ya kasance tare da kai, kamar yadda ya kasance da Musa.18Duk wanda ya yi tawaye gãba da umarninka ya kuma yi rashin biyayya da maganarka za a kashe shi. Ka dage ka yi ƙarfin hali."

2

1Sai Yoshuwa ɗan Nun a asirce ya aiki mutum biyu daga Shittim magewaya. Ya ce; "Ku je, ku dubo ƙasar, musamman Yeriko." Su ka yi tafiyarsu su ka isa gidan wata karuwa mai suna Rahab, a nan ne su ka sauka.2Aka cewa sarkin Yeriko, "Duba, mutanen Isra'ila sun zo nan domin su leƙi ƙasar."3Sai sarkin Yeriko ya aika wa Rahab cewa, "Ki fito da mutanen da su ka zo wurinki waɗanda su ka shiga gidanki, gama sun zo ne domin leƙen dukkan ƙasar."

4Amma matar ta rigaya ta ɗauki mutanen nan biyu ta ɓoye su. Sai ta amsa masu, "I, mutanen sun zo wurina amma ban san daga inda su ka fito ba.5Sun bar nan da sauran duhu, lokacin da ake kulle ƙofar birni. Ban san inda su ka tafi ba. Mai yiwuwa ku cim masu idan kun bi su da sauri."
6Gama ta rigaya ta kai su bisa rufin ɗakinta ta rufe su da ƙeƙasheshen rama waɗanda ta shinfiɗa a bisa rufin.7Sai mutanen su ka bi su a kan hanya da ta kai su kwarin Yodan. Nan da nan aka rufe ƙofar bayan da masu bin su su ka fita.
8Kafin mutanen su kwanta da dare, sai ta zo wurinsu a rufin kan ɗaki.9Ta ce, "Na sani Yahweh ya rigaya ya ba ku ƙasar kuma tsoronku ya faɗo kanmu. Dukkan waɗanda ke zaune a ƙasar za su narke a gabanku.
10Mun ji yadda Yahweh ya sa ruwan Jan teku ya ƙafe dominku sa'ad da kuka fito daga Masar. Mun ji kuma abin da ku ka yi wa sarakunan nan biyu na Amoriyawa a hayin Yodan - Su Sihon da - Og waɗanda ku ka hallaka dukka.11Da dai mu ka ji haka, zukatanmu su ka narke har babu karfin hali da ya rage a cikin ko ɗayanmu. Domin Yahweh Allahnku, shi ne Allah na sama da na duniya a ƙasa.
12Yanzu dai, ku rantse mani da Yahweh cewa, kamar yadda na yi maku alheri, kuma ku yi wa gidan ubana alheri. Ku bani tabbatacciyar alama13cewa za ku tsirar da ran mahaifina, da mahaifiyata, da 'yan 'uwana maza, da mata da dukkan iyalansu, za ku kuma cece mu daga mutuwa."
14Mutanen su ka ce ma ta, "Ran mu a bakin na ki, har ma ga mutuwa! Idan baki tona al'amarin nan ba, idan Yahweh ya ba mu ƙasar za mu nuna maki jinkai da aminci."
15Sai ta zura su ƙasa ta taga da igiya. Gidan da take zaune an gina shi cikin ganuwar birnin.16Ta ce masu, "Ku hau cikin duwatsu ku ɓoye, ka da masu bin ku su same ku. ku ɓoye a can har kwana uku bayan masu bin ku sun dawo. Sa'annan ku yi tafiyarku."17Mutanen su ka ce ma ta, "Za mu zama kuɓutattu da ga rantsuwar da mu ka rantse ma ki, idan ba ki riƙe amanar ba.
18Lokacin da za mu zo ƙasar, dole ki ɗaura wannan jar igiya a tagar da ki ka zura mu, za ki kawo cikin gidan ki mahaifinki da mahaifiyarki, da 'yan'uwanki da dukkan gidan mahaifinki.19Duk wanda ya fita daga ƙofar gidanki zuwa titi, jininsu na bisa kansu, mu kuwa mun kuɓuta. Amma idan muka sa hannu a kan wanda ke cikin gida tare da ke, alhakin jininsa na kan mu.
20Amma idan ki ka furta al'amarin nan, za mu kuɓuta daga rantsuwar da ki ka sa mu ka rantse maki,"21Rahab ta amsa, "Bisa ga maganar da ku ka faɗa bari ya zama haka." Sai ta sallame su, su ka tafi. Sai ta ɗaura jar igiyar a tagar.
22Su ka tafi su ka haye cikin tsaunuka su ka kuma zauna can kwana uku har sai da masu bin sawun su su ka koma. masu bin sawunsu su ka yi ta neman su a kan hanya ba su sami komai ba.
23Mutanen biyu su ka ƙetare su ka komo wurin Yoshuwa, ɗan Nun, su ka labarta masa dukkan abubuwan da su ka faru da su.24Su ka ce ma Yoshuwa, "Gaskiya Yahweh ya ba mu wannan ƙasar. Dukkan mazaunan ƙasar su na ta narkewa sabili da mu."

3

1Yoshuwa ya tashi da sassafe, sai su ka yi ƙaura daga Shittim. Su ka iso Yodan, shi da dukkan mutanen Isra'ila, su ka sauka a nan kafin su haye.

2Bayan kwana uku, sai shugabanni su ka ratsa ta tsakiyar zangon;3su ka umarci mutane, "Lokacin da ku ka ga akwatin alƙawari na Yahweh Allahnku, da firistoci daga kabilar Lebiyawa ɗauke da shi, sai dole ku bar nan wajen ku bi shi.4Dole ku sa ratar ƙafa dubu biyu tsakanin ku da akwatin. Kada ku je kusa da shi, domin ku iya hango inda za ku bi, da shike ba ku taɓa bin wannan hanyar ba,"
5Yoshuwa ya cewa jama'a; "Ku tsarkake kanku gobe, domin Yahweh zai yi abin al'ajibi a tsakanin ku."6Sa'annan Yoshuwa ya cewa Firistoci, "Ku ɗauki akwatin alƙawari ku wuce gaban jama'a." Sai su ka ɗauki akwatin alƙawarin su ka wuce gaban jama'a da shi.
7Yahweh ya cewa Yoshuwa, "A ranar yau zan maishe ka babban mutum a idanun Isra'ilawa dukka. Za su sani, kamar yadda na kasance da Musa, zan kasance da kai.8Za ka umarci Firistoci su ɗauki akwatin alƙawari, 'Lokacin da ku ka isa bakin ruwayen Yodan, dole ku tsaya cik a cikin Kogin Yodan."'
9Yoshuwa ya cewa mutanen Isra'ila, "Ku zo nan ku saurari maganar Yahweh Allahnku.10Ta wurin wannan za ku sani Allah mai rai na tare da ku zai kori Kan'aniyawa, Hatiyawa da Hibiyawa da Farizziyawa da Girgashiyawa da Amoriyawa da Yebusawa daga gaban ku.11Duba! Akwatin alƙawari na Ubangijin dukkan duniya ya shiga gaban ku zuwa cikin Yodan.
12Yanzu ku zaɓi mutum goma sha biyu daga ƙabilar Isra'ila, mutum guda daga kowannen su.13Sa'ad da tafin sawun firistoci masu ɗauke da akawatin Yahweh, Ubangijin dukkan duniya, ya taɓa ruwayen Yodan, ruwayen za su datse, har ma ruwayen da suke kwararowa daga bisan kogin za su daina kwararowa su tsaya a tari guda."
14A lokacin da jama'a su ka tashi domin su ƙetare Yodan, firistoci ɗauke da akwatin alƙawari su ka wuce gaban jama'a.15Da zarar mutane masu ɗauke da akwatin su ka iso Yodan, da ƙafafunsu su ka taɓa gacin ruwan (Yodan dai yakan yi ambaliya dukkan lokacin girbi),16sai ruwayen da suke gangarowa daga tudun rafin su ka taru wuri guda. Ruwan ya dena gangarowa daga nesa. Ya kuma dena gagarowa daga Adam, birnin da ke kusa da Zaretan, har ya zuwa tekun Negeb, Tekun Gishiri. Jama'a su ka ƙetare kurkusa da Yeriko.
17Firistocin da ke ɗauke da akwatin alƙawari na Yahweh su ka tsaya a kan busasshiyar ƙasa a tsakiyar Yodan har sai da jama'ar Isra'ila su ka ƙetare a kan busasshiyar ƙasa.

4

1Sa'ad da dukkan mutane su ka ƙetare Yodan, Yahweh ya cewa Yoshuwa,2"Ku zaɓa wa kan ku mutum goma sha biyu, daga kowanne kabila mutum ɗaya.3Ka ba su wannan umarni: 'Ku ɗauki duwatsu goma sha biyu daga tsakiyar Yodan inda firitoci ke tsaye a kan busasshiyar ƙasa, ku kawo su ku ajiye su inda za ku kwana daren yau."'

4Sai Yoshuwa ya kira mutanen nan goma sha biyu waɗanda ya zaɓo daga kabilar Isra'ila, guda ɗaya daga kowacce kabila.5Yoshuwa ya ce masu, "Ku wuce gaban akwatin Yahweh Allahnku zuwa cikin tsakiyar Yodan. Kowannen ku zai ɗauki dutse a kafaɗarsa, bisa ga yawan kabilun mutanen Israila.
6Wannan zai zamar ma ku alama a tsakanin ku sa'ad da 'ya'yanku za su tambaya a kwanaki masu zuwa, 'Menene ake nufi da waɗannan duwatsu?'7Sa'annan za ku ce, 'An yanke ruwayen Yodan a gaban akwatin alƙawari na Yahweh. Lokacin da ya ƙetare Yodan, ruwan Yodan ya yanke. Saboda haka waɗannan duwatsu za su zama abin tunawa ga jama'ar Isra'ila har abada."'
8Jama'ar Isra'ila su ka yi dai-dai abin da Yoshuwa ya umarce su, su ka ɗauki duwatsu goma sha biyu daga tsakiyar Yodan, kamar yadda Yahweh ya cewa Yoshuwa. Suka shirya duwatsun yadda lambar kabilar Isra'ila ta ke. Su ka ɗebo duwatsu, su ka kawo masaukinsu su ka shirya su a nan.9Sa'annan Yoshuwa ya jera wasu duwatsu a tsakiyar Kogin Yodan, a inda sawun firistoci da su ka ɗauki akwatin alƙawari su ka tsaya. Wannan alamar tana nan har yau.
10Firitoci da ke ɗauke da akwatin alƙawari su ka tsaya a tsakiyar Yodan cik har sai duk abubuwan da Yahweh ya umarci Yoshuwa ya faɗa wa mutane sun cika sarai, bisa ga duk abin da Musa ya umarci Yoshuwa.11Sa'ad da dukkan jama'a su ka gama ƙetarewa, akwatin Yahweh da firistoci su ka ƙetare a gaban jama'a.
12Kabilar Ruben, da kabilar Gad, da rabin kabilar Manasse su ka wuce a gaban Isra'ilawa shirye 'yan yaƙi, kamar yadda Musa ya ce masu.13Kimanin maza dubu arba'in shiryayyu mayaƙa su ka wuce a gaban Yahweh, domin yaƙi wajen filayen Yeriko.14A ranan nan Yahweh ya ɗaukaka Yoshuwa a idanun dukkan Isra'ilawa. Su ka girmama shi - dai dai da yadda su ka ga ƙwarjinin Musa - dukkan kwanakinsa.
15Sai Yahweh ya yi magana da Yoshuwa,16"Ka umarci firistoci masu ɗauke da akwatin alƙawari su hauro daga cikin Yodan."
17Sai, Yoshuwa ya umarci firistoci, "Ku fito daga cikin Yodan."18Da firistoci da ke ɗauke da akwatin alƙawari na Yahweh su ka fito daga tsakiyar Yodan, su ka sa tafin ƙafarsu a busasshiyar ƙasa, sai ruwayen Yodan su ka koma magudanarsu su ka cike ta da ambaliya, kamar yadda ta ke kwanaki hudu da su ka wuce.
19Jama'a su ka fito daga Yodan a rana ta goma ga watan ɗaya. Su ka zauna a Gilgal, gabashin Yeriko.20Duwatsu sha biyu da su ka ɗauko daga Yodan, Yoshuwa ya shiryasu a Gilgal.21Ya cewa jama'ar Isra'ila, "Sa'ad da zuriyarku za su tambayi ubanninku a zamanai masu zuwa, 'Waɗannan duwatsun fa?'
22Ku gayawa 'ya'yanku, 'Nan ne Isra'ila ya ƙetare Yodan kan busasshiyar ƙasa.'23Yahweh Allahnku ya janye ruwan Yodan domin ku, har sai da su ka ƙetare, kamar yadda Yahweh Allahnku ya yi wa Jan Teku, wadda ya busar da ita domin mu sai da muka haye,24domin mutanen duniya dukka su sa ni hannun Yahweh mai karfi ne, ku kuma ku girmama Yahweh Allahnku har abada."

5

1Nan da nan da dukkan sarakunan Amoriyawa na yamma da Yodan, da dukkan sarakunan Kan'aniyawa, waɗanda su ke gefen Babbar Teku, su ka ji yadda Yahweh ya sa ruwayen Yodan su ka ƙafe har sai da jama'ar Isra'ila suka haye zuwa ɗaya gacin, sai zukatansu suka narke, ba su da sauran wani ƙarfin hali kuma saboda mutanen Isra'ila.

2A lokacin sai Yahweh ya cewa Yoshuwa, "Ka yi wuƙar dutse ka sake yi wa dukkan mazajen isra'ila kaciya."3Sai Yoshuwa ya yi wuƙar dutse ya yi wa dukkan mazajen Isra'ila kaciya a Gibiyat Hãralot.
4Wannan shi ne dalilin da Yoshuwa ya yi masu kaciya: dukkan mazajen da su ka fito daga Masar, tare da dukkan mayaƙa, sun mutu a cikin jeji a kan hanya, bayan sun baro Masar,5Ko da shike dukkan mazajen da su ka baro Masar suna da kaciya, amma, duk yara maza da aka haifa cikin jeji a kan hanyar fitowar su daga Masar ba su da kaciya.
6Gama mutanen Isra'ila su ka yi tafiya shekara arba'in a jeji, har sai da dukkan mazajen da su ka fito Masar mayaƙa su ka mutu, domin ba su yi biyayya da muryar Yahweh ba. Yahweh ya rantse masu ba za su shiga ƙasar da ya rantse wa kakanninsu zai ba mu, ƙasa wadda take zubo da madara da zuma.7'Ya'yansu ne waɗanda Yahweh ya tăda a madadinsu, su ne Yoshuwa ya yi wa kaciya, domin ba a yi masu kaciya a hanya ba.
8Sa'ad da aka yi wa dukkan su kaciya, su ka zauna cikin sansani har sai da su ka warke.9Sai Yahweh ya cewa Yoshuwa, "Wannan rana ta yau na cire ƙunyar Masar daga gare ku." Saboda haka, ake kiran sunan wurin Gilgal har wa yau.
10Jama'ar Isra'ila su ka yi sansani a Gilgal. Su ka kiyaye Idin Ketarewa a rana ta goma sha hudu ga wata, da yammaci, a filayen Yeriko.11Su ka ci daga waɗansu amfanin ƙasar a rana ta fari bayan Idin Ketarewa: waina marar yisti da gasasshen hatsi.
12Manna ta dena saukowa bayan ranar da su ka ci daga amfanin ƙasar. Babu manna kuma domin jama'ar Isra'ila, amma su ka ci daga cikin amfanin ƙasar Kan'ana a shekaran nan.
13Sa'ad da Yoshuwa ya kusa da Yariko, sai ya tada idanunsa ya duba, sai, ga wani mutum tsaye a gabansa; da takobi a zare a hannunsa. Yoshuwa ya tafi wurin sa ya ce, "Kana wajenmu ne ko kana wajen abokan găbarmu?"
14Sai ya ce, "Ko ɗaya. Ni ne sarkin yaƙin rundunar Yahweh. Yanzu na zo." Sai Yoshuwa ya russuna da fuskarsa ƙasa ya yi masa sujada ya ce, "Menene ubangijina zai faɗa wa bawansa?"15Sai sarkin yaƙin rundunar Yahweh ya cewa Yoshuwa, "Ka cire takalmanka daga ƙafafunka, domin inda ka ke tsaye wuri mai tsarki ne." Haka kuwa Yoshuwa ya yi.

6

1Aka rufe dukkan ƙofofin shiga Yeriko saboda mayaƙan Isra'ila. Ba wanda ya fita ko ya shigo.2Yahweh ya cewa Yoshuwa, "Duba, na bada Yeriko da sarkinta, da horarrun sojojinta a hannunka.

3Dole ku zagaya birnin, dukkan mazaje mayaƙa za su zaga birnin sau ɗaya. Dole za ku yi haka har kwana shida.4Dole firistoci bakwai su ɗauki ƙahonni bakwai na raguna a gaban akwati. A rana ta bakwai, dole ku zagaya brinin sau bakwai, firistoci kuma dole su busa ƙahonni da babbar busa.
5Daga nan dole su yi doguwar busa da ƙahon rago, kuma sa'ad da ku ka ji busar ƙahon dukkan mutane dole su yi ihu da babbar murya, garun birnin zai faɗi ya rushe. Dole sojojin su kai hari, kowannensu ya miƙe ya tafi gaba."
6Sa'annan Yoshuwa ɗan Nun ya kira firistoci ya ce masu, "Ku ɗauki akwatin alƙawari, kuma firistoci bakwai su ɗauki ƙahonnin raguna bakwai a gaban akwatin Yahweh."7Ya cewa jama'a, "Ku tafi ku zagaya birnin, masu makamai kuma za su je gaban akwatin Yahweh."
8Kamar yadda Yoshuwa ya cewa mutane, firistoci bakwai su ka ɗauki ƙahonni bakwai na raguna a gaban Yahweh. Da su ka cigaba da tafiya sai su ka busa ƙaho da babbar murya. Akwatin alƙawari na Yahweh na biye da su.9Masu makamai su ka tafi gaban firistoci, su ka yi babbar busa, wasu masu makamai kuma su ka bi bayan akwatin, firistoci kuma su ka yi ta busa ƙahonni.
10Amma Yoshuwa ya dokaci mutane, cewa, "Kada ku yi ihu. Kada wata ƙara ta fito daga bakinku sai randa na ce ku yi ihu. Lokacin ne za ku yi ihu."11Sai ya sa aka zagaya birnin da akwatin Yahweh sau ɗaya a ranar. Sa'annan suka komo sansaninsu, su ka kwanta daren nan.
12Sai Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma su ka ɗauki akwatin Yahweh.13Firistoci bakwai, masu ɗauke da ƙahonnin raguna bakwai a gaban akwatin Yahweh su ka yi ta busa ƙahonni su na tafiya gaba gaɗi. Sojoji masu makamai suna tafiya a gabansu. Amma sa'ad da 'yan tsaron baya su ka biyo akwatin Yahweh, sai aka dinga busa ƙahonni.14Su ka zaga birnin sau daya a rana ta biyu su ka komo sansaninsu. Haka suka dinga yi har kwana shida.
15A rana ta bakwai su ka tashi da sassafe kafin gari ya waye, su ka zãga birnin kamar yadda su ka saba yi, wannan karon sau bakwai.16A wannan ranar ce su ka zagaya birnin sau bakwai, firistoci su ka busa ƙahonni, sai Yoshuwa ya umarci mutane, "Ku yi ihu! Gama Yahweh ya ba ku birnin.
17Za a keɓe wa Yahweh birnin da dukkan abin da ke cikinta domin hallakarwa. Rahab karuwan nan ce kaɗai za ta rayu - ita da dukkan waɗanda ke tare da ita a gidanta - domin ta ɓoye waɗanda mu ka aika.18Amma ku kam, ku yi lura game da abubuwan da aka ƙeɓe domin hallakarwa, domin kada bayan kun waresu saboda hallakarwa, ku koma ku ɗauka. Idan ku ka yi haka, za ku maida sansanin Isra'ila abin da za a hallakar kuma za ku jawo ma ta masifa.19Dukkan azurfa, zinariya da abubuwan tagulla da ƙarfe a keɓe su ga Yahweh. Dole a kai su cikin ma'ajin Yahweh."
20Da su ka yi babbar busa ƙahonni, sai mutane su ka yi gawurtaccen ihu ganuwar ta faɗi ƙasa, sa'annan kowanne mutum ya shiga ciki kai tsaye su ka ci birnin.21Su ka lalatar da dukkan abin da ke birnin da kaifin takobi - maza da mata, yaro da tsoho, shanu, tumaki, da jakai.
22Sa'annan Yoshuwa ya cewa mutanen biyu da su ka leƙo asirin ƙasar, "Ku shiga gidan karuwar nan. Ku fitar da ita waje da dukkan waɗanda suke tare da ita, kamar yadda ku ka rantse ma ta."
23Sai samarin nan biyu magewaya su ka shiga ciki su ka fitar da Rahab. Su ka fitar da mahaifinta, mahaifiyarta, 'yan'uwanta maza da dukkan 'yan'uwanta da su ke tare da ita. Su ka kai su wani wuri dabam da sansanin Isra'ila.24Su ka ƙona garin da dukkan abin da ke cikinsa. Sai dai azurfa, zinariya da kwanonin tagulla da na ƙarfe ne su ka ajiye a ma'ajin gidan Yahweh.
25Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwa, gidan ubanta, da dukkan waɗanda ke tare da ita da rai. Tana zaune a Isra'ila har wayau domin ta ɓoye masu leƙen asirin ƙasa waɗanda Yoshuwa ya aika su leƙo Yeriko.
26Sai Yoshuwa ya umarce su a lokacin da rantsuwa, ya kuma ce, "La'anannen mutum ne a idon Yahweh wanda ya sake gina wannan birni, Yeriko. A bakin ran ɗan farinsa, zai sa harsashen, a kuma bakin ran ɗan autansa, zai kafa ƙofofinta."27Haka Yahweh ya kasance tare da Yoshuwa, sunansa ya shahara ko'ina a faɗin ƙasar.

7

1Amma jama'ar Isra'ila su ka yi rashin aminci game da abubuwan da aka ƙeɓe domin hallakarwa. Akan ɗan Karmi, ɗan Zabdi ɗan Zera, daga kabilar Yahuda ya ɗauka daga cikin abubuwan da aka ƙeɓe domin hallakarwa, sai fushin Yahweh ya yi ƙuna a kan 'ya'yan Isra'ila.

2Yoshuwa ya aiki mutane daga Yeriko zuwa Ai da take kusa da Bet Aben gabas da Betel. Ya ce masu, "Ku tafi ku leƙo ƙasar." Sai mutanen su ka tafi su ka leƙo Ai.3Da su ka dawo wurin Yoshuwa, su ka ce masa, "Kada ka aika mutane dukka zuwa Ai. Ka aika misalin dubu biyu ko uku kawai, su je su kai ma ta hari. Kada ka bari dukkan mutane su wahala a yaƙi, domin ba su da yawa."
4Saboda haka mutum dubu uku ne kaɗai cikin mayaƙa su ka tafi.5Mutanen Ai su ka kashe misalin mutane talatin da shida su ka fafare su daga ƙofar birnin har zuwa mafasar duwatsu, su ka karkashe su sa'ad da su ke gangarowa daga kan tudu. Zukatan mutanen su ka tsorata ƙarfin halinsu kuma ya rabu da su.
6Sai Yoshuwa ya yayyage tufafinsa. Da shi da shugabanin Isra'ila su ka zuba ƙura a kansu su ka faɗi rub da ciki a ƙasa a gaban akwatin Yahweh har yamma.7Sa'annan Yoshuwa ya ce, "Ya Ubangiji Yahweh, me ya sa ma ka haye da mutanennan daga Yodan? Don ka bashe mu a cikin hannun Amoriyawa su hallakar da mu? Ai da mun gwammace mu yi zamanmu a wancan hayin Yodan!
8Ubangiji, me zan ce, bayan Isra'ila ta juya ta guje ma abokan gabanta?9Gama Kan'aniyawa da dukkan mazaunan ƙasar za su ji. Za su kewaye mu su sa mutanen duniya su manta da sunanmu. To me za ka yi domin sunanka mai girma?"
10Yahweh ya cewa Yoshuwa, "Tashi! Me ya sa ka kwanta fuskarka ƙasa?11Isra'ila ta yi zunubi. Sun karya dokata da na umurce su. Sun sãci waɗansu abubuwan da aka keɓe. Sun sata sun kuma ɓoye zunubinsu ta wurin aje abubuwan da su ka ɗauka cikin kayansu.12Saboda haka ne, mutanen Isra'ila ba za su iya tsayawa a gaban maƙiyansu ba. Sun juya wa maƙiyansu baya domin su kan su an ƙebe su domin hallakarwa. Ba zan kasance tare da ku kuma ba sai ko kun hallaka waɗannan abubuwa da ya kamata an hallakar da su, amma suna nan tare da ku.
13Tashi! Ka tsarkake jama'ar a gareni ka ce masu, 'Ku tsarkake kanku domin gobe. Domin Yahweh, Allah na Isra'ila ya ce, "Akwai abubuwan da aka keɓe saboda hallakarwa waɗanda su ke a tsakaninku, Isra'ila. Ba za ku iya tsayawa gaban maƙiyanku ba, sai kun fitar da dukkan abubuwan da aka keɓe domin hallakarwa daga tsakaninku."
14Da safe, dole ku taru bisa ga kabilarku. Kabilar da Yahweh ya zaɓa za ta matso iyali - iyali. Iyalin da Yahweh ya zaɓa dole su matso gida - gida. Gidan da Yahweh ya ware dole a gabatar da su mutum - mutum.15Zai zamana duk wanda aka zaɓa, da yake da waɗannan keɓaɓɓun abubuwan hallakarwa, za a ƙone shi, da duk abin da yake da shi, domin ya karya dokar Yahweh, kuma ya yi abin ban kunya a Isra'ila."'
16Saboda haka, Yoshuwa ya tashi da sassafe, ya gabatar da Isra'ilawa, kabila - kabila, sai aka zaɓi kabilar Yahuda.17Yoshuwa ya gabatar da kabilar Yahuda, sai aka zaɓi iyalin Zera. Ya gabatar da iyalin Zera mutum - mutum, sai aka zaɓi gidan Zabdi.18Ya gabatar da gidan Zabdi, mutum - mutum, sai aka zaɓi Akan, ɗan Karmi, ɗan Zera daga kabilar Yahuda, shi ne aka zaɓa.
19Sai Yoshuwa ya cewa Akan, "‌Ɗana, ka faɗi gaskiya a gaban Yahweh Allah na Isra'ila, ka ba da shaidarka gareshi. Idan ka yarda, ka gaya ma ni abin da ka yi. Ka da ka ɓoye ma ni."20Akan ya amsa wa Yoshuwa, "Gaskiya na yi wa Yahweh zunubi, Allah na Isra'ila. Ga abin da na yi:21Sa'ad da na ga wata kyakkyawar alkyabba daga Babila, a cikin ganima, da shekel dari biyu na azurfa, da curin zinariya mai nawin shekel hamsin, sai na yi sha'awarsu na ɗauka. Sunanan a binne a ƙasa a tsakiyar rumfata, azurfar kuwa ta na ƙarƙashinsu.
22Yoshuwa ya aiki manzanni, da su ka sheƙa da gudu zuwa rumfar, sai kuwa gasu. Da suka duba, su ka tarar da abubuwan bizne cikin rumfarsa, da azurfar a ƙarƙashi.23Sai su ka kwaso su daga tsakiyar rumfar su ka kawo wa Yoshuwa da dukkan mutanen Isra'ila. Su ka zuba su gaban Yahweh.
24Sai Yoshuwa, tare da dukkan Isra'ila, su ka ɗauki Akan ɗan Zera, da azurfar, da alkyabbar, da curin zinariyar, da 'ya'yansa maza da mata, da shanunsa, da jakunansa da tumakinsa, da rumfarsa da dukkan mallakarsa, su ka kawo su Kwarin Akor.
25Sa'annan Yoshuwa ya ce, "Don me ka wahalshe mu? Yahweh zai wahalsheka yau." Dukkan Isra'ila su ka jejjefe shi da duwatsu. Su ka jejjefi sauran da duwatsu su ka ƙone su da wuta.26Su ka tula duwatsu a kansa mai tudu da su ke nan har yau. Yahweh ya juya daga fushinsa mai zafi. Saboda haka aka kira sunan wurin Kwarin Akor har zuwa yau.

8

1Yahweh ya cewa Yoshuwa, "Ka da ka ji tsoro; ka da ka karaya. Ka ɗauki dukkan mayaƙa. Ku haura zuwa Ai. Duba, na rigaya na ba ka sarkin Ai, da mutanensa, birninsa da kuma ƙasarsa a hunnunka.2Za ka yi wa Ai da sarkinta kamar yadda ka yi wa Yeriko da sarkinta, amma za ku washe ganima da dabbobi domin kan ku. Ku yi kwanto a bayan birnin."

3Saboda haka Yoshuwa ya tashi ya ɗauki dukkan mazaje mayaƙa zuwa Ai. Sa'annan Yoshuwa ya zaɓi mazaje dubu talatin - ƙarfafa, jarumawa -- ya aike su da dare.4Ya umarce su, "Ku duba, za ku yi wa birnin kwanto, a bayansa. ka da ku yi nisa da birnin sosai, amma dukkan ku ku kasance a shirye.
5Ni da dukkan mutanen da ke tare da ni za mu kusanci birnin, sa'ad da da za su fito su yi karo da mu, za mu guje da ga garesu kamar dă.6Za su fito su fafare mu har sai mun rinjayesu daga birnin. Za su ce, 'Suna guje ma na karmar dă.' Haka za mu gudu da ga garesu.'7Sa'annan za ku fito da ga maɓuyarku, ku ci birnin. Yahweh Allahnku zai ba da shi a hannunku.
8Sa'ad da ku ka ci birnin, za ku cinna masa wuta. Za ku yi wannan lokacin da ku ka yi biyayya da umarnin da aka bayar cikin maganar Yahweh. Duba, na umarce ku."9Yoshuwa ya aike su, su ka tafi wurin kwanto, su ka yi faƙo tsakanin Betal da Ai, wato yamma da Ai ke nan. Yoshuwa kuwa ya kwana cikin jama'a a daren nan.
10Yoshuwa ya tashi da sassafe ya shirya sojojinsa, shi da shugabannin Isra'ila su ka kai wa mutanen Ai hari.11Dukkan mayaƙa maza da ke tare da shi su ka tafi tare da shi su ka kusanci birnin. Su ka matsa kusa arewa da Ai. Akwai kwari tsakaninsu da Ai.12Ya ɗauki mayaƙa kusan dubu biyar ya sa su ka yi kwanto yamma da birnin tsakanin Betel da Ai.
13Ya sanya dukkan sojojin ko'ina, muhimman rundunar ya sa su arewa da birnin, 'yan tsaron baya kuwa a yammancin birnin. Yoshuwa ya kwana a kwari a darennan.14Ananan da sarkin Ai ya ga haka, sai shi da mayaƙansa suka tashi da sassafe su ka gaggauta su ka kai wa Isra'ila hari ta gefen da ya fuskanci kwarin kogin Yodan. Bai sani ba cewa 'yan kwanto suna jiran su auka wa birnin ta baya.
15Yoshuwa da dukkan Isra'ila suka yi kamar an rinjayesu su ka gudu cikin jeji.16Aka kira dukkan mutane da ke cikin birnin su ka fafare su, su ka sheƙa da gudu su na bin Yoshuwa, aka kuwa rinjaye su nesa da birnin.17Ba a bar ko mutum ɗaya a cikin Ai da kuma Betel da bai fito ya fafari mutanen Isra'ila ba. Su ka bar birnin da ƙofofin sa a buɗe sa'ad da suke fafarar Israi'ila.
18Yahweh ya cewa Yoshuwa, "Ka miƙa mashin da ke hannun ka wajen Ai, domin zan ba da Ai cikin hannunka."Yoshuwa ya miƙa mashin da ke hannunsa wajen birnin.19Sai sojojin da su ka yi kwanto a saura su ka fito da ga inda suke sa'ad da ya mika hannunsa. Su ka yi gudu su ka shiga birinin su ka cinye shi. Nan da nan su ka cinna wa birnin wuta.
20Mutanen Ai su ka waiga baya. Su ka ga hayaƙi da ga birnin ya turmuƙe ya tashi sama, ba su iya kuɓucewa nan ko can ba. Gama sojojin Isra'ila da su ka gudu jeji su ka juyo su ka fuskanci masu fafarar su.21Sa'ad da Yoshuwa da dukkan Isra'ila su ka ga mutanen da su ka ɓoye sun kone birnin, da kuma hayaƙin da ke tashi, su ka juyo su ka karkashe mutanen Ai.
22Sauran sojojin Isra'ila, waɗanda su ka shiga birnin, su ka fito su kai masu hari. Ta haka aka cafke mutanen Ai gaba da baya a tsakiyar rundunar Isra'ila, wasu a wannan gefe wasu a can. Isra'ila su ka buga mayaƙan Ai; ba wanda ya tsira ko ya kuɓuce.23Su ka tsare sarkin Ai, wanda suka kama da rai, su ka kawo shi wurin Yoshuwa.
24Ana nan da Isra'ila ta gama karkashe mazaunan Ai a fili kusa da jejin da su ka fafare su, sa'ad da dukkansu, har ga na ƙarshe su ka mutu da kaifin takobi, dukkan Isra'ila su ka koma Ai. Su ka faɗa masu da kaifin takobi.25Dukkan waɗanda aka kashe maza da mata, dubu goma sha biyu ne, dukkan mutanen Ai.26Yoshuwa bai janye hannunsa ba da ya mika ta sa'ad da ya ke rike da mashi, har sai da ya gama hallakar da dukkan mutanen Ai.
27Isra'ila su ka ɗauki dabbobi kawai da ganimar da ke cikin birnin don kan su, kamar yadda Yahweh ya umarci Yoshuwa.28Yoshuwa ya ƙone Ai ya maishe ta kango har abada. Yasasshen wurin ne har yau.
29Ya rataye sarkin Ai akan bishiya har sai maraice. Da rana ta kusan faɗuwa, Yoshuwa ya umarta a saukar da gangar jikin sarki da ga itace a jeffa shi a kofar birnin. A nan ne su ka tula tarin duwatsu akansa. Tsibin ya na nan har yau.
30Sai Yoshuwa ya ginawa Yahweh bagadi, Allah na Isra'ila, a kan Dutsen Ebal,31dai - dai yadda Musa bawan Yahweh ya umarci mutanen Isra'ila, kamar yadda aka rubuta a littafin shari'a ta Musa: "Bagadi da ga duwatsun da ba a sassaƙa ba, wanda ba mutumin da ya ɗibiya guduma a kai." Ya mika hadayun ƙonawa ga Yahweh akan bagadin, su ka kuma miƙa hadayun salama.32A nan a gaban mutanen Isra'ila ya rubuta shari'ar Musa bisa duwatsun.
33Dukkan Isra'ila, da shugabanninsu, da hakimai, da mahukuntansu, su ka tsaya a gefe biyu na akwatin alƙawari a gaban firistoci da Lebiyawa da ke ɗaukar akwatin alƙawari na Yahweh - baƙi da haifaffun wurin - rabinsu su ka tsaya a gaban Dutsen Gerizin, rabin kuma su ka tsaya a gaban Dutsen Ebal. Su ka albarkaci mutanen Isra'ila, kamar yadda Musa bawan Yahweh ya umarce su tun da farko.
34Bayan haka, Yoshuwa ya karanta dukkan zantattukan shari'a, da albarkun da la'anun, kamar yadda aka rubuta a littafin shari'a.35Babu kalma ko ɗaya da ga dukkan abin da Musa ya umarta da Yoshuwa bai karanta a gaban taron Isra'ila ba, har ma da mata, da ƙananan yara. da baƙin da su ke zaune tare da su.

9

1Sai dukkan sarakunan dake zaune a ƙetaren Yodan a ƙasar duwatsu, da kuma kwarin gaɓar Babbar Teku wajen Lebanon - Hitiyawa, Amoriyawa Kan'aniyawa, Feriziyawa Hiwiyawa da kuma Yebusiyawa -2waɗannan su ka tattaru ƙarƙashin tuta guda, domin su yaƙi Yoshuwa da Isra'ila.

3Da mazaunan Gibiyon su ka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,4su ka yi masu hila. Suka tafi kamar jakadu. Su ka ɗauki koɗaɗɗun buhuna su ka ɗibiya su kan jakunansu. Su ka kuma ɗauki tsofaffin salkunan ruwan inabi da su ka ƙoɗe, yagaggu, sun kuma sha ɗinki.5Su ka sa tsoffofin takalman da suka sha gyara a ƙafafunsu, su ka sa ka tsofoffin riguna da su ka koɗe. Guzurin wainarsu kuma duk sun bushe sun yi fumfuna.
6Su ka tafi wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal, su ka ce masa da shi da mutanen Isra'ila, "Mun taho da ga ƙasa mai nisa, saboda haka sai ku yi alƙawari da mu."7mutanen Isra'ila su ka cewa Hiviyawa, "Watakila ku na zaune kusa da mu. ‌Ƙaƙa za mu yi alƙawari da ku?"8Su ka cewa Yoshuwa, "Mu bayinka ne," Yoshuwa ya ce masu, "Ku su wanene? Daga ina ku ka fito?"
9Su ka ce masa, "Barorinka sun zo daga ƙasa mai nisa, sabili da sunan Yahweh Allahnka. Mun ji rahoto a kan sa da kuma dukkan abubuwan da ya yi a Masar -10da dukkan abubuwan nan da ya yi wa sarakunan nan biyu na Amoriyawa da ke hayin Yodan - Sihon sarkin Hesbon da kuma Og sarkin Bashan da ke Astarot.
11Dattawanmu da dukkan mazaunan ƙasarmu su ka ce mana, 'Ku ɗauki guzuri a hannuwanku saboda tafiyarku. Ku je ku same su ku ce masu, "Mu bayinku ne. Ku yi yarjejeniya da mu."12Waɗannan gurasunmu ne, da ɗumi mu ka ɗauko su daga gida ranar da mu ka fito tafiya gunku. Amma yanzu, ku duba, sun bushe sun kuma yi funfuna.13Wannan salkunan ruwan inabi sabbi ne da muka cika su, amma ku duba, yanzu suna ɗiga. Rigunanmu da takalmanmu sun koɗe saboda nisan tafiya."'
14Sai Isra'ilawa su ka karɓi waɗansu guzurinsu, amma ba su biɗi shawara ba da ga Yahweh domin ya bishe su.15Yoshuwa ya dai - daita da su ya kuma yi alƙawari da su, a barsu su rayu. Shugabannin mutanen kuma su ka yi masu alƙawari.
16Bayan kwana uku da Isra'ilawa su ka yi alƙawari da su, sai su ka ji ai makwabtansu ne kuma su na zaune kurkusa.17Sai mutanen Israa'ila su ka tashi su ka isa biranensu a kan rana ta uku. Biranensu kenan Gibiya, Kefira, Birot, da Kiriyet - Yarim.
18Mutanen Isra'ila ba su kai masu hari ba saboda shugabanninsu sun rantse masu a gaban Yahweh, Allah na Isra'ila. Isra'ilawa dukka su ka yi ta gunaguni găba da shugabanninsu.19Amma dukkan shugabanni su ka cewa mutane dukka, "Mun rigaya mun rantse masu da Yahweh Allah na Isra'ila, yanzu fa ba za mu cuce su ba.
20Ga abin da za mu yi masu: Domin mu guji duk wani fushi da zai afko mana sabili da rantsuwa da mu ka yi masu, za mu bar su su rayu.21Shugabanni su ka cewa mutanensu, "Mu bar su su rayu." Sabili da haka, Gibiyaniyawa su ka zama masu sarar itace da masu jan ruwa domin dukkan Israa'ilawa, kamar yadda shugabanni su ka umarta game da su.
22Yoshuwa ya kira su ya ce, "Me ya sa ku ka ruɗemu ku ka ce, 'Muna nesa da ku', alhali kuwa ku na nan cikinmu?23Yanzu fa, sabili da wannan, la'anannu ne ku waɗansunku za su zama bayi ko yaushe, masu saro itace da masu jan ruwa domin gidan Allahnmu."
24Su ka amsa wa Yoshuwa su ka ce, "Sabili da an faɗa wa bayinka cewa, Yahweh Allahnku ya umarci bawansa Musa ya ba ku dukkan ƙasar, ya kuma karkashe dukkan mazaunan ƙasar a gabanku - shi ne mu ka ji tsoronku saboda ranmu. Shi ya sa mu ka yi wannan abu.25Yanzu dai, ku duba, muna ƙalƙashin ikonku. Duk iyakar abin da ku ka ga ya dace kuma dai -dai ne ku yi da mu, sai ku aiwatar."
26Sai Yoshuwa ya yi masu haka: ya fitar da su da ga ƙarƙashin mallakar mutanen Isra'ila. Isra'ilawa kuwa ba su kashe su ba.27A ranar Yoshuwa ya maida Gibiyanawa masu sarar itace da masu jawo ruwa domin mutanen Isra'ila, da na bagadin Yahweh, har wa yau, duk inda Yahweh ya zaɓa.

10

1Yanzu da Adonizedek, sarkin Yerusalem, ya ji yadda Yoshuwa ya kama Ai kuma har ya hallakar da ita baki ɗaya (kamar yadda ya yi da Yeriko da kuma sarkinta) ya kuma ji yadda mutanen Gibeyon suka ƙulla alkawarin zaman lafiya da Isra'ila har ma suna acikinsu.2Mutanen Yerusalem sun tsorata ƙwarai gama Gibeyon babban birnin ainin, kamar ɗaya daga cikin manyan sarakunan biranen. Har ma ta fi Ai ga shi kuma dukkan mayaƙan mazaje ne ƙarfafa.

3Saboda haka Adonizedek, sarkin Yerusalem, ya aika da saƙo ga Hoham, sarkin Hebron, ga Piram, sarkinYarmut, da Yafiya sarkin Lakish, da kuma Debir sarkin Eglon:4"Ku zo nan wurina ku taimake ni. Bari mu je mu yaƙi Gibeyon gama sun ƙulla alkawarin salama tare da Joshuwa da kuma mutanen Isra'ila."
5Sarakunan nan biyar na Amoriyawa, sarkin Yerusalem da sarkin Hebron da sarkin Yarmut da sarkin Lakish, da sarkin Eglon sun zo, dukkansu kuma da abokan gãbarsu. Sun kafawa Gibeyon sansani domin su yaƙe ta.
6Mutanen Gibeyon sun aika da saƙo ga Yoshuwa da kuma sojojin Gilgal. Sun ce, "Zo da sauri! Kada ka janye hanuwanka daga bayinka. Zo wurinmu da sauri ka ce-ce mu. Taimaka mana, domin dukkan sarakunan Amoriyawa da suke zaune a ƙasar tuddai sun tattaru a kanmu."7Joshuwa ya tafi daga Gilgal, shi da dukkan mutanen yaƙinsa, tare da dukkan jarumawa.
8Yahweh kuma ya ce da Yoshuwa, "Kada ka ji tsoronsu. Na riga na ba da su a hannunka. Babu wani daga cikinsu da zai hana ka yaƙe su."
9Yoshuwa ya tafi nan da nan ya auka masu, bayan ya yi tattaki dukkan dare daga Gilgal.10Yahweh kuwa ya rikita abokan gãbar Isra'ila, Isra'ilawa kuwa su ka kashe su da yawa a Gibeyon su ka bi su ta hanyar haurawa zuwa Ber-horon, a nan masu ka yi ta karkashe su a hanyar Azeka da Makkeda.
11A sa'ad da suke gudu daga Isra'ilawa, a gangarar hawan Bet-horon, Yahweh ya jefe su da manyan duwatsu daga sama a kansu dukka hanyar zuwa Azeka, sun kuma mutu. Waɗanda suka mutu ta ƙanƙarar duwatsu sun fi yawan mutanen Isra'ila su ka kashe da takobi.
12Sai Yoshuwa ya yi magana da Yahweh a ranar da Yahweh ya ba mutanen Israila nasara a kan Amoriyawa. Wannan shi ne abin da Yoshuwa ya ce da Yahweh a gaban Isra'ila, "Rana, ki tsaya a Gibeyon, wata kuma, a kwarin Ayalon."
13Rana ta tsaya cik, wata kuma ya tsaya ba ya motsi har al'ummar ta ɗauki fansa a kan abokan gãbarsu. Wannan ba shi ne ke rubuce a Littafin Yashar ba? Rana ta tsaya a tsakar sararin sama; ba ta faɗi ba dukkan yini.14Ba a taba yin yini kamar wannan ba ko kuma makamancinsa ba, da Yahweh ya saurari muryar mutum. Domin Yahweh ya yi yaƙi a madadin Isra'ila.
15Yoshuwa tare da dukkan Isra'ila sun koma zango a Gilgal.16Yanzu waɗannan sarakuna biyar kuma suka gudu suka ɓuya a cikin kogon Makkeda.17Sai aka faɗawa Yoshuwa, "An same su-sarakuna biyar suna ɓoye a kogon Makkeda."
18Yoshuwa ya ce, "Murgina manyan duwatsu a kan bakin kógon a kuma sa sojoji a wurin don su tsaresu.19Amma kada ku tsaya. Sai ku runtumi abokan ǧabanku ku kuma faɗa masu daga baya. Kada ku bar su su shiga biranensu, gama Yahweh Allahnku ya rigaya ya ba da su a hannunku."
20Yoshuwa da 'ya'yan Isra'ila sun gama karkashe su kisa mai yawa ƙwarai, har sai da aka kusan halaka su dukka; sai sauran kaɗan ne ba a kashe ba; sauran da su ka ragu suka shige birane masu garu.21Sa'annan dukkan sojojin sun koma da salama wurin Joshuwa a sansani a Makkeda. Ba kuma mutumin da ya faɗi wata kalmar ǧaba da ɗaya daga cikin mutanen Isra'ila.
22Sai Yoshuwa ya ce, "Ku buɗe bakin kógon kuma daga cikin kogon ku ba ni waɗannan sarakuna biyar."23Sun aikata kamar yadda ya ce. Sun kawo masa waɗannan sarakuna biyar daga kógon--sarkin Yerusalem, sarkin Hebron, sarkin Yarmut, sarkin Lakish, da kuma sarkin Eglon.
24Da su ka kawo sarakunan a wurin Yoshuwa, ya ƙirawo kowanne mutum da ke Isra'ila. Ya cewa shugabanin mayaƙa waɗanda su ka tafi tare da shi, "Ku sa ƙafafunwanku a wuyansu."Su kuwa sun zo sun taka wuyansu da ƙafafuwansu.25Sai ya ce da su, "Kada ku ji tsoro ko kuwa ku razana. Ku yi ƙarfin hali. Wannan shi ne abin da Yahweh zai yi da dukkan abokan gãbarku waɗanda za ku yi yaƙi da su.
26Sai Yoshuwa ya kai masu hari har ya kashe sarakunan. Ya kuma rataye su a kan itatuwa biyar. An rataye su a kan itatuwa har yamma.27Amma sa'ad da rana take faɗuwa, Yoshuwa ya ba da umarni, sai aka saukar da gawawwakinsu daga bisa itatuwan sai aka jefa su cikin kõgon da su ka ɓoye kansu. Sai su ka sa manyan duwatsu aka rufe baƙin kõgon. Waɗannan duwatsun suna nan har wannan rana.
28Ta wannan hanya, Yoshuwa ya kama Makkeda a ranar, ya kuma kashe kome a wurin da takobi, har ma da sarkin. Ya hallakar da su da dukkan wani abu mai rai a wurin. Bai ƙyale kowa da rai ba. Ya yi wa sarkin Makkeda kamar yadda ya yi wa sarkin Yeriko.
29Yoshuwa tare da dukkan Isra'ilawa sun zarce daga Makkeda zuwa Libna.30Yahweh kuma ya ba su ita ta hannun Isra'ila -- tare da sarkinsu. Yoshuwa kuwa ya kashe kowanne abu da ke rayuwa a cikinta da takobi. Bai bar wani abu da zai rayu ba a cikinta. Ya yi wa sarkin kamar yadda ya yi wa sarkin Yeriko.
31Sai Joshuwa tare da dukkan Isra'ila su ka zarce daga Libna zuwa Lakish. Ya kewaye ta kuma ya auka mata da yaƙi.32Yahweh ya ba da Lakish a hannun Isra'ila. Yoshuwa ya cinye ta a rana ta biyu. Ya kashe kowanne abu mai rayuwa da takobi wanda ke cikinta, kamar yadda ya yi da Libna.
33Sai Horam, sarkin Gezer, ya zo ya kawo wa Lakish taimako. Yoshuwa kuwa ya fãɗa masa shi da sojojinsa har babu wani abu mai rai da ya rage.
34Sai Yoshuwa tare da dukkan Isra'ila su ka zarce zuwa Lakish ta Eglon.35Sun kewaye ta sun auka mata da yaƙi, a wannan rana su ka cinyeta da yaƙi. Sun buge ta da takobi sun kuma hallaka kowanne mutum da ke cikinta, kamar yadda Yoshuwa ya yi a Lakish.
36Sai Yoshuwa tare da dukkan Isra'ila su ka haura daga Eglon zuwa Hebron.37Sun auka mata da yaƙi. Sun cinyeta suka kuma bugi kowanne mutum da ke cikinta da takobi, har ma da sarkin da kuma dukkan ƙauyukan da ke kewaye da ita, sun karkashe komai da ke rayuwa a cikinta, ba su ƙyale wani abu da zai rayu ba, kamar yadda Yoshuwa ya yi wa Eglon. Ya hallaka komai da kowanne abu mai raI a cikinta.
38Sai Yoshuwa ya juya, tare da dukkan sojojin Isra'ila da ke tare da shi, sun kuma wuce zuwa Debir sun kuma auka mata da yaƙi.39Ya kame ta tare da sarkinta, da dukkan ƙauyukan da ke kewaye da ita. Sun buge su da takobi har sun kashe dukkan abun da ke rayuwa a cikinta. Yoshuwa bai bar masu rayuwa ba, kamar yadda ya yi a Hebron da sarkinta, da kuma kamar yadda ya yi a Libna da sarkinta.
40Yoshuwa ya ci nasara da dukkan ƙasar, da tuddan ƙasar, da Negeb, da filayen kwarurruka, da kuma gangare. Da dukkan sarakunansu babu wanda ya tsira. Ya karkashe su babu wani abu mai rai, kamar yadda Yahweh, Allah na Isra'ila, ya ummarta.41Yoshuwa kuwa ya kai masu hari da takobi tun daga Kadesh Barneya har zuwa Gaza, da dukkan ƙasar Goshen zuwa Gibeyon.
42Yoshuwa kuma ya cinye dukkan waɗannan sarakuna da kuma ƙasashensu a lokaci ɗaya domin Yahweh Allah na Isra'ila, ya yi yaƙin don Isra'ila.43Sa'annan Yoshuwa, da dukkan Isra'ila tare da shi, sun koma zuwa zango a Gilgal.

11

1Sa'ad da Yabin, sarkin Hazor, yaji wannan, ya aika da saƙo ga Yobab, sarkin Madon, zuwa ga sarkin Shimron, da sarkin Akshaf.2Ya kuma aika da saƙon ga sarakuna waɗanda suke arewacin ƙasar tuddai, da ke cikin kudancin Kinneret, da ke cikin filayen kwari da kuma tuddai da ke cikin Dor a yamma.3Ya kuma aika da saƙon zuwa ga Kanaaniya gabas da yamma da Amoriyawa da Hatiyawa da Ferizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa da suke cikin ƙasar tuddai, da kuma Hiwiyawa da ke Tsaunin Harmon a ƙasar Mizfa.

4Dukkan mayaƙansu su ka fito wurinsu, babbar rundunar sojoji mai yawa kamar yashin teku. Su na da yawan dawakai da karusai ƙwarai da gaske.5Dukkan waɗannan sarakuna kuwa su ka shirya lokacin da za su haɗu, sun yi sansani a bakin ruwayen Merom don su yi yaƙi da Isra'ila.
6Yahweh ya cewa Yoshuwa, "Kada ka ji tsoron kasancewarsu, domin gobe war haka zan ba da su ga dukkan Isra'ila kamar matattun mutane. Za ku daddatse agaran dawakansu, za ku kuma ƙone karusansu"7Yoshuwa da dukkan mayaƙansa za su ma-mayesu. Nan da nan suka zo ruwayen Meron, suka karkashe abokan ǧabarsu.
8Yahweh kuma ya ba da abokan gãbar a hannun Isra'ila, sun kuma hallaka su da takobi su ka runtume su har zuwa Sidon, Misrefot Ma'im, har zuwa gabashin ƙwarin Mizfa. Sun karkashe su har babu wani mai tsira da ya rage a cikinsu.9Yoshuwa kuwa ya yi masu kamar yadda Yahweh ya faɗa masa. Ya daddatse agaran dawakansu ya kuma ƙone ƙarusansu.
10A wannan lokaci Yoshuwa ya juya da baya ya ci Hazor. Ya kashe sarkinta da takobi. (Hazor ita ce cibiyar dukkan waɗannan mulkokin.)11Sun kashe dukkan abin da ke raye a wannan wurin da takobi, ya kuma hallakar da su kakaf, saboda haka babu wanda aka rage da rai a wurin. Ya kuma ƙone Hazor.
12Yoshuwa kuwa ya ci dukkan biranen sarakunan. Ya kuma ci dukkan sarakunansu da takobi. Ya hallakar da su kakaf kamar yadda Musa bawan Yahweh ya ummarta.13Isra'ila ba su ƙone ko ɗaya daga cikin biranen da aka gina bisa tuddai ba, sai dai Hazor, ita kaɗai Yoshuwa ya ƙone.
14Sojojin Isra'ila kuwa su ka kwashe dukkan ganima daga waɗannan birane tare da shanu domin kansu. Sun kashe kowanne mutum da takobi har sai da dukkansu su ka mutu. Ba su bar wata hallita da ke da rai ba.15Kamar yadda Yahweh ya ummarci bawansa Musa, ta hanyar da Musa ya ummarci Yoshuwa, haka nan Yoshuwa ya yi da ita. Bai bar kome ba da bai aikata ba cikin dukkan abin da Yahweh ya ummarci Musa ya yi.
16Yoshuwa ya ɗauke dukkan ƙasar, da ƙasar tuddai, da dukkan Negeb, da dukkan ƙasar Goshen, da filayen kwari, da Yodan Kogin kwari, da ƙasar tuddai ta Isra'ila, da filayen gangare.17Daga Tsaunin Halak kusa da Idom, da wanda ya tafi zuwa arewa har zuwa wajen Ba'al Gad a kwari kusa da Lebanon a ƙarƙashin Tsaunin Hermon, ya kama dukkan sarakunansu ya kuma kashe su.
18Yoshuwa ya ɗauki dogon lokaci yana yaƙi da dukkan sarakunan.19Ba bu wani birni da ya yi zaman salama da sojojin Isra'ila sai dai Hiwiyawa da su ke zaune a Gibiyon. Isra'ila kuwa ta ci dukkan sauran biranen da yaƙi.20Domin Yahweh ne ya taurare zukatansu har da za su tasar ma Isra'ila da yaƙi, don a hallaka su a kuma shafe su ba tare da tausayi ba, kamar yadda aka ummarci Musa.
21A wannan lokaci kuwa Yoshuwa ya tafi ya kuma hallaka Anakawa. Ya kuma yi wannan a ƙasar tuddai, da Hebron, da Debir, da Anab, da kuma dukkan ƙasar tuddai ta Yahuda, da dukkan ƙasar tuddai ta Isra'ila. Yoshuwa ya hallaka su sarai duk da biranensu.22Babu wani gwarzon da ya ragu a ƙasar Isra'ila sai ko Gaza, da Gat, da kuma Ashdod.
23Ta haka Yoshuwa ya ci dukkan ƙasar, kamar yadda Yahweh ya faɗawa Musa. Yoshuwa kuwa ya ba da ita gãdo ga Israila bisa ga kabilar kowa, Sai ƙasar ta shaƙata daga yaƙe -yaƙe.

12

1Yanzu waɗannan su ne sarakunan ƙasar, wadda mutanen Isra'ila su ka cinye da yaƙi. Isra'ilawa sun mallaki ƙasar a gabashin Yodan inda rana ta ke fitowa daga Kwarin Kogin Arnon zuwa Tsaunin Harmon, da dukkan Arabah wajen gabas.2Sihon, sarkin Amoriyawa, wanda yake zaune a Heshbon. Ya yi mulki daga Arower, wadda ta ke iyakar kwarin Arnon Gorge daga tsakiyar kwarin, har rabin Giliyad zuwa ga Kogin Yabbok iyakar Amoniyawa.

3Sihon kuma ya yi mulki a kan Arabah zuwa Tekun Kinneret, da zuwa gabashin Tekun Arabah (Tekun Gishiri) a wajen gabas, da dukkan hanyar Ber Yeshimot da wajen kudu, zuwa gangaren gindin Tsaunin Fisga.4Og, sarkin Bashan, ɗaya daga cikin sauran Refayim, wanda ya zauna a Ashtarot da Edirai.5Ya yi mulki a Tsaunin Hermon, Salika, da dukkan Bashan, har zuwa iyakar mutanen Geshur da kuma Ma'akatiyawa, da rabin Giliyad, zuwa kan iyakar Sihon, sarkin Heshbon.
6Musa bawan Yahweh, da mutanen Isra'ila sun yi nasara da su, kuma Musa bawan Yahweh ya ba su ƙasar gãdo ga Rubenawa, da Gadawa, da kuma rabin kabilar Manassa.
7Waɗannan su ne sarakunan ƙasar waɗanda Yoshuwa da mutanen Isra'ila suka ci a yammacin Yodan, daga Ba'al Gad a ƙwari kusa da Lebanon zuwa Tsaunin Halak kusa da Idom. Yoshuwa ya ba da ƙasar ga kabilun Isra'ila don su ǧada.8Ya ba da tuddan ƙasar, da kwaruruka, da Arabah, da gefan tuddai, da jejin da kuma Negeb - ƙasar Hitiyawa, Amoriyawa, Kan'aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa, da kuma Yebusiyawa.
9Sarakunan sun haɗa da sarkin Yeriko da sarkin Ai da ke kusa da Betel,10da sarkin Yerusalem da sarkin Enayim,11da sarkin Yarmut da sarkin Lakish,12da sarkin Eglon da sarkin Gezer,
13da sarkin Debir da sarkin Geder,14da sarkin Horma da sarkin Arad,15da sarkin Libna da sarkin Adullam,16da sarkin Makkeda da sarkin Betel,
17da sarkin Taffuwa da sarkin Hefer,18da sarkin Afek da sarkin Lasharon,19da sarkin Madon da sarkin Hazor,20da sarkin Shimron Meron da sarkin Akshaf,
21da sarkin Ta'anak da sarkin Megiddo,22da sarkin Kedesh da sarkin Yokniyam a Karmel,23da sarkin Dor a Nafat Dor da sarkin Goyim a Gilgal,24da kuma sarkin Tirza. Yawan sarakunan kuwa talatin da ɗaya ne dukkansu.

13

1Yanzu Yoshuwa ya tsufa ƙwarai sai Yahweh ya ce da shi, "Ka tsufa ƙwarai, amma har yanzu akwai sauran ƙasar da yawa da ba a mallaka ba.

2Wannan ita ce ƙasar da ta rage: a dukkan sashin Filistiyawa, da dukkan waɗanda ke Geshuriyawa,3(daga Shihor, wanda ke gabas da Masar da wajen arewanci iyakar Ekron, wanda ake ɗauka ta Kan'aniyawa ce, da sarakuna biyar na Filistiyawa, da su ke Gaza, Ashdod, Ashkelon, Gat da Ekron - da ƙasar Aviyawa).
4A kudu (da ƙasar Aviyawa); akwai sauran ƙasashen Kan'aniyawa, da Ara wanda ta ke ta Sidoniyawa, zuwa Afek har kuma iyakar Amoriyawa;5da ƙasar Gebaliyawa, dukkan Lebanon wajen fitowar rana, zuwa Ba'al Gad ƙasar Tsaunin Hermon zuwa Lebo Hamat.
6Kuma da dukkan mazaunan ƙasar tuddai daga Lebanon har zuwa can Misrefot Mayim, da dukkan mutanen Sidon. Zan kore su a gaban sojojin Isra'ila. Ka tabbatar ka raba ƙasar ga Isra'ila a matsayin gãdonsu, kamar yadda na ummarce ka.7Raba wannan ƙasar a matsayin gãdo ga kabilu tara, da kuma ga rabin kabilar Manasse.
8Tare da sauran rabin kabilar Manasse, da Rubenawa da kuma mutanen Gad sun karɓi nasu gãdon wanda Musa ya ba su a wajen gabas da Yodan,9daga Arowa wadda take a gefen kwarin Kogin Arnon (ya hada da birnin da ke tsakiyar kwarin), da dukkan ƙasar tudu ta Medeba har zuwa Dibon;
10dukkan biranen Sihon da sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon, zuwa ga iyakar Amoniyawa;11Giliyad, da kuma yankin Geshuriyawa da Makatiyawa da dukkan na Tsaunin Harmon da dukkan Bashan zuwa Saleka;12da dukkan mulkin Og a Bashan, wanda ya yi sarauta a Ashtarot da Edirai - waɗannan su ne ragowar mutanen Refayim - Musa ya buge su ya kuma kore su.
13Amma duk da haka mutanen Israila ba su kori Geshuriyawa ko Makatiyawa ba. Maimakon haka, Geshuriyawa da Makatiyawa sun zauna a cikin Isra'ila har wa yau.
14Ga kabilar Lebi ne kaɗai Musa bai ba da ta gado ba. Hadayu na Yahweh, Allah na Isra'ila, wanda aka yi da wuta, ǧadonsu, kamar yadda Allah ya faɗawa Musa.
15Musa ya riga ya ba kabilar Ruben nasu ǧadon bisa ga iyali-iyali.16Nasu yankin ƙasar daga Arowa, a gefen ƙwarin Kogin Arnon, da kuma birnin da yake tsakiyar kwarin, da dukkan tuddai kusa da Medeba.
17Ruben kuma ya sami Heshbon da dukkan biranenta da suke kan tudu, Dibon, da Bamot Ba-al, da Bet Ba'al Miyon,18da Yahaz, da Kedemot, da Mefa'at,19da Kiriyatayim, da Sibma, da Zeret Shahar da ta ke bisa tudun da yake cikin kwarin.
20Ruben kuma ya karɓi Bet Feyor, da gangaren Fisga, da Bet Yeshimot,21da dukkan biranen kan tudu, da dukkan masarautar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya sarauci Heshbon, wanda Musa ya ci shi da yaƙi tare da shugabanin Midiyawa, Ewi, Rekem, Zur, Hur da Reba, sarakunan Sihon, wanda ya zauna a ƙasar.
22Mutanen Isra'ila kuma su ka kashe shi da takobi, Balaam ɗan Beyor, matsubbaci, daga cikin sauran waɗanda da su kashe.23A iyakar kabilar Ruben akwai Kogin Yodan, wannan shi ne iyakarsu. Wannan shi ne ǧadon kabilar Ruben, da aka ba kowanensu na iyalinsu, tare da biranensu da ƙauyukansu.
24Wannan shi ne abin da Musa ya ba kabilar Gad, bisa ga iyalinsu:25Yankin ƙasarsu shi ne Yaza, da dukkan biranen Giliyad da rabin ƙasar Ammoniyawa, zuwa Arowa, wadda ke gabas da Rabbah,26daga Heshbon zuwa Ramat Mizfa da Betonim, daga Mahanayim zuwa iyakar Debir.
27A kwarin, Musa ya ba su Bet Haram, Bet Nimrah, Sukkot da Zafon da sauran ragowar mulkin Sihon sarkin Heshbon, tare da Yodan ne iyaka, zuwa iyakar Tekun Kinneret a gabashin hayin Yodan.28Wannan shi ne gãdon kabilar Gad bisa ga iyalinsu, tare da biranensu da ƙauyukansu.
29Musa ya ba da gãdo ga rabin kabilar Manasse. An ba da ita ga rabin kabilar mutanen Manasse, bisa ga iyalinsu.30Yankin ƙasarsu daga Mahanayim, da dukkan Bashan da dukkan sarautar Og sarkin Bashan da dukkan garuruwan Yayir da waɗanda su ke a Bashan, birane sittin ne;31rabin Giliyad, da Ashtarot da Edirai (biranen masarautar Og a Bashan). Waɗannan ne aka ba da su ga iyalin Makir ɗan Manasse - rabin mutanen Makir, an ba kowanne iyali.
32Wannan shi ne gãdon da Musa ya ba su a kan filayen Mowab, a hayin gabashin Yodan na Yeriko.33Musa bai ba kabilar Lebi gãdo ba. Yahweh, Allah na Isra'ila, shi ne gãdonsu, kamar yadda ya faɗa masu.

14

1Waɗannan su ne yankunan ƙasar da mutanen Isra'ila suka karɓa matsayin gãdo a ƙasar Kan'ana, wanda Eliyeza firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da kuma iyalin shugabainin kabilun kakaninsu na mutanen Isra'ila.

2Gãdonsu ya sa mu ne ta hanyar jefa kuri'a don kabilun nan tara da rabi, kamar yadda Yahweh ya ummarta ta hannun Musa.3Domin Musa ya riga ya ba da gãdon ga kabilu biyu da rabi can hayin Yodan, amma ga Lebiyawa bai ba su gãdo ba.4Kabila Yosef kuma kabilu biyu ne, Manasse da Ifaim. Lebiyawa kuwa ba a ba su wani yanki na ƙasar gãdo ba, sai dai an ba su birane da za su zauna, tare da filayen da za su yi kiwon garkensu da kuma kayan da su ke bukata.5Mutanen Isra'ila kuwa su ka yi kamar yadda Yahweh ya ummarci Musa, sun rarraba ƙasar.
6Sai kabilar Yahuda suka je wurin Yoshuwa a Gilgal. Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze, ya ce masa, "Ka san abin da Yahweh ya ce da Musa mutumin Allah a kanka da ni a Kadesh Barneya.7Ina da shekaru arba'in sa'ad da Musa bawan Yahweh ya aike ni daga Kadesh Barneya in leƙo asirin ƙasar. Na kuma kawo masa ainihin rahoton yadda ya ke a zuciyata.
8Amma 'yan'uwana da mu ka tafi tare sun karyar da zukatan mutanen da tsoro. Amma ni da na bi Yahweh Allahna.9Musa kuwa ya rantse a wannan rana, cewa, 'Hakika a ƙasar nan wanda ƙafafunka su ka ta ka za ta zama gãdonka da kai da 'ya'yanka har abada, domin ka bi Yahweh Allahnka sosai.'
10Yanzu, duba! Yahweh ya kiyaye ni da rai waɗannan shekaru arba'in da biyar, kamar yadda ya faɗa-daga lokacin da Yahweh ya faɗi wannan magana ga Musa, sa'ad da Isra'ila suke tafiya a jeji. Yanzu, duba! ina mai shekaru tamanin da biyar da haihuwa.11Har wannan rana ina nan kamar ranar da Musa ya aike ni waje. ƙarfina yanzu yana nan kamar ƙarfin dă domin yaƙi da kuma zuwa da kowowa.
12Saboda haka yanzu ka ba ni ƙasar tuddai, wadda Yahweh ya yi mani alkawari a waccan rana. Gama ka ji a wannan rana yadda gwarzaye suke a can da manyan birane masu garu. Watakila Yahweh zai kasance tare da ni, ni kuma in kore su, kamar yadda Yahweh ya faɗa."
13Sai Yoshuwa ya sa masa albarka ya kuma ba da Hebron a matsayin gãdo ga Kalibu ɗan Yefunne.14Saboda haka Hebron ta zama gãdon Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze har zuwa wannan rana, domin ya bi Yahweh, Allah na Israila sosai.15Yanzu sunan Hebron kamar da Kiriyat Arba ne. (Arba kuwa ya zama babbban mutum ne cikin gwarzayen.) ‌Ƙasar kuwa ta huta daga yaƙi.

15

1Rabon ƙasar da aka yi wa kabilar mutanen Yahuda, an ba su ne bisa ga iyalansu, ya kai kudu iyaka da Idom, zuwa jejin Zin wanda ta ke can kudu nesa.2Iyakarsu wajen kudu ta mike tun daga ƙarshen Tekun Gishiri, daga sashen gaɓar da ta fuskanci kudu.

3Iyakarsu ta tafi har kudancin tuddan Akrabbim ta kuma zarce zuwa Zin, ta kuma tafi har zuwa kudancin Kadesh Barneya, ta wajen Hezron, har kuma zuwa Addar, ta kuwa karkata zuwa Karka.4Ta wuce zuwa Azmon, ta bi ta rafin Masar, kuma ta zo ƙarshe a teku. Wannan ita ce iyakarsu a kudu.
5Iyakarsu wajen gabas ta kama daga Tekun Gishiri, har zuwa bakin Yodan. Iyakar arewa kuma ta miƙe daga teku zuwa bakin Yodan.6Ta tafi zuwa Bet Hogla ta kuma wuce zuwa arewa da Bet Arabah. Sai ta haura zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.
7Iyakar da ta tafi Debir zuwa Kwarin Achor, da kuma arewacin, sa'an nan ta juya zuwa Gilgal, wadda ta ke daura da tuddun Adummim, wanda ke kudu da gefen kwari. Sai ta zarce zuwa ruwan En Shemesh ta kuma tafi En Rogel.8Sai iyakar ta bi ta Kwarin Ben Hinnom a wajen kudancin birnin Yebusawa (wato Yerusalem). Sa'an nan ta bi ta sashen tuddun da ke shimfiɗe daura da kwarin Hinnom, wajen yamma, a arewacin ƙarshen Kwarin Refayim.
9Sa'an nan iyakar ta faɗaɗa daga bisan tuddai zuwa maɓuɓɓugar ruwan Neftowa, har zuwa can biranen Tsaunin Efron. Sai iyakar ta karkata zuwa Ba'ala (wato Kiriyat Yeyarim).10Sa'an nan iyakar ta kewaye yammacin Ba'ala zuwa Tsaunin Seyir, daga nan kuma ta zarce gefen Tsaunin Yeyarim a arewa (wato Kesalon), sai ta gangara zuwa Bet Shemesh, ta kuma ƙetare har can zuwa Timna.
11Iyakar kuwa ta bi ta gefen arewacin tuddun Ekron, sa'an nan ta karkata kewayin Shikkeron ta kuma wuce zuwa Tsaunin Ba'ala, daga wurin ta tafi zuwa Yabneyel. Iyakar ta ƙare a teku.12Yammacin iyakar Babbar Tekun da kuma gaɓarta. Wannan iyakar na kewaye da kabilar Yahuda, bisa ga iyalin kowa.
13Don kiyaye ummarnin Yahweh ga Yoshuwa, Yoshuwa ya ba Kaleb ɗan Yefunne rabonsa na ƙasar a tsakiyar kabilar Yahuda, Kiriyat Arba, wato, Hebron (Arba shi ne uban Anak).14Kaleb kuwa ya kori mazan 'ya'yansa uku daga wurin Anak: Sheshai, Ahiman da Talmai, zuriyar Anak.15Ya tafi daga wurin ta wurin rashin amincewar mazaunan Debir (Debir da dã ake Kiriyat Sefer).
16Kaleb yace, "Duk mutumin da ya kai hari ga Kiriyat Sefer har kuma ya kama ta, zan ba shi 'yata Aksa a matsayin mata."17Da Otniyel ɗan Kenaz, ɗan'uwan Kaleb, ya ci ta, Kalibu kuwa ya ba shi Aksa 'yarsa matsayin matarsa.
18Bayan wannan, Aksa ta zo ga Otniyel ta kuma iza shi ya roƙi babanta fili. Da ta sauka daga kan jakinta, Kaleb ya ce mata, "Me kike bukata?"
19Aksa ta amsa, "Ka yi mani alheri na musamman, da yake ka ba ni ƙasa a Negeb: ka kuma ba ni maɓuɓɓugar ruwa."Kaleb kuwa ya ba ta maɓuɓɓugar tuddu da kuma maɓuɓɓugar kwari.
20Wannan shi ne gãdon kabilar Yahuda, da aka ba iyalinsu
21Biranen na kabilar Yahuda da ke can kudu sosai, suna wajen iyakar Idom, su ne Kabzeyel, Eder, Yagur,22Kina, Dimona, Adada,23Kedesh, Hazor, Yitnan,24Zif, Telem, Beyalot.
25Hazor Hadatta, Kiriyot Hezron (wato an san shi da Hazor),26Amam, Shema, Molada,27Hazar Gadda, Heshmon, Bet Felet,28Hazar Shuwal, Biyasheba, Biziyotiya.
29Ba'ala, Iyim, Ezem,30Eltolad, Kesil, Horma,31Ziklag, Madmanna, Sansanna,32Labayot, Shilhim, Ayin, Rimmon. Wadannan su ne birane ashirin da tara dukkansu, har da ƙauyukansu.
33A kwarin ƙasar tuddu ta yamma, akwai su Eshtawol, Zora, Ashna,34Zanowa, En Gannim, Taffuwa, Enam,35Yamut, Adullam, Soko, Azeka36Shayarim, Aditayim, Gedera, (wato Gederotayim). Waɗannan su ne birane goma sha huɗu yawansu duk da ƙauyukansu.
37Zenan, Hadasha, Migdalgad,38Diliyan, Mizfa, Yokteyel,39Lakish, Bozkat, Eglon.
40Kabbon, Lahmas; Kitlish,41Gederot, Bet Dagon, Na'ama, Makkeda. Waɗannan su ne birane goma sha shida yawansu duk da ƙauyukansu.
42Libna, Eter, Ashan,43Yifta, Ashna, Nezib,44Kaila, Akzib, Maresha. Waɗannan su ne birane tara, duk da ƙauyukansu.
45Ekron, tare da kewayan garuruwa da ƙauyuka;46daga Ekron zuwa Babbar Teku, dukkan mazaune waɗanda su ke kusa da Ashdod, da dukkan ƙauyukanta.47Ashdod, da kewayan garuruwa da ƙauyukanta; Gaza, da kewayan garuruwa da ƙauyukanta; zuwa rafin Masar, da kuma zuwa Babbar Teku tare da gaɓarta.
48A tuddun ƙasar, Shamir, Yattir, Soko,49Danna, Kiriyat Sanna (wato Debir),50Anab, Eshtimo, Anim,51Goshen, Holon, da Gilo. Waɗannan su ne birane goma sha daya, tare da ƙauyukansu.
52Arab, Duma, Eshan,53Yanim, Bet Taffuwa, Afeka,54Humta, Kiriyat Arba (wato Hebron), da Ziyor. Waɗannan su ne birane tara, tare da ƙauyukansu.
55Mawon, Karmel, Zif, Yutta,56Yezriyel, Yokdiyam, Zanowa,57Kayin, Gibiya, da kuma Timna, Waɗannan su ne birane goma, tare da ƙauyukansu.
58Halhul, Bet Zur, Gedor,59Ma'arat, Bet Anot, da kuma Eltekon. Waɗannan su ne birane shida, tare da ƙauyukansu.
60Kiriyat Ba'al (wato Kiriyat Yeyarim), da kuma Rabba. Waɗannan su ne birane biyu, tare da ƙauyukansu.61A cikin jeji kuwa, akwai su Bet Arabah, Middin, Sekaka,62Nibshan, da Birnin Gishiri, da En Gedi. Waɗannan su ne birane shida, tare da ƙauyukansu.
63Amma domin Yebusiyawa, mazaunan Yerusalem, kabilar Yahuda ba su iya korar su ba, don haka Yebusiyawa su ka yi zamansu tare da kabilar Yahuda har zuwa wannan ranar.

16

1Ƙasar da aka ba kabilar Yosef ta kama tun daga Yodan har zuwa Yeriko, gabas da ruwan Yeriko, zuwa daji, ta haura daga Yeriko zuwa ƙasar tuddun Betel.2Sai ta tafi zuwa Betel ta Luz ta kuma zarce zuwa Atarot, karkarar Arkiyawa.

3Sai ta gangara yammacin karkarar Yafletiyawa, har can ƙarƙashin karkarar Bet Horon, ta kuma tafi har Gezer; ta ƙare a teku.4Ta wannan hanyar ce kabilun Yosef, da Manasse da kuma Ifraim su ka sami na su gãdon.
5Karkarar kabilar Ifraim wadda aka ba iyalinsu ta kama kamar haka: iyakar gãdonsu a wajen gabas ta tafi zuwa Atarot Addar har can kwarin Bet Horon,6daga can ta cigaba har teku. Daga Mikmetat a arewa ta juya zuwa gabashin Ta'anat Shilo, ta kuma wuce gaba wajen gabas da Yanowa.7Sai ta tafi can har Yanowa zuwa Atarot ta kuma tafi Na'ara, ta kuma kai Yeriko, ƙarshen Yodan.
8Daga Taffuwa iyakarta ta tafi yammacin rafin Kana ta kuma ƙare a teku. Wannan shi ne gãdon kabilar Ifraim, wadda aka ba iyalinsu,9tare da biranen da aka zaɓa don kabilar Ifraim a cikin gãdon kabilar Manasse - dukkan biranen, tare da ƙauyukansu.
10Su ba su ƙore Kan'aniyawa waɗanda su ke zama a Gezer ba, saboda haka Kan'aniyawan da ke zama cikin Ifraim su na nan har wannan rana, amma waɗannan mutanen an sa su yin aikin dole.

17

1Wannan it ce ƙasar da aka ba kabilar Manasse (wanda ya ke shi ne ɗan farin Yosef) - wato, Makir wanda ya ke ɗan farin Manasse shi ma kuma uban Giliyad. Zuriyar Makir an ba su ƙasar Giliyad da Bashan, domin Makir mutum ne jarumi a gun yaƙi.2Ƙasar an ba da ita ga sauran kabilar Manassa, an ba da ita ga iyalinsu -- Abiyeza, Helek, Asriyel, Shekem, Hefer, da Shemida. Waɗannan su ne zuriyar maza na Manasse ɗan Yosef, bisa ga iyalinsu.

3Yanzu Zelofehad ɗan Hefer ɗan Giliyad ɗan Makir ɗan Manasse ba shi da 'ya'ya maza, amma sai 'ya'ya mata kaɗai. Sunayen 'ya'yansa mata su ne Mala, Noah, Hogla, Milka, da Tirza.4Sun zo wurin Eliyeza firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabanin, sun kuma ce, "Yahweh ya umarci Musa da ya ba mu gãdo tare da 'yanuwanmu maza." Saboda, bin umarnin Yahweh, ya ba waɗannan matan gãdo a cikin 'yan'uwansu maza na mahaifinsu.
5Yanki goma na ƙasar da aka ba Manasse a Giliyad da Bashan, wanda ya na ɗaya gefen Yodan,6domin 'ya'ya mata na Manasse sun karɓi gãdonsu tare da 'ya'yansa maza. Ƙasar Giliyed an ba sauran kabilar Manasse.
7Yankin ƙasar Manasse ya kai daga Ashar zuwa Mikmetat, wadda ta ke gabas da Shekem. Sai kuma iyakarta ta tafi kudu zuwa waɗanda su ke zama kusa da ruwan Taffuwa.8(Ƙasar Taffuwa ta ƙarƙashin Manasse, amma garin Taffuwa ya na kan iyakar Manassa ƙarƙashin kabilar Ifraim.)
9Iyakar kuma ta gangara zuwa rafin Kana. Waɗannan biranen kudu da rafin da ke cikin garuruwan Manasse su na ƙarƙashin Ifraim. Iyakar Manasse kuwa tana arewacin rafin, ta kuma ƙarashe a teku.10Ƙasar da ke kudu ta na ƙarƙashin Ifraim, kuma ƙasar da ke arewa ta Manasse ce; kuma teku ce ƙarshen iyakarta. A arewacin gefenta kuwa Ashar za a tarar, a kuma gabashinta, Issaka.
11A cikin Issaka kuma da Ashar, Manasse ya sa mi Bet Shan da ƙauyukanta, Ibleyam da ƙauyukanta, mazaunan Dor da ƙauyukanta, mazaunan Endor da ƙauyukanta, mazaunanTa'anak da ƙauyukanta, da mazaunan Megiddo da ƙauyukanta, (da kuma sulusin birin Nafet).12Duk da haka kabilar Manasse ba su iya mallakar waɗannan biranen ba, domin Kan'aniyawa sun ci gaba da zama a wannan ƙasar.
13Lokacin da mutanen Isra'ila su ka yi ƙarfi, sai su ka tilasta wa Kan'aniyawa su yi aikin dole, amma ba su kore su gaba ki ɗaya ba.
14Sai zuriyar Yosef su ka ce da Yoshuwa, "Me ya sa ka ba mu ƙasa ɗaya kaɗai da kuma kashin gãdo ɗaya, da ya ke mu mutane masu yawa ne, duk da albarkar da Yahweh ya yi mana?"15Yoshuwa yace da su, "Idan ku babbar jama'a masu yawa ce, ku tafi can da kanku a jeji ku gyarawa kanku ƙasa acikin ƙasar Ferizziyawa da kuma Refayawa. Ku yi haka, a tuddan ƙasar Ifraim da ya ke ta yi ma ku kaɗan ainun.
16Sai zuriyar Yosef su ka ce, "Ƙasar tuddai ba za ta ishe mu ba. Amma dukkan Kan'aniyawa da su ke zaune a kwarin su na da karusai na ƙarafa, dukkan waɗanda zaune a Bet Shan da ƙauyukanta, da kuma waɗanda ke zaune a kwarin Yezriyel."17Yoshuwa kuwa ya cewa gidan Yosef - wato Ifraim da Manasse, "Ku mutane ne masu girma da yawa, kuma ku na da iko da ƙarfi. Kada ku tsaya a kashin ƙasa ɗaya kaɗai da aka ba ku.18Ƙasar tuddai ma za ta zama taku. Ko da yake daji ne, ku gyara ta ku kuma mallake ta har iyakokinta masu nisa. Sai ku kore Kan'aniyawa daga cikinta, ko da ya ke su na da karusai na ƙarfe, kuma su na da ƙarfi ainun."

18

1Sai dukkan taron jama'ar Isra'ila su ka taru a Shilo. A wurin su ka kafa rumfar taruwa sun ci nasara akan ƙasar dake gabansu.2Har yanzu akwai kabilu bakwai cikin mutanen Isra'ila waɗanda ba a ba su na su gãdon ba tukuna.

3Yoshuwa ya ce da mutanen Isra'ila, "Har yaushe za ku ƙi tafiya cikin ƙasa wadda Yahweh, Allah na kakanninku ya ba ku?4Ku sanya wa kanku mutum uku daga kowacce kabila, kuma zan aike su waje. Za su fita su duba ƙasar tudu da gangare. Za su rubuta bayanin ta bisa ga gădon kowannensu, sa'an nan za su komo wuri na.
5Za su raba ta kashi bakwai. Yahuda za su kasance cikin na su yanki wajen kudu, sai gidan Yosef kuma za su ci gaba da zama a yankin arewa.6Za ku kasa ƙasar kashi bakwai sa'annan ku kawo taswirar ƙasar wurina. Zan jefa ma ku ƙuri'u a nan gaban Yahweh Allahn mu.
7Gama Lebiyawa ba su da gădo a cikin ku, gama aikin Lebiyanci na Yahweh shi ne rabon su. Gad, da Ruben da rabin ƙabilar Manasse sun karɓi gadon su a ƙetaren Yodan. Wannan shi ne gãdon da Musa bawan Yahweh ya ba su."
8Sai mutanen su ka tashi su ka tafi. Yoshuwa ya umarci waɗan da su ka tafi domin su rubuta tsarin taswirar ƙasar, ya ce, "Ku tafi ku kai ku komo cikin ƙasar ku rubuta adadinta sa'annan ku komo wurina. Zan jefa ƙuri'u a nan domin ku a gaban Yahweh a Shilo."9Mutanen kuwa su ka tashi suka tafi cikin ƙasar tudu da gangare su ka rubuta bayanin yadda ƙasar take kashi bakwai bisa ga biranenta, sun tsara biranen da sashin sa. Daga nan suka dawo wurin Yoshuwa cikin sansani a Shilo.
10Sai Yoshuwa ya jefa masu ƙuri'u a Shilo gaban Yahweh. A can ne Yoshuwa ya rabawa mutanen Isra'ila ƙasar, kowannesu aka bashi nasa rabon ƙasar.
11‌Ƙasar da aka ba kabilar Benyamin kowanne an ba su bisa ga iyalinsu. Yankin ƙasarsu tana tsakanin zuriyar Yahuda da zuriyar Yosef.12Ta ɓangaren arewa, iyakarsu ta fara daga Yodan. Iyakar ta hau wajen sashin arewacin Yeriko, daga nan ta hau zuwa wajen tudun ƙasar yamma. Can ta kai jejin Bet Aben.
13Daga can iyakar ta wuce zuwa kudu sashen Luz (wato Betel ke nan). Iyakar kuwa ta gangara zuwa Atarot Addar, tabi ta tsaunin da ke kwance a kudancin Bet Horon.14Sai iyakar tabi ta wani sashi dabam: ta ɓangaren yamma ya juya wajen kudu, ta nufi wajen hayin dutse daga Bet Horon. Wannan iyakar ta ƙarasa a Kiriyet Baal (wato Kiriyet Yeyarim), birni wanda mallakar kabilar Yahuda ne. Wannan ta haɗa iyakar yammaci.
15Iyaka ta wajen kudu ta fara daga wajen Kiriyat Yeyarim. Iyakar ta tafi daga nan zuwa Efron, zuwa maɓulɓular ruwayen Neftowa.16Sai iyakar ta gangaro ƙasa zuwa iyakar dutsen dake akasi da Kwarin Ben Hinom, wanda ke arewacin ƙarshen Kwarin Refayim. Daga nan ya gangara zuwa Kwarin Hinnom, kudancin gangaren Yebusiyawa ya nausa ƙasa zuwa En Rogel.
17Ta juya wajen arewa, ta nufi wajen En Shemesh, daga nan kuma ta fita zuwa Gelilot, wanda ke akasi da mahayin Adumim. Daga nan sai ya gangara zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.18Ya wuce zuwa arewa inda suke kafaɗa da Bet Arabah ta gangara zuwa Arabah.
19Iyakar ta wuce arewa kafaɗa da Bet Hogla. Iyakar ta ƙarasa arewa wajen gaɓar Tekun Gishiri, ta ɓangaren kudu ta ƙare a Yodan. Iyaka ta kudu kenan.20Yodan kuwa ta kafa iyakarta ta ɓangaren gabas. Wannan shi ne gadon Kabilar Benyamin, an kuma ba kowannensu bi sa ga zuriyar su, iyaka bayan iyaka, a ko'ina.
21Biranen kabilar Benyamin bisa ga iyalansu su ne; Yeriko, Bet Hogla, da Emek Keziz,22Bet Arabah, Zemarayim, Betel,23Abbim, Fara, Ofra,24Kefar Ammoni, Ofni da Geba. Birane goma sha biyu ne haɗe da ƙauyukansu.
25Akwai kuma biranen Gibiyon, Ramah,26Birot, Mizfa, Kefira, Mozah,27Rekem, Irfil, Tarala,28Zela, Hayelef, Yebus, (wato Yerusalem ke nan) Gibiya da Kiriyat. Akwai birane goma sha hudu, duk da ƙauyukan su. Wannan shi ne gãdon Benyamin domin zuriyarsu.

19

1Kaɗa ƙuri'u na biyu ta faɗa kan Simiyon aka ba su bisa ga zuriyarsu. Gãdonsu ya na tsakiyar gãdon kabilar Yahuda.

2Su ka samu domin gãdonsu Biyasheba, Sheba, Modala,3Hazar Shuwal, Balal, Ezem,4Eltolad, Betul, da Hormah.
5Simiyon kuma ya na da Ziklag, Bet Markabot, Hazar Susa,6Bet Lebayot, da Sharuhen, Waɗannan birane goma sha uku sun haɗa da ƙauyukansu.7Har yanzu Simiyon ya na da Ayin, Rimmon, Etar da Ashan. Birane huɗu kenan duk da ƙauyukansu.
8Waɗannan tare da ƙauyaukan dake tare da biranen har zuwa Ba'alat Biya (ɗaya suke da Ramah cikin Negeb). Wannan shi ne gãdon ƙabilar Simiyon, wanda aka ba iyalinsu.9Daga cikin gãdon ƙabilar Simiyon aka sami wani sashin rabon kabilar Yahuda. Saboda rabon ƙasar da aka ba Yahuda ya yi masu yawa, ƙabilar Simiyon sun karɓi gădonsu daga cikin tsakiyar nasu rabo.
10Kaɗa ƙuri'u na uku ya faɗa akan kabilar Zebulun, aka kuma ba da ita ga zuriyarsu. Iyakar gãdonsu ta fara daga Sarid.11Iyakar su ta hau wajen yammaci ta nufi Marala, ta kai Dabbeshet; ta malala zuwa rafin dake akasi da Yokneyam.
12Daga Sarid iyakar ta karkato zuwa gabashi ta tafi zuwa iyakar Kislot Tabor. Daga nan ta fita zuwa Daberat ta hau zuwa Yafiya.13Daga can ta ratsa zuwa gabas har Gat Hefa, zuwa Et Kazin; ta sake fita zuwa Rimmon ta juya zuwa wajen Neya.
14Iyakar ta karkato zuwa wajen arewa zuwa Hannaton ta ƙarasa a Kwarin Ifta El.15Wannan yankin ya hada da biranen Kattat, Nahalal, Shimron, Idala da Betlehem. Akwai birane goma sha biyu duk da ƙauyukansu.16Wannan shi ne gãdon ƙabilar Zebulun, wanda aka ba zuriyarsu - da birane duk da ƙauyukansu.
17Kaɗa kuri'u na hudu ya faɗa kan Issaka, an ba su bisa ga zuriyarsu.18Iyakarsu ta haɗa da Yezriyel, Kesulot, Shunem,19Hafarayim, Shiyon da Anaharat.
20Ya haɗa da Rabbit, Kishon, Ebez,21Remet, En Gannim, En Hadda da Bet Fazzez.22Iyakarsu takai Tabor, Shahazuma, da Bet Shemesh, ta ƙarasa a Yodan. Birane goma sha shida, duk da ƙauyukansu.
23Wannan shi ne gãdon kabilar Issaka, wanda aka ba su bisa ga zuriyarsu - birane da ƙauyukansu.
24Kaɗa Kuri'u na biyar ya faɗa kan kabilar Asha, aka kuma ba zuriyarsu.25Iyakarsu ta hada da Helkat, Hali, Beten, Akshaf,26Allammelek, Amad da Mishall. Daga yamma iyakar ta kai zuwa Karmel da Shiho Libnat.
27Daga nan ta karkata zuwa gabas zuwa Bet Dagon sa'an nan ta tafi har Zebulun, zuwa Kwarin Ifta El, arewaci zuwa Bet Emek da Neyiyel. Taci gaba zuwa Kabul wajen arewa.28Daga nan tayi wajen Abdon, Rehob, Hammon da Kana har zuwa Babban Sidon.
29Iyakar tayi kwana zuwa Ramah, zuwa birnin Taya mai ganuwa. Sai iyakar ta karkata zuwa Hosa ta ƙarasa a teku a yankin Akzib,30Umma, Afek, da Rehob. Akwai birane ashirin da biyu duk da ƙauyukansu.
31Wannan shi ne gãdon kabilar Asha, an basu bisa ga zuriyarsu - birane da ƙauyukansu.
32Kaɗa Kuri'u na shida ya faɗa kan Naftali, aka kuma ba zuriyarsu.33Iyakar ta fara daga oak a Za'ananim, zuwa Adami Nekeb da Yabneyel, zuwa Lakkum; ta ƙarasa a Yodan.34Iyakar ta karkata zuwa yammaci har Aznot Tabor ta nausa zuwa Hukkok; ta taɓa Zebulun daga kudanci ta kai Asha daga yamma da Yahuda daga gabas har Kogin Yodan.
35Birane masu ganuwa sune Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,36Adama, Ramah, Hazor,37Kedesh, Edirai da En Hazor.
38Har yanzu akwai Yiron, Migdal El, Horem, Bet Anat da Bet Shemesh. Akwai birane goma sha tara, duk da ƙauyukansu.39Wannan shi ne gãdon kabilar Naftali wanda aka ba zuriyarsu biranensu duk da ƙauyukansu.
40Kãɗa kuri'u na bakwai suka faɗa kan kabilar Dan an basu bisa ga zuriyarsu.41Iyakar rabon su ya haɗa da Zora, Estawol, Ir Shemesh,42Sha'alabbin, Aijalon da Itla.
43Ta haɗa da Elon, Timna, Ekron,44Elteke, Gibbeton, Ba'alat,45Yehud, Bene Berak, Gat Rimmon.46Me Yarkon da Rakkon tare da iyaka a ƙetare daga Yoppa.
47Lokacin da iyakar kabilar Dan ta ɓace masu, sai su ka kaiwa Leshem hari su ka yi yaƙi da su, suka ci su, su ka kashe kowanensu da kaifin takobi, suka kwashe mallakar su, suka zauna cikin ta. Suka sake ma Leshem suna zuwa Dan sunan kakansu.48Wannan shi ne gãdon kabilar Dan, an ba zuriyarsu - biranensu, da ƙauyukansu.
49Bayan da suka gama rarraba ƙasar a matsayin gãdonsu, mutanen Isra'ila suka ɗauka daga cikin gãdonsu suka ba Yoshuwa ɗan Nun.50Bisa ga umarnin Yahweh suka bashi birnin daya roƙa, an bashi Timnat Sera cikin ƙasar duwatsu ta Ifraim. Ya gina birni ya zauna ciki.
51Waɗannan sune gãdon da Eliyeza firist, Yoshuwa ɗan Nun, da shugabannin kabilu na mutanen Isra'ila suka raba bisa ga ƙuri'a a Shiloh, a gaban Yahweh a ƙofar shiga rumfar taruwa. Da haka suka gama rarraba ƙasar.

20

1Sai Yahweh yace da Yoshuwa.2"Kayi magana da mutanen Isra'ila, kace, 'Ka keɓe biranen mafaka wanda nayi magana da kai ta hannun Musa.3Kayi haka domin duk wanda ya kashe wani bada gangan ba zai iya zuwa can. Waɗannan birane za su zama wurin mafaka domin duk wanda ya nemi ɗaukar fansar jinin mutumin da aka kashe.

4Zai ruga zuwa ɗaya daga cikin waɗannan biranen zai tsaya a ƙofar shiga birnin, zai bayyyana damuwarsa ga dattawan garin. Daga nan za su ɗauke shi zuwa cikin birni su bashi wuri domin ya zauna a cikinsu.
5Idan wani daga cikin su ya zo domin ya yi ƙoƙarin ɗaukar fansar jinin wanda aka kashe, mutanen garin ba za su bada wanda ya yi kisan ga hukuma ba. Ba za su yi haka ba domin ba da gan - gan ne ya kashe maƙwabcinsa ba, kuma bashi da wata ƙiyayya game dashi a baya.6Dole ya zauna cikin birnin har lokacin da zai tsaya gaban jama'a domin hukunci, har lokacin mutuwar babban Firist mai aiki a kwanakin nan, daga nan sai shi wanda ya yi kisan bisa ga kuskure ya koma garinsu gidansa kuma, daga in da ya gudu."'
7Sai Isra'ilawa suka zaɓi Kedesh cikin Galili, cikin ƙasar duwatsu ta Naftali, Shekem cikin ƙasar duwatsu ta Ifraim da Kiriyet Arba (wato Hebron ke nan) cikin ƙasar duwatsu ta Yahuda.8Ƙetaren Yodan gabashin Yeriko, suka zaɓi Beza, cikin jeji bisa tudu daga kabilar Ruben; Ramot Giliyad, daga kabilar Gad; da Golan cikin Bashan, daga kabilar Manasse.
9Waɗannan sune biranen da aka zaɓa domin dukkan mutanen Isra'ila da kuma baƙin dake zaune cikinsu, domin duk wanda ya kashe wani bada gan - gan ba zai iya rugawa don tsirar da ransa. Wannan mutum ba zai mutu ta hanun wanda yake son ɗaukar fansar jinin da aka zubar ba, har sai shi wanda ake zargin ya tsaya gaban taron jama'a.

21

1Daga nan sai shugabanni na zuriyar Lebiyawa suka zo wurin Eliyeza firist, da Yoshuwa ɗan Nun da shugabanni na iyalan kakanninsu a tsakanin mutanen Isra'ila.2Sai suka yi magana da su a Shilo cikin ƙasar Kan'ana suka ce, "Yahweh ya umarta ta hannun Musa a ba mu birane mu zauna ciki, tare da makiyayarsu domin dabbobinmu."

3Bisa ga umarnin Yahweh, mutanen Isra'ila suka ɗiba daga cikin gãdonsu na birane da makiyayarsu suka ba Lebiyawa.
4Kaɗa kuri'u domin zuriyar Kohatawa ya bada wannan sakamako: Firistoci - zuriyar Haruna waɗanda su ke daga Lebiyawa - sun karɓi birane goma sha uku daga kabilar Yahuda, daga kabilar Simiyon da kuma daga kabilar Benyamin.5Sauran zuriyar Kohatawa bisa ga kuri'u sun karɓi birane goma daga zuriyar kabilar Ifraim, Dan da rabin kabilar Manasse.
6Mutanen zuriyar Gashon an basu, ta wurin kaɗa kuri'u birane goma sha uku daga zuriyar Issaka, Asha, Naftali da rabin kabilar Manasse cikin Bashan.7Mutanen da su ke daga zuriyar Merari sun karɓi birane goma sha biyu daga kabilar Ruben, Gad da Zebulun.
8Don haka mutanen Isra'ila sun bada waɗannan birane, ga Lebiyawa ta wurin jefa kuri'u (duk da makiyayarsu) kamar yadda Yahweh ya umarta ta hannun Musa.9Daga kabilun Yahuda da Simiyon aka bada waɗannan birane da aka lisafta sunayensu a nan.10Waɗannan birane an bayar da su ga zuriyar Haruna, waɗanda su ke daga zuriyar Kohatawa waɗanda daga kabilar Lebi su ke. Waɗanda kaɗa ƙuri'un farko kansu ya faɗa.
11Isra'ilawa sun basu Kiriyat Arba (Arba shi ne uban Anak), wato Hebron ke nan, cikin ƙasar duwatsu ta Yahuda, tare da makiyayar da ke kewaye da ita.12Amma gonakin da ke birane da ƙauyukansu an riga an ba Kaleb ɗan Yefunne, a matsayin mallakarsa.
13Ga zuriyar Haruna firist sun bashi Hebron da makiyayarta, wanda shi ne birnin mafaka ga wanda ya kashe wani cikin kuskure da Libna duk da makiyayarta.14Yattir da makiyayarta da Eshtemowa da makiyayarta.15Suka kuma ba da Holon da makiyayarta, Debir da makiyayaarta,16Ayin da makiyayarta, Jutta da makiyayarta da Bet Shemesh da makiyayarta. Akwai birane tara da aka bayar daga cikin kabilun nan biyu.
17Daga kabilar Benyamin an bada Gibiyon duk da makiyayarta, Geba da makiyayarta,18Anatot duk da makiyayarta, da Almon da kewayenta birane huɗu ke nan.19Biranen da aka ba firistoci zuriyar Haruna, dukkan su birane goma sha uku ne, haɗe da makiyayarsu.
20Sauran Kohatawa - su Lebiyawan nan waɗanda su ke daga iyalin Kohat - sun sami nasu biranen daga kabilar Ifraim, ta wurin jefa kuri'u.21An basu Shekem duk da makiyayarsu cikin ƙasar duwatsu ta Ifraim - birnin mafaka domin wanda ya yi kisan kai cikin kuskure - Geza da makiyayarsu.22Kibzayim da makiyayarsu, da Bet Horon da makiyayarsu - birane huɗu ne dukka.
23Daga kabilar Dan, zuriyar Kohat an ba su Eltike da makiyayarsu, Gibbeton da makiyayarsu.24Aijalon da makiyayarsu da Gat Rimmon da makiyayarsu - duka birane huɗu ne.
25Daga rabin kabilar Manasse, zuriyar Kohat an basu Ta'anak tare da makiyayarsu da Gar Rimmon tare da makiyayarsu - birane biyu.26Akwai birane goma dukka domin sauran zuriyar Kohatawa, duk da makiyayarsu.
27Daga rabin kabilar Manasse, zuwa zuriyar Gashon waɗannan sauran zuriyar Lebi ne, an bada Golan cikin Bashan tare da makiyayarsu - birnin mafaka domin wanda ya yi kisan kai bisa ga kuskure, tare da Be Eshtera da makiyayarsu - birane biyu ne duka.
28Ga zuriyar Gashon an basu Kishon daga kabilar Issaka, tare da makiyayarsu, Daberat tare da makiyayarsu,29Yarmut tare da makiyayarsu, da En Gannim tare da makiyayarsu.- birane hudu.30Daga kabilar Asha, sun bada Mishal tare da makiyayarsu, Abdon tare da makiyayarsu,31Helkat tare da makiyayarsu da Rehob tare da makiyayarsu - birane huɗu ne dukka.
32Daga kabilar Naftali, sun ba zuriyar Gashon Kedesh cikin Galili tare da makiyayarsu - birnin mafaka domin wanda ya yi kisan kai cikin kuskure; Hammot Dor tare da makiyayarsu, da Kartan tare da makiyayarsu - birane uku ne duka.33Akwai birane goma sha uku duka, daga zuriyar Gashon, tare da makiyayarsu.
34Ga sauran Lebiyawa - na zuriyar Merari - an ba su daga cikin kabilar Zebulun: Yokniyam tare da makiyayarsu, Karta tare da makyyayarsu,35Dimna tare da makiyayarsu, da Nahalal tare da makiyayarsu - dukka birane huɗu ke nan.
36Ga zuriyar Merari an ba su daga kabilar Ruben: Bezer tare da makiyayarsu, Yahaz tare da makiyayayarsu,37Kedemot tare da makiyayarsu, da Mefa'at tare da makiyayarsu - birane huɗu.38Daga cikin kabilar Gad an ba su Ramot cikin Giliyad tare da makiyayarsu - birnin mafaka domin wanda ya yi kisan kai cikin kuskure - da Mahanayim tare da makiyayarsu.
39Zuriyar Merari an ba su Heshbon tare da makiyayarsu, da Yazer tare da makiyayarsu. Waɗannan birane huɗu ne dukka.40Dukkan waɗannan birane ne na zuriyar Merari, waɗanda su ke daga kabilar Lebi - dukka birane goma sha biyun an ba su ne bisa ga kaɗa ƙuri'u.
41Biranen Lebiyawa da aka ɗauka daga cikin tsakiyar mallakar Isra'ila sun kai birane arba'in da takwas, ya haɗa da wuraren kiwonsu.42Waɗannan birane kowanne ya haɗa da makiyayarsu da ke kewaye da su. Haka ya ke ga dukkan waɗannan birane.
43Haka nan Yahweh ya ba da wannan dukkan ƙasa da ya rantse wa kakanninsu, Isra'ilawa su ka mallaketa, su ka zauna cikinta.44Yahweh ya ba su hutawa ta kowanne gefe, kamar yadda ya rantse wa kakanninsu. Babu wani daga cikin maƙiyansu da zai yi nasara da su. Yahweh ya ba da dukkan abokan gabarsu cikin hannunsu.45Babu wani cikin dukkan alƙawura masu kyau da Yahweh ya furta a kan gidan Isra'ila da ya kasa cika. Dukkan su sun tabbata.

22

1A wan can lokaci Yoshuwa ya kira Rubenawa da Gadawa da rabin kabilar Manasse.2ya ce masu, "Kun yi dukkan abin da Musa bawan Yahweh ya umarce ku. Kunyi biyayya da muryata a kan dukkan abinda na umarce ku.3Baku yãshe da 'yan uwanku a yawan kwanakin nan ba, har ya zuwa wannan rana, kun kuma kiyaye umarnan Yahweh Allahn ku.

4Yanzu Yahweh Allahnku ya ba da hutu ga "yan'uwanku, kamar yadda ya alƙawarta masu. Don haka ku juya ku tafi rumfunanku cikin ƙasar mallakarku, wadda Musa bawan Yahweh ya baku a ƙetaren Yodan.5Don haka sai ku kula sosai ku kiyaye dokoki da umarnai waɗanda Musa bawan Yahweh ya umarce ku, ku ƙaunaci Yahweh Allahnku. Kuyi tafiya cikin hanyoyinsa, ku kiyaye dokokinsa, ku manne masa kuyi masa sujada da dukkan zuciyarku da ranku."6Sai Yoshuwa ya albarkace su ya sallame su sai su ka koma rumfunansu.
7Yanzu ga rabin kabilar Manasse Musa ya rigaya ya ba su gãdonsu cikin Bashan, amma ga ɗaya rabin Yoshuwa ya bada gãdo daga cikin na 'yan'uwansu a yammacin Yodan. Yoshuwa ya sallamesu zuwa rumfunansu; ya sa masu albarka, ya ce da su,8"Ku koma rumfunanku da kuɗi masu yawa, da dabbobi masu yawa, da azurfa da zinariya, da tagulla da ƙarfe, da tufafi masu yawan gaske. Ku raba ganimar abokan gabanku tare da 'yan'uwanku."
9Sai zuriyar Ruben da zuriyar Gad, da rabin kabilar Manasse su ka koma gida, suka bar mutanen Isra'ila a Shilo, wadda ke cikin ƙasar Kan'ana. Sun tafi zuwa yankin ƙasar Giliyad, zuwa ƙasar su, wadda su da kansu su ka mallaka, cikin biyayya ga umarnin Yahweh, ta hannun Musa.
10Sa'ad da suka zo Yodan wadda ke cikin ƙasar Kan'ana, sai Rubenawa da Gadawa da rabin kabilar Manasse su ka gina bagadi kusa da Yodan, babban bagadi shahararre kuma.11Da mutanen Isra'ila suka ji labarin nan cewa, "Duba! mutanen Ruben da Gad da rabin kabilar Manasse sun gina bagadi a gaban ƙasar Kan'ana a Gelilot, a yankin da ke kusa da Yodan, a yankin da ke mallakar mutanen Isra'ila."
12Da mutanen suka ji haka, sai dukkan mutanen Isra'ila suka taru a Shilo domin su je su yi yaƙi gãba da su.
13Sai mutanen Isra'ila suka aiki 'yan saƙo ga su Rubenawa da Gadawa da rabin kabilar Manasse, cikin ƙasar Giliyad. Sun kuma aiki Finehas ɗan Eliyeza, Firist.14Tare da shi kuma akwai shugabanni goma, ɗaya daga cikin kowacce kabilar Isra'ila, kuma kowannensu shugabane daga cikin zuriyar mutanen Isra'ila.
15Suka zo wurin mutanen Ruben da Gad da rabin kabilar Manasse, cikin ƙasar Giliyad, suka yi magana da su:16"Dukkan taron jama'ar Yahweh sun faɗi haka, "Wanne irin rashin aminci ne wannan ku ka aikata gãba da Allah na Isra'ila, a wannan rana kun juya daga bin Yahweh kun ginawa kanku bagadi don ku tayarwa Yahweh?
17Zunubinmu a Feyor bai ishe mu ba? Har yanzu bamu tsarkake kanmu daga gare shi ba. Saboda wannan zunubi annobai su ka abko wa jama'ar Yahweh.18Ko ya zama dole ne ku juya ga bin Yahweh a wannnan rana? Idan kuma ku ka yi wa Yahweh tayarwa yau, gobe zai yi fushi da dukkan taron jama'ar Isra'ila.
19Idan ƙasar da ku ka mallaka ta ƙazantu, sai ku ƙetaro ƙasa inda mazaunin Yahweh ya ke zaune domin ku samar wa kanku mallaka daga cikin mu. Ku dai kada ku tayarwa Yahweh, ko ku tayar mana ta wurin gina wa kanku bagadi banda bagadin Yahweh Allahnmu.20Ko Akan ɗan Zera, bai yi laifin karya imani akan zancen waɗannan abubuwa da su ke keɓaɓɓu domin Allah ba? ko hasala ba ta afko wa mutanen Isra'ila ba? Wannan mutum bai mutu shi kaɗai domin laifinsa ba."
21Daga nan sai kabilar Ruben Gad da rabin kabilar Mannasse suka amsa wa shugabannin zuriyar Isra'ila:22"Maigirman nan, Allah, Yahweh! Maigirman nan, Allah, Yahweh! - Ya sani, bari Isra'ila kanta kuma ta sani! Idan cikin tayaswa ne ko cikin saɓawa imani gãba da Yahweh, kada ka yi mana ceto yau23domin mun gina bagadi muka juya ga bin Yahweh. Idan mun gina wannan bagadi domin mu miƙa hadayun ƙonawa, hadayun gari, ko hadayun salama a kansa to bari Yahweh yasa mu biya.
24A'a! Munyi shi cikin tsoro da nufin cewa a lokaci mai zuwa 'ya'yanku za su iya cewa da 'ya'yanmu, 'Ina ruwanku da Yahweh, Allah na Isra'ila?
25Gama Yahweh ya sa Yodan ta zama iyaka tsakanin mu da ku. Ku mutanen Ruben da mutanen Gad, baku da abinda zaku yi da Yahweh.'Da haka 'ya'yan ku zasu iya sa 'ya'yan mu su dena yin sujada ga Yahweh.
26Don haka sai mu ka ce, 'Bari yanzu mu gina bagadi, ba don ƙonannun hadayu ba ba kuma domin wasu hadayu ba,27amma domin zama shaida tsakanin mu da ku, da kuma don zuriya masu tasowa bayan mu, da kuma zamu bauta wa Yahweh a gaban sa, da ƙonannun hadayu da kuma hadayun mu tare da hadayun mu na salama, domin kada 'ya'yanku su ce da 'ya'yanmu a lokaci mai zuwa, "Baku da rabo cikin Yahweh."'
28Sai mu ka ce, 'Idan zasu faɗi mana haka ko su faɗi wa zuriyarmu a lokaci mai zuwa, za mu ce, "Duba! wannan shi ne kwatancin bagadin Yahweh, wanda kakanninmu suka yi, ba domin ƙonannun hadayu ba, ba kuma don hadayu ba, amma domin shaida tsakanin mu da ku".29Bari tayaswa ga Yahweh ta yi nesa da mu, har yau mu juya daga bin sa ta wurin gina bagadi domin ƙonanniyar hadaya, domin hadaya ta gari, ko domin hadayar yanka, banda bagadin Yahweh Allahn mu wanda ke gaban mazamninsa."'
30Sa'ad da Fenihas firist da shugabannin jama'a, wato shugabannin zuriyar Isra'ila waɗanda suke tare dashi, su ka ji kalmomin mutanen Ruben, Gad, da Manasse suka ce, wannan ya zama abu mai kyau a garesu.31Sai Fenihas ɗan Eliyeza firist ya ce da mutanen Ruben, Gad, da Manasse, "Yau mun sani cewa Yahweh yana tsakiyar mu, saboda baku aikata wannan saɓo gãba da shi ba. Yanzu kun ceci mutanen Isra'ila daga hannun Yahweh."
32Daga nan sai Fenihas ɗan Eliyeza firist da shugabannin su ka juya su ka bar Rubenawa da Gadawa, suka bar ƙasar Giliyad, su ka koma ƙasar Kan'ana, zuwa ga mutanen Isra'ila, su ka dawo masu da magana.33Rahoton su ya gamshi mutanen Isra'ila. Mutanen Isra'ila suka albarkaci Allah ba su ƙara maganar yaƙi da Rubenawa da Gadawa ba kan zancen hallaka ƙasar da su ke zaune a ciki.
34Sai mutanen Ruben da Gadawa suka ba bagadi suna, "Shaida" gama suka ce, "Shaida ce tsakanin mu cewa Yahweh shi ne Allah."

23

1Bayan kwanaki masu yawa, bayan da Yahweh ya bada hutu ga Isra'ila daga abokan gãbansu da ke kewaye da su, Yoshuwa kuma ya tsufa ƙwarai.2Sai Yoshuwa ya kira dukkan Isra'ila, da dattawansu, da shugabanninsu, da alƙalansu, da manyansu - ya ce masu, "Ni na tsufa sosai.3Kunga dukkan abin da Yahweh Allahn ku ya yi da dukkan ƙasashen nan domin ku, domin Yahweh Allahn ku shi ne ya yi yaƙi domin ku.

4Duba! Na sanya sauran al'umman da su ka rage a cisu su zama abin gãdo ga kabilun ku tare da dukkan ƙasashen dana rigaya na hallakar daga Yodan zuwa Babban Teku daga yamma.5Yahweh Allahnku zai kore su. Zai tuttura su daga gaban ku. Zai ƙwace ƙasar su, za ku mallaki ƙasar su, kamar yadda Yahweh ya alƙawarta ma ku.
6Sai ku yi ƙarfafa sosai, ku kuma kiyaye dukkan abin da aka rubuta cikin shari'ar Musa kada ku kauce daga gare ta dama ko hagu,7domin kada ku yi cuɗanya da waɗannan al'ummai da su ka rage a cikin ku kada ma ku ambaci sunayen allolin su, ko ku rantse da su, ko ku yi masu sujada, ko ku russuna masu.8Maimakon haka; dole ku manne wa Yahweh Allahn ku kamar yadda ku ka yi zuwa wannan rana.
9Gama Yahweh ya kori al'ummai da manya, masu ƙarfi daga gaban ku. Amma ku, ba mutumin da ya iya tsayawa a gaban ku har wa yau.10Kowanne mutum ɗaya daga cikinku za ya runtumi dubu, domin Yahweh Allahnku, shi ne ya ke yaƙi domin ku, kamar yadda ya alƙawarta maku.11Ku kula da kyau, domin ku ƙaunaci Yahweh Allahnku.
12Amma idan ku ka juya ku ka manne wa waɗannan sauran al'ummai waɗanda su ka rage a tsakiyar ku, ko idan ku ka yi auratayya da su, ko in ku ka yi huɗɗa tare da su su kuma tare da ku,13ku sani tabbas cewa Yahweh Allahnku ba zai ƙara korar waɗannan al'ummai daga gaban ku ba, maimakon haka, za su zama azargiya da tarko gareku, bulala a bayanku, ƙayayuwa cikin idanunku, har sai kun hallaka daga ƙasan nan mai kyau wadda Yahweh Allahnku ya baku.
14Gashi yanzu ina kan tafiya hanya ta dukkan duniya, kuma kun sani da dukkan zukatanku da rayukanku, babu wata kalma data kasa zama gaskiya cikin dukkan abubuwa masu kyau da Yahweh Allahnku ya alƙawarta game da ku, dukkan waɗannan abubuwa sun tabbata game da ku, babu wani abu daya ka sa cika.15Ya zama kuwa kamar yadda kowacce maganar Yahweh Allahnku ya alƙawarta ma ku ta cika, Yahweh zai kawo ma ku dukkan miyagun abubuwa har sai ya hallakar da ku daga ƙasa mai kyau wadda Yahweh Allahnku ya baku.
16Zai yi haka idan har kuka karya alƙawarin Yahweh Allahnku, wadda ya umarce ku ku kiyaye. Idan ku ka je ku ka yi sujada ga waɗansu alloli ku ka russuna masu, sa'annan fushin Yahweh zai yi ƙuna a kan ku, da sauri zaku hallaka daga ƙasa mai kyau wadda ya baku."

24

1Sai Yoshuwa ya tara dukkan kabilun Isra'ila a shekem, ya kira dattawan Isra'ila, da shugabanninsu, da alƙalansu, da magabatansu, suka bayyana kan su gaban Allah.2Sai Yoshuwa ya cewa dukkan jama'a, "Wannan shi ne abinda Yahweh Allah na Isra'ila, ya ce, 'Kakanninku da daɗewa su ka zauna a ƙetaren kogin Yuferatis - Tera, mahaifin Ibrahim da mahaifin Naho - sun kuma yi sujada ga waɗansu alloli.

3Amma na ɗauki mahaifinku zuwa ƙetaren Yuferitis na bishe shi cikin ƙasar Kan'ana na bashi zuriya masu yawa ta wurin ɗan sa Ishaku.4Ga Ishaku na bashi Yakubu da Isuwa. Na ba Isuwa ƙasar tudu ta Seyir domin ya mallaketa, amma Yakubu da 'ya'yansa suka gangara zuwa Masar.
5Na aika masu Musa da Haruna, Na azabtar da Masarawa da annobai. Bayan haka, sai na fito da ku daga ciki,6Na fito da kakanninku daga Masar. Ku ka zo teku. Masarawa su ka bi su da karusai da mahayan dawakai har zuwa jan teku.
7Sa'ad da kakannin ku su ka yi kira ga Yahweh, ya sa duhu tsakanin ku da Masarawa. Ya jawo teku a kan su ta rufe su. Kun ga abin da na yi cikin Masar. Da ga nan ku ka zauna kwanaki da yawa cikin jeji.
8Na kawo ku cikin ƙasar Amoriyawa, waɗanda su ke zaune a ƙetaren Yodan. Sun yi yaƙi da ku, na kuma bashe su cikin hannun ku. Ku ka mallaki ƙasar su, kuma na hallakar da su a gabanku.
9Sai Balak ɗan Ziffor, sarkin Mowab, ya ta shi ya kai hari a Isra'ila. Ya aika a kira Balaam ɗan Beyor, ya la'antaku.10Amma ban saurari Balaam ba. Babu shakka, sai ya albarkaceku. Da haka na cece ku daga hannunsa.
11Kuka haye Yodan ku ka zo Yeriko. Shugabannin Yeriko su ka yi yaƙi da ku, tare da Amoriyawa da Ferizziyawa da Kan'aniyawa, da Hittiyawa da Girgashiyawa da Hibiyawa da Yebusiyawa na ba ku nasara a kansu na sa su ƙarƙashin mulkinku.12Na ku ma aike da zirnaƙo gabanku, ya kore su daga gabanku da sarakuna biyu na Amoriyawa daga gabanku, wannan bai faru ta wurin takobinku ko bakanku ba.
13Na ba ku ƙasa wadda ba ku yi aikin kome ba da biranen da ba ku gina ba, yanzu ku na zaune a cikinsu. Ku na cin 'ya'yan kuringar inabi da na zaitun wanda ba ku ne ku ka dasa su ba.'
14Yanzu fa sai ku ji tsoron Yahweh ku bauta masa da dukkan sahihanci da gaskiya; sai ku ƙi allolin da kakannin ku suka yi wa sujada a ƙetaren Yodan da cikin Masar, ku yi wa Yahweh sujada.15Idan a gare ku ba daidai bane a yi wa Yahweh sujada, ku zaɓa da kan ku yau wanda zaku bautawa, ko dai alloli waɗanda kakanninku su ka yi wa sujada na ƙetaren Yufiretes ko kuwa allolin Amoriyawa, waɗanda ku ke zaune cikin ƙasarsu. Amma ni da gidana, Yahweh za mu yi wa sujada."
16Daga nan mutanen suka amsa suka ce, "Ba zamu taɓa yashe da Yahweh sa'annan mu bautawa wa su alloli ba,17gama Yahweh Allahnmu wanda ya fitar da mu da kakanninmu da ga ƙasar Masar, da ga gidan bauta, wanda ya aikata manyan al'ajibai a idanun mu, ya ku ma tsare mu cikin dukkan hanyar da mu ka bi, da ku ma cikin dukkan al'umman da mu ka ratsa ta tsakiyarsu.18Yahweh kuma ya kori dukkan mutane daga gabanmu, har da Amoriyawa da su ke zaune cikin ƙasar. Don haka mu ma zamu yi wa Yahweh sujada, gama shi ne Allahnmu."
19Amma Yoshuwa ya cewa mutane, "Ba zaku bautawa Yahweh ba, gama shi Allah ne mai kishi; ba zai gafarta laifofinku ko zunubanku ba.20Idan ku ka yashe da Yahweh ku ka yi sujada ga baƙin alloli, daga nan zai juya ya azabtar da ku. Daga nan zai hallaka ku, bayan da ya riga ya kyautata ma ku."
21Amma mutanen suka cewa Yoshuwa, "Sam, za mu yi sujada ga Yahweh."22Daga nan sai Yoshuwa ya ce ma mutanen, "Ku shaidu ne bisa kanku kun zaɓi Yahweh, ku yi masa sujada." Su ka ce, "Mu shaidune"23Yanzu ku kawar da baƙin allolin da ke tare da ku, ku juyo da zuciyarku ga Yahweh, Allah na Isra'ila."
24Sai mutanen suka cewa Yoshuwa, "Za mu yi sujada ga Yahweh Allahnmu. Za mu saurari muryarsa."25Yoshuwa ya yi wa'adi tare ta mutanen a wannan rana. Ya shimfiɗa masu dokoki da farillai a Shekem.26Yoshuwa ya rubuta waɗannan maganganu cikin littafin shari'ar Allah. Ya ɗauki babban dutse ya kafa shi ƙarƙashin itacen oak da ke kusa da wuri mai tsarki na Yahweh.
27Yoshuwa ya cewa dukkan mutanen, "Duba, wannan dutse zai zama shaida a kanmu. Gama ya ji dukkan maganganun da Yahweh ya ce da mu. Don ha ka zai zama shaida a kanku, Idan har ku yi musun Allahnku."28Sai Yoshuwa ya sallami mutanen, kowanne ya tafi wurin gãdonsa.
29Bayan waɗannan abubuwa Yoshuwa ɗan Nun, bawan Yahweh, ya rasu, yana da shekaru 110.30Aka bizne shi cikin iyakar, gãdonsa a Timnat Sera, wadda ke cikin ƙasar tuddai ta Ifraim, arewacin Tsaunin Gaash.
31Isra'ila su ka yi sujada ga Yahweh dukkan kwanakin Yoshuwa, da dukkan kwanakin dattawan da su ka kasance bayan Yoshuwa, waɗanda su ka san dukkan abin da Yahweh ya yi domin Isra'ila.
32Ƙasusuwan Yosef, da mutanen Isra'ila suka ɗauko daga Masar - aka bizne su a Shekem, ciki yankin ƙasar da Yakubu ya sayo daga 'ya'yan Hamor, mahaifin Shekem. Ya saye ta a bakin azurfa ɗari, ta zama gãdon zuriyar Yosef.33Eliyeza ɗan Haruna shi ma ya mutu. Su ka bizne shi a Gibiya, a birnin Fenihas ɗansa, wanda aka bashi. Tana cikin ƙasar duwatsu ta Ifraim.

Littafin alƙalai

1

1Bayan mutuwar Yoshuwa, mutanen Isra'ila suka tambayi Yahweh cewa, "Wane ne zai fara kai wa kan'aniyawa hari domin mu, don yin faɗa da su?"2Sai Yahweh yace "Yahuda zai kai hari, Duba, na ba su iko a kan ƙasar."3Mutanen Yahuda suka ce da mutanen Simiyon, 'yan'uwansu, "Ku zo tare da mu a yankin da aka ɗebo mana don mu je tare mu yi yaƙi da Ka'aniyawa. Mu ma za mu je tare da ku a yankin da aka ɗiba maku". Sai kabilar Simiyon ta tafi tare da su.

4Mutanen Yahuda suka kai hari kuma Yahweh ya ba su nasara a kan Ka'aniyawa, da Feriziyawa. Suka kashe masu mutum dubu goma a Bezek.5Suka sami Adoni-Bezek a Bazek, sai suka yi yaƙi da shi suka kuma cinye Kan'aniyawa da Feriziyawa a yaƙi.
6Amma Adoni-Bezek ya gudu, sai suka fafare shi suka kamo shi suka yanke yatsunsa da tafin ƙafafunsa.7Adoni-Bezek yace "Sarakuna saba'in da aka yanke masu yatsunsu da tafin ƙafafunsu suna neman abincinsu a ƙarƙashin teburina. "Kamar yadda na yi haka nima Allah ya yi mani." Sai suka kawo shi Yerusalem, ya kuma mutu a can.
8Mutanen Yahuda sun yaƙi birnin Yerusalem suka kuma ɗauke ta. Sun kai hari da kaifin takobi kuma suka banka wa garin wuta.9Bayan haka mutanen Yahuda suka je suyi faɗa da Ka'aniyawa da ke zaune a bisan tsibirin ƙasar, a cikin Negeb, da cikin tsibirin duwatsun yammacin.10Yahuda ya haura gãba da Ka'aniyawa da ke zaune a Hebiron (sunan Hebiron a dã shi ne Kiriyat Arba), suka kuma buge Sheshai, da Ahiman, da Talmaye.
11Daga can sai mutanen Yahuda suka nausa gãba da mazaunan Debir (sunan Debir a dã shi ne Kiriyat Sefa).12Kalibu ya ce, "Duk wanda ya kai wa Kiriyat Sefa hari ya kuma ɗauke ta, Zan ba shi Aksa, ɗiyata, ta zama matarsa."13Otniyel ɗan Kenaz (ƙanin Kaleb) ya yi nasara a kan Debir, sai Kaleb ya ba shi Aksa, ɗiyarsa, ta zama matarsa.
14Da sauri Aksa ta zo wurin Otniyel, sai ta iza shi ya sa mahaifinta ya bata fili. Da ta ke saukowa a kan jaki, Kaleb ya tambaye ta, "Mene ne zan yi maki?"15Ta ce da shi, "Ba ni albarka. Tun da ka ba ni ƙasar Negeb, ka kuma ba ni maɓulɓullan ruwa." Sai Kaleb ya ba ta maɓulɓullan tudu da na fadama.
16Zuriyar surukin Musa Bakenine sun hauro daga Birnin Dabino tare da mutanen Yahuda, zuwa ga tsibirin Yahuda, wanda ke cikin Negeb, su zauna tare da mutanen Yahuda kusa da Arad.17Mutanen Yahuda suka tafi tare da mutanen Simiyon 'yan'uwansu sai suka tunkari Kan'aniyawan da ke zaune a Zefat suka hallakar da su kakaf. Sunan birnin Hormah.
18Mutanen Yahuda suka kuma kame Gaza da ƙasashen da ke kewaye da ita, Ashkelon da ƙasar da ke maƙwabtaka da ita, da kuma Ekron tare da ƙasar da ke kewaye da ita.19Yahweh na tare da mutanen Yahuda suka kuma ɗauki mallakar ƙasar kan tudu, amma ba su iya korar mazaunan ƙasar kan tudun ba don su masu karusan ƙarfe ne.
20Hebron kuwa Kaleb aka baiwa (kamar yarda Musa yace), ya kuma kori 'ya'yan Anak uku daga wurin.21Amma mutanen Benyamin ba su kori Yebusiyawan da ke zaune a Yerusalem ba. Sai Yebusiyawan suka zauna tare da mutanen Benyamin a Yerusalem har ranar nan.
22Gidan Yosef suka yi shirin kai wa Betel hari, kuma Yahweh na tare da su.23Suka aiki maza su leƙo asirin Betel (Birnin da dã ake kira Luz).24Masu leken asirin suka ga wani mutum na fitowa daga birnin, sai suka ce da shi, "In ka yarda, nuna mana yadda za a shiga cikin birnin nan, kuma za mu yi maka alheri."
25Ya nuna masu hanyar zuwa cikin birnin, sai suka kai wa birnin hari da kaifin takobi, amma suka bar mutumin da dukkan iyalinsa suka kuɓuta.26Sai mutumin ya je ƙasar Hitiyawa ya gina wani birnin da ya kira shi Luz, shi ne kuwa sunansa har wa yau.
27Mutanen Manasse ba su kori mutanen da ke zama a biranen Bet Shan da ƙauyukansu ba, ko Ta'anak da ƙauyukansu, ko waɗanda suka zauna a Dor da ƙauyukansu, ko waɗanda suka zauna a Ibilim da ƙauyukansu, ko waɗanda suka zauna a Megiddo da ƙauyukansu ba, domin Ka'aniyawan sun bugi ƙirjinsu don zama a cikin ƙasar.28Da Isra'ila ta yi ƙarfi, suka tilasta wa Ka'aniyawa su yi masu bauta ta aiki mai tsanani, amma ba su taɓa korar su kakaf ba.
29Ifraim bai kori Ka'aniyawan da suka zauna a Gezer ba, don haka Ka'aniyawa suka ci gaba da zama a Gezer a cikin su.
30Zebulun bai tumɓuke mutanen da ke zama a Kitiron, ko mutanen da ke zama a Nahalol ba, saboda haka Ka'aniyawan suka ci gaba da zama a cikinsu, amma Zebulun ya tilasta wa Ka'aniyawan su bauta masu tare da aiki mai tsanani.
31Asha bai tumɓuke mutanen da ke zama a Akko, ko mutanen da ke zama a Sidon, ko waɗanda ke zama a Alab, Akzib, Helba, Afek, ko Rehob ba.32Don haka kabilar Asha ta zauna cikin Ka'aniyawan (waɗanda ke zaune a ƙasar), saboda ba su kore su ba.
33Kabilar Naftali ba su kori waɗanda ke zaune a Bet Shemesha, ko waɗanda ke zaune a Bet Anat ba. Don haka kabilar Naftali ta zauna cikin Ka'aniyawa (mutanen da tun asali ke zaune a ƙasar). Duk da haka, aka nawaita wa mazaunan Bet Shemesha da Bet Anata aikin bauta ga Naftali
34Amoriyawa suka tilasta wa kabilar Dan su zauna a ƙasar kan tudu, ba su kuma ba su damar saukowa kwari ba.35Don haka Amoriyawa suka zauna a Tsaunin Heres, a Aijalon, da Sha'albim, amma ƙarfin mayaƙan gidan Yosef ya mamaye su, ya kuma sa aka tilasta masu su bauta masu da aiki mai tsanani.36Iyakar Amoriyawa ta kama daga tudun Akrabbim a Sela zuwa cikin ƙasar kan tudu.

2

1Mala'ikan Yahweh ya taso daga Gilgal zuwa Bokim ya ce, "Na fitar da ku daga Masar, na kuma kawo ku ƙasar da na yi rantsuwa zan ba kakaninku. Na ce 'ba zan taɓa karya alƙawarina da ku ba.2Ba za ku yi yarjejeniya da mazaunan garin nan ba. Wajibi ne ku rurrushe bagadansu.' Amma ba ku saurari muryata ba. Me kenan ku ka yi?

3Yanzu sai na ce, 'ba zan kori Kan'aniyawa daga gare ku ba, amma za su zama ƙaya a gare ku, kuma allolinsu za su zama tarko a gare ku."'4A lokacin da mala'ikan Yahweh ya furta waɗannan kalmomin ga mutanen Isra'ila, sai suka yi kuka mai ƙarfi.5Suka kira wurin Bokim. A wurin suka miƙa hadayu ga Yahweh.
6Sa'ad da Yoshuwa ya aike mutanen a hanyarsu, kowanne ɗaya daga mutanen Isra'ila kuwa kowa ya nufi wurin da aka sa shi don mallakar ƙasar.7Mutanen kuwa sun bauta wa Yahweh a zamanin Yoshuwa da kuma ta dattawan da suka bi bayansa, waɗanda suka ga dukkan abubuwa masu girma da Yahweh ya yi wa Isra'ila.8Yoshuwa ɗan Nun, bawan Yahweh, ya rasu yana da shekaru 110.
9Aka kuwa binne shi a tsibirin ƙasar da aka ba shi ya mallaka a Timnat Heres, a tudun ƙasar Ifiraim, arewa da Tsaunin Ga'ash.10Dukkan wannan tsarar kuwa sun kasance tare da kakaninsu. bayansu sai wata tsara da ba ta san Yahweh ko abin da ya yi wa Isra'ila ba ta taso biye da su.
11Mutanen Isra'ila kuwa sun yi mugun abu a fuskar Yahweh suka kuma bautawa Ba'aloli.12Sun kauce daga Yahweh, Allahn kakaninsu, wanda ya fitar da su daga ƙasar Masar. Sun bi waɗansu alloli, wato allolin mutanen da ke kewaye da su, kuma sun rusuna ƙasa gare su. Suka sa Yahweh ya fusata domin13sun kauce daga Yahweh sun kuma yi wa Ba'al da Ashtoret sujada.
14Fushin Yahweh ya taso wa Isra'ila, sai ya sa 'yan fashi suka ƙwace mallakarsu daga gare su. Ya maishe su barorin da ke ƙarƙashin ƙarfin maƙiyansu da ke kewaye da su, saboda haka ba su iya kare kansu daga maƙiyansu ba.15Duk inda Isra'ila su ka je faɗa, hanuwan Yahweh na gãba da su don a yi nasara da su, kamar dai yadda ya rantse masu kuma sun shiga ƙunci mai tsanani.
16Sa'an nan Yahweh ya taso da Alƙalai, waɗanda su ka ceto su daga hanuwan masu satar mallakarsu.17Duk da haka ba su saurari alƙalansu ba. Suka zama marasa aminci ga Yahweh, suka kuma maida kansu kamar karuwai ga waɗansu alloli suka kuma yi masu sujada. Suka juya baya daga hanyar da kakaninsu suka yi rayuwarsu - waɗanda suka yi biyayya da umurnin Yahweh - amma su da kansu ba su yi haka ba.
18A lokacin da Yahweh ya naɗa masu alƙalai, Yahweh ya taimaki alƙalan ya kuma ƙuɓutar da su daga hanuwan maƙiyansu a dukkan kwanakin alƙalan. Yahweh ya yi masu tagomashi yayin da suke nishi saboda waɗanda ke zalunta da kuma ƙuntata masu.19Amma sa'ad da alƙalan su ka mutu, sai suka juya baya suna yin miyagun abubuwan da suka fi waɗanda ma ubaninsu suka yi. Suka biɗi waɗansu alloli don su bauta masu su kuma yi masu sujada. Suka ƙi barin miyagun ayukansu ko taurin kansu.
20Fushin Yahweh kuwa ya taso ma Isra'ila; ya ce "Saboda wannan al'umma ta karya sharuɗan alkawarina wanda na kafa domin ubaninsu-saboda ba su saurari muryata ba -21Daga yanzu ba zan korar masu ko ɗaya daga cikin al'umman da Yoshuwa ya rage kafin mutuwarsa ba.22Zan yi haka domin in gwada Isra'ila, ko za su yi biyayya da hanyar Yahweh da tafiya cikinta ko ba za su yi ba. Kamar yadda ubaninsu suka yi biyayya."23Shi ya sa Yahweh ya bar al'ummomin nan bai kuma kore su da sauri ya ba da su ga hannun Yoshuwa ba.

3

1Yanzu kuwa Yahweh ya bar waɗannan ƙasashen domin ya gwada Isra'ila ne, wato duk wanda bai taɓa sanin yaƙe-yaƙen da Isra'ila ta yi da Kan'ana ba2(Ya yi wannan ne domin ya koyar da al'amarin yaƙi ga sabon zamanin Isra'ilawan da ba su san shi ba.)3Waɗannan su ne alu'mman: sarakuna biyar wato Filistiyawa da dukkan Kan'aniyawa da Sidoniyawa, da Hibitiyawa da ke zaune a duwatsun Lebanon, daga Tsaunin Ba'al Hermon zuwa Hamat Fass.

4Waɗannan al'umman aka rage da manufar kasancewar hanyar da Yaahweh zai gwada Isra'ila, ko tabbas za su yi biyayya da dokokin da ya ba kakaninsu ta wurin Musa.5Mutanen Isra'ila kuwa sun yi zama a cikin Kan'aniyawa da Hitiyawa da Amoriyawa da Feriziyawa da Hibiyawa da Yebusiyawa.6Suka ɗauki 'yammatansu su zama matayensu, haka kuma nasu 'yammatan suka bayar ga samarinsu, suka kuma bauta wa allolinsu.
7Mutanen Isra'ila sun yi mugun abu a fuskar Yahweh kuma sun mance da Yahweh Allahnsu. Suka bauta wa gumakan Ba'al da Ashira.8Ta haka, fushin Yahweh mai zafi ya sauko wa Isra'ila, sai ya sayar da su ga hannun Kushan Rishata'imi sarkin Aram Naharayim. Mutanen Isra'ila kuwa sun bautawa Kushan Rishatayim shekaru takwas.
9Sa'ad da mutanen Isra'ila suka yi kira ga Yahweh, sai Yahweh ya tayar da wani wanda zai taimaka wa mutanen Isra'ila, wanda kuma zai kuɓutar da su: Otniyel ɗan Kenaz (ƙanin Kaleb).10Ruhun Yahweh ya ƙarfafa shi, ya yi alƙalancin Isra'ila, ya kuma je yaƙi. Yahweh ya ba shi nasara a kan Kushan Rishatayim sarkin Aram. Hanuwan Otniyel ya ragargaza Kushan Rishatayim.11Ƙasar ta kasance da salama shekaru arba'in. Sai Otniyel ɗan Kenaz ya mutu.
12Bayan haka, Isra'ilawa kuma sun yi mugun abu a fuskar Yahweh, sai Yahweh ya ba Eglon sarkin Mowab ƙarfin da zai mallaki Isra'ilawa.13Eglon ya haɗu da Amoniyawa da Amelikawa sai suka yi nasara da Isra'ila, suka kuma ɗauki mallakar Birnin Dabino.14Mutanen Isra'ila sun bauta wa Eglon sarkin Mowab shekaru goma sha takwas.
15Sa'ad da mutanen Isra'ila suka yi kira ga Yahweh, sai Yahweh ya tayar da wani mai taimako wanda zai taimake su, Ehud ɗan Gera, na kabilar Benyamin, bahago ne shi. Mutanen Isra'ila sun aike shi, da kyautukkansu, zuwa ga Eglon sarkin Mowab.
16Ehud ya ƙera wa kansa takobi mai ƙaifi biyu, kamu guda a tsawo; ya yi ɗammara da ta a ƙarƙashin tufafinsa ta wajen cinyarsa ta dama.17Ya ba da kyautar ga sarki Eglon na Mowab. (Eglon kuwa mai ƙiba ne.)18Bayan Ehud ya gama miƙa kyautar, sai ya bar wurin tare da waɗanda suka ɗauke ta suka kai ciki.
19Ehud da kansa kuwa, ko da yake, lokacin da ya iso wurin da ake yin siffofi kusa da Gilgal, sai ya juyo ya koma baya, sai ya ce, "Ina da saƙo a asirce domin ka, sarkina." Eglon yace, "Shiru" Sai dukkan waɗanda ke yi masa hidima suka bar ɗakin.20Ehud ya je wurin sa. Sarkin yana zaune da kansa, shi kaɗai a inuwar bene. Ehud yace, "Ina da saƙo daga Allah domin ka." Sarkin ya miƙe tsaye daga kujerarsa.
21Ehud ya shigar da hannun hagunsa ya ɗauki takobin daga cinyarsa ta dama, sai ya cake jikin sarkin.22Ƙotar takobin kuma ta shige cikin jikinsa biye da wuƙar. Tsinin takobin ya fita ta bayansa kuma rufe da ƙitse, domin Ehud bai zaro takobin daga tumbinsa ba.23Sai Ehud ya fita daga shirayin ya kukkulle ƙofofin babban benen a bayansa.
24Bayan Ehud ya tafi, barorin sarki suka zo; suka ga ƙofofin ɓenen a kulle, sai suka yi zaton, "Tabbas ya na hutawa a inuwar benen ne."25Suka yi ta ƙaruwa da kulawa har sai da suka ji lallai suna sakaci da aikinsu ne yayin da sarki fa bai buɗe ƙofofin babban benen ba. Sai suka ɗauki makullin suka buɗe, sai ga ubangijinsu a kwance, a ƙasa, matacce.
26Yayin da barorin ke jira, suka rasa mema za su yi, Ehud kuwa ya tsere har ya wuce wurin da ake sassaƙa sifofin gumaka, sai ya tsere zuwa Se'ira.27Sa'ad da ya iso, sai ya busa kakaki a ƙasar tudu ta Ifraim. Sa'an nan mutanen Isra'ila suka je ƙasa tare da shi daga tuddai, kuma yana yi masu jagora.
28Ya ce masu, "Ku biyo ni, gama Yahweh na gab da yin nasara da maƙiyanku, Mowabawa. "Suka bi shi suka kuma kama mashigin Yodan ƙetare zuwa Mowabawa, ba su kuma bar wani ya ƙetare kogin ba.29A lokacin nan ne suka kashe kusan dubu goma na mazajen Mowab, kuma dukkan su masu ƙarfi ne gwarzaye. Babu ko ɗayan da ya tsere.30Wato, a ranar nan ne Isra'ila ta mamaye Mowab da ƙarfinta, kuma ƙasar ta sami hutawa shekaru tamanin
31Bayan Ehud, alƙali na biye shi ne Shamgar ɗan Anat wanda ya kashe maza 600 na Filistiyawa da tsabgar dabbobi. Ya kuma kuɓutar da Isra'ila daga hatsari.

4

1Bayan da Ehud ya mutu, mutanen Isra'ila suka sake yin mugun abu a fuskar Yahweh.2Yahweh ya sayar da su ga hanun Yabin sarkin Kan'ana wanda ya yi mulki a Hazor. Babban shugaban rundunar sojojinsa shi ne Sisera, yana zaune a Haroshet Haggoyim.3Mutanen Isra'ila sun yi kira ga Yahweh domin taimako, saboda Sisera na da karusan ƙarfe guda ɗari tara ya kuma ƙuntata wa mutanen Isra'ila shekaru ashirin.

4Debora kuwa, annabiya (matar Laffidot), tana jagoranci a matsayin mai sharia a Isra'ila a lokacin.5Ta kan zauna a ƙarƙashin itacen dabino na Debora tsaƙanin Ramah da Betel a tuddun ƙasar Ifraim, kuma mutanen Isra'ila na zuwa wurinta domin sassanta jayayya a tsakaninsu
6Ta aika saƙo ga Barak ɗan Abinowam daga Kedesh a Naftali. Ta ce masa, "Yahweh, Allahn Isra'ila, ya umarce ka, 'Jeka Tsaunin Tabor, tare da kai ka ɗauki maza dubu goma daga Naftali da Zabulun.7Zan ciro Sisera, shugaban rundunar sojojin Yabin, ya haɗu da kai a Kogin Kishon, tare da karusansa da sojojinsa, kuma Zan ba ka nasara a kansa."
8Barak yace ma ta, "Idan za ki tafi tare da ni zan je, amma idan ba za ki tafi tare da ni ba, ba za ni ba."9Ta ce, "Zan tafi tare da kai tabbas. Ko da yake, hanyar da ka ke tafiya ba za ta kai ka ga martaba ba, domin Yahweh zai sayar da Sisera ga hannun mace." Sai Debora ta tashi tsaye ta tafi tare da Barak zuwa Kedesh.
10Barak ya yi kira ga mazan Zebulun da Naftali su zo tare a Kedesh. Maza dubu goma suka bi shi, kuma Debora ta tafi tare da shi.
11Haber kuwa (Bakeniye) ya raba kansa daga Keniyawa - su zuriyar Hobab ne (surukin Musa) - ya kuma kafa rumfarsa a gefen itacen al'ul a Za'ananim kusa da Kedesh
12Sa'ad da suka faɗa wa Sisera cewa Barak ɗan Abinowam ya hauro Tsaunin Tabor,13Sisera ya kira dukkan karussansa, karussan ƙarfe ɗari tara, da dukkan sojojin da ke tare da shi, daga Haroshet Haggoyim zuwa Kogin Kishon.
14Debora ta ce da Barak, "Jeka! Domin wannan ranar ce Yahweh ya ba ka nasara a kan Sisera. Ashe ba Yahweh ne ke jagorantakar ka ba?" Sai Barak ya je gangare daga Tsaunin Tabor tare da maza dubu goma biye da shi.
15Yahweh ya sa sojojin Sisera su ruɗe, dukkan karusansa, da dukkan sojojinsa. Mazajen Barak suka faɗa masu har Sisera ya sauko daga karusa ya gudu da ƙafa.16Amma Barak ya runtumi karusan da sojojin zuwa Haroshet Haggoyim, sai aka kashe dukkan sojojin Sisera da kaifin takobi, kuma babu mutumin da ya tsira.
17Amma Sisera ya ruga a guje da kafa zuwa rumfar Ya'el, matar Heber Bakenine, gama akwai salama tsakanin Yabin sarkin Hazor, da gidan Heber Bakenine.18Ya'el ta fito ta sadu da Sisera sai ta ce masa, juyo, ubangijina; juyo gare ni kar ka ji tsoro." Sai ya juyo gare ta ya zo wurinta cikin rumfarta, sai ta rufe shi da bargo.
19Ya ce mata, "In kin yarda ki ba ni ruwa kaɗan in sha, don ina jin ƙishi." Ta buɗe jakar fata ta madara ta ba shi ya sha, sai ta sake rufe shi.20Ya ce mata, "Tsaya a ƙofar rumfar. Idan wani ya zo ya tambaye ki, 'akwai wani a nan ne?', ki ce 'A a'."
21Sai Ya'el (matar Heber) ta ɗauki turken rumfar da guduma a hannunta ta je gunsa a asirce, gama ya na cikin zurfin barci, sai ta kafa turken rumfar ta ɗora guduma har ta soke gefen kansa zuwa ƙasa, har ya mutu.22Yayin da Barak ke fakon Sisera, Ya'el ta je ta tarye shi ta ce masa, "Zo, Zan nuna maka mutumin da ka ke nema." Sai ya je tare da ita, sai ga Sisera kwance matacce, tare da turken rumfar a gefen kansa.
23Don haka a ranar nan Allah ya yi nasara da Yabin, sarkin Kan'ana, a idon mutanen Isra'ila.24Ƙarfin mutanen Isra'ila ya ƙaru sosai gãba da Yabin sarkin Kan'ana, har suka hallakar da shi.

5

1A ranar nan ne Debora da Barak ɗan Abinowam suka rera wannan waƙa:2"Sa'ad da shugabanin suka ɗauki jagorancin Isra'ila, sa'ad da mutane cikin murna suka miƙa kai domin yaƙi - mu yabi Yahweh!

3Ku saurara, ku sarakuna! Mai da hankali, ku shugabanni! Ni, Zan raira waƙa ga Yahweh, Allahn Isra'ila.4Yahweh, sa'ad da ka fito daga Se'ir, a sa'ad da ka tako daga Idom, ƙasa ta girgiza, kuma sammai sun yi makyarkyata; har giza-gizai sun zubo ruwa ƙasa.
5Duwatsu na rawa a gaban Yahweh; har Tsaunin Sinai na rawa a gaban Yahweh, Allahn Isra'ila.6A kwanakin Shamgar (ɗan Anat), a kwanakin Ya'el, an ƙyale manyan hanyoyi, kuma waɗanda ke tafiya na yin amfani da ƙananan hanyoyin ne kurum.
7Akwai jarumawa ƙaɗan ne a Isra'ila, har sai lokacin da ni Debora, na ɗauki matsayin shugabanci a Isra'ila - uwa ta ɗauki shugabancin a Isra'ila!8Sa'ad da suka zaɓi sababbin alloli, an yi faɗa a ƙofofin biranen amma duk da haka babu garkuwoyin yaƙi ko mãsu da aka gani a cikin mutum dubu arba'in a Isra'ila.
9Zuciyata ta tafi ga shugabanin rundunar sojojin Isra'ila, tare da mutanen da a cikin murna suka miƙa kansu - mu yabi Yahweh domin su!10Yi tunani a kan wannan - ku masu hawan fararen jakuna kuna zaune a shinfiɗun ɗaurawa, da ku masu tafiya a hanyar.
11Ji muryoyin waɗanda ke waƙa a cikin lambu. A wurin suke sake faɗin adalcin ayyukan Yahweh, da aikin adalcin jarumansa a Isra'ila. Sai mutanen suka sauko ƙasa zuwa ƙofofin birnin
12Tashi, tashi, Debora! Tashi, tashi, ki raira waƙa! Tashi tsaye, Barak, ka kama 'yan kurkukunka, kai ɗan Abinowam.13Sai waɗanda suka tsira suka zo gun masu martaba; mutanen Yahweh suka zo gare ni tare da jarumawa.
14Suka iso daga Ifraim, waɗanda asalinsu na Amalek ne; mutanen Benyamin sun bi ka. Daga Makir shugabanin yaƙi suka iso, daga Zebulun kuma waɗanda ke ɗauke da sandar hafsan.
15Sarakunan da ke Issaka na tare da Debora; kuma Issaka na tare da Barak yana biye da shi da sauri har cikin kwari a bisa ga umurninsa. Cikin zuriyar Ruben ana ta nazari a zuci.
16Me ya sa kuka zauna a tsaƙanin wuraren jin ɗumi, kuna sauraron makiyaya na wasa da sandunansu domin garkensu? Zuriyar Ruben dai suna ta nazari a zuci.
17Giliyad ya tsaya a ƙeteren Yodan; kuma Dan, me ya sa yake ta zirgazirga a jiragen ruwa? Asha ya kasance a bakin teku ya kuma zauna kusa da babbar matsayar jiragen teku,18Zebulun kabila ce waɗanda suka sadaukar da rayukansu har ga mutuwa, har da Naftali ma, a filin yaƙi.
19Sarakunan suka iso, suka yi faɗa; sarakunan Kan'ana suka yi faɗa a Ta'anak cikin ruwayen Megiddo, Amma ba su ɗauki azurfa a matsayin ganima ba.20Daga sammai, taurari suka yi faɗa, daga hanyoyinsu a ƙeteren sammai suka yi faɗa gãba da Sisera.
21Kogin Kishon ya share su daga nan, wannan tsohon kogin, Kogin Kishon. Taka ya raina, ka yi ƙarfin hali!22Sai ƙarar kofaton dawakan - sukuwa, sukuwar jarumawansa.
23'La'anta Meroz!' inji mala'ikan Yahweh. 'Tabbas la'anta mazaunanta! - saboda ba su zo sun taimake Yahweh ba - su taimaki Yahweh a yaƙi gãba da manyan jarumawa.'
24An albarkaci Ya'el fiye da dukkan mata, Ya'el (matar Heber Bakenine), ita mai albarka ce fiye da dukkan matan da ke zama a rumfuna.25Mutumin ya biɗi ruwa, sai ta ba shi madara; ta kawo masa nono a akushin da ya cancanci a ba 'ya'yan sarki.
26Ta sa hannunta a turken rumfa, da guduma a hannun damarta; da gudumar ta buge Sisera, ta ragargaza kansa. ta farfasa masa ƙwaƙwalwa sa'ad da ta soke shi ta gefen kansa.27Ya kasa tashi tsakanin tafinta, ya kwanta warwas a wurin. Tsakanin tafin kafafunta ya faɖi laƙwas. A wurin da ya ɓungire ne aka kashe shi ƙarfi da yaji.
28Ta taga ta duba - mahaifiyar Sisera ta duba ta taga ta yi kira cikin baƙinciki, 'Me ya sa aka ɗauki tsawon lokaci karusansa basu iso ba? Me ya sa karar kofaton dawakan da ke jan karusansa suka yi jinkiri?'
29Gimbiyoyinta masu hikima suka ba ta amsa, ita kuma ta ba kanta amsa irin tasu.30Ko basu samo ganima sun raba ba ne? - Mace, mata biyu domin kowanne mutum; ganimar kyawawan tufafi domin Sisera, tufafi masu tsada, kashi biyu na tufafi masu tsada domin wuyan waɗanda suka kwaso ganima?
31Don haka bari dukkan maƙiyanka su lalace, Yahweh! Amma abokanka su zama kamar rana sa'ad da ta tashi a cikin ƙarfinta." Sai ƙasar ta sami salama shekaru arba'in.

6

1Mutanen Isra'ila sun kuma yin abin da ke mugu a fuskar Yahweh, sai ya bada su ga hannun Midiyan na tsawon shekaru bakwai.2Ikon Midiyan ya ƙuntata wa Isra'ila. Saboda Midiyan, mutanen Isra'ila sun yi wa kansu mafaka a ramummuka a tuddai da kogonni da wuraren ɓoyewa.

3Sai ya zamana a duk lokacin da Isra'ila suka shuka amfanin gona, sai Midiyanawa da Amelikawa da mutanen gabas su kai wa Isra'ila hari4Sukan sa mayaƙansu a ƙasar su lalatar da hatsi, har zuwa Gaza. Ba za su bar ko abinci a Isra'ila ba, ko tumaki, ko shanu, ko jakuna ba.
5Sa'ad da suka iso da dabbobbinsu da rumfuna, sukan shigo kamar cincirundon fãri, kuma ya kan zama da wuya a ƙidaya mutanen ko raƙumansu, Sun farmaƙe ƙasar ne don su hallaka ta.6Midiyan sun rage ƙarfin Isra'ilawa ƙwarai har ya kai ga mutanen Isra'ila yin kira ga Yahweh.
7Sa'ad da mutanen Isra'ila suka yi kira ga Yahweh saboda Midiyan,8Yahweh ya aiko annabi ga mutanen Isra'ila. Anabin ya ce masu, "Wannan ne abin da Yahweh, Allahn Isra'ila ya faɗi: 'Na kawo ku daga Masar; Na fitar da ku daga gidan bauta.
9Na kuɓutar da ku daga hannun Masarawa, daga kuma hannun dukkan waɗanda ke muzguna maku. Na kore su daga gare ku, na kuma ba ku ƙasarsu.10Na ce da ku, "Ni ne Yahweh Ahllahnku; Na Umurce ku kada ku bauta wa allolin Amoriyawa, waɗanda a cikin ƙasarsu ku ke." Amma ba ku yi biyayya da muryata ba,"'
11Yanzu kuwa Malai'kan Yahweh ya zo ya zauna a ƙarƙashin itacen rimi a Ofra, wanda yake na Yowash (Ba'abiyezare), sa'ad da Gidiyon, ɗan Yowash, ke bugun alkama a masussuka, a wurin matsar ruwan inabi - don ya ɓoye shi daga Midiyanawa.12Mala'ikan Yahweh ya bayyana gare shi ya ce masa, "Yahweh na tare da kai, kai jarumi mai ƙarfi!"
13Gidiyon yace masa, "Kash, ubangijina, idan Yahweh na tare da mu, me yasa dukkan waɗannan abubuwan suke faruwa da mu? Ina dukkan ayyukan al'ajibansa da ubaninmu suka labarta mana, sa'ad da suka ce, 'Ba Yahweh ba ne ya kawo mu daga can Masar ba? Amma yanzu Yahweh ya yashe mu ya bayar da mu ga hannun Midiyanawa."
14Yahweh ya dube shi ya ce, "Jeka cikin ƙarfin da ka ke da shi. Ka kuɓutar da Isra'ila daga hannun Midiyan. Ko ban aike ka ba ne?"15Gidiyon yace masa, "In ka yarda Ubangiji, ta yaya zan kuɓutar da Isra'ila? Duba, iyalina su ne mafi rashin ƙarfi a Manasse, kuma ni ne mafi ƙarancin muhimmanci a gidan mahaifina."
16Yahweh yace masa, "Zan kasance tare da kai, kuma za ka yi nasara da dukkan sojojin Midiyanawa kai kaɗai kuwa."17Gidiyon yace masa, "Idan kana farinciki da ni, ka ba ni allamar cewa kai ne ka ke magana da ni.18In ka yarda, kar ka bar nan, sai na zo gare ka na kawo kyautata na ajiye a gabanka." Yahweh ya ce, "Zan jira sai ka dawo."
19Gidiyon kuwa ya je ya shirya ɗan'akuya ya kuma auna gari misalin mudu guda, ya yi gurasa mara yisti. Ya sa nama a kwando, ya kuma sa romon a tukunya ya kawo su gare shi a ƙarƙashin itacen rimi, sai ya miƙa su.20Mala'ikan Allah ya ce masa, "Ɗauki naman da gurasa mara yisti ka sa su a wannan dutsen, ka kuma zuba romon a bisan su." Haka kuwa Gidiyon ya yi.
21Sai mala'ikan Yahweh ya miƙo kan sandar da ke hannunsa. Da ita ya taɓa naman da gurasa mara yisti; Wuta kuwa ta fito daga dutsen ta cinye naman da gurasar mara yisti. Sai mala'ikan Yahweh ya tafi Gidiyon kuma bai kara ganin shi ba.
22Gidiyon ya fahimci cewa wannan mala'ikan Yahweh ne. Gidiyon yace, Ah! Ubangiji Yahweh! Gama na ga mala'ikan Yahweh fuska da fuska!"23Yahweh yace ma sa, Salama a gareka! Kada ka ji tsoro, ba za ka mutu ba."24Sai Gidiyon ya gina bagadi a wurin domin Yahweh. Ya kira shi, "Yahweh salama ne." Har yau yana nan a Ofra ta iyalin Abiyeza.
25A daren nan Yahweh yace masa, "Ka ɗauki bijimin mahaifinka, da bijimi na biyu mai shekara bakwai, kuma ka rurushe bagadin mahaifinka, ka sare Ashera da ke kusa da shi.26Ka gina wa Yahweh Allahnka bagadi a kan wannan wurin fakewa, ka gina shi da kyau. Ka miƙa bijimi na biyu a matsayin hadaya ta ƙonawa, kana amfani da itacen Ashera da ka sare."
27Sai Gidiyon ya ɗauki goma daga cikin barorinsa ya yi dai dai yadda Yahweh ya faɗa masa. Amma saboda tsananin tsoron iyalin gidan mahaifinsa da mutanen gari bai yi shi da rana ba sai da dare.
28Da sassafe lokacin da mutanen gari suka tashi, an kakkarya bagadin Ba'al, Ashera da ke kusa da shi kuma an datse shi, bajimi na biyu kuma an miƙa shi hadaya a kan bagadin da aka gina.29Mutanen gari suka ce da junansu, "wa ya yi wannan abu?" Da suka yi magana da waɗansu suka nemi amsoshi, suka ce, "Gidiyon ɗan Yowash ne ya yi wannan abu."
30Daga nan sai mutanen gari suka ce da Yowash, Ka fiito da ɗanka domin a kashe shi, saboda ya rushe bagadin Ba'al, ya kuma datse Ashera da ke gefensa."
31Yowash yace da dukkan mutanen da ke jayayya da shi, "Za ku yi hamayya domin Ba'al ne? Za ku cece shi ne? Duk wanda ya yi hamayya dominsa, bari a kashe shi da safe, Idan Ba'al allah ne, bari ya kare kansa sa'ad da wani ya rushe bagadinsa."32Saboda haka a ranan nan suka kira Gidiyon "Yerub Ba'al," domin ya ce, "Bari Ba'al ya kare kansa," domin Gidiyon ya rushe bagadin Ba'al.
33Yanzu dukkan Midiyanawa da Amelikawa da mutanen gabas suka taru wuri ɗaya. Suka ƙetare kogin Yodan suka kuma kafa sansaninsu a kwarin Yezriyel
34Amma Ruhun Yahweh ya sauko wa Gidiyon. Gidiyon ya busa ƙaho, yana kiran zuriyar Abiyeza, ko za su bi shi.35Ya aiki 'yan saƙo ga dukkan Manasse, kuma suma an kirawo su su bi shi. Ya kuma aiko da 'yan saƙo ga Asha da Zebulun da Naftali, suka kuma fito su tarbe shi.
36Gidiyon yace da Allah, "Idan ka yi niyar ka more ni don ka ceci Isra'ila, kamar yadda ka faɗa -37Duba, Zan shimfiɗa ƙyallen ulu a masussuka. Idan da safe akwai raɓa a kan kyallen ulu kaɗai, amma ƙasa ta kasance a bushe, to zan sani cewa zaka more ni ka ceci Isra'ila kamar yadda ka ce."
38Ga abin da ya faru - washegari Gidiyon ya tashi da sassafe, ya matse kyallen ulun wuri ɗaya, har ruwan raɓar daga kyallen ulun ya cika ƙwarya.
39Sai Gidiyon yace da Allah, "Kada ka yi fushi da ni, Zan yi magana sau ɗaya kuma. In ka yarda ka bari in ƙara gwaji ɗaya kuma da ƙyallen ulun. Wannan karon, ka sa ƙyallen ulun ya bushe amma bari dukkan ƙasa ta kasance da raɓa.40Allah ya yi abin da ya roƙa a cikin daren nan. ƙyallen ulun ya bushe amma ƙasa ta kasance da raɓa kewaye da shi.

7

1Sai Yerub Ba'al (wato Gidiyon) ya tashi da sassafe, da dukkan mutanen da ke tare da shi, sai suka yi sansani a gefen rafin Harod. Zangon Midiyan kuwa na ɓangaren arewa da su a kwari kusa da tuddun Moreh.

2Yahweh yace da Gidiyon, "Ana da sojoji fiye da yadda nake so domin in ba ka nasara kan Midiyanawa, don kar Isra'ila ta yi taƙama a kaina, cewa, 'Ikonmu ne ya cece mu.' Yanzu kuwa, ka shaida a cikin kunuwan mutanen ka ce,3'Duk wanda ya ke jin tsoro, duk wanda ke rawar jiki, bari ya koma ya tashi daga Tsaunin Giliyad."' Sai mutane dubu ashirin da biyu suka tafi, dubu goma kuma suka rage.
4Sai Yahweh yace da Gidiyon, "Mutanen sun yi yawa har yanzu, Kai su wurin ruwa, Ni kuma zan rage yawansu domin ka a wurin. Idan nace maka, 'Wannan zai tafi da kai,' zai tafi da kai; amma idan na ce, 'Wannan ba zai tafi da kai ba,' ba zai tafi ba."
5Sai Gidiyon ya kawo mutanen wurin ruwan, Yahweh kuma ya ce masa, "Ware duk wanda ya lashi ruwan, kamar yadda kare ke lasa, daga waɗanda suka durƙusa ƙasa suka sha."6Mutum ɗari uku suka lasa.
7Yahweh yace da Gidiyon, "Da mutum ɗari ukun da suka lashi ruwa, zan 'yantar da kai in ba ka nasara a kan Midiyanawa. Sai kowanne mutum ya koma wurinsa."8Saboda haka waɗanda aka zaɓa suka ɗauki kayayyakin aiki da kakakinsu. Gidiyon ya komar da mazan Isra'ila, kowanne zuwa rumfarsa, amma ya keɓe mutum ɗari uku. Midiyanawan kuwa sun yi zango a ƙasa da shi a cikin kwari.
9A wannan daren Yahweh ya ce masa, "Tashi! ka kai wa sansanin hari, domin zan ba ka nasara a kansa.10Amma idan kana tsoron gangarawa kai kaɗai, ka tafi tare da Fura, baranka,11sai ka ji abin da suke faɗi, ƙarfin halinka kuma ya ƙarfafa har ka kai hari a sansanin." Sai Gidiyon ya tafi da Fura baransa, zuwa ƙofar sansanin.
12Midiyanawa, da Amelikawa da dukkan mutanen gabas suka yi shiri a kwarin, yawansu kamar cincirindon fãra. Raƙumansu sun fi ƙarfin a ƙirga; sun fi yashin teku yawa.
13Sa'ad da Gidiyon ya iso wurin, wani mutum ya na gaya wa abokinsa mafarkin da ya yi. Mutumin yace, "Duba! Na yi mafarki, sai na ga dunƙulen gurasar bali mai fuskar waina ta na gangarawa zuwa sansanin Midiyanawa. Ta iso rumfar, ta kuma buge ta da ƙarfi har sai da ta faɗi ta juyad da rumfar, ta kuma kwantar da ita ƙasa.14Sai ɗaya mutumin ya ce, "Wannan ba komai ba ne ban da takobin Gidiyon (ɗan Yowash), Ba'isra'ile. Allah ya ba shi nasara a kan Midiyan da dukkan sojojinsu."
15Sa'ad da Gidiyon ya ji yadda aka sake faɗin mafarkin da fasararsa, ya russuna ƙasa ya yi sujada. Ya koma sansanin Isra'ila ya ce, "Ku tashi tsaye! Yahweh ya ba ku nasara a kan sojojin Midiyan."16Ya raba mutun ɗari uku kashi uku, sai ya ba dukkansu kakaki da gorunan da ba kome a ciki, sai cocila.
17Ya ce masu, "Dube ni ku yi abin da na yi. Duba! Sa'ad da na iso gab da iyakar sansanin, dole ku yi abin da na yi.18Sa'ad da na busa kakaki, Ni da duk waɗanda ke tare da ni, sai ku busa naku kakakin har a dukkan gefen sansanin gaba ɗaya kuma ku yi ihu, 'Domin Yahweh da kuma domin Gidiyon!'"
19Sai Gidiyon da mazaje ɗari uku waɗanda ke tare da shi suka iso gabashin sansanin, misalin ƙarfe goma na dare. Dai-dai lokacin da Midiyanawan na canjin masu gadi, suka busa kakaki suka kuma farfasa gorunan da ke hanuwansu
20Rundunoni ukun suka busa kakaki suka kuma farfasa gorunan. Suka riƙe tociloli a hannayen hagunsu da kuma kakaki a hannayen damarsu don su busa su. suka yi ihu, "Takobin Yahweh da na Gidiyon."21Kowanne mutum ya tsaya a wurinsa a kewaye da sansanin sai dukkan sojojin Midiyanawa suka tsere suka yi ihu suka ruga a guje.
22Sa'ad da suka busa kakaki ɗari ukun, Yahweh ya sa kowanne sojan Midiyanawa ya ɗauki takobi gãba da ɗan'uwansa da kuma gãba da dukkan sojojin. Sojojin suka tsere ta Bet Shitta har zuwa Zerera, harma ga iyakar Abel Mehola, kusa da Tabbat.23Aka kira mazajen Isra'ila daga Naftali da Asha, da dukkan Manasa, suka kuma fafari Midiyan.
24Gidiyon ya aiki masu ba da saƙo a ko'ina a duk tuddun ƙasar Ifraim, cewa, "A gangara gãba da Midiyan a mamaye Kogin Yodan, har faɗin Bet Bara, a tsayar da su." Saboda haka dukkan mutanen Ifraim suka taru suka kuma mamaye ruwayen, har zuwa Bet Bara da Kogin Yodan.25Suka cafko 'ya'yan sarakuna biyu na Midiyan wato Oreb da Ze'eb. Suka kashe Oreb a dutsen Oreb, suka kuma kashe Ze'eb a wurin matsar ruwan Inabi ta Ze'eb. Suka bi bayan Midiyanawa, suka kuma taho da kawunan Oreb da Ze'eb ga Gidiyon, wanda ke a keteren Yodan.

8

1Mutanen Ifraim suka ce da Gidiyon, "Mene ne wannan da ka yi mana? Ba ka kira mu ba sa'ad da ka tafi wurin faɗa da Midiyan." Daga nan sai suka yi gardama mai zafi da shi.

2Sai ya ce da su, "Me na yi idan a ka kwatanta da ku?" Kalar inabin Ifraim, ba ta fi cikakken girbin inabin Abiyeza ba?3Allah ya ba ku nasara a kan 'ya'yan sarakunan Midiyan -- Oreb da Ze'eb! Wacce riba na ci idan an kwatanta da ku?" Sai fushinsu ya huce sa'ad da ya faɗi masu haka.
4Gidiyon ya zo ya haye Yodan, shi da mutane ɗari uku da ke tare da shi. Sun gaji, amma duk da haka ba su fasa bi ba.5Ya ce da mutanen Sukkot, "Idan kun yarda ku ba mutanen da suka biyo ni dunƙulen gurasa, gama sun gaji, domin ina bin sawunsu Zeba da Zalmunna sarakunan Midiyan."
6Sai shugabannin suka ce, "Hannuwan Ziba da Zalmunna suna hannunka ne a yanzu? Me zai sa mu ba sojojin ka gurasa?"7Gidiyon yace, "Idan Yahweh ya ba mu nasara a kan Zeba da Zalmunna, zan yayyaga maku fata da ƙayayuwan sahara da tsabgogi."
8Ya wuce zuwa Feniyel ya yi magana ga mutanen can ma, mutanen Feniyel masu ka ba shi amsa dai-dai da ta mutanen Sukkot.9Shi kuma ya yi magana da mutanen Feniyel ya ce, "Idan na dawo cikin salama, zan rushe wannan hasumiyar."
10Zeba da Zalmunna kuwa suna Karkor tare da sojansu, wajan mutum dubu goma sha biyar, dukkan waɗanda suka rage a sojojin mutanen Gabas, gama mutane 120,000 waɗanda a ka koyar a yaƙi da takobi sun faɗi.
11Gidiyon ya yi gaba kan hanyar da mazauna rumfa, ya wuce Nabo da Yogbeha. Ya ci nasara a kan sojojin abokan gãba, da yake ba su yi zaton za a kawo masu hari ba.12Zeba da Zalmunna suka gudu, Gidiyon kuma ya bi su, ya kamo sarakunan Midiyan su biyu - Zeba da Zalmunna - ya sa sojojinsu cikin ruɗami.
13Gidiyon ɗan Yowash ya dawo daga yaƙi, ya bi ta Heres.14Ya gamu da wani saurayi daga mutanen Sukkot, ya nemi shawara daga wurinsa. Shi kuma ya baiyana masa game da shugabannin Sukkot da dattawansu mutum saba'in da bakwai.
15Gidiyon ya zo ya sami mutanen Sukkot, ya ce "Da su ga Zeba da Zalmunna, da ku ka yi mani ba'a a kansu cewa, ka riga ka kama Zeba da Zalmunna ne?" Ba mu sani wai sai mun ba sojojinka gurasa ba.16Gidiyon ya ɗauki dattawan ya hori mutanen Sukkot da ƙayayuwa.17Ya rushe hasumiyar Feniyel ya kashe mutanen wannan birnin.
18Sa'an nan Gidiyon yace da Zeba da Zalmuna, "Wadanne irin mazaje ku ka kashe a Tabor"? Suka amsa, "Kamar yadda ka ke haka su ke, kowannensu kamar ɗan sarki ya ke."19Gidiyon yace, 'Yan'uwana ne, 'ya'yan mamata ne. Muddin Yahweh na raye, da ba ku kashe su ba, ni ma da ba zan kashe ku ba."
20Ya ce da Yeter (ɗansa na fari), "Tashi ka karkashe su!" Amma matashin bai zaro takobinsa ba, yana jin tsoro, saboda shi yaro ne.21Sai Zeba da Zalmunna suka ce, "Tashi ka kashe mu kai da kan ka! gama yadda mutum yake, haka ƙarfinsa yake." Gidiyon ya tashi ya kashe Zeba da Zalmunna, kuma ya ɗauke kayan adon da ke a wuyan raƙumansu.
22Mutanen Isra'ila suka ce da Gidiyon, "Ka yi mulkin mu da kai - da 'ya'yanka da jikokinka,- saboda ka cece mu daga hannun Midiyan."23Gidiyon yace da su, "Ni ba zan mulke ku ba, ɗana kuma ba zai mulke ku ba. Yahweh ne zai yi mulkinku.
24Gidiyon yace da su, "Zan roƙe ku: abu ɗaya, kowannenku ya ba ni ɗankunne daga abin da ya samu ganima." (Midiyanawa su na da 'yankunne na zinariya saboda su "ya'yan Isma'ila ne.)25Suka amsa suka ce, "Da farinciki za mu baka su". Suka yi shimfiɗa, kowannen su ya buɗe ganimarsa suka yi ta jefa 'yan kunnen a kan ta daga cikin ganima.
26'Yankunnen da ya buƙata, nauyinsu shekel 1,700 na zinariya ne. Wannan ganimar ƙari ee a kan kayan adon sarakunan Midiyan wato tufafinsu na shunaiya. Da kuma sarƙoƙin da ake sawa a wuyan raƙumansu.
27Gidiyon ya yi falmara da 'yankunnen da yakarɓa yasa a cikin birnisa, a Ofra, dukkan Isra'ila suka yi karuwanci ta wurin yi masa sujada a can. Wannan ya zama tarko ga Gidiyon da waɗanda ke cikin gidansa.28Mutanen Isra'ila suka mallake Midiyanawa, kuma basu ƙara tada kansu ba. Ƙasar ta zauna cikin salama shakara arba'in a cikin kwanakin Gidiyon.
29Yerub Ba'al ɗan Yowash ye je ya zauna a cikin gidansa.30Gidiyon yana da 'ya'ya saba'in a zuriyarsa, da yake yana da mata da yawa.31Ƙwarƙwararsa wadda ke a Shekem ma ta haifa masa ɗa, Gidiyon kuma ya ba shi suna Abimelek.
32Gidiyon ɗan Yowash ya mutu cikin shekarun tsufa masu kyau, aka bizne shi cikin kabarin Yowash ubansa, na kabilar Abiyeza.33Bayan mutuwar Gidiyon mutanen Isra'ila suka koma karuwanci ta wurin bautawa Ba'aloli, sun maida Ba'al Berit allahnsu.
34Mutanen Isra'ila ba su tuna su girmama Yahweh Allahnsu ba, wanda ya kuɓutar da su daga hannun abokan gãbarsu ta kowanne gefe.35Ba su kiyaye alƙawuransu ga gidan Yerub Ba'al ba (wato Gidiyon), sakamakon dukkan abin kirki da ya yi a Isra'ila.

9

1Abimelek ɗan Yarub Ba'al, ya tafi wajan 'yan'uwan mamarsa a Shekem, ya ce da su da dukkan dangin mamarsa,2"Idan ka yarda ka fadi wannan domin dukkan shugabannin Shekem su ji, 'Wanne ya fi a gare ku, dukkan 'ya'ya saba'in na Yerub Ba'al su yi mulki a kanku ko kuwa guda ɗaya ya mulke ku?' Ku tuna ni ƙashinku ne da jikinku."

3Dangin mamarsa suka yiwa shugabannin Shekem magana a kansa, suka amince, gama suka ce, "Shi ɗan'uwanmu ne"4Suka ba shi azurfa guda saba'in daga gidan Ba'al Berit, Abimelek kuma ya yi anfani da ita ya gaiyato mutane marasa ɗa'a da rashin hankali suka yi tafiya tare da shi.
5Abimelek ya tafi gidan ubansa a Ofra ya yi makokin 'yan'uwansa su saba'in, 'ya'yan Yerub Ba'al a bisa wani dutse. Yotam ƙaraminsu kaɗai ya rage cikin 'ya'yan Yerub Ba'al, gama ya ɓoye kansa.6Dukkan shugabannin Shekem da Bet Millo suka zo suka taru suka maida Abimelek ya zama sarki daura da rimi, kusa da ginshiƙi wanda ke cikin Shekem.
7Sa'ad da Yotam ya ji haka, ya tafi ya tsaya a kan Tsaunin Gerizim. Ya tada murya ya ce da su, "Ku saurare ni, ku shugabannin Shekem, ko Allah ya ji ku.8Itatuwa suka je domin su naɗa sarki. Gama sun ce da itacen zaitun ka zama sarkinmu,'
9Amma itacen zaitun yace da su, 'In dena ba da maina da ake anfani da shi ana girmama alloli da mutane, in kuma dawo wurin sauran itatuwa?'10Itatuwan suka ce da itacen ɓaure, 'Kazo ka yi mulkin mu,'11Amma itacen ɓaure yace da su, 'Zan bar zaƙina da 'ya'yana masu kyau, domin in dawo in dogara ga sauran itatuwa?'
12Itatuwa suka ce da inabi, 'Kazo ka yi mulkin mu,'13Inabi ya cewa, 'Zan bar ba da sabon ruwan anab ɗina mai ƙarfafa alloli da mutane, in dawo in dogara ga sauran itatuwa?'14Sai dukkan itatuwa suka ce da ƙaya, 'Ki zo ki yi mulkin mu.'
15Sai ƙaya ta ce da itatuwa, 'Idan gaskiya ne kuna so ku naɗa ni sarauniya a bisanku, sai kowannenku ya zo ya sami wuri a ƙarƙashin inuwata. Idan ba haka ba, bari wuta ta fito daga cikin ƙaya ta ƙone rimi na Lebanon.16To yanzu, idan dai gaskiya ne kun yi aminci, da kuka sa Abimelek ya zama sarkinku, idan kun yi abin da ya wajaba ga Yerub Ba'al da gidansa, kuma kun yi masa horon da ya kamata -
17- da tunanin ubana ya yi faɗa dominba, ya sa ransa cikin hatsari ya kuɓutar da ku daga hannun Midiyan -18amma yau kun tashi gãba da gidan ubana, kun kashe 'ya'yansa saba'in a bisa dutse ɗaya. Sa'an nan kun maida Abimelek ɗan baiwarsa ya zama sarkin shugabanin Shekem, da yake shi ɗan'uwanku ne.
19Idan dai kun yi gaskiya da girmamawa ga gidan Yerub Ba'al, to ku yi farinciki da Abimelek shi ma ya yi farinciki da ku.20Amma idan ba haka ba ne, bari wuta ta fito daga cikin Abimelek ta cinye mutanen Shekem da na Bet Millo. Bari wuta ta fito daga mutanen Shekem da Bet Millo ta cinye Abimelek.21Yotam ya gudu ya tafi ya gudu ya tafi Biya. Ya zauna a can da ya ke nesa ta ke da Abimelek, ɗan'uwansa.
22Abimelek ya yi mulkin Isra'ila shekaru uku.23Sai Yahweh ya aiko da mugun ruhu tsakanin Abimelek da shugabannin Shekem. Shugabannin Shekem suka juyawa Abimelek baya.24Yahweh ya yi haka ne domin a rama muguntar da aka yi a kan 'ya'yan Yerub Ba'al su saba'in, aka kuma lissafta muguntar a kan Abimelek ɗan'uwansu. Haka kuma aka lissafta muguntar kisan a kan shugabannin Shekem saboda sun taya Abimelek ya kashe 'yan'uwansa maza.
25Shugabannin Shekem suka sa mazaje su yi masa kwanton ɓauna, suka yiwa dukkan masu wucewa fashi a kan hanyar. Aka kaiwa Abimelek rahoton wannan abu.
26Ga'al ɗan Ebed yazo shi da 'yan'uwansa suka je Shekem. Shugabannin Shekem kuwa sun amince da shi.27Suka je cikin gona suka kakkaryo kuringar anab domin su bi ta kai. Suka yi buki a gidan allahnsu, suka ci suka sha, suka la'anci Abimelek.
28Ga'al ɗan Ebed ya ce, "Wane ne Abimelek, kuma wane ne Shekem da za mu bauta masa? Shi ba ɗan Yerub Ba'al ba ne? Zebul ba jami'in sa ba ne? Ya bautawa mutanen Hamor, uban Shekem! Me zai sa mu bautawa Abimelek?29Dama mutanen nan ƙarƙashi na suke! In fitar da Abimelek. In ce da Abimelek, 'Ka kira dukkan sojanka dukka.'"
30Sa'ad da Zebul, jami'in birni, ya ji maganar Ga'al da Ebed, ya ji haushi sosai.31Ya aika da 'yan saƙo zuwa ga Abimelek domin ya ruɗe shi, cewa, "Duba, ga Ga'al ɗan Ebed da 'yan'uwansa suna zuwa Shekem, suna kuma zuga birnin gãba da kai.
32Ka tashi idan dare ya yi, kai da sojojin da ke tare da kai ku yi masu kwanton ɓauna a cikin daji.33Da safiya ta yi, sa'ad da rana ta fito, ka shiga ka kaiwa birnin hari. Idan shi da mutanensa suka taso maka, ka yi masu abin da ka ga dama."
34Abimelek ya tashi daddare, suka kasu huɗu suka yiwa Shekem kwanton ɓauna.35Ga'al ɗan Ebed ya tashi ya tsaya a ƙofar birni. Abimelek da mazajen da ke tare da shi suka fito daga inda suke a ɓoye.
36Da Ga'al ya ga mazajen, ya ce da Zebul, "Duba ga mutane na gangarowa daga kan duwatsu!" Zebul ya ce da shi, "Kana ganin inuwoyi a kan duwatsu ne kamar mutane."37Ga'al ya ƙara cewa, "Duba mutane suna gangarowa daga tsakiyar ƙasa, wani kashi kuma na zuwa ta hanyar rimi na masu duba."
38Sai Zebul ya ce da shi, "Ina maganarka ta fankama yanzu, 'Kai da ka ce wane ne Abimelek da zamu bauta masa?' Waɗannan ba su ne mazajen da ka rena ba? Ka fita yanzu ka yi faɗa da su."39Ga'al ya jagoranci mazajen Shekem, suka yi faɗa da Abimelek.40Abimelek ya kore shi, Ga'al ya gudu daga gabansa. Da yawa suka faɗi da raunuka kafin mashgin ƙofar birni.
41Abimelek ya tsaya a Aruma, Zebul ya kori Ga'al da 'yan'uwansa daga cikin Shekem.42Washegari mutanen Shekem suka fita cikin jeji, a ka kaiwa Abimelek rahoton haka.43Ya ɗauki mazajensa ya raba su uku, su ka yi kwanton ɓauna a jeji. Ya ga mazajen suna fitowa daga cikin birni, ya kai masu hari ya kashe su.
44Abimelek da ƙungiyoyin da ke tare da shi suka kai hari suka toshe ƙofar birni. Sauran kungiyoyi biyu suka kaiwa waɗanda ke cikin jeji suka kashe su.45Abimelek ya yi faɗa da birnin dukkan yini, ya ci birnin ya kashe mutanen da ke cikinsa. Ya rushe ganuwar birnin ya barbaɗa mata gishiri.
46Sa'ad da shugabannin hasumiyar Shekem suka ji, suka shiga babbar maɓoya ta gidan El-Berit.47Aka kaiwa Abimelek labari cewa dukan shugabannin sun taru a hasumiyar Shekem.
48Abimelek tare da mazajen da ke tare shi suka hau Tsaunin Zalmon. Abimelek ya ɗauki gatari ya datso rassa. Ya ɗora a kafaɗarsa ya ummurci mazajen da ke tare da shi. "Abin da ku ka ga na yi, ku yi sauri kowa ya yi."49Haka kowannen su ya saro rassa suka bi Abimelek. Suka tara su jikin hasumiyar birni, suka sa wuta, dukkan mutanen da ke hasumiyar Shekem suka mutu, kusan su dubu maza da mata.
50Sai Abimelek ya tafi Tebez, ya ya kafa sansani a Tebez ya mallake ta.51Amma akwai wata hasumiya mai karfi a birnin, dukan mazaje da mata suka shiga cikin ta suka kulle kansu. Sa'an nan sai suka hau can kan hasumiyar.
52Abimelek yazo wurin hasumiyar da faɗa, ya zo kusa kofar domin ya ƙone ta.53Amma wata mace ta sako nuƙunyar dutsen niƙa a kan Abimelek ta fasa masa kwanya.54Nan da nan ya kira saurayin da ke ɗaukar masa kayan yaƙi ya ce masa, "Ka zaro takobinka ka kashe ni, domin kada a ce, 'mace ce ta kashe shi.'" Sai saurayin ya soke shi, ya mutu.
55Sa'ad da mazajen Isra'ila suka ga Abimelek ya mutu, sai suka koma gida.56Yahweh ya ɗauki fansa a kan Abimelek saboda muguntar da ya yi ta kashe 'yan'uwansa su saba'in.57Yahweh ya mai da muguntar mutanen Shekem ta koma kan su, da la'anar Yotam ɗan Yerub Ba'al.

10

1Bayan Abimelek, Tola ɗan Fuwa ɗan Dodo, mutumin Issaka wanda ya zauna a Shamir, a ƙasar duwatsu ta Ifraim, ya taso domin ya ceci Isra'ila.2Ya alƙalanci Isra'ila shekara ashirin da uku. Ya mutu aka binne shi a Shamir.

3Ya'ir Bagiliyade ya bi bayansa, ya yi alƙalancin Isra'ila shekara ashirin da biyu.4Yana da 'ya'ya talatin, masu hawan jakuna talatin, suna da birane talatin, waɗanda a ke kira Habbot Ya'ir har zuwa yau, suna cikin ƙasar Giliyad.5Ya'ir ya mutu a ka binne shi a cikin Kamon.
6Mutanen Isra'ila suka ƙara a kan muguntar da suka yi a idanun Yahweh, suka bautawa Ba'al, da Ashtoret allolin Aram, da allolin Sidon, da allolin Mowab da allolin mutanen Amon da allolin Filistiyawa. Suka watsar da Yahweh suka dena bauta masa.7Yahweh ya yi fushi da mutanen Isra'ila, ya sayar da su a hannun Filistiyawa da Amoniyawa.
8Suka ragargaza Isra'ila suka gallaza masu azaba a wannan shekara, shekara goma sha takwas suna gallazawa mutanen Isra'ila waɗanda suke a ƙetaren Yodan a ƙasar Amoriyawa wadda ke cikin ƙasar Giliyad.9Sai Amoniyawa suka ƙetare Yodan garin su yi faɗa da Yahuda, da Benyamin da gidan Ifraim, domin a wulaƙanta Isra'ila.
10Sa'an nan mutanen Isra'ila suka yi kira ga Yahweh, suka ce, "Mun yi maka zunubi da yake mun watsar da kai mun bautawa Ba'al."11Yahweh yace da mutanen Isra'ila, "Ban ceto ku daga Masarawa da Amoriyawa da Amoniyawa da Filistiyawa12da kuma Sidoniyawa ba?" Amelikawa da Ma'oniyawa waɗanda suke gallaza maku; kuka kira ni na, ceto ku daga ikonsu.
13Duk da haka kuka watsar da ni kuka bautawa waɗansu alloli. Saboda haka ba zan ƙara wani lokaci na ceton ku ba.14Ku tafi wurin allolin da ku ke bautawa. Sai su kuɓutar da ku idan kuna da damuwa."
15Mutanen Isra'ila suka ce da Yahweh, "Mun yi zunubi. Ka yi mana abin da ya yi maka kyau. Sai dai idan ka yarda ka cece mu yau."16Suka rabu da baƙin allolin da ke tare da su, suka yi sujada ga Yahweh. Daga nan ne Yahweh bai ƙara riƙe damuwarsu ba.
17Sa'an nan Amoniyawa suka taru suka kafa sansani a Giliyad. Isra'ilawa kuma suka taru suka kafa sansaninsu a Mizfa.18Shugabannin Giliyad suka ce da junansu, "Wane ne zai fara yin faɗa da Amoniyawa? Shi ne zai zama shugaba a kan dukkan mazauna Giliyad."

11

1Sai ga Yafta mutumi Giliyad babban mayaƙi ne, amma ɗan karuwane. Giliyad ne ubansa.2Matar Giliyad ta haifa masa waɗansu 'ya'ya, sa'ad da suka yi girma sai suka kori Yafta daga gidan, suka ce masa, "Ba zaka gaji kome a iyalinmu ba. Kai ɗan wata mata ne."3Sai Yafta ya gudu daga wurin 'yan'uwansa, ya tafi ya zauna a ƙasar Tob. Mutane marar sa ɗa'a suka haɗu da Yafta, suka tafi tare da shi.

4Bayan waɗansu kwanaki, mutanen Amon suka yi yaƙi da Isra'ila.5Sa'ad da mutanen Amon suka yi yaƙi da Isra'ila, sai shugabannin Giliyad suka je suka dawo da Yafta daga ƙasar Tob.6Suka ce da Yafta, "Zo ka zama shugabanmu domin mu yi faɗa da mutanen Amon."
7Yafta yace da shugabannin Giliyad, "Kun ƙi ni kun kore ni daga gidan ubana. Me ya sa kuka zo wurina yanzu da kuka sami damuwa?"8Shugabannin Giliyad, suka ce da Yafta, "Shi yasa muka zo wurin ka yanzu, ka zo muje ka yi faɗa da mutanen Amon, za ka zama shugaba a kan dukan mazauna a Giliyad."
9Yafta yace da Shugannin Giliyad, "Idan ku ka kawo ni gida domin in yi faɗa da mutanen Amon, idan Yahweh ya ba mu nasara a kan su, zan zama shugabanku."10Shugabannin Giliyad suka ce da Yafta, "Yahweh ya zama shaida tsakanin mu da kai idan ba mu yi yadda muka ce ba."11Sai Yafta ya tafi tare da shugabannin Giliyad, mutanen suka sa ya zama jagora da shugaban sojojinsu. Sa'ad da yake a gaban Yahweh a Mizfa, Yafta ya maimaita dukkan alƙawuran da ya yi.
12Daga nan Yafta ya aika jakadu wurin sarkin mutanen Amom, cewa, "Wacce matsala ce tsakaninmu da ku? Me ya sa kuka zo ku ƙwace kasarmu?13Sarkin mutanen Amon ya amsa wa jakadun Yafta, "Saboda lokacin da Isra'ila suka fito daga Masar, sun ƙwace ƙasarmu daga Arnon zuwa Yabbok har zuwa Yodan. Yanzu ku maido mana da ƙasarmu cikin salama."
14Yafta ya sake aikawa da jakadu wurin sarkin mutanen Amon,15ya ce, "Ga abin da Yafta ke cewa: Isra'ila ba su ɗauki ƙasar Mowab da ƙasar mutanen Amon ba,16amma Isra'ila sun fito daga Masar suka bi ta jeji zuwa Tekun Iwa zuwa Kadesh."
17Sa'ad da Isra'ila suka aika jakadu zuwa sarkin Idom, cewa, 'Idan ka yarda ka bari mu wuce ta ƙasarka', amma sarkin Idom bai saurare su ba. Suka kuma aika da jakadu wurin sarkin Mowab, amma ya ƙi, sai Isra'ila suka tsaya a Kadesh.18Sai suka bi ta jeji su kewaye ƙasar Idom da ƙasar Mowab, sai suka bi ta gabas da ƙasar Mowab, suka raɓi ƙasar Arnon suka sauka. Amma ba su je yankin Mowab ba, da ya ke Arnon iyakar Mowab ce.
19Isra'ila suka aika da jakadu wurin Sihon, sarkin Amoriyawa, wanda yake mulki a Heshbon; Isra'ila suka ce masa, 'Idan ka yarda ka bari mu bi ta ƙasarka mu je wurin da ke namu.'20Amma Sihon bai amince da Isra'ila su bi ta yankinsa ba. Sai Sihon ya tattara sojojinsa ya zakuɗa zuwa Jahaz, can ya yi faɗa da Isra'ila.
21Yahweh, Allah na Isra'ila, ya ba da Sihon da mutanensa a hannun Isra'ila suka yi nasara a kan su. Isra'ila suka mallaki ƙasar Amoriyawa waɗanda ke zaune a wannan, ƙasar.22Suka mallake komi da komi na ƙasar Amoriyawa tun daga Arnon har zuwa Yabbok, daga jeji kuma har zuwa Yodan.
23Haka kuma Yahweh, Allah na Isra'ila ya kori Amoriyawa a gaban mutanen Isra'ila, ko yanzu kuma za ku mallake ƙasarsu?24Ba zaku mallaki ƙasar da Kemosh, allahnku yake ba ku ba? Domin haka duk ƙasar da Yahweh Allahnmu ya ba mu za mu mamaye ta.25Yanzu ka fi Balak ɗan Ziffo, sarkin Mowab ne? Ya taɓa yin jayayya da Isra'ila ne? Ya taɓa yin yaƙi da su ne?
26Sa'ad da Isra'ila suka zauna a Hesbon da ƙauyukanta shekara dari uku, da Arowa da ƙauyukanta, da kan iyakokin Arnon - meyasa ba ka mallake su a wancan lokaci ba?27Ni ban yi maka laifi ba, kai ne ka yi mani laifi da ka kawo mani hari. Yahweh mai shari'a, yau zaya hukunta tsakanin mutanen Isra'ila da mutanen Amon."28Amma sarkin mutanen Amon ya yi ƙi gargaɗin da Yafta ya aika masa.
29Sai Ruhun Yahweh ya sauko kan Yafta, ya ratsa ta Giliyad da Manasse, ya kuma ratsa ta Giliyad ɗin Mizfa, daga Giliyad ɗin Mizfa ya bi ta mutanen Amon.30Yafta ya yi alƙawari da Yahweh ya ce, "Idan ka ba ni nasara a kan mutanen Amon, idan na dawo cikin salama,31duk abin da ya fito daga ƙofofin gidana ya tarbe ni zai zama na Yahweh, zan miƙa shi hadaya."
32To sai Yafta ya bi ta wurin mutanen Amon ya yi faɗa da su, Yahweh kuma ya ba shi nasara.33Yakai masu hari ya yi babban kisa tun daga Arowa har zuwa Minnit - birane ashirin - da zuwa Abel Keramim. Ta haka mutanen Amon suka zauna a ƙarƙashin mutanen Isra'ila.
34Yafta ya koma gidansa a Mizfa, sai ga ɗiyarsa ta fito tarbarsa da kayan kiɗi da rawa. Ita kaɗai ce ɗiyarsa, banda ita ba shi da wani ɗa ko ɗiya.35Da dai ya gan ta ya yage tufafinsa ya ce, "Haba ɗiyata! Kin sa ni nukura, kin sa mani jin zafi a raina! Gama nayi alƙawari ga Yahweh, ba zan iya janye alƙawarina ba.
36Ta ce masa "Babana, Ka yi wa Yahweh alƙawari, ka yi mani ko mene ne ka yi wa Yahweh alƙawari gama Yahweh ya ɗaukar maka fansa a kan abokan gabarka, Amoniyawa.37"Ta cewa babanta, "Bari wannan alƙawari ya zauna a kaina, ka bani wata biyu da zan je kan duwatsu in yi kukan budurcina ni da ƙawayena."
38Ya ce da ita. "Jeki." Ya bata wata biyu. Ta tafi, ta bar shi ta tafi ita da Ƙawayenta suka yi kukan budurci a cikin tuddai.39Bayan watanni biyun ta dawo wurin babanta, wanda da ita bisa ga alƙawari na wa'adi. Ita kuwa ba ta san namiji ba, wannan ya zama al'ada a cikin Isra'ila40'yan'matan Isra'ila kowacce shekara sukan ɗauki kwanaki huɗu, suna maimaita labarin ɗiyar Yafta Bagiliyade.

12

1Kira ya zo ga mazajen Ifraim, suka bi ta Zafon suka ce da Yafta, "Meyasa ka wuce ka yi faɗa da mutanen Amon baka ce mu zo mu tafi tare da kai ba? Za mu ƙone gidanka a kan ka."2Yafta ya ce da su, "Ni da mutanena muna da babbar matsala da mutanen Amon. Sa'ad da na kira ku baku cece ni daga wurinsu ba."

3Sa'ad da naga ba ku cece ni ba, sai na sa raina da ƙarfina na wuce gãba da su, kuma Yahweh ya ba ni nasara. Meyasa kuka zo ku yi faɗa da ni yau?4Yafta ya tattaro dukan mazajen Giliyad ya yi faɗa da Ifraim. Mazajen Giliyad suka kai hari ga mazajen Ifraim saboda sun ce, "Ku Giliyadawa masu gudu ne na cikin Ifraim - da Ifraim da cikin Manasse."
5Giliyadawa suka kama magangarun Yodan masu kaiwa Ifraim. Idan wani wanda ya tsira na Ifraim ya zo yace, "Bari in haye kogin", sai mazajen Giliyad su ce da shi, "Kai Ba'ifrane ne?" Idan ya ce, "A'a,"6sai su ce da shi ka ce, "Shibbolet," idan ya ce, "Sibbolet" (gama ba zai iya fadin kalmar dai-dai ba), Giliyadawa sai su kama shi su kashe shi a magangarun Yodan. Mutanen Ifraim dubu arba'in da biyu aka kashe a wannan lokacin.
7Yafta ya yi alƙalanci a Isra'ila shekara shida. Sa'an nan Yafta ya mutu aka bizne shi a cikin ɗaya daga biranen Giliyad.
8Bayan shi Ibzan na Betlehem ya yi alƙalancin Isra'ila.9Yana da 'ya'ya talatin. Ya aurar da 'ya'ya mata talatin, kuma ya kawo wa 'ya'yansa 'yan'mata talatin, daga waje. Ya yi alƙalancin Isra'ila shekara bakwai.
10Ibzan ya mutu aka bizne shi a Betlehem.11Bayan shi Ilon mutumin Zebulun ya yi alƙalanci a Isra'ila, ya yi alƙalancin Isra'ila shekara goma.12Ilon mutumin Zebulun ya mutu aka bizne shi a Aijalon cikin ƙasar Zebulun.
13Bayan shi, Abdon ɗan Hillel Ba-firatone ya yi alƙalancin Isra'ila.14Yana da 'ya'ya arba'in da jikoki talatin. Suna hawan jakai saba'in, ya yi alƙalancin Isra'ila shekara takwas.15Abdon dan Hillel Ba-firatone ya mutu aka bizne shi a Firaton cikin ƙasar Ifraim a ƙasar duwatsu ta Amelikawa.

13

1Mutanen Isra'ila suka sake yin aikin mugunta a fuskar Yahweh, kuma ya bayar da su a hannun Filistiyawa shekara arba'in.2Akwai wani mutumin Zorah, na iyalin Danawa, sunansa Manowa. Matarsa ba ta iya ɗaukar juna biyu saboda haka bata haihu ba.

3Mala'ikan Yahweh ya baiyana ga matar ya ce da ita, "Duba, baki iya kin ɗauki juna biyu ba, kuma baki haihu ba, amma za ki sami juna biyu, za ki haifi ɗa.4Duba, kada ki sha ruwan inabi, kada ki ci abu marar tsarki.5Duba za ki sami juna biyu, za ki haifi ɗa. Ba za a yi anfani da reza a kansa ba, gama yaron zai zama Naziri ga Yahweh tun daga cikin ciki. Shi zaya fara kuɓutar da Isra'ilawa daga hannun Filistiyawa."
6Matar ta je ta gaya wa mijinta, "Wani mutumin Yahweh, ya zo wurina, kamanninsa kamar na mala'ikan Yahweh, da ban razana ƙwarai. Ban tambaye shi daga inda ya fito ba, kuma bai faɗa mani sunansa ba.7Ya ce da ni, "Duba! Za ki yi juna biyu za ki haifi ɗa. Kada ki sha ruwan inabi ko wani abin sha mai ƙarfi, kada ki ci abin da shari'a ta ce ba shi da tsarki, gama yaron zai zama Naziri ga Yahweh tun daga cikin ciki har ranar mutuwarsa."
8Sai Manowa ya yi addu'a ga Yahweh, ya ce, "Ya Yahweh, idan ka yarda ka sake aiko da wannan mutum domin ya koya mana yadda za mu yi da yaron da za a haifa ba da daɗewa ba."9Yahweh ya saurari muryar Manowa, kuma sai mala'ikan Yahweh ya zo wurin matar lokacin da ta ke zaune a fili. Amma mijinta Manowa ba ya tare da ita.
10Sai matar ta yi gudu da sauri ta gaya wa mijinta, "Duba! Mutumin ya baiyana gare ni, wanda ya zo wuri na waccan ranar!"11Manowa ya tashi ya bi matarsa. Sa'ad da ya zo wurin mutumin, ya ce, "Kai ne mutumin da ya yi magana da matata?" Mutumin yace, "Ni ne."
12Sai Manowa yace, bari maganganunka su zama gaskiya. Mene ne zai zama ka'idodi game da yaron, kuma mene ne zai zama aikinsa?"13Mala'ikan Yahweh ya ce da Manowa, "Dole ta yi hankali ta yi dukan abin da na faɗa mata.14Kada ta ci kowanne abu da ya fito daga kuringa, kada ta sha ruwan inabi ko abin sha mai ƙarfi; kada ka bari ta ci kowanne abinci da shari'a ta ce ba shi da tsarki. Ta yi biyaiya da dukan abin da na ummurce ta ta yi."
15Manowa yace da mala'ikan Yahweh, "Idan ka yarda ka ɗan jira, ka ba mu lokaci mu shirya maka 'yar burguma."16Sai mala'ikan Yahweh yace da Manowa, "Ko na tsaya ba zan ci abincinku ba. Idan kun shirya hadaya ta ƙonawa, ku miƙa ta ga Yahweh." (Manowa bai san cewa shi mala'ikan Yahweh ne ba.)
17Manowa yace da mala'ikan Yahweh, "Mene ne sunanka, domin mu darajanta ka, idan kalmominka suka zama gaskiya?"18Mala'ikan Yahweh ya ce masa, "Meyasa ka ke tambayar sunana? Shi ne abin mamaki!"
19Sai Manowa ya ɗauki 'yar akuya da baiko na hatsi ya miƙa su a dutsen Yahweh. Ya yi wani abin mamaki Manowa da matasa suna kallo.20Sa'ad da harshen wuta ya tashi sama daga bagadin, mala'ikan Yahweh ya tafi sama cikin harshen wuta na bagadin. Da ganin haka Manowa da matarsa suka faɗi da fuskokinsu a ƙasa.
21Mala'ikan Yahweh bai ƙara baiyana ga Manowa ba ko matarsa. Sa'an nan ne Manowa ya sani mala'ikan Yahweh ne.22Manowa yace da matarsa, "Ba shakka za mu mutu da ya ke mun ga Yahweh!"
23Matarsa ta ce da shi, "Da Yahweh ya so ya kashe mu, da bai karɓi baiko na ƙonawa da hatsin da muka ba shi ba. "Da bai nuna mana dukkan waɗannan abubuwan ba, ko ya bari mu ji waɗannan abubuwa a wannan lokaci."
24Daga baya, matar ta haifi ɗa, aka kira sunansa Samsin. Yaron ya yi girma, Yahweh ya albarkace shi.25Ruhun Yahweh ya fara ƙarfafa shi a cikin Mahane Dan, tsakanin Zora da Eshtawol.

14

1Samsin ya je Timna, a can ya ga wata mata, ɗiyar Filistiyawa.2Sa'ad da ya dawo ya ce da babansa da mamarsa, "Na ga wata mata a Timna, ɗaya daga cikin 'ya'yan Filistiyawa. Sai ku ɗauko mani ita ta zama mata ta."

3Babansa da mamarsa suka ce da shi, "Ba wata mata a cikin 'ya'yan danginka, ko cikin dukkan mutanen mu?" Za ka ɗauko mata daga Filistiyawa marasa kaciya?" Samsin yace da babansa, "A ɗauko ta domi na, idan na dube ta, ta gamshe ni."4Amma babansa da mamarsa ba su sani ba wannan daga wurin Yahweh ne, domin ya yi shirin ƙulla husuma da Filistiyawa (gama a wannan lokaci Filistiyawa ne ke mulki a Isra'ila).
5Samsin ya gangara zuwa Timna tare da babansa da mamarsa, suka zo gonakin Timnah. Sai ga wani ɗan zaki ya taso masa ya na ruri.6Ruhun Yahweh ya zo kansa ya yayyaga ɗan zakin kamar ɗan akuya, kuma ba komi a hannunsa. Amma bai gaya wa babansa ko mamarsa abin da ya yi ba.
7Ya je ya yi magana da matar, sa'ad da ya dube ta ta gamshi Samson.8Bayan 'yan kwanaki da ya dawo ya aure ta, ya juya ya dubi gawar zakin. Sai ga kututun zuma a cikin abin da ya rage na gawar zakin.9Ya yagi zuman ya tafi, yana tafiya ya na ci. Ya zo wurin babansa da mamarsa ya ba su su ma suka ci. Amma bai gaya masu ya samo zuman daga abin da ya rage na jikin gawar zakin ba ne.
10Baban Samsin ya je wurin da matar ta ke, Samson ya yi buki a wurin gama wannan ita ce al'adar samarin.11Da dai danginta suka gan shi suka kawo masa abokai talatin su zauna tare da shi.
12Samsin ya ce masu, "Bari in gaya maku wani karin magana. Idan wani a cikin ku ya gaya ma ni ma'anarsa cikin kwanakin nan bakwai na biki, zan ba da rigunan lilin guda talatin da suturu guda talatin.13Amma idan ba ku iya ba ni amsa ba, za ku ba ni rigunan lilin talatin da suturu guda talatin. Suka ce da shi, "Ka faɗa mana karin maganarka mu ji."
14Ya ce da su, "A cikin maciyi, akwai abin da za a ci; a cikin mai ƙarfi akwai abu mai zaƙi." Amma baƙinsa ba su iya gano amsar cikin kwana uku ba.
15A kan rana ta huɗu suka ce da matar Samsin, "Ki zolayi mijinki domin ya gaya mana amsar karin maganar, ko kuma mu ƙone gidan mahaifinki. Kin gaiyato mu nan ne domin ki mai da mu marasa anfani?"
16Matar Samsin ta fara yin kuka a gabansa ta ce, "Dukkan abin da ka ke yi ƙi na! Ka ke yi ba ka ƙauna ta. Ka gaya wa waɗansu mutanena karin magana, amma ba ka gaya mani amsar ba." Samsin yace da ita, "Duba nan, abin da ban gaya wa babana ko mamata ba, sai in gaya maki?"17Dukkan kwanakin nan bakwai na buki ita tana ta kuka. Ta matsa masa ƙwarai, a rana ta bakwai ya gaya mata amsar. Ita kuma ta gayawa dangin mutanenta amsar.
18A rana ta bakwai kafin rana ta faɗi, mazajen garin suka ce da shi, "Me ya fi zuma zaƙi? Me ya fi zaki ƙarfi? Samsin yace da su, "Da ba domin kun yi huɗa da karsanata ba, da ba ku gano amsar karin maganata ba."
19Sai Ruhun Yahweh ya zo kan Samsin da iko. Samsin ya je Ashkelon ya kashe mazajen su guda talatin. Ya kwashe ganimarsu, ya bada tufafinsu ga waɗanda suka baiyana masa karin zaurancensa. Ya tafi gidan ubansa cikin fushi mai zafi.20Aka bada matar Samsin ga babban abokinsa.

15

1Bayan waɗansu kwanaki, a lokacin girbin alkama, sai Samsin ya ɗauki 'yar akuya ya tafi domin ya ziyarci matarsa. Ya ce a ransa, "Zan shiga ɗakin matata." Amma mahaifinta bai bar shi ya shiga ba.2Sai mahaifinta yace, "Tabbas na zaci ka ƙi jininta, sai na bayar da ita ga abokinka. Ai ƙanwarta ta fi ta kyau, ko kuwa? Sai ka ɗauke ta a maimakonta."

3Samsin yace masu, "Wannan karon ba ni da hakkin Filistiyawa duk zafin da zan sa masu game da wannan al'amari."4Samsin ya tafi ya kamo diloli ɗari uku ya ɗaura su biyu-biyu, bindi da bindi. Sai ya ɗauko gaushen wuta ya ɗaɗɗaura a tsakiyar kowanne ɗaurin bindi biyu.
5Da ya kunnawa gaushen wuta, sai ya tura dilolin cikin hatsin Filistiyawa, suka cinnawa hatsin wuta duk da zangarniyar da ke cikin gonakin, duk da Inabinsu garka-garka da lambunan zaitun.6Filistiyawa kuwa suka yi tambaya, "Wane ne ya yi wannan?" Aka gaya masu, "Samsin ne, surukin Batimne ya yi haka, domin Batimnen ya ɗauki matar Samsin ya ba abokinsa." Sai Filistiyawan suka tafi suka ƙone ta tare da mahaifinta.
7Samsin yace masu, "Idan haka ku ka yi, zan ɗauki ramuwata a kanku, bayan haka ya faru, zan dakata."8Sai ya datsa su gunduwa-gunduwa, kwankwaso da cinya, da babbar gunduwa. Sai ya gangara ya tafi ya zauna cikin kogon dutsen Itam.
9Sai Filistiyawa suka fito da shirin yaƙi cikin Yahuda suka kuma jera sojojinsu a Lehi.10Mutanen Yahuda suka ce, "Mene ne ya sa ku ka fito ku kawo mana hari?" Suka ce, "Mun kawo hari ne domin mu kama Samsin, kuma mu yi masa yadda ya yi mana."
11Sai mutanen Yahuda su dubu uku suka tafi suka gangara kogon dutsen Itam, suka kuma cewa Samsin, "Ba ka san cewa Filistiyawa ne ke mulkinmu ba? Mene ne ka yi mana haka?" Samsin yace masu, "Sun yi mani, saboda haka nima na yi masu."
12Suka cewa Samsin, "Mun gangaro ne domin mu ɗaure ka kuma mu miƙa ka cikin hannun Filistiyawa." Samsin yace masu, "Ku rantse mani cewa ku da kanku ba za ku kashe ni ba."13Suka ce masa, "A a, zamu ɗaure ka ne kawai da igiyoyi kuma mu miƙa ka gare su. Mun yi alƙawari ba za mu kashe ka ba." Daga nan suka ɗaure shi da sabbin igiyoyi biyu suka fito da shi daga dutsen.
14Da ya zo Lehi, Filistiyawa suka fito da Ihu yayin da suke zuwa su gamu da shi. Sai Ruhun Yahweh ya sauko kansa da iko. Sai igiyoyin da ke bisa hannuwansa suka zama kamar ƙonannar ciyawa, suka kuma zube daga hannuwansa.
15Sai Samsin ya samo sabon ƙashin muƙamuƙin jaki, ya ɗauko ya kuma kashe mutane dubu da shi.16Samsin yace, "Da ƙashin muƙamuƙin jaki, tari bisa tari, da ƙashin muƙamuƙin jaki na kashe mutane dubu."
17Da Samsin ya gama magana, sai ya jefar da ƙashin muƙamuƙin jakin, sai ya kira wurin da suna Ramat Lehi.18Samsin ya ji ƙishi sosai sai ya yi kira ga Yahweh ya ce, "Ka bayar da nasara mai girma ga bawanka. Amma yanzu zan mutu da ƙishi ne kuma in faɗa cikin hannuwan waɗancan marasa kaciyar?"
19Sai Allah ya tsaga cikin sararin da ke Lehi sai ruwa ya ɓulɓulo. Da ya sha, sai karfinsa ya dawo kuma ya farfaɗo. Saboda haka ya kira sunan wannan wuri En Hakkori, kuma yana nan a Lehi har yau.20Samsin ya yi alƙalancin Isra'ilawa a zamanin Filistiyawa har shekaru ashirin.

16

1Samsin ya tafi Gaza sai ya ga karuwa a can, sai kuwa ya kwana da ita.2Aka faɗa wa Gazawa, "Samsin ya shigo nan fa." Gazawa suka kewaye wurin a asirce, suka yi masa kwanto tsawon dare a ƙofar birnin. Suka yi tsit dukkan tsawon daren. Sun riga sun ce, "Mu jira har sai wayewar gari, sa'an nan kuma mu kashe shi."

3Samsin ya yi kwance bisa gado har tsakiyar dare. Da dare ya yi tsaka sai Samsin ya tashi ya tafi ya kama ƙofar birnin da ginshiƙanta biyu. Ya tumɓuko su daga ƙasa, duk da ƙarafunan da komai, ya ɗorasu bisa kafaɗunsa, ya tafi da su bisa tudu, a gaban Hebron.
4Bayan wannan, Samsin ya zo ya ƙaunaci wata mata da ke zaune a Kwarin Sorek. Sunanta Delila.5Masu mulkin Filistiyawa suka zo wurinta, suka ce da ita, "Ki yaudari Samsin domin ki gane inda babban ƙarfinsa yake, da kuma ta yaya zamu sha ƙarfinsa, domin mu ɗaure shi mu kuma yi masa wulaƙanci. Ki yi mana wannan, mu kuma kowanne zai ba ki azurfa 1,100 ."
6Daga nan Delila ta ce da Samsin, "Ina roƙonka, ka gaya mani yadda aka yi ka ke da ƙarfi haka, kuma ta yaya za a iya ɗaure ka, domin a mulke ka?"7Samsin yace mata, "Idan aka ɗaure ni da ɗanyen ƙiri guda bakwai, daga nan zan zama marar ƙarfi kuma in zama kamar kowanne mutum."
8Sai masu mulkin Filistiyawa suka kawo wa Delila igiyoyin ƙiri guda bakwai ɗanyu, ita kuwa ta ɗaure Samsin da su.9Ta riga ta ɓoye mutane a asirce, suna jira cikin ƙuryar ɗakinta. Sai ta ce da shi, "Filistiyawa suna kanka, Samsin!" Amma ya tsisttsinke igiyoyin kamar zare a mazari idan ya taɓa wuta. Ta haka ba a gane asirin ƙarfinsa ba.
10Daga nan Delila ta ce da Samsin, "Yadda ka ruɗe ni kenan kuma ka yi mani ƙarya. Ina roƙon ka, ka faɗa mani yadda za a sha ƙarfinka."11Sai ya ce mata, "Idan aka ɗaure ni da sabbin igiyoyin da ba a taɓa aiki da su ba, daganan zan zama marar ƙarfi kuma in zama kamar kowanne mutum."12Sai Delila ta ɗauki sabbin igiyoyi ta ɗaure shi da su, sai ta ce da shi, "Filistiyawa suna kanka, Samsin!" Mutanen kuwa 'yankwanto suna cikin ƙuryar ɗakin. Samsin kuwa ya tsisttsinke igiyoyin kamar zare.
13Delila ta ce da Samsin, "Har yanzu ruɗi na ka ke yi kuma kana faɗa mani ƙarairayi. Ka gaya mani yadda za a sha ƙarfinka." Samsin yace mata, "Idan ki ka saƙa tukkun kaina guda bakwai bisa masaƙa kamar yadda ake saƙa sutura, sa'an nan ki sa allura ki kafe gashin bisa gungumen masaƙar, zan zama kamar kowanne mutum."14Yayin da ya yi barci, sai Delila ta yi wa tukkun kansa bakwai saƙa kamar an saƙa sutura bisa masaƙa ta kuma sa allura ta kafe shi bisa masaƙa, sai ta ce da shi, "Filistiyawa suna kanka, Samsin!" Ya farka daga barci kuma ya yage gashin duk da allurar daga jikin masaƙar.
15Sai ta ce masa, "Ta yaya za ka ce, 'Ina son ki,' amma baka iya faɗa mani asirinka ba? sau uku kenan kana yi mani ba a kuma ba ka gaya mani yadda aka yi ka ke da babban ƙarfi haka ba."16Kowacce rana ta dinga gasa masa tsanani ta wurin maganganu, ta tsananta masa ƙwarai da gaske har ya gwammace ya mutu.
17Sai Samsin ya faɗa mata dukkan komai ya ce mata, "Ba a taɓa sa reza aka yanke gashin kaina ba, Gama ni Naziri ne domin Allah tun daga mahaifar uwata. Idan aka aske kaina, to ƙarfina zai rabu da ni, daganan zan zama marar ƙarfi kuma in zama kamar kowanne mutum."
18Da Delila ta ga cewa ya faɗa mata gaskiya game da komai, sai ta aika aka kira masu mulkin Filistiyawa, ta na cewa, "Ku sake dawowa, gama ya faɗa mani komai." Sai masu mulkin Filistiyawa suka tafi wurinta, suna ɗauke da azurfa a hannuwansu.19Sai ta sa barci ya kwashe shi a bisa cinyarta. Ta kira wani mutum yazo ya aske tukkaye bakwai da ke a kansa, daga nan ta dinga jujjuya shi, domin ƙarfinsa ya riga ya rabu da shi.
20Ta ce, "Filistiyawa suna kanka, Samsin!" ya farka daga barcinsa ya ce, "Zan tashi kamar lokutan baya in kuma girgije kaina kuɓutacce." Amma ba ya sani cewa Yahweh ya riga ya rabu da shi ba.21Filistiyawa suka kama shi suka ƙwaƙule masa idanu. Suka kawo shi har Gaza suka kuma ɗaure shi da sarƙoƙin tagulla. Shi ne ke aikin juya dutsen niƙa a kurkuku.22Amma gashin kansa ya soma sake tuƙowa bayan askin da aka yi masa.
23Masu mulkin Filistiyawa suka taru domin su miƙa babbar hadaya ga Dagon allahnsu, su kuma yi farinciki. Suka ce, "Allahnmu ya yi nasara da Samsin, maƙiyinmu, ya kuma sa shi cikin hannuwanmu."24Da mutanen suka gan shi, sai suka yi yabo ga allahnsu, domin suka ce, "Allahnmu ya yi nasara da maƙiyinmu kuma ya miƙa shi gare mu - mai lalatar da ƙasarmu, wanda ya kashe masu yawa daga cikinmu."
25Yayin da suke cikin shagali, sai suka ce, "A kira mana Samsin, domin ya zo ya sa mu dariya." Aka kira Samsin daga cikin kurkuku ya zo ya yi ta ba su dariya. Suka sa ya tsaya a tsakanin ginshiƙan ginin.26Samsin yace da saurayin da ya riƙe hannunsa, "Ka bar ni in taɓa ginshiƙan da ke riƙe da ginin, domin in jingina da su."
27Yanzu fa gidan na cike da mutane maza da mata. Dukkan masu mulkin Filistiyawa suna wurin. A bisa rufin ginin akwai mutum dubu uku maza da mata, waɗanda ke kallo yayin da Samsin ke yi masu wasa.
28Samsin ya yi kira ga Yahweh ya ce, "Ubangiji Yahweh, ka tuna da ni! Ina roƙon ka ka ƙarfafa ni sau ɗaya kacal, ya Allah, domin in ɗauki fansa bugu ɗaya tak akan Filistiyawa saboda idanuna biyu da suka ƙwaƙule."29Samsin ya riƙe ginshiƙan nan biyu da ke ɗauke da ginin, sai ya jingina kansa da su, hannunsa na dama na riƙe da ɗaya, kuma hannunsa na hagu na riƙe da ɗayan.
30Samsin yace, "Bari in mutu tare da Filistiyawa!" Ya miƙe iya ƙarfinsa ginin kuwa ya rugurguje bisa masu mulkin da dukkan mutanen da ke ciki. Saboda haka matattun da ya kashe a mutuwarsa sun fi waɗanda ya kashe a lokacin rayuwarsa.31Daga nan 'yan'uwansa da dukkan gidan mahaifinsa suka gangaro. Suka ɗauko shi, suka dawo da shi suka kuma binne shi tsakanin Zora da Eshtawol a maƙabartar Manowa, mahaifinsa. Samsin ya yi alƙalacin Isra'ila shekaru ashirin.

17

1Akwai wani mutum a ƙasar tudu ta Ifraim, sunansa Mika.2Sai ya ce da mahaifiyarsa, "Azurfarki 1,100 da aka ɗauke maki, wanda kuma ki ka furta la'ana akai, wanda kuma na ji - duba nan! azurfar na wurina. Ni ne na sace." Mahaifiyarsa ta ce, "Yahweh ya albarkace ka, ɗana!"

3Sai ya maido wa mahaifiyarsa azurfa 1,100 sai mahaifiyarsa ta ce, "Na keɓe wannan azurfa ga Yahweh, domin ɗana ya sassaƙa kuma ya sarrafa siffofi na ƙarfe. Saboda haka yanzu, na maido maka azurfar."4Da ya maido wa mahaifiyarsa kuɗin, sai mahaifiyarsa ta ɗauki azurfa ɗari biyu ta ba maƙeri wanda shi kuma ya sassaƙa ya kuma sarrafa siffofi na karfe da su, sai aka ajiye su a gidan Mika.
5Mutumin nan Mika ya na da gidan gumaka sai ya yi falmarar haikali da kuma allolin gida, sai ya ɗauki hayar ɗaya daga cikin 'ya'yansa maza ya zama firist.6A waɗannan kwanaki ba sarki a Isra'ila, kowa na yin abin da ya yi dai-dai a idanunsa.
7Akwai wani saurayi daga Betlehem ta cikin Yahuda, daga iyalin Yahuda, shi kuwa Balebi ne. Ya na zaune anan domin ya aiwatar da ayyukansa.8Mutumin ya bar Betlehem ta Yahuda ne domin ya fita ya je ya sami wani wurin zama. Yayin da ya ke tafiya, sai ya zo gidan Mika da ke ƙasar tuddun Ifraim.9Sai Mika yace masa, "Daga ina ka fito?" Mutumin yace masa, "Ni Balebi ne na Betlehem ta cikin Yahuda, kuma na fito tafiya ne domin neman wurin zama."
10Mika yace da shi, "Ka zauna da ni, sai ka zama uba da firist a gare ni. Zan ba ka azurfa goma a shekara, da kayan sawa, da abinci." Sai Balebin ya shiga cikin gidansa.11Balebin ya dangana da zama da mutumin, kuma saurayin ya zame wa Mika kamar ɗaya daga cikin 'ya'yansa maza.
12Mika ya keɓe Balebin saboda ayyukan ibada, sai saurayin ya zama firist ɗinsa, kuma yana cikin gidan Mika.13Sai Mika yace, "Yanzu na sani cewa Yahweh zai yi mani abin alheri, domin Balebin nan ya zama firist ɗina."

18

1A waɗannan kwanaki babu sarki a Isra'ila. Kabilar zuriyar Dan suna neman wajen da za su yi wa kansu wurin zama, domin har zuwa wannan lokaci ba su karɓi wani gãdo daga cikin kabilun Isra'ila ba.2Mutanen Dan suka aika da mutum biyar daga dukkan cikin kabilarsu, mutanen da suka ƙware wajen yaƙi daga Zora zuwa Eshtawol, domin su kewaye ƙasar da ƙafa, kuma su duba ta. Suka ce masu, "Ku je ku duba ƙasar." Suka zo ƙasar tudu ta Ifraim, suka zo gidan Mika, suka kwana anan.

3Da su na kusa da gidan Mika, sai suka gane karin harshen saurayin nan Balebiye. Sai suka tsaya suka tambaye shi, "Wa ya kawo ka nan? Me kake yi a nan wurin? Meyasa ka ke nan?"4Ya ce masu, "Ga abin da Mika ya yi mani: Ya ɗauki hayata in zama firist ɗin sa."
5Suka ce da shi, "Muna roƙon ka ka nemi shawara daga Allah, domin mu sani ko tafiyar nan da muke yi za ta yi nasara."6Sai firist ɗin ya ce masu, "Ku tafi cikin salama. Yahweh za ya bi da ku hanyar da zaku bi."
7Sai mutanen nan biyar suka tafi har suka isa Layish, sai suka iske mutanen na zaune lafiya, hakanan kuma Sidoniyawa suke zaune, babu abin da ya dame su a tsare suke. Babu wanda ya taɓa yin nasara da su ko kuma ya taɓa tsananta masu a ƙasar ko kaɗan. Suna zaune nesa da Sidoniyawa kuma ba su da wata hurɗa da kowa.8Suka dawo wurin kabilarsu a Zora da Eshtawol. 'Yan'uwansu suka tambaye su, "Mene ne rahotonku?"
9Suka ce, "Ku zo! Mu kai masu hari! Mun ga ƙasar kuma mai nagarta ce. Ba za kuyi wani abu ba? Kada ku yi jinkirin kai hari kuma ku ci ƙasar.10Idan ku ka je, za ku iske mutane waɗanda ke tunanin a tsare suke, kuma ƙasar na da fãɗi! Allah ya bayar da ita a gare ku - wurin da babu rashin komai a ƙasar."
11Mutane ɗari shida daga kabilar Dan, shirye da kayan yaƙi, suka fito daga Zora da Eshtawol.12Suka tafi su ka yi sansani a Kiriyat Yerayim, cikin Yahuda. Wannan ya sa mutane ke kiran wurin Mahane Dan har wa yau; yana yamma da Kiriyat Yerayim.
13Suka tafi daga wurin zuwa ƙasar tudu ta Ifraim sai suka zo gidan Mika.14Sai mutanen nan biyar da suka je gewayar ƙasar Layish suka ce da 'yan'uwansu, "Kun kuwa san cewa a cikin gidajen nan akwai falmarar haikali, da allolin gida, sassaƙaƙƙiyar siffa, da siffar ƙarfe da aka sarrafa? Yanzu ku yi shawarar abin da za ku yi."
15Sai suka juya daga nan suka shiga gidan saurayin nan Balebi, a gidan Mika, sai suka gaishe shi.16Daga nan Danawan nan ɗari shida, shirye da kayan yaƙi, suka tsaitsaya a ƙofar gidan.
17Mutanen nan biyar da suka je gewayar ƙasar suka shiga suka ɗauko sassaƙaƙƙiyar siffar, da falmarar haikalin, da allolin gida, da sarrafaffiyar siffar ƙarfen, lokacin da firist ɗin ke tsaye bakin ƙofar gidan tare da mutanen nan ɗari shidda da ke shirye da kayan yaƙi.18Da waɗannan suka shiga cikin gidan Mika suka ɗauko sassaƙaƙƙiyar siffar nan, da falmarar haikali, da allolin gida, da sarrafaffiyar siffar ƙarfen nan, sai firist ɗin ya ce masu, "Me ku ke yi?"
19Suka ce da shi, "Yi shiru! Ka sa hannunka a bakinka ka taho tare da mu, sai ka zama Uba da firist a gare mu. Wanne ne ya fi maka ka zama firist na gidan mutum ɗaya, ko kuwa ka zama firist na kabila da kuma ɗaya daga cikin zuriyar Isra'ila?"20Firist ɗin ya yi murna a zuciyarsa. Ya ɗauki falmarar haikalin, da allolin gidan, da sassaƙaƙƙiyar siffar, sai ya tafi tare da mutanen.
21Sai suka juya suka yi tafiyarsu. Suka sa ƙananan yaran a gabansu, da kuma shanun da dukkan mallakarsu.22Da suka yi 'yar tazara daga gidan Mika, sai aka kira mutanen da ke maƙwaftaka da gidan Mika suka tattaru, suka tafi suka tarar da Danawan.23Suka yi kururuwa ga Danawan, suka juya suka ce wa Mika, "Me ya sa ku ka tattaro kanku?"
24Ya ce, "Kun sãce allolin da na yi, kun ɗauke mani firist, kuma kun tafi. Me kuma ya rage mani? ya ya za ku yi mani tambaya, "Me ke damun ka?"25Mutanen Dan suka ce da shi, "Kada ka bari mu ji ka ce wani abu, ko kuwa wasu mutane masu fushi da ke nan wurin ransu ya ɓaci sosai su kai maka hari, kai da iyalinka kuma a kashe ku."26Sai mutanen Dan suka yi tafiyarsu. Da Mika ya ga cewa sun sha ƙarfinsa, sai ya juya ya koma gidansa.
27Mutanen Dan suka ɗauke abin da Mika ya sassaƙa, duk da firist ɗinsa, sai suka zo Layish, wurin mutanen da babu abin da ya dame su kuma cikin tsaro suka kashe su da takobi suka ƙone birnin.28Babu wanda yazo ya cece su domin sun yi nisa da Sidon, kuma ba su da wata hurɗa da wani. A kwari ne da ke kusa da Bet Rehob. Danawan suka sake gina birnin suka zauna a ciki.29Suka sa wa birnin suna Dan, bisa ga sunan Dan kakansu, wanda ya ke ɗaya daga cikin 'ya'yan Isra'ila. Amma dã sunan birnin Layish ne.
30Mutanen Dan suka kafa wa kansu sassaƙaƙƙiyar siffar nan. Yonatan ɗan Gashom, ɗan Musa, shi da 'ya'yansa maza suka zama firistocin kabilar Danawa har zuwa ranar tafiya ƙasar bauta.31Haka nan suka yi sujada ga sassaƙaƙƙiyar siffar Mika wanda ya sarrafa dukkan tsawon kwanakin da gidan Allah ya ke a Shilo.

19

1A waɗannan kwanaki, sa'ad da babu sarki a Isra'ila, akwai wani mutum, Balebi, ya yi zama na ɗan wani lokaci a wani ƙauye a ƙasar tudu ta Ifraim. Sai ya ɗauko wa kansa mace, kuyanga daga Betlehem cikin Yahuda.2Amma kuyangar tasa ta yi masa rashin aminci; sai ta bar shi ta koma gidan mahaifinta a Betlehem cikin Yahuda. Ta zauna a can watanni huɗu.

3Sai mijinta ya tashi ya tafi wurinta domin ya lallashe ta ta dawo. Baransa kuwa na tare da shi, da jakai guda biyu. Sai ta kawo shi cikin gidan mahaifinta. Da mahaifin yarinyar ya gan shi, sai ya yi murna.4Sai surukinsa, mahaifin yarinyar, ya lallashe shi ya zauna kwana uku. Suka ci su ka sha suka kwana a can.
5A rana ta huɗu suka tashi suka yi asubanci suka shirya domin su tafi, amma mahaifin yarinyar ya ce da surukinsa, "Ka ci ɗan abinci domin ka sami ƙarfi, daga nan sai ka tafi."6Sai su biyun suka zauna domin su ci su kuma sha tare. Daga nan mahaifin yariyar ya ce, "Ina roƙon ka ka yarda ka sãke kwana domin ka wartsake."
7Da Balebin ya tashi zai tafi, sai mahaifin yarinyar ya roƙe shi da ya tsaya, sai ya canza shirinsa ya sake kwana.8A rana ta biyar ya tashi ya yi asubanci domin ya tafi, amma mahaifin yarinyar ya ce, "Ka ƙarfafa kanka, ka jira sai rana tayi." Sai suka zauna su ka ci abinci su biyu.
9Da Balebin da kuyangarsa da baransa suka tashi za su tafi, sai surukinsa, mahaifin yarinyar ya ce da shi, "Duba, yanzu yamma ta ƙarato. Ina roƙonka ka tsaya ka sãke kwana, ka kuma wartsake. Kana iya yin asubanci gobe ka tashi ka koma gida."
10Amma Balebin ba ya so ya sake kwana. Sai ya tashi ya tafi. Ya yi tafiya ya fuskanci Yebus (wato Yerusalem). Yana da jakai biyu shiryayyu domin hawa - kuma kuyangarsa na tare da shi.11Da suka iso gaf da Yebus, rana ta kusa faɗuwa, sai baran ya ce wa maigidansa, "Ka zo, mu juya mu shiga birnin Yebusawa mu kwana a ciki."
12Sai ubangidansa yace masa, "Ba za mu juya mu shiga birnin bãre waɗanda ba na mutanen Isra'ila ba ne. Mu ci gaba da tafiya mu kai Gibiya."13Balebin ya ce wa bãransa, "Zo, mu tafi ɗaya daga cikin wuraren nan, mu kwana a can ko dai Gibiya ko kuma Ramah."
14Sai suka ci gaba da tafiya, rana kuwa ta faɗi da suka yi gaf da Gibiya, cikin yankin Benyamin.15Sai suka juya suka shiga domin su kwana a Gibiya. Sai suka je suka zauna a dandalin birnin, amma babu wanda ya kira su domin su kwana a gidansa.
16Amma sai ga wani mutum tsoho yana dawowa daga aikin gonarsa a yammacin nan. Shi kuwa mutumin ƙasar tudu ta Ifraim ne, amma ya na zama a Gibiya na ɗan wani lokaci. Amma mutanen da ke zama a wannan wuri Benyaminawa ne.17Ya ɗaga idanunsa sai ya ga matafiyin a dandalin birni. Tsohon ya ce, "Ina za ku? Daga ina ku ka fito?"
18Balebinn yace masa, "Mun fito ne daga Betlehem cikin Yahuda za mu wani ƙauyen ƙasar tudu ta Ifraim, wato inda na fito. Na je Betlehem cikin Yahuda, kuma za ni gidan Yahweh, amma babu wanda zai karɓe ni cikin gidansa.19Muna da harawa da abinci domin jakkanmu, akwai gurasa da ruwan inabi domina da wannan mace baiwarka a nan, da kuma wannan saurayin tare da barorinka. Ba mu rasa komai ba."
20Sai tsohon nan ya gaishe su, "Salama a gare ku! Zan biya dukkan buƙatunku. Kada dai ku kwana a dandali kawai."21Sai mutumin ya kawo Balebinn cikin gidansa ya kuma ba da abinci ga jakunansa. Suka wanke sawayensu suka ci suka sha.
22Lokacin da suke cikin annashuwa, sai waɗansu mutanen birnin, 'yan'iskan gari, suka zo suka kewaye gidan, suna bubbuga ƙofar. Suka yi wa tsohon nan magana, wato mai gidan, suna cewa, "Ka fito da mutumin nan da ya shigo cikin gidanka, domin mu yi luɗu da shi."23Mutumin nan, mai gidan, ya fita ya same su ya ce masu, "A 'a, 'yan'uwana, ina roƙon ku kada ku yi wannan irin mugun abu! Tun da wannan mutum baƙon gidana ne, kada ku yi wannan irin mugun abu!
24Duba, ɗiyata budurwa da kuma kuyangarsa ga su nan. Bari in fito da su yanzu. Ku yi masu fyaɗe ku kuma yi yadda kuka ga dama da su. Amma kada ku yi wannan irin mugun abu ga mutumin nan!"25Amma mutanen nan ba su saurare shi ba, sai mutumin nan ya fizgi kuyangarsa ya kuma fitar masu da ita. Suka fizge ta, suka yi mata fyaɗe, suka wulaƙanta ta dukkan tsawon dare, da asuba ta yi suka bar ta ta tafi.26Da asuba matar ta dawo sai ta faɗi a bakin ƙofar gidan mutumin inda maigidanta ya ke, sai ta yi kwance a nan har gari ya waye sarai.
27Maigidanta ya tashi da safe ya buɗe ƙofofin gidan ya fita domin ya kama hanyar tafiyarsa. Sai ya lura da kuyangarsa a kwance a bakin ƙofa, da hannuwanta bisa dankarin ƙofar.28Balebin ya ce mata, "Tashi. Mu tafi." Amma ba ta amsa ba. Sai ya ɗora ta bisa jaki, mutumin kuwa ya kama hanya zuwa gidansa.
29Sa'ad da Balebin nan ya iso gidansa, sai ya ɗauko wuƙa, ya kuma kama kunyangar tasa, ya daddatsa ta, ya yi mata gunduwa-gunduwa, ya kasa ta kashi goma sha biyu, sai ya aika da kashi-kashin nan ko'ina cikin dukkan ƙasar Isra'ila.30Dukkan waɗanda suka ga wannan abu suka ce, "Wannan irin abu bai taɓa faruwa ba ko aka taɓa ganinsa ba tun daga ranar da mutanen Isra'ila suka fito daga ƙasar Masar har ya zuwa wannan rana. Ku yi tunani akai! Ku bamu shawara! Ku gaya mana abin da za'a yi!"

20

1Daga nan dukkan mutanen Isra'ila suka fito a matsayin mutum guda, daga Dan har zuwa Biyasheba, duk da ƙasar Giliyad ma, suka tattaru tare a gaban Yahweh a Mizfa.2Shugabannin dukkan mutanen, da kuma dukkan kabilun Isra'ila, suka ɗauki wurarensu a cikin taron mutanen Allah - Mutane 400,000 a ƙasa, waɗanda ke a shirye domin su tafi su yi yaƙi da takobi.

3Mutanen Benyamin suka ji cewa mutanen Isra'ila sun haye zuwa Mizfa. Mutanen Isra'ila suka ce, "Gaya mana yadda wannan mugun abu ya faru."4Balebin mai gidan matar wadda aka kashe, ya amsa, "Na zo Gibiya ne wadda ke yankin Benyamin, ni da kuyangata, domin mu kwana.
5A cikin dare, shugabannin Gibiya suka kawo mani hari, suka kewaye gidan suna nema su kashe ni. Suka fizge kuyangata su a yi mata fyaɗe, sai kuwa ta mutu.6Na ɗauki kuyangata na datsa ta kashi-kashi, na kuma aika cikin kowanne lardin gãdon Isra'ila, saboda sun aikata wannan irin mugunta da hasala a cikin Isra'ila.7Yanzu, dukkan ku Isra'ilawa, sai ku ba da shawara ku kuma ɗauki mataki a nan."
8Dukkan mutanen suka tashi tsaye a matsayin mutum guda, suka ce, "Babu wani cikinmu da za ya koma rumfarsa, babu kuma wani cikinmu da zaya koma gidansa!9Amma dole yanzu ga abin da zamu yi wa Gibiya: Za mu kai mata hari bisa ga yadda ƙuri'a za ta bi da mu.
10Za mu ɗauki mutane goma cikin ɗari daga cikin dukkan kabilun Isra'ila, da kuma mutane ɗari cikin dubu, mutane dubu cikin dubu goma, su samo kayan masarufi domin waɗannan mutanen, domin idan suka zo Gibiya ta Benyamin, su ba su horo domin muguntar da suka aikata a Isra'ila."11Sai dukkan sojojin Isra'ila suka taru a matsayin mutum guda, domin yin tsayayya da birnin.
12Sai kabilun Isra'ila suka aika da mutane cikin dukkan kabilar Benyamin, suna cewa, "Wacce irin mugunta ce haka aka aikata a cikinku?13Saboda haka, ku ba mu waɗannan miyagun mutanen na Gibiya, domin mu kashe su, ta haka za mu cire wannan mugunta da ke cikin Isra'ila ɗungun." Amma Benyaminawa suka ƙi sauraron muryar 'yan'uwansu, mutanen Isra'ila.14Sai mutanen Benyamin suka fito daga cikin biranensu suka tattaru a Gibiya domin su yi shirin yin yaƙi da mutanen Isra'ila.
15Mutanen Benyamin suka tattaro mutane daga cikin biranensu a wannan rana sojoji dubu ashirin da shida horarru wajen faɗa da takobi. Bugu da ƙari, akwai mutane ɗari bakwai zaɓaɓɓu daga cikin mazauna a Gibiya.16Daga cikin waɗannan sojoji dukka akwai mutane ɗari bakwai zaɓaɓɓu waɗanda su bahagwai ne. Kowannen su za ya iya wurga dutse ga gashin kai ba tare da yin kuskure ba.
17Mutanen Isra'ila, ba tare da lissafin mutanen Benyamin ba, su mutum dubu ɗari huɗu ne, waɗanda kuma horarru ne wajen faɗa da takobi. Dukka waɗannan mutanen yaƙi ne.18Mutanen Isra'ila suka tashi, suka hau zuwa Betel, suka tambayi shawara daga wurin Allah. Suka yi tambaya,"Wane ne za ya fara kai wa mutanen Benyamin hari domin mu?" Yahweh yace, "Yahuda ne za ya fara kai hari."
19Mutanen Isra'ila suka tashi da sassafe suka matsa da sansaninsu kusa da Gibiya.20Mutanen Isra'ila suka tafi yin yaƙi da Benyamin. Suka tashi suka yi jeren yaƙi da Gibiya.21Mutanen Benyamin suka fito daga cikin Gibiya, suka kashe mutum dubu ashirin da biyu na sojojin Isra'ila a wannan rana.
22Amma mutanen Isra'ila suka ƙarfafa kansu suka sãke kafa layin yaƙi dai-dai wurin da suka jera a rana ta farko.23Sai mutanen Isra'ila suka haye suka yi kuka a gaban Yahweh har zuwa yamma, suka kuma nemi bishewa daga wurin Yahweh. Suka ce, "Mu kuma sãke tafiya mu yi yaƙi da 'yan'uwanmu, mutanen Benyamin?" Yahweh yace, "Ku kai masu hari!"
24Sai mutanen Isra'ila suka kai hari ga sojojin Benyamin a rana ta biyu.25A rana ta biyu, Benyamin ya fito daga Gibiya suka kuma kashe mutum dubu sha takwas daga cikin mutanen Isra'ila. Dukkan su horarru ne wajen faɗa da takobi.
26Daga nan dukkan sojojin Isra'ila da dukkan mutanen Isra'ila suka tashi su ka haye zuwa Betel suka yi kuka, a nan suka zauna a gaban Yahweh suka yi azumi a wannan rana har zuwa yamma suka miƙa baye-baye na ƙonawa da baye-baye na salama a gaban Yahweh.
27Mutanen Isra'ila su ka tambayi Yahweh - domin akwatin alƙawari na Allah na nan a waɗannan kwanaki,28a sa'annan Fenihas, ɗan Eliyeza ɗan Haruna, yana hidima a gaban akwatin a waɗannan kwanaki - "Mu sake tafiya mu yaƙi mutanen Benyamin, 'yan'uwanmu, ko mu tsaya?" Yahweh yace, "Ku kai hari, gama gobe zan taimake ku ku yi nasara da su."
29Sai Isra'ila suka sa mutane suka kewaye Gibiya gaba ɗaya a asirce.30Mutanen Isra'ila suka yi yaƙi da mutanen Benyamin a rana ta uku, suka kafa layin yaƙi da Gibiya kamar yadda suka yi a dã.
31Mutanen Benyamin suka fita suka yi yaƙi da mutanen, har suka fita suka yi nisa da birnin. Suka fara kashe wasu daga cikin mutanen. Wajen mutane talatin na Isra'ila suka mutu cikin gonaki da bisa hanyoyi.‌ Ɗaya daga cikin hanyoyin ta hawa zuwa Betel ce, ɗayar kuma ta tafi zuwa Gibiya.
32Sai mutanen Benyamin suka ce, "An kãshe su gashi nan suna guduwa daga gare mu, kamar yadda ya faru da farko." Amma sojojin Isra'ila suka ce, "Mu gudu baya domin mu janye su daga cikin birnin zuwa bisa hanyoyi."33Dukkan mutanen Isra'ila kuwa suka fito daga wurarensu suka jera kansu layi-layi domin yaƙi a Ba'al Tama. Sai sojojin Isra'ila waɗanda ke ɓoye a asirtattun wurare suka fito da gudu daga wurarensu daga Ma'are Gibiya.
34Sai ga shi an fito wa Gibiya da yaƙi mutane dubu goma daga cikin dukkan Isra'ila, yaƙi kuwa ya yi zafi, amma mutanen Benyamin ba su san bala'i na gaf da su ba.35Sai Yahweh ya kayar da Benyamin a gaban Isra'ila. A wannan rana, sojojin Isra'ila suka kashe mutum 25,100 na Benyamin. Dukkan waɗanda suka mutu horarru ne wajen faɗa da takobi.
36Sai sojojin Benyamin suka ga cewa an kayar da su. Mutanen Isra'ila kuwa sun ba Benyamin sarari, sabo da suna la'akari da mutanen da ke ɓoye a kewaye da Gibiya.37Sai mutanen da ke a ɓoye suka tashi da sauri suka auka cikin Gibiya, da takubbansu kuwa suka kashe duk wanda ke zaune a cikin birnin.38Alamar da aka shirya tsakanin sojojin Isra'ila da mutanen da ke ɓoye a asirtattun wurare shi ne za su ga girgijen hayaƙi ya turniƙe yana fitowa daga birnin.
39Idan aka aika da alamar sojojin Isra'ila za su juya daga yaƙin. To Benyamin ya fara kai hari har sun kashe mutane wajen talatin na Isra'ila, sai suka ce, "babu shakka an kayar da su a gabanmu, kamar a yaƙin farko."
40Amma da tuƙuƙin hayaƙi ya fara tashi sama daga cikin birnin, mutanen Benyamin kuwa suka juya suka ga hayaƙi na tashi daga cikin dukkan birnin har zuwa sararin sama.41Sai kuwa mutanen Isra'ila suka juyo kansu. Mutanen Benyamin suka tsorata, domin sun ga bala'in da ya afko masu.
42Sai suka gudu daga wurin mutanen Isra'ila, suna tserewa hanyar zuwa jeji. Amma yaƙin ya ci ƙarfinsu. Sojojin Isra'ila suka fito daga birane suka kuwa karkashe su a inda suke tsaye.
43Suka kewaye mutanen Benyamin, su a kora su, suka tattake su a Noha, har ya zuwa gabashin Gibiya.44Daga kabilar Benyamin, mutane dubu goma sha takwas suka mutu, dukkan su mutane ne ƙwararru a yaƙi.
45Suka juya suka sheƙa da gudu zuwa jeji zuwa dutsen Rimon. Isra'ilawa suka ƙara kashe mutane dubu biyar a kan hanyoyi. Suka ci gaba da bin su, suna binsu ƙut da ƙut har zuwa Gidom, suka kuma ƙara kashe dubu biyu a can.46Dukkan sojojin Benyamin da suka fãɗi a wannan rana mutane dubu ashirin da biyar ne - horarrun mutane wajen faɗa da takobi, dukkan su ƙwararru ne a wajen yaƙi.
47Amma mutane ɗari shida suka juya suka gudu zuwa jeji, zuwa dutsen Rimon. Suka yi wata huɗu suna zama a dutsen Rimon.48Sojojin Isra'ila suka juya su ka fãɗa wa mutanen Benyamin suka hare su suka kashe birnin gaba ɗaya, da shanu dukka, da dukkan abin da suka iske. Suka kuma ƙone duk wani gari da suka iske a hanyarsu.

21

1Daga nan mutanen Isra'ila suka ɗauki alƙawari a Mizfa, "Babu wani cikin mu da zai bada ɗiyarsa aure ga Benyamine."2Sai mutanen suka haye zuwa Betel suka zauna can a gaban Allah har yamma, da muryoyi masu ƙarfi suka yi kuka mai zafi.3Suka yi kira, "Meyasa, Yahweh, Allah na Isra'ila, wannan irin abu ya faru da Isra'ila, cewa a yau ɗaya daga cikin kabilunmu ya ɓace?"

4Washegari mutanen suka tashi da sassafe suka gina bagadi suka miƙa baiko na ƙonawa da na salama.5Mutanen Isra'ila suka ce, "Daga cikin kabilun Isra'ila dukka wane ne bai fito taron Yahweh ba?" Gama sun riga sun ɗauki alƙawari mai muhimmanci game da duk wanda bai zo wurin Yahweh ba a Mizfa. Suka ce, "Babu shakka za a kashe shi."
6Sai mutanen Isra'ila suka ji tausayin ɗan'uwansu Benyamin. Suka ce, "A yau an datse kabila ɗaya daga cikin Isra'ila.7Wane ne za ya bada matayen aure ga waɗanda suka rage, tun da mun riga mun yi alƙawari ga Yahweh cewa babu wanda za ya bar wani daga cikin su ya auri 'ya'yanmu mata?"
8Suka ce, "Wace ce cikin kabilun Isra'ila ba ta zo wurin Yahweh ba a Mizfa?" Sai aka iske cewa babu wanda yazo taron daga Yabish Giliyad.9Domin da aka sa mutane suka tsaya jeri-jeri, duba, babu ko ɗaya daga cikin mazaunan Yabish Giliyad da ya kasance.10Sai taron suka aika da jarumawansu mutum dubu sha biyu da umarnin cewa su je Yabish Giliyad su kai masu hari, su kuma kashe su, har ma da mata da 'ya'ya.
11"Haka za ku yi: dole ne ku kashe kowanne namiji da kowace mace da ta san namiji."12Mutanen suka samo daga cikin mazauna Yabish Giliyad 'yanmata ɗari huɗu waɗanda ba su taɓa sanin namiji ba, suka kawo su sansani a Shilo, cikin Kan'ana.
13Taron ga baki ɗaya suka aika da saƙo ga mutanen Benyamin da ke a dutsen Rimon su na cewa muna neman ku da salama.14Mutanen Benyamin suka dawo a wannan lokacin kuma suka basu matan Yabish Giliyad, amma kuma matan basu isa kowannen su ya samu ba.15Mutanen suka yi juyayin abin da ya faru da Benyamin, saboda Yahweh ya sa rarrabuwa a tsakanin kabilun Isra'ila.
16Sai shugabannin taron suka ce, "Yaya za mu shirya wa mutanen Benyamin da suka rage matan aure, tun da an kashe matayen Benyamin?"17Sai suka ce, "Dole ne a sami gãdo domin waɗanda suka tsira a Benyamin, domin ka da kabila ɗaya ta lalace a Isra'ila.
18Ba za mu iya ba su matan aure daga cikin 'ya'yanmu mata ba, gama mutanen Isra'ila sun yi alƙawari, 'La'ananne ne wanda ya ba da mace ga Benyamin.'"19Sai suka ce, "Kun san akwai bikin idin Yahweh kowacce shekara a Shilo (wadda ke arewa da Betel, gabas da hanyar da ke tafiya daga Betel zuwa Shekem, a kudacin Lebona)."
20Sai suka yi wa mutanen Benyamin umarni, suka ce, "Ku je ku ɓoye a asirce ku yi kwanto cikin garkar inabi.21Ku lura da lokacin da 'yanmata daga Shilo za su fito rawa, sai ku hanzarto daga garkar inabin kowanen ku ya kama wa kansa mata daga cikin 'yanmatan Shilo, daga nan ku koma ƙasar Benyamin.
22Idan ubanninsu ko 'yan'uwasu maza suka zo domin su yi mana tawaye, za mu ce masu, 'Ku yi mana tagomashi, ku bar su su zauna saboda ba mu samarwa dukkansu matan aure ba a lokacin yaƙin. Ba ku da laifi, tun da ba ku bayar da 'ya'yanku mata ba a gare su.'"
23Mutanen Benyamin suka yi yadda aka ce. Suka ɗauki iya matan auren da suke bukata daga cikin 'yan'matan da ke rawa sai su da ke raka kwashe su suka tafi da su su zama matansu. Suka koma wurin gãdonsu. Suka sake gina garuruwansu suka zauna a ciki.24Daga nan mutanen Isra'ila suka bar wurin suka koma gida, kowanensu ya koma cikin kabilarsa da zuriyarsa, kowanensu kuma ga gãdonsa.
25A cikin waɗannan kwanaki babu sarki a Isra'ila. Kowa yana yin abin da ya ga ya yi dai-dai a idanunsa.

Littafin rut

1

1Ya kasance a kwanakin da alƙalai ke mulki, sai a ka yi yunwa a cikin ƙasar, sai kuma wani mutumin Betlehem ta Yahuda ya tafi ƙasar Mowab tare da matarsa da 'ya'yansa maza guda biyu.2Sunan mutumin Elimelek, sunan matarsa kuma Na'omi. Sunayen 'ya'yansa biyu kuwa su ne Mahlon da Kiliyon, su Ifratawa ta Betlehem ta Yahuda ne, sai suka je ƙasar Mowab suka zauna a can.

3Ana nan sai Elimelek mijin Na'omi ya mutu a ka bar ta da 'ya'yanta maza biyu.4Waɗannan 'ya'ya maza suka yi aure da 'yan matan Mowabawa guda biyu, sunayensu kuwa shi ne Orfa da Rut sun zauna a can har kusan shekaru goma.5A na nan sai Mahlon da Kiliyon suka mutu, aka bar Na'omi ba miji ba 'ya'yanta guda biyu.
6Daga nan sai Na'omi ta yanke shawara ta bar Mowab tare da matan 'ya'yanta zuwa Yahuda saboda ta ji cewa Yahweh ya taimaki mutanensa da ke cikin buƙata ya kuma basu abinci.7Saboda haka sai ta bar wurin da take tare da surukanta biyu, suka kama hanya don su koma ƙasar Yahuda.
8Sai Na'omi ta ce da surukanta biyu "Kowaccenku ta koma gidan iyayenta. Dama Yahweh ya yi mu ku jinkai, kamar yadda ku ka nuna jinkai gare ni da kuma mamatan.9Dama Ubangiji ya ba ku hutu a gidan mazanku da za ku aura. "Sai ta sunbace su sai suka tada murya suka yi kuka.10Sai suka ce da ita "A'a za mu koma wurin mutanenki tare da ke".
11Amma Na'omi ta ce, "ku koma, 'ya'yana! Don me za ku tafi tare da ni? Har yanzu ina da sauran 'ya'ya maza a cikina dominku, da za su aure ku?12Haba 'ya'yana ku koma, don na tsufa sosai har da zan yi aure, Ko da ma ace ina begen yin aure yanzu, in haifi 'ya'ya maza,13Za ku jira har su yi girma? Za ku yi ta jira ba za ku yi aure yanzu ba? A'a 'ya'yana! Hakika ina cike da baƙin ciki sosai, fiye da na ku bakin cikin, Don Yahweh ya juya mani baya."
14Sai surukanta su ka sake ɗaga murya su ka ɓarke da kuka. Sai Orfa ta sumbaci surukarta suka yi ban kwana, amma Rut ta manne mata.15Na'omi ta ce, kin ga 'yar'uwarki ta koma wurin mutanenta da kuma allolinta. Ki koma tare da 'yar'uwarki."
16Amma Rut ta ce, "Kar ki sa in rabu da ke, don inda za ki can za ni; inda kika zauna nan zan zauna, mutanenki za su zama mutanena, kuma Allahnki zai zama Allahna.17Inda ki ka mutu can zan mutu, a binne ni a can. Yahweh ya hukunta ni fiye da haka, idan har wani abu in ba mutuwa ba ya raba mu."18Sa'adda Na'omi ta ga Rut ta ƙudurta ta bi ta, sai ta dena gardama da ita.
19Sai su biyun su ka yi tafiya har garin Betlehem. Bayan sun zo sai duk garin ya cika da murna saboda su, Sai mataye suka ce "Na'omi ce wannan?"20Amma ta ce da su "Kada ku kira ni Na'omi. Ku kira ni mai baƙinciki, don Mai Iko Dukka ya azabtar da ni.21Na fita a wadace, amma Yahweh ya sake dawo da ni gida hannu wofi. To don me ku ke kira na Na'omi, da ya ke Yahweh ya yashe ni, Mai iko dukka ya wahalshe ni?"
22To Na'omi da surukarta Rut 'Yar Mowabawa su ka komo daga ƙasar Mowab. Suka zo Betlehem a farkon kakar bali.

2

1Mijin Na'omi Elimelek ya na da ɗan'uwa mai suna Bo'aza, shi mawadaci ne, sananne.2Sai Rut 'yar Mowabawa ta ce da Na'omi, "Yanzu ki bar ni in je in yi kalar abin da ya ragu a gonakin hatsi. Zan bi duk wanda na sami tagomashi a wurinsa". Sai Na'omi ta ce da ita, '"Yata, ki je."

3Sai Rut ta tafi ta yi kalar abin da ya ragu a gonaki bayan sun yi girbi, Sai ta je yankin gonar Bo'aza, wanda ɗan'uwa ne ga Elimelek.4Sai Bo'aza ya zo daga Betlehem ya ce da masu girbin, "Yahweh ya kasance tare da ku" Suka amsa masa, "Yahweh ya albarkace ka."
5Sai Bo'aza ya ce wa barorinsa da ke kula da masu girbin, "Wannan yarinyar ɗiyar wanene?"6Baran da ke kula da masu girbin ya amsa, "Yar Mowabawa ce da ta zo tare da Na'omi daga ƙasar Mowab.7Ta ce da ni, "Ina roƙon ka bar ni in yi kalar abin da ya rage a gonar bayan masu girbin sun girbe hatsin. Sai ta zo nan tun da safe har yanzu, sai dai ɗan shaƙatawa da ta yi a gida"
8Daga nan sai Bo'aza ya ce da Rut, 'Yata ki na ji na? Kada ki bar gonata ki je wata gona don ki yi kala, amma ki tsaya nan ki yi aiki tare da barorina mata da ke aiki.9Ki zuba idonki kawai a inda masu girbin ke girbi ki na bin bayan sauran matan. Ashe ban umarci mazan da kada su taɓa ki ba? Duk lokacin da ki ka ji ƙishi sai ki je wurin tulunan ruwa ki sha ruwan da mazan su ka ɗebo."
10Daga nan sai ta sunkuyar da kanta har ƙasa a gaban Bo'aza. Ta ce, 'Ta yaya na sami tagomashi a gabanka, har da zaka kula da ni, ni da nake baƙuwa?"11Bo'aza ya amsa ya ce da ita, an labarta mini duk abin da ki ka yi tun lokacin da mijinki ya mutu, kin bar babanki, da kuma ƙasarki, ki ka biyo surukarki, ki ka zo wirin mutanen da ba ki sani ba.12Yahweh ya ba ki lada kan abin da ki ka yi, dama ki sami cikkaken lada daga Yahweh, Allah na Isra'ila, wanda ki ka sami mafaka a gare shi."
13Sai ta ce, "Bari in sami tagomashi a gareka, shugabana, don ka ta'azzantar da ni, ka yi mani maganar kirki, ko da ya ke ni ba ɗaya daga cikin barorinka mata ba ce."
14A lokacin cin abinci sai Bo'aza ya ce da Rut "Zo nan ki ci wani abinci, ki kuma sa gutsuranki a cikin kunu." Sai ta zauna a gefen masu girbin, sai ya ba ta wani gasasshen hatsi. Ta ci har sai da ta ƙoshi ta bar sauransa.
15Da ta tashi za ta yi kala sai Bo'aza ya ce da ma'aikatansa, "Ku barta ta yi kala har ma daga cikin dammunan, kada ku hana ta.16kuma ku dinga zarar ma ta zangarkun hatsin daga dammuna, ku bar ma ta ta tara ka da ku tsauta ma ta."
17To sai ta yi ta kala a gonar har yamma. Daganan ta sussuke zangarkun hatsin ta sami kusan garwa biyu na bali.18Sai ta ɗauka ta tafi gari. Sai surukarta ta ga abin da ta samo. Rut kuma ta zo mata da soyayyen hatsin da ta ci ta rage sai ta bata.
19Surukarta ta ce da ita, "Ina ki ka je kala yau? Ina ki ka je aiki yau? Dama mutumin da ya taimake ki ya sami albarka". Sai Rut ta faɗawa surukarta labarin mutumin da ya ke da gonar da kuma inda ta yi aiki. Ta ce "Sunan mutumin da na yi aiki a gonarsa Bo'aza"20Na'omi ta ce da surukarta Yahweh ya albarkace shi, wanda bai dena nuna amincinsa ga rayayyu da matattu ba." Na'omi ta ce wannan mutumin danginmune na kusa mai kuma fansarmu."
21Rut mutumiyar Mowab ta ce, "Hakika, ya ce mani, "Ki dinga bin bayan ma'aikatana har sai sun gama girbin dukkan amfanin".22Sai Na'omi ta ce da Rut surukarta, '"Yata ya fi kyau da kike tafiya tare da ma'aikatansa 'yanmata, don ka da ki je wata gonar ki cutu."
23To sai ta tsaya kusa da ma'aikatan Bo'aza 'yanmata don ta dinga kala har ya zuwa karshen kakar bali, don haka sai ta zauna tare da surukarta.

3

1Surukarta, Naomi ta ce ma ta, '"Yata "Ba sai in samar miki wurin da za ki huta ba, don komai ya zamar miki dai-dai?2To yanzu shi Bo'aza da ki ke aiki tare da ma'aikantansa mata ba danginmu ba ne? Kin ga zai je shikar bali yau a masussuka.

3Don haka, sai ki yi wanka ki yi kwalliya, ki sa tufafinki mafi kyau, ki tafi masussukar. Amma kada ki yarda ya gan ki har sai ya gama ci da sha.4Amma bayan ya kwanta, sai ki kula da inda ya kwanta don in an jima ki je wurinsa, ki yaye mayafinsa, ki kwanta a ƙafafunsa. Daga nan zai faɗa miki abin da za ki yi"5Rut ta ce wa Na'omi, "Zan yi duk abin da ki ka ce."
6To sai ta tashi ta tafi masussukar, ta kuma bi umarnin surukarta.7Bayan Bo'aza ya ci ya sha zuciyarsa na annashuwa, sai ya je don ya kwanta a ƙarshen tarin hatsinsa. Daga nan sai ta lallaɓa ta yaye ƙafafunsa, ta kwanta.
8Can wajen tsakar dare bayan mutumin ya farka, sai ya juya kawai sai ya ji mace kwance a ƙafafunsa!9Ya ce, "Ke wacece?". Ta ce, "Ni ce Rut baiwarka. Gama kai danginmune na kusa, sai ka bude mayafinka ka rufe ni."
10Bo'aza ya ce '"Yata, Yahweh ya sa miki albarka. Yanzu a ƙarshe kin nuna kirki fiye da na farko, saboda ba ki je wurin matasa, ko matalauta, ko mawadata ba.11Yanzu, 'yata, ka da ki ji tsoro! Zan yi miki duk abin da ki ka ce, don duk mutanen garin nan sun san ke mace ce da ta can-canta.
12Gaskiya ne ni dangi ne, amma akwai ɗan'uwan da ya fi kusa da ku fiye da ni.13Yanzu sai ki tsaya nan, da safe kuma in zai cika hakin ɗan'uwa a kanki to ya yi dai-dai, sai ya cika, Amma idan ba zai cika hakin ɗan'uwa ba to ni zan cika hakin ɗan'uwa a kanki, na rantse da Yahweh. Ki kwanta har sai da safe."
14To sai ta kwanta a ƙafafunsa har sai da gari ya waye. Amma ta tashi tun kamin a fara gane mutane da sassafe. Don Bo'aza ya ce, "Don ka da a san cewa mace ta zo massusukar"15Bo'aza ya ce, "Kawo gyalenki ki shimfiɗa." Bayan ta yi haka, sai ya auna ma ta bali tiya shida a ciki ya dora ma ta. Daga nan sai ya tafi gari.
16Bayan Rut ta dawo wurin surukarta sai ta ce, "Yaya ki ka yi ɗiyata?." Rut ta faɗa ma ta duk abin da mutumin ya yi ma ta.17Ta ce, "Wannan tiya shida ta bali shi ne ya ba ni, don ya ce, "Kada ki koma wurin surukarki ba tare da komai ba".18Sai Na'omi ta ce, "Yata ki zauna a nan, har sai kin san yadda al'amarin zai zama, don mutumin ba zai huta ba har sai ya gama wannan al'amarin yau."

4

1To sai Bo'aza ya tashi ya tafi ƙofar gari ya zauna a can. Ba da jimawa ba, sai ga wani daga cikin dangin Na'omi na kusa wanda Bo'aza ya yi maganarsa ya zo zai wuce. Bo'aza yace da shi. "Abokina, zo nan ka zauna." Sai mutumin ya zo ya zauna.2Sai Bo'aza ya kira dattawan garin guda goma ya ce, "Ku zauna nan." Sai suka zauna.

3Bo'aza yace da ɗan'uwan na kusa, "Na'omi, da ta dawo daga ƙasar Mowab, za ta sayar da wata gonar ɗa'uwanmu Elimelek.4Na yi tunanin in sanar da kai in kuma yi maka magana, 'ka saye ta a gaban waɗanda ke zaune tare da mu a nan, da a gaban dattawan mutanena, In har kana so ka fanshe ta. Amma in ba ka so ka fansa sai ka faɗa mani don in sani, don ba wanda ya dace ya fanshe ta daga kai sai ni a bayanka. "Sai mutumin ya ce zan fanshe ta."
5Sai Bo'aza yace "A ranar da ka sayi gonar daga hannun Na'omi, dole ne kuma ka haɗa da Rut 'yar Mowabawa, matar marigayin, don a tada sunan marigayin akan gãdonsa."6Sai wannan ɗan'uwan na kusa ya ce ba zan iya fansar ta don kaina ba, ba tare da ɓata nawa gãdon ba. Ka ɗauki tawa damar ta fansar don kanka, don ba zan iya fansar ta ba."
7To wannan ita ce al'adar Isra'ila a waɗancan kwanakin akan al'amuran fansa da kuma canjin kayayyaki. Don a tabbatar da komai, sai mutum ya cire takalminsa ƙafa ɗaya ya ba maƙwabcinsa, haka ake yin yarjejeniyar da ta dace a Isra'ila.8To sai ɗan'uwan mafi kusa ya ce da Bo'aza, "Ka saye ta don kanka," sai ya tuɓe takalminsa.
9Daga nan sai Bo'aza yace da dattawan da dukkan jama'ar, "Ku ne shaidu cewa yau na saye dukkan mallakar Elimelek, da duk abin da ke na Kiliyon da Mahlon daga hannun Na'omi.10Bugu da ƙari game da Rut ɗiyar Mowab, matar Mahlon; ita ma na mallake ta ta zama matata, don in tãda sunan marigayin a kan gãdonsa, don in kafa ma sa zuriya, don kada a yanke sunansa daga cikin 'yan'uwansa da kuma gidansa. Yau ku ne shaidu."
11Dukkan mutanen da ke ƙofar da dattawan su ka ce, "Mu shaidune. Dãma Yahweh ya sa matar da ta zo gidanka ta zama kamar Rahila da Lai'atu, su biyu da su ka kafa gidan Isra'ila; kuma dãma ka azurta a Ifarata ka kuma yi suna a Betlehem12Dãma gidanka ya zama kamar na Ferez wanda Tamar ta haifawa Yahuda, Ta wurin zuriyar da Yahweh zai ba ka tare da wannan matashiyar mata."
13Sai Bo'aza ya ɗauki Rut, daga nan ta zama matarsa. Sai ya kwana da ita, sai Yahweh ya sa ta yi ciki, sai ta haifi ɗa namiji.14Sai mataye su ka ce da Na'omi, "Albarka ta tabbata ga Yahweh, wanda bai bar ki yau ba ɗan'uwa na kusa ba, wannan yaron. Dãma ya zama sanannen mutum a Isra'ila.15Dãma ya zama mai dawo maki da rayuwa ya kuma inganta kwanakinki na tsufa, saboda wannan surukar ta ki, wadda ta ƙaunace ki, wadda ta fi 'ya'ya bakwai maza a gare ki, ce ta haife shi."
16Na'omi ta ɗauki ɗan, ta rungume shi a kafaɗarta, ta kuma kula da shi.17Mataye maƙwabta su ka ba shi suna cewa, "An haifawa Na'omi ɗa," Sai suka raɗa masa suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, wanda ya haifi Dauda.
18To waɗanan su ne zuriyar Ferez: Ferez ya haifi Hezron,19Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,20Aminadab ya haifi Nahshon, Nahshon ya haifi Salmon,21Salmon ya haifi Bo'aza, Bo'aza ya haifi Obed,22Obed ya haifi Yesse, Yesse ya haifi Dauda.

Littafin sama'ila na farko

1

1Akwai wani mutumin Ramatayim ta Zufiyawa, ta ƙasar tudu na Ifraim; Sunansa Elkana ɗan Yeroham ɗan Elihu ɗan Tohu ɗan Zuf, Ifraimiye.2Yana da mata biyu; Sunan ta farkon Hannatu, sunan ta biyun kuma Fenina. Fenina na da 'ya'ya, amma Hannatu ba ta da ko ɗaya.

3Wannan mutum yakan fita daga birninsa shekara bayan shekara domin ya yi sujada ya kuma yi hadaya ga Yahweh mai runduna a Shilo. 'Ya'yan Eli maza guda biyu, Hofni da Finehas, firistocin Yahweh, suna wurin.4Idan ranar ta zo wadda Elkana ke yin hadaya ko wace shekara, koyaushe yakan ba Fenina matarsa kason nama mai yawa, da dukkan 'ya'yan ta maza da mata.
5Amma ga Hannatu a koyaushe yakan ba ta kaso ruɓi biyu, gama yana ƙaunarta, koda ya ke Yahweh ya rufe mahaifarta.6Kishiyarta kuma na tsokanar ta ƙwarai da gaske domin ta tunzura ta, saboda Yahweh ya rufe mahaifarta.
7Domin haka shekara bayan shekara, idan ta tafi gidan Yahweh tare da iyalinta, kishiyarta a koyaushe tana tsokanar ta. Saboda haka takan yi kuka ta ƙi cin komai.8Elkana mijinta a koyaushe sai ya ce mata, "Hannatu, me yasa ki ke kuka? Me yasa ba za ki ci komai ba? Me yasa zuciyarki ta ɓaci? Ban fi 'ya'ya maza goma ba a gareki?"
9A ɗaya daga cikin irin wannan tattaruwar, sai Hannatu ta tashi bayan da suka gama ci da sha a Shilo. Yanzu dai Eli firist yana zaune a bisa mazauninsa a ƙofar hanyar zuwa shiga Haikalin Yahweh.10Tana cikin ɓacin rai mai zurfi; ta yi addu'a ga Yahweh ta kuma yi kuka mai ɗaci.
11Sai ta yi wa'adi ta ce, "Yahweh mai runduna, idan za ka dubi azabar baiwarka ka kuma tuna da ni, ba za ka kuma manta da baiwarka ba, amma za ka ba baiwarka ɗa namiji, daga nan zan ba da shi ga Yahweh dukkan kwanakin ransa, ba bu kuma wata aska da za ta taɓa kansa ko kaɗan."
12Yayin da ta ci gaba da addu'a a gaban Yahweh, Sai Eli ya lura da bakinta.13Hannatu ta yi magana a zuciyarta. Leɓunanta na motsawa, amma ba a jin muryarta. Sai Eli ya yi tunanin ta bugu ne.14Eli ya ce mata, "Har yaushe za ki zama cikin buguwa? ki kawar da ruwan inabinki."
15Hannatu ta amsa, "A a, shugabana, ni mace ce mai ruhu cike da baƙinciki. Ban sha ruwan inabi ba ko abin sha mai ƙarfi, amma ina kwarara rai na ne a gaban Yahweh.16Kada ka ɗauki baiwar ka a matsayin mace marar kunya; Ina magana ne daga cikin yalwar damuwata da tsokanata."
17Daga nan Eli ya amsa ya ce, "Tafi cikin salama; bari Allah na Isra'ila ya ba ki abin nan da ki ka roƙe shi."18Ta ce, "Bari baiwarka ta sami tagomashi a gaban ka." Daga nan matar ta yi tafiyarta ta kuma ci abinci; fuskarta kuma ba ta sake nuna baƙinciki ba.
19Suka tashi da sassafe suka kuma yi sujada a gaban Yahweh, daga nan kuma suka sake komawa gidansu a Rama. Elkana ya kwana da Hannatu matarsa, Yahweh kuma ya tuna da ita.20Da lokacin ya zo, Hannatu ta ɗauki ciki ta haifi ɗa namiji. Ta kira sunansa Sama'ila, tana cewa, "Saboda na roƙo shi daga Yahweh."
21Sa'an nan kuma, Elkana da dukkan gidansa suka tafi domin su miƙa wa Yahweh hadaya ta shekara - shekara ya kuma biya wa'adinsa.22Amma Hannatu ba ta tafi ba; ta riga ta faɗa wa mijinta, "Ba zan tafi ba sai an yaye yaron; daga nan zan kawo shi, domin ya kasance gaban Yahweh ya kuma zauna wurin har abada."23Elkana mijinta ya ce da ita, "Ki yi abin da ya yi dai-dai a gare ki. Ki jira sai kin yaye shi; Yahweh ya tabbatar da maganarsa, kaɗai." Sai matar ta jira ta kuma yi renon ɗanta har sai da ta yaye shi.
24Da ta yaye shi, sai ta ɗauke shi tare da ita, tare da sã ɗan shekara uku, da gari mudu ɗaya, da kwalbar ruwan inabi ɗaya, ta kawo shi kuma gidan Yahweh a Shilo. To har yanzu dai yaron ƙarami ne.25Suka yanka sãn, suka kuma kawo yaron wurin Eli.
26Ta ce, "Ya, shugabana! muddin ka na raye, shugabana, ni ce matar nan da ta tsaya kusa da kai tana addu'a ga Yahweh.27Domin wannan yaron na yi addu'a kuma Yahweh ya ba ni abin da na roƙa daga gare shi.28Na bayar da shi ga Yahweh, dukkan tsawon ransa an ba da shi rance ga Yahweh." Daga nan ya yi sujada ga Yahweh a wurin.

2

1Hannatu ta yi addu'a ta ce, "Zuciyata ta ɗaukaka Yahweh. ‌Ƙahona ya ɗaukaka cikin Yahweh. Bakina ya yi kuri mai yawa akan maƙiyana, saboda na yi farinciki cikin cetonka.

2Babu wani mai tsarki kamar Yahweh, Gama babu wani baya gare ka; babu wani dutse kamar Allahnmu.
3Kada a ƙara kuri cikin matuƙar girman kai; kada wata gadara ta fito daga bakinku. Gama Yahweh Allah ne masani; shi ne ke gwada ayyuka.4Bakan mutane masu ƙarfi ya karye, amma waɗanda suka yi tuntuɓe suka sanya ƙarfi kamar ɗamara.
5Waɗanda suke a cike sun bayar da kansu haya domin gurasa; waɗanda suke jin yunwa sun daina jin yunwa. Bakarariya mata haifi bakwai, amma mace mai 'ya'ya da yawa ta yi yaushi.
6Yahweh na kashewa kuma ya rayar. Yana korawa ƙasa zuwa lahira yana kuma ɗagawa sama.7Yahweh yana maida wasu mutane talakawa wasu kuma masu arziki. Yana ƙasƙantarwa yana kuma ɗaukakawa sama.
8Yana ɗaga talaka daga turɓaya. Yana ɗaukaka mabuƙaci daga tarin toka ya sa ya zauna tare da sarakuna ya kuma sa ya gaji wurin zama mai daraja. Gama ginshiƙan duniya na Yahweh ne ya kuma ɗora duniyar a bisan su.
9Yana bida sawayen amintattun mutanensa, amma za a rufe bakin mai mugunta cikin duhu, gama babu mai yin nasara ta ƙarfi.
10Waɗanda ke tsayayya da Yahweh zasu karye gutsu-gutsu; zaya yi cida daga sama a kansu. Yahweh za ya hukunta ƙarshen duniya; zaya bada ƙarfi ga sarkinsa ya kuma ɗaukaka ƙahon shafaffensa."
11Daga nan Elkana ya tafi Rama, zuwa gidansa. Yaron ya bauta wa Yahweh a gaban Eli firist.
12Yanzu dai 'ya'yan Eli mutane ne marasa cancanta. Ba su san Yahweh ba.13Al'adar firistoci da mutanen shi ne idan kowanne mutum ya miƙa hadaya, bawan firist za ya zo da cokali mai yatsu uku a hannunsa, yayin da naman ke tafasa.14Za ya caka cokalin a cikin kaskon, ko garwar, ko tanderun, ko tukunyar. Duk abin da cokalin ya tsamo sama firist za ya ɗaukar wa kansa. Haka suka riƙa yi a Shilo ga dukkan Isra'ilawa da suka zo wurin.
15Mafi ɓaci, kafin su ƙona kitsen, bawan firist za ya zo, ya kuma cewa mutumin da ke yin hadayar, "Bayar da naman gashi domin firist; domin ba za ya karɓi dafaffen nama ba daga gare ka, sai ɗanye kaɗai."16Idan mutumin ya ce masa, "Dole ne su ƙona kitsen da farko, daga nan sai ka ɗauki iya yadda kake so." Daga nan sai ya ce, "A a, yanzu zaka ba ni; idan ba haka ba, zan ɗauka da ƙarfi da yaji."17Zunubin waɗannan yara maza ya yi girma sosai a gaban Yahweh, gama sun wulaƙanta baikon Yahweh.
18Amma Sama'ila ya bauta wa Yahweh a matsayin yaro yana sanye da falmarar linin.19Mahaifiyarsa takan yi masa ƙaramar riga ta kuma kai masa daga shekara zuwa shekara, idan ta zo tare da mijinta domin miƙa hadaya ta shekara-shekara.
20Eli za ya albarkaci Elkana da matarsa ya ce, "Bari Yahweh ya ba ka ƙarin 'ya'ya ta wurin wannan matar saboda roƙon da ta yi ga Yahweh." Daga nan sai su koma nasu gidan.21Yahweh ya sake taimakon Hannatu, ta kuma sake ɗaukar ciki. Ta haifi 'ya'ya maza uku mata biyu. Yayin da ake haka, yaron kuwa Sama'ila ya yi girma gaban Yahweh.
22Yanzu dai Eli ya tsufa; ya ji kuma dukkan abin da 'ya'yansa maza ke yi ga dukkan Isra'ila, da yadda suke kwana da dukkan matayen da ke bauta a ƙofar shiga rumfar taruwa.23ya ce masu, "Me yasa kuke yin irin abubuwan nan? gama na ji ayyukan muguntarku daga dukkan mutanen nan."24A'a, 'ya'ya na; Ba rahoto bane mai kyau da na ji. Ku na sa mutanen Yahweh rashin biyayya.
25Idan mutum ɗaya ya yi zunubai gãba da wani, Allah za ya hukunta shi; amma idan mutum ya yi zunubai gãba da Yahweh, wane ne za ya yi magana a madadinsa?" Amma ba zasu saurari muryar mahaifinsu ba, saboda Yahweh ya shirya kashe su.26Yaron kuwa Sama'ila ya girma, ya ƙaru a tagomashi tare da Yahweh tare kuma da mutane.
27Yanzu dai wani mutumin Allah ya zo wurin Eli ya ce ma shi, "Yahweh ya ce, 'Ban bayyana kai na ba ga gidan kakanka, sa'ad da suke a Masar cikin ƙangin gidan Fir'auna?28Na zaɓe shi daga cikin dukkan kabilun Isra'ila ya zama firist ɗi na, ya hau zuwa bagadi na, ya kuma ƙona turare, ya sanya falmara a gabana. Na bayar ga gidan kakanka dukkan baye-bayen mutanen Isra'ila da aka yi tare da wuta.
29Me yasa, daga nan, ka yi ba'a ga hadayu na da baye-bayen da na buƙata a wurin da nake zama? Me yasa ka girmama 'ya'yanka fiye da ni ta wurin mai da kanka mai ƙiba tare da kowanne baikon mutane na Isra'ila?'30Gama Yahweh, Allah na Isra'ila, ya ce, 'Na yi alƙawarin cewa gidanka, da gidan kakanka, zasu yi tafiya a gabana har abada.' Amma yanzu Yahweh ya ce, 'Ya yi nesa da ni in yi haka, gama zan girmama waɗanda ke girmama ni, amma waɗanda suka rena ni zasu sha ƙasƙanci.
31Duba, kwanaki na zuwa da zan datse ƙarfinka da ƙarfin gidan mahaifinka, yadda ba za a sake samun tsohon mutum ba a cikin gidanka.32Za ka ga ƙunci a cikin wurin da nake zama. Koda ya ke abu mai kyau za a ba Isra'ila, ba za a sake samun tsohon mutum ba a gidanka.33Kowanne daga cikinku da ban datse ba daga bagadina, Zan kawo faɗawa ga idanunku, Zan kawo baƙinciki ga rayukanku. Dukkan mazajen da aka haifa a iyalinku zasu mutu.
34Wannan zai zamar maka alama da zata zo bisa 'ya'yanka maza biyu, bisa Hofni da Finehas: Dukkan su zasu mutu a rana ɗaya.35Zan tayar wa kaina amintaccen firist wanda zai yi abin da ke cikin zuciyata da cikin raina. Zan gina masa tabbataccen gida; kuma za ya yi tafiya a gaban shafaffen sarkina har abada.
36Duk wanda aka bari daga cikin gidanka zaya zo ya rusuna masa, yana roƙon ɓallin azurfa da gutsuren gurasa, kuma za ya ce, "Ina roƙon ka ka naɗa ni ɗaya daga cikin guraben firistoci domin in samu in ci gutsuren gurasa.""'

3

1Yaron nan Sama'ila ya bauta wa Yahweh a gaban Eli. Maganar Yahweh ta yi ƙaranci a waɗannan kwanaki; babu yawan wahayin anabci.2A wannan lokaci, sa'ad da Eli, wanda idanunsa sun fara yin dishi-dishi yadda ba ya iya gani sosai, yana kwance a bisa nasa gadon.3Fitilar Allah bata riga ta mutu ba, kuma Sama'ila yana kwance domin ya yi barci a haikalin Yahweh, inda akwatin Yahweh ya ke.4Yahweh ya yi kira ga Sama'ila, wanda ya ce, "Ga ni nan."

5Sama'ila ya ruga wurin Eli ya kuma ce, "Ga ni nan, gama ka kira ni." Eli ya ce, "Ban kira ka ba, ka sake kwantawa." Sai Sama'ila ya koma ya sake kwantawa.6Yahweh ya sake kira, "Samai'la." Sama'ila ya sake tashi ya tafi wurin Eli ya kuma ce, "Gani nan, gama ka kira ni." Eli ya amsa, "Ban kira ka ba, ɗana, ka sake kwantawa."
7Yanzu dai Sama'ila bai taɓa samun wata gamuwa da Yahweh ba, ko wani saƙo daga Yahweh ya taɓa bayyana a gare shi ba.8Yahweh ya sake kiran Sama'ila karo na uku. Sama'ila ya sake ta shi ya tafi wurin Eli ya ce, "Ga ni nan, gama ka kira ni." Daga nan Eli ya fahimci cewa Yahweh ya kira yaron.
9Daga nan Eli ya cewa Sama'ila, "Ka je ka sake kwantawa kuma, idan ya sake kiran ka, dole ka ce, 'Yi magana, Yahweh, gama bawanka yana saurare."' Daga nan Sama'ila ya tafi kuma ya sake kwantawa a na sa wurin kuma.
10Yahweh ya zo ya tsaya; ya yi kira kamar sauran lokuttan, "Sama'ila, Sama'ila." Daga nan Sama'ila ya ce, "Yi magana, gama bawanka yana sauraro."11Yahweh ya cewa Sama'ila, duba, Ina gaf da yin wani abu a Isra'ila wanda kunnuwan dukkan wanda za ya ji za su karkaɗa.
12A wannan rana zan aiwatar ga Eli dukkan abin da na ce game da gidansa, daga farko har ƙarshe.13Na gaya masa ina gaf da hukunta gidansa karo ɗaya tak domin zunubin da ya riga ya sani, saboda 'ya'yansa sun kawo la'ana a kansu bai kuma hana su ba.14Saboda wannan na yi rantsuwa game da gidan Eli cewa zunuban gidansa ba za a iya yi masu kaffara ba da hadaya ko baiko."
15Sama'ila ya kwanta har gari ya waye; daga nan ya buɗe ƙofofin gidan Yahweh. Amma Sama'ila ya ji tsoron gaya wa Eli game da wahayin.16Daga nan Eli ya kira Sama'ila ya ce, "Sama'ila, ɗana." Sama'ila ya ce, "Ga ni nan."
17ya ce, "Wacce magana ce ya faɗi maka? Ina roƙon ka kada ka ɓoye mani. Bari Allah ya yi maka haka, fiye da haka ma, idan ka ɓoye wani abu daga gare ni a dukkan maganganun da ya faɗi maka."18Sama'ila ya faɗi masa dukkan abu; bai ɓoye masa komai ba. Eli ya ce, "Yahweh ne. Bari ya yi abin da ya yi kyau a gare shi."
19Sama'ila ya yi girma, kuma Yahweh na tare dashi kuma bai bar ko ɗaya daga cikin maganganun anabcinsa ba su kãsa zama gaskiya.20Dukkan Isra'ila daga Dan zuwa Biyasheba suka sani cewa an naɗa Sama'ila annabin Yahweh.21Yahweh ya sake bayyana a Shilo, gama ya bayyana kansa ga Sama'ila a Shilo ta wurin maganarsa.

4

1Maganar Sama'ila ta zo ga dukkan Isra'ila. Yanzu dai Isra'ila sun fita yaƙi gãba da Filistiyawa. Suka kafa sansani a Ebeneza, Filistiyawa kuma sukakafa sansani a Afek.2Filistiyawa suka jera domin yaƙi gãba da Isra'ila. Da aka baza yaƙin, Filistiyawa sukakayar da Isra'ila, wanda sukakashe wajen mutum dubu huɗu a filin yaƙin.

3Da mutanen suka zo cikin sansanin, dattawan Isra'ila suka ce, "Me yasa Yahweh yakayar damu yau a gaban Filistiyawa? Bari mu kawo akwatin alƙawarin Yahweh a nan daga Shilo, domin yakasance a nan tare da mu, domin ya ajiye mu a tsare daga hannun maƙiyanmu."4Sai mutanen suka aiki mazaje zuwa Shilo; daga nan suka ɗauko akwatin alƙawarin Yahweh mai runduna, wanda ke zaune a bisa kerubim. 'Ya'yan Eli maza biyu, Hofni da Finehas, suna nan tare da akwatin alƙawarin Allah.
5Da akwatin alƙawarin Yahweh ya iso cikin sansani, dukkan mutanen Isra'ila suka yi babbar kururuwa, har ƙasa ta amsa.6Da Filistiyawa suka ji ƙarar kururuwar, suka ce, "Me wannan ƙarar kururuwar a cikin sansani Ibraniyawa ke nufi?" Sai suka tantance cewa akwatin Yahweh ya zo cikin sansanin.
7Filistiyawa suka tsorata; suka ce, "Wani allah ya shigo cikin sansanin." Suka ce, "Kaitonmu! Babu wani abu kamar haka da ya faru a dã!8Kaitonmu! Wane ne zai cece mu daga ƙarfin waɗannan alloli masu iko? Waɗannan allolin ne sukakaiwa Masarawa hari da allobai iri-iri a cikin jeji.9Ku yi ƙarfin hali, ku kuma zama mazaje, ku Filistiyawa, ko kuwa ku zama bayi ga Ibraniyawa, kamar yadda suke bayi a gare ku. Ku zama mazaje, ku kuma yi faɗa."
10Filistiyawa suka yi faɗa, aka kumakayar da Isra'ila. Kowanne mutum ya tsere zuwa gidansa, kisan da aka yi babba ne ƙwarai; gama sojojin ƙasa dubu talatin ne daga Isra'ila suka faɗi.11Aka ɗauke akwatin Allah, 'ya'yan Eli maza biyu kuma, Hofni da Finehas, suka mutu.
12Wani mutumin Benyamin ya gudu daga fagen yaƙin ya kuma zo Shilo a ranar nan, ya iso da tufafinsa a yage da kuma ƙasa bisakansa.13Da ya iso, Eli na zaune bisa mazauninsa a bakin hanya yanakallo saboda zuciyarsa na fargaba tare da damuwa domin akwatin Allah. Da mutumin ya shiga cikin birnin ya faɗi labarin, dukkan birnin aka yi kuka.
14Da Eli ya ji ƙarar kukan, ya ce, "Mene ne ma'anar wannan yamitsin?" Mutumin ya zo da sauri ya kuma faɗa wa Eli.15Yanzu dai Eli shekarunsa tasa'in da takwas; idanunsa ba su fuskanta dai-dai, kuma baya gani.
16Mutumin ya cewa Eli, "Ni ne na zo daga fagen yaƙin. Na gudo daga yaƙin yau." Eli ya ce, "Ya abin ya tafi, ɗa na?"17Mutumin da yakawo labarin ya amsa kuma ya ce, "Isra'ila sun gudu daga Filistiyawa. Haka kuma, babbar kayarwa takasance a tsakanin mutanen. Haka kuma, 'ya'yan ka maza biyu, Hofni da Finehas, sun mutu, akwatin Allah kuma an ɗauke."
18Da ya faɗi akwatin Allah, Eli ya fãɗi ta baya daga bisa kujerarsa ta gefen ƙofa. Wuyansa yakarye, ya kuma mutu, saboda ya tsufa kuma yana da nauyi. ya yi alƙalancin Isra'ila shekaru arba'in.
19Yanzu dai surukarsa, matar Finehas, tana da ciki kuma ta yi gaf da haihuwa. Da ta ji labarin an cafke akwatin Allah da surukinta da mijinta kuma sun mutu, ta durƙusa kuma ta haihu, amma zafin naƙudarta ya mamaye ta.20Wajen lokacin mutuwarta matan da ke yi mata unguwar zoma suka ce mata, "Kada ki ji tsoro, gama kin haifi ɗa namiji." Amma ba ta amsa ba ko ta ɗauki abin da suka ce a zuciya.
21Ta raɗa masa suna Ikabod, cewa, "‌Ɗaukaka ta tafi da ga Isra'ila!" domin an cafke akwatin Allah, saboda kuma surukinta da mijinta.22Ta ce, "‌Ɗaukaka ta tafi daga Isra'ila, saboda an cafke akwatin Allah."

5

1Yanzu dai Filistiyawa sun cafke akwatin Allah, su ka kumakawo shi daga Ebeneza zuwa Asdod.2Filistiyawa suka ɗauki akwatin Allah, sukakawo shi cikin gidan Dagon, suka jera shi a gefen Dagon.3Da mutanen Asdod suka tashi da sassafe washegari, duba, Dagon ya faɗi ƙasa da fuskarsa ƙasa gaban Yahweh. Sai suka ɗauki Dagon suka kuma sake jera shi a wurinsa.

4Amma da suka tashi da sassafe washegari, duba, Dagon ya faɗi ƙasa da fuskarsa ƙasa a gaban akwatin Yahweh. Kan Dagon da hannuwansa suna kwance datsastsu a hanyar ƙofa. Gangar jikin Dagon kawai ya rage.5Wannan ne yasa, har yau ma, firistocin Dagon da ko wane ne ya zo cikin gidan Dagon ba ya taka hanyar ƙofar Dagon a Asdod.
6Hannun Yahweh kuwa ya yi nauyi a bisa mutanen Asdod. Ya lalatar da su ya azabce su da marurai. Asdod duk da kewayenta.7Da mutanen Asdod suka lura da abin da ke faruwa, suka ce, "Akwatin Allahn Isra'ila dole ba za ya zauna ta re da mu ba, saboda hannunsa ya yi tsanani gãba da mu da gãba da allahnmu Dagon."
8Sai suka aika suka kuma tattaro tare dukkan shugabannin Filistiyawa; suka ce masu, "Me za mu yi da akwatin Allah na Isra'ila?" Suka amsa, "Bari akawo akwatin Allah na Isra'ila zuwa Gat." Sai suka ɗauki akwatin Allah na Isra'ila zuwa can.9Amma bayan da sukakawo shi wurin, hannun Yahweh ya yi gãba da birnin, ya sanya babbar ruɗewa. Ya azabtar da mutanen birnin, ƙarami da babba dukka; marurai kuma suka faso akansu.
10Sai suka aika da akwatin Allah zuwa Ekron. Amma nan da nan da akwatin Allah ya zo cikin Ekron, Ekroniyawa suka koka, cewa, "Sun kawo mana akwatin Allah na Isra"ila domin yakashe mu da mutanenmu."
11Sai suka aika aka tattaro tare dukkan shugabannin Filistiyawa; suka ce masu, "Ku aika da akwatin Allah na Isra'ila, bari kuma ya koma na sa wurin, domin kada yakashe mu da mutanenmu." Domin akwai razana mai mutuwa cikin dukkan birnin; hannun Allah yana da nauyi sosai a wurin.12Mutanen da ba su mutu ba an azabce su da marurai, kukan birnin kuma ya hau zuwa sammai.

6

1Yanzu dai akwatin Yahweh na cikin ƙasar Filistiyawa har watanni bakwai.2Daga nan Mutanen Filistiyawa suka kira firistoci da masu sihiri; suka ce masu, "Me zamu yi da akwatin Yahweh? ku gaya mana yadda zamu aika da shi zuwa ƙasarsa."

3Firistoci da masu sihiri suka ce, "Idan kuka aika da akwatin Allah na Isra'ila, kada ku aika da shi ba tare da kyauta ba; ta ko ƙaƙa ku aika masa da baiko na laifi. Daga nan zaku warke, daga nan kuma zaku ga ne dalilin da yasa hannunsa bai ɗauke ba daga bisanku har yanzu.4Daga nan suka ce, "Mene ne za ya zama baiko na laifin da zamu maida masa?" Suka maida amsa, "Marurai na zinariya biyar da ɓerayen zinariya biyar, biyar lissafin yawa ne wanda ya yi dai-dai da lissafin yawan shugabannin Filistiyawa. Domin annoba iri ɗaya ce ta azabce ku da shugabanninku.
5Dole ku yi marurai na kwaikwayo, da ɓerayen kwaikwayo da suka addabi ƙasar, ku kuma bada ɗaukaka ga Allah na Isra'ila. Wataƙila zai ɗauke hannun sa daga gare ku, daga allolinku, daga kuma ƙasarku.6Me yasa zaku taurare zukatanku, kamar yadda Masarawa da Fir'auna suka taurare zukatansu? Ta haka Allah na Isra'ila ya tsananta masu da zafi; Ashe Masarawan basu fitar da mutanen ba, suka kuma tafi?
7To yanzu, ku shirya amalanke da shanu biyu masu shayarwa waɗanda ba a taɓa ɗaurawakarkiya ba. Ku ɗaura shanun ga amalanken, amma ku ɗauki 'yan maruƙansu daga gare su, ku kai gida.8Daga nan ku ɗauki akwatin Yahweh ku sa cikin amalanken. Ku sanya siffofin zinariyar da zaku maida masa a matsayin baiko na laifi cikin wani akwatin a gefensa. Daga nan ku aika da shi kuma bari ya tafi hanyarsa.9Daga nan ku kalla; Idan ya yi tafiyarsa bisa hanya zuwa cikin ƙasarsa zuwa Bet Shemesh, to Yahweh ne ya zartar da wannan babban bala'i. Amma idan ba haka ba, daga nan za mu sani cewa ba hannunsa ba ne ya azabtar damu ba; maimakon haka, zamu sani cewa ya faru da mu ne hakakawai."
10Mutanen suka yi yadda aka gaya masu; suka ɗauki shanu biyu masu shayarwa; suka ɗaura su ga amalanken, suka tsare 'yan maruƙansu a gida.11Suka sanya akwatin Yahweh a cikin amalanken, tare da akwatin da ke ɗauke da ɓerayen zinariyar da sarrafaffun maruransu.12Shanun suka tafi a miƙe a hanyar Bet Shemesh. Suka tafi bisa babbar hanya, suna tafiya suna kuka, ba su kumakauce daga hanya ba ko zuwa dama ko zuwa hagu. Shugabannin Filistiyawa suka bi bayansu har zuwakan iyakar Bet Shemesh.
13Yanzu dai mutanen Bet Shemesh suna girbin alkamarsu a kwari. Da suka ɗaga idanunsu suka ga akwatin, suka yi farinciki.
14Amalanken ya iso cikin gonar Yoshuwa daga Bet Shemesh ya kuma tsaya a wurin. Wani babban dutse na wurin, suka tsinke itacen amalanken, suka miƙa shanun a matsayin baikon ƙonawa ga Yahweh.15Lebiyawa suka sauke akwatin Yahweh da akwatin da ke tare da shi, inda siffofin zinariyar suke, suka ɗora su bisa babban dutsen. Mutanen Bet Shemesh suka miƙa baye-baye na ƙonawa suka kuma yi hadayu a wannan rana ga Yahweh.
16Da shugabannin Filistiyawa biyar suka ga haka, suka koma Ekron a ranar.
17Waɗannan ne maruran zinariya da Filistiyawa suka maido domin baiko na laifi ga Yahweh: ɗaya domin Asdod, ɗaya domin Gaza, ɗaya domin Askelon, ɗaya domin Gat, ɗaya domin Ekron.‌18Ɓerayen zinariyar ma lissafinsu ya yi dai-dai da lissafin dukkan biranen Filistiyawa da sukakasance na shugabannin biyar, dukkansu tsararrun birane ne da ƙauyukansu. Babban dutsen, gefen da aka ajiye akwatin Yahweh, ya zama shaida har yau a cikin filin Yoshuwa Betshemiye.
19Yahweh yakai hari ga wasu daga cikin mutanen Bet Shemesh saboda sun duba cikin akwatin Yahweh. Yakashe mutum 50,070. Mutanen suka yi makoki, saboda Yahweh ya ba mutanen babban naushi.20Mutanen Bet Shemesh suka ce, "Wane ne zaya iya tsayawa gaban Yahweh, wannan Allah mai tsarki? daga gare mu wurin wa akwatin zaya tafi?"
21Suka aika manzanni zuwa ga mutanen Kiriyat Yerim, cewa, "Filistiyawa sun maido da akwatin Yahweh; ku zo ku ɗauka ku kuma koma da shi tare da ku."

7

1Mutanen Kiriyat Yerim suka zo, suka ɗauki akwatin Yahweh, suka kumakawo shi cikin gidan Abinadab a bisa tudu. Suka keɓe ɗansa Eliyeza ya ajiye akwatin Yahweh.2Daga ranar da akwatin ya zauna a Kiriyat Yerim, lokaci mai tsawo ya wuce, shekaru ashirin. Dukkan mutanen Isra'ila suka yi makoki kuma suka yi marmarin komawa ga Yahweh.

3Sama'ila ya cewa gidan Isra'ila gaba ɗaya, "Idan kun dawo ga Yahweh da dukkan zuciyarku, ku cire bãƙin alloli da kuma Ashtoret daga cikinku, ku juyo da zukatanku ga Yahweh, ku kuma yi masa sujada shi kaɗai, daga nan zai kuɓutar daku daga hannun Filistiyawa."4Daga nan mutanen Isra'ila suka fitar da Ba'aloli da Ashtoret, suka kuma yi sujada ga Yahweh kaɗai.
5Daga nan Sama'ila ya ce, "Ku kawo a tattare dukkan Isra'ila zuwa Mizfa, zan kuma yi addu'a ga Yahweh domin ku."6Suka tattaru a Mizfa, suka jawo ruwa suka zuba kuma a gaban Yahweh. Suka yi azumi a ranar suka ce, "Mun yi zunubi ga Yahweh." A can ne Sama'ila ya sasanta saɓanai domin mutanen Isra'ila ya kuma shugabanci mutanen.
7Yanzu da Filistiyawa suka ji mutanen Isra'ila sun taru a Mizfa, sai shugabannin Filistiyawa sukakai hari ga Isra'ila. Da mutanen Isra'ila suka ji haka, suka ji tsoron Filistiyawa.8Daga nan mutanen Isra'ila suka cewa Sama'ila, "Kadaka daina kira ga Yahweh Allahnmu domin mu, domin ya cece mu daga hannun Filistiyawa."
9Sama'ila ya ɗauki ɗan rago mai shan nono ya miƙa shi gaba ɗaya a matsayin baikon ƙonawa ga Yahweh. Daga nan Sama'ila ya yi kuka ga Yahweh domin Isra'ila, Yahweh kuma ya amsa masa.
10Yayin da Sama'ila ke miƙa baikon ƙonawar, Filistiyawa suka matso domin su kawo hari ga Isra'ila. Amma Yahweh ya yi kwarankwatsi da babbar ƙara a wannan rana ga Filistiyawa ya kuma watsa su cikin ruɗewa, kuma suka shakaye a gaban Isra'ila.11Mutanen Isra'ila suka tafi daga Mizfa, suka kuma runtumi Filistiyawa suka kumakarkashe su har ya zuwa ƙarƙashin Bet Ka.
12Daga nan Sama'ila ya ɗauki dutse yakafa tsakanin Mizfa da Shen. Ya raɗa masa suna Ebeneza, cewa, "Har ya zuwa haka Yahweh ya taimake mu."
13Saboda haka Filistiyawa suka shakaye ba su kuma iya shigakan iyakar Isra'ila ba. Hannun Yahweh ya yi gãba da Filistiyawa dukkan kwanakin Sama'ila.14Garuruwan da Filistiyawa sukakarɓe daga Isra'ila aka maidawa Isra'ila, daga Ekron zuwa Gat; Isra'ila suka maido da lardinsu daga Filistiyawa. Daga nan aka sami salama tsakanin Isra'ila da Amoriyawa.
15Sama'ila ya yi alƙalancin Isra'ila dukkan kwanakin ransa.16Kowacce shekara yakan tafi ya zagaye zuwa Betel, da Gilgal, da Mizfa. Yana ɗaukar mataki akan saɓanai domin Isra'ila a dukkan waɗannan wurare.17Daga nan sai ya koma Rama, saboda gidansa na wurin; haka kuma a anan yana ɗaukar mataki akan saɓanai domin Isra'ila. Ya kuma gina bagadi a wurin ga Yahweh.

8

1Da Sama'ila ya tsufa, sai ya naɗa 'ya'yansa alƙalai bisa Isra'ila.2Sunan ɗan farinsa Yowel, sunan kuma ɗansa na biyu Abiya.3Su alƙalai ne a Biyasheba. 'Ya'yansa ba su yi tafiya bisa hanyoyinsa ba, amma suka bi bayan ƙazamar riba. Sukakarɓi cin hanci suka danne adalci.

4Daga nan dukkan dattawan Isra'ila suka tattaru tare suka kuma zo wurin Sama'ila a Rama.5Suka ce masa, "Duba, ka tsufa, kuma 'ya'yanka ba su yi tafiya cikin hanyoyinka ba. Ka naɗa mana sarki ya yi hukunci akan mu kamar sauran al'ummai."
6Amma Sama'ila bai ji daɗi ba da suka ce, "Ka bamu sarki ya yi hukuncinmu." Sai Sama'ila ya yi addu'a ga Yahweh.7Yahweh ya cewa Sama'ila, "Ka yi biyayya da muryar mutanen a cikin dukkan abin da suka ce maka; gama bakai suka ƙi ba, amma ni suka ƙi da zama sarki a bisansu.
8Suna aikatawa yanzu dai-dai yadda suka yi tun daga ranar dana fito da su daga Masar, suka yashe ni, da bautar wasu alloli, haka kumakaima suke yi maka.9Yanzu ka saurare su; ammaka gargaɗe su da aniya bari kuma su san yadda sarkin zai yi mulki akansu."
10Sai Sama'ila ya faɗi dukkan maganganun Yahweh ga mutanen da ke tambaya domin sarki.11Ya ce, "Wannan zai zama al'adar sarkin da zai yi mulki a bisanku. Zai ɗauki 'ya'yanku maza ya naɗa su gakarusansa ya kuma sa su zama mutanen dawakansa, su kuma yi gudu a gaban karusansa.12Zai naɗa wakansa ofisoshin bataliyar sojoji dubbai, da ofisoshin bataliyar sojoji hamsin. Zai sa wasu su yi noman gonarsa, wasu suyi girbin amfaninsa, wasu kuma suyi masa makaman yaƙi dakayan karusansa.
13Zai kuma ɗauki 'ya'yanku mata su zama masu yi masa turare, da girke-girke, da gashe-gashe.14Zai ɗauki gonakinku mafi kyau, da garkunan inabinku, da kuma fadamunku na itatuwan zaitun, ya bayar dasu ga bayinsa.15Zai ɗauki kashi goma daga cikin hatsinku da garkarku ya kuma ba ofisoshinsa da bayinsa.
16Zai ɗauki bayinku maza da bayinku mata da mafi nagarta na matasanku maza da jakanku; zai sanya su duka su yi masa aiki.17Zai ɗauki kashi goma daga cikin garken dabbobinku, kuma za ku zama bayinsa.18Daga nan a wannan rana za ku koka game da sarkinku wanda kuka zaɓarwakanku; amma Yahweh ba zai amsa maku ba a ranar."
19Amma mutanen suka ƙi sauraron Sama'ila; suka ce, "A a! dole sarki yakasance a bisanmu20saboda mu zamakamar dukkan sauran al'ummai, saboda kuma sarkinmu ya hukunta mu ya kuma fita a gabanmu ya kuma yi faɗan yaƙe-yaƙenmu."
21Da Sama'ila ya ji dukkan maganganun mutanen sai ya maimaita su a kunnuwan Yahweh.22Yahweh ya cewa Sama'ila, "Ka yi biyayya da muryarsu ka kuma sa wani ya zama sarki domin su." Sai Sama'ila ya cewa mutanen Isra'ila, "Kowanne mutum dole ya tafi nasa birnin."

9

1Akwai wani mutum a Benyamin, sanannen mutum. Sunansa Kish ɗan Abiyel ɗan Zeror ɗan Bekorat ɗan Afiya, ɗan wani Benyamine.2Yana da wani ɗa mai suna Saul, kyakkyawan saurayi. Babu wani taliki a cikin mutanen Isra'ila wanda ya ke mai asali ne fiye da shi. Dagakafaɗarsa zuwa sama yafi kowanne mutanen tsayi.

3Yanzu dai jakan Kish, mahaifin Saul, sun ɓace. Sai Kish ya cewa ɗansa Saul, "Ka ɗauki ɗaya daga cikin bayin tare dakai; ka ta shi ka tafi neman jakan."4Sai Saul ya ratsa ta cikin ƙasar tudu ta Ifraim ya kuma tafi ta cikin ƙasar Shalisha, amma ba su same su ba. Daga nan suka ratsa ta cikin ƙasar Sha'alim, amma ba su a wurin. Sai ya ratsa ta cikin ƙasar Benyaminawa, amma ba su same su ba.
5Da suka zo ƙasar Zuf, sai Saul ya cewa bawansa da ke tare da shi, "Zo, bari mu koma, ko mahaifina na iya daina damuwa domin jakan ya fara damuwa game da mu."6Amma bawan ya ce masa, "Saurara, akwai mutumin Allah a cikin wannan birnin. Mutum ne da aka riƙe da daraja; duk abin da ya ce yana zama gaskiya. Mu tafi can; watakila zai iya gaya mana wacce hanya zamu bi a tafiyarmu."
7Daga nan Saul ya cewa bawansa, "Amma idan muka je, me za mu kawo wa mutumin? Domin gurasar da ke jakarmu ta ƙare, ba bu kuma wata kyauta da za mu kawo wa mutumin Allahn. Me muke da shi?"8Bawan ya amsa wa Saul ya kuma ce, "Nan, akwai tare da ni kwatar shekel na azurfa da zan ba mutumin Allahn, ya gaya mana hanyar da za mu je."
9(A dã a Isra'ila, idan mutum ya tafi neman sanin nufin Allah, zai ce, "Zo, bari mu tafi wurin mai gani." Gama annabi a yau mai gani ake kiran sa a dã.)10Daga nan Saul ya cewa bawansa, "Faɗar ta yi dai-dai. Zo, bari mu tafi." Sai suka tafi birnin inda mutumin Allah ya ke.11Yayin da suka tafi zuwa tudun birnin, sai suka sami 'yan mata na fitowa jan ruwa; Saul da bawansa suka ce masu, "Mai ganin na nan?"
12Suka amsa, suka kuma ce, "Yana nan; kalli, yana ɗan gaba da ku. Yi sauri, gama yana zuwa birnin yau, saboda mutanen suna hadaya a yau a wuri mai bisa.13Da zarar kun shiga birnin zaku same shi, kafin ya hau zuwa wuri mai bisa domin cin abinci. Mutanen ba zasu ci ba sai ya zo, saboda zai albarkaci hadayar; bayan haka waɗanda aka gayyata zasu ci. yanzu ku haura, gama zaku same shi nan da nan."
14Sai suka tafi zuwa birnin. Yayin da suke shiga birnin, suka ga Sama'ila na zuwa ta wurinsu, domin ya tafi zuwa wuri mai bisa.
15Yanzu dai ana gobe Saul zai zo, Yahweh ya bayyanawa Sama'ila:16"Gobe war haka zan aiko maka wani mutum daga ƙasar Benyamin, zaka kuma naɗa shi ya zama shugaba bisa mutane na Isra'ila. za ya ceci mutanena daga hannun Filistiyawa. Domin na dubi mutanena tare da tausayi saboda kiran su domin taimako ya zo gare ni."
17Da Sama'ila ya ga Saul, Yahweh ya ce masa, "Shi ne mutumin da na gaya maka game da shi! shi ne wanda zai yi mulki bisa mutanena."18Daga nan Saul ya zo kusa da Sama'ila a ƙofa kuma ya ce, "Ka gaya mani ina ne gidan mai gani?"19Sama'ila ya amsa wa Saul ya ce, "Ni ne mai gani. Ka hau a gabana zuwa wuri mai bisa, domin yau zaka ci tare da ni. Da safe zan bar kaka tafi, kuma zan gaya maka kowanne abu da ke cikin ranka.
20Game da jakanka da suka ɓace kwana uku da suka wuce, kadaka damu game da su, domin an same su. Daga nan akan wane ne dukkan marmarin Isra'ila yakasance? Ba akanka ba ne da kuma dukkan gidan mahaifinka?"21Saul ya amsa ya ce, "Ni ba Benyamine ba ne, daga mafi ƙanƙanta nakabilun Isra'ila? Ba zuriyarmu ce mafi ƙanƙanta ba a cikin dukkan zuriyar Benyamin? To me yasakake magana da ni irin haka.
22Sai Sama'ila ya ɗauki Saul da baransa, yakawo su cikin harabar, ya zaunar da su a wuri mafi girma na waɗanda aka gayyata, waɗanda kimanin mutum talatin ne.
23Sama'ila ya cewa mai girkin, "Kakawo kason da na baka, wanda na ce maka, 'Ka ajiye shi a gefe."'24Sai mai girkin ya ɗauko cinyar da abin da ke bisanta ya kuma sanya a gaban Saul. Daga nan Sama'ila ya ce, "Kalli abin da aka ajiye an sanya a gabanka. Ka ci, saboda an ajiye maka har zuwa zaɓaɓɓen lokaci, daga lokacin da na ce, 'Na gayyaci mutanen."' Sai Saul ya ci tare da Sama'ila a ranar.
25Da suka sauko daga wuri mai bisa zuwa cikin birnin, Sama'ila ya yi magana da Saul a bisa saman rufi.26Daga nan da gari ya waye, Sama'ila ya yi kira ga Saul a bisa saman rufi ya kuma ce, "Ta shi, domin in aika dakai kan hanyarka." Sai Saul ya tashi, da shi da Sama'ila kuma dukka suka fita bisa titi.
27Suna cikin tafiya zuwa waje da birnin, Sama'ila ya cewa Saul, "Ka cewa baran ya tafi gaba da mu" - sai ya tafi gaba - "amma dole ka tsaya a nan na ɗan lokaci, domin in shelar da saƙon Allah a gare ka."

10

1Sai Sama'ila ya ɗauki kwalbar mai, ya zuba akan Saul, ya kuma sumbace shi. Ya ce, "Ba Yahweh ya shafe ka baka zama shugaba bisa gãdonsa?2Idan ka bar ni yau, zaka sami mutum biyu kusa dakabarin Rahila, cikin lardin Benyamin a Zelza. Zasu ce maka, 'Jakan dakake nema an same su. Yanzu mahaifinka ya daina kula wa da jakan yana damuwa game dakai, cewa, "Me zanyi game da ɗa na?"'

3Daga nan zaka tafi daga wurin, zaka kuma zo rimin Tabor. Mutane uku masu tafiya wurin Allah a Betel zasu gamu dakai a wurin, ɗaya na ɗauke da 'yan awaki uku, wani kuma na ɗauke da dunƙulen gurasa uku, wani kuma na ɗauke da salkar inabi.4Zasu gaishe ka su baka dunƙulen gurasa biyu, wanda zakakarɓa daga hannuwansu.
5Bayan wannan, zaka zo tudun Allah, inda sansanin Filistiyawa ya ke. Idan ka isa birnin, zaka iske ƙungiyar annabawa na saukowa daga wuri mai bisa tare da algaita, da tambari, dakakaki, da sarewa, a gabansu; za su riƙayin anabci.6Ruhun Yahweh zai abko maka, zaka kuma yi anabci tare da su, zaka kuma sauya zuwa wani mutum daban.
7Yanzu, idan waɗannan alamu suka zo maka, ka aiwatar da duk abin da hannunka ya sami damar yi, gama Allah na tare dakai.8Ka gangara gaba da ni zuwa Gilgal. Daga nan zan gangaro zuwa gare ka in miƙa baye-baye na ƙonawa in kuma yi hadayar baye-baye na salama. Ka jira kwana bakwai har sai na zo gare ka in kuma nuna maka abin da dole ka yi."
9Da Saul ya juya bayansa domin ya bar Sama'ila, Allah ya ba shi wata zuciyar. Daga nan dukkan waɗannan alamu suka faru a ranar.10Da suka iso tudun, wata ƙungiyar annabawa ta gamu da shi, Ruhun Allah kuma ya abko bisansa har ya yi anabci tare da su.
11Da dukkan waɗanda suka san shi a dã suka ga yana anabci tare da annabawan, mutanen suka ce da junansu, "Mene ne ya faru da ɗan Kish? Saul shi ma ɗaya daga cikin annabawan ne yanzu?"12Wani mutum da ya fito daga wuri ɗaya da shi ya amsa, "To wane ne mahaifinsa?" Saboda wannan, ya zama abin faɗi, "Saul shi ma ɗaya ne daga cikin annabawan?"13Da ya gama anabcin, ya zo wuri mai bisan.
14Daga nan kawun Saul ya ce masa da kuma bawansa, "Ina kuka je?" Ya mai da amsa, "Neman jakan. Da muka ga ba mu iya samo su ba, muka je wurin Sama'ila."15Kawun Saul ya ce, "Ina roƙon kaka gaya mani abin da Sama'ila ya ce maka."16Saul ya amsa wakawunsa, "Ya gaya mana a sarari cewa an samo jakan." Amma bai gaya masa game da al'amarin masarautar ba, wanda Sama'ila ya yi magana akai.
17Yanzu Sama'ila ya kira mutanen tare a gaban Yahweh a Mizfa.18Ya cewa mutanen Isra'ila, "Wannan ne abin da Yahweh, Allah na Isra'ila ya faɗa: 'Nakawo Isra'ila daga ƙasar Masar kuma na ƙwato ku daga hannun Masarawa, daga kuma hannun dukkan masarautun da suka tsananta maku.'19Amma yau kun watsar da Allahnku, wanda ya cece ku daga dukkan bala'o'inku da ƙuncinku; kuma kun ce da shi, 'Naɗa sarki a bisanmu.' Yanzu ku gabatar dakanku a gaban Yahweh takabilunku da zuriyarku."
20Sai Sama'ila yakawo dukkan kabilun Isra'ila kusa, kumakabilar Benyamin aka zaɓa.21Daga nan yakawo kabilar Benyamin kusa ta zuriyarsu; kuma zuriyar Matirawa aka zaɓa; kuma Saul ɗan Kish aka zaɓa. Amma da suka tafi neman sa, ba a iya samun sa ba.
22Daga nan mutanen suka so su roƙi Allah ƙarin tambayoyi, "Akwai kuma wani mutumin da zai zo?" Yahweh ya amsa, "Ya ɓoye kansa cikin kayayyaki."23Daga nan suka ruga suka tsamo Saul daga wurin. Da ya tsaya cikin mutanen, yafi kowanne daga cikin mutanen tsayi, dagakafaɗarsa zuwa sama.
24Daga nan Sama'ila ya cewa mutanen, "Kun ga mutumin da Yahweh ya zaɓa?" Babu wani kamar sa daga cikin dukkan mutanen!" Dukkan mutanen suka yi sowa, "Ran sarki ya daɗe!"
25Daga nan Sama'ila ya gaya wa mutanen al'adu da dokokin sarautar, ya rubuta su cikin littafi, ya kuma ajiye su gaban Yahweh. Daga nan Sama'ila ya sallami dukkan mutanen, kowanne mutum zuwa nasa gidan.
26Saul shi ma ya tafi gidansa a Gibiya, tare da shi kuma wasu ƙarfafan mutane, waɗanda Allah ya taɓa zukatansu.27Amma wasu mutane marasa amfani suka ce, "Ta yaya wannan mutum zai cece mu?" Waɗannan mutane suka rena Saul, ba su kumaka wo masa wata kyauta ba. Amma Saul ya yi shiru.

11

1Daga nan Nahash Ba'ammoniye ya tafi yakafa sansani ga Yabesh Giliyad. Dukkan mutanen Yabesh suka cewa Nahash, "Ka yi alƙawari da mu, kuma za mu bauta maka."2Nahash Ba'ammoniye ya maida amsa, "Bisa wannan matsayin zan yi alƙawari da ku, cewa zan ƙwaƙule dukkan idanunku na dama, ta wannan hanya kuma in kawo kunya bisa dukkan Isra'ila."

3Daga nan dattawan Yabesh Giliyad suka mai da masa amsa, "Ka rabu da mu na kwana bakwai, saboda mu aika da saƙonni ga dukkan lardin Isra'ila. Daga nan, idan ba bu wani da zai cece mu, za mu sadauƙar a gare ka."
4Manzannin suka zo Gibiya, inda Saul ke zama, suka kuma gayawa mutanen abin da ya faru. Dukkan mutanen suka yi kuka da ƙarfi.5Yanzu dai Saul na biye da shanu daga saura. Saul ya ce, "Me ke damun mutanen da suke kuka?" Suka gaya wa Saul abin da mutanen Yabesh suka ce.
6Da Saul ya ji haka, Ruhun Allah ya afko masa, ya kuma fusata sosai.7Ya ɗauki shanun huɗa biyu, ya datse su gunduwa-gunduwa, ya kuma aika da su cikin dukkan lardin Isra'ila tare da manzanni. ya ce, "Duk wanda bai fito bayan Saul da bayan Sama'ila ba, haka za a yi wa shanun huɗarsa." Daga nan razanar Yahweh ta faɗo bisa mutanen, suka kuma fito tare a matsayin mutum ɗaya.8Da ya tattara su a Berek, mutanen Isra'ila dubu ɗari uku ne, mutanen Yahuda kuma dubu talatin.
9Suka ce wa manzannin da suka zo, "Za ku cewa mutanen Yabesh Giliyad, "Gobe, lokacin da rana takai tsaka, za a ceto ku." Sai manzannin suka tafi suka gaya wa mutanen Yabesh, suka kuma yi farinciki.10Daga nan mutanen Yabesh suka cewa Nahash, "Gobe za mu sadaukar a gare ka, sai kumaka yi da mu duk abin da ya yi kyau a gare ka."
11washegari Saul yasa mutanen ƙungiya uku. Suka zo tsakiyar sansanin a lokacin wayewar gari, suka kumakai hari suka kumakayar da Ammoniyawa har zafin rana. Waɗanda suka tsira su ka watse, har babu mutum biyun su da aka bari tare.
12Daga nan mutanen suka ce wa Sama'ila, "Wane ne wanda ya ce, 'Saul zai yi mulki a bisanmu?' akawo mutanen, domin mu kashe su."13Amma Saul ya ce, "Babu wanda za akashe dole a wannan ranar, saboda a wannan ranar Yahweh ya ceto Isra'ila."
14Daga nan Sama'ila ya cewa mutanen, "Ku zo, bari mu tafi Gilgal mu sabunta sarautar a can."15Saboda haka dukkan mutanen suka tafi Gilgal suka kuma maida Saul sarki a gaban Yahweh a Gilgal. A can suka yi hadayar baye-baye don salama a gaban Yahweh, da Saul da dukkan mutanen Isra'ila suka yi farinciki babba.

12

1Sama'ila ya cewa dukkan Isra'ila, "Na saurari dukkan abin da kuka faɗi mani, na kuma naɗa sarki a bisanku.2Yanzu, ga sarkin nan na tafiya a gabanku; kuma na tsufa da furfura; kuma, 'ya'yana maza na tare da ku. Nayi tafiya a gabanku daga ƙuruciyata har wa yau.

3Ga ni nan; ku yi shaida gãba da ni a gaban Yahweh da gaban shafaffensa. Saniyar wa na ɗauka? Jakin wa na ɗauka? Wane ne na yi wa damfara? Wane ne na tsanantawa? Daga hannun wa nakarɓi cin hanci don ya makantar da idanuna da shi? Ku shaida gãba da ni, kuma zan maido maku da shi."
4Suka ce, "Baka cuce mu ba, baka tsananta mana, ko ka saci wani abu daga hannun wani mutum ba."5ya ce masu, "Yahweh ne shaida gãba da ku, kuma shafaffensa shaida ne a yau, cewa ba ku sami komai ba a cikin hannuna." Suka mai da amsa, "Yahweh ne shaida."
6Sama'ila ya ce da mutanen, "Yahweh ne ya naɗa Musa da Haruna, wanda kuma ya fito da ubanninku daga ƙasar Masar.7Yanzu daga nan, ku miƙakanku, domin in yi roƙo tare da ku a gaban Yahweh game da dukkan ayyukan adalci na Yahweh, wanda ya yi domin ku da ubanninku.
8Da Yakubu ya zo Masar, kumakakanninku suka yi kuka ga Yahweh, daga nan Yahweh ya aika da Musa da Haruna, waɗanda suka bi dakakanninku fita daga Masar suka kuma zauna a wannan wuri.9Amma suka manta da Yahweh Allahnsu; ya sayar da su cikin hannun Sisera, shugaban sojojin Hãzo, cikin hannun Filistiyawa, kuma cikin hannun sarkin mutanen Mowab; dukkan waɗannan suka yi faɗa gãba dakakanninku.
10Suka yi kuka ga Yahweh suka kuma ce, 'Mun yi zunubi, saboda mun yashe da Yahweh kuma mun bauta wa Ba'aloli da Ashtatori. Amma yanzu ka cece mu daga hannun maƙiyanmu, kuma za mu bauta maka.'11Sai Yahweh ya aika da Yerub Ba'al, Bedan, Yefta, da Sama'ila, ya kuma ba ku nasara akan maƙiyanku dukka a kewaye da ku, yadda kuka zauna cikin tsaro.
12Da kuka ga Nahash sarkin mutanen Ammon yakawo maku hari, kuka ce mani, "A a! maimako, dole wani sarki ya yi mulki akanmu' - ko da ya ke Yahweh Allahnku, shi ne sarkinku.13Yanzu ga sarkin daku ka zaɓa, wanda kuka yi roƙo domin sa wanda kuma Yahweh ya naɗa sarki a bisanku.
14Idan ku na tsoron Yahweh, ku bauta masa, ku yi biyayya da muryarsa, kuma ba wai ku kangare ga dokokin Yahweh ba, daga nan ku dukka da sarkin da ke mulki a bisanku za ku zama masu bin Yahweh Allahnku.15Idan ba ku yi biyayya da muryar Yahweh ba, amma kukakangare ga dokokin Yahweh, daga nan hannun Yahweh zai yi gãba da ku, kamar yadda ya yi gãba dakakanninku.
16Ko yanzu ma ku miƙakanku kuma ku ga wannan babban abu wanda Yahweh zai yi a gaban idanunku.17Ba kamar alkama ba ce yau? Zan yi kira ga Yahweh, domin ya aiko da aradu da ruwan sama. Daga nan za ku sani ku kuma gani cewa muguntarku babba ce, wadda kuka aikata a idanun Yahweh, cikin roƙar wakanku sarki."18Sai Sama'ila ya yi kira ga Yahweh; a wannan rana kuma Yahweh ya aiko da aradu da ruwan sama. Daga nan dukkan mutanen suka ji tsoron Yahweh da Sama'ila ƙwarai.
19Daga nan dukkan mutanen suka ce da Sama'ila, "Ka yi addu'a domin bayinka ga Yahweh Allahnka, domin kada mu mutu. Gama mun ƙara wakanmu dukkan zunubanmu wannan muguntar cikin roƙo domin sarki domin kanmu."20Sama'ila ya maida amsa, "Kada ku ji tsoro. Kun yi dukkan wannan mugunta, ammakada ku juya ga Yahweh, amma ku bauta wa Yahweh da dukkan zuciyarku.21Kada ku juya zuwa holoƙan abubuwa waɗanda ba za su iya bada riba ko cetonku ba, saboda ba su da amfani.
22Domin albarkacin sunansa mai girma, Yahweh ba zai watsar da mutanensa ba, saboda ya gamshi Yahweh ya maida ku mutane domin kansa.23Game da ni, ya yi ne sa da ni in yi zunubi gãba da Yahweh ta wurin tsaida yin addu'a domin ku. Maimako, zan koyar da ku hanya da ke mai kyau kuma dai-dai.
24Kawai dai ku ji tsoron Yahweh kuma ku bauta masa cikin gaskiya da dukkan zuciyarku. Kuyi la'akari da manyan abubuwan da ya yi domin ku.25Amma idan kuka nace ga aikata mugunta, ku dukka da sarkinku zaku lalace."

13

1Saul na da shekaru talatin sa'ad da ya fara mulki; sa'ad da ya yi mulki shekaru arba'in a bisa Isra'ila,2ya zaɓi mutane dubu uku na Isra'ila. Dubu biyu suna tare da shi a Mikmash da kuma ƙasar tudu ta Betel, dubu ɗaya kuma suna tare da Yonatan a Gibiya ta Benyamin. Sauran sojojin ya aika da su gida, kowanne mutum zuwa rumfarsa.

3Yonatan yakayar da sansanin Filistiyawa da ke Geba Filistiyawa kuma suka ji haka. Daga nan Saul ya busa ƙaho cikin dukkan ƙasar, cewa, "Bari Ibraniyawa su ji."4Dukkan Isra'ila kuwa suka ji cewa Saul yakayar da sansanin Filistiyawa, da cewa kuma Isra'ila ta zama ɗoyi mai ruɓa ga Filistiyawa. Daga nan aka yi wa sojojin sammace tare su haɗu da Saul a Gilgal.
5Filistiyawa suka tattaru tare suyi faɗa gãba da Isra'ila: karusai dubu uku, mutane dubu shida suyi tuƙin karusan, rundunai kuma yawan su kamar rairayin da ke bakin teku. Suka zo sukakafa sansani a Mikmash, gabas da Bet Aben.
6Da mutanen Isra'ila suka ga cewa suna cikin matsala - domin mutanen sun ƙuntata, mutanen suka ɓoɓɓoye a kogonni, da ƙarƙashin zangarniyoyi, da duwatsu, da rijiyoyi, da ramuka.7Wasu Ibraniyawan suka tafi ƙetaren Yodan zuwa ƙasar Gad da Giliyad. Amma Saul yana Gilgal tukuna, dukkan mutanen kuma suka bi shi suna rawar jiki.
8Ya jira kwana bakwai, lokacin da Sama'ila ya tsaida. Amma Sama'ila bai zo Gilgal ba, mutanen kuma suna warwatsewa daga Saul.9Saul ya ce, "Kawo mani baikon ƙonawar da baye-bayen salamar." Daga nan ya miƙa baikon ƙonawar.10Nan da nan yana gama miƙa baikon ƙonawar Sama'ila ya iso. Saul ya fita domin ya same shi ya kuma gaishe shi.
11Daga nan Sama'ila ya ce, "Mene ne ka yi?" Saul ya maida amsa, "Da naga cewa mutanen na bari na, kuma cewa baka zo ba cikin lokacin da aka tsaida, kuma cewa Filistiyawa sun riga sun taru a Mikmash,12Na ce, 'Yanzu Filistiyawa zasu gangaro gãba da ni a Gilgal, kuma ban biɗi tagomashin Yahweh ba.' Sai na tilasta wakaina in miƙa baikon ƙonawar."
13Daga nan Sama'ila ya cewa Saul, "Ka yi wawanci. Baka kiyaye dokar Yahweh Allahnka ba wadda ya baka. Domin daga nan da Yahweh ya tabbatar da mulkin ka bisa Isra'ila har abada.14Amma yanzu mulkin ka ba zai ci gaba ba. Yahweh ya samo wani mutum bisa ga zuciyarsa, kuma Yahweh ya naɗa shi ya zama shugaba bisa mutanensa, saboda baka yi biyayya da abin da ya dokace ka ba."
15Daga nan Sama'ila ya tashi ya tafi ya haye daga Gilgal zuwa Gibiya ta Benyamin. Daga nan Saul ya lissafa mutanen da ke tare da shi, kimanin mutane ɗari shida.16Saul, da ɗansa Yonatan, da mutanen da ke tare da su, suka tsaya a Geba ta Benyamin. Amma Filistiyawan suka yi sansani a Mikmash.
17Mahaya suka zo daga sansanin Filistiyawa cikin ƙungiyoyi uku. ‌Ƙungiya ɗaya ta juya wajen Ofra, zuwa ƙasar Shuwal.18Wata ƙungiyar ta juya wajen Bet Horon, wata ƙungiyar kuma ta juya wajen kan iyakar da ke fuskantar kwarin Zeboyim wajen jeji.
19Babu wani maƙeri da aka iya samu cikin dukkan ƙasar Isra'ila, saboda Filistiyawan sun ce, "Idan ba haka ba Ibraniyawa zasu yi takubba da mãsu domin kansu."20Amma dukkan mutanen Isra'ila sukan je wurin Filistiyawa, kowanne domin ya wãsakayan aikin gonarsa, da addarsa, da gatarinsa, da laujensa.21Farashin kuwakashi biyu cikin uku ne na shekel akan kowanne washin bakin kayan aiki, da adduna, dakashi ɗaya cikin uku na shekel domin washin gatura, domin kuma miƙar da silkuna.
22Saboda haka a ranar yaƙi, babu takubba ko mãsu da aka samu a hannuwan ko ɗaya daga cikin sojojin da ke tare da Saul da Yonatan; Saul ne kaɗai da ɗansa Yonatan suke da su.23Sai sansanin Filistiyawa suka fita zuwa hanyar Mikmash.

14

1Wata rana, Yonatan ɗan Saul ya cewa saurayin da ke ɗauke da makamansa, "Zo, mu tafi zuwa sansanin Filistiyawa da ke ɗaya ɓarayin." Amma bai gaya wa mahaifinsa ba.

2Saul na zama a waje da Gibiya a ƙarƙashin itacen manta'uwa da ke cikin Migron. Wajen mutane ɗari shida na tare da shi,3har da Ahija ɗan Ahitub (ɗan'uwan Ikabod) ɗan Fenihas ɗan Eli, firist ɗin Yahweh a Shilo, wanda ya sanya falmara. Mutane ba su san cewa Yonatan ya tafi ba.
4A kowanne gefen hanyar inda Yonatan ya so ya bi domin yakai ga sansanin Filistiyawan, akwai dutse mai tsini a gefe ɗaya da kuma wani dutsen mai tsini a ɗayan gefen. ‌Ɗaya dutse mai tsinin a na kiran sa Bozez ɗaya kuma dutsen mai tsini a na kiran sa Sene.5‌Ɗ‌aya dutsen mai tsini yana tsaye a arewa a gaban Mikmash, ɗayan kuma a kudu a gaban Geba.
6Yonatan ya ce da saurayin da ke ɗauke da makamansa, "Zo, mu ƙetara sansanin waɗannan marasakaciyar. Zai yiwu cewa, Yahweh ya yi aiki a madadin mu, domin babu abin da zai tsaida Yahweh daga yin ceto ta wurin masu yawa ko mutane kaɗan."7Mai ɗaukar makamansa ya maida amsa, "Ka yi duk abin da ke cikin zuciyarka. Ka yi gaba, duba, ina tare dakai, in yi biyayya ga dukkan dokokinka."
8Daga nan Yonatan ya ce, "Za mu ƙetara zuwa ga mutanen, za mu kuma nunakanmu gare su.9Idan suka ce mana, 'Ku dakata nan har sai mun hauro gare ku'- daga nan za mu tsaya a wurinmu ba kuma za mu ƙetara zuwa gare su ba.10Amma idan suka maida amsa, 'Ku ƙetaro zuwa gare mu,' daga nan za mu ƙetara; saboda Yahweh ya bayar da su cikin hannunmu. Wannan ne zai zama alama a gare mu."
11Sai dukkan su suka bayyanakansu ga sansanin Filistiyawa. Filistiyawan suka ce, "Duba, Ibraniyawa na fitowa daga ramukan da suka ɓoye kansu."12Daga nan mutanen sansanin suka yi kira ga Yonatan da mai ɗaukar makamansa, suka ce kuma, "Ku zo gare mu, za mu kuma nuna maku wani abu." Yonatan ya ce da mai ɗaukar makamansa, "Bi yo bayana, saboda Yahweh ya bayar da su cikin hannun Isra'ila."
13Yonatan ya hau bisa hannuwansa da ƙafafunsa, mai ɗaukar makamansa kuma ya bi bayansa. Filistiyawa suka sha kisa a gaban Yonatan, kuma mai ɗaukar makamansa yakarkashe wasu bayansa.14Wannan hari na farko da Yonatan da mai ɗaukar makamansa sukakai, yakashe mutane ashirin a cikin yankin fili kimanin rabin Eka.
15akayi fargaba a sansanin, da cikin filayen, da kuma cikin mutane. Har sansanin da mahayansu suka yi fargaba. ‌Ƙ‌asa ta girgiza, aka kuma yi babbar fargaba.
16Daga nan matsaran Saul a Gibiya ta Benyamin suka duba; taron sojojin Filistiyawa na bajewa, kuma suna tafiya nan da can.17Daga nan Saul ya ce da mutanen da ke tare da shi, "Ku lissafa ku gani wane ne ya ɓace a cikinmu." Da suka yi lissafi, Yonatan da mai ɗaukar makamansa sun ɓace.
18Saul ya cewa Ahija, "Kawo akwatin Allah a nan," domin a lokacin yana tare da mutanen Isra'ila.19Yayin da Saul ke magana da firist, yamutsin a cikin sansanin Filistiyawa yana ci gaba kuma yana ƙaruwa. Daga nan Saul ya cewa firist, "Janye hannunka."
20Saul da dukkan mutanen da ke tare da shi suka jera kuma suka shiga cikin yaƙin. Kowacce takobin Bafaliste tayi gãba da mutumin garinta, aka kuma yi babbar rikicewa.21Yanzu waɗannan Ibraniyawa waɗanda dã suke tare da Filistiyawa, waɗanda kuma suka tafi tare da su cikin sansani, su ma kuma suka haɗe tare da Isra'ilawan da ke tare da Saul da Yonatan.
22Da mutanen Isra'ila waɗanda suka ɓoye kansu cikin tuddai kusa da Ifraim suka ji cewa Filistiyawa na tserewa, su ma suka bi bayansu cikin yaƙi.23Haka Yahweh ya ceto Isra'ila a wannan rana, Yaƙi kuma ya wuce har gaban Bet Aben.
24A wannan rana mutanen Isra'ila sukakasance cikin ƙunci saboda Saul ya sanya mutanen ƙarƙashin rantsuwa ya kuma ce, "La'ananne ne mutumin da yaci wani abin ci har sai da yamma kuma nayi ramuwa akan maƙiyana." Don haka babu wani cikin mayaƙan da ya ɗanɗana abinci.25Daga nan dukkan mutanen suka shi ga cikin jeji kuma akwai zuma a bisa ƙasar.26Da mutanen suka shiga cikin jejin, zuman ya malalo, amma babu wanda ya sanya hannunsa ga bakinsa domin mutanen sun ji tsoron rantsuwar.
27Amma Yonatan bai ji cewa mahaifinsa ya ɗaure mutanen tare da rantsuwa ba. Ya miƙa tsinin sandar da ke hannunsa ya luma cikin saƙar zuman. Ya ɗaga hannunsa zuwa bakinsa, idanunsa kuma suka wartsake.28Daga nan ɗaya daga cikin mutanen, ya amsa, "Mahaifinka ya yi wa mutane umarni mai tsanani tare da rantsuwa, ta wurin cewa, 'La'ananne ne mutumin da yaci abinci a wannan ranar,' ko da ya ke mutanen sun yi yaushi saboda yunwa.
29Daga nan Yonatan ya ce, "Mahaifina ya aiwatar da matsala a ƙasar. Kalli yadda idanuna suka wartsake saboda na ɗanɗanakaɗan daga cikin zuman nan.30Yaya kuma in da mutanen yau sun ci a sake daga cikin ganima daga maƙiyansu da suka samo? Saboda yanzu kisan bai yi yawa ba a cikin Filistiyawa."
31Sukakaiwa Filistiyawa hari a wannan rana daga Mikmash zuwa Aiyalon. Mutanen suka gaji sosai.32Mutanen suka afka da haɗama bisa ganimar suka kuma ɗauki tumaki, da shanu da maruƙa, suka kuma yanka su a ƙasa. Mutanen suka cinye su tare da jinin.
33Daga nan suka gayawa Saul, "Duba, mutanen suna zunubi gãba da Yahweh ta wurin ci tare da jinin." Saul ya ce, "Kun aikata rashin aminci. Yanzu, a gangaro da wani babban dutse nan a gare ni."34Saul ya ce, "Fita cikin mutanen, ku kuma gaya masu, 'Bari kowanne mutum yakawo sansa da tunkiyarsa, ya yanka su a nan, ya kuma ci. Kada kuyi zunubi gãba da Yahweh ta wurin ci tare da jinin."' Sai kowanne mutum yakawo sansa tare da shi a wannan dare ya kuma yanka a wurin.
35Saul ya gina bagadi ga Yahweh, shi ne kuma bagadi na farko da ya gina ga Yahweh.
36Daga nan Saul ya ce, "Bari mu runtumi Filistiyawa da dare mu kuma warwatsa su har wayewar gari; kada mu bar ko ɗayan su da rai." Suka amsa, "Kayi duk abin da ya yi kyau a gare ka." Amma firist ɗin ya ce, "Bari mu kusanci Allah a nan."37Saul ya tambayi Allah, "In runtumi Filistiyawa? Zaka bayar da su cikin hannun Isra'ila?" Amma Allah bai amsa masa ba a wannan ranar.
38Daga nan Saul ya ce, "Ku zo nan, dukkan ku shugabannin mutane; ku koya ku kuma duba yadda wannan zunubin ya faru a yau.39Domin, da wanzuwar Yahweh, wanda ke ceton Isra'ila, ko ma idan yana cikin Yonatan ne ɗana, tabbas zai mutu." Amma ba ko ɗaya daga cikin jama'ar daga cikin dukkan mutanen ya amsa masa.
40Daga nan ya ce da dukkan Isra'ila, "Dole ku tsaya gefe ɗaya ni da Yonatan ɗana kuma mu tsaya gefe ɗaya." Mutanen suka ce da Saul, "Ka yi abin da ya yi kyau a gare ka."41Saul ya ce, Yahweh, Allah na Isra'ila! Idan ni ne na yi wannan zunubin ko kuma ɗana ne Yonatan ya yi shi, daga nan, Yahweh, Allah na Isra'ila, ka bada Urim. Amma idan wannan zunubi mutanenka Isra'ila ne suka aikata shi"Ka bada Tummim." Sai Yonatan da Saul aka ɗauka ta ƙuri'a, amma mayaƙan sukakaucewa Zaɓen.42Daga nan Saul ya ce, "akaɗa ƙuri'u tsakani na da Yonatan ɗa na." Daga nan aka ɗauki Yonatan ta ƙuri'a.
43Daga nan Saul ya ce wa Yonatan, "Gaya mani abin daka yi." Yonatan ya gaya masa, "Na ɗanɗana zumakaɗan dakarshen sandar da ke hannuna. Ga ni nan; zan mutu."44Saul ya ce, "Allah ya yi haka kuma fiye ma a gare ni, idan baka mutu ba, Yonatan."
45Daga nan mutanen suka cewa Saul, "Yonatan ya mutu kuwa, wanda ya aiwatar da wannan babbar nasara ga Isra'ila? Ya yi nesa da shi! da wanzuwar Yahweh, ba bu ko gashi ɗaya bisakansa da zai faɗi ƙasa, gama ya yi aiki tare da Allah a yau." Haka mutanen suka kuɓutar da Yonatan yadda bai mutu ba.46Daga nan Saul ya tsaida runtumar Filistiyawa, kuma Filistiyawan suka tafi na su wurin.
47Da Saul ya fara mulki bisa Isra'ila, ya yi yaƙi gãba da maƙiyansa ta kowanne gefe. Ya yi yaƙi gãba da Mowab, Ammoniyawa, Idom, da sarakunan Zoba, da Filistiyawa. Duk inda ya juya, yana azabta horo akansu.48Ya yi aiki da ƙarfin hali mai girma yakayar da Amalekawa. Ya kuɓutar da Isra'ila daga hannuwan waɗanda suka washe su.
49'Ya'yan Saul maza su ne Yonatan, Ishbi, da Malkishuwa. Sunayen 'ya'yansa mata biyu kuwa su ne Merab, ta fari, da Mikal, ƙaramar.50Sunan matar Saul shi ne Ahinowam; ita ce ɗiyar Ahimãz. Sunan shugaban sojojinsa kuwa Abna ɗan Nã, kawun Saul.51Kish ne mahaifin Saul; Nã kuma, mahaifin Abna, shi ne ɗan Abiyel.
52An yi yaƙi mai tsanani gãba da Filistiyawa dukkan kwanakin Saul. Idan Saul ya ga wani ƙaƙƙarfan mutum, ko mutum mai ƙwazo, sai ya jawo shi a gare shi.

15

1Sama'ila ya cewa Saul, "Yahweh ya aiko ni in shafe ka sarki bisa mutanensa Isra'ila. Yanzu ka saurari maganganun Yahweh.2Wannan ne abin da Yahweh mai runduna ya ce, 'Na lura da abin da Amalek ya yiwa Isra'ila cikin tsayayya da su a bisa hanya, sa'ad da suka fito daga cikin Masar.3Yanzu ka je kakai hari ga Amalek ka kuma lalata duk abin da suke da shi ɗungum. Kadaka raga masu, ammaka kashe su maza da mata, yaro da jariri, saniya da tunkiya, raƙumi da jaki."'

4Saul ya tattaro mutanen ya ƙidaya su a birnin Telem: mutane dubu ɗari bisa ƙafa, da mutanen Yahuda dubu goma.5Daga nan Saul ya zo cikin birnin Amalek ya kuma jira a cikin kwari.
6Daga nan Saul ya cewa Keniyawa, "Ku je, ku tafi, ku fito daga cikin Amalekawa, domin kada in lalatar da ku tare da su. Domin kun nuna halin kirki ga dukkan mutanen Isra'ila, sa'ad da suka zo daga Masar." Sai Keniyawa suka wãre daga Amalekawa.7Sai Saul yakai hari ga Amalekawa, daga Habila har ya zuwa Shur, wadda ke gabas da Masar.
8Daga nan ya ɗauki Agag sarkin Amalekawa da rai; gaba ɗaya ya lalatar da dukkan mutanen dakaifin takobi.9Amma Saul da mutanen suka bar Agag, duk da mafi kyau daga cikin tumaki, da shanu, da maraƙai masu ƙiba, da raguna. Kowanne abu da ke da kyau, ba su lalatar ba. Amma gaba ɗaya suka lalatar da duk wani abu wulaƙantacce marar amfani kuma.
10Daga nan maganar Yahweh ta zo ga Sama'ila, cewa,11"Ya ba ni ɓacin rai cewa na naɗa Saul sarki, domin ya juya baya daga bi na bai kuma aiwatar da dokokina ba." Sama'ila ya fusata; ya yi kuka ga Yahweh dukkan dare.
12Sama'ila ya farka da wurwuri domin ya sami Saul da safe. Aka cewa Sama'ila, "Saul ya tafi Kamel kuma yakafa wakansa wurin tunawa, daga nan ya juya kuma ya ci gaba zuwa Gilgal."13Daga nan Sama'ila ya zo wurin Saul, Saul kuma ya ce masa, "Mai albarka ne kai daga Yahweh! Na cika dokar Yahweh."
14Sama'ila ya ce, "Daga nan mene ne wannan kukan tumakin a kunnuwa na, da kukan shanun da na ke ji?"15Saul ya maida amsa, "An kawo su ne daga Amalekawa. Domin mutanen sun keɓe mafi kyau daga cikin tumakin da shanun, domin hadaya ga Yahweh Allahnka. Sauran gaba ɗaya mun hallakar da su."16Daga nan Sama'ila ya cewa Saul, "Jira, kuma zan faɗi maka abin da Yahweh ya ce mani da daren nan." Saul ya ce masa, "Yi magana!"
17Sama'ila ya ce, "Koda ya ke kai ƙarami ne a idanunka, ba an mai she ka shugaban kabilun Isra'ila ba? Daga nan Yahweh ya shafe ka sarki bisa Isra'ila,18Yahweh kuma ya aike ka bisa hanyarka ya kuma ce, 'Je kuma gaba ɗayaka hallakar da masu zunubi, Amalekawa, ka kuma yi faɗa gãba da su har sai sun hallaka.'19Me yasa baka yi biyayya da muryar Yahweh ba, amma a maimako ka ƙwato ganimaka kuma yi abin da ke mugunta a gaban Yahweh?"
20Daga nan Saul ya cewa Sama'ila, "Lallai na yi biyayya da muryar Yahweh, kuma na tafi bisa hanyar da Yahweh ya aike ni. Nakamo Agag, sarkin Amalek, kuma gaba ɗaya na hallakar da Amalekawa.21Amma mutanen suka ɗauko wasu daga cikin ganimar - tumaki da shanu, abubuwa mafi kyau da aka keɓe ga hallakarwa, domin hadaya ga Yahweh Allahnka a Gilgal."
22Sama'ila ya maida amsa, "Yahweh yana gamsuwa da baye-baye na ƙonawa da hadayu, fiye da biyayya da muryar Yahweh? Biyayya tafi hadaya, kuma saurare ya fi kitsen raguna.23Domin tawaye kamar zunubin tsafi ya ke, taurin kai kumakamar mugunta da ƙazanta. Sabodaka yi watsi da maganar Yahweh, shi ma ya ƙika da ga zama sarki."
24Daga nan Saul ya cewa Sama'ila, "Na yi zunubi; domin nakarya dokar Yahweh da maganganunka, saboda ina jin tsoron mutanen na kuma yi biyayya da muryarsu.25Yanzu, ina roƙon kaka yafe zunubina, ka kuma juyo tare da ni domin in yi sujada ga Yahweh."
26Sama'ila ya cewa Saul, "Ba zan koma tare dakai ba; domin ka yi watsi da maganar Yahweh, Yahweh kuma ya ƙika da zama sarki bisa Isra'ila."27Yayin da Sama'ila ya juya domin ya tafi, Saul ya riƙe haɓar rigarsa, ta kuma yage.
28Sama'ila ya ce masa, "Yahweh ya yage sarautar Isra'ila daga gare ka a yau ya kuma bayar da ita ga makwabcinka, wani wanda ya fi ka.29Haka kuma, ‌Ƙarfin Isra'ila ba zai yi ƙarya ba ko ya canza ra'ayinsa; domin shi ba mutum ba ne, da zai canza ra'ayinsa."
30Daga nan Saul ya ce, "Na yi zunubi. Amma ina roƙon kaka darajanta ni yanzu a gaban dattawan mutanena da gaban Isra'ila. Ka sake juyowa tare da ni, domin in yi sujada ga Yahweh Allahnka."31Sai Sama'ila ya sake juyowa bayan Saul, Saul kuma ya yi sujada ga Yahweh.
32Daga nan Sama'ila ya ce, "Kawo Agag sarkin Amalekawa nan wurina." Agag ya zo gare shi ɗaure cikin sarƙoƙi ya kuma ce, "Tabbas ɗacin mutuwa ya wuce."33Sama'ila ya maida amsa, "Kamar yadda takobin ka ta maida mata marasa 'ya'ya, haka mahaifiyarka za ta zama marar ɗa a cikin mata." Daga nan Sama'ila ya datse Agag gunduwa-gunduwa a gaban Yahweh a Gilgal.
34Sama'ila ya tafi Rama, Saul kuma ya tafi gidansa a Gibiya ta Saul.35Sama'ila bai sake ganin Saul ba har sai ranar mutuwarsa, gama ya yi makoki domin Saul. Yahweh ya yi baƙinciki da cewa ya naɗa Saul sarki bisa Isra'ila.

16

1Yahweh ya cewa Sama'ila, "Har yaushe zaka yi makoki domin Saul, tunda nayi watsi da shi daga zama sarki bisa Isra'ila? Ka cika ƙahonka da mai ka kuma tafi. Zan aike ka ga Yesse na Betlehem, domin na zaɓar wakaina sarki cikin 'ya'yansa maza."

2Sama'ila ya ce, "Yaya zan tafi? Idan Saul ya ji haka, zai kashe ni." Yahweh ya ce, "Ka ɗauki maraƙi tare dakai ka kuma ce, 'Na zo in yi hadaya ga Yahweh.'3Ka kira Yesse zuwa hadayar, zan kuma nuna maka abin da zaka yi. Zaka shafe mani wanda zan gaya maka."
4Sama'ila ya yi yadda Yahweh ya faɗi ya kuma tafi Betlehem. Dattawan birnin suna rawar jiki yayin da su ka zo suka same shi suka kuma ce, "Kana zuwa cikin salama?"5Ya ce, "Cikin salama; Na zo in yi hadaya ga Yahweh. Ku shirya ku keɓe kanku ku kuma zo tare da ni wurin hadayar." Daga nan ya ware Yesse da kuma 'ya'yansa maza ya kuma gayyace su zuwa hadayar.
6Da suka zo, yakalli Iliyab ya kuma faɗi wakansa cewa shafaffe na Yahweh ba bu shakka yana tsaye a gaba na.7Amma Yahweh ya cewa Sama'ila, "Kadaka dubi siffarsa ta zahiri, ko tsawon ƙirarsa; saboda na ƙi shi. Domin Yahweh ba ya duba yadda mutum ke duba wa; mutum yanakallon siffa a zahiri, amma Yahweh yanakallon zuciya."
8Daga nan Yesse ya kira Abinadab ya kuma sa ya gitta a gaban Sama'ila. Daga nan Sama'ila ya ce, "Wannan ma Yahweh bai zaɓe shi ba."9Yesse daga nan yasa Shamma ya gitta, amma Sama'ila ya ce, "Wannan ma Yahweh bai zaɓe shi ba."10Yesse yasa 'ya'yansa maza bakwai suka gitta a gaban Sama'ila. Daga nan Sama'ila ya cewa Yesse, "Yahweh bai zaɓi ɗaya daga cikin waɗannan ba."
11Daga nan Sama'ila ya cewa Yesse, "Dukkan 'ya'yanka maza suna nan?" Ya maida amsa, "Akwai ƙaramin su da ya rage, amma yana lura da tumaki." Sama'ila ya cewa Yesse, "Ka aika akawo shi; domin ba za mu zauna ba har sai ya zo nan."12Yesse ya aika aka zo da shi ciki. Yanzu dai wannan ɗa jã ne da kyawawan idanu da kyakkyawar siffa. Yahweh ya ce, "Tãshi, shafe shi; domin shi ne."
13Daga nan Sama'ila ya ɗauki ƙahon mai ya kuma shafe shi a tsakiyar 'yan uwansa. Ruhun Yahweh ya afko bisa Dauda daga wannan rana har zuwa gaba. Daga nan Sama'ila ya tashi ya kuma tafi Rama.
14Yanzu Ruhun Yahweh ya bar Saul, ruhu mai illa kuma daga Yahweh yana azabtar da shi a maimako.15Bãyin Saul suka ce masa, "Duba, ruhu mai illa daga Allah na azabtar dakai.16Bari ubangijinmu yanzu ya umarci bãyinsa waɗanda ke tsaye a gabanka su nemo mutum wanda ya kware a kiɗin garaya. Daga nan idan ruhu mai illa daga Allah yana bisanka, zai kaɗa ta kuma zaka sami lafiya."
17Saul ya cewa bãyinsa, "Ku samo mani mutum da ya iyakaɗa wa sosai ku kumakawo mani shi."18Daga nan ɗaya daga cikin samarin ya amsa, ya kuma ce, "Na ga wani ɗan Yesse Betlehemiye, wanda ya kware akaɗa wa, ƙaƙƙarfa, mutum mai ƙarfin hali, mutumin yãƙi, mai tattali a zance, mutum mai asali; kuma Yahweh yana tare da shi."19Sai Saul ya aika da manzanni wurin Yesse, ya kuma ce, "Ka aiko mani da ɗanka Dauda, wanda ke tare da tumaki."
20Yesse ya ɗauki jaki danƙare da gurasa, da salkar inabi, da 'yar akuya, ya kuma aika da su tare da ɗansa Dauda wurin Saul.21Daga nan Dauda ya zo wurin Saul ya kuma shiga hidimarsa. Saul ya ƙaunace shi sosai, ya kuma zama mai ɗaukar makamansa.
22Saul ya aika wa Yesse, cewa, "Bari Dauda ya tsaya a gabana, domin ya sami tagomashi a idanu na."23Duk sa'ad da ruhu mai illa daga Allah yana bisan Saul, Dauda zai ɗauki garaya ya kumakaɗa ta. Sai Saul ya wartsake ya kuma yi lafiya, kuma ruhu mai illar sai ya tafi daga gare shi.

17

1Yanzu Filistiyawa suka tara rundunarsu domin yaƙi. Suka taru a Soko, wacce take ta Yahuda. Suka yi sansani tsakanin Soko da Azeka, cikin Ifes Dammim.

2Saul tare da mutanen Isra'ila suka taru sukakafa sansani a kwarin Ila, suka jã layin dãga dominsu fuskanci Filistiyawa.3Filistiyawa suka tsaya a bisa dutse a sashen gefe, Isra'ila kuma na bisa dutse a wancan gefen a kwari da ke tsakaninsu.
4Wani mutum mai ƙarfi ya fito daga cikin sansanin Filistiyawa, mutum mai suna Goliyat daga Gat, wanda tsayinsa kãmu shida ne da rabi.5Yana da hular tagulla a bisakansa, yana kuma sanye da tufafin yaƙi. Rigar nada nauyin Shekel dubu biyar na tagulla.
6Yana sanye da makarin ƙafa na tagulla da kuma mãshi na tagulla a tsakiyar kafaɗunsa.7Sandar mashinsa na da girma, da tausasshen igiya domin harba takamar dirkar masaka. Kan mashinsa na da nauyin shekel na ƙarfe ɗari shida. Mai ɗaukar masa garkuwa na a gaba da shi.
8Ya tsaya ya yi ihu ga sojojin Isra'ilawa, "Donme kuka fito waje kukakafa sansanin yaƙi? Ni ba Bafiliste ba ne, ku kuma ba bayi ne na Saul ba? Ku zaɓa wakanku mutum kuma bari ya sauko gare ni.9Idan ya iya faɗa da ni ya kumakashe ni, sa'an nan zamu zama bayinku. Amma idan na kãda shi na kumakashe shi, sai ku zama bayinmu ku kuma bauta mana."
10Sai kuma Bafilisten ya ce, "Na ƙalubalanci rundunar Isra'ila yau. Ku ba ni wanda zamu yi faɗa tare."11Lokacin da Saul da dukkan Isra'ila suka ji abin da Bafilisten ya faɗi, sai sukakaraya da babban tsoro.
12Yanzu dai Dauda ɗan Ifraimiye ne na Betlehem cikin Yahuda, mai suna Yesse. Yana da 'ya'ya maza takwas. Yesse tsohon mutum ne a cikin kwanakin Saul, tsoho ne tukub a tsakanin mutane.13Manyan 'ya'ya maza na Yesse suna tare da Saul a filin dãga. Sunayen 'ya'yansa maza uku da suka tafi bakin dãga su ne Iliyab wanda shi ne ɗan fari, na biyun Abinadab, sai na ukun Shammah.
14Dauda shi ne ɗan ƙaraminsu. Yayyensa uku suka bi Saul.15Yanzu dai Dauda yana fita yana shigowa gaba da baya tsakanin rundunar Saul da kuma tumakin babansa a Betlehem, domin ya ciyar da su.16Kwana arba'in mai ƙarfin nan Bafilisten yana zuwa gaba safiya da yamma domin ya miƙakansa ga yaƙi.
17Sai Yesse ya cewa ɗansa Dauda, "Ka ɗauko wa 'yan uwanka mudu 22 na wannan gasasshen hatsin da kuma wannan gurasar goma, ka kuma ɗauko su da sauri kakai su sansani zuwa ga 'yan'uwanka.18Ka kuma ɗauki curin man shanu goma ga shugabansu na dubu. Ka duba lafiyar 'yan'uwankaka kuma dawo da tabbacin suna lafiya.
19'Yan'uwanka suna tare da Saul da dukkan mazajen Isra'ila a cikin kwarin Ila, suna yaƙi da Filistiyawa."20Dauda ya tashi da sassafe ya bar garken cikin hannun wani makiyayi domin ya kula da su. Ya ɗauki abincin ya tafi, kamar yadda Yesse ya umarce shi. Ya iso sansani lokacin da rundunar ke fitowa zuwa filin dãga suna sowa ta yaƙi.21Sa'an nan Isra'ila da Filistiyawa sukakafa layi domin dãga, runduna gãba da juna.
22Dauda ya bar kayayyakinsa ajiya wurin maitsaron kayayyaki, ya ruga da gudu zuwa wurin rundunar, ya gaida 'yan'uwansa.23Yayin da ya ke cikin magana da su, mutumin mai ƙarfin, Bafilisten na Gat, mai suna Goliyat, ya kuma fito daga cikin rundunar Filistiyawa, ya kuma furta maganganun da ya ke furtawakamar da farko, Dauda kuwa ya ji su.24A lokacin da dukkan Isra'ila suka ga mutumin, suka yi gudu daga wurinsa kuma suka ji tsoro matuƙa.
25Mazajen Isra'ila suka ce, "Ko kun ga wannan mutumin wanda ya fito? Ya fito domin ya cakuni Isra'ila. Sarki zai bai wa duk wadda yakashe shi dukiya mai yawa. kuma zai ba da ɗiyarsa gare shi ya aura, Kuma za ya raba gidan ubansa daga biyan haraji a Isra'ila."
26Dauda ya cewa mutanen da ke tsaye kusa da shi, "Mene ne za a yiwa mutumin da yakashe wannan Bafilisten domin yakawar da kunya ga Isra'ila? Wane ne wannan Bafilite marar kaciya da har ya ke rena rundunar Allah mai rai?"27Sai mutanen suka furta abin da suka faɗa tun farko kuma suka ce masa, "Haka za a yiwa mutumin da yakashe shi."
28Iliyab babban ɗan'uwansa ya ji sa'ad da ya yi magana da mutanen. Sai fushin Iliyab ya yi ƙuna a bisa Dauda, sai ya ce, "Mene ne dalilin da yasaka gangaro nan wurin? A hannun wane ne ka baro 'yan tumakan nan cikin jeji? Na san girman kanka, da kuma fahariyar zuciyarka; domin ka gangaro nan domin kayi kallon yaƙi ne."29Dauda ya ce, "Mene ne na yi yanzu? Ba tambayakawai na yi ba?"30Ya juya ya bar shi zuwa wurin wani, ya sake irin magana a yadda ya yi dã. Mutanen suka amsa masakamar dã.
31Da aka ji maganganun da Dauda ya faɗa, sojoji suka maimaita su ga Saul, shi kuwa ya aika akakawo Dauda.32Sai Dauda ya cewa Saul. "Kada zuciyar kowanne mutum takaraya sabili da wancan Bafilisten; bawanka zai tafi ya yi faɗa da wannan Bafilisten."33Saul ya cewa Dauda, "Ba zaka iya fãɗawa Bafilisten nan ba domin ka yi faɗa da shi; gamakai matashi ne, amma shi mutum ne mayaƙi tun yana saurayi."
34Amma Dauda ya cewa Saul, "Bawanka yana kula da tumakin mahaifinsa. Lokacin da zaki ko damisa ya taso ya ɗauki 'yar akuya daga cikin garken,35nakan bisu in kumakai masu farmaki, in kuma ƙubutar da shi daga bakinsa. Lokacin da zai tayar mani, nakama shi a gemunsa, na buga shi, na kumakashe shi.
36Bawanka yakashe zaki da damisa. Wannan Bafilisten marar kaciya zai zamakamar ɗayansu, tunda ya ƙalubalanci rundunar Allah mai rai."
37Dauda ya ce, "Yahweh ya ƙubutar da ni daga hannun zaki da kuma hannun damisa. Za ya ƙubutar da ni daga hannun wannan bafilisten." Sa'an nan Saul ya cewa Dauda, "Je ka, bari kuma Yahweh yakasance tare dakai."38Saul ya sanya wa Daudakayan yaƙinsa. Yasa masa hular tagulla akansa, ya kuma sanya masa mayafin wayoyi.
39Dauda ya ɗaura takobinsa a rigar yaƙi. Amma yakasa tafiya ciki, domin baya yi koyi da su ba. Sai Dauda ya cewa Saul, "Ba zan iya fita in yi faɗa da wannan kaya ba, gama ban yi koyo da su ba." Saboda haka Dauda ya kwaɓe kayan.40Ya ɗauki sandar kiwonsa cikin hannunsa ya kuma zaɓi duwatsu biyar daga cikin rafi; ya zuba su cikin jakarsa ta kiwo. Majajjawarsa na cikin hannunsa sa'ad da ya fuskanci Bafilisten.
41Bafilisten ya rugo zuwa wurin Dauda, da mai ɗaukar masa makamai a gabansa.42A lokacin da Bafilisten ya juya ya kuma ga Dauda, sai ya rena shi, gama ɗan yaro ne kawai, kuma jã, mai asalin siffa.43Sai Bafilisten ya cewa Dauda, "Ni kare ne, da zaka zo gare ni da sanduna?," sai kuma Bafilisten ya la'anci Dauda da allolinsa.
44Bafilisten ya cewa Dauda, "Zo gare ni, zan kuma bada namanka ga tsunytsayen sammai ga kuma namomin jeji."45Dauda kuwa ya amsa wa Bafilisten, "Kai kana zuwa gare ni da takobi, da mashi, da kibiya. Amma na zo gare ka a cikin sunan Yahweh mai runduna, Allah na rundunar Isra'ila, wandaka rena.
46Yau Yahweh zai ba ni nasara bisanka, zan kumakashe ka in kuma cire kanka daga jikinka. Yau zan miƙɑ gawawakin rundunar Filistiyawa ga tsuntsayen sammai ga kuma namomin jeji na ƙasa, saboda dukkan duniya ta san cewa akwai Allah a Isra'ila,47kuma dukkan wannan taro su san cewa Yahweh ba ya ba da nasara ta dalilin takobi ko mãshi. Gama yaƙin na Yahweh ne, kuma za ya miƙaka cikin hannunmu."
48A lokacin da Bafilisten ya tashi ya kuma taso ga Dauda, sai Dauda ya rugo da sauri zuwa ga rundunar magabcin domin ya gamu da shi.49Dauda yasa hannunsa cikin jaka, ya ɗauko dutse daga ciki, sai ya jefi Bafilisten a tsakiyar goshi, sai ya faɗi a fuskarsa ƙasa.
50Dauda ya ci nasara ga Bafilisten da majajjawa da dutse. Ya jefe Bafilisten ya kumakashe shi. Babu takobi cikin hannun Dauda.51Sai Dauda ya sheƙa a guje ya kuma tsaya a bisa Bafilisten ya kuma dauƙe takobinsa, ya zaro ta daga gidanta, yakashe shi, ya datse kansa da ita. A lokacin da Filistiyawa suka ga cewa mutuminsu mai ƙarfi ya mutu, suka gudu.
52Sai mazajen Isra'ila da na Yahuda suka tashi da sowa, suka kuma runtumi Filistiyawa har zuwa kwari da ƙofofin Ekron. Matattun Filistiyawa suka kwanta akan hanya zuwa Sharem, hanyar zuwa Gat da Ekron.53Mutanen Isra'ila suka dawo daga runtumar Filistiyawa, suka kuma washe sansaninsu.54Dauda ya ɗauki kan Bafilisten yakawo shi Yerusalem, amma ya ajiye rigar yaƙinsa a tasa rumfar.
55Da Saul ya ga Dauda ya fita gãba da Filistiyawa, ya cewa Abna, shugaban runduna, "Abna, yaron wane ne wannan matashin?" Abna ya ce, "Ranka ya daɗe, sarki, ban sani ba."56Sarkin ya ce, "Ka tambayi waɗanda suna iya sani, ɗan wane ne."
57Da Dauda ya dawo daga kisan Filistiyawan, Abna ya ɗauke shi, yakawo shi wurin Saul tare dakan Bafilisten a cikin hannunsa.58Saul ya ce masa, "Kai ɗan wane ne, ɗan saurayi?" Dauda ya amsa, "Ni yaron bawanka ne Yesse mutumin Betlehem."

18

1Bayan da ya gama magana da Saul, sai ran Yonatan ya manne wa ran Dauda, Yonatan kuwa ya ƙaunace shi kamar ransa.2Saul ya ɗauki Dauda zuwa cikin hidimarsa a wannan rana; baya barshi ya koma gidan mahaifinsa ba.

3Sai Yonatan da Dauda suka yi alƙawari da juna na abokantaka domin Yonatan ya ƙaunace shi kamar ransa.4Yonatan ya tuɓe rigarsa wadda ya ke yãfe da ita ya kuma ba Dauda tare da rigar yaƙinsa, har da takobinsa, bakansa, da kuma maɗaurinsa.
5Dauda ya tafi duk inda Saul ya aike shi, kuma ya ci nasara. Saul ya maida shi kai bisa mazajen yaƙi. Wannan ya ƙayatar a idanun dukkan mutanen da kuma idanun bayin Saul.
6Da suka dawo daga hallaka Filistiyawan, matayen suka fito daga dukkan biranen Isra'ila, suna raira waƙa da rawa, su taryi Saul, dakacakaura, da farinciki, da kumakayan kiɗe-kiɗe.7Matayen suka riƙa yin waƙa da juna sa'ad da suke kaɗawa. Suka raira: "Saul yakashe dubbansa, Dauda kuma dubbansa goma."
8Saul ya ji haushi ƙwarai, kuma wannan waƙa ta baƙanta masa rai. Ya ce, "Sun ba Dauda dubbai goma, amma ni sun ba ni dubbai kawai. To mene ne ya rage masa idan ba mulkin ba?"9Saul kuwa daga wannan rana ya fara yi wa Daudakallon rashin yarda.
10washegari wani mugun ruhu daga wurin Allah ya saukar wa Saul ya kuma yi hauka cikin gidan. Sai Dauda yakaɗa garayarsa, kamar yadda ya saba kowacce rana. Saul yana ɗauke da mashi cikin hannunsa.11Saul ya jefa mashin, gama ya yi tunani, "Zan tsire Dauda ga bango." Amma Dauda ya tsira daga gaban Saul sau biyu kamar haka.12Saul ya ji tsoron Dauda, gama Yahweh na tare da shi, amma baya kuma tare da Saul.
13Sai Saul ya fitar da shi daga gabansa ya kuma maishe shi shugaban dubu. Da haka Dauda ya dinga fita yana shigowa a fuskar mutanen.14Dauda ya yi nasara a dukkan hanyoyinsa, gama Yahweh na tare da shi.
15Da Saul ya ga yana ci gaba, sai ya ji tsoronsa.16Amma dukkan Isra'ila da Yahuda suka ƙaunaci Dauda, gama yana fita yana shigowa a idanunsu.
17Sai Saul ya cewa Dauda, "Ga babbar ɗiyata Merab. Zan baka ita ta zama matarka. Sai dai ka yi mazakutta dominaka kuma yi yaƙin Yahweh." Gama Saul ya yi tunani, "Kada hannuna ya tayar masa, amma bari hannun Filistiyawa ya sauka bisansa."18Dauda ya cewa Saul, "Ni wane ne, kuma su wane ne 'yan uwana, ko gidan mahaifina cikin Isra'ila, da zan zama suruki ga sarki?"
19Amma a lokacin da Merab, ɗiyar Saul, yakamata a bada ita ga Dauda, sai aka bada ita ga Adriyel mutumin Meholat ta zama matarsa.
20Amma Mikal, ɗiyar Saul, ta ƙaunaci Dauda. Suka gaya wa Saul, wannan kuma ya yiwa Saul daɗi.21Sai Saul ya ce a zuciyarsa, "Zan ba da ita gare shi, domin ta zama tarko a gare shi, kuma hannun Filistiyawa ya yi gãba da shi." Saboda haka Saul ya cewa Daudakaro na biyu, "Zaka zama surukina."
22Saul ya umarce bayinsa, "Ku yi magana da Dauda a asirce, ku ce, 'Duba, sarki yana jin daɗinka, kuma dukkan bayinsa suna ƙaunar ka. To yanzu, ka zama surukin sarki."'
23Saboda haka bayin Saul suka furta waɗannan maganganu ga Dauda. Sai Dauda ya ce, "Ko ƙaramin abu ne gare ku zaman surukin sarki, ganin cewar ni talaka ne, kuma ba sananne ba?"24Bayin Dauda suka mayar wa Saul da maganganun da Dauda ya faɗa.
25Sai Saul ya ce, "Ku faɗi wannan ga Dauda, 'Sarki ba ya buƙatar wani sadãki, sai dai fatar loɓar Filistiyawa ɗari daya, da za a rama daga maƙiyan sarki."' Yanzu Saul ya yi tunani dai yasa Dauda ya mutu ta hannun Filistiyawa.26Da bayinsa suka gaya wa Dauda waɗannan maganganu, sai ya yiwa Dauda dai-dai ya zama surukin sarki.
27Kafin waɗanan kwanaki su wuce, Dauda ya tafi tare da mazajensa ya kumakashe Filistiyawa ɗari biyu. Dauda ya dawo da fatar loɓarsu, sai aka miƙa su cikakku ga sarki, domin ya zama surukin sarki. Sai Saul ya ba Dauda Mikal ɗiyarsa ta zama matarsa.28Da Saul ya gani, ya kuma sasance da cewa Yahweh na tare da Dauda, kuma Mikal, ɗiyar Saul, ta ƙaunace shi,29Saul ya ƙara jin tsoron Dauda. Saul ya ci gaba da zama magabcin Dauda.
30Sai sarakunan Filistiyawa suka fito domin yaƙi, kamar dai yadda suke fitowa, hakannan Dauda ya ke nasara fiye da dukkan bayin Saul, har sunansa ya zama abin girmamawa.

19

1Saul ya cewa Yonatan ɗansa da kuma dukkan bayinsa cewa su kashe Dauda. Amma Yonatan, ɗan Saul, ya yi fahariya da Dauda.2Saboda haka Yonatan ya gaya wa Dauda, "Saul mahaifina na neman yakashe ka. Saboda hakaka yi zaman tsaro da safe ka kuma ɓoye kanka a boyayyen wuri.3Zan fita in tsaya kusa da mahaifina cikin fili a indakake, zan kuma yi magana da mahaifina game dakai. Idan na ji wani abu akanka, zan gaya maka."

4Yonatan ya yi maganar alheri game da Dauda ga Saul mahaifinsa ya kuma ce masa, "Bari kada sarki ya yi laifi ga bawansa Dauda. Gama ba ya yi maka laifi ba, kuma ayyukansa masu kyau sun kawo maka alheri.5Gama ya ɗauki ransa cikin hannunsa ya kumakashe Bafilisten. Yahweh yakawo babbar nasara ga dukkan Isra'ila. Ka gani ka kuma yi murna. Donme zaka yi zunubi ga jinin marar laifi da zakakashe Dauda babu dalili?"
6Saul ya saurari Yonatan. Saul ya rantse, "Har ga Allah, ba zai kashe shi ba."7Sai Yonatan ya kira Dauda, sai kuma Yonatan ya gaya masa dukkan waɗannan abubuwan. Yonatan kuma yakawo Dauda wurin Saul, yana kuma tsayawa a gabansakamar dã.
8Sai aka sake yin yaƙi, Dauda kuma ya fita ya yi faɗa da Filistiyawa ya kuma ci nasara da su da babbar hallaka. Suka gudu daga fuskarsa.9Wani mugun ruhu daga wurin Yahweh ya saukar wa Saul da ya ke zaune a gidansa da mashinsa cikin hannunsa, kuma yayin da Dauda ke kaɗakayan kiɗinsa.
10Saul ya yi koƙarin tsire Dauda har ga bango da mashinsa, amma ya tsere daga gaban Saul, har Saul yakafe mashin cikin bangon. Dauda ya gudu ya tsere a wannan dare.11Saul ya aika da manzanni zuwa gidan Dauda su kula da shi domin yakashe shi da safe. Mikal, matar Dauda, ta ce masa, "Idan baka ceci ranka a wannan daren ba, gobe za akashe ka."
12Saboda haka Mikal ta zura Dauda ta tãga. Ya tafi ya gudu, ya tsere.13Mikal ta ɗauki gunkin gida ta ajiye bisa gado. Sai ta sanya matashin kai na gashin akuya akansa, ta kuma rufe shi dakayayyaki.
14Da Saul ya aika 'yan saƙo su ɗauko Dauda, ta ce, "Yana barci."15Sai Saul ya aika 'yan saƙo su ga Dauda; ya ce, "Ku kawo mani shi akan gadon, domin in kashe shi."
16A lokacin da 'yan saƙon suka shigo ciki, gashi, gunkin gida na bisakan gado bisa matashin kai mai gashi na ɗan rago a bisakansa.17Saul ya cewa Mikal, "Donme ki ka ruɗe ni har ki ka bar makiyina ya tafi, har ya tsira?" Mikal ta amsa wa Saul, "Ya ce mani, 'Bar ni in tafi. Donme zan kashe ka?"
18Yanzu Dauda ya gudu ya kuma tsira, ya tafi wurin Sama'ila a Rama ya kuma gaya masa dukkan abin da Saul ya yi masa. Sa'annan shi da Sama'ila suka tafi suka zauna a Nayot.19Aka gaya wa Saul, cewa, "Duba, Dauda na Nayot cikin Rama."20Sai Saul ya aika da 'yan saƙo su kamo Dauda. Da suka ga taron annabawa na annabci, Sama'ila kuma na tsaye a matsayin shugabansu, sai Ruhun Allah ya sauko bisa 'yan saƙon Saul, sai su ma suka yi annabci.
21Da aka gaya wa Saul wannan, sai ya aika da wasu 'yan saƙon, sai suma suka yi anabci. Sai Saul ya sake aikawa da wasu 'yan saƙo kãro na uku, sai suma suka yi anabci.22Sai shi ma ya tafi Rama ya zo wurin rijiya mai zurfi da ke a Seku. Ya yi tambaya, "Ina Sama'ila da Dauda?" Wani ya ce, "Duba, suna a Natot cikin Rama."
23Saul ya tafi Nayot a Rama. Sai Ruhun Allah ya sauko bisansa, yayin da ya ke tafiya ya yi ta anabci har ya iso Nayot a Rama.24Ya tuɓe rigunansa ya kuma yi anabci a gaban Sama'ila. Ya kwanta tsirara dukkan rana da dukkan dare. Shi yasa suke tambaya, "Wai Saul na ɗaya daga cikin annabawa ne?"

20

1Sai Dauda ya gudu daga Nayot a Rama ya kuma zo ya cewa Yonatan, "Me na yi? Mene ne laifina? Mene ne zunubina ga mahaifinka, da ya ke neman ɗaukan raina?"2Yonatan ya cewa Dauda, "Sam ba haka ba ne; ba zaka mutu ba. mahaifina ba ya yin wani abu mai girma ko ƙanƙani ba tare da ya gaya mani ba. Donme mahaifina zai ɓoye mani wannan abu daga gare ni? Ba haka ba ne."

3Duk da haka Dauda ya sake rantsuwa kuma ce, "Mahaifinka ya san da cewar na sami tagomashi a idanunka. Dama ya ce, 'Kada a bari Yonatan ya san wannan, don kada ya damu.' Amma tabbas tun da Yahweh na raye, kumakamar yaddakaimaka ke rayuwa, rãtakaɗan ne tsakani na da mutuwa."
4Sai Yonatan ya cewa Dauda, "Duk abin daka ce, zan yi maka."5Dauda ya cewa Yonatan, "Gobe ne sabon wata, kuma yakamata in zauna wurin cin abinci da sarki. Ammaka bar ni in tafi, domin in ɓoye kaina cikin saura har kwana na uku da yamma.
6Idan mahaifinka ya damu game da ni sarai, sai kace, 'Dauda ya nemi izini daga wajena domin ya tafi Betlehem birninsa. Domin lokacin hadaya ta shekara ce ga dukkan dangin.'7Idan ya ce, 'lafiya lau,' bawanka zai sami salama. Amma idan ya husata ƙwarai, to ka sani ya ƙudurci aikata mugunta.
8Saboda hakaka kyauta wa bawanka. Gamaka jawo bawanka cikin alƙawari na Yahweh tare dakai. Amma idan akwai zunubi cikina, kakashe ni dakanka; gama mene ne dalilin da zai saka kawo ni ga mahaifinka?"9Yonatan ya ce, "Sam haka ba zai yiwu ba! Idan na gane mahaifina yana da niyyar cutar dakai, ba zan gaya maka ba?"
10Sai Dauda ya cewa Yonatan, "wane ne zai gaya mani idan ya zama cewa mahaifinka ya amsa maka da faɗa?"11Yonatan ya cewa Dauda, "Zo, mu tafi cikin saura." Sai suka tafi cikin saura tare su biyu.
12Yonatan ya cewa Dauda, "Bari Yahweh, Allah na Isra'ila, ya zama shaida. A lokacin da zan tambayi mahaifina gobe war haka, ko rana ta uku, duba, idan akwai shirin alheri game da Dauda, ba zan aika gare ka in kuma sanar dakai ba?13Idan ya gamshi mahaifina da ya cutar dakai, bari Yahweh ya yi wa Yonatan har fiye kuma idan ban sanar dakai in kuma sallame kaka tafi ba, domin ka tafi cikin salama. Bari Yahweh yakasance tare dakai, kamar yadda ya ke tare da mahaifina.
14Idan ina nan da rai, ba zaka nuna mani amintaccen alƙawarin Yahweh ba, domin kada in mutu?15Kadaka datse amintaccen alƙawarinka daga gidana har abada- koda Yahweh ya datse kowanne magabcin Dauda daga fuskar ƙasa.16Saboda haka Yonatan ya yi alƙawari da gidan Dauda ya kuma ce, "Bari Yahweh ya nemi lissafi daga hannun magabtan Dauda."
17Yonatan yasa Dauda ya yi rantsuwa kuma domin ƙaunar da ya ke kaunarsa, gama yanakaunarsakamar yadda ya ke kaunar ransa.18Sai Yonatan ya ce masa, "Gobe ne sabon wata. Za a yi kewarka domin mazauninka zai zama babu kowa.19Bayan ka zauna can har kwana uku, sai ka sake komawa can indaka ɓoye kanka a lokacin da al'amuran ke ci gaba, ka tsaya kusa da dutsen Ezel.
20Zan harba kibiyoyi uku gefensa, kamar ina auna inda nakeso in harba.21Daga nan zan aika ɗan matashina in kuma ce masa, 'Tafi ka nemo kibiyoyin.' Idan na cewa ɗan yaron, 'Duba, kibiyoyin suna wannan gefenka; nemo su."; sai ka zo; gama akwai kariya dominka kuma ba cutarwa, na rantse da ran Yahweh.
22Amma idan na ce wa matashin, 'Duba, kibiyoyin suna can gaba dakai,' sai ka yi tafiyarka, gama Yahweh ya sallame ka.23Amma batun alƙawarin da ni dakai mu ka furta, gama, Yahweh na tsakani na dakai har abada."
24Sai Dauda ya ɓoye kansa cikin saura. Lokacin da sabon wata ya fito, sarkin ya zauna domin cin abinci.25Sarkin ya zauna a bisa kujerarsa, yadda ya saba, a bisa kujera ta jikin bango. Yonatan ya tashi, Abna kuma ya zauna ta gefen Saul. Amma kujerar Dauda babu kowa.
26Duk da haka Saul baya ce komai ba wannan rana, domin ya yi tunani, "Wani abin ne ya faru da shi. Ba shi da tsarki; tabbas ba shi dai da tsarki."27Amma a rana ta biyu, ranar bayan sabon wata, wurin zaman Dauda babu kowa. Saul ya cewa Yonatan ɗansa, "Me yasa ɗan Yesse bai zo ya ci abinci jiya da yau ba?"
28Yonatan ya amsa wa Saul, "Dauda ya nemi izini sosai daga wurina domin ya tafi Betlehem.29Ya ce, 'Na roƙe ka. Gama iyalina na da hadaya a birni, kuma ɗan'uwana ya umarce ni da in kasance. Yanzu, idan na sami tagomashi a idanunka, Na roƙe ka bari in je in ga 'yan'uwana. Saboda wannan dalili yasa bai zo kujerar sarki ba."
30Sai haushin Saul ya yi ƙuna bisa Yonatan, ya kuma ce masa, "Kai ɗan lalatacciya, mace mai tayarwa! Ashe ban sani baka zaɓi ɗan gidan Yesse ga kunyarka, ga kuma kunyar tsiraicin mahaifiyarka?31Idan har ɗan Yesse na a raye a ƙasar, ko kai ko mulkinka ba zai kafu ba. To yanzu, ka aika akawo shi gare ni, gama dole ne ya mutu."
32Yonatan ya amsa wa mahaifinsa, "Da wane dalili za akashe shi? Me ya yi?"33Sai Saul ya jefa mashinsa don yakashe shi. Sai Yonatan ya gane cewa mahaifinsa ya ƙudurta yakashe Dauda.34Yonatan ya tashi ya bar teburin cikin hasalar fushi baya kuma ci abinci ba a rana ta biyu ga watan, gama yana baƙinciki saboda Dauda, domin mahaifinsa ya wulaƙanta shi.
35Da safe, Yonatan ya fita zuwa saura inda suka shirya su haɗu da Dauda, kuma ɗan saurayin na tare da shi.36Ya cewa ɗan saurayin, "Ka yi gudu ka nemi kibiyoyin da na harba." Yayin da ɗan saurayin ya ruga, ya harba wata kibiyar gaba da shi.37Lokacin da ɗan saurayin ya iso inda kibiyar da Yonatan ya harba ta sauka, Yonatan ya kira ɗan saurayin, ya ce, "Ba kibiyar na gabanka ba?"
38Sai Yonatan ya kirawo ɗan saurayin, "Yi sauri, hanzarta, kadaka tsaya!" Sai ɗan saurayin Yonatan ya tattara kibiyoyin ya dawo wurin ubangidansa.39Amma ɗan saurayin bai san komai ba. Yonatan da Dauda ne kaɗai suka san zancen.40Yonatan ya ba ɗan saurayin makamansa ya ce masa, "Tafi, kakai su cikin birnin."
41Ba da jimawa ba bayan tafiyar ɗan saurayin, Dauda ya fito daga bayan dutsen, ya kwanta fuskarsa ƙasa, ya durƙusa ƙasa har sau uku. Suka yi wa juna sumba da kuka tare, Dauda ya yi kuka sosai.42Yonatan ya cewa Dauda, "Ka tafi cikin salama, gama mu biyu mun rigaya mun rantse da sunan Yahweh muka kuma ce, 'Bari Yahweh yakasance tsakanin kai da ni, kuma tsakanin zuriyata da zuriyarka, har abada."' Sa'an nan Dauda ya tashi tsaye ya tafi, Yonatan kuma ya koma cikin birnin.

21

1Sa'an nan Dauda ya zo Nob domin ya ga Ahimelek babban firist. Ahimelek yazo domin ya taryi Dauda jikinsa na rawa ya kuma ce masa, "Donme kake kai kaɗai kuma babu wani tare dakai?"2Dauda ya cewa Ahimelek babban firist, "Sarki ya aike ni wata hidima ya kuma ce da ni, 'Kada kowa yasan komai game da abin nan da na aike ka, da kuma abin da na umarce ka.' Na aike 'yan matasan wani wurin.

3Yanzu dai me kake da shi a hannu? Ba ni 'yar gurasa guda biyar, ko duk abin da ke samuwa."4Firist ya amsa wa Dauda ya kuma ce, "Babu gurasa da ba a tsarkake ba, amma akwai gurasa mai tsarki- Idan 'yan samarin sun keɓe kansu daga mata."
5Dauda ya amsa wa firist, "Tabbas mata sun yi nisa da mu tun kwana uku da suka wuce, kamar yadda ya ke idan na fita. Abin da ke na mazajen an keɓe su har ma game da ɗan ƙanƙanin hidimomi. Balle irin wannan na yau lalle duk abin da suke da shi za a keɓe!"6Saboda haka sai firist ya ba shi gurasa da aka keɓe. Gama babu wata gurasa a wurin sai dai gurasar bagadi, wadda aka cire daga wurin Yahweh, domin ya sanya gurasa mai zafi a wurinta a ranar da aka ɗauke ta.
7Yanzu dai ɗaya daga cikin bayin Saul yana nan a wannan rana, tsararre a gaban Yahweh. Sunansa Doweg mutumin Idom, shugaban makiyayan Saul.
8Dauda ya cewa Ahimelek, "Yanzu babu wani mashi ko takobi? Domin ban kawo takobi ko makamaina tare da ni ba, domin hidimar sarki na buƙatar hanzari."9Firist ya ce, "takobin Goliyat Bafiliste, wandaka kashe a cikin kwarin Ila, tana nan nannaɗe cikin kaya a bayan falmara. Idan kana so ka ɗauki wannan, ka ɗauke ta, gama babu wani makami a nan." Dauda ya ce, "Babu wata takobi irin wannan; ba ni ita."
10Dauda ya tashi ya gudu daga wurin Saul a wannan rana ya kuma tafi wurin Akish, sarkin Gat.11Bayin Akish suka ce masa, "Ba wannan ba ne Dauda, sarkin ƙasar? Ba sun yi waƙa da rawa ga juna dominsa ba, 'Saul yakashe nasa dubbai, Dauda kuma yakashe nasa dubbai goma?"
12Dauda ya ajiye waɗannan maganganu cikin zuciyarsa yana kuma jin tsoran Akish, sarkin Gat.13Sai ya canza yanayinsa ya yi kamar marar hankali cikin hannuwansu; sai ya yi alamomi a bisa ƙofofin kyamaren ya kuma bar yawu na zubowa ƙasa zuwa gemunsa.
14Sai Akish ya cewa bayinsa, "Duba, ku ga mutumin na hauka. Donme kukakawo shi wurina?15Ko na rasa mahaukatan mutane ne, har da zaku kawo mani wannan talikin yana yin wannan hali a gabana? Anya wannan taliki zai shigo cikin gidana?"

22

1Sai Dauda ya bar can ya kuma tsere zuwa ƙogon Adullam. A lokacin da 'yan'uwansa da dukkan gidan mahaifinsa suka ji haka, sai suka gangara zuwa wurinsa.2Duk wanda ke cikin ƙunci, da duk wanda ke cikin bãshi, da kuma marar jin daɗi-dukkansu suka taru wurinsa. Dauda ya zama shugabansu. An sami mazaje kamar ɗari huɗu tare da shi.

3Sai Dauda ya bar wurin zuwa Mizfa cikin Mowab. Ya cewa sarkin Mowab, "Na roƙe kaka bar mahaifina da mahaifiyata su zauna dakai har sai na san abin da Allah zai yi mani."4Sai ya bar su tare da sarkin Mowab. Mahaifinsa da mahaifiyarsa suka zauna tare da shi dukkan kwanakin da Dauda ke cikin sansaninsa.5Sai annabi Gad ya cewa Dauda, "Kadaka tsaya a sansaninka. Tashi ka kuma shiga cikin ƙasar Yahuda." Sai Dauda ya bar wurin ya kuma tafi cikin jejin Heret.
6Saul ya ji cewa an ga Dauda, tare da mutanen da ke tare da shi. A yanzu dai Saul yana a Gibiya ƙarƙashin itaciyar tamarisk a Rama, da mashinsa a hannu, kuma dukkan bayinsa na tsaye zagaye da shi.
7Saul ya cewa bayinsa da ke tsaye zagaye da shi, "Ku saurara yanzu, mutanen Benyamin! Ko ɗan Yesse zai ba kowannenku filayen zaitun ne? Zai maida ku dukka shugabannin dubbai da shugabannin ɗari,8domin misanyar dukkan ku don tayar mani? Babu wani daga cikin ku da ya gaya mani lokacin da ɗa na ya yi alƙawari da ɗan Yesse. Babu waninku da ya ji tausayi na. Babu waninku da ya gaya mani cewar ɗana ya zuga bawana Dauda gãba da ni. Yau ya ɓoye yana jirana domin su kai mani farmaki."
9Sai Doweg mutumin Idom, wanda ya tsaya kusa da bayin Saul, ya amsa, "Na ga ɗan Yesse ya iso Nob, wurin Ahimelek ɗan Ahitub.10Ya yi addu'a ga Yahweh don ya taimake shi, kuma ya bashi guziri da kuma takobin Goliyat Bafiliste."
11Sai sarki ya aiki wani domin yakawo Ahimelek Firist ɗan Ahitub da dukkan gidan mahaifinsa, su firistocin da ke a Nob. Dukkansu suka zo wurin sarkin.12Saul ya ce, "Saurara yanzu, ɗan Ahitub." Ya amsa, "Ga ni nan, ubangidana."13Saul ya ce masa, "Donme ka yi mani makirci, kai da ɗan gidan Yesse, har ka ba shi gurasa, da takobi, ka kuma yi addu'a ga Allah domin ya taimake shi, domin ya tayar mani, ya ɓoye a asirce, kamar yadda ya ke yi a yau?"
14Sai Ahimelek ya amsa wa sarki ya kuma ce, "Wane ne cikin dukkan bayinka da ke amintacce kamar Dauda, wanda ya ke surukin sarki kuma shugaba bisa 'yan tsaro, kuma ana girmama shi cikin gidanka?15Yau ne na fara yi masa addu'a Allah ya taimake shi? Nesa da ni! Kada sarki ya sanya wa bawansa wani laifi ko ga dukkan gidan mahaifina. Gama bawanka bai san komai ba game da wannan batu."
16Sarki ya amsa, "Dole ka mutu, Ahimelek, kai da gidan mahaifinka."17Sarki ya cewa mai tsaron da ke tsaye kusa da shi, "Ka juyaka kashe firistocin Yahweh. Domin hannunsu na tare da Dauda, kuma domin sun san ya gudu, amma ba su gaya mani ba." Amma bayin sarkin ba su iya ɗibiya hannunsu su kashe firistocin Yahweh ba.
18Sa'an nan ya cewa Doweg, "Juyaka kashe firistocin." Sai Doweg Ba-Idome ya juya ya fãɗawa firistocin; yakashe mutum tamanin da biyar waɗanda suke yafe da falmarar linin a wannan rana.19Dakaifin takobi, ya abkawa Nob, birnin firistocin, mazaje da mataye, yara da jarirai, kuma bijimai da jakai da tumakai yakashe su dukka dakaifin takobi.
20Amma ɗaya daga cikin 'ya'yan Ahimelek ɗan Ahitub, mai suna Abiyata, ya tsere ya gudu zuwa wurin Dauda.21Abiyata ya gaya wa Dauda cewar Saul yakashe firistocin Yahweh.
22Dauda ya cewa Abiyata, "Na sani a wannan ranar, da Doweg Ba-Idome ke wajen, zai faɗa wa Saul. Ni ke da laifi domin mutuwar kowanne a cikin iyalin mahaifinka!23Ka zauna tare da ni kumakadaka ji tsoro. Gama wanda ya ke neman ranka shi ke neman nawa kuma. Zaka zauna lafiya tare da ni."

23

1Aka gaya wa Dauda, "Ga shi, Filistiyawa na yaƙar Keila kuma suna washe wurin shiƙar hatsi."2Sai Dauda ya yi addu'a ga Yahweh domin taimako ya kuma tambaye shi, "Ko na tafi in kai wa waɗannan Filistiyawan farmaƙi? Yahweh ya cewa Dauda, "Tafi kakai wa Filistiyawa farmaƙi ka ƙubutar da Keila."

3Mazajen Dauda suka ce masa, "Duba, muna jin fargaba a nan Yahuda. Balle wai har mu tafi Keila Gãba da rundunar Filistiyawa?"4Sai Dauda ya yi addu'a ga Yahweh domin taimako kuma. Yahweh ya amsa, "Ka tashi, gangara zuwa Keila. Gama zan baka nasara a bisa Filistiyawan."
5Dauda da mutanensa suka tafi Keila suka kuma yi yaƙi da Filistiyawa. Ya kora garkunansu ya kuma buga su da babban yanka. Da haka Dauda ya kuɓutar da mazaunan Keila.6Lokacin da Abiyata ɗan Ahimelek ya gudu zuwa wurin Dauda a Keila, ya zo da falmara a hannunsa.
7Aka gaya wa Saul cewa Dauda ya tafi Keila. Saul ya ce, "Allah ya ba da shi cikin hannuna. Gama yana tsare domin ya shiga cikin birnin da ke da ƙofofi da ƙyamare."8Saul ya tattara dukkan rundunarsa domin yaƙi, don ya gangara zuwa Keila, don ya kewaye Dauda da mutanensa.9Dauda na sane da cewar Saul na ƙulla cuta gãba da shi. Ya cewa Abiyata firist, "Kawo falmara nan."
10Sai Dauda ya ce, "Yahweh, Allah na Isra'ila, bawanka tabbas ya ji cewa Saul na shirin zuwa Keila, ya lallatar da birnin sabili da ni.11Mutanen Keila zasu bashe ni cikin hannunsa? Saul zai gangaro, kamar yadda bawanka ya ji? Yahweh, Allah na Isra'ila, na roƙe ka, ka gaya wa bawanka." Yahweh ya ce, "Zai gangaro ya zo."
12Sai Dauda ya ce, "Mutanen Keila zasu miƙa ni da mazaje na cikin hannun Saul?" Yahweh ya ce, "Zasu miƙaka."
13Sai Dauda tare da mazajensa, da suke kamar ɗari shida, suka tashi suka fita daga Keila, suka kuma tafi daga wancan wuri zuwa wancan wurin. Aka gaya wa Saul da cewar Dauda ya kubce daga cikin Keila, daga nan kuma ya fãsa bin sa.14Dauda ya zauna cikin ƙarfafan wuraren tsaro cikin jeji, a cikin ƙasar duwatsu cikin hamada ta Zif. Saul ya nace da nemansa kowacce rana, amma Allah bai miƙa shi cikin hannunsa ba.
15Dauda yaga cewar Saul ya fito neman ransa; a yanzu dai Dauda na cikin Hamadar Zif a Horesh.16Sa'an nan Yonatan, ɗan Saul, ya tashi ya tafi wurin Dauda a Horesh, ya kuma ƙarfafa hannunsa cikin Allah.
17Ya ce masa, "Ka daka ji tsoro. Gama hannun Saul mahaifina ba zai same ka ba. Zaka zama sarki bisa Isra'ila, ni kuma zan zama na kusa dakai. Saul mahaifina shi ma ya san da haka."18Suka yi alƙawari a gaban Yahweh. Dauda ya zauna a Horesh, Yonatan kuma ya tafi gida.
19Sai Zifiyawa suka zo wurin Saul a Gibiya suka ce, "Ba a wurinmu Dauda ya ke ɓuya ba cikin ƙarfafan wuraren tsaro na Horesh, a bisa tudun Hakila, wanda ya ke kudu da Yeshimon?20Yanzu ka zo, sarki! Bisa ga buƙatarka, ka zo! Namu fannin shi ne mu miƙa shi a hannun sarki."
21Saul ya ce, "Bari Yahweh ya albarkace ku. Gama kun ji tausayina.22Ku tafi, ku tabbatar da hakan. Ku lura ku gane inda ya ke ɓuya da kuma wane ne ya gan shi a wurin. An gaya mani cewa yana da wayau ƙwarai.23Sai ku lura, ku kuma fahimci dukkan wuraren da ya ke ɓoye kansa. Ku dawo gare ni da tabbataccen zance, sa'an nan zan tafi tare da ku. Idan yana cikin ƙasar, zan binciko shi waje daga dukkan dubban Yahuda."
24Sai suka tashi suka riga Saul zuwa Zif. Yanzu Dauda da mazajensa suna a cikin hamadar Mawon, a cikin Araba zuwa Kudu da Yeshimon.25Saul da mutanensa suka tafi neman shi. Amma aka gaya wa Dauda wannan, sai ya tafi zuwa tudun duwatsu ya kuma zauna a hamadar Mawon. Lokacin da Saul ya ji, ya runtumi Dauda zuwa hamadar Mawon.
26Saul ya bi ta wancan sashen tudun, Dauda kuma da mazajensa na tafiya a wancan sashen tudun. Dauda ya hanzarta ya guje wa Saul. Da Saul da mutanensa na kewaye da Dauda da mazajensa don su kama su,27sai ɗan saƙo ya iso wurin Saul ya kuma ce, "Hanzartaka kuma zo, gama Filistiyawa sun kawo hari a ƙasar."
28Saboda haka Saul ya komo daga bin Dauda ya kuma tafi gãba da Filistiyawa. Saboda haka ake kiran wurin Dutsen Tsira.29Dauda ya tafi daga nan ya kuma zauna cikin ƙarfafan wuraren tsaro na Engedi.

24

1Lokacin da Saul ya komo daga bin Filistiyawa, aka gaya masa, "Dauda na cikin Hamadar Engedi."2Sai Saul ya ɗauki mazaje zaɓaɓɓu dubu uku daga dukkan Isra'ila ya tafi neman Dauda da mazajensa a bisa Duwatsu na Awakin jeji.

3Ya zo wurin mazamnin awakai nakan hanya, a inda akwai kogo. Saul ya shiga ciki don ya rufe ƙafarsa. Yanzu Dauda da mazajensa na zama a can ƙarshen ƙurewar kogon.4Mazajen Dauda suka ce masa, "Wannan ita ce ranar da Yahweh ya yi magana da ya ce maka, 'Zan bã da maƙiyanka cikin hannunka, don ka yi masa duk abin daka ga dama."' Sai Dauda ya tashi a hankali yana tafiya gaba a rarrafe ya kuma yanko sashen rigar Saul.
5Daga baya sai zuciyar Dauda ta dame shi domin ya yagi sashen rigar Saul.6Ya cewa mazajensa, "Yahweh ya sauwaƙe da yiwa ubangidana haka, shafaffen Yahweh, har da zan miƙa hannu gãba da shi, ganin cewar shafaffe ne na Yahweh."7Don haka sai Dauda ya tsauta wa mazajensa da waɗannan maganganu, kuma bai bar su su kai wa Saul farmaƙi ba. Saul ya tashi, ya fita daga cikin kogon, yakama hanyarsa.
8Bayan haka, Dauda shi ma ya tashi, ya fita daga cikin kogon, ya yi kira ga Saul: "Ubangidana sarki." Lokacin da Saul ya waiga bayansa, sai Dauda ya rusuna da fuskarsa ƙasa ya nuna masa bangirma.9Dauda ya ce wa Saul, "Me yasakake sauraron mutanen da ke cewa, 'Duba, Dauda yana neman ya cutar dakai?'
10Yau ka ga yadda Yahweh ya miƙaka cikin hannuna sa'ad da muke a cikin kogon. Wasu suka ce mani in kashe ka, amma na bar ka. Na ce, 'Ba zan miƙa hannuna gãba da ubangidana ba; gama shafaffe ne na Yahweh.'11Duba, mahaifina, dubi sashen rigarka a hannuna. Ai ko yadda na yanki sashen rigarka amma ban kashe ka ba, kana iya fahimta da ganin cewa babu wata mugunta ko makirci cikin hannuna, kuma ban yi maka zunubi ba, ko da ya ke kana neman rainaka ɗauke.
12Bari Yahweh ya shar'anta tsakanina dakai, kuma bari Yahweh ya sãka mani gãba dakai, amma hannuna ba zai tayar maka ba.13Kamar yaddakarin maganar mutanen dã ke cewa, 'Daga cikin mugu mugunta ke fitowa.' Amma hannuna ba za ya tayar maka ba.
14Wane ne sarki ke fita neman sa? Wane ne kake kora? Mataccen kare! Wofi!15Bari Yahweh ya zama mai shari'a ya kuma shar'anta tsakani na dakai, ya kuma tabbatar, ya kuma tsaya mani ya kuma sa in tsira daga hannunka."
16Bayan da Dauda ya gama furta waɗannan maganganun ga Saul, Saul ya ce, "Muryarka ce wannan, ɗana Dauda?" Saul ya tãda muryarsa ya yi kuka.
17Ya ce wa Dauda, "Kai mai adalci ne fiye da ni. Gamaka sake biya na da alheri, inda na maido maka mugunta.18Ka furta yau yaddaka yi mani alheri, gama baka kashe ni ba lokacin da Yahweh ya miƙa ni ga jinƙanka.
19Domin idan mutum ya sami maƙiyinsa, zai bar shi ya tafi lafiya? Bari Yahweh ya sãka maka da alheri yaddaka yi mani a yau.20Yanzu, na sani tabbas zaka zama sarki kuma sarautar Isra'ila zatakafu a hannunka.
21Ka rantse mani har ga Yahweh cewar ba zaka datse zuriyata bayana ba, kuma ba zaka lallatar da sunana daga gidan mahaifina ba.22Sai Dauda ya yi alƙawari ga Saul. Sa'an nan Saul ya tafi gida, amma Dauda da mazajensa suka haura zuwakagara mai ƙarfi.

25

1Yanzu dai Sama'ila ya mutu. Dukkan Isra'ila suka taru tare suka kuma yi masa makoki, suka kuma binne shi a cikin gidansa a Rama. Sa'an nan Dauda ya tashi ya kuma tafi cikin hamadar Faran.

2Akwai wani mutum a Mawon, wanda dukiyarsa na cikin Karmel. Mutumin mai arziki ne ainun. Yana da tumakai dubu uku da awakai dubu ɗaya. Yana sausayar gashin tumakinsa akamel.3Sunan mutumin Nabal, kuma sunan matarsa Abigel. Mata ce mai hikima da kyan gani. Amma mutumin mai zafin hali da mugun tafarki ne a al'amuransa. Shi daga zuriyar gidan Kaleb ne.
4Dauda ya ji daga cikin hamada cewa Nabal yana sausayar gashin tumakinsa.5Don haka Dauda ya aika samari mutum goma. "Ku tafi zuwakamel, ku tafi wurin Nabal, ku gaishe shi da sunana.6Za ku ce masa, 'Ka zauna cikin wadata. Salama gare ka salama ga gidanka, kuma salama ga dukkan mallakarka.
7Na ji cewakana da 'yan sausaya. Makiyayanka na tare da mu, kuma bamu cutar da su ba, basu kuma rasa komai ba cikin dukkan lokacin da suke akarmel.8Ka tambayi samarinka, zasu kuma gaya maka. Yanzu bari 'yan samarina su sami tagomashi a idanunka, gama mun kawo ga ranar buki. Na roƙe kaka bã da duk abin dakake da shi a hannunka ga bayinka ga kuma ɗan ka Dauda."
9Lokacin da samarin Dauda suka iso, suka faɗi dukkan wannan ga Nabal a madadin Dauda suka kuma jira.10Nabal ya amsa wa bayin Dauda, "Wane ne Dauda, kuma wane ne ɗan Yesse? Akwai bayi da yawa da ke ƙaurace wa iyayen gidansu a wannan kwanaki.11To na ɗauki gurasata da ruwa na da namana da na yanka domin 'yan sausayata, in kuma bada su ga mutanen da ban san ko daga ina suke ba?"
12Saboda haka 'yan samarin Dauda suka juya suka tafi suka kuma dawo, suka kuma gaya masa duk abin da aka ce.13Dauda ya cewa mazajensa, "Kowanne mutum ya ɗaura takobinsa." Sai kowanne mutum ya ɗaura takobinsa. Dauda shi ma ya ɗaura takobinsa. Mazajen wajen ɗari huɗu suka bi Dauda, ɗari biyu kuma suka tsaya wurin kayayyaki.
14Amma ɗaya daga cikin 'yan samarin ya gaya wa Abigel, matar Nabal; ya ce, "Dauda ya aiko da manzanni daga cikin hamada domin su gaishe da ubangidanmu, amma ya zage su.15Kuma mazajen sun nuna mana alheri. Ba mu cutu ba kuma ba mu ɓatar da komai ba cikin dukkan tafiyar da muka yi da su lokacin da muke cikin filaye.
16Sun zama ganuwa a garemu da rana da dare, dukkan lokutan da muke tare da su muna kula da garken.17Saboda haka ki san wannan ki kuma san abin da zaki yi, gama akwai shirin mugunta game da ubangidanmu, kuma gãba da dukkan gidansa. Shi mutum ne marar cancanta da ba mai iya shawartar sa."
18Sai Abigel ta tashi da sauri ta ɗauki gurasa curi ɗari biyu, inabi kwalba biyu, tumakai guda biyar gyararru, awo biyar na busasshen hatsi, da curin kauɗar inabi guda ɗari, da wainar 'ya'yan ɓaure guda ɗari biyu, ta ɗora su bisa jakai.19Ta cewa matasanta, "Ku sha gabana, zan kuma bi ku a baya." Amma bata gaya wa mijinta Nabal ba.
20Yayin da take zuwa bisa jakinta ta kuma sauka daga bakin ƙofar dutsen, Dauda da shi da mazajensa suna saukowa zuwa gare ta, ta kuma tarbe su.
21Yanzu Dauda ya riga ya faɗa cewa, "Tabbas a banza na tsare dukkan mallakar wannan mutum cikin hamada, har babu abin da ya ɓace cikin dukkan abin da ke nasa, kuma sai ya sãka mani da mugunta.22Bari Allah ya yi mani haka, Dauda, fiye da haka kuma, idan war haka da safe na bar ko da namiji ɗaya wanda ke nasa."
23Lokacin da Abigel ta ga Dauda, ta hanzarta ta sauko daga jakarta ta kuma kwanta a gaban Dauda da fuskarta ƙasa ta kuma rusunar dakanta zuwa ƙasa.24Ta kwanta dab da ƙafafunsa ta kuma ce, "akainakaɗai, ubangidana, laifin yakasance. Na roƙe ka bari baiwarka ta yi magana dakai, ka kuma saurari maganganun baiwarka.
25Kada ubangidana ya kula da wannan talikin marar amfani, Nabal, gama yadda sunansa ya ke, haka ya ke. Nabal ne sunansa, kuma sakarci na tare da shi. Amma ni baiwarka ban ga 'yan samarin ubangidana ba, waɗandaka aiko.26Yanzu dai, ubangidana, a bisa ran Yahweh, da kuma ranka, har tun da Yahweh ya tsare ka daga zubda jini, kuma daga ramuwa domin kanka da hannunka, yanzu bari maƙiyanka, da waɗanda ke neman yin mugunta ga ubangidana, su zamakamar Nabal.
27Yanzu bari wannan kyautar da baiwarka takawo ga ubangidana a ba 'yan samarin da ke biye da ubangidana.28Na roƙe ka daka gafarta wa bawanka, gama Yahweh za ya gina wa ubangidana tabbataccen gida, domin ubangidana yana yaƙin Yahweh ne; kuma ba za a sami mugunta a cikinka ba dukkan kwanakin ranka."
29Koda shi ke mutane sun tashi neman ranka, duk da haka ran ubangidana za a kãre shi cikin taro na masu rai daga wurin Yahweh Allahnka; kuma za ya ɗauke rayukan maƙiyanka, kamar daga aljihu na majajjawa.
30Yahweh zai aiwatar wa ubangidana komai da ya alƙawarta maka, ya kuma zaɓe ka shugaba bisa Isra'ila.31Wannan ba zai zama abin nauyi gare ka ba - cewaka zubar da jinin marar laifi, ko domin ubangidana na ƙoƙarin kuɓutar dakansa. Gama a lokacin da Yahweh zai yi wa ubangidana alheri, ka tuna da baiwarka."
32Dauda ya cewa Abigel, "Mai albarka ne Yahweh, Allah na Isra'ila, shi wanda ya aiko ki da kika same ni yau.33Hikimarki mai albarka ce kuma ke mai albarka ce, domin kin tsare ni daga zubar da jini kuma daga rama wakaina da hannuna!
34A gaskiya, yadda Yahweh, Allah na Isra'ila, ke raye, shi wanda ya kiyaye ni daga cutar da ke, da ba domin kin yi sauri kin zo gare ni ba, da ba za a sami wani ragowa domin Nabal ko da ɗan jariri ne zuwa wayewar gari ba."35Sai Dauda yakarɓi abin da takawo masa daga hannunta; ya ce ma ta, "Tafi cikin salama zuwa gidanki; duba, na saurari muryarki kuma na gamsu."
36Sai Abigel ta koma ga Nabal; gashi kuwa, ya shirya shagali a gidansa, kamar shagali na sarki; kuma zuciyar Nabal ta shagalta cikinsa, gama ya bugu ainun. Sai ta ƙi gaya masa komai har hasken safiya.
37Sai ya zamana da safe, lokacin da ƙarfin giya ya fita daga Nabal, sai matarsa ta gaya masa waɗannan abubuwan; zuciyarsa ta mutu cikinsa, sai ya zamakamar dutse.38Sai ya zama bayan kwana goma sai Yahweh yakai wa Nabal farmaƙi har yakashe shi.
39Da Dauda ya ji cewa Nabal ya mutu, ya ce, "Albarka ta tabbata ga Yahweh, wanda ya ɗauki zargin zãgin da na sha daga hannun Nabal ya kuma kãre bawansa daga mugunta. Ya juyar da aikin muguntar Nabal bisakansa." Sai Dauda ya aika ya kuma yi magana da Abigel, domin ya ɗauke ta a matsayin matarsa.40Lokacin da bayin Dauda suka iso wurin Abigel akarmel, suka yi mata magana suka ce, "Dauda ya aike mu gare ki mu ɗauke ki zuwa wurinsa ki zama matarsa."
41Ta tashi, ta sunkuyar dakanta zuwa ƙasa, ta kuma ce, "Duba, baiwarka baiwa ce da za ta wanke ƙafafun bayin ubangidana."42Sai Abigel ta yi sauri ta tashi, ta hawo bisa jaka tare da bayi 'yanmata biyar da ke nata waɗanda suka biyo ta; sai kuma ta biyo bayin Dauda ta kuma zama matarsa.
43Yanzu dai Dauda ya ɗauko wakansa Ahinowam ta Jezril a matsayin matarsa; su biyu suka zama matansa.44Haka kuma, Saul ya rigaya ya bayar da 'yarsa, matar Dauda, ga Falti ɗan Layish, wanda mutumin Galim ne.

26

1Sai Zifiyawa suka zo wurin Saul a Gibiya suka kuma ce, "Ba Dauda yana ɓoyewa a cikin tudun Hakila ba, wanda ya ke kamin Yeshimon?"2Sai Saul ya tashi ya kuma tafi zuwa hamada ta Zif, tare da zaɓaɓɓun mutane dubu uku na Isra'ila, domin neman Dauda a cikin hamadar Zif.

3Saul yakafa sansani a bisa tudun Hakila, wanda ke kafin Yeshimon, a gefen hanya. Amma Dauda na zama cikin hamadar, kuma ya ga cewa Saul na zuwa gare shi a cikin hamadar.4Sai Dauda ya aiki 'yan leken asiri kuma ya fahimci cewa tabbas Saul ya zo.
5Dauda ya tashi ya kuma tafi wurin da Saul yakafa sansani; ya ga inda Saul ya kwanta, tare da Abna ɗan Nã, shugaban rundunarsa; Saul ya kwanta cikin sansanin, kuma mutanen suka zagaye shi, dukkansu suna barci.
6Sa'an nan Dauda ya cewa Ahimelek Bahittiye, kuma ga Abishai ɗan Zeruwa, ɗan'uwan Yowab, "Wane ne zai tafi da ni wurin Saul a cikin sansani?" Abishai ya ce, "Ni! Zan tafi tare dakai."7Sai Dauda tare da Abishai suka tafi wurin rundunar cikin dare. Saul na barci cikin tsakiyar sansani tare da mãshinsakafe da ƙasa kusa dakansa. Abna da kuma sojojinsa suka kwanta zagaye da shi.8Sai Abishai ya cewa Dauda, "Yau Allah ya miƙa maƙiyinka cikin hannunka. Yanzu na roƙe kaka bar ni in cake shi har ƙasa da mashi da bugu ɗaya tak. Ba zan cake shi sau biyu ba."
9Dauda ya cewa Abishai, "Kadaka hallaka shi; gama wane ne za ya miƙa hannunsa gãba da shafaffen Yahweh ya kuma zama marar laifi?"10Dauda ya ce, "Na rantse da ran Yahweh, Yahweh zai kashe shi, ko kuma ranar mutuwarsa ta zo, ko kuma ya tafi yaƙi ya mutu.
11Bari Yahweh ya sauwaƙe mani da in miƙa hannuna gãba da shafaffe; amma yanzu, na roƙe ka, ka ɗauki mashin da ke kusa dakansa da kuma gorar ruwa, sai mu tafi."12Sai Dauda ya ɗauke mashin da gorar ruwan da ke kusa dakan Saul, suka kuma tafi. Babu wanda ya gansu ko ya san komai game da haka, ko wani ya farka, gama duk sun yi barci, gama barci mai nauyi daga wurin Yahweh ya faɗo bisansu.
13Sa'an nan Dauda ya tashi ya tafi wancan ɓangaren ya kuma tsaya akan tsauni can nesa; akwai babbar rãta tsakaninsu.14Dauda ya yi kira da ihu ga mutanen ga kuma Abna ɗan Nã; ya ce, "Baka amsa ba, Abna?" Sai Abna ya amsa ya ce, "Kai wane ne da ke yi wa sarki ihu?"
15Dauda ya cewa Abna, "Kai ba mutum ba ne mai ƙarfin hali? Wane ne kamarka a Isra'ila? To donme baka yi tsaron ubangidanka sarki ba? Gama wani ya shigo domin yakashe sarki ubangidanka.16Wannan abin daka yi ba shi da kyau. Na rantse da ran Yahweh, ka cancanci ka mutu domin baka yi tsaron ran sarki ubangidanka ba, shafaffe na Yahweh. Yanzu ka duba inda mashi da gorar ruwa da ke kusa dakansa suke!"
17Saul ya sasance muryar Dauda ya kuma ce, "Wannan muryarka ce, ɗana Dauda?" Dauda ya ce, "Muryata ce, ubangidana, sarki."18Ya ce, "Me yasa ubangidana ke neman bawansa? Me na yi? Wacce mugunta ce ke cikin hannuna?
19Yanzu saboda haka, na roƙe ka, bari ubangidana sarki ya saurari maganganun bawansa. Idan Yahweh ne ya zugaka gãba da ni, bari yakarɓi baiko; amma idan mutum ne, bari ya la'anta a fuskar Yahweh, gama yau sun kore ni waje, domin kada in manne wa gãdon Yahweh; sun ce mani, "Je ka yi sujada ga wasu alloli.'20Saboda haka yanzu, kadaka bar jinina ya zuba nesa da fuskar Yahweh; gama sarkin Isra'ila ya fito neman ƙwaro ɗayakamar yadda wani ke fita farautar makwarwa a bisa duwatsu."
21Sai Saul ya ce, "Na yi zunubi. Dawo, Dauda, ɗana; domin ba zan ƙara cutar dakai ba, domin yau raina ya zama abin daraja a idonka. Duba, na yi kamar wawa kuma na yi mugun kuskure."
22Dauda ya amsa ya kuma ce, "Duba, mashin ka yana nan, sarki! Bari ɗaya daga cikin samarin ka ya zo yakarɓa yakai maka.23Bari Yahweh ya sãka wa kowa bisa ga adalcinsa da amincinsa; domin Yahweh ya miƙaka cikin hannuna yau, amma ba zan bugi shafaffensa ba.
24Duba, kamar yadda ranka ke da daraja a idanuna yau, bari raina ya zama da daraja a fuskar Yahweh, kuma bari ya kuɓutar da ni daga dukkan wahala."25Sai Saul ya cewa Dauda, "Bari ka yi albarka, Dauda ɗana! Lallai zaka yi manyan abubuwa kuma zaka yi nasara cikin dukkansu." Sai Dauda yakama hanyarsa, Saul kuma ya koma fadarsa.

27

1Dauda ya faɗi a cikin zuciyarsa, "Wata rana zan hallaka ta hannun Saul; ba abin da ya fiye mani sai in tsere zuwa ƙasar Filistiyawa; da haka Saul zai dena nema na cikin dukkan iyakar Isra'ila; ta haka zan kubce daga hannunsa."

2Dauda ya tashi ya tsallaka can, shi da mazajensa ɗari shida da ke tare da shi, wurin Akish ɗan Mawok, sarkin Gat.3Dauda ya zauna tare da Akish a Gat, shi da mazajensa, kowanne mutum da iyalansa, Dauda tare da matayensa biyu, Ahinowam Yeziriya, da kuma Abigel Bakameliya, matar Nabal.4Da aka gaya wa Saul cewa Dauda ya tsere zuwa Gat, sai bai sãke neman sa ba.
5Dauda ya cewa Akish, "Idan na sami tagomashi a idanunka, bari su bani wuri cikin ɗaya daga cikin biranen ƙasar, domin in zauna nan: donme bawanka za shi zauna cikin masarauta tare dakai?"6Sai Akish ya ba shi Ziklag a wannan rana; shi yasa Ziklag ta zama ta sarakunan Yahuda har wa yau.7Shekarun da Dauda ya zauna cikin ƙasar Filistiyawa shekara ɗaya ce cikakkiya da wata huɗu.
8Dauda da mazajensa sukakaiwa wurare dabam dabam farmaƙi, suka hari Geshurawa, da Girziyawa, da Amalekawa; gama waɗannan al'ummai su ne asalin mazaunan ƙasar, idan kana tafiya zuwa Shur, har zuwa ƙasar Masar. Suna zama a nan wurin tun zamanun dã.9Dauda yakai wa ƙasar farmaƙi kuma bai bar namiji ko mace da rai ba; ya kwashi tumaki, da awakai, da jakuna, da raƙuma, da kumakayayyaki; sai ya dawo kuma zuwa Akish.
10Akish zai ce, "Gãba da su waye yau kakai hari?" Dauda zai amsa, "Gãba da kudancin Yahuda," ko "Gãba da kudancin Yeramiyawa," ko "Gãba da kudancin Keniyawa."
11Dauda bai bar namiji ko mace da rai domin yakawo su zuwa Gat ba, ya ce, "Sabodakada su yi magana game da mu, su ce 'Dauda ya yi kaza dakaza.'" Haka ya yi dukkan lokutan da ya ke zama a ƙasar Filistiyawa.12Akish ya amince da Dauda, yana cewa, "Ya sa mutanensa Isra'ilawa suna ƙyamarsa; zai zama bawana har abada."

28

1Sai ya zama a wannan kwanaki Filistiyawa suka tara rundunar yaƙinsu domin yaƙi da Isra'ila. Akish ya cewa Dauda, "Ka san da cewar zaka fita tare da ni cikin runduna, kai da mazajenka."2Dauda ya cewa Akish, "Da haka zaka san abin da bawanka zai iya aikatawa." Akish ya cewa Dauda, "Da haka zan maishe ka mai tsarona na din-din din."

3Yanzu dai Sama'ila ya mutu, kuma dukkan Isra'ila sun yi masa makoki suka kuma binne shi a Rama, a cikin birninsa. Haka kuma, Saul ya fanfari masu hurɗa da matattu ko da ruhohi.4Sai Filistiyawa suka tarakansu wuri ɗaya suka zo sukakafa sansani a Shunem; Saul kuma ya tara dukkan Isra'ila tare, suka kumakafa sansani a Gilbowa.
5Lokacin da Saul ya ga rundunar Filistiyawa, sai ya ji tsoro, zuciyarsa kuma ta yi rawa sosai.6Saul ya yi addu'a ga Yahweh domin taimako, amma Yahweh bai amsa masa ba - ko ta mafarki, ko da Urim, kuma wurin annabawa ba.7Sai Saul ya cewa bayinsa, "Ku nemo mani mace wadda ta ke magana da matattu, domin in tafi wurinta in nemi shawararta." Bayinsa suka ce masa, "Duba, akwai wata mace a Endo wadda ta ke faɗin cewa tana magana da matattu."
8Saul ya ɓaddakama, ya sanya wasu kaya, ya tafi, shi da mutum biyu tare da shi; suka tafi wurin matar da dare. Ya ce, "Ki duba mani, na roƙe ki, da ruhu, ki kuma kirawo mani duk wanda na faɗi maki."9Matar ta ce masa, "Duba, kasan dai abin da Saul ya yi, yadda ya kori waɗanda ke magana da matattu ko ga ruhohi. To me yasakake shirya wa raina tarko, ka sa ni in mutu?"10Saul ya rantse mata har ga Yahweh ya kuma ce, "Na rantse da ran Yahweh, babu hukuncin da zai same ki domin wannan."
11Matar ta ce, "Wane ne kake so in kirawo maka?" Saul ya ce, "Kirawo mani Sama'ila."12Da matar ta ga Sama'ila, sai tayi ihu da babbar murya ta kuma yi magana da Saul, cewa, "Donme ka ruɗe ni? Gamakai Saul ne."
13Sarkin ya ce ma ta, "Kada ki ji tsoro. Me kika gani?" Matar ta cewa Saul, "Na ga wani allah yana fitowa daga ƙasa."14Ya ce mata, "Yayakamaninsa ya ke?" Ta ce, "Tsohon mutum yana haurowa sama; yana sanye dakaya." Saul ya gane cewa Sama'ila ne, sai ya faɗi ƙasa fuskarsa ƙasa ya kuma nuna bangirmansa.
15Sama'ila ya cewa Saul, "Donme ka dame ni har daka hauro da ni sama?" Saul ya amsa, "Na gaji sosai, Filistiyawa suna yaƙi da ni, Allah kuma ya rabu da ni kuma ya ƙi ya amsa mani, ko ta wurin annabawa, ko ta mafarkai. Saboda haka na kirawo ka, domin ka sanar da ni abin da zan yi."
16Sama'ila ya ce, "Mene ne kake tambaya ta, tun da Yahweh ya bar ka, kuma ya zama abokin gãbarka?17Yahweh ya aiwatar maka da abin da ya faɗa zai yi. Yahweh ya raba mulkin daga hannunka ya kuma bayar ga wani - ga Dauda.
18Domin bakayi biyayya da muryar Yahweh ba kuma baka aiwatar da fushinsa mai ƙuna bisa Amalekawa ba, shi kuma ya yi maka haka a wannan rana.19Duk da haka, Yahweh zai miƙa Isra'ila dakai cikin hannuwan Filistiyawa. Gobe kai da 'ya'yanka maza zaku kasance tare da ni. Yahweh kuma za ya miƙa rundunar Isra'ila cikin hannuwan Filistiyawa."
20Sa'an nan Saul nan da nan ya faɗi da ƙarfinsa zuwa ƙasa da kuma fargaba saboda maganganun Sama'ila. Babu wani sauran ƙarfi a cikinsa, gama bai ci abinci ba dukkan yini, ko a wannan dare.21Macen ta zo wurin Saul ta ga cewa yana cikin babbar damuwa, Ta ce masa, "Duba, baiwarka ta saurari muryarka; Na ɗibiya raina a cikin hannuwana na kuma saurari maganganun daka faɗi mani.
22Don haka yanzu, na roƙe ka, kai maka saurari muryar baiwarka macen, na kuma shirya maka abinci ɗan kaɗan a gabanka. Ka ci sabodaka maido da ƙarfi domin sa'ad da zakakama hanyarka."23Amma Saul bai yarda ba ya kuma ce, "Ba zan ci ba." Amma bayinsa, tare da macen, suka nace masa, ya kuma saurari muryarsu. Saboda haka ya tashi daga ƙasa ya zaunakan gado.
24Matar tana da ɗan maraƙi mai ƙiba a cikin gidan; ta yi sauri ta yanka shi; ta ɗauki gari, ta cuɗa shi, ta kuma shirya gurasa da shi.25Takawo ga Saul da bayinsa, suka kuma ci. Sa'an nan suka tashi suka kuma yi tafiyarsu a wannan daren.

29

1Yanzu Filistiyawa sun taru tare dukkan rundunarsu a Afek; Isra'ilawa suka yi sansani kusa da magudanar ruwa da ke cikin Yezril.2Sarakunan Filistiyawa suka wuce a ɗari-ɗarinsu da kuma dubbai; Dauda da mazajensa suka wuce suna daga baya tare da Akish.

3Sai sarakunan Filistiyawa suka ce, "Mene ne wannan Ibraniyawan ke yi a nan?" AKish ya cewa sauran sarakunan Filistiyawan, "Ba wannan ba ne Dauda, bawan Saul, sarkin Isra'ila, wanda ke tare da ni kwanakin nan, ko ace waɗannan shekaru, kuma ban same shi da wani laifi ba tun ranar da ya zo wurina har wa yau?"
4Amma sarakunan Filistiyawa suka yi fushi da shi; suka ce masa, "Ka sa wannan mutum ya tafi, domin ya tafi wurin daka bashi, kadaka bar shi ya biyo mu zuwa filin dãga, domin kada ya juya ya zama maƙiyinmu cikin yaƙi. Don ta yaya wannan talikin zai yi sulhu da ubangidansa? Ba ta ɗaukar kawunan mutanen mu ba ne?
5Ba wannan ba ne Dauda wanda aka yi wa waƙa a junansu cikin rawa, cewa, 'Saul yakashe dubbansa, Dauda kuma yakashe nasa dubbai goma'?"
6Sai Akish ya kirawo Dauda ya kuma ce masa, "Na rantse da ran Yahweh, ka zama nagari, kuma fitarka da shigowarka tare da ni cikin runduna mai kyau ne a gani na; gama ban iske wani laifi gare ka ba tun randa ka zo wurina zuwa wannan rana.7Sai ka juya yanzu ka kuma tafi cikin salama, domin kada ka yi wa sarakunan Filistiyawa laifi."
8Dauda ya cewa Akish, "Amma me na yi? Mene ne ka samu a cikin bawanka duk sa'ad da nake tare da kai zuwa wannan rana, da har ba zan je inyi yaƙi da maƙiyan ubangidana sarki ba?"9Akish ya amsa ya kuma cewa Dauda, "Na san da cewa kai marar laifi ne a idanuna kamar mala'ikan Allah; duk da haka sarakunan Filistiyawa suka ce, 'Ba zai haura tare da mu ba zuwa yaƙin.'
10Saboda haka sai ka tashi da sassafe tare da bayin ubangidanka waɗanda suka zo tare da kai; da zarar ka tashi da asussuba ka kuma sami haske, ka tafi."11Sai Dauda ya tashi da sauri, shi da mazajensa, don su tafi da safe, su dawo ƙasar Filistiyawa. Amma Filistiyawan suka haura zuwa Yezril.

30

1Ya zama kuma, da Dauda da mazajensa suka iso Ziklag a rana ta uku, da Amalekawa suka kawo farmaki bisa Negeb da kuma kan Ziklag. Suka kai wa Ziklag hari, suka ƙona ta,2suka kwashe matayen da kowa da ya ke ciki, da manya da ƙanana. Ba su kashe kowa ba, amma suka kwashe suka yi tafiyarsu.

3Lokacin da Dauda da mazajensa suka iso birnin, an ƙone, kuma matayensu, da 'ya'yansu maza, da 'ya'yansu mata an ɗauke su zuwa bauta.4Sa'an nan Dauda da mutanen da ke tare da shi suka tãda murya suka yi kuka har sai da babu wani sauran ƙarfi kuma da za su yi kuka.
5Aka kwashe matan Dauda guda biyu, Ahinowam Yeziriya, da Abigel matar Nabal mutumiyar Karmel.6Dauda ya dãmu ƙwarai, gama mutanen suna magana game da su jefe shi da duwatsu, gama dukkan mutanen suna ɓacin rai, kowanne mutum domin 'ya'yansa maza da mata; amma Dauda ya ƙarfafa kansa cikin Yahweh, Allahnsa.
7Dauda ya cewa Abiyata ɗan Ahimelek, firist, "Na roƙe ka, ka kawo mani falmara a nan wurina." Sai Abiyata ya kawo falmarar wurin Dauda.8Dauda ya yi addu'a ga Yahweh domin bishewa, cewa, "Idan na bi wannan mayaƙan, zan sha kansu?" Yahweh ya amsa, "Bi su, domin lallai za ka sha kansu, kuma tabbas za ka sake ƙwato dukkan abubuwan."
9Sai Dauda ya tafi, shi da mazajensa ɗari shida waɗanda ke tare da shi; suka iso magudanar Beso, inda waɗanda aka bari suka zauna.10Amma Dauda ya ci gaba da runtumar su, shi da mazaje ɗari huɗu; gama ɗari biyu sun tsaya a baya, wato waɗanda ƙarfinsu ya gãza da baza su iya haurawa zuwa magudanar Beso ba.
11Suka gamu da wani Bamasare cikin saura suka kawo shi ga Dauda; suka ba shi gurasa, ya kuma ci; suka ba shi ruwa ya sha;12sai kuma suka ba shi gutsuren wainar 'ya'yan ɓaure da curin kauɗar inabi guda biyu. Bayan da ya ci, ƙarfinsa ya dawo kuma, gama bai ci gurasa ba ko ya sha wani ruwa har kwana uku da yini uku.
13Dauda ya ce masa, "Kai na wane ne? Daga ina ka fito?" Ya ce, "Ni ɗan matashin ƙasar Masar ne, bawan Ba-amaleke; ubangidana ya baro ni domin kwana uku da suka shige rashin lafiya ta same ni.14Mu ka kai farmaƙi a yankin Negeb na Keretiyawa, da abin da ya ke na Yahuda, da kuma Nageb na Kaleb, kuma muka ƙona Ziklag."
15Dauda ya ce masa, "Za ka kawo ni zuwa wurin waɗannan maharan?" Bamasaren ya ce, "Ka rantse mani ga Allah da cewar ba zaka kashe ni ko ka bashe ni a cikin hannuwan ubangidana ba, ni kuma zan kawo ka wurin waɗannan maharan."
16Da Bamasaren ya kawo Dauda wurin, maharan na nan barbaje a dukkan ƙasar, suna ci suna sha suna rawa saboda dukkan ganimar da suka kwaso daga cikin ƙasar Filistiyawa da kuma ƙasar Yahuda.17Sai Dauda ya kai masu hari tun daga wayewar gari har yammancin da gari ya waye. babu mutum wanda ya tsira sai dai 'yan matasa guda ɗari, waɗanda suka haura bisa raƙuma suka kuma gudu.
18Sai Dauda ya maido da dukkan abin da Amalekawa suka ɗauke; kuma Dauda ya ƙubutar da matansa biyu.19Babu abin da ya ɓace, ko ƙarami ko babba, ko 'ya'ya maza ko 'ya'ya mata, ko kayan ganima, ko wani abu da maharan suka ɗauko wa kansu.20Dauda ya dawo da komai. Dauda ya ɗauko dukkan garken da kuma dabbobin, waɗanda mazajen suka koro gaba da sauran garkunan. Suka ce, "Wannan ganimar Dauda ce."
21Sai Dauda ya komo wurin sauran ɗari biyun da ƙarfinsu ya gãza ba su bi shi ba, waɗanda sauran suka sa su jira a magudanar Beso. Waɗannan mazajen suka zo domin su tarbi Dauda da kuma mutanen da ke tare da shi. Da Dauda ya iso wurin mutanensu, ya gaishe su.22Sai dukkan mugayen mutanen da marasa amfani da ke cikin waɗanda suka tafi tare da Dauda suka ce, "Domin waɗannan mazajen ba su tafi tare da mu ba, ba za mu ba su komai daga cikin ganimar da muka samu ba. Sai dai kowanne ɗaya daga cikinsu ya ɗauki matarsa da 'ya'yansa, ya bishe su, su tafi."
23Sa'an nan Dauda ya ce, "Ba za ku yi haka ba, 'yan'uwana, da abin da Yahweh ya ba mu. Ya kiyaye mu ya kuma bayar da maharan da suka tayar mana a hannuwanmu.24Waye zai saurari ku a kan wannan zance? Gama kamar yadda rabon kowanne da ya tafi yaƙin, haka zaya zama rabon duk wadda ya jira wurin kaya; za su sami rabo dai-dai da kowa."25Haka ya ci gaba da zama daga wannan rana har wa yau, gama Dauda ya maida haka doka da kuma ka'ida a Isra'ila.
26Da Dauda ya kai Ziklag, ya aika daga cikin ganimar zuwa ga shugabannin Yahuda, zuwa ga abokansa, cewa, "Duba, ga kyauta domin ku daga ganimar maƙiyan Yahweh."27Ya kuma aika da waɗansu zuwa ga shugabannin da ke a Betel, da kuma waɗanda ke a Ramot na Kudu, kuma ga waɗanda suke daga Jattir,28kuma ga waɗanda ke cikin Arowa, kuma zuwa ga waɗanda ke a Sifmot, kuma ga waɗanda suke a Ishtemowa.
29Ya kuma aika zuwa ga shugabannin da ke cikin Rakal, kuma zuwa ga waɗanda ke cikin biranen Yeramilawa, kuma ga waɗanda ke cikin biranen Kenawa,30kuma ga waɗanda ke cikin Homa, da kuma waɗanda ke zama a Borashan, ga kuma waɗanda ke cikin Atak,31ga kuma waɗanda ke cikin Hebron, ga kuma dukkan wuraren da Dauda da kansa da mazajensa ke zuwa kodayaushe.

31

1Yanzu Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra'ila. Mazajen Isra'ila suka gudu daga fuskar Filistiyawa suka kuma faɗi matattu a Tsaunin Gilbowa.2Filistiyawa suka runtumi Saul da 'ya'yansa. Filistiyawa suka kashe Yonatan, Abinadab, da Malkishuwa, 'ya'yansa maza.3Yaƙin ya yi zafi gãba da Saul, kuma masu harbin bãka suka sha kansa. Yana cikin ƙunci da zafi sabili da su.

4Sai Saul ya cewa mai ɗaukar masa makamai, "Zaro takobinka ka soke ni da ita. In ba haka ba, waɗannan marasa kaciyar zasu zo su wulaƙanta ni." Amma mai ɗaukar masa makamai ya ƙi, gama yana jin tsoro. Sai Saul ya ɗauki takobinsa ya faɗi bisanta.5Da mai ɗaukar masa makamai ya ga Saul ya mutu, sai shi ma ya ɗauki ta sa takobin ya faɗa kanta ya mutu da shi.6Haka Saul ya mutu, 'ya'yansa uku, da kuma mai ɗaukar masa makamai - waɗannan mutanen dukka suka mutu tare rana ɗaya.
7Lokacin da mutanen Isra'ila da ke a wancan ɓangaren kwarin, da kuma waɗanda ke gaba da Yodan, suka ga cewa mazajen Isra'ila sun gudu, kuma Saul da 'ya'yansa maza sun mutu, sai suka ƙaurace wa ƙauyukansu suka gudu, sai kuma Filistiyawa suka zo suka zauna cikinsu.8Sai ya zama kuma washegari, da Filistiyawa suka zo domin su washe kayan matattun, sai suka ga Saul tare da 'ya'yansa maza uku sun faɗi a Dutsen Gilbowa.
9Suka yanke kansa suka kuma cire kayan yaƙinsa, suka kuma aika 'yan saƙo cikin ƙasar Filistiyawa ko'ina domin su kai labarai ga haikalin gumakansu kuma ga mutanensu.10Suka ajiye rigar yaƙinsa cikin haikalin Ashtoret, kuma suka rataye jikinsa ga ganuwar birnin Bet Shan.
11Lokacin da mazaunan Yabesh Giliyad suka ji abin da Filistiyawa suka yi wa Saul,12dukkan mazaje 'yan yaƙi suka tashi suka yi tafiya dukkan dare suka ɗauki jikin Saul da kuma jikkunan 'ya'yansa daga ganuwar Bet Shan. Suka tafi Yabesh suka ƙona su a can.13Sai Suka ɗauki ƙasusuwansu suka binne su a ƙarƙashin itaciyar tamarisk a Yabesh, suka yi azumi na kwana bakwai.

Littafin sama'ila na biyu

1

1Bayan mutuwar Saul, Dauda ya dawo daga harin Amelikawa ya kuma zauna a Ziglak kwana biyu.2A rana ta uku, wani mutum ya zo daga sansanin Saul da tufafinsa a yage da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dauda sai ya kwanta rub da ciki a ƙasa ya miƙe jikinsa ya yi ruku'u a gabansa.

3Dauda ya ce masa, "Daga ina ka fito?" Ya amsa, "Na kubce daga sansanin Isra'ila ne."4Dauda ya ce masa, Idan ka yarda ka gaya mani yadda abubuwa suka kasance." Ya amsa, "Mutane sun gudu daga yaƙi. Da yawa sun faɗi kuma da yawa sun mutu. Saul da Yonatan ɗansa su ma sun mutu."5Dauda ya ce ma saurayin, "Yaya ka sani cewa Saul da Yonatan ɗansa sun mutu?"
6Saurayin ya amsa, "Sa'a ce na ci. ya zamana ne ina kan Dutsen Gilbowa, sai ga Saul yana jingine akan mashinsa, karusai da mahaya suka kusa rutsasu.7Saul ya juya ya gan ni ya kuma kira ni da murya. Na amsa, 'Ga ni.'
8Ya ce mani, "Waye kai?" Na amsa masa, 'Ni Ba-amelike ne.'9Ya ce mani, ' Idan ka yarda ka tsaya a kaina ka kasheni, gama zafin azaba ya sha kaina, amma duk da haka rai yana ciki na'10Saboda haka na tsaya a kansa na kasheshi, domin na sani ba zai rayu ba bayan ya faɗi. Sa'an nan na ɗauki kambin da ke kansa da ɗamarar da ke damtsensa kuma, na kawo su nan gunka, ubangidana."
11Sai Dauda ya ƙeƙƙece tufafinsa dukkan mutanen da ke tare da shi suka yi haka su ma.12Suka yi makoki, da kuka, kuma suka yi azumi har yamma saboda Saul, domin ɗansa Yonatan, domin mutanen Yahweh, domin kuma gidan Isra'ila sabili da sun faɗi ta hannun takobi.13Dauda ya cewa saurayin, 'Daga ina ka ke?' Ya amsa, 'Ni yaron wani baƙo ne a ƙasar, Ba-amaleke."
14Dauda ya ce masa, "Me ya sa ba ka ji tsoron kashe shafaffen sarki na Yahweh da hannunka ba?"15Dauda ya kira ɗaya daga cikin samarin ya ce, "Tafi ka kashe shi." Sai wannan mutumin ya tafi ya buga shi ƙasa. Sai Ba-ameliken ya mutu.16Sai Dauda ya cewa mataccen Ba'ameliken, '" Alhakin jininka na kanka domin bakinka da kansa yana shaida gãba da kai ya ce, 'Na kashe shafaffen sarki na Yahweh.'"
17Sa'an nan Dauda ya yi wannan waƙar makoki game da Saul da Yonatan ɗansa.18Ya bada doka ga mutane su koyar da Waƙar Bãka ga 'ya'yan Yahuda, wanda aka rubuta a Littafin Yashar.19"‌Ɗ‌aukakarki, Isra'ila, ya mutu, an yi kisa a tuddanki! Aiya jarumawa sun faɗi!20Kada ku faɗa a Gat, kada ku yi shelarsa a titunan Askelon, domin kada 'yan'matan Filistiyawa su yi farinciki, domin kada 'yan'matan marasa kaciya su yi biki.
21Duwatsun Gilbowa, kada raɓa ko ruwan sama su kasance a kanku, ko gonaki masu bada hatsi domin baiko, gama a nan aka lalata garkuwar ƙarfafa. Garkuwar Saul ba a ƙara shafe ta da mai ba.22Daga jinin waɗanda aka kashe, daga jikin ƙaƙƙarfa, bãkan Yonatan bai juya ba, kuma takobin Saul bata dawo wofi ba.
23Saul da Yonathan ƙaunatattu ne masu alheri a rayuwa, a mutuwarsu ba a raba su ba. Sun fi gaggafai zafin gudu, sun fi zakoki ƙarfi.24Ku 'yan'matan Isra'ila, ku yi kuka domin Saul, wanda ya suturtar daku cikin shunayya da duwatsu masu daraja da kayan zinariya masu ƙayatarwa a tufafinku.
25Aiya jarumawa sun faɗi tsakiyar yaƙi! An kashe Yonatan a tuddanki,26Ina da damuwa domin ka, ɗan'uwana Yonatan. Amintacce kake a gare ni. ‌Ƙaunarka a gare ni abin al'ajibi ne, ya zarce ƙaunar mata.27Aiya jarumawa sun faɗi, makaman yaƙi kuma sun lalace!"

2

1Bayan wannan Dauda ya tambayi Yahweh ya ce, 'Ko in haura zuwa ɗaya daga cikin biranen Yahuda?" Yahweh ya amsa masa, "Ka haura." Dauda ya ce, "Wanne birnin zan je?" Yahweh ya amsa, "Zuwa Hebron."2Sai Dauda ya tafi Hebron da matayensa guda biyu, Ahinowam daga Yezril, da Abigel daga Karmel, gwauruwar Nabal.3Dauda ya kawo mutanen da ke tare da shi, waɗanda kowannen su ya kawo nasa iyalin, zuwa biranen Hebron inda suka fara zaunawa.

4Sa'an nan mutane daga Yahuda suka zo suka naɗa Dauda sarki bisa gidan Yahuda. Aka cewa Dauda, '"Mutanen Yabes Giliyad ne suka bizne Saul."5Sai Dauda ya aiki manzanni ga mutanen Yabes Giliyad suka kuma ce masu, "Yahweh ya albarkace ku, tunda ku ka nuna wannan riƙon amana ga ubangidanku Saul har ku ka bizne shi.
6Bari yanzu Yahweh ya nuna maku alƙawarin riƙon amana da aminci. Ni kuma zan yi maku wannan alheri domin kun yi wannan abu.7Yanzu dai, bari hannuwanku su ƙarfafa; ku yi ƙarfin hali domin Saul ubangidanku ya mutu kuma gidan Yahuda sun naɗa ni shafaffen sarki bisan su."
8Amma Abna ɗan Nã, sarkin yaƙin rundunar Saul, ya ɗauki Ishboshet ɗan Saul ya kuma kawo shi Mahanam,9Ya naɗa Ishboshet sarki bisa Giliyad, Ashar, Yazril, Ifraim, Benyamin, da kuma bisa dukkan Isra'ila.
10Ishboshet ɗan Saul, yana da shekaru arba'in da ya soma mulki bisa Isra'ila, ya kuma yi mulki shekara biyu. Amma gidan Yahuda suka bi Dauda.11Lokacin da Dauda ke sarki cikin Hebron bisa gidan Yahuda shekara bakwai ne da wata shida.
12Abna ɗan Nã, da barorin Ishboshet ɗan Saul, su ka tafi daga Mahanayim zuwa Gibiyan.13Yowab ɗan Zeruya da barorin Dauda suka fita suka gamu da su a tafkin Gibiyan. A nan suka zauna, ɗaya ƙungiyar a ɗaya gefen tafkin ɗayan kuma a ɗaya wancan gefen.
14Abna ya cewa Yowab, "Bari samarin su tashi su yi gãsa a gabanmu." Sai Yowab ya ce, "Bari su tashi."15Sai samarin suka tashi suka tattaru tare, sha biyu domin Benyami da Ishboshet ɗan Saul, kuma sha biyu daga barorin Dauda.
16Kowanne ya danƙe abokin gasarsa a kai ya soke gefen cikin ɗan'uwansa da takobi, sai su ka faɗi ƙasa tare. Shi ya sa aka kira wurin nan da Ibraniyanci, "Helkat Hazzurim." ko "Filin Takkuba" wanda ya ke cikin Gibiyan.17Yaƙin ya yi zafi ainun a ranar nan kuma aka buga Abna da mutanen Isra'ila a gaban barorin Dauda.
18'Ya'ya maza uku na Zeruya suna wurin: Yowab, Abishai, da Asahel. Asahel mai zafin gudu da ƙafa ne kamar barewar jeji.19Asahel ya sheƙa da gudu bayan Abna ya bishi kurkusa ba ratsewa wani gefen.
20Abna ya waiga bayansa ya ce, "Kai ne kuwa Asahel?" Ya amsa, "I, ni ne."21Abna ya ce masa, "Ka juya zuwa gefenka na dama ko hagunka, ka cafke ɗaya daga cikin samarin ka karɓe makaminsa." Amma Asahel ya ƙi ratsewa wani gefen.
22Sai Abna ya sãke cewa Asahel, "Ka dena bi na donme zan buga ka ƙasa? ‌Ƙaƙa kuma zan fuskanci, ɗan'uwanka Yowab?"23Amma Asahel ya ƙi ratsewa, saboda haka Abna ya soki jikinsa da kan mashinsa marar kaifi har ma mashin ya fito ta wancan gefen. Asahel ya faɗi ya mutu. Ya zamana fa duk wanda ya iso inda Asahel ya faɗi ya mutu, sai ya dakata ya tsaya shuru.
24Amma Yowab da Abishai suka bi Abna. Sa'ad da rana take faɗuwa, suka iso tudun Amana, da ke kusa da Giya a hanyar da ta bi ta jejin Gibiyon.25Mutanen Benyaminu suka haɗa kansu gaba ɗaya suka goyi bayan Abna suka tsaya a kan tudu.
26Sai Abna ya kira Yowab ya ce, "Dole ne takobi ya hallakar har abada? Ba ka sani zai zama da ɗaci a ƙarshe ba? Har yaushe zai zamana kafin ka gaya wa mutanenka su janye daga fafarar 'yan uwansu?"27Yowab ya amsa, "Na rantse da Yahweh, hakika da baka faɗi haka ba, da sojojina sun fafari 'yan 'uwansu har zuwa safiya!"
28Sai Yowab ya busa ƙaho, mutanensa duk suka tsaya suka dena fafarar Isra'ila, kuma ba su sake yin faɗa ba.29Abna da mutanensa suka yi ta tafiya dare farai cikin Araba. Suka haye Yodan, suka yi ta tafiya dukkan safiyan nan, sa'annan ne suka kai Mahanayim.
30Yowab ya juyo daga fafarar Abna. Ya tara dukkan mutanensa, cikinsu aka rasa Asahel da sojojin Dauda guda goma sha tara.31Amma mutanen Dauda sun riga sun kashe mutane 360 na Benyamin da ke tare da Abna.32Sai suka ɗauki Asahel suka binne shi cikin kabarin mahaifinsa, da ke a Baitalami. Yowab da mutanensa suka yi tafiya dare farai, gari kuma ya waye masu a Hebron.

3

1Akwanakin nan dai aka yi dogon yaƙi tsakani gidan Saul da gidan Dauda. Gidan Dauda ya yi ta ƙara ƙarfi, amma gidan Saul ya yi ta raguwa.

2Aka haifa wa Dauda 'ya'ya maza a Hebron.‌ Ɗan farinsa Amon, da Ahinowam daga Yazril ta haifa masa.3‌Ɗansa na biyu, Kilyab, Abigel gwauruwar marigayi Nabal daga Karmel ta haifeshi, Ɗansa na ukun Absalom ne, ɗan Ma'aka, ɗiyar Talmai, sarki Geshu.
4‌Ɗan Dauda na huɗu, Adonija, ɗan Hagit ne. ‌Ɗansa na biyar Sefatiya ne ɗan Abtiyal,5na shidan, Itram ne, ɗan Egla matar Dauda. Waɗannan 'ya'ya maza aka haifa wa Dauda a Hebron.
6Ya zamana fa a lokacin yaƙi tsakanin gidan Saul da gidan Dauda sai Abna ya ƙarfafa kansa a gidan Saul.7Saul na da kwarkwara wadda sunanta Risfa, ɗiyar Aya ce. Sai Ishboshet ya cewa Abna, "Me yasa ka kwana da ƙwarƙwarar mahaifina?"
8Sai Abna ya husata da maganganun Ishboshet ya ce, "Ni kan kare ne na Yahuda? Yau ina nuna aminci ga gidan Saul, mahaifinka, da 'yan'uwansa, da kuma abokanansa, ta wurin yadda ban basheku ba cikin hannun Dauda. Amma yanzu kana zargi na da laifi game da wannan matar.
9Bari Allah ya yi mani, Abna, harma fiye da haka, idan ban yi wa Dauda yadda Yahweh ya rantse masa ba,10a tada masarautar daga gidan Saul, a kafa kursiyin Dauda bisa Isra'ila da bisa Yahuda daga Dan zuwa Bayasheba."11Ishboshet bai iya amsa wa Abna ba koda magana ɗaya, domin yana jin tsoronsa.
12Sa'an nan Abna ya aika manzanni ga Dauda su yi masa magana dominsa cewa, "‌Ƙ‌asar wane ne wannan? Ka yi yarjejeniya da ni, gama hannuna na tare da kai, in kawo maka dukkan Isra'ila."13Dauda ya amsa, "Da kyau zan yi yarjejeniya da kai. Abu ɗaya na ke biɗa a gare ka shi ne cewa ba za ka ga fuskata ba sai dai da farko ka kawo Mikal, ɗiyar Saul, sa'ad da za ka zo ka gan ni."
14Sai Dauda ya aika manzanni zuwa wurin Ishboshet, ɗan Saul, cewa, "Ka ba ni matata Ishboshet Mikal, wadda na biya sadakin loɓar kaciya ɗari na Filistiyawa domin ta.15Sai Ishboshet ya aika a kawo Mikal, ya kuma karɓe ta daga mijinta, Faltiyel ɗan Layis.16Mijinta ya tafi tare da ita, yana tafiya yana kuka, ya bi ta zuwa Bahurim. Sai Abna ya ce masa, "Ka koma gida yanzu." Sai ya koma.
17Abna ya yi magana da dattawan Isra'ila cewa, "Da daɗewa kun yi ta ƙoƙarin ku naɗa Dauda ya zama sarki bisan ku.18Yanzu ku yi haka. Gama Yahweh ya yi magana game da Dauda cewa, 'Ta hannun bawana Dauda zan ceci mutanena Isra'ila daga hannun Filistiyawa daga kuma dukkan hannun maƙiyansu.'"
19Abna kuma da kansa ya yi magana da mutanen Benyamin. Sai Abna kuma ya tafi ya yi magana da Dauda a Hebron domin ya bayyana masa dukkan abin da Isra'ila da dukkan gidan Benyamin gaba ɗaya suka yi niyar aikatawa.20Da Abna da mutanensa guda ashirin suka iso cikin Hebran domin su ga Dauda, Dauda ya shirya masu liyafa.
21Abna ya bayyana wa Dauda, "Zan tashi in tattaro maka dukkan Isra'ila, ubangidana sarkina, domin su yi alƙawari da kai, domin ka yi mulki bisa dukkan abin da kake marmari." Sai Dauda ya sallami Abna, Abna kuma ya koma da salama.
22Sai sojojin Dauda da Yowab suka dawo daga hari, tare da ganima mai tarin yawa. Amma Abna ba ya tare da Dauda a Hebran. Dauda ya rigaya ya sallame shi, Abna kuma ya tafi cikin salama.23Lokacin da Yowab da dukkan sojojin da ke tare da shi suka iso, aka gaya wa Yowab, "Abna ɗan Nã ya zo gun sarki, kuma sarki ya sallame shi, Abna kuma ya tafi cikin salama."
24Sai Yowab ya zo wurin Sarki ya ce, "Mene ne ke nan ka yi? Duba, Abna ya zo wurin ka! Me yasa ka sallame shi, kuma ga shi ya tafi?25Baka sani ba Abna ɗan Nã ya zo domin ya yaudare ka ya kuma san shirye-shiryenka ya gane duk abubuwan da kake yi?"26Da Yowab ya bar Dauda, sai ya aika manzanni su bi Abna, suka kuma dawo da shi daga rijiyar Sira, amma Dauda bai san wannan ba.
27Da Abna ya dawo Hebron, Yowab ya kai shi gefe a tsakiyar ƙofa domin ya yi magana da shi a kaɗaice. Nan Yowab ya soke shi a ciki ya kashe shi. Da haka Yowab ya ɗau fansar jinin ɗan'uwansa. Asahel.
28Da Dauda ya ji wannan ya ce, "Da ni da mulkina baratattu ne a gaban Yahweh har abada game da jinin Abna ɗan Nã.29Bari alhakin mutuwar Abna ya faɗi kan Yowab da kuma dukkan gidan mahaifinsa. Bari kada a taɓa rasa a cikin iyalin Yowab wani wanda ke ɗigar miƙi ko ciwon fata ko kuma wanda ya ke gurgu kuma dole ya yi tafiya tokare da sanda ko kuma wanda takobi ya kashe shi ko wanda ya ke da rashin abinci."30Haka Yowab da ɗan uwansa Abishai suka kashe Abna, domin ya kashe ɗan uwansu Asahel a Gibiyan cikin yaƙi.
31Dauda ya cewa Yowab da dukkan mutanen da ke tare da shi, "Ku kekketa tufafinku, ku sa tsumoki, ku yi makoki a gaban gawar Abna."32Sarki Dauda ya bi bayan gawar cikin tawagar makokin. Suka binne Abna a Hebron. Sarki ya yi kuka da kururuwa mai ƙara a kabarin Abna, dukkan mutane kuma su ka yi kuka.
33Sarki ya yi makoki domin Abna ya yi waƙa, "Ya ƙyautu Abna ya mutu kamar yadda wawa ke mutuwa?34Ba wai an ɗaure hannuwanka ba. ‌Ƙafafunka ba a ɗaure su da sarƙa ba. Kamar yadda mutum yakan faɗi a gaban 'ya'yan rashin gaskiya, haka ka faɗi." Sai kuma dukkan mutane suka ƙara kuka a bisansa.
35Dukkan mutane suka zo su sa Dauda ya ci abinci tun da sauran rana. Amma Dauda ya rantse, "Bari Allah ya hukunta ni, ya kuma ƙara yi, idan na ci abinci ko wani abu kafin rana ta faɗi."36Dukkan mutane suka lura da ɓacin ran Dauda, suka ji daɗi, duk abin da sarki ya yi suka ji daɗin sa.
37Sai dukkan mutane da kuma dukkan Isra'ila suka gane a ranar nan ba niyyar sarki ba ce a kashe Abna ɗan Nã.38Sarki ya cewa barorinsa, "Ba ku sani basarake da kuma babban mutum ne ya faɗi yau a cikin Isra'ila ba?39Yanzu na rarrauna yau, koda shi ke ni sarki ne zaɓaɓɓe. Waɗannan mutane, 'ya'yan Zeruya, sun fi kowa mugunta a gare ni. Bari Yahweh ya sãka wa mugu da hukuncin da ya cancanci muguntarsa."

4

1Lokacin da Ishboshet, ɗan Saul, ya ji Abna ya mutu a Hebron, sai hannuwasa suka yi rauni, dukkan Isra'ila suka tsorata.‌2Ɗan Saul yana da mutane biyu waɗanda shugabanni ne na ƙungiyoyin sojoji. Sunan ɗayan Bãna ɗayan kuma Rekab, 'ya'yan Rimon Babirote na mutanen Benyamin (gama ana ɗaukar Birot a yankin Benyamin ta ke),3Birotiyawa sun gudu ne zuwa Gittam kuma har yau suna zama a can.

4Yanzu dai, Yonatan ɗan Saul, yana da ɗa wanda gurgu ne a ƙafa. Yana da shekara biyar sa'ad da labari ya zo akan Saul da Yonatan daga Yeziril. Sai mai renonsa ta ɗauke shi don ta gudu da shi. Amma da ta ke gudu, sai ɗan Yonatan ya faɗi ya gurgunce. Sunansa Mafiboshet.
5Sai 'ya'yan Rimon Babirote, Rekab da Ba'ana, suka yi tafiya cikin zafin rana zuwa gidan6Mafiboshet lokacin da ya ke hutawa da tsakar rana. Matar da ke tsaron ƙofar barci ya kwashe ta sa'ad da ta ke tankaɗen alkama, sai Rekab da Bãna suka yi sanɗo shuru suka wuce ta.7To bayan da suka shiga ɗakin, sai suka faɗa masa suka kashe shi sa'ad da ya ke ƙwance kan gadonsa. Suka yanke kansa suka tafi da shi, suka yi tafiya dukkan dare zuwa Araba.
8Suka kawo kan Mafiboshet gun Dauda a Hebron, suka kuma ce da sarki, "Duba, wannan kan Mafiboshet ɗan Saul ne, maƙiyinka, wanda ya nemi ranka. Yau Yahweh ya sãka wa maigidanmu sarki gãba da Saul da zuriyarsa."9Dauda ya amsa wa Rekab da Bãna ɗan'uwansa, 'ya'yan Riman Babirote; ya ce masu, "Na rantse da ran Yahweh, wanda ya ceci raina daga kowacce wahala,10dã wani ya gaya mani; 'Duba, Saul ya mutu,' yana tsammanin ya kawo labari mai daɗi, sai na danƙe shi na kashe shi a Ziglag. Wannan shi ne ladan dana bashi don labarinsa mai daɗi.
11To ba zan yi fiye da haka ba, sa'ad da mugayen mutane suka kashe mutum marar laifi a cikin gidansa a kan gadonsa, yanzu ba zan nemi jininsa daga hannunku in kuma tumbuƙe ku daga duniya ba?"12Sa'an nan Dauda ya umarci samari, suka kashe su suka yanke hannuwansu da ƙafafunsu kuma suka rataye su a gaɓar tafki a Hebron. Amma suka ɗauki kan Mefiboshet suka binne shi a kabarin Abna a Hebron.

5

1Sa'an nan dukkan kabilun Isra'ila suka zo gun Dauda a Hebron suka ce, "Duba mu jikinka ne da ƙashinka.2A kwanakin baya, da Saul ya ke mulki bisanmu, kai ne ka bi da rundunar yaƙi ta Isra'ila. Yahweh ya ce maka, "Za ka yi kiwon jama'ata Isra'ila, za ka kuma zama sarki bisa Isra'ila.'"

3Sai dukkan dattawan Isra'ila suka zo wurin sarki a Hebron, Sarki Dauda ya yi alƙawari da su a gaban Yahweh. Suka naɗa Dauda sarki bisa Isra'ila.4Dauda yana da shekaru talatin sa'ad da ya fara sarauta, ya kuma yi mulki shekara arba'in.5A Hebron ya yi mulkin bisa Yahuda shekaru bakwai da wata shida, kuma a Yerusalem ya yi mulki shekaru talatin da uku bisa dukkan Isra'ila da Yahuda.
6Sarki da mutanensa suka zo Yerusalem gãba da Yebusiyawa, mazamnan ƙasar. Suka cewa Dauda, "Ba za ka iya zuwa nan sai dai idan makafi da guragu ne za su kore ka. Dauda ba zai iya zuwa nan ba."7Duk da haka Dauda ya ci kagarar Sihiyona, wadda yanzu shi ne birnin Dauda.
8A lokacin nan Dauda ya ce, "Waɗanda suka hari Yebusiyawa dole su bi ta wuriyar ruwa domin su kai ga "guragu da makafi' waɗanda su ne maƙiyan Dauda." Shi yasa mutane ke cewa, "Da 'makafi da kuma guragu' ba za su shiga fãda ba."9Sai Dauda ya zauna cikin kagara ya kira shi birnin Dauda. Ya tsare shi da gine- gine kewaye da shi tun daga waje zuwa ciki.10Dauda ya ƙasaita domin Yahweh, Allah mai runduna, yana tare da shi.
11Sa'an nan Hiram sarkin Taya ya aika da manzanni gun Dauda, da itacen sida, da masassaƙa da masu fãsa duwatsu. Suka gina wa Dauda gida.12Dauda ya sani Yahweh ya naɗa shi sarki bisa Isra'ila kuma ya ɗaukaka masarautarsa sabili da mutanensa Isar'ila.
13Bayan da Dauda ya bar Hebron ya zo Yerusalem, ya ƙara ɗaukar ƙwaraƙwarai da mataye a Yerusalem, aka ƙara haifa masa 'ya'ya maza da 'ya'ya mata.14Waɗannan su ne sunayen yaran da aka haifa masa a Yerusalem: Shammuwa, Sobab, Natan, Suleman,15Ibha, Elisuwa, Nefeg, Yafiya,16Elishama, Eliyada, da Elifelet
17Da dai Filistiyawa suka ji cewa an naɗa Dauda sarki bisa Isra'ila, sai suka fita dukka suna nemansa. Amma Dauda ya ji abin, sai ya gangara zuwa mafaƙa.18Yanzu Filistiyawa sun rigaya sun fito sun bazu a Kwarin Refayim.
19Sai Dauda ya roƙi taimako daga Yahweh. Ya ce, "Ko in hari Filistiyawa? Za ka bani nasara akan su?" Yahweh ya cewa Dauda, "Ka hare su, domin hakika zan ba ka nasara bisa Filistiyawa."20Sai Dauda ya kai hari a Ba'al Ferazim, a nan ya kayar da su. Ya ce haka, "Yahweh ya fantsamo cikin maƙiyana a gabana kamar fantsamowar ruwan ambaliya." Saboda haka sunan wurin ya zama Ba'al Ferazim.21Filistiyawa suka bar gumakunsu a nan, Dauda kuma da mutanensa suka ɗauke su suka tafi da su.
22Sai Filistiyawa suka sake tasowa kuma suka ƙara bazuwa cikin Kwarin Refayim.23Sai Dauda ya sake roƙon taimako daga Yahweh. Yahweh kuma ya ce masa, "Kada ka kai hari ta gabansu, maimakon haka ka zagaya ta bayansu ku afka masu ta cikin itatuwan tsamiya.
24Sa'ad da kuka ji ƙarar takawar yaƙi cikin iska da ke bugawa a ƙwanƙolin itatuwan tsamiya, sai ku kai hari da karfi. Kuyi wannan domin Yahweh ya rigaya ya sha gabanku ya hari rundunar Filistiyawa."25Sai Dauda ya yi yadda Yahweh ya umarce shi. Ya kashe Filistiyawa daga Geba har zuwa Geza.

6

1Dauda ya sake tattaro dukkan zaɓabbun mutanen Isra'ila, dubu talatin.2Dauda ya tashi ya tafi da dukkan mutanensa da ke tare da shi daga Bãla cikin Yahuda domin a ɗauko akwatin Yahweh daga can wanda ake kira da sunan Yahweh mai runduna, wanda ya ke zaune a kursiyi bisa kerubim.

3Suka ɗora akwatin Yahweh bisa sabuwar karusa. Suka fito da shi daga gidan Abinadab, da ke kan wani tudu. Uza, da Ahiyo, 'ya'yansa, suke bi da sabuwar karusar.4Suka fito da karusar daga gidan Abinadab daga kan tudu tare da akwatin Yahweh a bisan sa. Ahiyo na tafiya a gaban akwatin.5Sai Dauda da dukkan gidan Isra'ila suka fara wasa a gaban Yahweh, suna biki tare da sassaƙaƙƙun kayayyakin waƙa, molaye, garayu, kacau-kacau, da kuge.
6Da suka iso masussukar Nakon, sai sãn ya yi tuntuɓe, sai Uza ya miƙa hannunsa ya tallafi akwatin Allah, ya kuma kama shi.7Sai fushin Yahweh ya yi ƙuna a kan Uza. Allahj ya kai masa hari nan take sabili da zunubinsa. Uza ya mutu nan take da akwatin Allah.
8Dauda ya yi fushi domin Yahweh ya kai wa Uza hari, ya kira sunan wurin nan Ferez Uza. Wurin nan har yau ana kiransa Ferez Uza.9Dauda ya ji tsoron Yahweh a ranan nan. Ya ce, "Ƙaƙa akwatin Yahweh zai zo gare ni."
10Saboda haka Dauda bai so ya ɗauki akwatin Yahweh tare da shi zuwa cikin birnin Dauda ba. Maimakon haka, sai ya ajiye shi a gefe cikin gidan Obed Idom Bagitte.11Akwatin Yahweh ya kasance a gidan Obed Idom Bagitte wata uku. Sai Yahweh yasa masa albarka da dukkan gidansa.
12Sai aka gaya wa sarki Dauda, "Yahweh ya albarkaci gidan Obed Idom da dukkan abubuwan da ke nasa saboda akwatin Yahweh" Sai Dauda ta tafi ya ɗauko akwatin Yahweh daga gida Obed Idom zuwa birnin Dauda da murna.13Lokacin da waɗanda suke ɗauke da akwatin Yahweh suka yi tafiya taki shida, sai ya yi hadayarsa da kiwataccen ɗan maraƙi.
14Dauda ya yi rawa a gaban Yahweh da dukkan ƙarfinsa; yana sanye da ɗan feton lilin kaɗai.15Sai Dauda da dukka gidan Isra'ila suka ɗauko akwatin Yahweh tare da sowa da kuma ƙarar ƙahonni.
16Sa'ad da akwatin Yahweh ya shigo birnin Dauda, Mikal, ɗiyar Saul, ta leƙa waje ta taga. Ta ga Sarki Dauda yana tsalle yana rawa a gaban Yahweh. Sai ta rena shi a zuciyarta.17Suka kawo akwatin Yahweh ciki suka ajeye shi a mazauninsa, a tsakiyar rumfar da Dauda ya shirya dominsa. Sai Dauda ya miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama a gaban Yahweh.
18Lokacin da Dauda ya gama miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama ya albarkaci mutane a cikin sunan Yahweh mai runduna.19Sai ya rarraba wa dukkan mutane, dukkan cin-cirindon Isra'ila gaba ɗaya, maza da mata, dunƙulen gurasa, ɗan gutsuren nama, da wainar kauɗar inabi. Sa'annan dukkan mutane suka tafi, kowanne ɗayan su ya koma zuwa nasa gida.
20Sai Dauda ya koma ya albarkaci iyalinsa. Mikal, ɗiyar Saul, ta fito ta taryi Dauda ta ce, "Ina misalin girmamawar da sarkin Isra'ila ya samu yau, wanda ya tsirance kansa yau a idanun bayi 'yan mata cikin barorinsa, kamar ɗaya daga cikin ashararrun mutane wanda ba ko kunya yana tsiraratar da kansa!"
21Dauda ya amsa wa Mikal, "Na yi wannan a gaban Yahweh, wanda ya zaɓe ni fiye da mahaifinki fiye kuma da dukkan iyalin gidansa, wanda ya aza ni shugaba bisa mutanen Yahweh, bisa Isra'ila, A gaban Yahweh zan yi murna!22Zan zama ma da tawali'u fiye da haka, in kuma kunyata a idanuna ma. Amma game da 'yan mata bayi da kika ambata, za a girmamani."23Saboda haka Mikal ɗiyar Saul, ba ta da 'ya'ya har ranar mutuwarta.

7

1Ya zamana sa'ad da sarki yana zaune cikin gidansa, kuma Yahweh ya bashi hutu daga dukkan maƙiyansa kewaye,2sarki ya cewa annabi Natan, "Duba, ina zaune cikin gidan sida, amma akwatin Yahweh yana zaune a cikin tsakiyar rumfa."

3Sai Natan ya cewa sarki, "Je ka, ka yi abin da ke zuciyarka, gama Yahweh yana tare da kai."4Amma a daren nan maganar Yahweh ta zo gun Natan cewa,5"Ka tafi ka gaya wa bawana Dauda, "Wannan shi ne abin da Yahweh ya faɗi: Zaka gina mani gida inda zan zauna a ciki?
6Gama ban taɓa zama a cikin gida ba daga ranar da na fitar da mutanen Isra'ila daga Masar har zuwa rana ta yau; maimakon haka ina ta yawo a cikin rumfa, a rumfar sujada.7A dukkan wuraren dana yi yawo a cikin mutanen Isra'ila, na taɓa gaya wa wani ɗaya daga cikin shugabannin Isra'ila wanda na naɗa ya yi makiyayancin mutanena Isra'ila, cewa, "Donme ba ka gina mani gidan itatuwan sida ba?'"'
8Yanzu dai, ka gaya wa bawana Dauda, "Wannan shi ne abin da Yahweh mai runduna ya ce: "Na ɗauko ka daga makiyaya, daga bin tumaki, domin ka zama mai mulki bisa mutanena Isra'ila.9Na kasance tare da kai duk inda ka tafi. Na datse dukkan maƙiyan ka daga gaban ka. Yanzu zan sa sunanka ya shahara kamar sunayen shahararrun nan na duniya.
10Zan sanya wa mutanena Isra'ila wuri, zan kuma kafa su a can, domin su zauna a mazaunin kansu kuma ba za a ƙara wahalshe su ba. Mugayen mutane ba za su ƙara zambatar su ba, kamar yadda suka yi a dã,11kamar yadda suke ta yi daga ranar dana umarci alƙalai su kasance bisa mutane na Isra'ila. Yanzu zan ba su hutawa daga dukkan magabtansu. Bugu da ƙari, "Ni, Yahweh, na furta maka cewa zan yi maka gida.
12Sa'ad da kwanakinka suka cika kuma ka kwanta tare da ubanninka, zan tada wani daga zuriyar ka a bayan ka, wanda zai fito daga cikin jikinka, kuma zan kafa mulkinsa.13Shi zai gina gida domin sunana, kuma ni zan kafa kursiyin mulkinsa har abada.14Zan zama uba a gare shi, shi kuma zai zama ɗana. Idan ya yi zunubi, zan hore shi da sandar mutane da kuma bulalar 'ya'yan mutane.
15Amma alƙawarin amincina ba zai barshi ba, kamar yadda da na ɗauke shi daga Saul, wanda na kawar daga gabana.16Gidanka da mulkinka za a tabbatar har abada a gabanka. Kursiyinka zai tabbata har abada.'"17Natan ya yi magana da Dauda ya kuma gaya masa dukkan maganganun nan, ya kuma gaya masa game da wahayin dukka.
18Sai sarki Dauda ya shiga ciki ya zauna a gaban Yahweh ya ce, "Wane ne ni, Yahweh Allah, kuma mene ne iyalina har daka kawo ni ga haka?19Yanzu dai wannan ƙaramin abu ne a idonka, Ubangiji Yahweh. Har ma ka yi magana game da iyalin bawanka a kan lokatai masu zuwa, ka kuma nuna mani tsararraki masu zuwa, Ubangiji Yahweh!20Me kuma ni, Dauda, zan ce maka? Ka girmama bawanka, Ubangiji Yahweh.
21Sabili da maganarka, domin kuma ka cika nufinka, ka yi wannan babban abu kuma ka bayyana shi ga bawanka.22Saboda haka kai mai girma ne, Ubangiji Yahweh, domin babu wani kamar ka, kuma babu wani Allah sai kai, kamar yadda muka ji da kunnuwanmu.23Wacce al'umma ce kamar mutanenka Isra'ila, al'umman nan guda ɗaya a duniya wadda, kai Allah, ka je ka fanshe mu domin kanka? Ka yi wannan domin su zama mutanenka, domin ka yiwa kanka suna, ka kuma yi manyan al'amura dana ban tsoro domin ƙasarka. Ka kori al'ummai da gumakunsu daga gaban mutanenka, waɗanda ka kuɓutar da su daga Masar.
24Ka kafa Isra'ila a matsayin mutanenka har abada, kuma kai, Yahweh, ka zama Allahnsu.25Saboda haka yanzu, Yahweh Allah, bari alƙawarin da ka yi game da bawanka da iyalinsa ya tabbata har abada. Ka yi yadda ka faɗa.26Bari sunanka ya zama da girma har abada, domin mutane su ce, Yahweh mai runduna shi ne Allah na Isra'ila,' sa'an nan gidana ni, Dauda, bawanka ya tabbata a gaban ka.
27Domin kai, Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ka bayyana wa bawanka cewa za ka gina masa gida. Shi yasa, ni, bawanka, na sami ƙarfin hali in yi addu'a gare ka.28Yanzu dai, Ubangiji Yahweh, kai ne Allah, maganganunka abin dogara ne a gare su, kuma ka yi wannan alƙawari mai ƙyau ga bawanka.29Yanzu dai, bari ya gamsheka ka albarkaci gidan bawanka, domin ya dawwama a gabanka har abada. Domin kai, Ubangiji Yahweh, ka faɗi waɗannan abubuwa, da kuma albarkarka gidan bawanka zai zama da albarka har abada."

8

1Bayan wannan ya zamana Dauda ya hari Filistiyawa ya kuma ci su, Sai Dauda ya karɓe Gat da ƙauyukanta daga karkashin linzamin Filistiyawa.

2Sa'an nan ya buga Mowabawa, ya gwada mutanensu da igiya ta wurin sasu su kwanta a ƙasa. Ya gwada layi biyu da zai kashe, layi ɗaya mai tsawo sosai da zai bari da rai. Haka Mowabawa suka zama bayi ga Dauda suka biya shi haraji.
3Dauda ya buga Hadadeza ɗan Rehob, sarkin Zoba, sa'ad da Hadadeza ya ke tafiya garin ya mai da mulkinsa na dã wajen Kogin Efratis.4Dauda ya ƙwace karusai daga gunsa guda 1,700 da matafiya a ƙasa dubu ashirin. Dauda ya yanke jijiyar ƙafafun dawakai masu jan karusai, amma ya bar wasu domin karusai ɗari.
5Lokacin da Armeniyawa na Damaskus suka zo su taimaki Hadadeza sarkin Zoba, Dauda ya kashe Armeniyawa mutum dubu ashirin da biyu.6Sai Dauda ya ajiye ƙungiyoyin sojojinsa a Aram ta Damaskus, kuma Armeniyawa suka zama bayinsa suna biyan haraji. Yahweh ya ba Dauda nasara duk inda ya tafi.
7Dauda ya ɗauko garkuwoyin zinariya da suke kan bayin Hadadeza ya kawo su Yerusalem.8Daga Beta da Berotai, biranen Hadadeza, Sarki Dauda ya kwaso tagulla masu ɗumbun yawa.
9Da Tou, sarkin Hamat, ya ji Dauda ya kayar da dukkan rundunar Hadadeza,10Tou ya aika Hadoram ɗansa gun Sarki Dauda ya gaishe shi ya kuma sa masa albarka, domin Dauda ya yi yaƙi gãba da Hadadeza ya kuma ci shi, domin kuma a dã Hadadeza ya yi yaƙi gãba da Tou. Hadoram kansa ya zo tare da kayayyakin azurfa, zinariya, da tagulla.
11Sarki Dauda ya ƙeɓe waɗannan kayayyaki domin Yahweh, su azurfa da zinariya daga dukkan al'umman da ya ci da yaƙi -12Aram, Mowab, da mutanen Ammon, da Filistiyawa, da Amelik, tare kuma da dukkan kayayyakin ganima na Hadadeza ɗan Rehob sarkin Zoba.
13Sunan Dauda ya shahara sa'ad da ya komo daga bugun Armeniyawa cikin Kwarin Gishiri, da su da mutanensu dubu goma sha takwas.14Ya ajiye ƙungiyoyin sojoji cikin dukkan yankin Idom, dukkan Idomiyawa suka zama bayi gare shi. Yahweh ya ba Dauda nasara duk inda ya tafi.
15Dauda ya yi mulki bisa dukkan Isra'ila, ya kuma aikata adalci da gaskiya ga dukkan mutanensa.16Yowab ɗan Zeruya shi ne shugaban rundunar yaƙi, Yehoshafat ɗan Alihud kuwa shi ne magatakarda.17Zadok ɗan Ahitub da Ahimelek ɗan Abiyata su ne firistoci, Seraya ne marubuci.18Binaya ɗan Yehoyaida shi ne mai lura da Keretiyawa da Feletiyawa, 'ya'yan Dauda su ne manyan hakimai masu ba sarki shawara.

9

1Dauda yace, "Akwai ko ɗaya wanda ya rage cikin iyalin Saul wanda zan nuna masa alheri sabili da Yonatan?"2Akwai wani bawa cikin iyalin Saul mai suna Ziba, aka kuma kira shi ga Dauda. Sarki ya ce masa, "Kai ne Ziba," Ya amsa, "I. Ni ne bawanka."

3Sai sarki yace, "Babu ko ɗaya da ya rage daga iyalin Saul wanda zan nuna masa alherin Allah." Ziba ya amsa wa sarki, "Yonatan har yanzu yana da ɗa, wanda yana da gurguntaka."4Sarki ya ce masa, "Ina ya ke." Ziba ya amsa wa sarki ya ce, "Duba, yana cikin gidan Maki ɗan Ammiyel a Lo Deba."
5Sa'an nan Sarki Dauda ya aika a ka fito da shi daga gidan Maki ɗan Ammiyel a Lo Deba.6Sai Mefiboshet ɗan Yonatan ɗan Saul, ya zo gun Dauda ya russuna fuskarsa ƙasa ya girmama Dauda. Dauda ya ce, '"Mefiboshet," Ya amsa, "Duba, ni baranka ne!"
7Dauda ya ce masa, "Kada ka ji tsoro, gama hakika zan nuna maka alheri sabili da Yonatan mahaifinka, kuma zan mayar maka dukkan ƙasar kakanka, za ka kuma ci kullum a teburina."8Mefiboshet ya russuna ya ce, "Wane ne ni baranka, da za ka dube ni da tagomashi mataccen kare kamar ni?"
9Sai sarki ya kira Ziba, baran Saul, ya ce masa, "Duk mallakar Saul da iyalinsa na ba jikan ubangidanka.10Da kai, da 'ya'yanka maza, da kuma barorinka dole ku noma masa gonakansa dole kuma ku yi masa girbi domin jikan ubangidanka ya sami abinci. Gama dole Mefiboshet, jikan ubangidanka, ya riƙa ci kullum a teburina." Ziba yana da 'ya'ya maza goma sha biyar da barori ashirin.
11Sai Ziba ya cewa sarki, bawanka zaiyi dukkan abin da ubangijinsa sarki ya dokaci bawansa." Sarki ya ƙara da cewa, "Game da Mefiboshet zai riƙa ci a teburina, kamar ɗaya daga cikin 'ya'yan sarki."12Mefiboshet yana da wani ɗa ƙarami mai suna Mika, Duk waɗanda suke zauna a gidan Ziba barori ne na Mefiboshet.13Sai Mefiboshet ya zauna a Yerusalem, kullum kuwa ya na ci a teburin sarki, koda shi ke gurgu ne a dukkan ƙafafunsa biyu.

10

1Ananan da jimawa sai sarkin mutanen Ammon ya mutu, kuma ɗansa Hanun ya zama sarki a madadinsa.2Dauda ya ce, "Zan nuna alheri ga Hanun ɗan Nahas, kamar yadda mahaifinsa ya nuna mani alheri." Sai Dauda ya aiki barorinsa su kai ta'aziya ga Hanun domin mahaifinsa. Barorinsa suka shiga ƙasar mutanen Ammon.3Amma shugabannin mutanen Ammon suka cewa Hanun ubangijinsu, Kana tsammani da gaske Dauda ya ke girmama mahaifinka saboda ya aiko mutane su yi maka ta'aziya? Ba Dauda ya aiko barorinsa domin su dubi birnin ba, su san shi, domin su hallaka shi?"

4Sai Hanun ya ɗauki barorin Dauda, ya aske rabin gemunsu, ya yanke rigunansu har zuwa ɗuwawunsu, a sa'annan ya sallame su suka tafi.5Da suka labarta wa Dauda wannan, ya aika domin ya sadu da su, domin mutanen sun kunyata ainun. Sarki ya ce, "Ku dakata a Yeriko har sai gemunku ya toho, sa'annan ku dawo.
6Lokaci da mutanen Ammon suka ga sun zama abin ƙyama ga Dauda, sai suka aika manzanni suka kuma yi hayar Aremiyawan Bet Rehob da Zoba, da sojoji 'yan tafiya a ƙasa dubu ashirin, da sarkin Mãka mai dubun mutane, da mutanen Tob masu mutane dubu goma sha biyu.7Da Dauda ya ji haka, sai ya aiki Yowab da dukkan rundunar sojoji.8Ammonawa suka fito suka ja dagar yaƙi a mashigar ƙofar garinsu, Aremiyawan Zoba kuwa da na Rehob, da kuma mutanen Tob da Mãka, suka tsaya su kaɗai a filaye.
9Da Yowab ya ga dagar yaƙi biyu sun fuskance shi gaba da baya, sai ya zaɓi ƙwararrun mayaƙa na Isra'ila ya jera su gãba da Aremiyawa.10Sauran rundunar kuwa, ya bashe su ƙarƙashin jagorancin Abishai ɗan'uwansa ya sa kuma suka ja dagar yaƙi gaba da rundunar Ammon.
11Yowab ya ce, Idan Aremiyawa suka sha ƙarfi na, sai kai Abishai ka ƙwace ni, amma idan rundunar Ammon suka sha ƙarfinka zan zo in ƙwace ka.12Ku ƙarfafa, mu kuma nuna kanmu masu ƙarfi ne domin mutanenmu da kuma biranen Allahnmu, gama Yahweh zai yi abin da ke da kyau domin nufinsa.
13Sai Yowab da sojojin rundunarsa suka tashi zuwa yaƙi gãba da Aremiyawa waɗanda dole suka gudu daga gaban rundunar Isra'ila.14Da rundunar Ammoniyawa suka ga Aremiyawa sun gudu, sai suma suka gudu daga Abishai suka koma cikin birni. Sai Yowab ya dawo daga fafarar mutanen Ammon ya koma Yerusalem.
15Da Aremiyawa suka ga Isra'ila na cinsu, suka sake tattara kansu.16Sai Hadareza ya aika sojojin Aremiya su zo daga ƙasar ƙetaren Kogin Yuferetis. Suka zo Helam da Shobak, sarkin yaƙi na rundunar Hadareza ya shugabance su.
17Da aka gaya wa Dauda wannan, sai ya tara dukkan Isra'ila gaba ɗaya, suka haye Yodan, suka iso Helam. Aremiyawa suka ja dagar yaƙi gãba da Dauda suka yaƙe shi.18Aremiyawa suka gudu a gaban Isra'ila. Dauda ya kashe mahayan karusai ɗari bakwai na Aremiyawa, da dubu arba'in na mahaya dawakai. Shobak sarkin yaƙin rundunarsu aka ji masa rauni, ya mutu a nan.19Sa'ad da dukkan sarakunan da ke barorin Hadareza suka ga Isr'ila ta ci su, sai suka biɗi sulhu da Isra'ila suka zama bayinsu. Sai Aremiyawa suka ji tsoron su ƙara taimakon mutanen Ammon.

11

1Ya zamana da bazara, lokacin da sarakuna ke tafiya yaƙi, sai sarki Dauda ya aiki Yowab, da barorinsa, da dukkan rundunar Isra'ila. Suka ragargaza rundunar Ammon, suka kafa wa Rabba sansani. Amma Dauda ya zauna a Yerusalem.

2A na nan wata rana da yammaci, Dauda ya tashi daga gadonsa yana tafiya a kan soron fadarsa, Daga nan ya hango wata mata wadda take wanka, matar kuwa kyakkyawa ce ƙwarai abar sha'awa.3Sai Dauda ya aika ya kuma tambayi mutane waɗanda suka san wani abu game da matar. Sai wani ya ce, "Ashe wannan ba Batsheba ce ba, ɗiyar Eliyam, kuma ashe ba matar Yuriya ba ce Bahitte?"
4Dauda ya aika manzanni, aka ɗaukota, ta shiga ciki wurinsa sai ya kwana da ita (gama ba ta daɗe da tsarkake kanta daga hailarta ba). Sa'an nan ta koma gidanta.5Matar ta yi ciki sai ta aika aka gaya wa Dauda; ta ce, "Ina da ciki."
6Sai Dauda ya aika wurin Yowab, "Ka aiko mani Yuriya Bahitte. Sai Yowab ya aika wa Dauda Yuriya.7Da Yuriya ya iso, Dauda ya tambaye shi yadda Yowab ya ke, yadda rundunar take, da kuma yadda yaƙin ke tafiya.8Dauda ya cewa Yuriya, "Ka gangara zuwa gidanka, ka wanke ƙafafuwanka." Sai Yuriya ya bar fadar sarki, sai sarki ya aika wa Yuriya kyauta bayan tafiyarsa.
9Amma Yuriya ya yi barci a ƙofar fadar sarki tare da dukkan barorin maigidansa, bai kuwa gangara zuwa gidansa ba.10Da aka gaya wa Dauda, "Yuriya bai gangara zuwa gidansa ba." Dauda ya cewa Yuriya, "Ashe ba yanzu ka dawo daga tafiya ba, me yasa ba ka tafi gida ba?"11Yuriya ya amsa wa Dauda, "Akwatin alƙawari, da Isra'ila da Yahuda suna zaune cikin rumfa, maigidana kuma Yowab da barorin maigidana sun kafa sansani a fili.‌ Ƙaƙa fa zan tafi cikin gidana in ci in sha in kuma kwana da mata ta? Na rantse da ranka, ba zan yi wannan abu ba."
12Sai Dauda ya cewa Yuriya, "Ka zauna a nan gobe zan barka ka tafi." Sai Yuriya ya zauna a Yerusalem ranar nan da kashegari kuma. Lokacin da Dauda ya kira shi, ya ci ya sha a gabansa,13Dauda ya bugar da shi. Da yamma Yuriya ya fita ya je ya kwanta a gadonsa tare da barorin maigidansa bai gangara zuwa gidansa ba.
14Saboda haka da safe Dauda ya rubuta wa Yowab takarda, ya ba da ita ta hannun Yuriya.15Dauda ya rubuta cikin wasiƙar cewa, "A sa Yuriya a gaba in da yaƙi yafi zafi sosai, sa'an nan ku janye daga gare shi, domin a buge shi ya mutu."
16Sa'ad da Yowab ya kafa wa birnin daga, ya sa Yuriya a inda ya sani ƙarfafan sojojin abokan gaba za su yi yaƙi.17Da mutanen garin suka fito suka gwabza yaƙi da rundunar Yowab, waɗansu sojojin Dauda suka faɗi, kuma Yuriya Bahitte shi ma aka kashe shi a wurin.
18Da Yowab ya aika saƙo ga Dauda yadda dukkan abu ya gudana a yaƙin,19ya umarci manzon cewa, '"Sa'ad da ka gama faɗin komai game da yaƙin ga sarki,20mai yiwuwa sarki ya husata, ya kuma ce maka, "Me ya sa kuka matsa kusa da birnin kuka yi yaƙi? Ba ku sani za su yiwo harbi daga garun ba?
21Wa ya kashe Abimelek ɗan Yerubeset? Ba wata mace ce ta jeho dutsen niƙa daga kan garu a kansa ba, sai ya zo ya mutu a Tebez? Me ya sa kuka matsa kurkusa da garun?' Sa'an nan dole za ka amsa, "Bawanka Yuriya Bahitte shi ma ya mutu.'"
22Sai manzon ya tashi ya tafi wurin Dauda ya faɗa masa dukkan abin da Yowab ya aike shi ya faɗa.23Sai manzon ya cewa Dauda, "Abokan gãba suka fi mu ƙarfi da fari; suka fafaremu har zuwa jeji, amma muka kora su baya har zuwa ƙofar gari.
24Sai maharbansu suka harbi sojojinka daga kan garu, aka kashe waɗansu barorin sarki, shi ma baranka Yuriya Bahitte an kashe shi."25Sai Dauda ya cewa manzon, "Ka faɗa wa Yowab wannan, 'Kada ka da mu, 'Kada ka bar wannan ya ɓata maka rai, gama takobi ya kan hallakar da wannan da kuma wancan. Ka matsa wa birnin lamba da yaƙi, ku kãda shi,' ka kuma ƙarfafa shi."
26Sa'ad da matar Yuriya ta ji cewa Yuriya mijinta ya mutu, ta yi makoki sosai domin mijnta.27Sa'ad da makokinta ya wuce, Dauda ya aika aka ɗaukota aka kawota gida a fãdarsa, ta zama matarsa ta kuma haifa masa yaro. Amma abin da Dauda ya yi ya baƙanta wa Yahweh rai.

12

1Sa'an nan Yahweh ya aiki Natan wurin Dauda. Ya tafi wurinsa ya ce, "A kwai waɗansu mutum biyu cikin wani birni.‌ Ɗaya mutumin mai arziƙi ne ɗayan kuwa matalauci.2Mai arziƙin na da tumaki masu tarin yawa a garkunansa,3amma talakan nan ba shi da komai sai dai wata 'yar ƙaramar tunkiya, wacce ya saya ya yi kiwonta. Ta yi girma tare da shi da kuma yaransa. Har ma 'yar tunkiyar takan ci tare da shi ta kuma sha daga moɗarsa, takan yi barci cikin hannuwansa har ma kamar ɗiya take a gunsa. '

4Wata rana wani baƙo ya zo gun mutumin nan mai arziƙi, amma mai arziƙin nan bai so ya ɗauki dabba daga cikin nasa garken domin ya ciyar da shi ba. Mai makon haka ya ɗauki 'yar tunkiyar matalaucin nan ya yi wa baƙon abinci da ita.5Dauda ya husata ƙwarai gãba da mutumin nan mai arziƙi, sai ya tasar wa Natan da ihu,6"Na rantse da ran Yahweh, mutumin da ya yi wannan ya cancanci mutuwa. Dole ya biya ninki huɗu tamanin 'yar tunkiyan nan domin ya yi wannan domin kuma bai ji tausayin matalaucin nan ba.
7Sai Natan ya cewa Dauda, "Kai ne mutumin! Yahweh, Allah na Isra'ila, ya ce, 'Na naɗa ka sarki bisa Isra'ila, na kuma kuɓutar da kai daga hannun Saul.8Na baka gidan ubangidanka, da matan ubangidanka a hannnuwanka. Na kuma ba ka gidan Isra'ila da Yahuda. Idan dã waɗannan sun yi ƙanƙanta dana ba ka waɗansu abubuwa ƙari bisansu.
9To me yasa ka raina dokokin Yahweh, har ka aikata abin da ke na mugunta a idonsa? Ka kashe Yuriya Bahitte da takobi ka ɗauki matarsa ta zama matarka. Ka kashe shi da takobin rundunar Ammon.10Saboda haka yanzu takobi ba zata taɓa rabuwa da gidanka ba, domin ka rena ni ka ɗauki matar Yuriya Bahitte ta zama matarka.'
11Yahweh ya ce, "Duba, zan tayar maka da masifa gãba da kai daga cikin gidanka. A idanunka, zan ɗauki matanka in ba da su ga maƙwabcinka, zai kwana da matanka rana katã.12Gama ka yi naka zunubin a asirce, amma ni zan yi wannan a gaban duk Isra'ila, rana katã.'"13Sai Dauda ya cewa Natan, "Na yiwa Yahweh zunubi." Natan ya amsa wa Dauda, "Yahweh ma ya shafe zunubinka. Ba za a kashe ka ba.
14Duk da haka, domin ta wurin yin wannan ka rena Yahweh, yaron da za a haifa maka hakika zai mutu."15Sa'an nan Natan ya bar shi ya tafi gida. Yahweh ya kai wa yaron da matar Yuriya ta haifa Dauda hari, da matsanancin ciwo.
16Dauda ya roƙi Yahweh domin yaron. Dauda ya yi azumi ya shiga cikin ɗaki ya kwanta a ƙasa dukkan dare.17Dattawan gidansa suka tashi suka tsaya a gefensa, domin su tashe shi daga ƙasa, amma yaƙi ya tashi kuma ya ƙi ya ci tare da su.18Sai ya zamana a rana ta bakwai yaron ya mutu. Barorin Dauda suka ji tsoron su gaya masa cewa yaron ya rasu, domin sun ce, "Duba, sa'ad da yaron ke raye mun yi masa magana bai saurari muryar mu ba. Me zai yiwa kansa idan muka ce masa yaron ya mutu?!"
19Amma da Dauda ya ga barorinsa suna raɗa da junansu, Dauda ya gane yaron ya mutu. Ya cewa barorinsa, "Yaron ya mutu?" Suka amsa, "Ya mutu."20Sai Dauda ya tashi daga ƙasa ya wanke kansa, ya shafa mai, ya canza rigunansa. Ya tafi zuwa rumfar sujada ta Yahweh, ya yi sujada a can, sa'an nan ya dawo fadarsa. Da ya buƙata, sai suka sa abinci a gabansa, ya kuma ci.
21Sai barorinsa suka ce masa, "Me yasa ka yi haka? Ka yi azumi da kuka saboda yaron, sa'ad da ya ke da rai, amma da yaron ya mutu, ka tashi ka ci abinci."22Dauda ya amsa, "Sa'ad da yaron ke da rai na yi azumi da kuka. Na ce, 'Wa ya sani watakila Yahweh zai yi mani alheri, ya bar yaron da rai?'23Amma yanzu ya mutu, to donme zan yi azumi? Zan iya komo da shi da rai ne? Ni zan je gunsa, amma shi ba zai komo wuri na ba."
24Dauda ya ta'azantar da Batsheba matarsa, ya shiga wurinta, ya kwana da ita. Daga baya ta haifi yaro, aka sa wa yaron suna Suleman. Yahweh ya ƙaunace shi25ya kuma aika da saƙo ta hannun annabi Natan cewa a sa masa suna Yedidiya, domin Yahweh ya ƙauna ce shi.
26Yanzu dai Yowab ya yi yaƙi gãba da Rabba, birnin masarautar mutanen Ammon, ya kama kagararta.27Sai Yowab ya aiki manzanni ga Dauda ya ce, "Na yaƙi Rabba, na kuma kama mashigar ruwan birnin.28Yanzu fa ka tattaro sauran rudunar ka kafa wa birnin sansani ka ci shi, domin in na ci birnin, za a kira shi da sunana."
29Sai Dauda ya tattaro dukkan rundunar ga baki ɗaya suka tafi Rabba; suka yaƙi birnin, suka ci shi.30Dauda ya cire kambin zinariya da ke kan sarkin - nauyinsa talanti guda ne na zinariya, akwai wani dutse mai daraja a cikinsa. Aka ɗora wannan kambi a kan Dauda. Sa'an nan ya fito da ganimar birnin masu ɗumbun yawa.
31Ya fitar da mutanen da ke cikin birnin, ya tislasta masu su yi aiki da zartuna, faretani, da gatura; ya kuma sa su su yi aiki a maginar tubali. Dauda ya tilasta wa dukkan biranen mutanen Ammon su yi wannan aiki tuƙuru. Sai Dauda da dukkan rundunarsa suka koma Yerusalem.

13

1Ya zama fa bayan wannan sai Amnon ɗan Dauda, ya yi sha'awar 'yar'uwarsa Tama kyakkyawa wanda ubansu ɗaya ne, amma 'yar'uwar Absalom ce uwa ɗaya uba ɗaya, shi ma ɗaya ne daga cikin 'ya'yan Dauda maza.2Amnon ya jarabtu har ya kama ciwo saboda 'yar 'uwarsa Tama. Ita kuwa budurwa ce, a ganin Amnon ba zai taɓa yiwuwa ya yi ma ta wani abu ba.

3Amma Amnon ya na da wani aboki mai suna Yonadab ɗan Shimeya, ɗan'uwan Dauda. Yehonadab wani mutum ne mai hila.4Yehonadab ya cewa Amnon, "Me yasa ga ka ɗan sarki, kake damuwa kowacce safiya? Ba za ka gaya mani ba?" Amnon ya amsa masa, "Ina ƙaunar Tamar, 'yar 'uwar ɗan'uwana Absalom."
5Sai Yonadab ya ce masa, "Ka kwanta a gadonka ka yi kamar baka da lafiya. Sa'ad da mahaifinka zai zo ganin ka, ka tambaye shi, "Idan ka yarda ka aiko Tama 'yar'uwata ta ba ni wani abu in ci, bari ta girka shi a gaba na, domin in gan shi in kuma ci shi daga hannunta?'"6Sai Amnon ya kwanta kamar ba shi da lafiya. Da sarki ya zo domin ya dube shi, Amnon ya cewa sarki, "Idan ka yarda ka aiko 'yar'uwata Tama ta yi mani ɗan abinci saboda rashin lafiyata domin in ci daga hannunta.'"
7Sai Dauda ya aika saƙo ga Tama a fãdarsa, cewa, "Ki tafi yanzu gidan ɗan'uwanki Amnon ki shirya masa abinci."8Sai Tama ta tafi gidan ɗan'uwanta Amnon in da ya ke kwance. Sai ta ɗauki ƙullu ta cuɗa ta yi waina a idonsa, sa'an nan ta toya.9Ta ɗauki kaskon kuma ta ba shi wainar, amma ya ƙi ci. Sa'an nan Amnon ya cewa waɗanda ke wurinsa, '"Kowa ya fita waje, ku ba ni wuri." Sai kowanne ɗayan su ya fita daga gare shi.
10Sai Amnon ya cewa Tama, "Kawo abincin nan ɗakina domin in ci daga hannunki." Sai Tama ta ɗauki wainar da ta yi, ta kawo ta cikin ɗakin Amnon ɗan'uwanta.11Da ta kawo masa abincin, sai ya cafke hannunta ya ce mata, "Ki zo, ki kwana da ni, 'yar uwata."12Ta amsa masa, "A'a, ɗan'uwana, kada ka matsa mani, domin ba makamancin abu haka da ya kamata ya faru a Isra'ila. Kada ka yi wannan abin kunya!
13‌Ƙaƙa zan rabu da kunyata? Kai kuma fa? Za ka zama kamar ɗaya daga cikin sakarkaru na Isra'ila! Yanzu fa in ka yarda ka yiwa sarki magana, ba zai hana ka ni ba."14Duk da haka Amnon ya ƙi ya saurare ta. Tun da ya fi Tama ƙarfi, sai ya kama ta ya kwana da ita.
15Sa'an nan Amnon ya ƙi Tama da mummunar ƙiyayya. Ya ƙi ta fiye da yadda dã ya yi sha'awarta. Amnon ya ce mata,16"Tashi ki tafi." Amma ta amsa masa, "A, a! Wannan babbar muguntar sallamata in tafi ta fi muni da abin da ka yi mani!" Amma Amnon bai saurare ta ba.17Maimakon haka, sai ya kira baransa ya ce, "Ka fitar da wannan mata daga gabana, ka kulle ƙofar a bayanta."
18Sai baransa ya fitar da ita ya kulle ƙofar a bayanta. Tama ta na saye da wata taguwa mai ado sosai domin 'ya'yan sarki mata waɗanda budurwai ne suna yin shiga irin haka.19Tama ta baɗa toka a kanta ta keta taguwarta. Ta ɗibiya hannayenta a kanta ta tafi, tana rusa kuka sa'ad da take tafiya.
20Absalom ɗan'uwanta ya ce mata, "Ko ɗan'uwanki Amnon ya sadu da ke ne? Amma yanzu ki yi shuru, 'yar uwata. Shi ɗan'uwanki ne. Ka da ki riƙe wannan a zuciya." Haka Tama ta zauna ita kaɗai a gidan wanta Absalom.21Sa'ad da Sarki Dauda ya ji dukkan waɗannan abubuwa, sai ya husata ƙwarai.22Absalom bai cewa Amnon komai ba, gama Absalom ya ƙi shi sabili da abin da ya yi mata da yadda ya kunyatar da 'yar'uwarsa Tama.
23Ya zama fa bayan shekara biyu cur, Absalom na da masu sausayar tumaki da ke aiki a Bãl Hazor, wadda ke kusa da Ifraim, Absalom kuma ya gayyaci dukkan 'ya'yan sarki maza su ziyarci wurin.24Absalom ya tafi wurin sarki ya ce, "Duba yanzu, bawanka yana da masu sausayar tumaki. Idan ka yarda bari sarki da barorinsa su zo tare da ni, bawanka."
25Sarki ya amsa wa Absalom, "A'a, ɗana kada dukkanmu mu tafi domin za mu wahalshe ka." Absalom ya ƙarfafa sarki, amma bai yarda ya tafi ba, sai dai ya albarkaci Absalom.26Sai Absalom ya ce, "In ba haka ba, idan ka yarda bari ɗan'uwana Amnon ya je tare da mu." Sai sarki ya ce masa, "Donme Amnon zai je tare da ku?"
27Absalom ya matsa wa Dauda, sai ya bari Amnon da dukkan 'ya'yan sarki maza su tafi tare da shi.28Absalom ya dokaci barorinsa cewa, "Ku saurara sosai. Sa'ad da Amnon ya soma buguwa sosai da ruwan inabi, kuma sa'ad da zan ce maku, 'Ku hari Amnon,' sai ku kashe shi. Kada ku ji tsoro. Ba nine na dokace ku ba? Ku yi ƙarfin hali ku yi mazakutta."29Sai barorin Absalom suka yiwa Amnon yadda aka dokace su. Sai dukkan 'ya'yan sarki maza suka tashi, kowanne mutum ya haye bisa alfadarinsa ya tsere.
30Ya zamana fa, lokacin da suke kan hanya, sai labari ya kai wurin Dauda cewa, "Absalom ya kashe dukkan 'ya'yan sarki maza kuma babu ko ɗaya da ya rage a cikinsu."31Sai sarki ya miƙe ya kekketa tufafinsa, ya kwanta a ƙasa; dukkan barorinsa suka tsaya nan da tufafinsu a yayyage.
32Yehonadab ɗan Shimeya, ɗan'uwan Dauda, ya amsa ya ce, "Kada ubangidana ya gaskata cewa sun kashe dukkan samari waɗanda 'ya'yan sarki maza ne, gama Amnon ka ɗai ya mutu. Absalom ya ƙudura wanna abu tun daga randa Amnon ya ɓata 'yar'uwarsa Tama.33Saboda haka fa, kada maigidana sarki ya riƙe wannan rahoto a zuciyarsa har da zai gaskata cewa dukkan 'ya'yan sarki maza suka mutu, gama Amnon ne kaɗai ya mutu."
34Absalom ya gudu. Wani bawa da ke tsaro ya tada idanunsa ya ga mutane da yawa suna zuwa a kan hanya a gefen dutse yamma da shi.35Sai Yonadab ya cewa sarki, "Duba, 'ya'yan sarki maza suna zuwa. Ya yi dai-dai da yadda bawanka ya faɗa."36Ya zama fa sa'ad da ya gama magana sai 'ya'yan sarki maza suka iso suka tada muryoyinsu suka yi kuka. Sarki da dukkan barorinsa ma suka yi kuka mai zafi.
37Amma Absalom ya gudu ya tafi gunTalmai ɗan Ammihud, sarkin Geshu. Dauda ya yi ta makokin ɗansa da daɗewa.38Sai Absalom ya gudu ya tafi Geshu, inda ya kasance har shekara uku.39Ran Sarki Dauda ya yi marmarin ya tafi ya ga Absalom, gama ya ta'azantu game da Amnon da mutuwarsa.

14

1Yanzu fa Yowab ɗan Zeruya ya fahimci cewar ran sarki na marmarin ganin Absalom.2Yowab ya aika da kalmar saƙo a Tekowa yasa a kawo masa mace mai hikima. Ya ce mata, "Ina roƙonki kiyi kamar kina makoki kisa tufafin makoki. Ina roƙon ki kada ki shafa mai a jikinki, amma kiyi kamar mace wadda ta daɗe tana makoki domin matacce.3Daga nan sai ki je wurin sarki kiyi magana da shi game da abin da zan kwatanta." Sai Yowab ya faɗa mata maganganun da za ta faɗi a wurin sarki.

4Sa'ad da matar nan daga Tekowa ta yi magana da sarki, sai ta kwanta da fuskarta a ƙasa ta ce, "Ka taimake ni, ya sarki."5Sarki ya ce mata, "Me ya faru?" Sai ta amsa, "Gaskiyar ita ce ni gwauruwa ce, maigidana kuma ya mutu.6Ni baiwarka, ina da 'ya'ya biyu, sun yi faɗa tare a cikin saura, ba kuwa wani wanda zai raba su. ‌Ɗ‌aya ya bugi ‌ɗ‌ayan har ya kashe shi.
7Yanzu duk zuriyar sun tashi gãba da baiwarka, su ka ce, 'Ki ba mu mutumin da ya kashe ɗan'uwansa cikin hannunmu, domin mu kashe shi, domin biyan ran ɗan'uwansa wanda ya kashe.' Da haka kuma za su hallaka magajin. Ta yin haka za su ɓice wutata da ta rage, kuma ba za su bar wa maigidana suna ko zuriya a doron ƙasa ba."
8Sai sarki ya cewa matar, "Ki tafi gidanki, kuma zan umarta ayi wani abu domin ki."9Sai matar nan ta Tekowa ta amsa wa sarki, "Ya shugabana, sarki, bari alhakin laifin ya komo kaina da gidan iyalin mahaifina. Sarki da kursiyinsa basu da laifi."
10Sai sarki ya amsa, duk wanda ya ce maki wani abu, ki kawo shi wurina, ba zai ƙara taɓa ki ba."11Daga nan sai ta ce, "Ina roƙon ka, bari sarki ya tuna da Yahweh Allahnka, domin kada mai ɗaukar fansar jini ya ƙara hallakar da wani, domin kada su hallaka ɗana." Sai sarki ya amsa, "Bisa ran Yahweh, babu gashin ɗanki ko ɗaya da zai faɗi ƙasa."
12Daganan sai matar ta ce, "In ka yarda bari baiwarka ta sake yin magana ga shugabana sarki." Ya ce, "Ci gaba da magana"13Sai matar ta ce, "Donme ka kutta wannan maƙida gãba da mutanen Allah? Gama ta wurin faɗin wannan, sarki ya zama kamar wani mai laifi, saboda sarki bai sake dawo da korarren ɗansa gida ba.14Gama dukkan mu dole mu mutu, kuma muna kama da ruwan da aka zubar a ƙasa, wanda ba za a sake tattara shi ba. Amma Allah ba zai ɗauki rai ba; maimakon haka, ya kan nemi hanya domin waɗanda aka kora su dawo.
15Yanzu fa, ganin yadda na zo in faɗi wannan abu ga shugabana sarki, saboda mutane sun sa na ji tsoro. Sai baiwarka ta ce a ranta, 'yanzu zan yi magana da sarki. Maiyiwuwa ne sarki ya aikata bisa ga roƙon baiwarsa.16Watakila sarki zai saurare ni kuma ya ceci baiwarsa daga hannun mutumin da zai hallaka ni da ɗana tare, daga cikin gãdon da Allah ya ba mu.'17Daga nan baiwarka ta yi addua, ta ce, Yahweh, in ka yarda bari maganar shugabana sarki ta ba ni sauƙi, gama kamar yadda mala'ikan Allah ya ke, haka shugabana sarki ya ke wajen faɗin abu mai kyau daga mugunta.' Bari Yahweh Allahnka ya kasance tare da kai."
18Daga nan sarki ya amsa wa matar ya ce, 'Ina roƙon ki kada ki ɓoye mani komai da zan tambaye ki." Sai matar ta amsa ta ce, 'Yanzu bari shugabana sarki ya yi magana."19Sai sarki ya ce "Ko hannun Yowab bai tare da ke cikin dukkan al'amarin nan?" Sai matar ta amsa ta ce, "Bisa ga ranka, ya shugaba sarki, ba wani ko ɗaya da zai kuɓuta daga hannun dama ko hagu daga duk wani abin da shugabana sarki ya faɗi. Gama bawanka Yowab ne ya umarce ni ya kuma gaya mani dukkan abubuwan da baiwarka ta faɗi.20Bawanka Yowab ya yi wannan domin ya canza yanayin abin da ya ke faruwa. Shugabana kuma yana da hikima, hikima irinta mala'ikan Allah, kuma ya san dukkan abin da ya ke faruwa a cikin ƙasa."
21Sai sarki ya cewa Yowab, Yanzu fa ka duba, zan yi wannan, jeka fa, ka komo da saurayin nan Absalom."22Sai Yowab ya kwanta da fuskarsa ƙasa cikin darajantawa da godiya ga sarki. Yowab ya ce, "Yau bawanka ya sani cewa Na sami tagomashi a idonka, ya shugabana, sarki, da shi ke sarki ya aikata bisa ga roƙon bawansa."
23Sai Yowab ya ta shi, ya tafi Geshu, kuma ya zo da AbsalomYerusalem.24Sarki ya ce, "Zai iya komawa gidansa, amma ba lallai ya ga fuskata ba." Absalom ya dawo gidansa, amma bai ga fuskar sarki ba.
25Yanzu kuwa a cikin dukkan Isra'ila babu wanda ake yabo domin kyansa fiye da Absalom. Daga tafin sawunsa zuwa bisa kansa babu wani aibi a cikinsa.26Sa'ad da ya aske gashin kansa a ƙarshen kowacce shekara, saboda ya kan yi masa nauyi, yakan auna gashin kansa, ya kan kai kimanin awo ɗari biyu, bisa ga mizanin ma'aunin sarki.27An haifa wa Absalom 'ya'ya uku maza da 'ya mace ɗaya, sunanta Tama. Ita kyakkyawar mace ce.
28Absalom ya zauna cikakkun shekaru biyu a Yerusalem, ba tare da ganin fuskar sarki ba.29Daga nan Absalom ya aika a kira Yowab domin ya aike shi wurin sarki, amma Yowab ya ƙi zuwa wurinsa. Har yanzu Absalom ya sake aikawa karo na biyu, duk da haka Yowab ya ƙi zuwa.
30Domin wannan Absalom ya ce da barorinsa, "Duba, gonar Yowab tana kusa da tawa, ga shi yana da bali a wurin. Ku je ku sa mata wuta."31Sai barorin Absalom suka sawa gonar wuta. Daga nan sai Yowab ya tashi ya zo wurin Absalom a gidansa, ya ce masa, "Donme barorinka suka sawa gonata wuta?"
32Absalom ya amsa wa Yowab, "Duba na aika maka cewa, ka zo nan domin in aike ka wurin sarki ka ce, "Donme na dawo daga Geshu? ya fi mani sauƙi a ce har yanzu ina can. Yanzu bari in ga fuskar sarki, idan bani da gaskiya, bari ya kashe ni.'"'33Sai Yowab ya je wurin sarki ya faɗa masa. Sa'ad da sarki ya kira Absalom, sai ya sunkuyar da fuskarsa har ƙasa a gaban sarki, sarki kuwa ya sumbaci Absalom.

15

1Ana nan bayan wannan kuma Absalom ya shirya karusa da dawakai domin kansa, tare da mutane hamsin masu gudu a gabansa.2Absalom zai tashi da wuri ya tsaya a bakin hanya mai zuwa ƙofar birni, sa'ad da kowanne mutum ya ke da matsalar da za a kawo wa sarki domin shari'a, daga nan sai Absalom ya kira shi ya ce, "Daga wanne birni ka zo?" sai mutumin ya amsa, "Bawanka daga ɗaya daga cikin kabilun Isra'ila ya ke."

3Sai Absalom ya ce masa, Duba, maganarka tana da kyau da kuma gaskiya, amma sarki bai sanya kowa da zai ji maganarka ba."4Absalom ya ƙara da cewa, "Ina ma da ni aka sanya in zama alƙali cikin ƙasar, domin kowanne mutum da ke da kowacce irin matsala ko dalili ya zo wurina, kuma zan yi masa adalci!"
5Ya zama kuwa idan kowanne mutum ya zo wurin Absalom domin ya girmama shi, Absalom ya kan miƙa hannunsa ya kama shi ya yi masa sumba.6Absalom ya aikata wannan ga dukkan Isra'ila musamman wanda ya zo wurin sarki domin shari'a. Da haka Absalom ya sace zukatan mutanen Isra'ila.
7Ana nan bayan shekaru huɗu sai Absalom ya cewa sarki, "Ina roƙonka ka yardar mani in tafi in cika wa'adin da na yiwa Yahweh cikin Hebron.8Gama bawanka ya yi wa'adi lokacin da nake zama a Geshu cikin Aram, cewa, 'Idan ya tabbata Yahweh ya sake dawo da ni Yerusalem, daga nan zan yi wa Yahweh sujada.'"
9Sai sarki ya ce masa, "Tafi lafiya" Sai Absalom ya tashi ya tafi Hebron.10Amma Absalom ya aika da masu leƙen asirin ƙasa cikin dukkan kabilun Isra'ila, ya na cewa, da zarar kun ji busar ƙaho, daga nan dole ku ce, 'Absalom ne sarki cikin Hebron.'"
11Mazaje ɗari biyu suka ta fi tare da Absalom daga Yerusalem, waɗanda aka gayyata. Sun tafi cikin rashin sanin su, ba su da masaniyar abin da Absalom ya rigaya ya shirya.12Lokacin da Absalom ke cikin miƙa hadayu, ya aika a kirawo Ahitofel daga garinsa a Gilo. Shi ne mai ba Dauda shawara. Makircin Absalom kuwa ya yi ƙarfi, gama mutanen da ke bin Absalom kullum sai ƙaruwa suke yi.
13Wani ɗan saƙo ya zo wurin Dauda ya ce, "Zukatan mutanen Isra'ila sun koma wajen Absalom."14Sai Dauda ya cewa dukkan bayinsa da e tare da shi a Yerusalem, "Tashi bari mu gudu, in ba haka ba a cikinmu babu wanda zai kuɓuta daga hannun Absalom. Mu hanzarta tashi, kada ya same mu da sauri, kuma ya kawo bala'i a kanmu ya bugi birnin da kaifin takobi.15Bayin sarki suka cewa sarki, "Duba, bayin sarki a shirye suke su yi duk iyakar abin da shugabanmu sarki ya ayyana."
16Sarki ya fita dukkan iyalinsa kuma suka bi shi, amma sarki ya bar mata goma, waɗanda ƙwaraƙwarai ne domin su kula da fãda.17Bayan da sarki ya fita tare da dukkan mutanen da ke bayansa, suka tsaya a gida na ƙarshe.18Dukkan rundunarsa suka tafi tare da shi, a gaban sa kuma dukkan Keretawa, da dukkan Feletawa, da dukkan Gittiyawa - mutum ɗari shida waɗanda suka bi shi tun daga Gat.
19Sa'an nan sarki ya cewa Ittai Bagitti, "Donme za ka zo, tare da mu? Ka koma ka zauna tare da sarki Absalom, gama kai baƙo ne ɗan bauta kuma, ka koma wurinka.20Da ya ke jiya kaɗai ka tafi, donme zan sa ka kai da komowa tare da mu? Gashi kuwa ban ma san inda zan tafi ba. Don haka sai ka juya ka koma ka ɗauki 'yan ƙasarka. Bari bangirmanka da aminci su tafi tare da kai."
21Amma Ittai ya amsa wa sarki ya ce, "Na rantse da ran Yahweh, da ran shugabana sarki kuma, hakika duk wurinda shugabana sarki ya tafi, can ne kuma bawanka za shi, ko ya kai ga rayuwa ko ga mutuwa."22Sai Dauda ya cewa Ittai, "Jeka ka ci gaba tare da mu" Sai Ittai Bagitti ya haye tare da sarki, da dukkan mutane da dukkan iyalin da ke tare da shi.23Dukkan ƙasar kuwa ta yi kuka da babbar murya yayin da dukkan mutane suka ratsa ta hayin kwarin Kidron, sarki ma da kansa ya haye. Dukkan mutane suka yi tafiya a ƙasa zuwa wajen hanyar jeji.
24Har su Zadok da dukkan Lebiyawa, masu ɗauke da akwatin alƙawarin Allah, suna wurin. Suka ajiye akwatin Allah a ƙasa, Abiyata ya bi su. Suka jira har saida dukkan mutane suka gama fitowa daga cikin birni.25Sai sarki ya cewa Zadok, "Ka ɗauki akwatin Allah ka mai da shi cikin birni. Idan na sami tagomashi a idon Yahweh, zai komo da ni nan, ya kuma sake nuna mani akwatin da wurin zamansa.26Amma idan ya ce, "Ba na jin daɗinka,' Duba Ina nan, bari ya yi mani abin da ya ga ya yi masa kyau."
27Sai sarki ya cewa Zadok firist, kai ba mai gani ba ne? Ka koma cikin birni lafiya, da 'ya'yanka biyu tare da kai, Ahimãz ɗanka, da Yonatan ɗan Abiyata.28Duba, a wurin mashigai na jeji zan jira har sai magana ta zo daga gare ku ka sanar da ni."29Sai Zadok da Abiyata suka ɗauki akwatin alƙawari na Allah suka mai da shi cikin Yerusalem, suka kuma zauna can.
30Amma Dauda ya haura ba takalmi yana kuka har zuwa Dutsen Zaituna, kuma ya rufe kansa. Kowanne mutum cikin mutanen da ke tare da shi ya rufe kansa, suka hau suna kuka yayin da suke tafiya.31Sai wani ya faɗawa Dauda ya ce, Ahitofel na cikin masu maƙida da Absalom." Dauda ya yi addu'a ya ce, "Ya Yahweh, ina roƙonka ka juyar da shawarar Ahitofel ta zama wawanci."
32Ana nan sa'ad da Dauda ya kai kan hanya, inda a ke yiwa Allah sujada, Hushai Ba'arkite ya zo ya sadu da shi da yagaggar tufa da ƙura a kansa.33Dauda ya ce masa, "I dan za ka yi tafiya tare da ni, za ka zama nawaya a gare ni.34Amma idan ka juya cikin birni ka ce da Absalom, 'Zan zama bawanka, ya sarki, kamar yadda na zama bawan mahaifinka a kwanakin baya, haka kuma yanzu zan zama bawanka,' ta haka za ka ruɗar da shawarar Ahitofel domina.
35Ba za ka tafi tare da Zadok da Abiyata firist tare da kai ba? Zai zama kuwa duk abin da ka ji a fadar sarki, dole ka faɗawa Zadok da Abiyata firist.36Duba can suna tare da 'yayansu biyu, Ahimãz ɗan Zadok da Yonatan ɗan Abiyata. Dole ta hannunsu za ku aiko mani da dukkan abin da kuka ji."37Sai Hushai, abokin Dauda, ya zo cikin birni yayin da Absalom ya kai kuma ya shiga cikin Yerusalem.

16

1Sa'ad da Dauda ya hau har ya wuce kan tudu kaɗan, Ziba bawan Mefiboshet ya gamu da shi da jãkai guda biyu labtattu; a kansu kuwa dunƙulen gurasa guda ɗari biyu na curin kauɗar inabi ɗari, da curin 'ya'yan itacen ɓaure ɗari, da salkar ruwan inabi.2Sarki ya cewa Ziba, "Donme ka kawo waɗannan abubuwa?" Ziba ya amsa ya ce, "Jakai domin iyalin sarki ne su hau, gurasa da wainar itacen ɓaure domin mutanenka su ci, ruwan inabi kuma domin duk wanda ya sũma a cikin jeji ya sha."

3Sarki ya ce, Ina jikan shugabanka?" Ziba ya amsa wa sarki ya ce, "Duba, ya tsaya baya cikin Yerusalem, gama ya ce, 'Yau gidan Isra'ila za su mayar mani da sarautar mahaifina.'"4Daga nan sai sarki ya cewa Ziba, "Duba, dukkan abin da ke mallakar Mefiboshet yanzu naka ne,'" Sai Ziba ya amsa, na sunkuya cikin bangirma gare ka, ya shugabana, sarki. Bari in sami tagomashi a idanunka."
5Sa'ad da sarki Dauda ya gabato Bahurim, wani mutum daga gidan iyalin Saul ya zo, sunansa Shimei ɗan Gera. Ya fito yana tafiya yana la'antarwa.6Ya jefi Dauda da duwatsu har da shugabannin sarki, duk da sojoji da masu tsaro da ke hannun damansa da hannun hagu.
7Shimei ya yi kira cikin la'antarwa, "Tafi daga nan, mutumin banza, mutumin jini!8Yahweh ya sãka wa dukkanku domin jinin iyalin gidan Saul, wanda kake mulki a matsayinsa. Yahweh ya bada mulkin a cikin hannun Absalom ɗanka. Gashi yanzu kuma ka hallaka saboda ka zama mutum mai zubda jini."
9Daga nan sai Abishai ɗan Zeruya ya cewa sarki, "Donme wannan mataccen karen zai la'anta shugabana sarki? Ina roƙonka ka yardar mani in haye in fille masa kai."10Amma sarki ya ce, "Ina ruwana da ku, ku 'ya'yan Zeruya? Mai yiwuwa yana la'antani saboda Yahweh ne ya ce masa, "La'anta Dauda.' Wane ne zai ce masa, 'Donme kake la'antar sarki?'"
11Sai Dauda ya cewa Abishai da dukkan bayinsa, "Duba, ɗana, wanda aka haifa daga cikin jikina, yana so ya ɗauki raina. Balle wannan mutumin Benyamin da ke marmarin ganin hallaka ta, Ku ƙyale shi kawai ku bar shi ya yi ta la'antarwa, gama Yahweh ne ya umarce shi.12Maiyiwuwa Yahweh ya duba irin gagarumin baƙincikin da ke kaina, ya sãka mani da alheri saboda la'antarwar da ya yi mani yau."
13Hakanan Dauda da mazajensa suka yi tafiya kan hanya, Shimei kuma ya zaga gefen gangaren tudu, yana tafiya yana la'antarwa yana jifansa da duwatsu yana zuba masa turɓaya yayin da ya ke tafiya,14Daga nan sarki da dukkan mutanen da ke tare da shi suka zo da gajiya, can ya huta lokacin da suka tsaya da dare.
15Absalom kuwa da dukkan matanen Isra'ila waɗanda ke tare da shi, suka zo Yerusalem, Ahitofel kuma na tare da shi.16Ya zama kuwa sa'ad da Hushai - Ba'arkite, abokin Dauda, ya zo wurin Absalom Hushai ya cewa Absalom, "Ran sarki ya daɗe! Ran sarki ya daɗe!"
17Absalom ya cewa Hushai, "Wannan ita ce biyayyarka ga abokinka? Donme ba ka tafi tare da shi ba?"18Hushai ya cewa Absalom, "A'a! maimakon haka, shi wanda Yahweh da wannan jama'a da dukkan mutanen Isra'ila suka zaɓa, shi ne mutumin da ni zan zama nasa, kuma zan zauna tare da shi.
19Kuma, wanne mutum zan bautawa? Ba gaban ɗansa ya kamata in yi bautar ba? kamar yadda na yi bautar gaban mahaifinka, hakanan zan yi bautar a gabanka."
20Sa'an nan Absalom ya cewa Ahitofel sai ka ba mu shawara game da abin da za mu yi."21Ahitofel ya amsa wa Absalom, "Ka je ka kwana da bayin matan mahaifinka waɗanda ya bari domin su kula da fãda, daga nan dukkan Isra'ila za su ji ka zama abin ƙyama ga mahaifinka. Daga nan hannuwan dukkan waɗanda ke tare da kai za su yi ƙarfi."
22Sai suka baza wa Absalom rumfa a bisa fãda, Absalom kuwa ya kwana da mata bayin mahaifinsa a idanun dukkan Isra'ila.23Ya zama kuwa shawarar da Ahitofel ya bayar a waɗannan kwanaki ta zama kamar wadda mutum ya ji daga bakin Allah da kansa. Haka dukkan shawarar Ahitofel ta zama a wurin Dauda da Absalom.

17

1Daga nan sai Ahitofel ya cewa Absalom, "Yanzu bari in zaɓi maza dubu goma sha biyu, kuma zan tashi in fafari Dauda yau a daren nan.2Zan auka masa lokacin da ya yi raụni ya gaji in kuma ba shi mamaki da tsoro. Mutanen da ke tare da shi za su gudu, sarki kaɗai zan buge.3Zan dawo da dukkan mutane a gare ka. kamar amaryar da ke zuwa wurin mijinta, daga nan dukkan mutane za su zauna lafiya ƙarƙashinka."4Abin da Ahitofel ya faɗi ya faranta wa Absalom rai da dukkan dattawan Isra'ila.

5Daga nan sai Absalom ya ce, yanzu ku kira Hushai Ba'akite shima, bari mu ji abin da ya ce."6Sa'ad da Hushai ya zo wurin Absalom, Absalom ya bayyana masa abin da Ahitofel ya faɗi sai ya tambayi Hushai, "Ko za mu iya yin abin da Ahitofel ya ce? In ba haka ba sai ka faɗi shawararka."7Sai Hushai ya cewa Absalom, "Shawarar da Ahitofel ya bayar a wannan lokacin ba ta da kyau."
8Hushai ya ƙara da cewa, "Ka san mahaifinka da mazajensa jarumawa ne masu ƙarfi, kuma suna da zafin rai, kamar damisar da a ka ƙwace wa 'ya'yanta a cikin saura. Mahaifinka mayaƙine, ba zai kwana tare da mutane a daren nan ba.9Duba, yanzu haka mai yiwuwa yana wurin ɓuya cikin wasu ramummuka ko a wani wuri. Za ya zama kuwa idan aka kashe waɗansu mutanenka a farkon harin, iyakar wanda yaji zai ce, 'An yi yanka tsakanin sojojin da ke bin Absalom.'10Daga nan har su sojoji masu ƙarfin zuciya, waɗanda zukatansu suna kama da zuciyar zaki, za su ji tsoro domin dukkan Isra'ila sun sani cewa mahaifinka jarumi ne, kuma mutanen da ke tare da shi suna da ƙarfi ƙwarai.
11Shawarata a gare ka ita ce a tattara dukkan Isra'ila a gare ka, daga Dan zuwa Biyasheba, kamar yashin da ke bakin teku yawa, kai kuwa da kanka ka tafi yaƙi.12Daga nan zamu abka masa a wurin da za a same shi, za mu rufe shi kamar yadda raɓa take faɗowa ƙasa. Ba za mu bar ko ɗaya daga cikin mazajensa, ko shi kansa, da rai ba.
13Idan ya toge cikin birni, daga nan dukkan Isra'ila za su kawo igiyoyi zuwa ga birnin nan kuma za mu jãshi zuwa cikin rafi, har da ba za a tarar da ko ƙanƙanen dutse ɗaya a wurin ba."14Daga nan sai Absalom da dukkan mazajen Isra'ila suka ce, shawarar Hushai Ba-arkite tafi shawarar Ahitofel." Yahweh ya wajabta ƙin amincewa da shawara mai kyau ta Ahitofel domin a kawo hallakarwa a kan Absalom.
15Daga nan sai Hushai ya cewa Zadok da Abiyata firistoci, "Ahitofel ya ba Absalom da dattawan Israi'ila irin wannan shawarar, amma ni na bada wata shawarar dabam.16Yanzu kuwa, sai ku tafi da sauri ku sanar da Dauda; ku ce masa, 'Kada ku yi sansani a daren yau a mashigan Araba, amma ta ko ƙaƙa ka haye, in ba haka ba za a haɗiye sarki da dukkan mutanen da ke tare da shi."
17Yanzu Yonatan da Ahimãz suna zama a maɓuɓɓugar En-Rogel. Wata mace baiwa takan je ta sanar da su abin da ya kamata su sani, domin bashi yiwuwa su ɗauki kasadar a yi ta ganinsu suna tafiya cikin birni. Idan saƙo ya zo sukan je su faɗa wa sarki Dauda.18Amma wani saurayi ya gan su a wannan lokacin sai ya faɗa wa Absalom. Sai Yonatan da Ahimãz suka fita a gaggauce suka zo gidan wani mutum a cikin Bahurim, wanda ya ke da rijiya a harabar gidansa, inda suka sauka ciki.
19Matar mutumin kuma ta ɗauki murfin rijiyar ta rufe bakin rijiyar da shi, ta zuba hatsi a kai, ba wanda ya san cewa Yonatan da Ahimãz suna cikin rijiyar.20Mutanen Absalom suka zo wurin matar gidan suka ce, "Ina Ahimãz da Yonatan?" Sai matar tace masu, "Sun haye rafi." Bayan da suka dudduba ko'ina ba su same su ba, sai suka koma Yerusalem.
21Ya zama kuwa bayan da suka tafi sai Yonatan da Ahimãz suka fito daga cikin rijiyar. Suka tafi su kai wa sarki Dauda rahoto; suka ce masa, "Ku tashi ku haye ruwa da sauri saboda Ahitofel ya bada irin wannan shawarar game da ku."22Daga nan sai Dauda ya tashi da dukkan mutanen da ke tare da shi, suka haye Yodan. Kafin wayewar hasken safiya babu ko ɗaya daga cikin su da ya kasa hayewa Yodan.
23Sa'ad da Ahitofel ya ga ba a bi shawararsa ba, sai ya yiwa jãkinsa sirdi ya tafi. Ya koma gida cikin nasa birni, ya kimtsa al'amuransa, kuma ya rataye kansa. Ta haka ya mutu aka kuma bizne shi cikin kabarin mahaifinsa.
24Daga nan sai Dauda ya zo Mahanayim. Absalom kuma, ya hayeYodan, shi da dukkan mazajen Isra'ila tare da shi.25Absalom kuma yasa Amasa shugaban rundunar yaƙi maimakon Yowab. Amasa ɗan Yeta Isma'ile, wanda ya kwana da Abigel wadda take ɗiyar Nahash 'yar'uwar Zeruya uwar Yowab.26Daga nan Isra'ila da Absalom suka kafa sansani cikin ƙasar Giliyad.
27Ya zama kuwa sa'ad da Dauda ya zo Mahanayim, sai Shobi ɗan Nahash daga Rabbah na Ammonawa, da Maki ɗan Amiyel daga Lo Deba, da Barzillai Bagiliye daga Rogelim,28suka kawo tabarmin kwanciya da barguna, da masakai da tukwane, da alkama, garin bali, gasasshen hatsi, wake, da ganye,29zuma, da mai, tumaki da manshanu, domin Dauda da mutanen da ke tare da shi su ci. Mutanen nan suka ce, "Mutanen nan suna jin yunwa, da gajiya, da ƙishi a cikin jeji."

18

1Dauda ya ƙidaya sojojin da ke tare da shi ya naɗa shugabanni na dubbai da na ɗarurruka a bisansu.2Daga nan Dauda ya aika da rundunar soja, ɗaya bisa uku ƙarƙashin, umarnin Yowab, waɗansu kashi uku kuma ƙarƙashin umarnin Abishai ɗan Zeruya, ɗan uwan Yowab, har yanzu wani kashi na uku kuma ƙarƙashin umarnin Ittai Ba-gitte. Sarki kuma ya cewa rundunar yaƙi, "Lallai zan fita tare daku da kaina, nima."

3Amma mazajen suka ce, "Ba dole sai ka je yaƙi ba, gama idan mun gudu ba za su kula da mu ba, ko idan rabin mu sun mutu ba za su kula ba. Amma darajarka a bakin zambar goma tamu ce! Domin wannan ya fi kyau kai ka kasance da shirin yi mana taimako daga cikin birni."4Sai sarki ya amsa masu, "Zan yi duk abin da ku ka ga yafi maku kyau." Sarki ya tsaya a bakin ƙofar birni yayin da dukkan rundunar yaƙi suka fita ɗari-ɗari da dubu-dubu.
5Sai sarki ya umarci Yowab, Abishai, da Ittai cewa, "kuyi a hankali da saurayin nan, da Absalom, sabili da ni." Dukkan mutane sun ji cewa sarki ya ba shugabanni wannan umarni game da Absalom.
6Rundunar yaƙi suka fita zuwa cikin filin karkara garin suyi yaƙi da Isra'ila; yaƙin ya bazu zuwa cikin kurmin Ifraim.7Rundunar yaƙin Isra'ila sun sha kãshi a wurin a hannun sojojin Dauda; a rannar kuwa aka yi kisa mai yawa a wurin an kashe mazaje dubu ashirin.8Faɗan ya bazu ko'ina cikin ɓangaren ƙasar, mazajen da kurmi ya cinye suka fi waɗanda suka mutu ta kaifin takobi.
9Ya kasance kuwa Absalom ya gamu da waɗansu sojojin Dauda. Absalom yana tafiya kan alfadarinsa, alfadarin kuwa ya shiga ƙarƙashin cikin rassa masu kauri na itacen rimi, itacen kuwa ya kama kansa cikin rassan. Yana reto tsakanin sama da ƙasa alfadarin da ya ke haye akai kuwa ya ci gaba da tafiya.10Wani mutum daya gani sai ya fada wa Yowab, "Duba, na ga Absalom rataye a itacen rimi!"11Yowab ya ce da mutumin daya faɗa masa game da Absalom, "Duba! ka ganshi! donme ba ka buge shi a ƙasa ba? Ai da na baka azurfa goma da ɗammara."
12Sai mutumin ya amsa wa Yowab, "Koda na karɓi shekel ɗin azurfa dubu, duk da haka bazan miƙa hannuna gãba da ɗan sarki ba, domin mun ji umarnin da sarki ya ba ku, Abishai da Ittai cewa, 'kada kowa ya taɓa saurayin nan Abasalom.'13Da na yi kasada da raina ta wurin ƙarya (kuma babu abin da ke ɓoye a wurin sarki), da ka yashe ni,"
14Daga nan sai Yowab ya ce, "Ba zan jira ka ba." Sai Yowab ya ɗauki mãshi uku cikin hannunsa ya caka su cikin zuciyar Absalom, yayin da ya ke da rai ya ke kuma rataye a itacen rimi.15Daga nan majiya ƙarfi guda goma masu ɗauke da sulken Yowab suka kewaye Absalom, suka buge shi, suka kashe shi.
16Yowab ya busa ƙaho, rundunar yaƙi suka dawo daga runtumar Isra'ilawa, gama Yowab ya rinjayi mutane.17Suka ɗauki Absalom suka jefa shi cikin babban rami a cikin kurmin; suka bizne jikinsa cikin ƙarƙashin babban tarin duwatsu, sa'an nan dukkan Isra'ila suka gudu, kowanne mutum zuwa nasa gida.
18Yanzu kuwa, lokacin da Absalom ya ke da rai, ya gina wa kansa babban ginshiƙin dutse cikin kwarin sarki, gama ya ce, "Bani da ɗan da zai ɗauki suna na wanda za a tuna da ni." Ya kira ginshiƙin da sunansa, ana kiran sunansa Surar Absalom har wa yau.
19Sa'an nan Ahimãz, ɗan Zadok ya ce, "Bari in gudu yanzu in kai wa sarki labari mai daɗi, yadda Yahweh ya kuɓutar da shi daga hannun abokan gabarsa."20Yowab ya amsa masa, "Ba kai ne za ka zama mai ɗaukar labari yau ba; amma wata rana za ka kai. Yau ba za ka kai kowanne labari ba gama ɗan sarki ya mutu."
21Sai Yowab ya cewa Ba-kushi, "Jeka ka faɗa wa sarki abin da ka gani. Sai Ba-kushi ya sunkuyar da kansa gaban Yowab, sai ya ruga.22Daga nan sai Ahimãz ɗan Zadok ya sake cewa Yowab, ba tare da la'akari da komai zai faru ba, ina roƙon ka ka bar ni in ruga in bi Ba-kushen."Yowab ya amsa, donme kake so ka ruga, ɗana? Ganin ba za ka sami wa ta ladar kai labarin ba?"23Kome ya faru, in ji Ahimãz, "Zan ruga" Yowab ya amsa ya ce masa, "Ruga." Sa'an nan Ahimãz ya ruga ta hanyar fili, ya tsere wa Ba-kushen.
24Dauda kuwa yana zaune tsakanin ƙofofi biyu na ciki da na waje. Mai tsaro kuma ya hau benen ƙofa har zuwa cikin rufin garu ya tãda idanunsa. Da ya duba, sai ga wani ya sheƙo a guje shi kaɗai.25Sai mai tsaron ya tada murya ya faɗa wa sarki. Sai sarki ya ce, "Idan shi kaɗai ne, akwai labari a bakinsa." Mai gudun ya zo kurkusa kuma dab da birnin.
26Sai mai tsaron ya lura da wani mutum kuma yana gudu, sai mai tsaron ya kira mai kula da ƙofa; ya ce, "Duba, ga wani mutum kuma yana gudu shi kaɗai," Sai sarki ya ce, "Shi ma yana kawo labari."27Sai mai tsaron ya ce, "A ganina irin gudun na gaban nan ya yi kama da gudun Ahimãz ɗan Zadok." Sarki ya ce, "Shi nagarin mutum ne, yana zuwa da labari mai daɗi."
28Daga nan sai Ahimãz ya yi kira ya cewa sarki, "Komai lafiya lau ne" kuma ya sunkuyar da kansa da fuskarsa gaban sarki har ƙasa ya ce, "Mai albarka ne Yahweh Allahnka! Ya ba da mutanen da su miƙar da hannayensu gãba da shugabana sarki."29Sai Sarki ya amsa, "Ko saurayin nan Absalom yana lafiya?" Ahimãz ya amsa ya ce, lokacin da Yowab ya aike ni, bawan sarki, wurinka, ya sarki, na ga babban hargitsi, amma ban san ko mene ne ba."30Sai sarki ya ce, "Juya gefe ka tsaya nan." Sai Ahimãz ya juya ya tsaya cik.
31Nan da nan Ba-kushen ya zo ya ce, "Akwai albishir mai daɗi domin shugabana sarki, gama Yahweh ya ɗaukar maka fansa yau daga dukkan waɗanda suka tayar maka."32Daga nan sai sarki ya cewa Ba-kushen, ko lafiya dai da saurayin nan Absalom?" Ba-kushen ya amsa, maƙiyan shugabana sarki, da dukkan waɗanda suka tayar maka domin su cutar da kai, "Su zama kamar yadda saurayin nan ya ke."33Daga nan sarki ya yi juyayi mai zurfi, ya tafi ya hau kan ƙofar bene ya yi kuka. Yayin da ya ke baƙinciki yana tafe yana cewa "ɗana Absalom, ya ɗana, Absalom! Da ma ni ne na mutu a madadinka, Absalom, ɗana, ɗana!"

19

1Aka faɗa wa Yowab cewa, "Duba, sarki yana kuka yana makoki domin Absalom."2Wato nasara ta ranar nan ta koma makoki ga dukkan jama'a, gama jama'a sun ji cewa a ran nan sarki yana makoki saboda ɗansa."

3Ya zama lallai ga sojoji su saɗaɗa shiru cikin birni a wannan ranar, kamar mutane masu jin kunya su kan sace jiki sa'ad da suka gudu daga yaƙi.4Sarki ya rufe fuskarsa ya yi kuka da babbar murya, "Ya ɗana Absalom, Absalom, ya ɗana, ya ɗana!"
5Yowab ya shigo cikin gida wurin sarki ya ce masa, "Yau ka kunyatar da fuskokin dukkan sojoji, waɗanda suka ceci ranka yau, da rayukan 'ya'yanka maza da mata, da rayukan matanka, da rayukan matanka bayi,6saboda kafi ƙaunar waɗanda suke ƙinka, kuma kana ƙin masoyanka. Gama yau ka nuna cewa Hafsoshi da sojoji ba komai bane a gare ka. Yau na gaskanta da Absalom ya rayu, dukkan mu kuma da mun mutu, wannan da ya faranta maka rai.
7Yanzu fa sai ka tashi ka fita kayi magana mai daɗi ga sojojinka, gama na rantse da Yahweh, idan baka tafi ba, babu wanda zai zauna tare da kai a daren nan. Wannan zai fi maka muni cikin dukkan bala'o'in da suka faru da kai daga ƙuruciyarka zuwa yau."8Sa'an nan sarki ya tashi ya zauna a ƙofar birni, aka faɗa wa dukkan jama'a, cewa, "Duba fa, ga sarki can yana zaune a cikin ƙofa." Daga nan sai dukkan mutane suka zo gaban sarki. Isra'ila kuma suka gudu, kowanne mutum ya tafi gidansa.
9Dukkan mutane kuma suna ta muhawara da juna cikin dukkan kabilun Isra'ila suna cewa, "Sarki ya cece mu daga hannun abokan gabanmu, ya kuma cece mu daga hannun Filistiyawa yanzu kuma ya gudu daga ƙasar saboda Absalom.10Absalom kuma wanda muka sarautar da shi bisa kanmu, ya mutu cikin yaƙi, Yanzu fa donme bama cewa komai game da dawo da sarki?"
11Sarki Dauda ya aika wurin Zadok da Abiyata firist cewa, 'Kuyi magana da dattawan Yahuda cewa, donme kune na ƙarshe wajen dawo da sarki fãdarsa, da shi ke sarki ya sami tagomashi daga dukkan Isra'ila, a dawo dashi fãdarsa?12Ku 'yan'uwana ne, ƙashina ne da namana. Donme ku ne na ƙarshen dawo da sarki?'
13Ku cewa Amasa, 'Kai ba ƙashina bane da kuma namana? Allah ya yi mani haka, ya kuma ƙara mani, idan ba ka zama shugaban runduna ta ba daga yanzu zuwa nan gaba a madadin Yowab.'"14Kuma ya rinjayo da zukatan dukkan mutanen Yahuda kamar zuciyar mutum guda, sai suka aika wa sarki cewa, "Ka dawo, kai da dukkan mutanenka."15Sai sarki ya dawo, ya zo Yodan. Mutanen Yahuda kuma suka zo Gilgal don su tarbi sarki, daga nan suka kawo sarki ƙetaren Yodan.
16Shimei ɗan Gera, Benyamine, wanda ya zo daga Bahurim, ya hanzarta ya sauko tare da mutanen Yahuda domin taryar sarki Dauda.17Akwai mutanen Benyamin dubu goma tare da shi, da Ziba bawan Saul, da kuma 'ya'yansa goma sha biyar da barorinsa ashirin tare da shi.18Suka haye taYodan a gaban sarki. Suka haye domin su kawo iyalin sarki domin ya yi abin da ya yi masa kyau. Shimei kuma ɗan Gera ya sunkuya a gaban sarki tun kafin ya fara haye Yodan.
19Sai Shimei ya cewa sarki, "Kada, shugabana, ya same ni da laifi ko ya tuna da taurin kan da bawanka ya yi a ranar da shugabana sarki ya bar Yerusalem. In ka yarda, kada sarki ya ajiye wannan a zuciyarsa.20Gama bawanka ya sani na yi zunubi. Duba, shi yasa na zo yau a matsayin na fari daga cikin dukkan iyalin Yosef na zo domin in taryi shugabana sarki."
21Amma Abishai ɗan Zeruya ya amsa ya ce, "Ba za a kashe Shimei ba saboda wannan, saboda ya la'anta shafaffe na Yahweh?"22Daga nan sai Dauda ya ce, "Me zanyi da ku, ku 'ya'yan Zeruya, da yau za ku zama maƙiyana? Za a kashe wani mutum yau a cikin Isra'ila? Gama bana sani cewa yau ni ne sarki bisa Isra'ila ba?"23Sarki kuwa ya cewa Shimei, "Ba za ka mutu ba" Sai sarki ya yi masa alƙawari tare da rantsuwa.
24Daga nan sai Mefiboshet ɗan Saul ya zo domin ya tarbi sarki. Bai kuwa gyara ƙafafunsa ba, ko ya aske gemunsa, ko ya wanke tufafinsa tun daga lokacin da sarki ya tashi har ranar daya dawo cikin salama.25Ya zama kuwa sa'ad da ya zoYerusalem domin ya tarbi sarki, sarki ya ce masa, "Donme ba ka tafi tare da ni ba, Mefiboshet?
26Sai ya amsa, "Ya shugabana sarki, bawana ya ruɗe ni, gama Na ce, bari in yi ma jakina sirdi, domin in hau in tafi tare da sarki, gama bawanka gurgu ne.'27Bawana Ziba yaci zarafina, bawanka, a wurin shugabana sarki. Amma shugabana sarki kamar mala'ikan Allah ya ke. Don haka, sai ka yi duk abin da kaga ya gamshe ka.28Gama duk iyalin gidan mahaifina sun zama matattun mutane gaban shugabana sarki, amma ka sanya bawanka a cikin masu ci a teburinka. Wanne 'yanci nake dashi kuma da zan ƙara yiwa sarki kuka?"
29Daga nan sarki ya ce masa, "Donme ka ƙara wani abu kuma? Na yanke shawarar cewa kai da Ziba za ku raba gonakin."30Sai Mefiboshet ya amsa wa sarki, "I, bari ya ɗauka duka, da shi ke shugabana sarki ya dawo gidansa lafiya."
31Daga nan sai Barzillai Bagiliye ya zo daga Rogelim ya haye Yodan tare da sarki, domin ya raka shi hayin Yodan.32Yanzu dai Barzillai ya tsufa ƙwarai, shekarunsa tamanin. Ya tanadarwa sarki abin zaman gari lokacin da ya ke zaune a Mahanayim, gama shi mai arzaki ne.33Sarki ya ce da Barzillai, "Sai ka haye tare da ni, ni kuwa zan tanada maka ka zauna tare da ni a Yerusalem."
34Barzillai ya amsa wa sarki, "Sauran kwanaki nawa suka rage cikin shekarun rayuwata, da zan haura tare da sarki zuwa Yerusalem?35Shekaruna tamanin. Zan iya banbance tsakanin abu mai kyau da mugu? Ko bawanka zai iya ɗanɗana abin da nake ci ko abin da nake sha? Yanzu zan iya jin kowacce muryar mawaƙa maza da waƙar mata? Donme bawanka za ya zama nawaya ga shugabana sarki?36Bawanka yana so ya haye Yodan kaɗai tare da sarki. Donme sarki zai saka mani da irin wannan ladar?
37Ina roƙonka ka bar bawanka ya koma gida, domin in mutu cikin birnina a kabarin mahaifina da mahaifiyata. Amma ka duba, ga bawanka Kimham. Bari ya haye tare da shugabana sarki, kayi masa abin da ya yi maka kyau."
38Sarki ya amsa ya ce, "Kimham zai haye tare da ni, kuma zan yi masa abin da kake so, iyakar abin da kake nema kuma a gare ni, zan yi maka."39Daga nan sai dukkan mutane suka haye Yodan, sarki ma ya haye, sai sarki ya sumbaci Barzillai ya kuma albarkace shi. Daga nan sai Barzillai ya koma gidansa.
40Sai sarki ya haye zuwa Gilgal, Kimham kuma ya haye tare da shi. Dukkan jama'ar Yahuda kuma suka ƙetarar da sarki, da rabin jama'ar Isra'ila kuma.41Nan da nan sai dukkan mutanen Isra'ila suka fara zuwa wurin sarki suka ce da sarki, "Donme 'yan'uwanmu, mutanen Yahuda, suka sace ka suka kawo sarki da iyalinsa hayin Yodan, da dukkan mazajen Dauda tare da shi?"
42Sai mutanen Yahuda suka amsa wa mutanen Isra'ila suka ce, domin sarki danginmu ne na kusa. donme kuke fushi game da wannan? Mun ci wani abin da ya zama lallai sarki dole ya biya? Ko ya ba mu wasu kyaututtuka?"43Sai mutanen Isra'ila suka amsa wa mutanen Yahuda, "Mu na da kabilai goma da suke dangantaka da sarki, 'yancin da muke dashi wurin Dauda yafi naku. Donme ku ka rena mu? Ba shawarar mu aka fara ji ba ta dawo da sarkinmu?" Amma kalmomin mutanen Yahuda sun fi kalmomin mutanen Isra'ila zafi.

20

1Ya kasance kuma a wannan wurin akwai wani mai tada hankali sunansa Sheba ɗan Bikri, Benyamine. Sai ya busa ƙaho ya ce, "Ba mu da rabo cikin Dauda ba mu kuwa da gãdo cikin ɗan Yesse, bari kowanne mutum ya koma gidansa, Isra'ila,"2Sai dukkan mutanen Isra'ila suka yashe da Dauda suka bi Sheba ɗan Bikri. Amma mutanen Yahuda suka bi sarkinsu kurkusa, daga Yodan har zuwa Yerusalem.

3Lokacin da Dauda yazo fãdarsa a Yerusalem, sai ya ɗauki matan nan goma bayi waɗanda ya bari su kula da fãda, ya sa su cikin gida yasa a kula da su, ya biya buƙatunsu, amma bai ƙara kwana da su ba. An kulle su har ranar mutuwarsu, suna zama kamar gwamraye.
4Daga nan sai sarki ya ce da Amasa, ka kira mazajen Yahuda tare cikin kwana uku; dole kai ma ka kasance, a nan,5Sai Amasa ya tafi ya kira mutanen Yahuda tare, amma ya jinkirta ya wuce lokacin da sarki ya sanya dominsa.
6Sai Dauda ya ce da Abishai, "Yanzu Sheba ɗan Bikri za ya yi mana ɓarnar da ta fi wadda Absalom ya yi. Ka ɗauki bayin shugabanka, sojojina, ka bi bayansu, in ba haka ba zai iya samun birane masu ganuwa ya ɓace mana da gani."7Sai mutanen Yowab suka bi bayansa, da su da Keretawa da su da Feletawa, da dukkan jarumawa. Suka fita Yerusalem suka bi Sheba ɗan Bikri.
8Yayin da suke a babban dutsen da ke a Gibeyon, Amasa ya zo ya tarbe su, Yowab kuwa yana saye da tufafinsa na yaƙi, wanda ya haɗa da ɗammara kewaye da ƙugunsa da takobin yaƙi ɗaure da shi. Ya yin da ya ci gaba da tafiya sai takobin ya faɗi.
9Sai Yowab ya ce da Amasa, "Lafiya kake, ɗan'uwana?" Yowab ya kama Amasa wajen gemunsa da hannunsa na dama don ya yi masa sumba.10Amasa bai kula da takobin da ke cikin hannun Yowab na hagu ba. Yowab ya daɓa wa Amasa a ciki 'yan hanjinsa suka faɗi a ƙasa. Yowab bai sake bugunsa ba, Amasa kuwa ya mutu. Yowab da Abishai ɗan'uwansa suka bi Sheba ɗan Bikri.
11Sai ɗaya daga cikin mutanen Yowab ya tsaya wajen Amasa, mutumin ya ce, "Wanda ya ke wajen Yowab da wanda ke wajen Dauda, bari ya bi Yowab."12Amasa ya kwanta yana ta birgima cikin jini a cikin tsakiyar hanya. Yayin da mutumin yaga dukkan jama'a sun tsaya cik, sai ya ɗauki Amasa ya kawar dashi daga kan hanya zuwa cikin saura. Ya jefa mayafi a kansa saboda ya ga duk wanda ya zo sai ya tsaya a kansa.13Bayan da aka kawar da Amasa a kan hanya, dukkan mutane suka bi bayan Yowab, wajen bin Sheba ɗan Bikri.
14Sheba ya ratsa dukkan kabilun Isra'ila zuwa Abel ta Bet Maka, da zuwa dukkan kasar Beriyawa, waɗanda suka tattaru domin bin Sheba.15Suka kama shi suka kafa masa sansani cikin Abel ta Bet Maka. Suka tãra tulin tudun ƙasa gãba da birnin da ganuwar. Dukkan jama'ar da ke tare da Yowab suka bubbuge ganuwar suka rushe ta.16Sa'an nan wata mace mai hikima tayi kuka daga cikin birni ta ce, "Ku ji, ina roƙon ku kuji, Yowab, ka matso kusa da ni domin in yi magana da kai."
17Sai Yowab ya je kusa da ita, sai matar ta ce, kai ne Yowab?" Sai ya amsa ya ce, "Ni ne," Sa'an nan ta ce masa, ka saurari kalmomin baiwarka," Ya amsa ya ce, Ina ji."18Sai ta ce, kwanakin dã an saba cewa, 'Lallai sai ka nemi shawara a Abel.' Wannan shawarar kuwa takan kawo ƙarshen al'amarin.19Mu ne ɗaya daga cikin birni da ke da salama da aminci a cikin Isra'ila. Ka na ƙoƙarin ka hallaka birni wanda ya ke uwa a cikin Isra'ila. Donme za ka haɗiye gãdon Yahweh?"
20Sai Yowab ya amsa ya ce, "Hakika ba zai faru ba, bari ya zama nesa daga gare ni, da zan haɗiye ko in hallakar.21Wannan ba gaskiya ba ne. Amma wani mutum daga duwatsun ƙasar Ifraim sunan sa Sheba ɗan Bikri, ya ɗaga hannunsa sama gãba da sarki, gãba da Dauda. Shi kaɗai za a bayar ni kuwa zan janye daga birnin." Sai matar ta cewa Yowab, "Za a jefa maka kansa ta bisa ganuwa."22Daga nan sai matar taje wurin dukkan jama'a cikin hikimarta. Suka yanke kan Sheba ɗan Bikri, suka jefa shi waje wurin Yowab. Daga nan sai ya busa ƙaho mutanen Yowab suka bar birnin, kowa ya koma gidansa. Sai Yowab ya komaYerusalem wurin sarki.
23Yanzu fa Yowab yana kan rundunar yaƙi ta Isra'ila, Benaiya kuma ɗan Yehoyida yana bisa kan Keretawa da Feletawa.24Adoram yana bisa mutane masu yin aikin dole, Yehoshafat kuma ɗan Ahilud shi ne magatakarda.25Sheba kuma marubuci da Zadok da Abiyata su ne Firistoci.26Ira Bajairi kuma babban mai yin hidima ga Dauda

21

1A cikin zamanin Dauda aka yi yunwa shekara uku akai akai, Dauda kuwa ya nemi fuskar Yahweh. Sai Yahweh ya ce, "Wannan yunwar tana kan ka ne saboda Saul da iyalinsa masu kisa, saboda ya kashe Gibiyonawa."

2Yanzu fa Gibiyonawa ba daga jama'ar Isra'ila bane, amma daga wajen sauran Amoriyawa ne. Mutanen Isra'ila sun rantse masu ba za su kashe su ba, amma saul ya yi ƙoƙari ya kashe su dukka a cikin himmarsa domin mutanen Isra'ila da Yahuda.3Sai Dauda ya kira mutanen Gibiyonawa ya ce masu, "Me zan yi domin ku? Ta yaya zan yi kaffara, domin ku albarkaci mutanen Yahweh, waɗanda suka gãji alherinsa da alƙawarai?"
4Gibiyonawa suka ce masa, ba zancen azurfa ko zinariya tsakanin mu da Saul ko iyalinsa. Kuma ba domin mu za a kashe kowanne mutum a cikin Isra'ila ba." Dauda ya amsa, "Duk abin da za ku roƙa, shi ne abin da zan yi maku."
5Sai suka amsa wa sarki suka ce, mutumin da ya yi ƙoƙarin ya kashe mu dukka, wanda ya ƙulla mana makirci, wanda da yanzu an hallaka mu, mu rasa wuri a tsakanin iyakar Isra'ila.6Bari a bamu mutum bakwai daga cikin zuriyarsa, mu kuwa za mu rataye su ga Yahweh cikin Gibiya ta Saul, zaɓaɓɓe na Yahweh." Sai sarki ya ce, "Zan ba ku su."
7Amma sarki ya keɓe Mefiboshet ɗan Yonatan ɗan Saul, saboda rantsuwar Yahweh da ke tsakanin su, tsakanin Dauda da Yonatan ɗan Saul.8Amma sarki ya ɗauki 'ya'ya biyu na Rizfa ɗiyar Ayiya, 'ya'yan da ta haifawa Saul, sunayen 'ya'ya biyun data haifa su ne, Armoni da Mefiboshet; Dauda kuma ya ɗauki 'ya'ya biyar na Mirab ɗiyar Saul, waɗanda ta haifawa Adriyel ɗan Barzillai Meholatiye.9Ya miƙa su cikin hannun Gibiyonawa. Suka rataye su a kan dutse, gaban Yahweh. Dukkan su bakwai ɗin suka mutu tare. Sun mutu a lokacin girbi, kwanakin farko ne a farkon kakar bali.
10Daga nan sai Rizfa ɗiyar Ayiya ta ɗauki tsummoki ta shimfiɗa wa kanta su a bisa dutsen, gefen gawarwakin, daga farkon kãka har lokacin da ruwan sama ya sauko a kansu. Bata bari tsuntsayen sararin sama su dame su da rana ba, ko namomin jeji da dare.11Aka faɗa wa Dauda abin da Rizfa ɗiyar Ayiya, baiwar matar Saul, ta yi.
12Sai Dauda ya tafi ya ɗauki ƙasusuwan Saul da ƙasusuwan Yonatan ɗansa daga hannun mutanen Yabesh Giliyad, waɗanda suka sace a wurin filin Bet - Shan, inda Filistiyawa suka rataye su, bayan da Filistiyawa suka kashe Saul a Gilbowa.13Dauda ya kawar da ƙasusuwan Saul da ƙasusuwan Yonatan ɗansa, suka kuma tattara ƙasusuwan mutane bakwai waɗanda aka rataye su kuma.
14Suka bizne ƙasusuwan Saul da Yonatan ɗansa cikin ƙasar Benyamin cikin Zela cikin kabarin Kish mahaifinsa. Suka aikata dukkan abin da sarki ya umarta. Bayan wannan Allah ya amsa addu'o'insu domin ƙasar.
15Daga nan sai Filistiyawa suka je su sake yin yaƙi da Isra'ilawa. Sai Dauda ya sauka da shi da mutanensa su yi yaƙi da Filistiyawa. Amma gajiyar yaƙi ta sa Dauda ya yi suwu.16Ishbi-Benob na zuriyar ƙattin nan wanda nauyin mashinsa ya yi nauyin shekel ɗari uku na tagulla, yana kuma ɗauke da sabuwar takobi, ya yi nufin ya kashe Dauda.17Amma Abishai ɗan Zeruya ya ceci Dauda, ya bugi Bafilisten nan, ya kashe shi. Daga nan mazajen Dauda suka rantse masa, cewa, "Ba zaka ƙara tafiya yaƙi tare da mu ba, domin kada ka ɓice fitilar Isra'ila."
18Bayan wannan kuwa aka sake yin yaƙi da Filistiyawa a Gob, lokacin da Sibbekai Bahushati ya kashe Saf, wanda ke ɗaya daga cikin zuriyar Refayim.19Ya zama kuma aka sake yin yaƙi da Filistiyawa a Gob, Elhanan ɗan Yayir mutumin Betlehem ya kashe Goliyat Bagittiye, wanda mãshin sa yana kama da dirkar masaƙa.
20Ya zama kuma aka sake yin yaƙi a Gat inda akwai wani mutum mai tsayin gaske a kowanne hannunsa yana da yatsu shida a kowacce ƙafa kuma yana da yatsu shida, dukka ashirin da huɗu kenan. Shi ma har yanzu daga zuriyar Refayim ne.21Sa'ad da ya zazzagi Isra'ila, Yonatan ɗan Shimeya, ɗan'uwan Dauda, ya kashe shi.22Waɗannan su ne zuriyar Refahayim na Gat an kashe su ta hannun Dauda da kuma ta hannun sojojinsa.

22

1Dauda ya yi amfani da waɗannan kalmomi ya raira waƙa ga Yahweh a ranar da ya cece shi daga hannun dukkan abokan gabarsa, da kuma hannun Saul.2"Ya yi addu'a ya ce, Yahweh shi ne dutsena, da kagarata, shi wanda ya cece ni.

3Allah shi ne dutse na. A cikinsa na sami mafaka, garkuwata da ƙahon cetona, hasumiyata mai tsawo, mafakata kuma, shi ne wanda ya cece ni daga tashin hankali.4Zan kira bisa Yahweh, wanda ya isa a yabe shi, kuma zan tsira daga hannun maƙiyana.
5Gama ambaliyun mutuwa sun kewaye ni, haukan ruwayen hallakarwa sun tsoratadda ni.6Igiyoyin lahira sun kewaye ni; tarkunan mutuwa sun kama ni.
7A cikin ƙuncina na kira Yahweh; Na kira Allahna; daga cikin haikalinsa ya ji muryata, kira na na neman taimako ya kai cikin kunnuwansa.
8Sa'an nan ƙasa ta girgiza ta yi makyarkyata. Tussan sammai suka girgiza aka motsa su, saboda Allah ya yi fushi.9Hayaƙi ya fito daga hancinsa, wuta mai cinyewa ta fito daga bakinsa. Ta kunna gawayi ta wurinsa.
10Ya buɗe sammai ya sauko ƙasa, duhu baƙiƙƙirin yana ƙarƙashin sawayensa.11Ya hau bisa Kerub, ya tashi. A bisa fukafukan iska aka ganshi.12Ya kuma maida duhu rumfa kewaye da shi, manyan hadura na tattaruwa cikin sararin sammai.
13Daga sheƙin hasken gabansa gawayin wuta suka faɗo.14Yahweh ya yi tsawa daga sammai. Maɗaukaki ya tada muryarsa.15Ya harba kibawunsa, ya tarwatsa maƙiyansa - curirrikan walƙiya kuma sun tarwatsa su.
16Sa'an nan hanyoyin ruwa suka bayyana; harsasun duniya suka tonu a kukan tsautawar Yahweh, da jin hucin numfashi daga hancinsa.
17Daga bisa ya kai ƙasa; Ya riƙe ni! Daga cikin ruwaye masu yawa ya jawo ni.18Ya cece ni daga wurin maƙiyina mai ƙarfi, daga hannun waɗanda suka ƙi ni, gama sun fi karfina.
19Suka afko mani a ranar masifata, amma Yahweh shi ne abin dogarata.20Ya kuma kawo ni waje a buɗaɗɗen wuri. Ya cece ni saboda yana murna da ni.21Yahweh ya sãka mani bisa ga ma'aunin adalcina; ya sãke gyara ni bisa ga tsabtar hannuwana.
22Gama na kiyaye hanyoyin Yahweh ban kuma juya wa Allah baya ba ta wurin aikata mugunta.23Gama dukkan shari'unsa na adalci suna gabana; game da zancen farillansa kuma, ban rabu da su ba.
24Marar laifi nake a gabansa, na kuma kiyaye kaina daga zunubi.25Domin wannan Yahweh ya sabunta ni ya sãka mani bisa ga adalcina, bisa ga matsayin tsabtata a idonsa.
26Ga mai aminci, ka nuna kanka mai aminci ne; ga mutumin da ya ke marar laifi, zaka nuna kanka marar laifi.27Ga mai tsabta, ka zama da tsabta, amma ga fãsiki ka zama a murɗe.
28Ka ceci rauna nan mutane, amma idanun ka na gãba da masu girmankai, kuma ka kawo su ƙasa.29Gama kai ne fitilata, Yahweh. Yahweh ya haskaka duhuna.
30Gama ta wurinka zan iya zarce taron yaƙi; ta wurin Allahna nake tsallake ganuwa.31Domin Allah, hanyarsa cikakkiya ce. Shi garkuwa ne ga dukkan waɗanda suka nemi mafaka a cikin sa.
32Gama wane ne Allah sai Yahweh? Wane ne dutse kuma sai Allahnmu?33Allah shi ne mafakata, yana kuma bida mutum marar laifi cikin hanyarsa.
34Yana maida ƙafafuna suyi sauri kamar na naman jeji, ya kuma sanya ni a bisa dogayen tuddai.35Yana koyar da hannuwana domin yaƙi, damtsuna kuma su tausa baka na jan ƙarfe.
36Ka kuma bani garkuwar cetonka, tagomashinka ya maishe ni mai girma.37Ka sanya wuri mai faɗi ƙarƙashin sawayena, santsi bai kwashe ƙafafuna ba.
38Na fafari maƙiyana na kuma hallaka su. Ban juya ba har sai da suka hallaka.39Na cinye su na ragargaza su; ba za su tashi ba. Sun fãɗi ƙarƙashin sawayena.
40Ka sanya ƙarfi a jikina kamar ɗammara domin yaƙi; waɗanda suka tayar mani ka sanya su ƙarƙashina.41Ka bani bayan maƙiyana' da wuyansu; Na datse wuyan waɗanda suka ƙi ni.
42Sun yi kuka domin neman taimako, amma ba wanda ya cece su; sun yi kuka ga Yahweh, amma bai amsa masu ba.43Na buge su da kyau na niƙesu kamar turɓaya a ƙasa, na tattake su kamar laka na watsar da su cikin tituna.
44Ka kuma ƙwatoni daga husumar mutanena. Ka kiyayeni a matsayin shugaban al'ummai. Mutanen da ban sani ba sun yi mani hidima.45Baƙi sun russuna mani dole. Da jin labarina, sun yi mani biyayya.46Baƙi sun fito daga wurin ɓuyarsu suna rawar jiki.
47Yahweh mai rai ne! Bari a yabi dutsena. Bari Allah ya ɗaukaka, dutsen cetona.48Wannan shi ne Allah wanda ke tabbatar da sakayya domina, shi wanda ke ƙasƙantar da al'ummai ƙarƙashina.49Ya kuɓutar da ni daga hannun maƙiyana. Tabbas, ka ɗaukaka ni bisa kan waɗanda suka tayar mani. Ka kuɓutar da ni daga masu son cutar da ni.
50Domin wannan Zan yi godiya gare ka, Yahweh, a tsakanin al'ummai; Zan raira waƙoƙin yabbai ga sunanka.51Allah ya bayar da babban ceto ga sarkinsa, yana nuna alƙawarin biyayya ga shafaffe na sa, ga Dauda da zuriyarsa har abada."

23

1Yanzu fa waɗannan su ne ƙarshen zantattukan Dauda - Dauda ɗan Yesse, mutumin da aka girmama ƙwarai, shi wanda ya ke shafaffe daga Allahn Yakubu, mawaƙi mai daɗi na Isra'ila.2"Ruhun Yahweh ya yi magana da ni, maganarsa kuma tana kan harshena.

3Allah na Isra'ila ya faɗi, Dutsen Isra'ila ya ce mani, 'Shi wanda ya ke mulkin mutane cikin adalci, mai yin mulki cikin tsoron Allah.4Zai zama kamar hasken safiya sa'ad da rana take fitowa, safiyar da babu giza-gizai, sa'ad da ɗanyar ciyawa take tsirowa daga ƙasa ta wurin hasken rana bayan saukowar ruwan sama.
5Hakika ba haka iyalina suke a gaban Allah ba? Ko bai yi madawwamin alƙawari da ni, shimfiɗaɗɗe bisa ga ƙa'ida ya tabbatar ta kowacce hanya ba? Ko bai ƙara cetona ba kuma ya biya kowanne muradina ba?
6Amma marasa amfani za su zama kamar ƙayayuwa da za a zubar, gama ba za su tattaru da hannu ɗaya ba.7Mutumin daya taɓa su dole ya yi amfani da makamin ƙarfe ko mashi mai tsini. Dole a ƙone su sarai a wurin da suka kwanta."
8Waɗannan su ne sunayen shahararrun sojojin Dauda: Yeshbal mutumin Hakmoniya shugabane na sojoji masu ƙarfi. Ya kashe mutum ɗari takwas a lokaci ɗaya.
9Bayansa kuma sai Eliyazar ɗan Dodai Ba'ahotiye, ɗaya daga cikin jarumawa uku na Dauda. Yana nan lokacin da suka rena Filistiyawa da suka tattaru tare don suyi yaƙi, lokacin da mutanen Isra'ila sun rigaya sun bar wurin.10Eliyaza ya tashi tsaye ya bugi Filistiyawa har hannunsa ya gaji hannunsa kuma ya liƙe wa takobinsa. Yahweh ya kawo babbar nasara a wannan ranar. Jama'a suka koma bayan Eliyaza, domin kawai su tuɓe jikuna.
11Bayansa kuma sai Shamma ɗan Agee, Harariye. Filistiyawa suka taru a filin dagar yaƙi, mutane kuwa suka gudu daga gabansu.12Amma Shamma ya tsaya a tsakiyar yankin ƙasar ya kuma kareta. Ya kashe Filistiyawa, Yahweh ya kawo babbar nasara.
13Uku daga cikin su talatin sojojin suka gangaro zuwa wurin Dauda a lokacin girbi, zuwa kogon Adullam. Rundunar Filistiyawa sunyi sansani cikin kwarin Refim.14A lokacin nan Dauda yana cikin kagararsa, a kogo, yayin da Filistiyawa kuma suka kafu a Betlehem.
15Dauda ya ji ƙịṣḥi ya ce, "Ina ma wani zai bani ruwa daga rijiyar da ke a Betlehem, rijiyar da ke kusa da ƙofa!"16Sai jarumawannan uku suka fasa rundunar Filistiyawa suka ɗebo ruwa daga rijiyar da ke Betlehem, wadda ke kusa da ƙofa. Suka ɗauki ruwan suka kawowa Dauda, amma yaƙi sha, Maimakon haka sai ya zuba wa Yahweh.17Daga nan sai ya ce, "Bari wannan ya yi nesa da ni, Yahweh, har da zan sha wannan. Zan sha jinin mutanen da suka sadaukar da rayukansu?" Domin wannan bai yarda ya sha ba, Waɗannan su ne al'amuran da jarumawan nan uku suka yi.
18Abishai ɗan'uwan Yowab, ɗan Zeruya, shi ne babba cikin su uku. Ya taɓa yin yaƙi da mashinsa ya kuwa kashe mutum ɗari uku. An sha ambatonsa tare da sojojin nan guda uku.19Ba shi ya fi ukun suna ba? An sanya shi shugabansu. Duk da haka, sunansa ba a kwatanta shi da darajar sauran sojoji ukun.
20Benaiya daga Kabzeyel shi ɗa ne wurin Yahoiyada; shi mutum ne mai ƙarfi wanda ya yi manyan abubuwa na kasada. Ya kashe 'ya'ya biyu na Ariyel na Mowab. Ya kuma shiga cikin rami ya kashe zaki a lokacin dusar ƙanƙara.21Kuma ya kashe wani Bamasare mutum mai daraja. Bamasaren yana da mashi a hannunsa, amma Benaiya ya yi yaƙi dashi da sanda kawai, ya fizge mashin a hannun Bamasaren sa'an nan ya kashe shi da mashinsa.
22Benaiya ɗan Yehoiyada ya yi waɗannan ayyukan kasada, an lissafa sunansa cikin sunayen jarumawannan uku.23An mutumta shi fiye da sauran sojojin nan talatin gaba ɗaya. Amma bai kai sauran sojojin nan uku masu ƙarfi ba. Duk da haka Dauda ya sa shi a bisa matsaransa.
24Mutum talatin ɗin sun haɗa da: Asahel ɗan'uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,25Shamma Baharodiye, Elika Baharodiye,26Helez Bafaltiye, Ira ɗan Ikkesh Batekoyi,27Abiyeza Ba'anatote, Mebunnai Bahushatiye,28Zalmon Ba'ahohite, Maharai Banetofatiye;
29Heleb ɗan Bãna, Banetofatiye, Ittai ɗan Ribai daga Gibiya ta Benyamin,30Benaiya Bafiratoniye, Hiddai na wajen kwarin Gãsh.31Abi albon Ba'arbatiye, Azmabet Babarhumi,32Eliyaba Bashãlboniye 'ya'yan Yashen, Yonatan ɗan Shamma Baharariye;
33Ahiyam ɗan Sharar Ba'arariye,34Elifelet ɗan Ahasbai Ma'akatiye, Eliyam ɗan Ahitofel Bagilone,35Hezro Bakarmile, Fãrai Ba'abite,36Igal ɗan Natan daga Zoba, Bani daga kabilar Gad.
37Zelek Ammoniye, Naharai Baberote masu ɗaukarwa Yowab kayan yaƙi ɗan Zeruya,38Ira Ba'i tire, Gareb Ba'itire,39Yuriya Bahittiye dukkan su talatin da bakwai

24

1Fushin Yahweh ya sake ƙuna akan Isra'ila, ya kuma iza Dauda akansu ya ce, "Jeka ka ƙidaya Isra'ila da Yahuda."2Sarki ya ce da Yowab shugaban runduna, wanda ya ke tare dashi, "Ka tafi cikin dukkan kabilun Isra'ila, daga Dan zuwa Biyasheba, ka ƙirga dukkan mutane, domin in san jimillar dukkan mutane da suka cancanta domin yaƙi."

3Yowab ya cewa sarki, "Bari Yahweh Allahnka ya riɓanɓanya mutane sau ɗari, kuma bari idanun sarki shugabana ya ga faruwar haka. Amma donme shugabana sarki ya ke son wannan?"4Duk da haka maganar sarki ta zama ita ce ta ƙarshe akan ta Yowab da sauran shugabannin rundunar yaƙi. Sai Yowab da sarakunan rundunar yaƙi suka fita daga gaban sarki domin su ƙirga yawan mutanen Isra'ila.
5Suka haye Yodan suka sauka kusa da Arowa, hannun dama ga birnin da ke cikin kwari. Daga nan suka yi tafiya zuwa Gad har zuwa Yazer.6Suka zo Giliyad da kuma ƙasar Tahtim Hodshi, daga nan sai Dan yăn da kewayen wajen Sidon.7Suka zo kagarar Taya da dukkan biranen Hibiyawa dana Kan'aniyawa. Daga nan suka fita zuwa Negeb cikin Yahuda a Biyasheba.
8Ya yin da suka je dukkan ƙasar, sai suka dawo Yerusalem a ƙarshen watan tara da kwana ashirin.9Yowab ya bada rahoton jimillar yawan mayaƙa ga sarki. Akwai mutum 800,000 a cikin Isra'ila jarumawa masu zarar takobi, mazajen Yahuda kuma su 500,000 ne.
10Daga nan sai zuciyar Dauda ta soke shi bayan ya lissafta mutanen. Sai ya ce da Yahweh, "Na yi babban zunubi ta wurin yin wannan. Yanzu fa, Yahweh, ka ɗauke laifin bawanka, gama na aikata wauta ƙwarai."
11Sa'ad da Dauda ya tashi da safe, sai maganar Yahweh ta zo wurin annabi Gad, mai duba, na Dauda cewa,12"ka je kace da Dauda: 'Wanan shi ne abin da Yahweh ya ce: "'Ina miƙa maka abu uku, sai ka zaɓi ɗaya cikinsu.""
13Sai Gad ya je wurin Dauda ya ce masa, "Ko shekaru uku na yunwa su zo maka cikin ƙasarka, ko kuwa zaka yi ta gudu wata uku daga abokan gabarka suna bin ka? ko kuwa za ayi annoba kwana uku a cikin ƙasarka? Yanzu sai kayi shawarar amsar da zan maida wa shi wanda ya aiko ni."14Sai Dauda ya cewa Gad, "I na cikin babbar damuwa." Bari mu faɗa cikin hannun Yahweh da mu faɗa cikin hannun mutum, gama ayyukan jinƙansa da girma suke."
15Sai Yahweh ya aika da annoba kan Isra'ila daga safe zuwa lokacin da aka sanya, mutane dubu saba'in suka mutu daga Dan zuwa Biyasheba.16Lokacin da mala'ika ya miƙa hannunsa wajen Yerusalem domin ya hallakata, Yahweh ya canza tunaninsa game da ɓarnar, ya ce da mala'ikan da ke hallakar da mutanen, "Ya isa! Sai ka janye hannunka yanzu." A wancan lokacin mala'ikan Yahweh yana tsaye a masussukar Arauna Bayebushe.
17Dauda ya yi magana da Yahweh da ya ga mala'ikan da ya bugi mutanen, ya ce, "Na yi zunubi, kuma na yi aikin shiririta. Amma tumakin nan me suka yi? Ina roƙon ka bari hannunka ya hukunta ni da iyalin mahaifina!"
18Ran nan sai Gad ya zo wurin Dauda ya ce masa, "Ka hau ka gina bagade ga Yahweh a masussukar Arauna Bayebushe."19Dauda kuwa ya hau kamar yadda Gad ya faɗa masa ya yi, kamar yadda Yahweh ya umarta.20Arauna ya duba ya ga sarki da bayinsa suna isowa. Sai Arauna ya fito ya sunkuyar da kansa ga sarki da fuskarsa a ƙasa.
21Daga nan sai Arauna ya ce, "Donme shugabana sarki ya zo wurina, bawansa?" Dauda ya amsa, "Domin in sa yi masussukarka, domin in gina bagadi ga Yahweh, domin a iya kawar da annoba cikin mutane."22Arauna ya cewa Dauda, "Ka ɗauke ta kamar ta ka, ya shugabana sarki. Ka yi dukka abin da ka ga dama. Duba, ga shanu domin hadaya ta ƙonawa da kayan masussuka da karkiyoyin shanu domin itace.23Dukkan waɗannan, sarkina, Ni, Arauna, zan ba ka." Sai ya ce da sarki, "Bari Yahweh Allahnka ya karɓe ka."
24Sai sarki ya cewa Arauna, "A'a, lallai sai dai mu yi ciniki in saye ta. Ba zan miƙa hadayar ƙonawa ga Yahweh ta kowanne abin da ban biya ba." Dauda ya sayi masussukar da shanun akan awo hamsin na azurfa.25Dauda ya gina wa Yahweh bagadi a wurin ya miƙa ƙonannun hadayu, da hadayun zumunta. Da haka suka roƙi Yahweh a madadin ƙasar, ya kuma sa annobar ta tsaya a ko'ina cikin Isra'ila.

Littafin sarakuna na ɗaya

1

1Sa'ad da Sarki Dauda ya tsufa sosai, suka lulluɓe shi da barguna amma bai ji ɗumi ba.2Sai bayinsa suka ce, "Bari mu samo wa shugabanmu sarki wata budurwa domin ta yi wa sarki hidima ta kula da shi. Ta kwanta a damatsen shugabanmu sarki domin ya ji ɗumi."

3Suka bincika cikin dukkan lungunan Isra'ila, sai suka samo Abisha Bashunamiye su ka kawo ta wurin sarki. Budurwar kyakkyawa ce ƙwarai.4Ta yi wa sarki hidima ta lura da shi, amma sarkin bai kwana da ita ba.
5A wannan lokacin Adonija ɗan Haggit ya ɗaukaka kansa, cewa, "Ni zan zama sarki." Ya shirya wa kansa karusai da mahaya, mazaje hamsin su wuce gabansa.6Babansa bai dame shi ba da cewa, "Meyasa ka yi wannan ko wancan?" Adonija ma kyakkyawan mutum ne ƙwarai, shi aka haifa bayan Absalom.
7Ya haɗa kai da Yowab ɗan Zeruyiya da Abiyata firist. Suka bi Adonija suka taimaka masa.8Amma Zadok firist da Benayiya ɗan Yehoiada da Natan annabi da Shimai da Reyi da jarumawan da ke tare da Dauda ba su bi Adonija ba.
9Adonija ya yi hadayar tumaki da bijjimai da kiwatattun shanu kusa da dutsen Zohelet, wanda ke daura da En Rogel. Ya gayyaci dukkan 'yan'uwansa, 'ya'yan sarki da dukkan mazajen Yahuda da bayin sarki.10Amma Natan annabi da Benayiya da mazajen Suleman ɗan'uwansa bai gaiyace su ba.
11Sai Natan ya yi wa Batsheba uwar Suleman magana, cewa, "Ba ki ji cewa Adonija ɗan Haggit ya zama sarki ba, kuma ba da sannin Dauda shugabanmu ba?12Bari in ba ki shawara yanzu domin ki ceci ranki da na ɗanki Suleman.
13Ki je wurin sarki Dauda, ki ce, shugabana, ba ka yi rantsuwa ga baiwarka ba, cewa, "Babu shakka Suleman ɗanki shi ne zai yi sarauta bayana, ya zauna kan kursiyina ba?" Me ya sa Adonija ke mulki?'14Sa'ad da ki ke magana da sarki, zan zo in tabbatar masa da maganganunki."
15Sai Batsheba ta tafi ɗakin sarki. Sarki ya tsufa ƙwarai, Abisha Bashunamiya tana yi wa sarki hidima.16Batsheba ta sunkuya ta kwanta a gaban sarki. Sarki ya ce da ita, "Me ki ke so?"17Ta ce da shi, "Shugabana, ka rantsewa baiwarka da Yahweh Allahnka, cewa, 'Babu shakka Suleman ɗanki, shi zai yi mulki baya na, shi zai zauna a kursiyina?'
18To yanzu ka ga, Adonija ne sarki, kai kuma shugabana sarki ba ka sani ba.19Ya yi hadaya da bijjimai da kiwatattun shanu da tumaki da yawa, kuma ya gayyaci dukkan 'ya'yan sarki da Abiyata firist da Yowab shugaban sojoji, amma bai gayyaci Suleman bawanka ba.
20Game da kai shugabana sarki, dukkan idanun Isra'ila kai suke kallo, suna jira ka ce da su ga wanda zai yi mulki a bayana, shugabana.21Idan kuwa ba haka ba, zai zama bayan da shugana sarki ya yi barci tare da ubanninsa, ni da ɗana Suleman za a mai da mu kamar 'yan ta'adda."
22Tana cikin magana da sarki, sai Natan annabi ya shigo.23Barori suka ce da sarki, "ga Natan annabi ya zo." Sa'ad da ya shigo gaban sarki, ya kwanta da fukarsa a ƙasa a gaban sarki.
24Natan yace, "Shugabana sarki, ka ce Adonija zai yi mulki bayana, shi zai zauna kan kursiyina ne?'25Gama ya tafi yau ya yi hadaya da bijjimai da kiwattatun shanu da tumaki da yawa, kuma ya gayyaci dukkan 'ya'yan sarki da shugaban sojoji da Abiyata firist. Suna ci suna sha a gabansa, suna cewa, 'ranka ya daɗe sarki Adonija!'
26Amma ni, bawanka da Zadok firist da Benaiya ɗan Yehoiada da bawanka Suleman bai gayyace mu ba.27Shugabana ya yi haka ba tare da ya gaya mana bayinka ba, wanda zai zauna a kan kursiyinsa?"
28Sai sarki ya amsa ya ce, "kira mani Batsheba ta dawo." Ta zo gaban sarki ta tsaya.29Sarki ya yi alƙawari ya ce, "Da ran Yahweh wanda ya cece ni daga dukkan wahalhalu,30kamar yadda na rantse maku da Yahweh, Allah na Isra'ila, cewa, 'Suleman ɗanki, shi zai yi mulki bayana, zai zauna kan kursiyna, zan yi haka yau."31Sa'an nan sai Batsheba ta sunkuya da fuskarta a ƙasa ta kwanta gaban sarki ta ce, "Ranka ya daɗe shugabana, sarki Dauda!"
32Sarki Dauda yace, "A kira mani Zadok firist da Natan annabi da Benayiya ɗan Yahoiada." Sai su ka zo gaban sarki.33Sarki ya ce, "ku tafi da barorin shugabanku, ku sa Suleman ya hau alfadarina ku kai shi Gihon.34Bari Zadok firist da Natan annabi su shafe shi ya zama sarki akan Isra'ila su busa ƙaho su ce, 'Ranka ya daɗe sarki Suleman!'
35Sai ku biyo shi, ya zo ya zauna kan kursiyina; domin shi ne zai gaje ni. Na naɗa shi ya zama sarki bisa Isra'ila da Yahuda."36Benayiya ɗan Yehoiada ya amsawa sarki ya ce, "Bari ya zama haka! Yahweh Allah na shugabana sarki, ya tabbatar da shi.37Kamar yadda Yahweh ya kasance da shugabana sarki, bari ya kasance da Suleman, kursiyinsa ya ɗaukaka fiye da kursiyin shugabana sarki Dauda."
38Sai Zadok firist da Natan annabi da Benayiya ɗan Yehoiada da Keretawa da Feletiyawa suka je suka ɗora Suleman akan alfadarin Sarki Dauda; suka kawo shi Gihon.39Zadok firist ya ɗauko ƙahon mai daga cikin rumfa ya shafe Suleman. Sa'an nan suka busa ƙaho, sai dukan mutane suka ce, "Ranka ya daɗe sarki Suleman."40Sa'an nan dukkan mutane suka biyo shi suna busa sarewa suna farinciki da murna sosai, har ƙasa ta girgiza saboda ƙararsu.
41Adonija da bãƙinsa da ke tare da shi suka ji sa'ad da suka gama ciye-ciye. Sa'ad da Yowab ya ji ƙarar ƙahon ya ce, "Me ya sa a ke hargowa a cikin birni?"42Yana cikin magana Yonatan ɗan Abiyata firist ya zo. Adonija yace, "Shiga, kai mai aminci ne ka kuma kawo labari mai daɗi."
43Yonatan yace da Adonija, "Shugabanmu sarki Dauda ya sa Suleman ya zama sarki,44kuma sarki ya aiko shi tare da Zadok firist da Natan annabi da Benayiya ɗan Yehoiada da Keretawa da Feletiyawa. Sun sa Suleman ya hau alfadarin sarki.45Zadok firist da Natan annabi sun shafe shi ya zama sarki a Gihon, sun taho daga can su na murna, saboda haka birni ya cika da hargowa. Wannan ita ce hayaniyar da ka ke ji.
46Kuma, Suleman yana zaune akan kursiyin mulki.47Bayan haka, barorin sarki sun zo suna sawa sarki Dauda albarka suna cewa, 'Bari Allahnka ya sa sunan Suleman ya fi naka.' Sai sarki ya sunkuya akan gado.48Sai sarki ya ce, 'Albarka ga Yahweh Allah na Isra'ila, da ya bada wanda zai zauna akan kursiyina yau, kuma idona yana gani.'"
49Sai dukkan bãƙin Adonija suka firgita. Suka tashi tsaye kowa ya bi hanyarsa.50Adonija yana jin tsoron Suleman, ya je ya riƙe ƙahonin bagadi.51Sai aka gaya wa Suleman cewa, Duba, Adonija yana jin tsoron sarki Suleman, gama gashi can ya na riƙe da ƙahonin bagadi, yana cewa, 'Bari sarki Suleman ya rantse mani cewa ba zai kashe bawansa da takobi ba."'
52Suleman yace, "Idan zai nuna kansa mutumin kirki, ko gashin kansa ba zai faɗi a ƙasa ba, amma idan aka sami mugunta a wurinsa to zai mutu."53Sarki Suleman ya aika mutane suka saukar da Adonija daga bagadi. Ya zo ya russana a gaban Suleman, Suleman ya ce da shi, "Tafi gidanka."

2

1Sa'ad da ranar mutuwar Dauda ta gabato, ya umurci ɗansa, Suleman cewa,2"ina bin hanyar dukkan duniya, ka ƙarfafa, ka nuna kanka namiji.3Ka kiyaye dokokin Ubangiji Allahnka, ka yi tafiya cikin hanyoyinsa, ka kiyaye farillansa da dokokinsa da shawarwarinsa da alƙawaransa, kana kiyaye abin da da aka rubuta cikin dokokin Musa domin ka wadata cikin dukkan abin da ka ke yi, a dukkan inda ka nufa,4domin Yahweh ya cika maganarsa wadda ya faɗi game da ni, cewa, 'Idan 'ya'yanka suka lura da tafarkinsu, suka yi tafiya a gabana da aminci da dukkan zuciyarsu da dukkan ransu, ba za ka rasa mutum akan kursiyin Isra'ila ba.'

5Ka san abin da Yowab ɗan Zeruya ya yi ma ni da abin da ya yi wa jami'an sojojin Isra'ila su biyu, Abna ɗan Ner da Amasa ɗan Yatar waɗanda ya kashe. Ya zubar da jinin yaƙi cikin salama, ya sa jinin yaƙi akan ɗamarar da ke ƙugunsa da takalman da ke ƙafafunsa.6Ka yi da Yowab bisa ga hikimar da ka koya, amma kada ka bari furfurarsa ta tafi kabari cikin salama.
7Duk da haka, ku yi mutunci ga 'ya'yan Barzilai Bagilide, ku bar su su zauna a cikinku su ci a teburinka, gama sun je wurina sa'ad da na gudu daga wurin ɗan'wanka Absolom.
8Duba, Shimai ɗan Gera mutumin Benyamin ta Bahurim yana tare da ku, wanda ya zage ni, ya wulaƙanta ni, ya zazzage ni ranar da na je Mahanayim. Ya zo ya tarbe ni a Yodan, na rantse masa da sunan Yahweh cewa, 'Ba zan kashe ka da takobi ba.'9Kada ka bar shi ya tafi ba tare da ka hore shi ba. Kana da hikima ka san yadda za ka yi da shi. Ka sa furfurarsa ta faɗi cikin jini."
10Sa'an nan Dauda ya yi barci tare da ubanninsa aka bizne shi a birnin Dauda.11Dauda ya yi mulki a Isra'ila shekaru arba'in, shekaru bakwai ya yi mulki a Hebron, a Yerusalem kuma ya yi mulki shekaru talatin da uku.12Suleman ya zauna akan kursiyin Dauda ubansa, mulkinsa kuwa ya kahu da ƙarfi ƙwarai.
13Sai Adonija ɗan Haggit ya zo wurin Batsheba uwar Suleman. "Ta ce da shi cikin salama ka zo?" Ya ce, cikin salama ƙwarai."14Ya ce, ina da wani abu da zan faɗa maki." Sai ta ce, "To ka faɗi."15Adonija yace, "Kin san mulkin nawane, dukkan Isra'ila sun yi zaton ni zan zama sarki. Amma abubuwa sun canza, an ba ɗan'uwana sarauta, kuma wannan daga Yahweh ne.
16Zan roƙi abu ɗaya a wurin ki, kada ki juya mani baya, Batsheba ta ce, "Ka faɗi."17Ya ce, "Ki yi magana da Suleman sarki, na san ba zai ƙi jin maganar ki ba, ki ce da shi ya ba ni Abishag Bashunamiye ta zama matata.18Batsheba ta ce, "Ya yi kyau, zan yi magana da sarki."
19Sai Batsheba ta je wurin sarki ta faɗa masa maganar da Adonija ya yi. Sarki ya je ya tarbe ta, ya russana a gabanta. Sa'an nan ya zauna a kan kursiyinsa kuma ya sa aka kawo wa mamar sarki kujera. Ta zauna a hannun damarsa.20Ta ce da shi, "Zan roƙi wani ɗan abu daga wurinka, na sani ba za ka ƙi ba." Sai sarki ya ce, "Ki roƙa mama, ba zan ƙi ba."21Ta ce, "Ka bari a ba Adonija ɗan'uwanka Abishag Bashunamiye ta zama matarsa."
22Sarki Suleman ya amsa ya ce da mamarsa, "Meyasa ki ka ce a ba Adonija Abishag Bashunamiye ta zama matarsa? Meyasa ba ki ce a ba shi mulkin ba kuma gama shi yayana ne - ne dai, domin Abiyata firist, ko domin Yowab ɗan Zeruya?"23Sarki Suleman ya rantse da sunan Yahweh, ya ce, "Bari Allah ya yi mani fiye da haka, idan Adonija ba a bakin ransa ya faɗi wannan magana ba.
24Yanzu da ran Yahweh, wanda ya sa ni a kan kursiyin Dauda mahaifina, ya yi gida domina, babu shakka yau za a kashe Adonija."25Sarki Suleman ya aiki Benayiya ɗan Yehoiada, ya nemi Adonija ya kashe shi.
26Sa'an nan sarki ya ce da Abiyata firist, ka tafi Anatot, ga gonakinka, kaima ka isa mutuwa, amma ba zan kashe ka a wannan lokaci ba, domin ka ɗauki akwatin Ubangiji Yahweh a gaban Dauda mahaifina, ka sha wahala kamar yadda mahaifina ya sha."27Ta haka Suleman ya kori Abiyatar daga zama firist na Yahweh, domin maganar da Yahweh ya faɗi a Shilo game da gidan Eli ta cika.
28Sai maganar ta zo ga Yowab saboda ya goyi bayan Adonija, ko da ya ke bai goyi bayan Absolom ba. Sai Yowab ya gudu ya shiga rumfar Yahweh ya kama ƙahonin bagadi ya riƙe.29Sai aka gaya wa Suleman sarki, cewa ga Yowab can cikin rumfar Yahweh, sai ya ce da Benayiya ɗan Yehoiada, "Je ka same shi ka kashe shi."
30To sai Benayiya ya zo rumfar Yahweh, ya ce masa, "Sarki ya ce, 'ka fito"' Yowab ya amsa ya ce, "A'a ni zan mutu a nan." Sai Benaiya ya koma ya gaya wa sarki, cewa, Yowab yace, Yana so ya mutu a kan bagadi."31Sai sarki ya ce da shi, yi yadda ya faɗi. Kashe shi ka ɗauke shi, ka bizne domin a kawar da jinin da Yowab ya zubar ba dalili daga gidan mahaifina.
32Yahweh ya sa jininsa ya koma kansa, gama ya sami mutane biyu waɗanda sun fi shi, kuma sun fi shi sarki, ya kashe su da kaifin takobi. Wato Abna ɗan Na shugaban sojojin Isra'ila da Amasa ɗan Yeter shugaban sojojin Yahuda, ba tare da sanin mahaifina sarki Dauda ba.33Bari jininsu ya dawo kan Yowab da zuriyarsa har abada. Amma ga Dauda da zuriyarsa da gidansa da kursiyinsa, bari salama daga Yahweh ta kasance har abada."
34Sai Benayiya ya je ya sami Yowab, ya far masa ya kashe shi. A ka bizne shi a gidansa cikin daji.35Sarki ya sa Binayiya ɗan Yehoiada ya zama shugaban sojoji maimakon sa, ya kuma sa Zadok firist a gurbin Abiyata.
36Sai kuma sarki ya aika a ka kira Shimai, yace masa, "Ka gina gida domin kanka a cikin Yerusalem ka zauna nan, kada ka bar wurin ka je ko'ina.37Duk randa ka fita ka wuce kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu. Kuma jininka zai koma kanka."38Sai Shimai ya cewa sarki abin da ka faɗi ya yi kyau. Kamar yadda shugabana sarki ya faɗi, haka bawanka za ya yi." Daga nan Shimai ya zauna a Yerusalem kwanaki da yawa.
39Amma bayan shekaru uku, bayin Shemai guda biyu suka guda suka je wurin Akish ɗan Ma'aka, sarkin Gat. A ka gaya wa Shimai, cewa, duba, bayinka "biyu fa sun koma Gat."40Sai Shimai ya tashi, ya sa sirdi a kan jakinsa, ya je wurin Akish a Gat neman bayinsa. Ya dawo da bayinsa daga Gat.
41Sa'ad da a ka gaya wa Suleman, cewa Shimai ya fita daga Yerusalem ya je Gat ya dawo,42sarki ya aika a ka kira Shimai ya ce da shi, "Ba na sa ka yi rantsuwa da Yahweh ba na shaida maka, cewa, 'Ka sani duk randa ka bar nan ka je wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba.'? Ka ce mani, 'abin da ka faɗi ya yi kyau.'
43To meyasa ba ka cika alƙawarinka ga Yahweh ba, da abin da na umurce ka?"44Sa'an nan sarki ya cewa Shimai, "Ka sani cikin zuciyarka dukkan muguntar da ka yi wa mahaifina Dauda. To Yahweh zai sa muguntarka ta koma kanka.
45Amma sarki Suleman zai zama mai albarka, kursiyin Dauda kuma zai tabbata a gaban Yahweh har abada."46Sa'an nan sarki ya ummurci Benayiya ɗan Yehoiada. Ya fita waje ya kashe Shimai. Haka mulkin ya tabbata a hannun Suleman.

3

1Suleman ya yi yarjejeniya da Fir'auna sarkin Masar ta dalilin aure. Ya ɗauko ɗiyar Fir'auna ya kawo ta cikin birnin Dauda har sai lokacin da ya gama ginin gidansa da gidan Yahweh da ganuwar da ta kewaye Yerusalem.2Mutane suna ta miƙa hadayu a wurare masu bisa, saboda ba a gina gida saboda sunan Yahweh ba tukuna.3Suleman ya nuna ƙauna ga Yahweh ta wurin tafiya cikin tafarkun mahaifinsa Dauda, sai dai shi ma ya miƙa hadaya kuma ya ƙona turare a wurare masu bisa.

4Sarki ya je Gibiyon domin ya miƙa hadaya a can, domin can akwai wurare masu bisa sosai. Suleman ya miƙa hadayu dubu a kan bagadi.5Yahweh ya bayyana ga Suleman a cikin mafarki a Gibiyon, ya ce, "Ka roƙa! Mene ne zan ba ka?"
6Sai Suleman yace, "Ka nuna girman alƙawarinka da jinƙai da aminci ga bawanka, mahaifina Dauda, saboda ya yi tafiya a gabanka cikin aminci da tsarki da gaskiya cikin zuciyarsa. Ka riƙe wannan alƙawarin da aminci da ka ba shi ɗa wanda zai zauna a kan kursiyinsa yau.
7Yanzu fa, ya Yahweh Allahna, ka sa bawanka ya zama sarki a maimakon mahaifina Dauda, ko da ya ke ni ɗan yaro ne. Ban san yadda zan fita ko in shiga ba.8Bawanka yana cikin tsakiyar mutane waɗanda ka zaɓa, mutane masu yawa da sun fi gaban a lisafta ko a ƙidaya su.9Ka ba bawanka zuciya mai fahimta domin ya hukunta mutanenka, domin in gane bambanci tsakanin abu mai kyau da mummuna. Gama wane ne zai iya hukunta wannan jama'a taka mai yawa haka?"
10Wannan roƙo na Suleman ya gamshi Ubangiji.11Sai Allah ya ce da shi, "Saboda ka roƙi wannan, ba ka roƙi tsawon rai ba, ko dukiya ko ran maƙiyanka ba, Amma ka roƙi fahimta domin ka gane gaskiya,12duba zan yi maka dukkan abin da ka roƙa a gare ni. Na ba ka zuciya mai hikima da ganewa, ba a yi wani mai hikima kamar ka a dã ba, ba kuma za a sami wani mai hikima kamar ka ba a nan gaba bayanka.
13Kuma na ba ka har ma abin da ba ka roƙa ba, dukiya da martaba, yadda ba za a sami wani kamar ka ba a cikin sarakuna dukkan kwanakin ranka.14Idan ka yi tafiya cikin hanyoyina da farillaina da dokokina kamar yadda Dauda mahaifinka ya yi tafiya, zan haskaka kwanakinka."
15Sai Suleman ya farka, ashe mafarki ya yi. Ya zo Yerusalem ya tsaya a gaban akwatin alƙawarin Ubangiji. Ya miƙa hadayu na ƙonawa da na salama kuma ya yi liyafa domin dukkan bayinsa.
16Sai ga waɗansu mata biyu karuwai suka zo gabansa suka tsaya.17Sai ɗaya matar ta ce, "Ya shugabana, ni da wannan matar muna zama a gida ɗaya, ni da ita muka haihu a gidan.
18Bayan na haihu da kwana uku, wannan matar kuma sai ta haihu. muna tare. Ba kowa tare da mu sai mu biyu a gidan.19Sai ɗan wannan matar ya mutu cikin dare saboda ta kwanta a kansa.20Sai ta tashi cikin tsakiyar dare ta ɗauke ɗana daga kusa da ni, domin baiwarka ta yi barci, ta kwantar da shi a ƙirjinta, sai ta kwantar da nata mataccen ɗan a ƙirjina.
21Sa'ad da na tashi da safe domin in shayar da ɗana sai na ga ya mutu. Amma da na dube shi da kyau da safe, sai na ga ba ɗana ba ne wanda na haifa."22Sa'an nan sai ɗaya matar ta ce, "Ba haka ba ne, ɗan mai rai nawa ne ke kuma mataccen ne naki." Sai ɗaya matar ta ce, "A'a mataccen ne naki mai ran kuma shi ne ɗana." Haka suka yi ta magana a gaban sarki.
23Daga nan sarki yace, "Ke kin ce, "Wannan ɗana ne mai ran, kuma naki ne mataccen,' ɗayar kuma ta ce, 'A'a, ɗanki shi ne mataccen, ɗana kuma shi ne mai ran."'24Sai sarki yace, "Ku kawo mani takobi." Sai aka kawo wa sarki takobi.25Daga nan sarki ya ce, "Ku raba ɗan mai rai kashi biyu, ku ba wannan mata rabi, rabi kuma ga ɗayar."
26Sai ɗaya matar wadda ɗanta ne ya ke da rai, ta yi magana ta ce da sarki, gama zuciyarta ta cika da tausayi saboda ɗanta, ta ce, "Aiya, shugabana, a ba ta ɗan mai rai kada a kashe shi." Amma ɗaya matar ta ce, "Ba zai zama naki ko nawa ba. A raba shi."27Sai sarki ya yi magana ya ce, "Ku ba da ɗan mai rai ga matar ta farko, kada ku kashe shi, ita ce mahaifiyarsa."28Sa'ad da dukkan Isra'ila suka ji wannan hukunci, suka ji tsoron sarki, saboda sun ga hikimar Yahweh na tare da shi domin yanke hukunci.

4

1Suleman shi ne sarki a bisa dukkan Isra'ila.2Waɗannan su ne jami'ansa: Azariya ɗan Zadok shi ne firist.3Elihoref da Ahija 'ya'yan Shisha su ne magatakarda, Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubuci.4Benayiya ɗan Yehoiada shi ne shugaban sojoji. Zadok da Abiyata su ne firistoci.

5Azariya ɗan Natan shi ne shugaban ma'aikata. Zabud ɗan Natan shi ma firist ne kuma abokin sarki.6Ahisha shi ne sarkin gida. Adoniram ɗan Abda shi ne shugaban masu aikin ƙarfi.
7Suleman ya na da jami'ai goma sha biyu a dukkan Isra'ila waɗanda su ke tanada abinci domin sarki da mutanen gidansa. Kowanne mutum zai kawo abincin wata ɗaya a shekara.8Ga sunayensu: Ben Hur shi ne mai kula da tudun Ifraim;9Ben Deker shi ne a Makaz da Sha'albim da Bet Shemesh da Elon Bet Hanan;10Ben-Hesed a Arubbot (shi a ka damƙawa Sokoh da dukkan ƙasar Hefa);
11Ben Abinadab shi ne cikin dukkan Nafot Dor (Tafat ɗiyar Suleman ita ce matarsa);12Ba'ana ɗan Ahilud ya na cikin Ta'anak da Megiddo da dukkan Bet Shan, wato kusa da Zaretan gangaren Yeziriyel, daga Bet Shan zuwa Abel Meholah har zuwa ɗaya gefen na Yokmiyam;13Ben Geber cikin Ramot Giliyad (shi aka danƙawa garuruwan Ja'ir ɗan Manasse waɗanda ke cikin Giliyad yankin Argob na wanda ke cikin Bashan ma nasa ne, manyan birane sittin masu ƙofofin jan ƙarfe);14Abinadab ɗan Iddo cikin Mahaniyam;
15Ahima'az cikin Naftali (kuma ya auri Basemat ɗiyar Suleman ta zama matarsa);16Ba'ana ɗan Hushai cikin Asha da Bi'alot;17Yehoshafat ɗan Faruya cikin Issaka;
18Shimei ɗan Ela, cikin Benyamin;19da Geber ɗan Uri cikin ƙasar Giliyad, da ƙasar Sihon sarkin Amoriyawa da Og sarki Bashan, kuma shi ne kaɗai jami'in da ke cikin ƙasar.
20Yawan Yahuda da Isra'ila yana kama da yashin teku. Su na ci suna sha suna jin daɗi.21Suleman ya yi mulki kan dukkan mulkoki tun daga Kogi har zuwa ƙasar Filistiyawa da iyakar Masar. Suna bautawa Suleman suna kawo masa gaisuwa dukkan kwanakinsa.22Abincin gidan Suleman na rana ɗaya shi ne bahu talatin na niƙaƙƙen gari da kuma tsaba bahu sittin,23da bijimai masu ƙiba guda goma da shanu guda ashirin daga makiyaya, da tumaki ɗari, banda barewa da gadã da namijin barewai, da kaji masu mai.
24Gama shi ne ya ke mulkin dukkan yankin da ke hayin Kogi, tun daga Tifsa har zuwa Gaza, a bisa dukkan sarakunan da ke hayin Kogi, kuma yana da salama a kowanne gefe.25Yahuda da Isra'ila sun sami tsaro har kowanne mutum yana zuwa gonarsa ta inabi da ta ɓaure, tun daga Dan zuwa Biyasheba a dukkan kwanakin Suleman.
26Suleman yana da ɗakunan dawakai dubu arba'in domin karusansa, da masu hawan dawakai mutum dubu goma sha biyu.27Waɗannan jami'ai suna tanado abinci domin sarki Suleman da dukkan wanda ya zo ya ci a teburin sarki, kowanne mutum da watansa, ba su bari an rasa komai ba.28Kuma suna kawo hatsi da ciyawa saboda dawakan da suke jan karusai, kowanne mutum bisa ga iyawarsa.
29Allah ya ba Suleman ƙasaitacciyar hikima da fahimta, faɗin ganewarsa yana kama da yashin da ke bakin teku.30Hikimar Suleman ta fi ta dukkan mutanen gabas da dukkan hikimar Masar.31Hikimarsa ta fi ta dukkan mutane - ya fi Etan Ba-ezrahi hikima harma da Heman da Kalkol da Darda 'ya'yan Mahol - ya zama sananne a dukkan al'umman da ke kewaye.
32Ya faɗi misalai dubu uku, ya yi waƙoƙi dubu da biyar.33Ya yi bayani a kan tsire-tsire da itacen sidar da ke Lebanon har zuwa waɗanda suke fitowa a jikin bangon ɗaki. Ya yi bayani a kan namun daji da tsuntsaye da kifaye.34Mutane sukan zo daga wurare daban-daban domin su ji hikimar Suleman. Sukan zo daga wurin dukkan sarakunan da suka ji hikimar Suleman.

5

1Hiram sarkin Taya ya aiki barorinsa wurin Suleman saboda ya ji an naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa; gama Hiram mai ƙaunar Dauda ne.2Suleman ya aika da magana zuwa ga Hiram, cewa,3"Ka sani mahaifina Dauda bai iya gina gida domin Yahweh Allansa ba, saboda yaƙe-yaƙen da suka kewaye shi, gama a lokacinsa Yahweh na ta sa abokan gabarsa a ƙarƙashin tafin sawunsa.

4Amma yanzu, Yahweh ya ba ni hutawa a kowanne gefe. Ba abokin gãba kuma babu annoba.5To yanzu na yi niyya in gina haikali domin sunan Yahweh Allahna, kamar yadda Yahweh ya yi magana da mahaifina Dauda cewa, 'Ɗanka wanda zan sa a kan kursiyin mulki ya gaje ka, shi ne zai gina haikali domin sunana.'
6To yanzu sai ka ba da umurni a saro mani itacen sida daga Lebanon. Bayina za su haɗu da bayinka, kuma zan biya bayinka dai-dai bisa ga abin da ka yarda da shi. Domin ka san a cikin mu ba wanda ya iya yankan katako kamar Sidoniyawa."
7Lokacin da Hiram ya ji maganar Suleman, ya yi murna ƙwarai da gaske, ya ce, "Bari albarka ta kasance ga Yahweh yau, saboda ya ba Dauda ɗa mai hikima a kan jama'arsa mai girma."8Hiram ya aika da magana zuwa ga Suleman, cewa, "Na ji saƙon da ka aiko wurina. Zan ba ka dukkan katakon sida da na fir yadda ka ke bukata.
9Bayina za su kawo itatuwan daga Lebanon zuwa teku, zan sa a ɗaɗɗaure su yadda za a iya sawo su a teku yadda ka ke so in yi, zan sa a yayyanka su domin ka ɗauko. Zan so ka bada abinci domin iyalin gidana.
10Haka Hiram ya ba Suleman dukkan katakon sida da fir yadda ya bukata.11Suleman ya ba Hiram bahu dubu ashirin na alkama da mai wanda a ka tace garwa ashirin domin abincin gidansa, haka Suleman ya ba Hiram shekara biye da shekara.12Yahweh ya ba Suleman hikima, kamar yadda ya yi alƙawari. Salama ta kasance tsakanin Suleman da Hiram, suka ƙulla amana.
13Sarki Suleman ya sa wa Isra'ilawa aikin dole. Mutanen da a ka sa aikin dolen sun kai dubu talatin.14Ya aika su Lebanon, mutum dubu goma an sa kowanne wata, wata ɗaya suna Lebanon, wata biyu kuma su na gida. Adoniram ya shugabanci waɗanda a ka sa su yi aikin dole ɗin.
15Suleman yana da mutum dubu saba'in masu ɗaukar kaya, dubu takwas da kuma masu saro dutse cikin tsaunuka,16ban da haka Suleman yana da mutum 3,300 jami'ai ne na ma'aikata kuma masu duba ma'aikata.
17Bisa ga ummurnin sarki, suka sassaƙo manyan duwatsu masu ƙwari domin a kafa tushen haikali.18Haka masu gini na wajan Suleman da na wajan Hiram da Gebalawa suka saro katakan suka shirya su tare da duwatsun domin ginin haikali.

6

1Suleman ya fara gina haikalin Yahweh. Hakan ya faru a shekara ta 480 bayan dawowar 'ya'yan Isra'la daga Masar, a cikin shekara ta huɗu ta mulkin Suleman a bisa Isra'ila cikin watan Zif wato wata na biyu.2Haikalin da Sarki Suleman ya gina wa Yahweh, ratarsa kamu sittin ne, faɗinsa kamu ashirin ne, tsawonsa kuma kamu talatin ne.

3Ratar shirayin da ke ƙofar haikalin kamu ashirin ne, dai-dai suke da faɗin haikalin, a gaban haikalin kuma ta kai kamu goma.4Ya yi wa gidan tagogi waɗanda faɗinsu daga ciki ya fi daga waje.
5Ya gina ɗakuna kewaye da ɗakin taro, ɗakuna sun kewaye ɗakuna na ciki da na waje. Ya gina ɗakuna a kowanne gefe.6Bene na can ƙasa kamu biyar ne faɗinsa, na tsakiya kuma kamu shida ne a faɗi, na uku kuma kamu bakwai ne faɗinsa. Domin a kewaye da bangon gidan ya yi matokarai a bangon gidan a kowanne gefe domin kada a kafa wani abu a bangon gidan.
7An gina gidan da sassaƙaƙƙun duwatsun da a ka shiryo a mahaƙar duwatsu. Sa'adda a ke ginin gidan ba a ji ƙarar gatari ko guduma ba.8A fuskar kudu ta haikalin an yi wurin shigowa daga ƙasa, a ka yi matakalu suka yi sama zuwa tsakiya, suka tafi har zuwa hawa na uku.
9Haka Suleman ya gina haikalin ya gama shi; ya rufe gidan da matokarai da katakai na sida.10Ya yi ɗakuna a jikin ɗakunan taro na haikali, kowanne tsawonsa kamu biyar ne; a ka jingina su jikin gidan da katakai na sida.
11Sai maganar Yahweh ta zo ga Suleman, cewa,12"Game da gidan da ka ke ginawa, idan ka kiyaye farillaina ka yi adalci, ka kiyaye dokokina ka yi tafiya a cikin su, sa'an nan zan tabbatar maka da alƙawarin da na yi wa Dauda mahaifinka.13Zan zauna cikin mutanen Isra'ila, ba zan yashe su ba."
14Haka Suleman ya gina gidan ya gama shi.15Sa'an nan ya gina bangaye na ciki da falankai na sida. Ya rufe gidan da katakai tun daga ƙasa har sama, daɓen kuma ya rufe shi da falankai na fir.
16Daga bayan gidan ya gina waɗansu ɗakuna masu kamu ashirin da katakai na sida tun daga ƙasa har sama. Ya gina wani ɗaki can ciki, shi ne wuri mafi tsarki.17Babban ɗakin, wato wuri mai tsarki wanda ke gaban wuri ma fi tsarki, tsawonsa kamu arba'in ne.18Akwai itacen sida a gidan, wanda a ka sassaƙa shi kamar ƙwarya a buɗe da furanni. Dukka sida ne a ciki. Ba bu aikin duwatsu da ake gani a ciki.
19Suleman ya yi wani ɗaki can ciki domin a ajiye akwatin Yahweh a ciki.20Ratar ɗakin na can ciki kamu ashirin ne, faɗinsa kamu ashirin tsawonsa ma kamu ashirin ne. Suleman ya shafe bangayen da zinariya tsantsa bagadin kuma ya rufe shi da itacen sida.
21Suleman ya shafe haikalin da zinariya tsantsa, ɗaki na can ciki kuma ya yi masa dajiya da zinariya, ya shafe gabansa da zinariya.22Ciki dukka ya shafe shi da zinariya har sai da a ka gama haikalin dukka. Bagadi na ɗaki na can ciki kuma ya shafe shi da zinariya.
23Suleman ya yi sifofi biyu na kerubim da itacen zaitun, domin ɗaki na can ciki masu tsawon kamu goma.24Kowanne fiffike na kerub ɗin tsawonsa kamu biyar ne. Ya zama daga ƙarshen wannan fiffike zuwa ƙarshen wancan ya zama kamu goma kenan.25Ɗayan kerub ɗin ma faɗin fiffikensa kamu goma ne. Dukkan kerubim ɗin dai-dai suke da juna ba wanda ya fi wani.26Tsayin kerub ɗaya kamu goma ne haka kuma na ɗayan kerub ɗin.
27Suleman ya ajiye kerubim ɗin a ɗaki na can ciki. Suka buɗe fukafukansu na wannan ya taɓa wancan bango, na wancan kuma ya taɓa wancan bango. Fukafukansu suna taɓa juna a cikin wuri mafi tsarki.28Suleman ya shafe kerubin ɗin da zinariya.
29Bangayen ɗakin an zane su da yatsun kerubim da ganyen dabino da buɗaɗɗun furanni tun daga ciki har waje.30Ƙasan gidan Suleman ya shafe shi da zinariya tun daga ɗakuna na ciki har zuwa na waje.
31Ɗaki na ciki Suleman ya yi masa ƙofofin shiga da itacen zaitun. Dogaran ƙofar da ginshiƙansu suna da aiyanannun sassa guda biyar.32Haka ya yi ƙofofi biyu na itacen zaitun, ya sa a ka zana kerubim da ganyen dabino da furanni buɗaɗɗu. Ya shafe su da zinariya, kuma ya yayyafa zinariya a kan kerubim ɗin da kuma ganyen dabinan.
33Ta haka Suleman ya yi wa haikalin ƙofofin shiga da itacen zaitun da aiyanannun sassa guda huɗu34da ƙofofi biyu na itacen fir. Ɓangare biyu na wannan ƙofa a kan naɗe su haka ma ɓangare biyu na waccan ƙofa a kan naɗe su.35Ya zana kerubim da ganyen dabino da furanni buɗaɗɗu a kansu, ya shafe zanen da zinariya dai-dai wa daida.
36Ya gina farfajiya ta ciki da layika guda uku da sassaƙaƙƙen dutse da ginshiƙai na sida.
37An kafa tushen gidan Yahweh a cikin shekara ta huɗu, a watan zif.38Cikin shekara ta goma sha ɗaya, a watan Bul wato wata na takwas a ka gama gidan, yadda a ke so tsarinsa ya kasance duka. Suleman ya ɗauki shekara bakwai yana ginin haikalin.

7

1Suleman ya ɗauki shekaru goma sha uku yana ginin fadarsa.2Ya gina fada ta jejin Lebanon. Tsawonta kamu ɗari ne, faɗinta hamsin ratarta kuma kamu talatin ne. Fadar an gina ta layi huɗu da ginshiƙai na sida da kalankuwa a kan ginshiƙan.

3An rufe gidan da sida wanda ya kwanta a kan kalankuwoyin. Kalankuwoyin kuma ginshiƙai sun tallabe su.4Akwai kalankuwoyi arba'in da biyar, kowanne layi yana da goma sha biyar. Akwai kalankuwoyi a layuka uku.5Tagogin kuma suna duban junansu a layuka uku, dukkan ƙofofin tsawo da fãɗi bai ɗaya ne an yi masu kalankuwoyi kuma suna duban junansu layi uku.
6Akwai baranda mai tsawon kamu hamsin faɗinta kuma kamu talatin, a gaba an yi kwararo mai ginshiƙai da rufi.
7Suleman ya yi ɗakin kursiyinsa inda zai riƙa yin hukunci, wato ɗakin shari'ar adalci. An rufe dukkan daɓen shi da sida.
8Gidan da Suleman zai zauna kuma yana wani ɓangare na fãdar, an gina shi kamar yadda a ka gina ɗakin shari'ar. Ya yi wani gida kamar haka saboda ɗiyar Fir'auna wadda ya ɗauko ta zama matarsa.
9Gine-ginen an yi masu ado da duwatsu masu tsada waɗanda a ka sassaƙa su dai-dai a ka goge su a kowanne gefe. An yi amfani da duwatsun tun daga tushen ginin har zuwa sama, a waje kuma har zuwa babban ɗakin shari'a.10An kafa tushen gidan da manyan duwatsu masu tsada ratar su kamu takwas ne zuwa goma.
11A sama an yi ado da duwatsu masu tsada waɗanda a ka sassaƙo su dai-dai wa daida, kuma da kalankuwa ta sida.12Katafaren ɗakin taron da ya kewaye fadar ya na da layuka uku na sassaƙaƙƙen dutse da kalankuwa ta sida kamar wanda ya ke cikin haikalin Yahweh da wurin shan iskarsa.
13Sarki Suleman ya aika a ka kawo Huram daga Taya.14Huram ɗan wata gwauruwa ne ta kabilar Naftali, babansa kuma mutumin Taya ne, shi gwani ne a aikin tagulla. Huram yana cike da hikima da fasaha da basirar yin babban aiki da tagulla. Ya zo wurin sarki Suleman domin ya yi wa sarki aikin tagulla.
15Huram ya tsara ginshiƙai biyu na tagulla kowanne tsawonsa kamu goma sha takwas ne kaurinsu kuma kamu goma sha biyu.16Ya kuma yi zankaye biyu da za a sa a kan kowanne ginshiƙi. Tsawon kowanne zanko kamu biyar ne.17Ya yi aikin raga da sarƙa ya yi wa zankayen ado don a sa su can saman ginshiƙan, guda bakwai ya yi domin kowanne zanko.
18Haka Huram ya yi layika biyu na tagulla kewaye da ginshiƙan ya yi wa zankayensu ado.19Zankayen da ke kan ginshiƙan wurin shan iskar ya yi masu ado da furanni, kowanne fure, tsawonsa kamu huɗu.
20Zankayen da ke kan ginshiƙan nan biyu, an yi masu 'yan kwararo-kwararo guda ɗari biyu kewaye da su a can ƙoli.21Ya ɗaga ginshiƙan wurin shan iska na haikali. Ginshiƙi na hannun dama ya ba shi suna Yakin, ginshiƙi na hannun hagu kuma ya ba shi suna Bo'aza.22A bisa ginshiƙan akwai ado mai kama da furanni. Haka aka tsara ginshiƙan.
23Huram ya yi wani teku na zubi, kamu goma daga wannan gefe zuwa wancan. Tsawonsa kamu biyar ne, kewayensa kuma talatin.24A ƙarƙashin tekun na zubi ya yi butoci kamu goma, ya yi su lokacin da ya ke yin tekun na zubi ya yi su tare.
25Ya ɗora tekun a bisa bijimai goma sha biyu, uku suna duban arewa, uku suna duban yamma, uku suna duban kudu, uku kuma suna duban gabas. aka ɗora "Tekun" a kansu, dukkan su cibiyoyinsu suna daga ciki.26Kaurin tekun kamar tafin hannu ya ke, an yi masa baki kamar na ƙoƙo, kamar fure ya na sheƙi. Tekun ya na ɗaukar ruwa garwa dubu biyu.
27Huram ya yi diraku goma na tagulla. Ratar kowacce dirka kamu huɗu ne, faɗinta ma kamu huɗu, tsawonta kuma kamu uku.28Aikin dirakun shi ne, suna da mahaɗai a tsakaninsu,29kan dirakun da mahaɗarsu akwai zakuna da bijimai da kerubim. A saman zakunan da bijiman akwai zãnen furanni.
30Kowacce dirka ta na da ƙafafu huɗu na tagulla, kusurwoyinta huɗu suna da matokarai saboda bangajin. Matokaran an yi su da zanen furanni a gefen kowacce ɗaya.31Bakinsu buɗe ya ke kamar kwano, faɗinsa kamu ɗaya da rabi ne, yana da kambi kamu ɗaya. A bakin su akwai zane-zane, kuma gefensu yana da tsawo da fãɗa bai ɗaya ba zagayayye ya ke ba.
32Ƙafafunsu huɗu suna daga ƙarƙashinsu, abin da ya riƙe su kuma yana cikin dirkar. Tsayin gargaren kamu ɗaya da rabi ne.33Ƙafafunsu gargare kama da gargaren karusa. Abubuwan da suke riƙe da su da wayoyinsu ƙarfe ne na zubi.
34An yi wurin kamawa huɗu ga kowacce dirka waɗanda suke liƙe a jikinsu.35a kan kowacce dirka an yi kambi rabin zurfinsa rabin kamu. Saman inda ta tsaya da gefenta haɗe su ke.
36Jikin matokaran da gefensu, Huram ya zana zakuna da kerubim da ganyen dabino ya rufe inda ƙofofi suke ya zagaye su da furanni.37Yadda ya yi matokaran dukkan su zubinsu iri ɗaya ne girman su da tsarin su dukka ɗaya ne.
38Huram ya yi bangazai goma, kowannen su zai ɗauki ruwa garwa goma. Kowanne bangaji kamu huɗu ne kuma ya sa bangaji ɗaya a bisa matokaran su goma.39Ya yi matokarai biyar daga kudu suna fuskantar haikalin, biyar kuma daga arewa su masu na fuskantar haikalin. Ya sa "Tekun" a kusurwar gabas, yana fuskantar kudu da haikalin.
40Huram ya yi bangazai da moɗa da tasoshin yayyafawa. Daga nan ya gama dukkan aikin da zai yi wa Sarki Suleman cikin haikalin Yahweh.41Ginshiƙan biyu suna kama da zankayen da suke kan waɗancan ginshiƙan guda biyu. Ya yi zane guda biyu kamar tasoshi ya sa su domin su yi wa zankayen ado.
42Ya yi zãne-zãne ɗari huɗu saboda sahu biyu na kayan adon da ya yi (layi biyu na zãne-zãne domin su rufe zankayen da suke a kan ginshiƙan guda biyu da);43matokaran su goma da bangajin nan guda goma na bisa matokaran.
44Ya yi tekun da bajiman nan goma sha biyu da ke ƙarƙashinsa;45da tukwanen da moɗayen da bangazayen da dukkan sauran kayan aikin. Huram ya yi wa Sarki Suleman, su saboda haikalin Yahweh.
46Sarki ya sa a zuba su filin Yodan a ƙasar yumɓu da ke tsakanin Sokot da Zaretan.47Suleman bai auna kayan aikin ba domin yawansu ya fi gaban aunawa, nauyin tagullar kuma ba za a iya auna su ba.
48Dukkan kayan da ke cikin haikalin Yahweh Suleman ya yi su da zinariya: bagadi na zinariya da teburi wanda za a ajiye keɓaɓɓiyar gurasa.49Sandunan ajiye fitilu, biyar a hannun dama biyar kuma a hannun hagu, a gaba cikin ɗaki na can ciki an yi su da zinariya tsantsa da furannin da fitilun da yatsun dukka na zinariya ne.
50‌Kofinan da abubuwan kashe fitila da cokula da bangazaye da abubuwan ƙona turare dukka an yi su da zinariya tsantsa. Sakatu na ɗaki na can ciki wato wuri mafi tsarki da ƙofofin babban ɗakin taro na haikali dukka da zinariya aka yi su.
51Da haka aka gama dukkan aikin da Sarki Suleman ya yi domin gidan Yahweh. Sai Suleman ya kawo abubuwan da mahaifinsa Dauda ya keɓe, azurfa da zinariya da kayan ɗaki ya sa su a cikin ɗakin ajiya a gidan Yahweh.

8

1Sa'an nan Suleman ya tattara dukkan dattawan Isra'ila da shugabannin kabilu da shugabannin iyalai na mutanen Isra'ila a gabansa a Yerusalem, domin ya kawo akwatin alƙawarin Yahweh daga birnin Dauda wato Sihiyona.2Dukkan jama'ar Isra'ila suka taru a gaban Suleman a wurin liyafar, a cikin watan Itanim, wato wata na bakwai.

3Dukkan dattawan Isra'ila da firistoci suka ɗauki akwatin.4Suka kawo akwatin Yahweh da rumfar taruwa da dukkan kaya masu tsarki da suke cikin rumfar. Firistoci da Lebiyawa ne suka kawo waɗannan kaya.5Sarki Suleman tare da dukkan taron Isra'ila suka zo gaban akwatin, suna miƙa hadayar tumaki da bijimai waɗanda ba su ƙidayuwa.
6Firistoci suka kawo akwati na alƙawarin Yahweh suka sa shi a wurinsa, cikin ɗaki na can cikin gidan, wato wuri mafi tsarki a ƙarƙashin fukafukan kerubim.7Gama fukafukan kerubim ɗin sun kai wurin da akwatin ya ke, kuma sun rufe akwatin tare da sandunan da a ke ɗaukar sa.8Sandunan suna da tsawo sosai har ana iya ganin su daga wuri mafi tsarki a gaban ɗaki na can ciki, amma ba za a iya ganin su daga waje ba. Suna nan har zuwa yau.
9Babu kome a cikin akwatin sai dai allunan nan na dutse da Musa ya sa ciki a Horeb, sa'ad da Yahweh ya yi alƙawari da mutanen Isra'ila lokacin da suka fito daga ƙasar Masar.10Ya zama lokacin da firistocin suka fito daga wuri mai tsarki sai girgije ya cika haikalin Yahweh.11Firistoci ba su iya tsayawa su yi hidima ba saboda girgijen. Gama darajar Yahweh ta cika gidansa.
12Sa'an nan Suleman yace, "Yahweh ya ce zai zauna a cikin baƙin duhu,13Amma na gina maka wuri mai ƙawa, wurin da za ka zauna har abada."
14Sa'an nan sarki ya juya ya sa wa taron jama'ar Isra'ila albarka sa'ad da jama'ar Isra'ila suke a tsaye.15Ya ce, "Bari a yi yabo ga Yahweh Allah na Isra'ila wanda ya yi magana da mahaifina Dauda, kuma ya cika da hannunsa, cewa,16'Tun ranar da na kawo Isra'ila jama'ata daga Masar, ban zaɓi birni da zan gina gida domin in sa sunana a ciki ba. Na dai zaɓi Dauda ya yi mulkin jama'ata Isra'ila.
17Yana dai cikin zuciyar Dauda mahaifina ya gina gida domin Yahweh Allah na Isra'ila.18Amma Yahweh ya ce da Dauda mahaifina, 'Ya yi kyau da ka ke da tunani a zucyarka domin ka gina ma ni gida.19Duk da haka ba za ka gina gidan ba, sai dai ɗanka wanda za a haifa ma ka shi ne zai gina gida domin sunana.'
20Yahweh ya cika maganar da ya faɗi gama na taso a matsayin mahaifina Dauda, kuma ina zaune a kan kursiyi na mulkin Isra'ila kamar yadda Yahweh ya yi alƙawari. Na gina gida domin sunan Yahweh Allah na Isra'ila.21Na yi wa akwati wuri wanda a cikin sa alƙawarin Yahweh ya ke, wanda ya yi wa ubanninmu lokacin da ya fito da su daga ƙasar Masar."
22Suleman ya tsaya a gaban akwatin Yahweh, gaban taron jama'ar Isra'ila ya buɗe hannuwansa zuwa sama.23Ya ce, "Yahweh, Allah na Isra'ila, babu wani Allah kamar ka a bisa cikin sama ko a nan ƙasa wanda ke riƙe alƙawarinsa da aminci zuwa ga bayinka waɗanda suke tafiya a gabanka da dukkan zuciyarsu;24kai wanda ya riƙe alƙawarin da ka yi wa bawanka Dauda mahaifina. I, ka faɗi da bakinka kuma ka cika da hannunka, kamar yadda ya ke a yau.
25To yanzu dai, Yahweh, Allah na Isra'ila, ka cika alƙawarin da ka yi wa bawanka mahaifina Dauda, sa'ad da ka ce, 'Ba za ka rasa mutum wanda zai zauna a bisa kursiyin Isra'ila ba, idan dai zuriyarka za su yi hankali su yi tafiya a gabana kamar yadda ka yi tafiya a gabana.'26To yanzu dai Allah na Isra'ila, ina roƙon alƙawarin da ka yi wa bawanka Dauda mahaifina, ya zama gaske.
27Amma gaskiya ne Allah zai zauna a ƙasa? Da ya ke dukkan duniya da sama ba za su iya riƙe ka ba, balle fa wannan haikalin da na gina!28Duk da haka, Yahweh, Allahna, ka yarda da wannan addu'a da roƙo na bawanka; ka saurari kuka da addu'ar da bawanka ya yi a gabanka yau.
29Bari idanunka su zama a buɗe zuwa wannan haikali dare da rana, wanda ka yi magana a kansa cewa, 'Sunana da kasancewata za su zauna a can'- domin ka ji addu'o'in da bawanka zai yi a wurin nan.30Ka ji roƙon bawanka da na jama'ar Isra'ila sa'ad da muke yin addu'a a wannan wuri. I, ka ji daga wurin da ka ke, daga sama, kuma sa'ad da ka ji, ka yi gafara.
31Idan wani mutum ya yi wa maƙwabcinsa zunubi, aka nemi da ya rantse da alƙawari, idan ya zo ya yi rantsuwa da alƙawari a gaban bagadinka a wannan gida,32ka ji daga sama ka yi wa bayinka hukunci, ka hukunta mai laifi ka sa abin da ya yi ya koma kansa, ka baratar da mai adalci ka yi masa sakamako saboda adalcinsa.
33Idan abokin gãba ya yi nasara a kan bayinka jama'ar Isra'ila saboda suka yi maka zunubi, idan sun juyo sun kira sunanka a wnnan haikali, suka yi addu'a suka roƙi gafara -34idan ka yarda, ka ji daga sama ka gafarta zunubin jama'arka Isra'ila; ka dawo da su ƙasar da ka bayar ga kakanninsu.
35Idan sama ta rufe babu ruwa, saboda mutanenka sun yi ma ka zunubi - idan su ka yi addu'a su na fuskantar wannan wuri, su ka kira sunanka kuma su ka juwo daga zunubinsu, bayan ka wahalshe su -36sai ka ji daga sama ka gafarta zunubin bayinka da na mutanen Isra'ila, sa'ad da ka koya masu hanyoyi masu kyau da ya kamata su bi. Ka aiko da ruwa a ƙasar da ka ba mutanenka gãdo.
37A misali yunwa ta zo ƙasar ko cuta ko annobar gonaki ko cutar fatar jiki, ko fãri ko tsutsotsi, a misali kuma a ce abokin găba zai kawo hari a ƙasarsu, ko annoba ko wani ciwo -38A misali kuma wani ya yi addu'a ko roƙo ko dukkan jama'arka Isra'ila - kowanne ɗayansu yana sane da annobar a cikin zuciyarsa, idan suka tada hannuwansu zuwa wannan haikali.
39Sai ka ji daga sama inda ka ke zaune, ka yi gafara kuma ka sãka wa kowanne mutum bisa ga dukkan abin da ya yi; ka san zucyarsa saboda kai kaɗai ne ka san dukkan zukatan mutane.40Yi haka domin su ji tsoron ka muddin suna zaune a ƙasar da ka bayar ga kakanninmu.
41Har yanzu, game da baƙo wanda ba na cikin jama'arka Isra'ila ba ne: idan ya zo daga wuri mai nisa saboda sunanka -42gama za su ji labarin sunanka mai girma da hannunka mai iko da hannunka wanda ka tayar, idan ya yi addu'a yana fuskantar wannan haikali,43idan ka yarda, ka ji daga sama inda ka ke zaune, ka yi bisa ga abin da baƙon ya roƙe ka. Ka yi haka domin dukkan mutanen duniya su san ka su ji tsoron sunanka, kamar yadda jama'arka Isra'ila suke yi. Ka yi haka domin su san da sunanka a ke kiran wannan gida da na gina.
44Idan jama'arka suka je yaƙi da abokan gaba, ta kowacce hanya ka aike su, Yahweh, idan suka yi addu'a suna fuskantar wannan birni wanda ka zaɓa da wannan gida da na gina domin sunanka.45Sai ka ji addu'arsu da roƙonsu daga sama ka yi taimako.
46A misali idan suka yi maka zunubi, tun da ya ke ba wanda ba ya yin zunubi, a misali idan ka yi fushi da su, ka bashe su ga abokin găba, abokin găba ya kwashe su zuwa ƙasarsu, ko da nesa ko kusa.47A misali idan suka gane suna cikin ƙasar bauta, a misali idan suka tuba suka roƙi tagomashi a wurin ka daga ƙasar waɗanda suka bautar da su. A misali idan suka ce, 'Mun yi wauta mun yi zunubi. Mun yi aikin mugunta.'
48Amisali idan suka juwo gare ka da dukkan zuciyarsu da dukkan ransu a cikin ƙasar abokan gãbarsu waɗanda suka kwashe su, idan suka yi addu'a suna fuskantar ƙasarsu, suna fuskantar birnin da ka zaɓa da wannan gida da na gina domin sunanka.
49Sai ka ji addu'arsu da roƙonsu na neman taimako daga sama inda ka ke, ka dai-daita al'muransu.50Ka gafartawa mutanenka zunubin da suka yi maka da dukkan zunubansu da suka ƙetare dokokinka. Ka ji tausayin mutanenka a gaban abokan gãbarsu, domin abokan găbarsu su ji tausayin mutanenka.
51Su mutanenka ne da ka zaɓa, waɗanda ka kuɓutar daga Masar kamar daga cikin tanderu inda a ke narkar da ƙarfe.52Ina roƙon idanunka su buɗe ga roƙon bawanka da roƙe-roƙen mutanenka Isra'ila, ka ji su daga ko'ina suka yi kuka gare ka.53Gama ka keɓe su daga dukkan mutanen duniya su zama na ka, su kuma karɓi alƙawuranka, Yahweh Ubangiji, kamar yadda ka bayyana ta wurin bawanka Musa sa'ad da ka kawo ubanninmu daga Masar, Ubangiji Yahweh."
54Haka ya zama sa'ad da Suleman ya gama yin addu'a da dukkan roƙon da zai yi zuwa ga Yahweh, ya tashi daga gaban bagadin Yahweh, daga yin durƙusonsa a kan guiwoyinsa da ta da hannuwansa zuwa sama.55Ya miƙe ya sa wa dukkan taron jama'ar Isra'ila albarka da babbar murya, cewa,56yabo ga Yahweh wanda ya ba mutanensa Isra'ila hutawa, ya cika alƙawuransa. Ko kalma ɗaya ba a rasa ba cikin dukkan alƙawura masu kyau da Yahweh ya yi da bawansa Musa.
57Yahweh ya kasance tare da mu, kamar yadda ya kasance tare da kakanninmu, kada ya bar mu ko ya yashe mu,58ya sa zuciyarmu ta manne masa, mu rayu cikin dokokinsa da ka'idodinsa da farillansa, waɗanda ya umurci ubanninmu.
59Bari waɗannan maganganu da na faɗi, na yi roƙo ga Yahweh, su zauna a kusa da Yahweh Allahna, dare da rana, domin ya yi taimako cikin al'amuran bawansa da al'amuran jama'arsa Isra'ila a kowacce rana;60domin dukkan mutanen duniya su sani Yahweh shi ne Allah kuma ba bu wani Allah!61Saboda haka zuciyarku ta yi aminci ga Yahweh Allanmu, ku kiyaye farillansa da dokokinsa, kamar a yau."
62Sai sarki tare da dukkan Isra'ila suka miƙa hadayu ga Yahweh.63Suleman ya miƙa baye-baye na zumunci waɗanda ya yi wa Yahweh: bijimai dubu ashirin da biyu da tumaki 120,000. Haka sarki da dukkan Isra'ila su ka keɓe gidan Yahweh.
64A wannan ranar ne kuma sarki ya keɓe filin da ke tsakiya a gaban haikalin Yahweh. Gama a nan ne sarki ya miƙa baye-baye na ƙonawa, baye-baye na hatsi da kitsen baye-baye na zumunta, saboda bagadin da ya ke gaban Yahweh bai kai girman da zai ɗauki baikon ba, wato baye-baye na hatsi da kitsen baye-baye na zumunta.
65Haka sarki ya yi liyafa a wannan lokaci da dukkan Isra'ila tare da shi, babban taro. Tun daga Lebo Hamat har zuwa iyakar Masar, suna gaban Ubangiji Allah kwana bakwai da waɗansu kwana bakwai kuma, wato kwana goma sha huɗu kenan dukka.66A kan rana ta takwas ya sallami mutanen, suka sa wa sarki albarka kowanne ya tafi gidansa da murna da farinciki saboda abubuwa masu kyau waɗanda Yahweh ya yi wa Dauda bawansa, da Isra'ila, mutanensa.

9

1Bayan da Suleman ya gama ginin gidan Yahweh da fădar sarki, kuma bayan da ya gama dukkan abubuwan da ya ke so ya yi,2Sai Yahweh ya bayyana ga Suleman sau na biyu, kamar yadda ya bayyana gare shi a Gibiyon.

3Daga nan Yahweh ya ce da shi, "Na ji addu'arka da roƙon da ka yi zuwa gare ni. Na keɓe wannan gida, wanda ka gina, domin kaina, in sa sunana a wurin. Idanuna da zuciyata za su kasance a wurin kowanne lokaci.
4A gare ka kuma, idan ka yi tafiya a gabana kamar yadda Dauda mahaifinka ya yi cikin aminci da sahihancin zuciya, ka na yin biyayya ga dukkan abin da na ummurce ka ka na kiyaye farillaina da shari'una,5zan tabbatar da mulkinka a kan Isra'ila har abada, kamar yadda na yi wa Dauda mahaifinka alƙawari, cewa, 'Ba za a taɓa rasa zuriyarka a kan kursiyin Isra'ila ba.'
6Amma idan ka fanɗare, ko kai, ko 'ya'yanka, ba ku kiyaye dokokina da farillaina waɗanda na shimfiɗa a gabanka ba, idan ku ka je ku ka bauta wa waɗansu alloli ku ka russana masu,7zan kawar da Isra'ila daga ƙasar da na ba su, wannan gida kuma wanda na keɓe domin sunana, zan kawar da fuskata daga gare shi, Isra'ila kuma za su zama misali da abin ba'a da abin raini ga dukkan mutane.
8Wannan haikali kuma zai zama tarin juji, dukkan wanda ya wuce ta kusa da shi zai kaɗu ya yi ajiyar zuciya. Zai yi tambaya haka, 'Me ya sa Yahweh ya yi haka ga wannan ƙasa da wannan gida?'9Waɗansu za su amsa da cewa, 'Saboda sun watsar da Yahweh Allahnsu, wanda ya fito da kakanninsu daga ƙasar Masar, sun koma ga waɗansu alloli sun russana masu sun yi masu sujada. Shi ya sa Yahweh ya auko masu da wannan masifar.'"
10Ya zama shekaru ashirin bayan da Suleman ya gama gine-ginen nan biyu, wato haikalin Yahweh da fãdar sarki.11Hiram sarkin Taya ya tanadawa Suleman sida da itatuwan fir da zinariya da dukkan abin da Suleman ya bukata-sai sarki Suleman ya ba shi birane ashirin cikin ƙasar Galili.
12Sai Hiram ya zo daga Taya domin ya ga biranen da Suleman ya ba shi, amma ba su gamshe shi ba.13Hiram yace, "Waɗanne irin birane ne waɗannan da ka ba ni, ɗan'uwana?" Hiram ya ce da su ƙasar Kabul, haka a ke kiran su har yau.14Dã ma Hiram ya aika wa sarki zinariya awo 120.
15Wannan shi ne dalilin aikin dole wanda sarki Suleman ya sa a yi: wato a gina haikalin Yahweh da fãdarsa, kuma a gina Millo da garun Yerusalem da kuma kariya ta Hazor da Maggido da Gezer.16Fir'auna sarkin Masar ya je ya kama Gezer. Ya ƙone ta ya karkashe Kan'aniyawan cikin birnin. Sai Fir'auna ya ba ɗiyarsa matar Suleman, biranen a matsayin kyautar aure.
17Haka Suleman ya sake gina Gezer da Bet Horon ta gangare,18da Ba'alat da Tamar a ƙasar Yahuda cikin jeji,19da biranen da ya ke da su na ajiya da na karusansa da na mahaya dawakinsa da dukkan abin da ya yi sha'awar ginawa a Yerusalem domin jin daɗinsa a Lebanon da dukkan ƙasashen da su ke ƙarƙashin mulkinsa.
20Game da mutanen da su ka rage na wajen Amoriyawa da Hittiyawa da Ferizziyawa da Hiwiyawa da Yebusiyawa waɗanda ba sa cikin mutanen Isra'ila ba,21da zuriyarsu waɗanda mutanen Isra'ila ba su iya hallakawa duka ba, Suleman ya sa su ka zama masu aikin tilas haka kuwa su ke har yau.
22Amma Suleman bai sa mutanen Isra'ila aikin tilas ba. Maimakon haka sai ya sa suka zama sojojinsa da bayinsa da jami'ansa da jami'an karusansa da mahaya dawakinsa.
23Suleman ya na da jami'ai masu hidimar lura da masu duba aiki, yawan su shi ne 550, su ne suke lura da mutanen da suke yin aiki.
24Ɗiyar Fir'auna ta tashi daga birnin Dauda ta koma gidan da Suleman da ya gina mata, sa'an nan Suleman ya gina Millo.
25A shekara sau uku Suleman ya ke miƙa baye-baye na ƙonawa da baye-baye na salama a kan bagadin da ya gina wa Yahweh, a gaban Yahweh ya ke ƙona su da turare. Ya gama haikalin yanzu yana amfani da shi.
26Sarki Suleman kuma ya yi tashar jiragen ruwa a Eziyon Geber wadda ta ke kusa da Elat a bakin Jan Teku a ƙasar Idom.27Hiram ya aiko bayinsa zuwa tashar Suleman, masu tuƙin jirgi waɗanda suka saba da teku tare da bayin Suleman.28Suka je Ofir da bayin Suleman. Suka kawowa Suleman zinariya awo 420 daga can.

10

1Sa'ad da sarauniyar Sheba ta ji labarin Suleman ya zama sananne game da sunan Yahweh, sai ta zo ta gwada shi da tambayoyi masu wuya.2Ta zo Yerusalem da raƙuma da yawa, da raƙuman da aka ɗorowa kayan yaji da zinariya mai yawa da duwatsu masu daraja da yawa. Sa'ad da ta zo sai ta gayawa Suleman dukkan abin da ke cikin zuciyarta.

3Suleman ya amsa dukkan tambayoyinta. Ba wani abu da ta tambaya wanda Suleman bai ba da amsarsa ba.4Sa'ad da sarauniyar Sheba ta ga dukkan hikimar Suleman da fãdar da ya gina,5da abincin da ke kan teburinsa da wurin da bayinsa suke zama da ayyukan da bayinsa suke yi da tufafinsu, da masu yi ma sa hidima da yadda ya ke miƙa baye-baye na ƙonawa, sai ta zama ba ta da sauran ƙarfi.
6Ta ce da sarki, "Rahoton da na ji a ƙasata game da maganarka da hikimarka gaskiya ne.7Ban gaskata da abin da na ji ba sai da na zo nan, yanzu idanuna sun gani. Ko rabin hikimarka da wadatarka ma ba a gaya mani ba! Sunanka ya wuce abin da na ji.
8Matanka masu albarka ne, bayinka waɗanda suke tsayawa a gabanka kullum, masu albarka ne saboda suna jin hikimarka.9Yabo ga Yahweh Allahnka wanda ya yi farinciki da kai ya sa ka a bisa kursiyin Isra'ila. Saboda Yahweh ya ƙaunaci Isra'ila har abada ya sa ka zama sarki domin ka yi masu hukunci da adalci!"
10Ta ba sarki awo 120 na zinariya da kayan yaji da yawa da duwatsu masu daraja. Ba a ƙara ba sarki Suleman kayan yaji masu yawa fiye da wanda sarauniyar Sheba ta ba shi ba.
11Jiragen ruwa na Hiram da suka kawo zinariya daga Ofir, daga Ofir ɗin kuma sun kawo itacen almug mai yawa da duwatsu masu daraja.12Sarkin ya yi ginshiƙai na itacen almug a haikalin Yahweh da fãdar sarki, kuma ya yi wa mawaƙa molaye da girayu. Ba a ƙara ganin itacen almug da yawa haka ba har zuwa yau.
13Sarki Suleman ya ba sarauniyar Sheba dukkan abin da ta nuna sha'awa a kai da dukkan abin da ta roƙa, ƙari a kan kyautar da ya riga ya ba ta saboda karamci. Sai ta koma ƙasarta tare da bayinta.
14Nauyin zinariyar da ta zo wa Suleman a cikin shekara ɗaya awo 666 ne,15ban da zinariyar da "yan kasuwa da fatake suka kawo. Dukkan sarakunan Arebiya da hakiman ƙasar masu ka kawo wa Suleman zinariya da azurfa.
16Sarki Suleman ya yi manyan garkuwoyi ɗari biyu na gogaggiyar zinariya. Kowaccen su an yi ta da awo ɗari shida na zinariya.17Ya kuma yi waɗansu garkuwoyi ɗari uku na gogaggiyar zinariya, awon zinariya uku suka shiga kowacce garkuwa; sarki ya sa su can cikin fadar da ta ke a jejin Lebanon.
18Kuma sarki ya yi wani babban dakalin mulki na hauren giwa ya shafe shi da zinariya mafi kyau.19Dakalin yana da matakalai shida, bayan shi kuma shan ƙwai ne a can sama. Kowannen su yana da wurin ajiye hannu a gefe, akwai zakuna biyu a tsaye gefen wurin ajiye hannun.20Zakuna goma sha biyu suna tsaye a kan matakalun, ɗaya a kan kowacce matakala. Babu wata masarautar da take da dakali kamar sa.
21Dukkan kofinan sha na sarki Suleman na zinariya ne, dukkan kofinan sha da suke fãdar da ke cikin jejin Lebanon na zinariya ne tsantsa. Ba na azurfa ko ɗaya domin a zamanin Suleman azurfa ba ta da daraja.22Sarki ya na da jiragen ruwa masu yawo a kan teku, tare da jiragen Hiram. Sau ɗaya a cikin shekara uku jiragen ruwan sukan kawo zinariya da azurfa da hauren giwa da buka da ɗawisu masu daraja.
23Sarki Suleman ya fi dukkan sarakunan duniya arziki da hikima.24Kowa da kowa a duniya suna so su zo wurin Suleman domin su ji hikimar da Yahweh ya sa cikin zuciyarsa.25Waɗanda ke zuwa su na kawo haraji, na santulan azurfa da zinariya, da kayan sawa da sulke da kayan yaji da dawakai da alfadarai, shekara biye da shekara.
26Suleman ya tara karusai da mahaya dawaki. Ya na da karusai 1400 da mahaya dawaki dubu goma sha biyu waɗanda ya ajiye su a biranen da a ka ajiye karusai shi kansa kuwa ya na cikin Yerusalem.27Sarki ya na da azurfa a Yerusalem kamar yawan duwatsun da suke a doron ƙasa. Yana da itatuwan sida da yawa kamar yadda itatuwan ɓaure suke a cikin fadama.
28Suleman ya na da dawakai da aka kawo daga Masar da Kilikiya. Abokan cinikin sarki sukan saye su garke-garke kowanne garke bisa ga farashinsa.29Akan sayo karusai daga Masar kowacce akan awo ɗari shida na azurfa, dawaki kuma akan 150 kowanne. Akan sayar da wasu da yawa daga cikin su ga sarakunan Hittiyawa da Siriya.

11

1Yanzu sarki Suleman ya kaunaci baƙin mata: ɗiyar Fir'auna, da matan Mowabawa, da Ammonawa da Idomawa da Sidoniyawa da Hittiyawa.2Su na daga al'ummai waɗanda Yahweh ya ce da mutanen Isra'ila, "Ba za ku shiga cikinsu ba da aure, ko su zo cikinku, domin lallai za su juyar da zukatanku ga allolinsu." Amma duk da wannan Suleman kuwa ya ƙaunaci waɗannan mata.

3Suleman ya na da gimbiyoyin mata ɗari bakwai da kuma ƙwaraƙwarai ɗari uku. Matayensa su ka juyar da zuciyarsa.4Gama sa'ad da Suleman ya tsufa, sai matansa su ka juyar da zuciyarsa zuwa bin wasu alloli; bai miƙa dukkan zuciyarsa ga Yahweh Allahnsa ba, kamar zuciyar Dauda mahaifinsa.
5Gama Suleman ya bi Ashtoret, gunkin Sidoniyawa, ya kuma bi Molek, wato gunkin Ammonawa.6Suleman ya yi abin da ke mugu a fuskar Yahweh; bai bi Yahweh da zuciya ɗaya ba, ba kamar yadda mahaifinsa Dauda ya yi ba.
7Sai Suleman ya gina masujadai domin Kemosh, kyamattacen gunkin Mowab, akan dutsen gabashin Yerusalem, da kuma domin Molek, da kyamataccen gunkin mutanen Amonawa.8Ya kuma gina masujadai domin dukkan baƙin mata, waɗanda su ke ƙona turare da hadayu ga allolinsu.
9Yahweh kuwa ya yi fushi da Suleman, domin zuciyarsa ta rabu daga gare shi, Allah na Isra'ila, ko da ya ke ya bayyana a gare shi sau biyu,10ya kuma umarce shi akan wannan abu, da kada ya bi wasu allolin. Amma bai yi biyayya da wannan umarni na Yahweh ba.
11Saboda haka Yahweh ya ce da Suleman, "Domin ka yi wannan ka kuma ƙi kiyaye alƙawari da ka'idodina waɗanda na umarceka, hakika zan tsaga mulkin daga gare ka in ba baranka.12Amma, saboda mahaifinka Dauda, ba zan yi ba a lokacin rayuwarka, amma zan tsaga ta daga hannun ɗanka.13Duk da haka ba zan ƙwace dukkan mulkin ba, zan ba kabila ɗaya ga ɗanka, saboda bawana Dauda, don kuma Yerusalem, wanda na zaɓa."
14Sai Yahweh ya ta da abokin gãba ga Suleman, Hadad Ba'idome. Shi kuma daga iyalin sarautar Idom ne.15Gama sa'ad da Dauda yana cikin Idom, Yowab shugaban sojoji ya tafi don ya bizne matattu, kowanne mutum wanda aka kashe a Idom.16Yowab da dukkan Isra'ila su ka tsaya a Idom wata shida har sai da ya kashe mazajen Idom.17Amma an ɗauki Hadad tare da wasu Idomawa ta wurin bayin mahaifinsa zuwa Masar, tun lokacin da Hadad yana karamin yaro.
18Su ka bar Madayana su ka zo Faran, daga nan su ka ɗauki mutane tare da su zuwa Masar, wurin Fir'auna sarkin Masar, wanda ya ba shi gida da kuma ƙasa da abinci.19Hadad kuwa ya sami tagomashi ƙwarai a fuskar Fir'auna, saboda haka Fir'auna ya bashi mata, ƙanwar matarsa, wato ƙanwar Tafenes sarauniya.
20'Yar'uwar Tafenes ta haifa wa Hadad ɗa. Suka sa masa suna Genubat. Tafenes ta yi renon sa a fadar. Genubat ya zauna a fadar Fir'auna a cikin yaran Fir'auna.21A lokacin da ya ke a Masar, Hadad ya ji labari Dauda ya rasu aka kuma rufe shi tare da kakanninsa, Yowab shugaban sojoji kuma ya mutu, sai Hadad ya cewa Fir'auna, "Ka yardar mani in tashi, in koma ƙasata."22Sai Fir'auna ya ce masa, "Amma me ka rasa a nan har da ka ke neman komawa ƙasarka?" Hadad ya amsa, "Ba bu kome, idan ka yarda bar ni in koma.
23Allah kuma ya ta da wani abokin gãba ga Suleman, Rezon ɗan Eliyada, wanda ya zo daga wurin maigidansa Hadadezar sarkin Zobah.24Rezon ya tattaro wa kansa mutane har ya zama shugaba akan kananan mayaƙa, bayan da Dauda ya ci nasara akan mutanen Zobah. Rezo ya mulki Damaskus.25Ya zama abokin gãbar Isra'ila dukkan kwanakin Suleman, tare da wahalar da Hadad ya kawo. Rezon ya ƙi mutanen Isra'ila ƙwarai, ya yi mulkin Aram.
26Sai Yerobowam ɗan Nebat, Ba'ifraime na Zeredan, ma'aikacin Suleman ne, wanda sunan mahaifiyarsa Zeruya, wadda mijinta ya rasu, shi ma ya tayar wa sarki.27Dalilin da ya sa ya tayar wa sarki shi ne domin Suleman ya gina masujada a Millo ya kuma gyara garun birnin Dauda mahaifinsa.
28Yerobowam ƙaƙƙarfan mutum mai fasaha. Suleman ya ga saurayi ne mai himma, sai ya sa shi shugabanci akan dukkan aikin gidan Yosef.29A wanan lokacin, sai Yerobowam ya fita daga Yerusalem, annabi Ahijah mutumin Shilo ya same shi a hanya.30Yanzu kuwa Ahijah ya na saye da sabuwar riga tare da mutune biyu kaɗai a filin. Sai Ahijah ya kama sabuwar rigar da ya sa, ya kyakketa kashi goma sha biyu.
31Ya cewa Yerobowam, "Ɗauki kyalle goma, gama haka Yahweh, Allahn Isra'ila, ya faɗa, 'Duba, zan yaga mulkin daga hannun Suleman zan kuma ba da kabilu goma a gare ka32(amma Suleman zai sami kabila ɗaya, saboda bawana Dauda, ɗaya kuma saboda Yerusalem - birnin da na zaɓa daga cikin dukkan kabilan Isra'ila),33domin sun rabu da ni su na bauta wa Ashtoret gunkiyar Sidoniyawa, Kemosh allahn Mowab, da Milkon allahn mutanen Ammonawa. Ba su yi tafiya a hanyoyina ba, ko su yi abin da ke dai-dai a idanuna da kiyaye dokokina da ka'idodina, kamar yadda Dauda mahaifinsa ya yi.
34Duk da haka ba zan ɗauke dukkan mulkin daga hannun Suleman ba. A maimakon haka zan sa shi ya yi mulki dukkan kwanakin rayuwarsa, saboda bawana Dauda wanda na zaɓa, wanda ya kiyaye umarnina da dokokina.35Amma zan ɗauke mulkin daga hannun ɗansa, zan ba da shi gare ka, kabilu goma.36Zan ba da kabila ɗaya ga ɗan Suleman, saboda bawana Dauda wanda kullum yana riƙe fitila a gabana a Yerusalem, birnin da na zaɓa in sa sunana.
37Zan ɗauke ka, za ka yi mulki ka cika dukkan buƙatarka, kuma za ka zama sarki akan Isra'ila,38Idan za ka saurari dukkan abin da zan umarce ka, idan kuma ka bi hanyata ka yi abin da ke dai-dai a idanuna, ka kiyaye dokokina da umarnina, kamar yadda Dauda bawana ya yi, sai in kasance tare da kai zan sa gidanka ya kahu, kamar yadda na sa gidan Dauda, zan ba da Isra'ila a gare ka.39Zan hori zuriyar Dauda, amma ba har abada ba."
40Suleman kuwa ya yi ƙoƙarin kashe Yerobowam. Amma Yerobowam ya tashi ya tsere zuwa Masar, wurin Shishak sarkin Masar, ya zauna a can har mutuwar Suleman.
41Kamar sauran abubuwa game da Suleman, dukkan abin da ya yi da hikimarsa ba a rubuta su a littafin ayyukan Suleman ba?42Suleman ya yi mulki a Yerusalem akan dukkan Isra'ila har shekaru arba'in.43Ya mutu tare da kakaninsa kuma aka bizne shi a birnin Dauda mahaifinsa. Rehobowam ɗansa ya zama sarki a gurbin mahaifinsa.

12

1Rehobowam ya tafi Shekem, domin dukkan Isra'ila sun tafi Shekem su maida shi sarki.2Ya zamana sa'ad da Yerobowam ɗan Nebat ya ji wannan (domin shi yana Masar, inda, ya gudu daga gaban sarki Suleman), don Yerobowam ya na zaune a Masar.

3Sai su ka aika a kirawo shi, Yerobowam tare da dukkan taron mutanen Isra'ila suka zo suka ce da Rehobowam,4'"Mahaifinka ya nawaita mana. Yanzu sai ka rage mana wahalar aikin da tsohonka ya nawaita a kanmu, mu kuwa za mu bauta maka."5Yerobowam ya ce da su, "Ku tafi har nan da kwana uku, sai bayan kwana uku ku dawo wuri na." Sai mutanen su ka tafi.
6Sarki Rehobowam kuwa ya yi shawara tare da dattawa waɗanda suka tsaya tare da Suleman mahaifinsa a lokacin da ya ke da rai, sai ya ce masu, "Wacce shawara za ku ba ni don in amsa wa mutanen nan?"7Su ka yi magana da shi, suka ce, "Idan za ka zama bara yau ga waɗannan mutane sai ka bauta masu, ka kuma amsa masu da magana mai kyau, su kuwa kullum za su zama barorinka."
8Amma Rehobowam ya yi watsi da shawarar da dattawan mutanen su ka ba shi, sai ya yi shawara tare da matasan mutane waɗanda su ka yi girma tare da shi.9Ya ce masu, "Wacce shawara za ku ba ni don in amsa wa mutanen nan da suka yi magana da ni cewa, 'Ka rage wahalar da tsohonka ya aza mana?'"
10Matasan waɗanda su ka yi girma tare da Rehobowam su ka yi magana da shi, cewa, "Yi magana da mutanen nan waɗanda suka faɗa maka mahaifinka Suleman ya nawaita masu amma sai kai ka sauwaƙa masu. Sai ka ce da su, 'Karamin yatsana ya fi ƙugun mahaifina kauri.11To yanzu, ko da mahaifina ya wahalar da ku da bauta, zan ƙara maku nawayar. Mahaifina ya hore ku da bulala, amma ni zan hore ku da kunamai.'"
12Sai Yerobowom da dukkan mutane suka zo wurin Rehobowom a rana ta uku, kamar yadda sarki ya umarta a lokacin da ya ce, "Ku dawo wurina a rana ta uku."13Sarki ya amsa wa mutanen da zafi, ya kuma yi watsi da shawarar da dattawa suka ba shi.14Ya yi masu magana bisa ga shawarar matasa; ya ce, "Mahaifina ya nawaita maku, amma ni zan ƙara nawaita maku. mahaifina ya yi maku horo da bulala, amma ni zan yi maku da kunamai."
15Haka nan kuwa sarki bai saurari mutanen ba, gama wannan al'amarin ya zama haka bisa ga shirin Yahweh, akan yadda zai cika maganar da ya faɗa ta wurin Ahijah Bashiloniye zuwa ga Yerobowom ɗan Nebat.
16Sa'ad da dukkan mutane Isra'ila suka ga sarki bai saurare su ba, sai mutanen suka amsa masa suka ce, "Mene ne rabonmu da Dauda? Ba mu da gãdo a cikin ɗan Yesse! Ku tafi rumfunanku, Isra'ila. Yanzu ka duba gidanka, Dauda." Isra'ila suka koma rumfunansu.17Amma mutanen Isra'ila waɗanda suka zauna a biranen Yahuda, Rehobowom ya zama sarkinsu.
18Sai sarki Rehobowom ya aiki Adoniram, wanda ya ke shi ne shugaban aikin tilas, amma dukkan Isra'ila suka jajjefe shi da duwatsu har ya mutu. Sarki Rehobowom da gaggawa ya hau karusarsa ya tsere zuwa Yerusalem.19Mutanen Isra'ila kuwa suka tayar wa gidan Dauda har zuwa wannan rana.
20Ya zama haka dukkan Isra'ila suka ji Yerobowom ya komo, sai suka aika a kirawo shi ga taron, suka naɗa shi sarki akan dukkan Isra'ila. Babu wanda ya bi iyalin Dauda, sai dai kabilar Yahuda.
21Da Rehobowom ya komo Yerusalem, ya tara dukkan mutanen gidan Yahuda da kabilar Benyamin; suka kai mayaƙa 180,000 mutanen da aka zaɓa sojoji, da za su yi faɗa gãba da gidan Isra'ila, domin su komar da su a ƙarƙashin mulkin Rehobowom ɗan Suleman.
22Amma maganar Allah ta zo ga Shemayya, mutumin Allah; ta ce,23"Faɗa wa Rehobowom ɗan Suleman, sarkin Yahuda, da Benyamin da sauran jama'a, ka ce,24"Yahweh ya ce wannan: Ba za ka yi yaƙi ko faɗa da 'yan'uwanku mutanen Isra'ila ba. Kowannenku ya koma gidansa, gama wannan al'amari ya faru ne daga gare ni.'" Sai suka saurari maganar Yahweh, suka juya suka koma hanyarsu, suka yi biyayya da maganarsa.
25Sai Yerobowom ya gina Shekem a ƙasar tudu ta Ifraim, ya zauna a can. Ya fita daga can ya gina Feniyel.26Yerobowam kuwa ya yi tunani a cikin zuciyarsa, '"Yanzu mulki fa zai koma gidan Dauda.27Idan waɗannan mutanen suka ci gaba da miƙa hadiyu a haikalin Yahweh a Yerusalem, sai zuciyar waɗannan mutane su juya su yi gãba da maigidansu, Reroboam sarkin Yahuda. Za su kashe ni su koma wurin Rehobowom sarkin Yahuda."
28Sai sarki Yerobowom ya nemi shawara ya siffanta 'yan maruka biyu da zinariya; ya cewa mutane, "Zai yi maku wuya don ku yi ta tafiya zuwa Yerusalem. Duba, ga waɗannan allolinku, ya Isra'ila, waɗanda suka fito da ku daga ƙasar Masar."29Ya sa siffar ɗaya a Betel ɗaya kuma a Dan. Wannan abu ya zama zunubi.30Mutane suka tafi wurin ɗaya ko ɗayan, dukka suka kama hanya zuwa Dan.
31Yerobowom ya gina masujadai a tuddai, ya kuma sa firistoci a cikin dukkan mutanen, waɗanda ba 'ya'yan Lebi ba.32Yerobowom kuma ya sa a yi idi a watan takwas, ran goma sha biyar ga wata, kamar yadda ake yin idi a Yahuda, ya tafi bagadi. Ya yi kuma a Betel, hadayun siffofin maruƙan da ya yi a Betel ya sa firistoci a masujadan da ya gina.
33Yerobowom ya tafi gaban bagaden da ya gina a Betel a rana ta goma sha biyar ga wata na takwas, a watan ya shirya a tunaninsa; ya yi biki don mutanen Isra'ila ya kuma tafi bagade ya ƙona turare.

13

1Mutumin Allah ya fito daga Yahuda ta wurin maganar Yahweh zuwa Betel. Yerobowom yana tsaye kusa da bagadin ƙona turare.2Ya yi kuka akan wannan mugunta ta bagadi ta wurin maganar Yahweh: "Bagadi, bagadi! Wannan shi ne abin da Yahweh ya fada, 'Duba, mai suna Yosiya za a haife shi a iyalin Dauda, da kai zan yi hadayun firistoci na masujadan tuddai waɗanda za su ƙona turare a kanka. A kanka kuma za su ƙona ƙasusuwan mutane.'"3Sai mutumin Allah ya ba da alamar ranar, cewa, "Wannan shi ne alamar da Yahweh ya yi magana: 'Duba, za a rushe bagadin, za a kuma watsar da tokar waje.'"

4Da sarki ya ji abin da mutumin Allah ya ce, sai ya yi kuka akan bagadin da ya ke Betel, Yerobowam ya miƙa hannunsa daga bagadin, cewa, "Ku kama shi. "Sai hannun da ya miƙa akan mutumin ya bushe, domin bai iya komo da shi ba.5(Aka rushe bagadin aka kuma zubar da tokar bagadin, alamar da mutumin Allah ya ba da bisa ga maganar Yahweh.)
6Sarki Yerobowom ya amsa ya ce da mutumin Allah, "Ka yi roƙo domin in sami tagomashi a wurin Yahweh Allahnka kuma ka yi addu'a domina, saboda ya warkar da hannuna." Mutumin Allah ya yi addu'a ga Yahweh, hannun sarki kuwa ya dawo gare shi kuma, dai-dai kamar yadda ya ke a dã.7Sarki ya ce da mutumin Allah, "Ka zo gida tare da ni ka shakata, zan ba ka lada."
8Mutumin Allah kuwa ya ce da sarki, "Ko da za ka ba ni rabin mallakarka, ba zan tafi tare da kai ba, ko in ci abinci ko in sha ruwa a wannan wurin ba,9gama Yahweh ya umarce ni ta wurin maganarsa, 'Ba za ka ci gurasa ko ka sha ruwa, ko ka koma ta hanyar da ka zo ba.'"10Haka kuwa mutumin Allah ya koma ta wata hanya dabam zuwa gidansa ba ta hanyar da ya zo Betel ba.
11To akwai wani tsohon annabi wanda ke zaune a Betel, ɗaya daga cikin 'ya 'yansa maza ya tafi ya faɗa masa dukkan abubuwan da mutumin Allah ya yi a wannan rana a Betel. 'Ya'yansa kuwa suka faɗa wa mahaifinsu maganar da mutumin Allah ya faɗa wa sarki.12Mahaifinsu ya ce da su, "Wacce hanyar ya bi ya tafi?" 'Ya'yansa sun ga hanyar da mutumin Allah daga Yahuda ya bi ya tafi.13Ya ce da 'ya'yansa ku ɗaura wa jaki shimfiɗa domina." Sai suka ɗaura wa jaki shimfiɗa, shi kuwa ya hau ya tafi.
14Tsohon annabin ya bi bayan mutumin Allah har ya same shi yana zama a ƙarƙashin itacen rimi; ya ce masa, "Kai ne mutumin Allahn nan da ya zo daga Yahuda?" Ya amsa, "I, ni ne."15Sai tsohon annabi ya ce da shi, "Zo gida tare da ni ka ci abinci."16Mutumin Allah ya amsa, ba zan koma tare da kai ba ko kuwa in shiga tare da kai, ko kuwa in ci abinci ko in sha ruwa tare da kai a wannan wuri,17gama umarni gare ni ta wurin maganar Yahweh, 'ba za ka ci wani abinci ko ka sha ruwa a wurin ba, ko ka koma ta hanyar da ka zo.'"
18Sai tsohon annabin ya ce da shi, "Ai ni ma annabi ne kamar ka, mala'ika ya yi magana da ni ta wurin maganar Yahweh, cewa, 'Ka zo da shi tare da kai cikin gidanka, don ya ci abinci ya sha ruwa.'" Amma ƙarya ce tsohon annabin ya ke faɗa wa mutumin Allah.19Saboda haka sai mutumin Allah ya koma tare da tsohon annabi ya ci abinci ya kuma sha ruwa a gidansa.
20Ya yin da suka zauna a tebur, sai maganar Yahweh ta zo ga annabi wanda ya komo da shi,21sai ya kira mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda, cewa, "Yahweh ya ce, 'Domin ka yi rashin biyayya da maganar Yahweh, ba ka kuma kiyaye umarnin Yahweh Allahnka da ya ba ka ba,22amma ka komo ka ci abinci ka sha ruwa a wannan wurin wanda Yahweh ya faɗa ma ka kada ka ci abinci ko kuwa ka sha ruwa, saboda haka ba za a bizne jikinka a kabarin ubanninka ba.'"
23Bayan da ya ci abinci, ya kuma sha, sai annabin ya ɗaura wa jakin mutumin Allah sirdi, da kuma mutumin da ya komo tare da shi.24Sa'ad da mutumin Allah ya tafi, sai zaki ya gamu da shi a hanya ya kashe shi, ya bar gawar akan hanya. Sai jakin ya tsaya a gefenta, haka nan ma zaki ya tsaya kusa da gawar.25Sa'ad da mutane da ke wucewa ta wurin suka ga an yar da gawar akan hanya, zaki kuma ya tsaya a gefenta, suka zo suka faɗa a cikin birnin da tsohon annabi ya ke.
26Sa'ad da annabi wanda ya komo da shi daga hanyar ya ji, sai ya ce, "Wannan mutumin Allah ne wanda bai yi biyayya da maganar Yahweh ba. Saboda haka Yahweh ya ba da shi ga zaki, wanda ya yayyage shi, ya kuma kashe shi, kamar yadda maganar Yahweh ta gargaɗe shi."27Sai tsohon annabi ya yi magana da 'ya 'yansa maza, cewa, "Ku ɗaura wa jakina sirdi," su kuma suka ɗaura wa jakin sirdi.28Ya tafi ya sami gawar an bar ta a hanya, jakin da zaki su na tsaye a gefen gawar. Zaki bai ci gawar ba, ko ma ya farma jakin.
29Annabin ya ɗauki gawar mutumin Allah, ya ɗora ta akan jaki, ya komo da ita. Ya zo da ita birninsa ya yi makoki ya bizne shi.30Ya bizne gawar a cikin kabarinsa, suka yi makoki domin sa, cewa. "Kaito, ɗan'uwana!"
31To bayan da ya bizne shi, tsohon annabin ya faɗa wa 'ya'yansa maza, cewa, "Sa'ad da na mutu, ku bizne ni a cikin kabari inda aka bizne mutumin Allah. Ku sa ƙasusuwana a kusa da nasa.32Gama an furta saƙon maganar Yahweh, a bagadin da ke Betel da kuma dukkan gidajen da ke kan tuddai a biranen Samariya, abin da lallai zai faru."
33Bayan wannan Yerobowom bai juyo daga muguwar hanyarsa ba, amma ya naɗa firistoci don masujadai da ke kan tuddai a cikin dukkan mutane. Duk wanda ya ke so sai ya karɓe shi a matsayin firist.34Wannan abu ya zama zunubi ga iyalin Yerobowam ya yi dalilin da aka hallaka iyalinsa aka kuma shafe su kakaf daga fuskar duniya.

14

1A lokacin nan Abija ɗan Yerobowom ba shi da lafiya sosai.2Yerobowom ya cewa matarsa, "Idan kin yarda ki tashi ki bad da kamarki, don ka da a gane ke matata ce, ki tafi Shilo, domin Ahija annabi yana can, shi ne wanda ya ce mani zan zama sarki akan waɗannan mutane.3Tare da ke ki ɗauki malmalar abinci goma, da waina da kurtun zuma, ki tafi wurin Ahija. Zai faɗa ma ki abin da zai faru da yaron."

4Matar Yerobowom kuwa ta yi haka; ta tashi ta tafi Shilo har ta iso gidan Ahija. Yanzu Ahija ba ya gani; saboda ya rasa gani don tsufa.5Yahweh ya cewa Ahija, "Duba, ga matar Yerobowom ta na zuwa ta nemi shawara daga gare ka akan ɗanta, domin ba shi da lafiya. Ka ce haka, da haka da ita, gama sa'ad da ta zo, za ta nuna kamar ita wata mace ce dabam."
6Sa'ad da Ahija ya ji motsin takawarta a bakin kofa, ya ce, "Ki shigo ciki, matar Yerobowam. Meyasa ki ke yi kamar ba ke ce ba? An aiko ni gare ki da labari mara daɗi.7Tafi, ki faɗa wa Yerobowam cewa Yahweh, Allah na Isra'ila ya ce, 'Na ɗaukaka daga cikin mutane na sa ka zama shugaba akan mutanena Isra'ila.8Na yage mulki daga iyalin Dauda na baka, duk da haka ba ka zama kamar bawana Dauda ba, wanda ya kiyaye umarnina ya bi ni da dukkan zuciyarsa, ya yi abin da ke dai-dai a idanuna.
9Maimako haka, ka aikata mugunta, fiye da dukkan waɗanda suka riga ka. Ka yi waɗansu alloli, ka yi siffofi na zubi ka tsokane ni in yi fushi, ka jefar da ni a bayanka.10Saboda haka, duba, zan kawo masifa a iyalinka; zan datse daga gare ka kowanne ɗa namiji a Isra'ila, ko bawa ko 'yantacce, zan ƙori iyalinka gaba ɗaya, kamar mutum wanda ya ƙone juji kurmus.
11Duk wanda ya ke na iyalinka wanda ya mutu a birni karnuka su cinye shi, wanda kuma ya mutu a fili tsuntsayen sammai su cinye shi, gama ni, Yahweh na faɗa.12Ki tashi, matar Yerobowom ki koma gidanki; ya yin da ƙafarki ta shiga birni, yaron Abija zai mutu.13Dukkan mutanen Isra'ila za su yi makoki dominsa za a bizne shi. Shi kaɗai ne daga iyalin Yerobowom wanda zai je kabari, gama shi kaɗai ne, daga cikin gidan Yerobowom, aka sa me shi da aikata abu mai kyau a fuskar Yahweh, Allah na Isra'ila.
14Haka nan Yahweh zai ta da wani sarki a Isra'ila wanda zai yanke iyalin Yerobowom a wannan rana. Yau ita ce wannan rana, yanzun nan.15Gama Yahweh zai hukunta Isra'ila kamar yadda akan girgiza iwa a ruwa, zai tuge Isra'ila daga wannan ƙasa mai kyau wadda ya ba kakanninsu. Zai watsar da su bayan Kogin Yufiretis, domin sun yi wa kansu turaku na Ashera domin su tsokani Yahweh ya yi fushi.16Zai bayar da Isra'ila domin zunuban Yerobowom, zunuban da ya aikata, ta wurin sa Isra'ila su yi zunubi.
17Sai matar Yerobowom ta tashi ta tafi, ta zo Tirza. Tana zuwa bakin ƙofar gidanta kenan, yaron ya mutu.18Dukkan Isra'ila su ka bizne shi, suka yi makoki dominsa, kamar yadda aka faɗa masu ta wurin maganar Yahweh wanda ya yi magana ta wurin bawansa Ahija annabi.
19Game da sauran abubuwa akan Yerobowom, yadda ya yi yaƙe-yaƙensa da sarautarsa, duba, an rubuta su a cikin littafin tarihin sarakunan Isra'ila.20Yerobowom ya yi mulki shekaru ashirin da biyu sa'an nan ya rasu tare da kakaninsa, ɗansa Nadab ya gaji sarauta a matsayin mahaifinsa.
21Yanzu Rehobowom ɗan Suleman ya yi mulki a Yahuda. Rehobowom yana da shekare arba'in da ɗaya sa'ad da ya zama sarki, ya kuwa yi mulki shekaru goma sha bakwai a Yerusalem, birnin da Yahweh ya zaɓa daga dukkan kabilun Isra'ila in da ya sa sunansa. Sunan mahaifiyarsa kuwa Na'ama Ammoniya.22Yahuda ta yi abin da ke mugu a fuskar Yahweh; suka tsokane shi ya yi fushi saboda zunuban da suka aikata, fiye da abin da kakanninsu suka yi.
23Gama suma sun gina wa kansu wuraren tsafi, ginshiƙan dutse da turken Ashera a kan kowanne tudu mai tsawo da ƙarƙashin kowanne koren itace.24Akwai kuma karuwan tsafi a ƙasar. Suka yi abubuwan bankyama kamar al'ummai da Yahweh ya kawar daga wurin mutanen Isra'ila.
25Wannan ya faru a shekara ta goma sha biyar ta mulkin Rehobowom da Shishak sarkin Masar ya gãba da Yerusalem.26Ya kwashe dukiyar gidan Yahweh, da dukiyar gidan sarki. Ya ɗauke kome da kome ya tafi da shi; ya kuma ɗauki garkuwoyin zinariya waɗanda Suleman ya yi.
27Sarki Rehobowom ya yi garkuwoyin tagulla ya sa a hannun shugabannin masu tsaro, waɗanda ke tsaron ƙofar gidan sarki.28Ya zamana duk lokacin da sarki zai shiga gidan Yahweh, matsara za su ɗauke su; sai su kawo su a gidan tsaro.
29Game da sauran abubuwa akan Rehobowom, dukkan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuda.30Kullum ana ta yin yaƙi tsakanin Rehobowom da Yerobowom.31Rehobowom kuwa ya yi barci tare da kakaninsa aka kuma bizne shi tare da su a birnin Dauda. Sunan mahaifiyarsa kuwa Na'ama daga Ammoniyawa. Abija ya gaji sarauta a matsayin mahaifinsa.

15

1A shekara ta goma sha takwas ta sarki Yerobowom ɗan Nebat, Abija ya fara sarauta akan Yahuda.2Ya yi mulki shekaru uku a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Ma'aka. Ita ɗiyar Abishalom ce.3Shi ma ya yi tafiya a cikin dukkan irin zunubai da tsohonsa ya yi a lokacinsa; bai ba Yahweh Allahnsa dukkan zuciyarsa ba kamar yadda Dauda kakansa ya yi ba.

4Duk da haka, saboda Dauda, Yahweh Allahnsa ya ba shi fitila a Yerusalem ta wurin ba ɗansa ya gaje shi saboda ya ƙarfafa Yerusalem.5Allah ya yi wannan domin Dauda ya yi abin da ke dai-dai a idanuwansa; a cikin dukkan kwanakin ransa, bai juya daga kowanne umarnin da aka ba shi ba, sai dai akan Yuriya Bahitte.6Yanzu akwai yaƙi a tsakanin Abija ɗan Yerobowom dukkan kwanakin rayuwar Abija.
7Kamar sauran ayyukan Abija, duk da abubuwan da ya yi, ba suna rubuce a cikin littafin tarihi na sarakunan Yahuda ba? Akwai yaƙi tsakanin Abija ɗan Yerobowom.8Abija ya barci tare da kakaninsa, su ka bizne ne shi a birnin Dauda. Asa ɗansa ya zama sarki a maimakon mahaifinsa.
9A cikin shekara ta ashirin ta sarautar Yerobowom sarkin Isra'ila, Asa ya fara sarauta a Yahuda.10Ya yi shekaru arba'in da ɗaya yana sarauta a Yerusalem. Sunan kakarsa kuwa Ma'aka, yar Abishalom.11Asa ya yi abin da ke dai-dai a idanun Yahweh, kamar yadda Dauda, kakansa ya yi.
12Ya kori karuwai matsafa daga ƙasar ya kuma cire dukkan gumakun da kakaninsa suka yi.13Ya kuma fitar Ma'aka da kakarsa, daga zaman sarauniya, domin ta yi ƙazamar siffa daga turken Ashera. Asa ya sassare ƙazamar siffar ya ƙone ta a Kwarin Kidron.
14Amma ba a kawar da wuraren tsafi na tuddai ba. Duk da haka, Asa ya ba Yahweh dukkan zuciyarsa a dukkan kwanakinsa.15Ya kawo abubuwan da mahaifinsa ya keɓe da kuma azurfa da zinariya da kwanoni waɗanda shi kansa ya yi a cikin gidan Yahweh.
16Akwai yaƙi tsakanin Asa da Ba'asha sarkin Isra'ila, dukkan kwanakinsu.17Ba'asha sarkin Isra'ila, ya kai wa Yahuda yaƙi ya gina Rama, don ya hana kowa ya fita ko kuma ya shiga ƙasar Asa sarkin Yahuda.
18Sai Asa ya kwashe dukkan azurfa da zinariya da suka rage a ɗakunan ajiya na gidan Yahweh, da na ɗakin ajiyar fãdar sarki. Ya sa su a cikin hannuwan barorinsa su kai su ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda ke zaune a Damaskus. Ya ce.19"Bari mu ƙulla alƙawari tsakani na da kai, kamar yadda ya ke tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, na aika maka da kyautar azurfa da zinariya. Ka karya alƙawarinka da Ba'asha sarkin Isra'ila, domin ya bar ni."
20Ben-Hadad kuwa ya saurari sarki Asa ya kuma aika shugabanin sojojinsa su ka yi yaƙi da biranen Isra'ila. Suka yi faɗa da Iyon da Dan da Abe ta bet Ma'aka, da dukkan Kenneret tare da dukkan ƙasar Naftali.21Da Ba'asha ya ji wannan, sai ya daina ginin Rama ya koma Tirzah.22Sa'an nan sarki Asa ya yi jawabi ga dukkan mutanen Yahuda. Ba wanda aka ɗauke wa. Suka tafi su ka ɗauki duwatsu da katakai a Ramah waɗanda Ba'asha ke gina birnin. Sai sarki Asa ya yi amfani da kayan ginin ya gina Geba ta Benyamin da Mizfa.
23Sauran dukkan abubuwa a game da Asa, dukkan ƙarfinsa, dukkan abubuwan da ya yi, da biranen da ya gina, ba su na nan ba a rubuce a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda?24Amma lokacin tsufansa, sai ya sami ciwo a ƙafafunsa. Asa ya rasu tare kakaninsa aka kuma bizne shi tare da su a cikin birnin Dauda mahaifinsa. Yehoshafat ɗansa ya zama sarki a matsayinsa.
25Nadab ɗan Yerobowom ya fara sarauta a Isra'ila a shekara ta biyu ta sarki Asa na yin mulkin a Yahuda; ya yi sarautar Isra'ila shekaru biyu.26Ya yi mugunta a fuskar Yahweh ya yi tafiya a hanyar da mahaifinsa ya yi a cikin zunubinsa, ya jagoranci Isra'ila su yi zunubi.
27Ba'asha ɗan Ahiji, na iyalin Issaka, ya yi wa Nadab maƙarƙashiya; Ba'asha kashe shi a Gibbeton wadda ke ta Filistiyawa, gama Nadab da dukkan Isra'ila sun kewaye Gibbeton da yaƙi.28A cikin shekara ta uku da sarki Asa ke mulkin Yahuda, Ba'sha ya kashe Nadab ya kuma zama sarki a gurbinsa.
29Nan da nan da ya zama sarki, Ba"asha ya kashe dukkan iyalin Yerobowom. Bai bar kowa ba a zuriyar Yerobowom wanda ke numfashi ba; a wannan hanya ya hallakar da gidan sarautarsa, kamar yadda Yahweh ya faɗa ta wurin bawansa Ahija mutumin Shilo,30domin zunuban Yerobowom wanda ya yi da kuma zunubin da ya sa mutanen Isra'ila suka yi, don ya tsokani Yahweh, Allah na Isra'ila ya yi fushi.
31Kamar sauran abubuwa a kan Nadab, da dukkan abin da ya yi, ba suna a rubuci ba a cikin littafin tarihi na ayyukan sarakunan Isra'ila?32Akwai yaƙi tsakanin Asa da Ba'asha sarkin Isra'ila a dukkan kwanakinsu.
33A cikin shekara ta uku da Asa sarkin Yahuda, Ba'asha ɗan Ahija ya fara sarauta akan dukkan Isra'ila a Tirza ya kuma yi mulki sheraka ashirin da huɗu.34Ya yi abin da ke na mugunta a fuskar Yahweh ya kuma bi hanyar Yerobowom da kuma zunubin da ya sa Isra'ila suka yi.

16

1Maganar Yahweh ta zo ga Yehu ɗan Hanani akan Ba'asha, cewa,2"Ko da ya ke na ɗauke ka daga cikin ƙura, na maishe ka shugaba akan mutanena Isra'ila, kai kuwa ka yi tafiya irin ta Yerobowom ka sa mutanena Isra'ila sun aikata zunubi, suka sa na yi fushi saboda zunubansu.

3Duba, zan shafe Ba'asha da iyalinsa gaba ɗaya, zan maida iyalinka kamar iyalin Yerobowom ɗan Nebat.4Karnuka ne za su cinye kowanne mutum da ke na Ba'asha idan ya mutu a birni, tsuntsayen sama kuma ne za su cinye kowanne mutum da ya mutu a saura."
5Sauran ayyuka akan Ba'asha, da abubuwan da ya yi, da ƙarfinsa, ba suna a rubuce a littafin tarihi na sarakunan Isra'ila ba?6Ba'asha ya yi barci aka kuma bizne shi tare da kakanninsa a Tirzah, Ela ɗansa kuma ya zama sarki a gurbinsa.
7Sai maganar Yahweh ta zo wurin annabi Yehu ɗan Hanani akan Ba'asha da iyalinsa, duka kuma saboda dukkan mugutar da ya aikata a fuskar Yahweh, har ya yi fushi da ayyukan hannuwansa, kamar iyalin Yerobowom, kuma saboda ya hallaka dukkan iyalin Yerobowom.
8A shekara ta ashirin da shida da Asa ke mulkin Yahuda, Ela ɗan Ba'asha ya fara sarauta akan Isra'ila a Tirzah; ya yi sarauta shekaru biyu.9Bawansa Zimri, shugaban rabin karusansa ya yi masa maƙarƙashiya. Sa'ad da Ela ya ke Tirzah, ya sha ya bugu a gidan Arza, wanda ya ke lura da fada a Tirzah.10Zimri ya tafi cikin gidan, ya buge shi har ya kashe shi, a shekara ta ashirin da bakwai ta mulkin Asa sarkin Yahuda, ya zama sarki a gurbinsa.
11Da Zimri ya fara sarauta ya zauna akan kujerar mulki, yakashe dukkan iyalin Ba'asha. Bai bar namiji ko ɗaya a raye ba dangi ko abokai.12Haka Zimri ya hallaka dukkan iyalin Ba'asha, bisa ga maganar da Yahweh wanda ya faɗa akan Ba'asha ta bakin annabi Yehu,13saboda dukkan zunuban Ba'asha da zunuban Ela ɗansa su ka yi, da wanda su ka sa Isra'ila su ka yi, don sun tsokani Yahweh, Allah na Isra'ila, ya yi fushi da gumakunsu.
14Game da sauran ayyukan Ela, da dukkan abin da ya yi, ba suna a rubuce a cikin littafin tarihi na sarakunan Isra'ila ba?
15A shekara ta ashirin da bakwai da sarki Asa ke mulkin Yahuda, Zimri ya yi sarauta kwana bakwai a Tirzah. A lokacin nan sojoji sun yi sansani a Gibbeton, wanda ta ke ta Filistiyawa.16Sojojin da suka yi sansani a wurin suka ji an ce, "Zimri ya shirya makirci ya kashe sarki." A wannan rana a sansanin, dukkan mutanen Isra'ila suka naɗa Omri, shugaban sojojin, sarkin Isra'ila.17Omri kuwa ya tafi daga Gibbeton da dukkan mutanen Israila tare da shi, su ka kewayeTirzah da yaƙi.
18Da Zimri ya ga an ci birnin sai ya tafi ya shiga hasumiyar da ta ke a fãdar sarki, ya sawa fãdar ginin wuta ta cinye duk da shi, ta wannan hanyar ya mutu a zafin wuta.19Wannan ya faru saboda da zunuban da ya aikata ta wurin aikata mugunta a fuskar Yahweh, ya bi hanyar Yerobowam da zunuban da ya sa mutanen Isra'ila suka yi zunubi.20Game da sauran ayyuka akan Zimri da makircin da ya aiwatar, ba a rubuce su ke ba a cikin littafin tarihi na sarakunan Isra'ila?
21Sai mutanen Isra'ila suka rabu gida biyu. Rabin mutanen suka bi Tibni ɗan Ginat, don su naɗa shi sarki, rabi kuma suka bi Omri.22Amma mutane waɗanda suka bi Omri suna da ƙarfi fiye da mutanen da suka bi Tibni ɗan Ginat. Sai Tibni ya mutu, Omri kuwa ya zama sarki.
23Omri ya fara sarauta akan Isra'ila a shekara ta talatin da ɗaya ta Asa sarkin Yahuda, ya yi shekaru goma sha biyu yana sarauta. Ya yi shekaru shida yana mulki a Tirzah.24Ya sayi tudun Samariya daga Shemer akan talanti biyu na azurfa. Ya gina birni a tudu aka kira sunansa birnin Samariya, bayan sunan Shemer, mai tudun.
25Omri kuwa ya aikata mugunta a fuskar Yahweh, ya yi mugunta fiye da dukkan waɗanda suka riga shi.26Gama ya yi tafiya a dukkan hanyoyin da Yerobowom ɗan Nebat da irin zunubansa wanda ya sa Isra'ila suka yi zunubi, suka sa Yahweh, Allah na Isra'ila, fushi don gumakunsu na wofi.
27Game da sauran ayyuka wanda Omri ya yi, da ƙarfinsa da ya nuna, ba suna nan a cikin littafin tarihin sarakunan Isra'ila ba?28Omri kuwa ya yi barci, aka bizne shi tare da kakaninsa a Samariya, Ahab ɗansa ya zama sarki a gurbin mahaifnsa
29A shekara ta talatin da takwas ta Asa sarkin Yahuda, Ahab ɗan Omri ya fara sarauta a Isra'ila. Ahab ɗan Omri ya yi mulkin Isra'ila a Samariya shekaru ashirin da biyu.30Ahab ɗan Omri ya yi abubuwan da ke mugunta a fuskar Yahweh, fiye da dukkan waɗanda su ka riga shi.
31Da ya ke Ahab abu ne mai sauki a gare shi ya bi zunuban Yerobowom ɗan Nebat, sai ya auro matarsa Yezebel 'yar Etba'al, sarkin Sidon; ya je yana bauta wa Ba'al, yana kuma yi masa sujada.32Ya gina bagadi domin Ba'al a gidan Ba'al, wanda ya gina a Samariya.33Ahab kuma ya yi turken gunkiyar nan Ashera. Ahab dai ya yi abin da zai tsokani Yahweh Allah na Isra'ila, zuwa fushi fiye da dukkan sarakunan Isra'ila waɗanda suka riga shi.
34A lokacin sarautar Ahab, Hiyel na Betel ya gina Yariko. Hiyel ya sa tushen birni da farashin ran Abiram, ɗan farinsa; Segub, ɗan autansa, ya rasa ransa a lokacin da ya ke gina ƙofofin birnin, ta cikin ajiye maganar Yahweh wanda ya yi magana ta wurin Yoshuwa ɗan Nun.

17

1Iliya Batishbe, daga Tishbi a Giliyad, ya ce da Ahab, "Kamar yadda Yahweh, Allah na Isra'ila ya ke raye wanda nake tsaye a gabansa, ba za a yi raɓa ko ruwan sama a waɗannan shekaru sai da faɗata."

2Maganar Yahweh ta zo ga Iliya, cewa,3"Tashi daga nan ka tafi wajen gabas; ka ɓoye kanka a rafin Kerit, gabashin Yodan.4A can zai zamana inda za ka riƙa samun ruwan sha daga rafin, na kuma umarci hankaki su ciyar da kai a can."
5Iliya kuwa ya tafi, ya yi yadda Yahweh ya umarta. Ya tafi ya zauna a rafin Kerit, gabas da Yodan.6Hankaki kuwa suka riƙa kawo masa abinci da nama da safe abinci da nama da maraice, yana shan ruwa daga rafin.7Amma bayan wani ɗan lokaci sai rafin ya ƙafe saboda ba a yin ruwan sama a ƙasar.
8Sai maganar Yahweh ta zo ga Iliya, cewa.9"Tashi ka tafi Zarefat, wadda da ta ke ta Sidon, ka zauna a can. Duba, na umarci wata mace gwauruwa ta ciyar da kai."10Shi kuwa ya tashi ya tafi Zarefat, sa'ad da ya isa ƙofar birnin sai ga wata gwauruwa a wurin ta na tattara itace. Sai ya kira ta ya ce, "Idan kin yarda ki kawo mani ɗan ruwa in sha."
11Tana juyawa za ta tafi ta kawo masa ruwan sha kenan, sai ya kira ta ya ce, "Idan kin yarda ki ba ni ɗan abinci a hannunki."12Sai ta amsa, "Kamar yadda Yahweh Allahnka ya ke da rai, ba ni da abinci, sai dai ɗan garin da ya ragu a tukunya da ɗan man da ke cikin kwalba. Ga ni, ina tattara yan itatuwa biyu don in je in girka shi domin ni da ɗana, mu ci, mu mutu."13Iliya ya ce mata, "Kada ki ji tsoro. Tafi ki yi yadda na ce, amma ki fara yi mani gurasa kaɗan tukuna ki kawo mani. Sa'an nan ki yi wa kanki da ɗanki.
14Gama Yahweh Allah na Isra'ila, ya ce, 'Garin da ya ke a tukunyarki ba zai ƙare ba, ko da man ma ba zai dena zubuwa ba, sai dai ranar da Yahweh ya aiko da ruwan sama a duniya."15Ta tafi ta yi yadda Iliya ya faɗa mata. Ita da Iliya da sauran yan gidan, sun ci har kwanaki da yawa.16Garin bai ƙare ba, kwalbar man ma bata dena zubuwa ba, kamar yadda maganar Yahweh ta ce, kamar kuma yadda Iliya ya faɗa.
17Bayan waɗannan abubuwa sai ɗan macen, matar wadda take da gidan, ya yi ciwo. Ciwonsa kuwa ya tsananta har ba sauran numfashi a cikinsa.18Sai mahaifiyar yaron ta ce da Iliya, "Me ya haɗa ni da kai, ya mutumin Allah? Ka zo gare ni ne don ka tuna ma ni da zunubina ka kuma kashe ɗa na?"
19Sai Iliya ya amsa ma ta, "Ki ba ni ɗanki." Ya ɗauki yaron daga hannuwanta, ya kai shi a ɗaki inda ya ke zama, ya kwantar da yaron akan gadonsa.20Ya yi kuka ga Yahweh ya ce, "Yahweh Allahna, ka kuma kawo masifa akan gwauruwar nan wadda na ke zaune wurinta, ta wurin kashe mata ɗa?21Sa'an nan Iliya ya kwanta ya miƙe akan yaron sau uku, ya kuma yi kuka sosai ga Yahweh ya ce, "Yahweh Allahna, ina roƙonka, idan ka yarda bari ran yaron nan ya komo gare shi."
22Yahweh kuwa ya saurari muryar Iliya; ran yaron ya komo gare shi sai ya farfaɗo.23Iliya ya ɗauki yaron daga ɗakinsa ya kawo shi ya kai shi cikin gida; ya bada yaron ga uwar ya ce, "Ki gani, ɗauki yaronki yana da rai." Matar kuwa ta cewa Iliya,24"Yanzu na sani kai mutumin Allah ne, kuma maganar Yahweh kuwa da ke cikin bakinka gaskiya ce."

18

1Bayan kwanaki masu yawa sai maganar Yahweh ta zo ga Iliya, a shekara ta uku ta farin, cewa,2"Tafi, ka nuna kanka ga Ahab zan aiko da ruwan sama a ƙasar." Iliya kuwa ya tafi ya nuna kansa ga Ahab; yanzu kuwa yunwa ta tsananta a Samariya.

3Ahab ya kira Obadiya, wanda ya ke shugaban fada. Obadiya kuwa yana girmama Yahweh sosai,4domin lokacin da Yezebel ta karkashe annabawan Yahweh, Obadiya ya kwashe annabawa ɗari ya raba su hamsin, hamsin ya ɓoye su a kogo, ya ciyar da su da gurasa ya kuma shayar da su.
5Ahab ya cewa Obadiya, "Tafi cikin ƙasar nan duk inda maɓuɓɓugar ruwa da fadamu suke. Watakila ma sami ciyawa mu ceci rayukan dawakai da alfadarai, don kada mu rasa dukkan dabbobin nan."6Saboda haka suka raba ƙasar a tsakaninsu suka shige ta su duba inda ruwa ya ke. Ahab ya bi ɗaya hanyar da kansa Obadiya kuma ya tafi wata hanyar.
7Sa'ad da Obadiya ya ke tafiya a hanya, Iliya ya yi kaciɓus da shi. Obadiya ya gane da shi sai ya russana a ƙasa. Ya ce, "Kai ne shugabana Iliya?"8Iliya ya amsa masa. "Ni ne. Tafi ka faɗa wa shugabanka, 'Duba, Iliya na nan.'"
9Obadiya ya amsa, "Wanne zunubi na yi, har da za ka bada bawanka a cikin hannun Ahab, domin ya kashe ni?10Kamar yadda Yahweh Allahnka ya ke raye, babu wata al'umma ko mulki da shugabana bai aika mutane a nemo ka ba. Duk wata al'umma ko mulki suka ce, 'Iliya ba ya nan,' Ahab ya sa su ɗauki rantsuwa ba su same ka ba.11Amma yanzu ka ce, "Tafi, faɗa wa shugabana cewa ga Iliya a nan.'
12Ya yin da na tafi daga wurin ka, Ruhun Yahweh ya kai ka wurin da ban sani ba. Don haka idan na tafi na faɗa wa Ahab, idan kuma bai same ka ba, zai kashe ni. Ko da ya ke ni bawanka, ina bauta wa Yahweh tun daga kuruciyata.13Ashe ba a faɗa maka ba, shugabana, abin da na yi a lokacin da Yezebel ta kashe annabawan Yahweh, abin da na yi na ɓoye annanbawan Yahweh ɗari na raba su hamsin hamsin a kogo na kuma ciyar da su da gurasa da ruwa?
14Yanzu kuwa ka ce da ni, "Tafi in faɗa wa shugabana ga Iliya a nan,' ai zai kashe ni."15Sai Iliya ya amsa, "Kamar yadda Yahweh mai runduna ya ke da rai, wanda nake tsaye a gabansa, hakika zan nuna kaina ga Ahab yau."
16Saboda haka sai Obadiya ya tafi ya sadu da Ahab, ya faɗa masa abin da Iliya ya ce. Sai sarki ya tafi ya sadu da Iliya.17Lokacin da Ahab ya ga Iliya, ya ce masa, "Kai ne? wanda ke kawo wahala ga Isra'ila!"
18Iliya ya amsa, "Ba ni ne na kawo wahala a Isra'ila ba, amma kai da iyalin mahaifinka su ne waɗanda suka jawo wahala ta wurin ƙin bin umarnan Yahweh kuna bin Ba'aloli.19Yanzu sai, ka aika da magana a tattara mani dukkan Isra'ila a Tsaunin Karmel, tare da annabawan Ba'al 450 da ɗari huɗu na annabawan Ashera waɗanda ke ci a teburin Yezebel."
20Sai Ahab ya aika da magana ga dukkan mutanen Isra'ila da su tara annabawa gaba ɗaya a Dutsen Karmel.21Iliya ya zo kusa da dukkan mutane ya ce, "Har yaushe ne za ku ci gaba da canza tunaninku? Idan Yahweh ne Allah, ku bi shi. Amma idan Ba'al shi ne Allah, sai ku bi shi." Duk da haka mutane ba su amsa masa da magana ba.
22Sai Iliya cewa mutane, "Ni, kaɗai ne na rage a matsayin annabin Yahweh, amma annabawan Ba'al su ɗari huɗu da hamsin.23Ku ba mu bijimai biyu. Bari su zaɓi ɗaya bijimin don kansu su yanyanka gunduwa gunduwa, su shimfiɗa su akan itacen, kada a sa masa wuta a ƙarƙashinsa.24Sai ku yi kira ga sunan allahnku, ni ma zan yi kira ga sunan Yahweh, duk Allahn da ya amsa da wuta bari ya kasance Allah. "Dukkan mutane suka amsa suka ce, "Wannan ya yi kyau."
25Sai Iliya yace da annabawan Ba'al, "Ku zaɓi bijimi ɗaya domin kanku ku kuma shirya shi da farko, gama kuna da mutane da yawa. Sa'an nan ku yi kira ga sunan allahnku, amma kada kuma fa ku sa wuta a ƙarƙashi bijimin."26Suka ɗauki bijimin da aka ba su suka shirya shi, suka yi kira da sunan Ba'al tun daga safe har rana ta yi tsaka, suna cewa, "Ba'al, ka ji mu mana." Amma babu wata murya, ko wani da ya amsa. Suka yi ta rawa a kewayan bagadin da suka gina.
27Da rana ta yi tsaka sai Iliya ya yi masu ba'a ya ce, "Ku yi ihu da ƙarfi! Shi allah ne! Watakila ya yi tafiya da nisa, ko watakila yana barci ne, sai ku tashe shi."28Suka yi ihu da ƙarfi sosai, suna kuma tsattsaga jikunansu, kamar yadda suke yi, tare da takubba da mãsu, har jini yana ta zuba daga jikunansu.29Da tsakar rana ta wuce, sai su kai ta yin sambatu har lokacin baikon hadayar yamma, amma ba bu wata murya ko wani wanda ya amsa; babu wani wanda ya kula da roƙe -roƙensu.
30Sai Iliya yace da dukkan mutane, "Ku zo kusa da ni," dukkan mutane kuwa suka zo kusa da shi. Ya gyara bagadin Yahweh wanda aka lalatar.31Iliya ya ɗauko duwatsu goma sha biyu bisa ga yawan 'ya 'yan Yakubu, ga Yakubu wanda maganar Yahweh ta zo, cewa, "Isra'ila ne zai zama sunanka."32Tare da duwatsun ya gina bagadi da sunan Yahweh, ya kuma haƙa rami babba sosai kewaye da bagadin isasshe da zai ci durom biyu na hatsi.
33Ya shirya itacen wuta, ya yanyanka bijimin gunduwa gunduwa, ya shimfiɗa shi bisa itacen. Ya ce, "Ku cika tuluna da ruwa a kwarara akan hadaya ta ƙonawar da kuma kan itacen."34Ya kuma ce, "Ku yi haka har sau lokaci na biyu," Suka yi haka a lokaci na biyu. Ya ce, "Su sake yi a lokaci na uku," suka yi haka a lokaci na uku.35Ruwa kuwa ya malale bagadin, ya kuma cika ramin.
36Ya zama kuwa a lokacin miƙa hadaya ta maraice, sai Iliya annabi ya matso kusa ya ce, "Yahweh, Allah na Ibrahim, na Ishaku da Isra'ila, bari ya zama sananne a wannan rana cewa kai ne Allah a Isra'ila, ni kuma bawanka ne, na yi waɗannan abubuwa dukka bisa ga maganarka.37Ka ji ni, Yahweh, ka ji ni, saboda waɗannan mutane su san ka, kai ne Yahweh, Allah, kai ne kuma ka juyo da zuciyarsu gare ka kuma."
38Sai wutar Yahweh ta faɗo, ta cinye hadaya ta ƙonawa, duk da itacen, da duwatsun da kurar, ta kuma lashe ruwan da ya ke cikin ramin.39Sa'ad da dukkan mutanen suka ga wannan, suka russana suka sunkuyar da kai suka ce, "Yahweh, shi ne Allah! Yahweh, shi ne Allah!"40Iliya kuma ya ce masu, "Ku kama annabawan Ba'al. Ka da ku bar ko ɗaya daga cikinsu ya tsere." Sai suka kama su, Iliya ya kai annabawan Ba'al rafin Kishon, ya karkashe su a can.
41Iliya ya cewa Ahab, "Tashi, ka ci ka sha, gama akwai motsin saukowar ruwan sama."42Sai Ahab ya haura don ya ci ya sha. Iliya ya tafi can konkoli Karmel, ya zauna a ƙasa ya haɗa kai da gwiwa.
43Ya ce da baransa, "Ka tafi ka duba wajen teku." Baran ya tafi ya duba, ya ce, "Ba bu kome." Sai Iliya ce, "Tafi kuma, har sau bakwai."44A zuwa na bakwai sai ya ce, "Na ga wani ɗan girgije yana zuwa daga teku, karami kamar tafin hannun mutum." Iliya ya amsa, "Tafi ka faɗa wa Ahab, 'Ya shirya karusarsa ya kuma gangara domin kada ruwan sama ya tsaida shi.'"
45Ya zamana fa jim kaɗan sai sararin sama ya yi baƙi ƙirin da giza-gizai da iska, aka yi ruwan sama mai yawan gaske. Ahab ya hau ya tafi wurin Yezriyel,46amma hannun Yahweh yana tare da Iliya. Ya sha ɗammara ya sheka a guje ya riga Ahab isa Yezriyel.

19

1Ahab ya faɗa wa Yezebel dukkan abin da Iliya ya yi da yadda ya kashe dukkan annanbawa da takobi.2Sai Yezebel ta aika wurin Iliya, cewa, "Bari alloli su yi mani, harma fiye kuma, idan ban mai da ran ka kamar ran ɗaya daga waɗannan annanbawa gobe a dai-dai wannan lokacin ba."3Sa'ad da Iliya ya ji haka, ya ji tsoro, ya tsere domin ransa ya zo Biyasheba, wadda take ta Yahuda, ya bar baransa a can.

4Amma shi da kansa ya yi tafiyar yini guda cikin jeji, ya zo ya zauna a gindin itacen aduwa. Ya yi roƙo domin kansa yadda zai mutu, ya kuma ce, "Ya isa haka, yanzu, Yahweh; ɗauke raina, gama ban fi kakannina ba."5Sai ya kwanta ya yi barci a gindin itace aduwa. Farat sai mala'ika ya taba shi, ya ce masa, "Tashi ka ci abinci."6Da Iliya ya duba, kusa da kansa sai ga gurasa ana gasawa akan garwashi da butar ruwa. Ya ci, ya sha, ya koma ya kwanta kuma.
7Mala'ikan Yahweh kuma ya sake zuwa sau na biyu ya taɓa shi, ya ce, "Tashi ka ci abinci, gama tafiyar za ta yi maka yawa.8Sai ya tashi ya ci ya sha, ya sami ƙarfin tafiya da wannan abincin har kwana arba'in dare da rana zuwa Horeb, wato tsaunin Allah.
9Ya tafi wani kogo a can ya tsaya a cikinsa. Sai maganar Yahweh ta zo wurinsa ta ce da shi, "Me kake yi a nan, Iliya?10Iliya ya amsa, "Ni mai kishi domin Yahweh, Allah mai runduna ne, gama mutanen Isra'ila suka manta da alƙawarin ka, suka lalata bagadanka, suka kuma karkashe annanbawanka da takobi. Yanzu ni kaɗai na rage da ba su kashe ba, suna ma ƙoƙarin su ɗauke raina."
11Yahweh ya amsa, "Tafi ka tsaya akan tsauni a gabana." Sai ga Yahweh yana wucewa, babbar iska mai ƙarfi ta tsaga duwatsun, ta kuma farfasa shi rugu rugua gabanYahweh, amma Yahweh ba ya cikin iskar. Bayan iskar sai girgizar ƙasa ta zo, amma Yahweh ba ya cikin girgizar ƙasar.12Bayan girgizar kuma sai wuta, amma Yahweh ba ya cikin wutar. Daga nan bayan wutar, sai natsastsar ƙaramar murya.
13Sa'ad da Iliya ya ji muryar, sai ya rufe fuskarsa da alkyabbarsa, ya fita, ya tsaya a bakin kogon. Sai murya ta zo gare shi ta ce, "Me ka ke yi a nan, Iliya?14Iliya ya amsa, "Ni na zama mai kishi domin Yahweh, Allah mai runduna ne, amma mutanen Israel sun karya alƙawarinka, suka lalata bagadannka suka kuma karkashe annabawanka da takobi. Yanzu ni, kaɗai na rage suna ma ƙoƙarin su ɗauki raina.
15Sai Yahweh yace da shi, "Tafi, ka juya akan hanyarka ta jeji kusa da Damaskus, idan ka isa can za ka zuba wa Hazayel mai, ka keɓe shi, ya zama sarkin Aram,16za ka kuma keɓe Yehu ɗan Nimshi ya zama sarkin Isra'ila, za ka kuma zuba wa Elisha ɗan Shafat na Abel Mehola mai ya zama annabi a gurbinka.
17Zai kasance Yehu zai kashe duk wanda ya tsere daga takobin Hazayel, Elisha zai kashe duk wanda ya tsere daga takobin Yehu.18Amma zan barwa kaina mutum dubu bakwai na Isra'ila don kaina, waɗanda ba su russuna wa Ba'al da gwiwonsu ba, ba su kuma sumbace shi da bakunansu ba."
19Iliya fa ya tashi daga wurin ya sami Elisha ɗan Shafat, wanda ke noma da shanun huɗa karkiya goma sha biyu, shi kansa kuma yana huɗa da karkiyar sha biyu. Iliya ya bi ta kusa da Elisha ya jefa masa alkyabbarsa.20Sai Elisha ya bar shanun noman, ya sheka da gudu gun Iliya ya ce, "Idan ka yarda bari in sumbaci mahaifina da mahaifiyata, in yi bankwana da su, sa'an nan in zo in bi ka." Sai Iliya ya ce da shi, "Koma, amma ka yi tunanin abin da na yi maka."
21Elisha ya komo daga wurin Iliya ya kama shanun noman, ya yanka dabbobin, ya dafa namansu da itace daga karkiyoyin. Sai ya ba mutane suka ci. Sa'an nan ya tashi, ya bi Iliya, ya zama mai taimakonsa.

20

1Ben-Hadad sarkin Aram kuwa ya tara dukkan sojojinsa. Akwai sanannun sarakuna talatin da biyu da suke tare da shi, da dawakai da karusai. Ya haura ya kai wa Samariya hari ya kuwa yi yaƙi da ita.2Ya aika da jakadu zuwa cikin birni wurin Ahab sarkin Isra'ila, ya ce da shi, "Ben Hadad ya ce wannan:3Azurfarka da zinariyarka nawa ne. Matanka da 'ya'yanka, masu kyau, nawa ne.'"

4Sarkin Isra'ila ya amsa ya ce, "Ya kasance kamar yadda ka ce, shugabana, sarki. Ni da dukkan abin da na ke da shi naka ne."5Jakadun suka dawo kuma suka ce, "Ben-Hadad ya ce wannan, 'Na aika maka da magana cewa dole ka ba ni azurfarka, da zinariyarka, da matanka da 'ya'yanka.6Amma zan aiko barorina wurinka gobe a dai-dai wannan lokacin, za su bincike gidanka da gidajen barorinka. Za su kwashe duk abin da ka ke da shi daga hannuwanka su ɗauke abubuwan da suka gamshi idanuwansu.'"
7Sai sarkin Isra'ila ya kirawo dukkan dattawan ƙasar ga baki ɗaya ya ce, "Idan kun yarda ku duba yadda wannan mutum ya ke neman rikici. Ya aiko wuri na domin in ba shi matana da 'ya'yana da azurfa da zinariyata, ni kuwa ban yardar masa ba."8Dukkan dattawa da dukkan mutane suka cewa Ahab, "Kada ka saurare shi ko ka da mu da abin da ya ke so."
9Ahab ya ce da jakadun Ben-Hadad, "Ku faɗa wa shugabana sarki, 'Na yarda da dukkan abin da ka aiko barorinka su yi da farko, amma ba zan yarda da wannan buƙatar ta biyu ba.'" Jakadun kuwa suka koma da wannan amsa ga Ben-Hadad.10Sai Ben-Hadad ya sake aikawa da saƙonsa ga Ahab, ya ce, "Bari alloli su yi mani haka harma fiye idan tokar Samariya ba za ta isa domin dukkan mutane waɗanda suka biyo ni kowannensu ya sami ɗan kaɗan ba.
11Sarkin Isra'ila ya amsa ya ce, "Ku faɗa wa Ben-Hadad, 'Ba wani wanda ya ke adali da zai sa sulke ya yi fahariya kamar ya ci yaƙin.'"12Ben-Hadad ya ji wannan saƙo sa'ad da ya ke sha, shi da sarakuna da ke ƙarƙashinsa waɗanda suke cikin rumfunoni. Ben-Hadad ya umarce mutanensa, "Kowa ya tsaya a wurinsa domin yaƙi. "Suka shirya kansu suka tsaya domin yaƙin ya fada wa birnin.
13Sai ga wani annabi ya zo wurin Ahab sarkin Isra'ila ya ce, "Yahweh ya ce, "Ka ga wannan babban taron sojoji? Duba, zan ba da su a hannunka yau, za ka sani ni ne Yahweh.'"14Ahab ya amsa, "Wane ne zai yi jagorar babbar rundunar?" Yahweh ya amsa ya ce, "Ta wurin matasan ofisoshi waɗanda su ke yi wa gwamnonin larduna hidima." Sai Ahab ya ce, "Wane ne zai fara yaƙin?" Yahweh ya amsa, "Kai ne."15Sai Ahab ya tara matasan ofisoshi waɗanda suke yi wa gwamnonin larduna hidima. Su ɗari 232. Bayansu kuma ya tara dukkan sojoji da dukkan rundunar yaƙIn Isra'ila, jimilla dubu bakwai.
16Suka tafi da tsakar rana. Ben-Hadad yana a buge da abin sha a rumfa, shi da sarakunan da ke ƙarƙashinsa su talatin da biyu waɗanda suke goyan bayansa.17Matasan ofisoshi waɗanda suke yi wa gwamnonin larduna hidima suka fara wucewa gaba. Sai Ben-Hadad ya ji labari ta wurin waɗanda ya aike su, "Mutane na zuwa daga Samariya."
18Ben-Hadad yace, "Ko da sun zo don salama ko da yaƙi, ku kama su da rai."19Matasan ofisoshi waɗanda suke wa gwamnonin larduna hidima sun fita daga birnin sojoji kuma suna bin su.
20Kowa ya kashe abokin gãbarsa, Aremiyawa suka gudu. Isra'ila kuwa suka rutume su. Ben-Hadad sarkin Aram ya tsere akan doki tare da mahayan dawakai.21Sarkin Isra'ila ya fita ya ƙwace dawakai da karusai, ya kashe Aremiyawa masu yawa.
22Sa'an nan annabi ya je wurin sarkin Isra'ila ya ce da shi, "Tafi, ka ƙarfafa kanka, ka fahimci shirin abin da zaka yi, gama da juyuwar shekara sarkin Aram zai zo maka da harin yaƙi."23Barorin sarkin Aram suka ce da shi, "Na su allahn allah ne na tuddai. Don haka suka fi mu ƙarfi. Amma yanzu bari mu yi yaƙi da su a kwari, ba bu shakka za mu fi su ƙarfi.
24Dole ka yi wannan: ka fitar da sarakuna daga matsayinsu na shugabanci ka maida hafsoshin sojoji a mamadinsu.25Ka tara sojoji kamar yawan waɗanda ka rasa-dawakai domin dawakai da karusai domin karusai, mu kuma za mu yi yaƙi da su a kwari. Babu shakka za mu yi ƙarfi fiye da su." Ben-Hadad ya saurari shawararsu ya yi yadda suka ba da shawarar.
26Bayan farkon sabuwar shekara, Ben-Hadad ya tara Suriyawa su ka haura zuwa Afek su yi yaƙi da Isra'ila.27Mutanen Isra'ila suka taru aka ba su guzuri da za su yi yaƙi da su. Mutanen Isra'ila suka kafa sasani a gabansu kamar kananan garkuna biyu na awaki, amma Aremiyawa suka cika ƙasar.
28Sai mutumin Allah ya zo kusa ya yi magana da sarkin Isra'ila ya ce, "Yahweh ya ce: 'Gama da ya ke Aremiyawa sun ce Yahweh shi allah na tuddai ne, amma ba shi ne allah na kwari ba, zan ba da dukkan wannan babban taron sojojin nan a hannunka, za ka sani Ni ne Yahweh.'"
29Sojojin suka kafa sansani daura da juna har kwana bakwai. A rana ta bakwai ɗin yaƙi ya fara. Mutanen Isra'ila suka kashe Aremiyawa nan ƙafa100,000 a rana ɗaya.30Sauran suka gudu zuwa Afek, cikin birni, garun kuma ya faɗo akan mutune dubu ashirin da bakwai waɗanda suka rage. Ben-hadad kuwa ya gudu ya shiga cikin birni, cikin ƙuryar ɗaki.
31Barorin Ben-Hadad suka ce da shi, "Duba yanzu, mun ji cewa sarakunan gidan Isra'ila sarakuna ne masu jinƙai. Idan ka yarda bari mu sa tufafin makoki mu ɗaura igiyoyi a kawunanmu, mu tafi wurin sarkin Isra'ila. Watakila zai bar ka da rai."32Sai suka sa tufafin makoki suka ɗaura igiyoyi a kawunansu suka tafi wurin sarkin Isra'ila suka ce, "Baranka Ben-Hadad ya ce, 'Idan ka yarda ka bar ni da rai.'" Ahab yace, "Har yanzu yana da rai? Shi ɗan'uwana ne."
33Yanzu mutanen suna sauraro kowace alama daga wurin Ahab, sai su yi saurin amsa masa, "I, ɗan'uwanka Ben-Hadad yana da rai." Sai Ahab ya ce, "Ku tafi ku kawo shi." Sai Ben-Hadad ya zo wurin sa, Ahab ya sa ya shiga da shi cikin karusarsa.34Ben-Hadad ya ce da Ahab, "Zan dawo maka da biranen da tsohona ya ƙwace daga wurin tsohonka, kai kuma za ka yi kasuwanci a Damaskus, kamar yadda tsohona ya yi a Samariya." Ahab ya ba shi amsa, "Zan bar ka, ka tafi a kan alƙawari." Ahab ya yi alƙawari da shi, sa'an nan ya bar shi ya tafi.
35Sai ga wani mutum, ɗaya daga cikin 'ya'yan annabawa, ya ce da ɗaya daga abokansa annabawa bisa ga maganar Yahweh, "Idan ka yarda ka buge ni." Amma mutumin ya ƙi ya buge shi.36Sai annabin ya ce da abokinsa annabi, "Da ya ke ba ka yi biyayya da muryar Yahweh ba, da zarar ka tashi daga wurina, zaki zai kashe ka." Da ya tashi daga wurinsa kuwa zaki ya zo ya gamu da shi, ya kashe shi.
37Annabin kuma ya sami wani mutum ya ce, "Idan ka yarda ka buge ni." Mutumin kuwa ya buge shi har ya ji masa ciwo.38Sai annabin ya tafi ya jira sarki a hanya; ya bad da kama, ya rufe idanunsa da ƙyalle.
39Sa'ad da sarki ya ke wucewa, sai annabi ya kira sarki ya ce, "Ni baranka na tafi wurin yaƙi mai zafi, sai soja ya tsaya ya kawo mani abokin gãba ya ce, 'Kula da wannan mutum. Idan wani abu ya sa ya tsere, za ka ba da ranka domin ransa, ko kuma ka biya talanti ɗaya na azurfa.'40Gama da ya ke baranka yana fama da kai da kawowa, abokin gãbar soja ya tsere." Sai sarkin Isra'ila ya ce da shi, "Wannan shi ne irin hukuncin da zan yi - kai da kanka ka shawarta haka."
41Sai annabi ya yi sauri ya cire ƙyalle daga idanunsa, sarkin Isra'ila ya gane, ashe ɗaya daga cikin annabawa ne.42Annabin ya cewa sarki, "Yahweh ya ce, 'Da ya ke ka bar shi ya tafi daga hannunka mutum wanda na ƙaddara ga mutuwa, ranka zai zama a maimakon ransa, mutanenka kuma maimakon mutanensa.'"43Sarkin Isra'ila kuwa ya tafi gidansa da baƙinciki, a Samariya.

21

1A wani lokaci kuma, Nabot Bayezrile yana da gonar inabi a Yezriyel, kusa da fãdar Ahab, sarkin Samariya.2Ahab ya yi magana da Nabot cewa, "Ka ba ni gonar inabinka, don in mai da ita lambu, domin gonar tana kusa da gidana. Ni kuwa zan ba ka wata gonar inabin mai kyau, ko kuma idan kana so, sai in biya ka tamanin kuɗinta."

3Amma Nabot ya amsa wa Ahab, "Yahweh ya sawwake in ba ka gãdon kakannina."4Ahab ya koma fãdarsa da baƙinciki, saboda amsar da Nabot Bayezrile ya ba shi da ya ce, "Ni ba zan ba ka gãdon kakannina ba." Ya zauna akan gado, ya juya fuskarsa, ya ƙi cin kowanne abinci.
5Yezebel matarsa ta zo wuinsa, ta ce da shi, "Me ya sa zuciyarka ta da mu, har ka ƙi cin kowanne abinci?"6Ya amsa mata, "Domin na yi magana da Nabot Bayezrile, na ce masa, 'Ya ba ni gonar inabinsa don in saya, idan ya yarda, zan ba ka wata gonar inabin ta zama ta ka.' Sai ya amsa mani, 'ba zan ba ka gonar inabina ba.'"7Yezebel matarsa ta amsa masa, "Ba kai ne ka ke mulkin Isra'ila ba? Tashi ka ci abinci; bari zuciyarka ta yi farinciki, zan samar maka gonar inabin Nabot Bayezrile."
8Yezebel ta rubuta wasiƙu da sunan Ahab, ta hatimce su da hatiminsa, sa'an nan ta aika da su zuwa ga dattawa da mawadata masu kuɗi waɗanda suke zaune tare da shi a taruruka, da waɗanda suke zama kusa da Nabot.9Ta rubuta a wasiƙun, cewa, "A yi shelar azumi, a sa Nabot a gaban mutane.10A kuma sa 'yan iskan mutane biyu su yi ta zarginsa, su riƙa cewa, 'Ka zagi Allah da sarki.'" Sa'an nan ku tafi da shi waje, ku jajjefe shi da duwatsu har ya mutu.
11Mutanen birnin da dattawa da masu arzaki da ke zaune a birnin Nabot, suka yi yadda Yezebel ta sa su yi, kamar yadda aka rubuta a wasiƙun da ta aika masu.12Su kuwa suka yi shelar azumi, suka zaunar da Nabot a gaban mutane.13Sai mutune biyu suka zo, suka zauna a gaban Nabot suka yi ta shaidar zur akan Nabot a gaban mutane, cewa, "Nabot ya zagi Allah da sarki." Sai suka ɗauke shi wajen birni suka jajjefe shi da duwatsu har ya mutu.14Dattawa suka aika da magana ga Yezebel, cewa, "An jajjefe Nabot da duwatsu ya mutu."
15Yayin da Yezebel ta ji labari an jajjefe Nabot da duwatsu har ya mutu, sai ta ce da Ahab, "Tashi ka mallaki gonar inabin Nabot Bayezrile wadda ya ƙi ya ba ka, ka ba shi kuɗi, gama Nabot ba shi da rai, ya mutu."16Da Ahab ya ji labarin Nabot Bayezrile ya mutu, sai ya tashi ya gangara zuwa gonar inabin Nabot Bayezrile ya ɗauke ta ya mallake ta.
17Sai maganar Yahweh ta zo ga Iliya Batishbe, cewa,18"Tashi ka tafi ka sadu da Ahab sarkin Isra'ila, wanda ya ke zaune a Samariya. Yana cikin gonar inabin Nabot, inda ya tafi don ya mallake ta.
19Dole ka yi magana da shi ka ce Yahweh ya ce, 'Ka yi kisa, ka kuma ɗauki abin da ya mallaka? Sai ka faɗa masa Yahweh ya ce, 'A wurin da karnuka suka lashe jinin Nabot, a nan ne kuma karnuka za su lashe jininka, i, jininka.'"20Ahab ya ce da Iliya, "Ka same ni ko, maƙiyina?" Iliya ya amsa, na same ka, gama ka bada kanka ga aikata abin da ke mugunta a fuskar Yahweh.
21Yahweh yace wannan da kai: 'Duba, zan kawo maka masifa, in shafe ka, in datse daga gare ka kowanne ɗa namiji bawa ko 'yantarcen mutum a Isra'ila.22Zan sa iyalinka kamar iyalin Yerobowam ɗan Nebat, su kuma zama kamar iyalin Ba'asha ɗan Ahija, saboda ka sani har na yi fushi, ka kuma sa mutanen Israila sun yi zunubi.'
23Yahweh kuma ya sake yin magana akan Yezebel, cewa, 'Karnuka za su cinye Yezebel a gefen katangar Yezriyel.'24Duk wanda ya ke na Ahab da zai mutu a birni karnuka ne za su cinye shi, tsuntsayen sararin sama ne kuma za su cinye duk wanda ya mutu a saura."
25Babu wani kamar Ahab, da ya ba da kansa ga aikata mugunta a fuskar Yahweh, wanda matarsa Yezebel ta zuga shi yin zunubi.26Ahab ya yi abin banƙyama ƙwarai saboda ya bi gumaka, kamar yadda Amoriyawa suka yi, waɗanda Yahweh ya kore su a gaban mutanen Isra'ila.
27Da Ahab ya ji waɗannan kalmomi, ya yage tufafinsa ya sa na makoki a jikinsa, ya yi azumi, ya kuma kwanta a tsummokaran makoki, ya zama da damuwa.28Sai maganar Yahweh ta zo ga Iliya Batishbe, cewa,29"Ka ga yadda Ahab ya ƙasƙantar da kansa a gabana? Da ya ke ya ƙasƙantar da kansa a gabana, ba zan kawo masifar a zamaninsa ba; sai dai a zamanin ɗansa ne, zan kawo masifar a cikin iyalinsa."

22

1Shekaru uku da suka wuce ba a yi yaƙi tsakanin Aram da Isra'ila ba.2Sai a cikin shekara ta uku ɗin, Yehoshafat sarkin Yahuda ya tafi wurin sarkin Isra'ila.

3Sarkin Isra'ila ya ce da barorinsa, "Ko kun san Ramot Giliyad tamu ce, amma ba ma yin komai domin mu ƙwace ta daga hannun sarkin Aram?"4Ya ce da Yehoshafat, "Za ka tafi tare da ni zuwa yaƙi a Ramot Giliyad?" Yehoshafat ya amsa wa sarkin Isra'ila, "Ni kamar ka ne, mutanena kuma kamar mutanenka ne, dawakaina suna kamar naka ne."
5Yehoshafat ya cewa sarkin Isra'ila, "Idan ka yarda ka nemi shawara daga Yahweh duk abin da za ka yi tukuna."6Sai sarkin Isra'ila ya tara annabawa wuri ɗaya, mutane ɗari huɗu ne, ya ce da su, "In tafi in yi yaƙi a Ramot Giliyad, ko kuwa kada in tafi?" Suka ce, "Ka haura, gama Ubangiji zai ba da ita a hannun sarki."
7Amma Yehoshafat ya ce, "Ba wani annabin Yahweh ne a nan wanda za mu nemi shawara daga wurinsa?8Sarkin Isra'ila ya cewa Yehoshafat, "Da sauran mutum ɗaya wanda za mu iya mu nemi shawara daga Yahweh da zai taimaka, Mikaiya ɗan Imla, amma ina ƙinsa gama bai taɓa yin wani annabcin alheri a kaina ba, amma sai dai na masifa." Amma Yehoshafat ya ce, "Kada sarki ya ce haka."9Sa'an nan sarkin Isra'ila ya kirawo wani bafade, ya bada umarni, "Kawo Mikaiya ɗan Imla, yanzu a nan."
10Ahab sarkin Isra'ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suna zaune akan gãdon sarautarsu saye da tufafinsu a dandalin ƙofar Samariya, da dukkan annabawa suna ananbci a gabansu.11Zedekiya ɗan Kena'ana ya yi wa kansa ƙahonin ƙarfe, ya ce, "Yahweh ya faɗi wannan: 'Tare da waɗannan za ka tunkuyi Aremiyawa har su hallaka.'"12Dukkan annabawan suka yi annabci iri ɗaya, cewa, "Ka haura zuwa Ramot Gileyad, zaka yi nasara, domin Yahweh zai ba da ita a hannun sarki."
13Ɗan saƙo wanda ya tafi ya kira Mikaiya ya yi magana da shi, cewa, duba yanzu, maganar annabawa abubuwa ne mai kyau ga sarki da baki ɗaya. Idan ka yarda bari maganarka ta zama kamar tasu ka faɗi abu mai kyau."14Mikaiya ya amsa, "Kamar yadda Yahweh ke raye, ga abin da Yahweh ya ce da ni zan faɗa."15Da ya zo gaban sarki, sarki ya ce da shi, "Mikaiya, mu tafi Ramot Giliyad don yaƙi, ko a'a?" Mikaiya ya amsa masa, "Ka haura za ka yi nasara, Yahweh zai ba da ita a hannun sarki."
16Sarki ya ce masa, "Sau nawa zan neme ka da ka rantse za ka faɗa mani kome idan ba gaskiya ba, da sunan Yahweh?"17Mikaiya ya ce, "Na ga dukkan Isra'ila a warwatse akan tuddai, kamar tumaki waɗanda ba su da makiyayi, Yahweh ya ce, "Waɗannan ba su da makiyayi. Bari kowanne mutum ya koma gidansa da salama."
18Sarkin Isra'ila ya cewa Yehoshafat, "Ban faɗa maka ba, ba zai yi wani annabcin alheri a kaina ba, amma sai dai na masifa?"19Mikaiya yace, "Saboda haka ka ji maganar Yahweh: na ga Yahweh yana zaune a kursiyansa tare da dukkan mala'ikun sama suna tsaye wajen damarsa da hagunsa.20Yahweh yace, 'Wa zai yaudari Ahab, ya tafi ya faɗawa Ramot Giliyad?' Ɗaya daga cikin su ya faɗi wannan, wani kuma ya faɗi abu kaza.
21Sai wani ruhu ya zo gaba, ya tsaya a gaban Yahweh, ya ce, 'Ni zan yaudare shi.' Yahweh ya ce da shi, 'Ta ya ya?'22Sai ruhun ya amsa, 'Zan tafi in zama ruhun ƙarya a bakin dukkan annabawansa. 'Yahweh ya amsa, 'Kai za ka iya yaudarsa, za ka kuma yi nasara sosai. Tafi yanzu ka yi.'23Duba yanzu, Yahweh ya sa ruhun ƙarya a bakin dukkan waɗannan annabawansa, Yahweh kuma ya zartar maka da masifa."
24Sai Zedekiya ɗan Kan'ana ya zo kusa ya mari Mikaiya a kumatu, ya ce, "Wacce hanya Ruhun Yahweh ya bar ni har ya zo wurinka ya yi magana da kai?"25Mikaiya yace, "Duba, za ka sani a ranar nan, lokacin da ka gudu ka shiga har ƙuryar ɗaki don ka ɓuya."
26Sarkin Isra'ila ya ce da baransa, "Ku kama Mikaiya, ku kai shi wurin Amon, gwamnan birni, da Yowash, ɗana.27Ku ce da shi, 'Sarki ya ce, a jefa wannan mutum a kurkuku a riƙa ciyar da shi da waina kaɗan da ruwan sha kaɗan, har sai na komo lafiya.'"28Sai Mikaiya yace, "Idan har ka dawo lafiya, Yahweh bai yi magana da ni ba." Ya ƙara da cewa, "Ku saurari wannan, dukkan ku mutane."
29Ahab sarkin Isra'ila, da Yehoshafat sarkin Yahuda, sun tafi Ramot Giliyad.30Sarkin Isra'ila ya ce da Yehoshafat, "Zan bad da kamata in tafi wurin yaƙi, amma kai ka sa tufafin sarautarka." Sai sarkin Isra'ila ya bad da kamarsa ya tafi wurin yaƙi.
31Yanzu sarkin Aram ya rigaya ya umarci shugabannin karusan yaƙinsa su talatin da biyu, cewa, "Kada ku yi yaƙi da kowa komai matsayin sojojinsa. Sai dai sarkin Isra'ila kaɗai."32Sa'ad da shugabannin karusai suka ga Yehoshafat sai suka ce, "Babu shakka wannan shi ne sarkin Isra'ila." Sun juya don su yi yaƙi da shi, Yehoshafat kuwa ya yi ihu.33Da shugabannin karusan yaƙi suka gane ba sarkin Isra'ila ba ne, sai su ka juya suka dena binsa.
34Sai wani mutum ya shilla kibiya kawai, sai ta sami sarkin Isra'ila a tsakanin ƙafar sulkensa. Ahab ya ce da mai kora karusarsa, "Ka juya ka ɗauke ni daga yaƙin nan gama an yi mani rauni sosai."
35A ran nan yaƙi ya yi tsanani ƙwarai, aka tallafi sarki a cikin karusarsa a gaban Aremiyawa. Ya mutu da yamma. Jinin yana fitowa daga raunin da aka yi masa yana zuba a cikin karusar.36A lokacin faɗuwar rana aka yi wa sojoji shelar cewa, "Kowanne mutum ya koma birninsa kuma kowanne mutum ya koma jiharsa.
37Sarki Ahab ya mutu, aka kawo shi Samariya, su ka bizne shi.38Su ka wanke karusarsa a tafkin Samariya, karnuka su ka lashe jininsa (wannan shi ne wurin da karuwai su ke yin wanka a tafkin) kamar yadda Yahweh ya furta.
39Game da sauran al'amuran Ahab da dukkan abin da ya yi, da gidan da ya gina na hauren giwa da biranen da ya gina, ba suna rubuce a littafin tarihin sarakunan Isra'ila ba?40Ahab ya yi barci tare da kakaninsa, Ahaziya ɗansa ya zama sarki a gurbin mahaifinsa.
41Yehoshafat ɗan Asa ya fara sarauta a Yahuda a shekara ta huɗu ta Ahab sarkin Isra'ila.42Yehoshafat yana da shekaru talatin da biyar sa'ad da ya fara sarauta, ya yi sarauta a Yerusalem yana da shekaru ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa Azuba 'yar Shilhi.
43Ya yi tafiya cikin hanyoyi irin na Asa, mahaifinsa; bai karkace daga gare su ba; ya yi abin da dai-dai a fuskar Yahweh. Duk da haka ba a ɗauke wuraren tsafi na tuddai ba. Mutanen sun ci gaba da miƙa hadayu da ƙona turare a tuddan.44Yehoshafat ya yi zaman salama da sarkin Isra'ila.
45Sauran ayyuka game da Yehoshafat, da ƙarfin da ya nuna, da yadda ya yi yaƙi, ba suna rubuce a littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?46Ya kori sauran karuwai daga ƙasar waɗanda suna nan tun zamanin mahaifinsa Asa.47Babu sarki a Idom, amma wakili ne ya yi mulki a wurin.
48Yehoshafat ya yi jiragen ruwa, za su tafi Ofir domin zinariya, amma ba su iya tafiya ba, gama jiragen sun farfashe a Eziyon Geber.49Sai Ahaziya ɗan Ahab ya ce da Yehoshafat, "Ka bar barorina su tafi tare da naka a cikin jirage." Amma Yehoshafat bai yarda ba.50Yehoshafat ya yi barci tare da kakaninsa aka bizne shi a wurin su a birnin Dauda, kakansa; Yahoram ɗansa ya zama sarki a gurbin mahaifinsa.
51Ahaziya ɗan Ahab ya fara sarauta a kan Isra'ila a Samariya a shekara ta goma sha bakwai ta Yehoshafat sarkin Yahuda, ya yi sarauta shekara biyu a Isra'ila.52Ya yi abin da ke mugu a fuskar Yahweh, ya yi tafiya ta hanyar mahaifinsa, a cikin hanyar mahaifiyarsa, da hanyar Yerobowom ɗan Nebot, wanda ya sa Isra'ila yin zunubi.53Ya bauta wa Ba'al ya yi masa sujada, ya kuma tsokani Yahweh na Isra'ila ya yi fushi, kamar yadda mahaifinsa ya yi.

Littafin sarakuna na biyu

1

1Mowab ta tayar wa Isra'ila a bayan mutuwa Ahab.2To sai Ahaziya ya faɗo daga sakatar gidan samansa a Samariya, har ya yi rauni. Sai ya aika 'yan saƙo ya ce da su, "Ku je ku tambayi Ba'al Zebub, allahn Ekron, ko zan warke daga wannan raunin."

3Amma mala'ikan Yahweh yace da Iliya Batishbe, "ka tashi ka je ka sadu da 'yan saƙon sarkin Samariya, ka tambaye su, ko domin ba Allah ne a Isra'ila shi ya sa kuka je kuka tuntuɓi Ba'al Zebub, allahn Ekron?4Domin haka Yahweh ya ce, ba za ka sauko daga wannan gadon da ka hau ba; a maimakon haka za ka mutu.'"' Daga nan sai Iliya ya tafi.
5Bayan 'yan saƙon sun dawo wurin Ahaziya, sai ya ce da su, "Meyasa ku ka dawo?"6suka ce da shi wani mutum ne ya zo ya gamu da mu ya ce mana, ku koma wurin wanda ya aiko ku ku ce da shi, "Yahweh ya faɗi wannan; Ashe babu Allah ne a Isra'ila da ka aika 'yan saƙo Ekron su tambayi Ba'al Zebub? saboda haka ba za ka tashi daga gadon jinyarka ba, a maimakon haka hakika zaka mutu."""
7Ahaziya yace da 'yansaƙonsa "wanne irin mutum ne shi, mutumin da ya zo wurinku ya faɗa muku wannan magana"?8Suka ce da shi yana saye da rigar da a ka yi da gasusuwa da kuma ɗammara ta fata a kwankwasonsa," sai sarkin ya amsa ya ce Iliya ne Batishbe."
9Sai sarki ya aika jami'ai da sojoji hamsin wurin Iliya. Jami'an suka je wurin Iliya a inda ya ke zaune a saman dutse. Jami'an suka yi magana da shi cewa, "Kai mutumin Allah, sarki ya ce ka sauko ƙasa."10Iliya ya amsa ya ce da jami'an, "In ni mutumin Allah ne, bari wuta tasauko daga sama ta ƙone mutanenku guda hamsin." Wuta ta sauko daga sama ta ƙone mutanensa hamsin tare da shi.
11Sai sarki Ahaziya ya sake yin aike wurin Iliya da wata runduna ta mutum hamsin tare da hafsa. shi ma wannan hafsan ya sake cewa da Iliya, "Kai mutumin Allah, sarki ya ce ka sauko da sauri."12Iliya ya amsa ya ce da su, in ni mutumin Allah ne, bari wuta ta sauko daga sama ta ƙone ku tare da mutanenka guda hamsin." Sai wuta ta sake saukowa daga sama ta ƙone shi tare da mutanensa guda hamsin.
13Sarki kuma ya sake aikawa da ƙungiya ta uku tare da mazaje hamsin mayaƙa. wannan hafsan sai ya je ya durƙusa a gwiwarsa a gaban Iliya, ya roƙe shi ya ce da shi, "kai mutumin Allah ina roƙonka bari raina da na waɗannan sojoji hamsin ya sami daraja a gabanka.14Hakika wuta ta sauko daga sama ta ƙone rundunoni guda biyu na farko tare da hafsoshinsu, amma yanzu ina roƙo bari raina ya zama da daraja a gabanka."
15Sai mala'ikan Yahweh yace da Iliya, "Ka sauka ƙasa tare da shi. kada ka ji tsoronsa." Sai Iliya ya tashi ya sauka ya tafi tare da shi zuwa wurin sarki.16Can sai Iliya ya ce da Ahaziya, "Wannan shi ne abin da Yahweh ya ce, 'Ka aika manzanni su tambayi Ba'al Zebub allan Ekron. Shin domin ba bu Allah ne a Isra'ila wanda zaka tambaya domin samun sadarwa? to yanzu hakika ba zaka sauko daga gadon da ka hau ba hakika za ka mutu."
17Don haka sarki Ahaziya ya mutu bisa maganar Yahweh wadda Iliya ya furta. Sai Yorom ya gaji sarautarsa, a shekara ta biyu ta Yehoram ɗan Yehoshafat sarkin Yahuda, saboda Ahaziya ba shi da ɗa.18Game kuma da sauran abubuwa game da Ahaziya, ashe ba a rubuta su a littafin ayyukan sarakunan Isra'ila ba?

2

1To sai ya zama a lokacin da Yahweh zai ɗauki Iliya zuwa sama ta guguwa, da Iliya ya rabu da Elisha zuwa Gilgal.2Iliya ya ce da Elisha "ka jira nan ina roƙonka domin Yahweh ya aike ni zuwa Betel, Elisha ya ce da shi "Muddin Yahweh na raye, kana kuma raye, ba zan bar ka ba." To sai suka tafi Betel tare.

3"Ya'yan annabawa da ke a Betel suka zo wurin Elisha suka ce da shi, Ko ka san Yahweh zai ɗauke shugabanka daga gare ka yau?" Elisha ya amsa masu, i na sani, amma kada ku yi magana tukuna."4Iliya ya ce da shi, Elisha ka jira a nan, Domin Yahweh ya aike ni Yeriko." Sai Elisha ya amsa, "Muddin Yahweh na raye, kai kuma kana raye, ba zan rabu da kai ba." Domin haka suka tafi Yeriko.
5Sai 'ya'yan annabawa da ke a Yariko suka zo wurin Elisha suka ce da shi, "Ko ka san cewa yau Yahweh zai ɗauke shugabanka da ga gare ka? "Elisha ya amsa, "I na sani, amma ka da ku yi maganar tukuna."6Sai Iliya ya ce da shi, "Ka tsaya nan, domin Yahweh ya aike ni Yodan.'" Elisha ya amsa, Muddin Yahweh na raye, kai kuma kana raye, Ba zan rabu da kai ba." domin haka su biyun suka tafi.
7Can an jima sai 'ya'yan annabawa hamsin suka tsaya a gefensu da ɗan nisa su kuma biyun suka tsaya a gefen Yodan.8Iliya ya cire tufafinsa, ya naɗe shi sai ya bugi ruwa da shi. sai rafin ya rabu biyu ta kowanne gefe su biyu suka taka sandararriyar ƙasa suka ƙetare.
9Bayan sun ƙetare, sai Iliya ya ce da Elisha, "ka roƙi abin da zan yi maka kafin a ɗauke ni daga gare ka." Elisha ya amsa, ina roƙo a ba ni riɓi biyu na ruhunka ya sauko a kaina."10Iliya ya amsa, "Ka roƙi abu mai wuya. amma duk haka, in ka gan ni a lokacin da aka ɗauke ni daga gare ka, wannan zai faru sabo domin ka, amma in ba haka ba, ba zai faru ba."
11Da suka ƙara tafiya suna magana, sai ga karusai na wuta da dawakai na wuta suka baiyana, waɗanda suka raba tsakanin su, Iliya ya tafi sama ta guguwa.12Da Elisha ya gani ya yi kuka, ya ce "Babana, Babana, karusai na Isra'ila da mahaya dawakansu!" Bai ƙara ganin Iliya ba, sai ya ɗauki tufafinsa ya keta su biyu.
13Sai ya ɗauki alkyabar Iliya da ta faɗo masa, ya koma ya tsaya a bakin Yodan. Ya bugi ruwan da tufafin Iliya wanda ya faɗo ya ce, "Ina Yahweh, Allah na Iliya?"14Bayan ya bugi ruwan sai ruwan ya rabu biyu ta kowanne gefe sai Elisha ya ƙetare.
15Lokacin da 'ya'yan annabawa da ke Yeriko suka ga ya ƙetaro daga wurinsu, suka ce "Ruhun Iliya ya sauko akan Elisha!" Sai suka zo domin su tare shi, suka sunkuyar da kawunansu a ƙasa a gabansa.16Suka ce da shi, Duba yanzu a cikin barorinka akwai mazaje hamsin majiya ƙarfi. Ka bar su su je su nemo shugabanka, ƙila ko Ruhun Yahweh ya ɗauke shi ya kai shi bisa wasu duwatsu, ko kuma waɗansu kwarurruka." Elisha ya amsa ya ce kada ku aike su."
17Amma bayan sun matsa masa sai ya ji nauyi, ya ce "ku aike su." Suka aiki mazaje hamsin suka yi ta nema har kwana uku amma basu same shi ba.18Suka dawo wurin Elisha, a lokacin da yake a Yeriko, sai ya ce da su, "Ashe ban ce da ku kada ku je ba'?"
19Mutanen birnin suka ce da Elisha, "Duba muna roƙon ka, halin da muke ciki a garin nan yana da faranta rai sosai kamar yadda shugabana ya gani, amma ruwan ba shi da kyau ƙasar kuma ba ta bada hatsi."20Elisha ya amsa, "Ku samo mini sabon daro ku sa gishiri a cikinsa," domin haka suka kawo masa daro.
21Sai Elisha ya fita ya tafi mafitar ruwan rafin ya sa gishirin a cikinsa; sai ya ce ga abin da Yahweh ya ce, na warkar da waɗannan ruwaye. daga yanzu ba za a sami mutuwa ko rashin 'ya'ya ba a cikin ƙasar.'"22Domin haka ruwan ya gyaru har ya zuwa yau, ta wurin maganar Elisha.
23Sai ya tafi can zuwa Betel. Lokacin da yake tafiya akan hanya, sai samari suka fito daga birni suka yi masa ba'a; suka ce da shi, "Kai mai saiƙo ka tafi, kai mai saiƙo ka tafi!"24Sai Elisha ya duba gefensa ya gan su; Sai ya yi kira ga Yahweh ya la'antasu. Sai matan damisa guda biyu suka fito daga kogo suka raunata samari guda arba'in da biyu.25Daga nan sai Elisha ya bar wurin ya tafi Tsaunin Karmel, daga can kuma sai ya koma Samariya.

3

1A shekara ta sha takwas ta Yohoshafat sarkin Yahuda, Yoram ɗan Ahab ya fara mulkin Isra'ila a Samariya; ya yi mulki na shekaru sha biyu.2Ya yi abin da ke mugu a gaban Yahweh, amma ba kamar mahaifinsa da mahaifiyarsa ba; domin ya kawar da masujadar Ba'al da mahaifinsa ya gina.3Duk da haka ya riƙe zunubin Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra'ila ta yi zunubi, bai kauce daga gare su ba.

4Sai Mesha sarkin Mowab ya yi sausayar tumaki. Ya ba sarkin Isra'ila raguna 100,000 da kuma fatun raguna 100,000.5Amma bayan Ahab ya mutu, sai sarkin Mowab ya tayar wa sarkin Isra'ila.6Domin haka sarki Yoram ya gudu daga Samariya a wancan lokacin domin ya shirya sojojin Isra'ila domin yaƙi.
7Sai ya aika da saƙo ga Yohoshafat sarkin Yahuda, cewa, Sarkin Mowab ya tayar mani. Ko za ka tafi tare da ni yaƙi gãba da Mowab?" Yehoshafat ya amsa, "Zan je. Ni ma kamar ka ne, mutanena kuma kamar mutanenka ne, dawakaina kamar dawakanka ne."8Sai ya ce, "Ta wacce hanya zamu kai masu hari?" Yehoshafat ya amsa, "Ta hanyar jejin Idom."
9To sai sarakunan Isra'ila da Yahuda dana Idom suka yi ta kai da kawowa har tsawon kwanaki bakwai. Babu ruwan sha domin sojojinsu, babu kuma domin dawakansu ko kuma sauran dabbobi.10To sai sarkin Isra'ila ya ce, Me kenan? ko Yahweh ya tattaro sarakuna guda uku ya bashe su a hannun Mowab ne?"
11Amma Yehoshafat ya ce, Ko babu wani annabin Yahweh ne, da zamu tambayi Yahweh ta wurinsa?" Sai ɗaya daga cikin barorin sarkin Isra'ila ya amsa ya ce, "Eleisha ɗan Shafat yana nan, shi ne ya zuba ruwa a hannun Iliya."12Yehoshafat ya ce Maganar Yahweh na tare da shi." Domin haka Yehoshafat sarkin Isra'ila da sarkin Idom suka tafi wurinsa.
13Elisha yace da sarkin Isra'ila, Me zan yi da kai? Ka tafi wurin annabawan mahaifinka da mahaifiyarka." Sai sarkin Isra'ila ya ce da shi, A'a domin Yahweh ya kira waɗannan sarakuna guda uku tare domin ya bashe su a hannun Mowab."14Elisha ya amsa, Muddin Yahweh na raye a gaban wanda nake tsaye, tabbas in da ba domin ina ganin darajar kasancewar Yehoshafat sarkin Yahuda ba, da ba zan ji ku ko in dube ku ba.
15Amma yanzu ka kawo mani makaɗi."Sai mai kiɗa ya yi kiɗa, sai hannun Yahweh ya zo kan Elisha.16Ya ce Yahweh ya faɗi wannan, 'Ka sa tsirai su fito daga wannan kwarin.'17Domin Yahweh ya faɗi wannan, Ba zaka ga iska ba, ko kuma ka ga ruwan sama ba, amma wannan rafin zai cika da ruwa, zaku kuma sha, kai da bisashenka da dukkan dabbobinka.'
18Wannan abu ne mai sauƙi a gaban Yahweh, Zai kuma ba ka nasara akan Mowabawa.19Za ka kai hari akan ƙayatatcen birni da kowanne birni ku sare kowacce bishiya mai kyau, ku kuma busar da kowanne wuri mai fid da ruwa, ku kuma mayar da kowanne wuri kufai da duwatsu."
20Da safe a kusan lokacin miƙa hadaya, sai ga ruwa daga wajejen Idom; sai ƙasar ta cika da ruwa.
21To bayan duk Mowabawa sun ji cewa sarakuna sun zo su yaƙe su, sai suka tattara kansu, duk waɗanda kan iya ɗaukar makami, sai suka tsaya akan iyaka.22Suka tashi da sassafe rana kuma ta haskaka. Da Mowabawa suka ga ruwa kusa da su, ya zama ja kamar jini.23Sai suka ce "Wannan jini ne! Hakika an hallaka sarakuna, sun kuma karkashe juna! To yanzu Mowab, ku mu je mu kwashe su ganima!"
24Bayan sun zo sansanin Isra'ilawa, Isra'ilawa suka ba su mamaki suka hari Mowabawa, waɗanda suka tsere daga gabansu. Sojojin Isra'ila suka kori Mowabawa daga ƙasar, suka karkashe su.25Suka rushe biranen, da kuma duk wani yankin ƙasa kowannen su ya dinga tura dutse har sai da suka rufe birnin suka cike kowanne kwari na ruwa, suka cinye kowanne ɗan itaciya. Amma sojojin saye da kayan yaƙi suka sake kai hari a kansa.
26Bayan sarki Mesha na Mowab ya ga ya yi rashin nasara, sai ya ɗauki mayaƙa masu sara domin su hari sarkin Idom, amma suka kasa.27Sai ya ɗauki babban ɗansa, wanda zai yi sarauta bayansa, ya miƙa shi a matsayin baiko na ƙonawa akan ganuwa. Domin haka aka sami babbar hasala gãba da Isra'ila, sojojin Isra'ila kuma suka rabu da sarki Mesha suka koma ƙasarsu.

4

1Sai matar ɗaya daga cikin 'ya'yan annabawa ta zo tana kuka da Elisah, tana cewa, "Baranka mai gidana ya mutu, kuma ka sani baranka ya ji tsoron Yahweh. To wanda ke binsa bashi ya zo ya kwashe 'ya'yana maza guda biyu su zama bayinsa.'2'Sai Elesha ya ce da ita "Me ki ke so in yi maki? Ki faɗa mani abin da ki ke da shi a cikin gida? "Ta ce, baiwarka ba ta da komai a cikin gida, sai 'yar tukunya ɗaya ta mai."

3Sai Elisha yace, "Ki je ki aro tuluna daga maƙwabtanki, tulunan da ba komai a ciki. Ki aro gwargwadon yadda za ki iya arowa.4Dole ne ki shiga ɗaki ki kulle ƙofa da ke da iyalanki sai ki zuzzuba mai a cikin dukkan tulunan; sai ki kawar da waɗanda suka cika."
5Sai ta bar wurin Elesha ta kulle ƙofa ita da 'ya'yanta suka kawo mata tulunan, ta kuma cika su da mai.6Da tulunan suka cika, ta ce da ɗanta "Ka ƙaro mani wani tulun." Amma ya ce da ita, "Babu sauran tuluna." Sai man ya dena tsiyayowa.
7Sai ta zo ta faɗawa damutumin Allah. Ya ce "Je ki sayar da man; ki biya bashinki, sauran sai ki gudanar da rayuwarki tare da 'ya'yanki da shi."
8Wata rana Elisha ya je Shunem inda wata mata mai muhimmanci ke zama; Ta roƙe shi ya ci abinci tare da ita. Sau da dama Elisha yakan wuce ta wurin, ya kan bi ta wurin ya ci abinci.9Sai matar ta ce da mijinta, "Duba, yanzu na gane wannan mutum mai tsarki ne na Allah wanda yake wucewa kullun.
10Sai mu yi masa ɗan ɗaki a saman rufi domin Elisha, sai mu sa gado a cikin ɗakin da teburi da kujeru da fitila. Domin in ya zo wurin mu, sai ya zauna a can."11To da ranar ta zo da Elisha ya tsaya a can, sai ya shiga can ya huta.
12Elesha yace da Gehazi baransa, "Ka kira wannan Bashumaniye." Bayan ya kira ta, ta tsaya a gabansu.13Elisha yace da shi, "Ka ce da ita, kin sha duk wannan fama domin ki kula da mu. Me zamu yi maki? Ko ma yi magana da sarki ko kuma da Kwamandan soja?'" Ta amsa "Ina zama a cikin mutanena."
1414 Domin haka Elisha yace,"To me za mu yi mata?" Gehazi ya amsa, "Hakika ba ta da ɗa Mai gidanta kuma ya tsufa."15Domin haka Elisha ya amsa, "Kira ta." Bayan ya kira ta, sai ta tsaya a ƙofa.16Elisha ya ce shekara mai zuwa war haka za ki riƙe ɗa." Ta ce, "A'a ya shugabana da kuma mutumin Allah, kada ka yi wa baiwarka ƙarya."
17Amma matar ta yi ciki sai ta haifi ɗa a dai-dai lokacin da Elisha ya faɗa mata.18Bayan yaron ya yi girma, sai ya tafi wurin mahaifinsa wata rana, wanda ya ke tare da masu girbi. Sai ya ce da babansa, "Kaina, kaina."19Mahaifinsa ya ce da bayinsa, "Ku kai shi wurin mahaifiyarsa."20Lokacin da bayin suka ɗauki yaron suka kawo shi wurin mahaifiyarsa, yaron ya zauna a gwiwarta har tsakar rana daga nan sai ya mutu.
21Sai matar ta tashi ta kwantar da yaron a gadon mutumin Allah, ta kulle ƙofa, ta fita.22Ta kira maigidanta, ta ce, "Ina roƙo ka aiko mani da ɗaya daga cikin bayi da kuma ɗaya daga cikin jakunan domin in yi sauri zuwa wurin mutumin Allah sa'an nan in dawo."
23Maigidanta ya ce donme ki ke so ki je wurinsa yau? Ba sabon wata ba ne ko kuma Asabar ba. "Sai ta amsa, "Komai zai yi dai-dai.24" Sai ta ɗaura wa jaki sirdi ta ce da bayinta, "Ku kora shi da sauri; kada ku sausauta har sai na ce ku yi haka."
25To sai ta tafi ta je wurin mutumin Allah a Tsaunin Karmel. Lokacin da mutumin Allah ya hange ta daga nesa, sai ya ce da Gehazi baransa, "Duba ga matar nan Bashunamiya tana tafe.26Ka ruga a guje ka tambaye ta, ko komai lafiya yake game da ita da maigidanta da kuma ɗanta?"' Ta amsa, "Ba damuwa."
27Lokacin da ta zo wurin mutumin Allah akan dutsen sai ta kama ƙafafunsa, sai Gehazi ya zo zai ture ta amma mutumin Allah ya ce "Ka ƙyale ta, domin hankalinta a tashe yake Yahweh kuma ya ɓoye mani al'amarin, bai kuma faɗa mani komai ba."
28Daga nan sai ta ce, "Na roƙe ka ɗa ne, ya shugaba na, Ashe ban ce kada ka yaudare ni ba?"29Sai Elisha ya ce da Gehazi, "Maza shirya ka riƙe sandana a hanunka. Ka je gidanta. "In ka gamu da wani in ya gaishe ka kada ka amsa, kada ka amsa masa. Ka ɗora sandana a fuskar yaron."
30Amma mahaifiyar yaron ta ce, "Muddin Yahweh na raye, kana kuma raye, ba zan bar ka ba."Saboda haka Elisha ya tashi ya bi ta.31Gehazi ya ruga kafin su kai ya ɗora sandan a fuskar yaron, amma yaron bai iya ji ko kuma ya yi magana ba. Saboda haka Gehazi ya dawo ya gamu da su, ya ce da Elisha "Yaron bai farfaɗo ba."
32Lokacin da Elisha ya shiga gidan yaron a mace yake, yana kuma kwance akan gado.33Sai Elisha ya shiga ya kulle ƙofa da yaron ya yi addu'a ga Yahweh.34Sai ya hau ya kwanta akan yaron; ya sa bakinsa a bakinsa, idonnsa a idonsa, hannunsa a hannunsa. Sai ya miƙe akan yaron sai jikinsa ya yi ɗumi.
35Sai Elisha ya tashi ya zagaya ɗakin ya sake kwantawa akan yaron ya miƙe, sai yaron ya yi atishawa sau bakwai, sai ya buɗe idonsa!36Sai Elisha ya kira Gehazi ya ce da shi "Ka kira Bashunamiye!" Sai ya kira ta, da ya kira ta, da ta shiga ɗakin sai Elisha ya ce da ita "Ɗauki ɗanki."37Sai ta kwanta a ƙafafunsa fuskarta a ƙasa, daga nan sai ta ɗauki ɗanta ta fita.
38Sai Elisha ya sake zuwa Gilgal. Akwai yunwa kuma a ƙasar, 'ya'yan annabawa kuma na zaune a gabansa. Ya ce da baransa. "Ka ɗora babbar tukunya ka dafa miya domin 'ya'yan annabawa."39Ɗaya daga cikinsu ya tafi saura domin ya samo ganyayen abinci sai ya samon ganyen inabi mai guba ya tara shi da yawa ya cika haɓar rigarsa, Suka yayyanka suka zuba a cikin abincin, amma ba su san irin su ba.
40Sai suka zuba masu abinci su ci, can suna cikin cin abincin sai suka yi kuka suka ce "Da guba a cikin tukunyar!" Domin haka basu ƙara cin abincin ba.41Amma Elisha ya ce "Ku kawo mani gãri." Sai ya zuba a tukunyar ya ce, ku zuba wa mutane su ci, daga nan ba a sami wata guba a cikin tukunyar ba.
42Sai wani mutum ya zo daga Ba'al Shalisha wurin mutumin Allah ya kawo masa curin gurasar sha'ir guda ashirin a cikin jakarsa daga cikin girbinsa, da kuma sababbin zargankun hatsi. Ya ce, "Ka ba mutane wannan domin su ci."43Bayinsa suka ce "Ƙaƙa zamu ba da wannan ga mutane ɗari?" Amma Elisha yace "Ku ba su wannan domin su ci, domin Yahweh ya ce, 'Za su ci su kuma bar saura.'"44Sai bayinsa suka ajiye shi a gabansu; suka ci suka bar saura, kamar yadda maganar Yahweh ta alkawarta.

5

1Na'aman kwamadan sojan sarkin Aram, yana da girma da ƙima a gun shugabansa, saboda shi Yahweh yakan ba Aram nasara. Hakannan shi mutum ne mai ƙarfi da kuma ƙarfin halin, amma shi kuturu ne.2Aremiyawa suka kai hari runduna runduna suka ɗauki wata yarinya daga ƙasar Isra'ila, ta yiwa matar Na'aman hidima.

3Sai yarinyar ta ce shugabarta, "Na so a ce shugabana tare yake da annabin da ke a Samariya! To zai warkar da shugabana daga kututtarsa."4Sai Na'aman ya je ya faɗa wa sarki abin da yarinyar da ta zo daga ƙasar Isra'ila ta faɗa.
5Saboda haka sarkin Aram ya ce, "Yanzu ka tafi, zan kuma aika da wasiƙa zuwa ga sarkin Isra'ila." Sai Na'amam ya tafi ya ɗauki talanti goma na azurfa, da tsabar zinariya dubu shida, da kuma sauyin sutura guda goma.6Hakannan ya kai wa sarkin Isra'ila wasiƙar da ta ce, Lokacin da wannan wasiƙa ta zo wurinka, za ka ga cewa na aiko da barana Na'aman zuwa wurinka domin ka warkar da shi daga kuturtarsa."
7Bayan sarkin Isra'ila ya karɓi wasiƙar ya karanta ta sai ya keta tufafinsa ya ce, "Ni Allah ne da zan iya rayarwa ko in kashe, da wannan mutum zai so in warkar da mutum daga kuturtarsa? Da alama yana neman jayayya da ni."
8To bayan Elisha mutumin Allah ya ji cewa sarkin Isra'ila ya keta tufafinsa, sai ya ce "Me yasa ka keta tufafinka? Ka bar shi ya zo wurina yanzu zai kuma sani akwai annabi a Isra'iula."9Sai Na'aman ya je da karusarsa ya tsaya a ƙofar gidan Elisha.10Elisha ya aika masa da 'yan saƙo gare shi cewa. "Ka je ka yi nutso sau bakwai a kogin Yodan, jikinka zai dawo, zaka kuma tsaftata.
11Amma Na'aman ya fusata ya tafi ya ce, "Duba na yi zaton tabbas zai zo wurina ya tsaya ya kira sunanYahweh Allahnsa, ya kuma ɗaga hannunsa a wurin ya warkar da kuturtar tawa,12Ashe kogunan Abana da na Farfar wato kogunan Damaskus, basu fi duk waɗannan ruwayen na Isra'ila tsafta ba?" Sai ya juya cikin matuƙar hasala.
13Sai bayin Na'aman suka zo kusa suka yi magana da shi, "Babana, in da annabin ya ce ka yi wani abu mai wuya ashe ba za ka yi ba? Amma me ya fi wannan da ya ce maka, "Ka yi nutso ka tsarkaka?'"14Daga nan sai ya gangara ya je ya yi nutson sau bakwai a kogin Yodan ya yi biyayya ga ummarnin mutumin Allah. Sai jikinsa ya dawo kamar na jariri sabuwar haihuwa, ya kuma warke.
15Sai Na'aman ya koma wurin mutumin Allah shi da rundunarsa, ya ce "Duba yanzu na sani babu wani Allah a duk duniya sai a Isra'ila. To yanzu sai ka karɓi kyautai daga wurin baranka",16Amma Elisha ya ce "Muddin Yahweh wanda nake tsaye a gabansa na raye ba zan karɓi komai ba," Na'aman ya matsa wa Elisha ya karɓa amma Elisha ya ƙi karɓa.
17To sai Na'aman yace, "In ba za ka karɓa ba sai a ba baranka kayan takarkari na kayan alatu, domin daga yanzu baranka ba zai miƙa hadaya ta ƙonawa ga wani allah ba sai ga Yahweh.18Ka gafarci baranka, wato a lokacin da sarkina ya je gidan Rimmon domin ya yi sujada a can, ya kuma lashe hannuna na kuma sunkuya a gidan Rimmon, ina roƙon Yahweh ya gafarci baranka akan wannan."19Elisha yace da shi, "Ka tafi da salama." Sai Na'aman ya tafi.
20Ya ɗan yi nisa kenan, lokacin da Gehazi baran Elisha mutumin Allah ya ce a ransa, Duba, shugabana ya kyale Na'aman ɗin nan mutumin Aremiya bai karɓi kyautai da ya ya kawo daga hannunsa ba. Muddin Yahweh na raye zan bi shi in karɓi wani abu daga wurinsa."21Sai Gehazi ya bi Na'aman. Da Na'aman ya ga wani na biye da shi, sai ya dirgo daga karusa domin ya tare shi ya ce, "In ce ko lafiya?"22Gehazi yace, "Lafiya ƙalau. Ubangidana ne ya aiko ni, cewa, 'Duba, yanzunan ya yi baƙi daga ƙasa mai duwatsu ta Ifiraim samari biyu na 'ya'yan annabawa. Ina roƙo ka ba su jaka biyu na zinariya, da kayan alfarma guda biyu."
23Na'aman ya amsa, "Ina murna sosai in ba ka talanti biyu." Na'aman ya bukaci Gehazi kuma ya ɗaure talanti biyu na azurfa a cikin jaka biyu, da riguna biyu, sai ya ɗora su akan bayinsa biyu, waɗanda ke ɗauke da jaka na azurfa a gaban Gehazi.24Bayan Gehazi ya zo wurin duwatsu, sai ya karɓe jaka na azurfa daga hannunsu ya ɓoye su a cikin gida; ya sallami mutanen, suka tafi.25Bayan Gehazi ya shiga ciki ya tsaya a gaban shugabansa, Elisha yace da shi, "Daga ina ka dawo, Gehazi?" Ya amsa, "Baranka bai je ko'ina ba."
26Elisha yace da Gehazi, "Ashe ruhuna baya tare da kai ne a lokacin da mutumin ya juyo da karusarsa domin ya gamu da kai? Ko wannan ne lokacin karɓar kuɗi da sutura da man zaitun da garkar inabi, da tumaki da bijimai, da bayi maza da mata?27To kuturtar Na'aman za ta koma kanka da kuma zuriyarka har abada." Sai Gehazi ya fita daga gabansa a kuturce fari fat kamar auduga.

6

1'Ya'yan annabawa suka ce da Elisha, "Wurin da muke zama tare da kai ya gaza mana dukkanmu.2Muna roƙo ka bar mu mu je Yodan, sai kowannen mu ya saro itace a can, sai mu gina wurin da zamu zauna." Elisha ya amsa, "To ku je"3Ɗaya daga cikinsu ya ce, "Ina roƙo ka tafi tare da barorinka." Elisha ya amsa "za ni."

4To sai ya tafi tare da su, a lokacin da suka fara saran itatuwan.5Amma a lokacin da ɗayansu ke sara sai kan gatarin ya faɗa a cikin ruwa; sai ya yi waiyo ya ce "Ya shugabana, aro shi aka yi!"
6Sai mutumin Allah yace, "A ina ya faɗa?" Mutumin ya nuna wa Elisha wurin. Sai ya saro 'yar tsafga, ya jefa ta cikin ruwa, sai ta sa ƙarfen ya ɗago sama.7Elisha yace, "Ka ɗauko shi." Sai mutumin ya ɗauko shi.
8Sai sarkin Aram ya shirya kai hari kan Isra'ila. ya tuntuɓi barorinsa, cewa, "Sansanina ga yadda zai kasance da kuma inda zai kasance."9Sai mutumin Allah ya aika wurin sarkin Isra'ila, cewa, "Ka yi hankali kada ka wuce ta wurin nan, domin Aremiyawa suna gangarawa can."
10Sai sarkin Isra'ila ya aika da saƙo can game da abin da mutumin Allah ya faɗa masa ya kuma gargaɗe shi. Ba sau ɗaya ko sau biyu ba duk lokacin da sarki zai wuce wurin yana cikin tsaro.11Sarkin Aram ya da mugame da wannan gargaɗi, sai ya kira bayinsa ya ce da su, "Ba za ku faɗa mani wane ne daga cikinmu ya ke goyon bayan sarkin Isra'ila ba"
12Sai ɗaya daga cikin bayin ya ce, "Ba haka ba ne shugabana, sarki, domin Elisha annabi na Isra'ila ne ya faɗawa sarkin Isra'ila maganar da ka faɗa a ɗakin kwananka!"13Sarki ya amsa, "ku je ku duba inda Elisha yake domin in aika da mutane su kamo shi." An faɗa masa, "Duba yana a Dotan."
14Domin haka sarki ya aika mahaya dawakai da karusai da sojoji masu yawa zuwa Dotan. Suka zo da dare suka kewaye birnin.15Da baran mutumin Allah ya tashi da asuba ya fita waje, sai ga rundunonin sojoji da karusai da mahaya dawakai sun kewaye birnin. Baransa ya ce da shi, "Ya shugabana! Me za mu yi?"16Elisha ya amsa, "Kada ka ji tsoro, domin waɗanda ke tare da mu sun fi waɗanda ke tare da su."
17Elisha ya addu'a ya ce, "Yahweh, ina roƙonka ka buɗe idanunsa domin ya gani." Sai Yahweh ya buɗe idanun baran, Sai ya ga tsaunin na cike da dawakai da karusai na wuta kewaye da Elisha!18Lokacin da Aremiyawa suka zo gare shi, Elisha ya yi addu'a ga Yahweh ya ce, "Ka bugi mutanen nan da makanta, ina roƙonka." Sai Yahweh ya makantar da su, kamar yadda Elisha ya roƙa.19Sai Elisha ya ce da Aremiyawa, "Ba wannan ba ce hanyar, ba kuma wannan ba ne birnin. Ku biyo ni zan kai ku wurin mutumin da ku ke nema." Sai ya kai su Samariya.
20Bayan sun zo Samariya, Elisha yace, "Yahweh, ka buɗe idanun mutanen nan domin su gani." Yahweh ya buɗe idanunsu, sai suka gan su a tsakiyar birnin Samariya.21Da sarkin Isra'ila ya gan su ya ce da Elisha "'Babana, in kashe su ne? In kashe sun ne?"
22Elisha ya amsa, "Kada ka kashe su. Ko ka kashe bayin da ka kama da bãkanka da kuma takobinka? Ka ba su gurasa da ruwa domin su ci su sha, sai su tafi wurin shugabansu."23Sai sarki ya shirya abinci sosai domin su, bayan su ci sun sha, sai ya sallame su, suka je wurin shugabansu. Waɗannan ƙungiyoyin sojojin Aremiyawan ba su daɗe ba sosai a Isra'ila.
24Bayan wannan Ben Hadad sarkin Aram ya tara dukkan sojojinsa ya kaiwa Samariya hari ya kwashe ta.25Domin haka aka yi babbar yunwa a Samariya. Duba sun washe ta har ana sayar da kan jaki tsaba tamanin na shekel, ana kuma sayar da kofin kashin kurciya a shekel biyar.26Da sarkin Isra'ila ya zo wucewa ta gefen katanga sai wata mata ta yi masa kuka, cewa, "Ka yi temako shugabana, sarki."
27Ya ce, "Idan Yahweh bai taimake ki ba, ta yaya zan taimake ki? Ana samun wani abu ne daga masussuka ko kuma daga wurin matsar ruwan inabi?"28Sarki ya ci gaba, "Me ke damun ki?" Ta amsa, "Wanan matar ta ce da ni, 'Ki ba ni ɗanki domin mu dafa mu ci yau, gobe kuma sai mu ci ɗana."'29Domin haka muka dafa ɗana mu ka cinye shi, da gari ya waye na ce da ita, "Ki bada ɗanki domin mu cinye shi, amma ta ɓoye ɗanta."
30To bayan sarki ya ji maganar wannan mata, sai ya keta tufafinsa (yana wucewa gefen katanga) sai mutane suka gan shi saye da tufafin makoki a jikinsa.31Sai ya ce "Dama Allah ya yi mini haka, in har kan Elisha ɗan Shafat ya tsaya a kansa yau."
32Amma Elisha na zaune a gidansa, dattawa kuma na zaune tare da shi. Sai sarki ya aika manzo ya zo wurinsa, amma da manzon ya zo wurin Elisha, sai ya ce da dattawan, "Dubi yadda wannan ɗan mai kisan kai ya aika a sare mani kai? Duba lokacin da manzon ya zo, kulle ƙofa kulle ƙofar a hana masa shiga. Ashe ba ƙarar sawun mai gidansa na biye da shi ba?"33Yana cikin yi masu magana sai ɗan saƙo ya zo wurinsa. "Sarki ya ce, "Duba wannan matsala daga wurin Yahweh ta zo. Donme kuma zan ƙara jiran Yahweh?"

7

1Elisha yace, ka ji maganar Yahweh, wannan shi ne abin da Yahweh ya faɗa: gobe kamar i yanzu a ƙofar shiga Samariya za a sayar da kofin garin alkama a shekel ɗaya, awo biyu na sha'ir a shekel,'"2Sai hafsan da aka aiko wurin Elisha ya ce da mutumin Allah, "Ko da ma ace Yahweh zai buɗe sakatun sama, wannan abin zai faru? "Elisha ya amsa, "Duba za ka ga abin na faruwa da idonka amma ba za ka ɗanɗana ko kaɗan daga cikinsa ba."

3To akwai mutun huɗu da ke da ciwon kuturta a wajen ƙofar birni. Sai suka cewa juna, "Domin me za mu yi ta zama a nan har mu mutu?4In mun ce za mu cikin birni yunwar na can, za mu kuma mutu a can. Bari mu je sansanin Aremiyawa. In sun bar mu da rai mu rayu, in kuma zamu mutu mu mutu a can, amma ko da ma mun tsaya a nan zamu mutu. To yanzu sai mu je sansanin Aremiyawa. In sun bar mu da rai to, za mu rayau, in kuma sun kashe mu mutuwa kawai zamu yi."
5To sai suka tashi da almuru suka nufi sansanin Aremiyawa; da suka isa tsakiyar wurin ba kowa a sansanin ba ko mutun ɗaya a wurin.6Domin Ubangiji yasa sojojin Aremiyawa su ji ƙarar karusai da ƙarar mahayan dawakai da kuma babbar ƙarar rundunar soja, suka ce da junansu. "Sarkin Isra'ila ya yi hayar sarakunan Hitiyawa da na Masar domin su kawo mana hari."
7Domin haka sojoji suka ruga da almuru; suka bar rumfunansu, da dawakansu, da jakunansu da sansanin kamar yadda yake suka gudu domin su tsirar da ransu.8Lokacin da mutanen da ke da kuturta suka shiga tsakiyar sansanin suka shiga wata rumfa suka ci suka sha, suka kwashi shekel da zinariya da azurfa da da suturu suka tafi da su suka ɓoye su suka sake dawowa suka shiga wani sansanin suka kwashi ganima daga can suka tafi suka ɓoye ta.
9Daga nan suka ce da juna, "Ba mu yin abin da ke dai dai ba yau. wannan ranar ta kai soƙo mai daɗi ce, amma munyi shiru game da batun. In mun jira har gari ya waye za mu fuskaci horo. To yanzu, ku zo mu je mu faɗa wa dukkan gidan sarki."10Sai suka tafi suka kira masu tsaron ƙofar birnin. Suka faɗa masu cewa, Mun je sansanin Aremiyawa, amma ba kowa a can, ba kuma motsin kowa, amma akwai dawakai a ɗaure, da jakai a ɗaure da kuma rumfunan kamar yadda suke."11Daga nan sai masu tsaron ƙofofin suka baza labarin, daga nan sai aka faɗa a cikin dukkan gidan sarki.
12Sai sarki ya tashi da dare ya ce da bayinsa, "Yanzu zan faɗa maku abin da Aremiyawa suka yi mana. Sun sani muna jin yunwa, to sai suka bar sansanin suka je suka ɓuya a cikin sauruka. Suna cewa, "in sun fito wajen birnin, zamu kama su da rai, mu shiga cikin birnin."'13Ɗaya daga cikin bayin sarki ya ce, "'Ina roƙonka ka bar waɗansu mutane su ɗauki dawakai biyar da suka rage a birnin. Su kamar sauran yawan Isra'ila ne da suka ragu - domin da yawansu sun mutu; sai mu aike su mu gani."
14Sai suka kwashi karusan dawakai guda biyu, sai sarki ya aike su su bi Aremiyawa cewa, "Ku je ku gani."15Sai suka tafi har zuwa Yodan, hanyar kuma ta cika da suturu birjik da kuma kayayyakin da Aremiyawa suka warwatsar cikin saurinsu. Sai manzannin suka dawo suka faɗawa sarki.
16Sai mutane suka fita suka kwashi ganimar sansanin Aremiyawa. Domin haka aka sayar da awon alkama a shekel ɗaya da kuma awon sha'ir biyu a shekel, kamar dai yadda maganar Yahweh ta faɗa.17Sai sarki ya sa wannan hafsan da ya aika ya zama mai kula da ƙofar, sai mutane suka tattake shi a ƙofar. Ya mutu kamar yadda mutumin Allah ya faɗa, a lokacin da sarki ya zo wurinsa.
18Haka ya kasance kamar yadda mutumin Allah ya faɗa wa sarki, cewa, war haka a ƙofar shiga Samariya, za, a sayar da awo biyu na sha'ir a shekel, awo ɗaya na alkama kuma a shekel."19Wannan hafsan ya ce da mutumin Allah, "Duba ko da Yahweh zai sa sakatun sama su buɗe, ko wannan zai faru?" Elisha ya ce, "Duba za ka gani yana faruwa a idanunka, amma ba za ka ci daga cikinsa ba."20Wannan shi ne hakikanin abin da ya faru da shi, domin mutane sun tattake shi a bakin ƙofa, ya kuma mutu.

8

1To sai Elisha ya yi magana da matar da ya komar da ɗanta da rai. Ya ce da ita, "Ki tashi, da dukkan gidanki, zauna a duk inda za ki zauna a wata ƙasa, domin Yahweh ya saukar da yunwa a wannan ƙasa har tsawo shekaru bakwai."2Sai matar ta tashi ta yi biyayya da maganar mutumin Allah. Ta tafi da ita da mutanen gidanta zuwa ƙasar Filistiyawa har tsawon shekaru bakwai.

3To a ƙarshen shekaru bakwai da wannan mata ta komo daga ƙasar filistiyawa, ta je wurin sarki ta roƙe shi domin gidanta da kuma ƙasarta.4To sarki na magana da Gehazi baran mutumin Allah, cewa "Ina roƙo ka faɗa mini dukkan manyan abubuwan da Elisha ya yi."
5A lokacin da yake faɗa wa sarki yadda Elisha ya komar da ran yaron da ya mutu, sai wannan dai matar ta zo ta roƙi sarki saboda gidanta da kuma ƙasarta. Gehazi yace, "Shugabana, sarki, ga matar da kuma ɗan nata, da Elisha ya mayar wa da rai."6Lokacin da sarki ya tambayi matar game da ɗanta, ta yi masa bayani. Sai sarki ya sa wani hafsa dominta ya ce, "Ka ba ta duk abin da ke nata da kuma dukkan girbin gonarta tun daga ranar da ta bar ƙasar har ya zuwa yanzu."
7Sai Elisha ya zo Damaskus. Inda Ben Hadad sarkin Aram ke ciwo. Sai aka faɗa wa sarki cewa, "Mutumin Allah ya zo nan."8Sai sarki yace da Hazayel, "Ɗauki kyauta a hannunka ka je wurin mutumin Allah, ka tuntuɓi Yahweh ta wurinsa, cewa 'Ko zan wartsake daga wannan rashin lafiyar?"'9To sai Hazayel ya tafi wurinsa da kyauta ta kowanne abu mai kyau na Damaskus, ya ɗora wa raƙuma arba'in. Sai Hazayel ya zo ya tsaya a gaban Elisha ya ce "Ɗanka Ben Hadad sarkin Aram ne ya aiko ni gare ka, cewa 'ko zan warke daga wannan rashin lafiyar?"'
10Elisha ya ce da shi, "Ka je ka ce da Ben Hadad, 'Hakika za ka warke; amma Yahweh ya nuna mani cewa hakika zai mutu."11Sai Elisha ya ƙarfafa Hazayel har sai da ya ji kunya, mutumin Allah kuma ya yi kuka.12Hazayel ya tambaya, "Meyasa ka yi kuka, ya shugabana?" Ya amsa, "Saboda na san irin muguntar da zaka yi wa mutanen Isra'ila. Za ka ƙone hasumayoyinsu da wuta, za ka kuma kashe samarinsu da takobi, zaka kuma daddatsa 'yan ƙananansu, za ka kuma feɗe matayensu masu juna biyu."
13Hazayel ya masa, "Wane ne baranka, da zai yi wannan babban abu? Ai shi kare ne kawai. Elisha ya amsa, Yahweh ya nuna mani cewa za ka yi sarautar Aram.14Daga nan Hazayel ya rabu da Elisha ya komo wurin mai gidansa, wanda ya ce da shi "Me Elisha ya faɗa maka?" ya amsa, ya faɗa mani hakika za ka warke."15To washegari Hazayel ya ɗauki bargo ya tsoma shi a ruwa, ya shimfiɗa shi a kan fuskar Ben Hadad da haka ya mutu. Sai Hazayel ya zama sarki a maimakon sa.
16A shekara ta biyar ta sarautar Yoram ɗan Ahab, sarkin Isra'ila, Yahoram ya fara sarauta. Shi ɗan Yehoshafat ne sarkin Yahuda. Ya fara sarauta a lokacin da Yehoshafat ke sarautar Yahuda.17Yahoram yana da shekaru talatin da biyu a lokacin da ya fara sarauta, ya yi sarauta ta shekaru takwas a Yerusalem.
18Yahoram ya bi tafarkin sarakunan Isra'ila, kamar yadda gidan Ahab ya yi; domin ya auri 'yar Ahab a matsayin matarsa, ya kuma yi abin da ke mugu a gaban Yahweh.19Duk da haka, saboda baransa Dauda bai so ya hallaka Yahuda ba, tun da ya yi masa alƙawari cewa har kullum ba za a rasa wanda zai yi sarauta daga zuriyarsa ba.
20A kwanakin Yahoram, sai Idom ta tayar wa mulkin Yahuda, suka kuma naɗa wa kansu sarki. Sai21Yahoram ya tsallake shi da hafsoshinsa da dukkan karusansa. Sai ya tashi da duhu ya kai hari ya washe Idomawa, waɗanda suka kewaye shi da kuma hafsoshin karusai. Sai sojojin Yaharom suka tsere gidajensu.
22To da haka Idom ta tayar wa mulkin Yahuda har ya zuwa yau. Libna ita ma ta tayar alokaci guda.23To game da sauran abubuwa game da Yahoram, da duk abin da ya yi, ashe ba a rubuce suke a littafin ayyukan sarakunan Yahuda ba?24Yahoram ya mutu ya huta tare da ubanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dauda. Daga nan ɗansa Ahaziya ya zama sarki a madadinsa.
25A shekara ta sha biyu ta Yoram ɗan Ahab, sarkin Isra'ila, da Ahaziya ɗăn Yehoram, sarkin Yahuda, suka fara mulki.26Ahaziya yana da shekara ashirin da biyu lokacin da ya fara sarauta; ya yi sarautar shekara ɗaya a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Ataliya; Ita 'yar Omri ce, sarkin Isra'ila.27Ahaziya ya bi tafarkin gidan Ahab; ya yi abin da ke mugu a gaban Yahweh, kamar dai sauran abin da Ahab ya yi, domin Ahaziya suruki ne ga gidan Ahab.
28Ahaziya ya tafi tare da Yoram ɗan Ahab, domin su yi yaƙi gãba da Hazayel, sarkin Aram, a Ramot Giliyad. Aremiyawa suka yi wa Yoram rauni.29Sarki Yoram ya koma gida domin ya warke a Yazriyel daga raunin da aka yi masa a Rama, a lokacin da ya yi yaƙi da Hazayel sarkin Aram. Sai Ahaziya ɗan Yahoram sarkin Yahuda, ya tafi Yezriyel domin ya ga Yoram ɗan Ahab, saboda an yi wa Yoram rauni.

9

1Sai annabi Elisha ya kira ɗaya daga cikin 'ya'yan annabawa ya ce da shi, "Ka shirya domin tafiya, ka riƙe wannan 'yar kwalbar man ka tafi Ramot Giliyad2lokacin da ka je sai ka nemi Yehu ɗan Yehoshafat ɗan Nimshi, sai ka shiga ciki ka sa shi ya tashi daga abokan taraiyarsa ka bi da shi can cikin lalloki rumfa3Sai ka ɗauki kwalbar ka tsiyaya masa mai aka ce Yahweh ya faɗi wannan: "Na keɓe ka ka zama sarkin Isra'ila" daga nan sai ka buɗe ƙofa ka yi sauri ka gudu, kada ka yi jinkiri.

4Sai saurayin, wato matashin annabin, ya tafi Ramot Giliyad.5Da ya isa sai ga hafsoshin sojoji na zaune. Sai matashin annabin ya ce, "Na zo wurin ɗaya daga cikinku, ne hafsoshi." Yehu ya amsa, Ga wa daga cikinmu?" Matashin annabin ya amsa "Gareka, hafsa"6Sai Yehu ya tashi ya shiga cikin gida, sai annabin ya zuba masa mai a kã yace da Yehu, "Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: 'Na keɓe ka ka zama sarki akan mutanen Yahweh, Isra'ila.
7Dole ne ka kashe iyalin Ahab shugabannka, domin in yi ramako akan bayina annabawa, da kuma jinin dukkan bayin Yahweh waɗanda Yezebel ta kashe.8Domin dukkan iyalan Ahab za su lalace zan kuma datse dukkan 'ya'ya maza na zuriyar Ahab ko shi bawa ne ko kuma mai 'yanci.
9Zan mayar da gidan Ahab kamar gidan Yerobowam ɗan Nebat, kamar kuma gidan Ba'asha ɗan Ahija.10Karnuka kuma za su ci naman Yezebel a Yezriyel kuma ba za 'a sami wanda zai bizne ta ba.'" Daga nan sai annabin ya buɗe ƙofar, ya gudu.
11Sai Yehu ya fito waje zuwa wurin bayin shugabansa, sai ɗaya daga cikinsu ya ce da shi, "Ko dai lafiya? Meyasa wannan mahaukacin ya zo wurinka?" Yehu ya amsa musu, "Kun san irin mutumin da irin abin da ya ke faɗi."12Suka ce, "Wannan ƙarya ne. Ka faɗa." Yehu ya amsa, "Ya faɗa mani abu kaza da kaza, hakan nan ya ce 'Ga abin da Yahweh yace: Na kebe ka ka zama sarkin Isra'ila."'13Sai dukkan su suka yi sauri suka tuɓe rigarsa ta waje suka sa ta ƙarƙashin Yehu akan matakan. Suka hura kakaki suka ce, "Yehu sarki ne."
14Ta haka Yehu ɗan Yehoshafat ɗan Nimshi suka ƙulla maƙarƙashiya kan Yoram. A lokacin, Yoram yana kare Ramot Giliyad, shi da dukkan Isra'ila, saboda Hazayel sarkin Aram,15amma sarki Yoram ya koma Yezriyel domin ya warke daga raunin da Aremiyawa suka yi masa, lokacin da suka yi faɗa da Hazayel sarkin Aram. Yehu yace da bawan Yoram, "In wannan shi ne ra'ayinka, to kada kowa ya tsira ya fita daga birnin, saboda aje a faɗi labarin a Yezriyel."16Sai Yehu ya tuƙa karusa zuwa Yezriyel; Yoram yana shaƙatawa a can. Sai Ahaziya sarkin Yahuda ya zo domin ya ga Yoram.
17Ɗan tsaro na tsaye akan hasumaya a Yezriyel, sai ya ga rundunar Yehu da ya matso kusa; sai yace, "Na ga kungiyar mazaje na zuwa." Yoram yace, "Ka kwashi mahayin dawakai, ka aike shi wurinsu; ka ce da shi ya tambaye su 'Kuna zuwa da salama ne?"'18Sai ya aika mutumin akan doki ya koma ya tare shi; sai ya ce, sarki ne ya faɗi wannan: 'Kuna zuwa da salama ne?"' Sai Yehu yace, "Me zaku yi da salama? Ka juya ka biyo ni."Sai ɗan tsaron ya faɗa wa sarki, "Ɗan saƙon ya same shi, amma ba zai dawo ba."
19Sai ya sake aikar mutum na biyu ya sake komawa akan doki, wanda ya zo wurinsu ya ce, "Sarki ya faɗi wannan: 'Kuna zuwa da salama ne?'" Yehu ya amsa "Me za ku yi da salama? ka juyo ka biyo ni."20Sai wannan manzon ya sake mayar da amsa, "Ya same su, amma ba zai dawo ba. Domin hanyar da ya ke tuƙa dawakan ita ce Yehu ɗan Nimshi ya bi; kuma yana tuki a sukwane."
21Sai Yoram yace, "Ka shirya karusata." Suka shiya karusarsa, sai Yoram sarkin Isra'ila da Ahaziya sarkin Yahuda suka fita akan dawakai, kowa da karusarsa domin su gamu da Yehu. Suka same shi a mallakar Nabot Bayezriyile.22Da Yoram ya ga Yehu, sai ya ce, "Yehu kana zuwa da salama ne?" Ya amsa, "Wacce salama kuma ke a can bayan akin zina da maitanci na mahaifiyarka Yezebel sun yi yawa?"
23Sai Yoram ya juya karusarsa ya tsere ya ce da Ahaziya, "Akwai tashin hankali Ahaziya."24Daga nan Yehu ya ɗauko bakãnsa da cikkakken ƙarfinsa ya harbi Yoram a tsakanin kafaɗunsa; kibiyar ta bi ta zuciyarsa, sai ya faɗi a cikin karusarsa.
25Sai Yehu yace da Bidkar hafsansa, "Ciro shi ka jefar da shi a filin Nabot Bayezriyile. Tuna da yadda muka bi babansa Ahab, Yahweh ya ajeye hukuncinsa a kansa:26'Jiya na ga jinin Nabot da kuma jinin 'ya'yansa - inji Yahweh - kuma hakika zan sa ka biya shi a wannan fili - inji Yahweh. Yanzu, sai ka ciro shi ka jefar da shi a filin, bisa ga maganar Yahweh."
27Da Ahaziya sarkin Yahuda ya ga wannan, sai ya gudu daga hanya zuwa Bet Haggan. Amma Yehu ya bi shi, ya ce "Shi maku kashe shi a cikin karusarsa," sai suka harbe shi kusa da Gur, wadda ke wajen Ibliyam. Ahaziya ya gudu zuwa Megiddo ya mutu a can.28Bayin suka ɗauke gawarsa a cikin karusa zuwa Yerusalem suka bizne shi a maƙabarta tare da ubanninsa a birnin Dauda.
29A shekara ta sha ɗaya ne ta Yoram ɗan Ahab Ahaziya ya fara mulkin Yahuda,
30Da Yehu ya zo Yezriyel, Yezebel ta ji labari, sai ta yi kwalliya ta yi wa idonta zane ta gyara gashinta, ta duba ta taga.31A lokacin da Yehu ke shiga ƙofar ta ce da shi, "Kana zuwa da salama ne, kai Zimri, an kashe shugabanka ne?"32Yehu ya dubi tagar ya cewa, "Ke tare da ni? Ke?" Sai bãbãni biyu ko uku suka duba waje.
33Sai Yehu yace, "Ku wurgo ta ƙasa." Sai su ka wurgo Yezebel ƙasa, har jininta ya fallatsa a bango da kuma jikin dawakai, Yehu kuma ya tattake ta da ƙafafu.34Da Yehu ya shiga fãdar sai ya ci ya sha. Ya ce, "Duba yanzu ku ɗauki wannan la'anarniyar matar ku bizne ta, domin ita 'yar sarki ce."
35Sai suka tafi domin su bizne ta, amma ba su tarar da komai nata ba sai ƙoƙon kanta da ƙafa da tafin hannuwa.36Sai suka dawo suka faɗa wa Yehu. Ya ce, "Wannan maganar Yahweh ce wadda annabi Iliya Batishbe, ya faɗa, cewa 'A filin Yezriyel karnuka za su cinye gangar jikin Yezebel,37gangar jikin Yezebel kuma za ta zama kamar ɗan kututture a cikin filaye a ƙasar Yezriyel, domin kada wani ya iya cewa, "Wannan ce Yezebel.'"'

10

1Ahab yana da zuriya saba'in a Samariya. Yehu ya rubuta wasiƙu ya aika da su Samariya, ga shugabannin Yezriyel, haɗe da dattawa da 'yan tsaro na zuriyar Ahab, cewa,2"Zuriyar shugabanku na tare da ku, kuma kuna da karusai da dawakai da ƙayatattun birane da makamai.3Domin haka da zarar wannan wasiƙa ta same ku, sai ku zaɓi wanda yafi cancanta daga cikin zuriyar shugabanku ku ɗora shi akan gadon sarautar mahaifinsa, ku kuma yi yaƙi domin gidan sarautar shugabanku."

4Amma suka tsorata suka ce da junansu, "Duba sarukuna biyu ma ba su iya ja da Yehu ba. To yaya zamu iya ja da shi?"5Daga nan sai wanda ke shugabantar fãdar, da mai kula da birnin da kuma dattawan da kuma masu renon yara, suka sake mayar da magana ga Yehu, cewa, "Mu bayinka ne. Za mu yi duk abin da ka umarce mu. Baza mu naɗa kowa a matsayin sarki ba. Ka yi abin da ka ga ya yi maka kyau a idanunka."
6Sai Yehu ya rubuta wasiƙa ta biyu zuwa gare su, cewa, "In kuna tare da ni, in kuma za ku ji muryata, dole ne ku ɗauko wanda yake shi ne shugaban zuriyarku ku zo da shi Yezriyel gobe war haka." To sai zuriyar sarkin, su saba'in, suka zama manyan mutane masu daraja a birnin waɗanda suke kula da su7To da wasiƙa ta zo gare su, sai suka kama 'ya'yan sarki suka karkashe su, mutane saba'in, suka ɗauki kawunansu suka aikawa da Yehu a Yezriyel.
8Sai manzo ya zo wurin Yehu, ya ce, "Sun kawo kawunan 'ya'yan sarki maza." Sai ya ce ku ajiye su a mazubin a ƙofar shiga har sai gari ya waye."9Da safe sai Yehu ya fito ya tsaya ya ce da dukkan mutane, "Ba ku da laifi. Na shirya makirci kan shugabana na kuma kashe shi, amma wane ne ya kashe dukkan waɗannan?
10To yanzu sai ku san cewa ba wani sashe na maganar Yahweh, da aka faɗa game da gidan Ahab, da zai faɗi ƙasa, domin Yahweh ya yi abin da ya faɗa ta bakin bawansa Iliya."11Sai Yehu ya karkashe duk waɗanda suka rage na iyalin Ahab a Yezriyel, ya kuma kashe mutanensa masu muhimmanci, da abokansa na ƙut da ƙut, da firistocinsa, har ta kai ga ba wanda ya ragu.
12Sai Yehu ya tashi ya tafi; ya tafi zuwa Samariya. Da ya je Bet Eked ta makiyaya,13sai ya tarar da 'yan'uwan Ahaziya sarkin Yahuda. Yehu yace da su "Ku su wane ne?" Suka ce, "Mu 'yan'uwan Ahaziya ne, kuma zamu mu gai da 'ya'yan sarki ne da kuma 'ya'yan Sarauniya Yezebel."14Yehu ya ce da mutanensa, "Ku kama su da ransu." Sai suka kama su da ransu suka karkashe su a ramin Bet Eked, dukkan mutanen arba'in da biyu ne. Bai bar ko ɗaya daga cikinsu da rai ba.
15Da Yehu ya bar wurin, sai ya tarar da Yonadab ɗan Rekab yana zuwa domin ya same shi. Yehu ya gaishe shi ya ce da shi, "Ko zuciyarka na tare da ni, kamar yadda zuciyata ke tare da taka?" Yonadab ya amsa, "Tana nan." Yehu ya amsa, "In tana nan, ka ba ni hannunka." Sai Yonadab ya ba shi hannunsa, sai Yehu ya ɗauke shi a cikin karusarsa.16Yehu ya ce, "Ka zo tare da ni ka ga himmata domin Yahweh." Sai ya tafi da Yonadab yana tuƙi tare da shi a karusarsa.17Da ya zo Samariya, sai Yehu ya karkashe duk waɗanda suka ragu daga zuriyar Ahab a Samariya, har sai da ya kashe duk wani mai jinin sarauta na iyalin Ahab, kamar dai yadda maganar Yahweh ta faɗa ta wurin Iliya.
18Sai Yehu ya tattara dukkan mutane wuri ɗaya ya ce da su, "Ahab ya bauta wa Ba'al ɗan kaɗan, amma Yehu ya fi bauta masa ya yawa.19To yanzu sai ku kirawo mani dukkan annabawan Ba'al, da duk masu bautarsa, da duk firistocinsa. Kar ku rage ko da guda ɗaya, domin ina da babbar hadaya da zan miƙa ga Ba'al. Duk wanda bai zo ba za, a kashe shi." Amma Yehu ya yi wannan yaudarar ne domin ya kashe duk masu bauta wa Ba'al.20Yehu yace, "Ku shirya lokaci da za mu yi taruwa domin Ba'al." Domin haka suka yi sanarwar ta.
21Sai Yehu ya aika a ko'ina cikin dukkan Isra'ila sai duk masu bautar Ba'al suka zo, har ba waninsu da bai zo ba. Suka zo masujadar Ba'al, ta kuma cika maƙil.22Yehu yace da mutane masu, kula da ma'ajiyar kayan firistoci, "Ku fito da tufafi domin duk masu bautar Ba'al." Sai mutumin ya fito da tufafi dominsu.
23Sai Yehu ya tafi tare da Yonadab ɗan Rekab zuwa gidan Ba'al, ya ce da masu bautar Ba'al, "Ku bincika ku tabbatar cewa ba wani daga cikin masu bautar Yahweh a cikinku, amma sai dai masu bautar Ba'al kaɗăi."24Sai suka shiga domin su miƙa hadayu da baiko na ƙonawa. Sa'an nan Yehu ya zaɓi mutane tamanin da ke tsaye a waje, ya ce da su, "In wani ya bar mutanen nan da na kawo ya kuɓuta to a bakin ransa, zan kashe wanda ya yi sakaci har wani ya gudu a madadin wancan da ya gudu."
25To nan da nan da Yehu ya gama miƙa hadaya da baiko na ƙona wa, ya ce da 'yan tsaro da hafsoshi, "Ku shiga ku kashe su. Kar ku bar wani ya fito waje." Domin haka suka karkashe su da kaifin takobi, da 'yan tsaro da hafsoshin suka jejjefar da su waje suka shiga can ƙuryar ɗakin gidan Ba'al.26Suka mummurgina duwatsun ginshiƙan gidan Ba'al suka ƙone su.27Suka kuma kakkarya ginshiƙan Ba'al, suka hallakar da gidan Ba'al suka mayar da shi makewayi wanda har yanzu haka wurin ya ke.28Da haka Yehu ya hallakar da bautar Ba'al daga Isra'ila.
29Amma Yehu bai ƙyale zunubin Yerobowom ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra'ila ta yi zunubi - wato bautar ɗan maraƙin zinariya a Betal da Dan.30Domin haka Yahweh yace da Yehu, "Saboda ka yi abin da ke dai dai a idona, ka kuma iy wa gidan Ahab gwargwadon abin da ke a zuciyata, zuriyarka zasu yi mulkin Isra'ila har ya zuwa tsara ta huɗju."31Amma Yehu bai da muya yi tafiya bisa tafarkin Yahweh, Allah na Isra'ila, da dukkan zuciyarsa ba. Bai kuma bar zunubinYarobowam ba, ta haka ya sa Isra'ila yin zunubi.
32A waɗancan kwanakin Yahweh ya fara yanke sassa daga Isra'ila, sai Hazayel ya ci Isra'ila akan iyakokin Isra'ila,33daga gabashin Yodan, dukkan ƙasar Giliyad da ta Gadiyawa da ta Rubenawa da ta Manassawa, daga Arowa wadda ke a Kwarin Arno har ya zuwa Giliyad da kuma zuwa Bashan.
34Game kuma da sauran abubuwa game da Yehu, da kuma duk abin da ya yi da dukkan ikonsa, ashe ba a rubuta su a cikin ayukan sarakunan Isra'ila ba?35Yehu ya yi barci tare da ubanninsa, suka kuma bizne shi a Samariya. Sai Yehoahaz ɗansa ya zama sarki a madadinsa.36Tsawon lokacin da Yehu ya yi mulkin Isra'ila a Samariya shi ne shekaru ashirin da takwas.

11

1To da Ataliya, mahaifiyar Ahaziya ta ga ɗanta ya mutu, sai ta tashi ta kashe duk 'ya'yan gidan sarauta.2Amma Yehosheba, 'yar sarki Yahoram da 'yar'uwar Ahaziya, ta ɗauki Yo'ash ɗan Ahaziya ta ɓoye shi daga cikin 'ya'yan sarki waɗanda aka kashe, tare da mai renonsa; ta sa su a ɗakin kwana. Suka ɓoye shi domin kada Ataliya ta gan shi ta kashe shi.3Yana tare da Yahosheba a ɓoye a gidan Yahweh har tsawon shekaru shida, a lokacin da Ataliya ke sarautar ƙasar.

4A shekara ta bakwai, Yeho'iada ya aika da saƙonnin ya kuma fito da kwamandojin na ɗari-ɗari na Karitawa wato wata ƙungiyar mayaƙa ta gidan sarauta da 'yan tsaro ya kawo su wurinsa, cikin haikalin Yahweh. Ya yi yarjejeniya da su, ya kuma sa su su rantse a gidan Yahweh. Daga nan sai ya nuna musu ɗan sarki.5Ya umarce su, da cewa, "Wannan shi ne abin da tilas za ku yi. Kashi uku daga cikinku waɗanda ke zuwa da ranar Asabaci za su yi tsaron gidan sarki,6kashi uku su tsaya a Ƙofaf Sur, kuma kashe uku su tsaya a ƙofar bayan gidan 'yan tsaro."
7Sauran ƙungiyoyin guda biyu da ba ku yin hidima da ranar asabar, dole ne ku yi tsaron gidan Yahweh domin sarki.8Dole ne ku kewaye sarki kowanne mutum da makaminsa a hannunsa, duk wanda ya shigo wurinku sai ku kashe shi. za ku kasance tare da sarki a lokacin da ya fita da lokacin da ya dawo ciki.
9Sai kwamandojin ɗari-ɗari suka yi biyayya da duk abin da Yeho'iada ya firist ya ba da umarni. Kowannen su ya ya kwashi mutanensa, waɗanda ke zuwa hidima da Asabaci, da waɗanda ke zuwa daina hidima da Asabaci; suka zo wurin Yeho'iada firist.10Sai Yeho'iada firist ya ya ba kwamandojin ɗari-ɗari mãsu da garkuwoyi na sarki Dauda da kuma waɗanda ke gidan Yahweh.
11Saboda haka 'yan tsaron suka tsaya, kowanne da makaminsa a hannunsa, daga gefen dama na haikalin zuwa gefen hagun na haikalin, kusa da bagadi da kuma haikalin, suna kewaye da sarki.12Sai Yeho'iada ya kawo ɗan sarki Yo'ash, ya sa masa kambi a kansa, ya kuma ba shi sharruɗan yarjejeniya. Sai suka naɗa shi sarki suka kuma shafe shi da mai. Suka tafa hannuwansu suka ce, "Ran sarki ya daɗe!"
13Da Ataliya ta ji hayaniya ta 'yan tsaro da ta mutane, sai ta zo wurin mutane a gidan Yahweh.14Tana dubawa sai ga sarki a tsaye a jikin ginshiƙin, kamar yadda al'adar ta ke, da hafsoshi da masu hura ƙahonni na tare da sarki. Dukkan mutanen ƙasar na murna suna hura ƙahonni. Sai Ataliya ta keta tufafinta ta yi ihu tana cewa, "Cin amanar ƙasa! Cin amanar ƙasa!"
15Sai Yeho'iada firist ya bada umarni ga kwamandoji na ɗari ɗari masu shugabantar sojojin cewa, "Ku kawo ta a tsakanin rundunarku. Kuma duk wanda ya biyo ta, ku kashe shi da takobi. Domin firist ya ce, "Kada ku kashe ta a gidan Yahweh."16Domin haka suka ja ta da ta kai dai dai inda dawakai ke shiga wurin 'yan tsaron fãda a can aka kashe ta.
17Sai Yeho'iada firist ya yi yarjejeniya da tsakanin Yahweh da sarki da kuma mutane, cewa za su zama mutanen Yahweh, hakannan kuma tsakanin mutane da sarki.18Domin haka dukkan mutanen ƙasar suka tafi gidan Ba'al suka rurrushe shi. Suka bubbuge bagadin Ba'al da gumakansa rugu rugu, suka kuma kashe Mattan firist na Ba'al a gaban bagadojin. Sai Yeho'iada firist ya naɗa 'yan tsaro a haikalin Yahweh.
19Sai Yeho'iada ya kwashi kwamandojin ɗari ɗari da Karitiyawa, mayaƙan fãda, da 'yan tsaro, da dukkan mutanen ƙasar tare suka ka kawo sarki daga gidan Yahweh suka tafi gidan sarki ta hanyar ƙofar 'yan tsaro. Sai Yo'ash ya hau gadon sarauta.20Domin haka duk mutanen ƙasar suka yi murna, sai birnin ya sami kwanciyar hankali bayan an kashe Ataliya da takobi a gidan sarki.
21Yo'ash yana da shekaru bakwai a lokacin da ya fara sarauta.

12

1A shekara ta bakwai ta Yehu, sarautar Yo'ash ta fara; ya yi sarauta tsawon shekaru arba'in a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Zibiya ta Biyasheba.2Yoash ya yi abin da ke nagari a gaban Yahweh a dukkan lokaci, saboda Yeho'iada firist yana yi masa gargaɗi.3Amma ba a kawar da manya manya wurare ba. Har yanzu mutane na yin hadaya da ƙona turare a manyan wurare.

4Sai Yo'ash yace da firistoci, "Dukkan ƙuɗaɗen da aka kawo a keɓaɓɓen wuri a cikin gidan Yahweh, wannan kuɗin da kuɗaɗen da aka tsara wa mutane - ko kuɗin da aka karɓa a wurin ƙidaya ne, ko kuma kuɗin da aka karɓa saboda wa'adi ne, ko kuma kuɗin da aka tara ta wurin yadda Yahweh ya zuga mutanensa -5sai firistoci su karbi kuɗin daga ɗaya daga cikin ma'ajiyarsu su gyara duk wata ɓarna da suka gani a cikin haikali."
6Amma a shekara ta ashirin ta sarautar sarkin Yo'ash, firistoci ba su gyara komai ba a cikin haikalin.7Sai sarki Yo'ash ya kira Yeho'iada firist da kuma sauran firistoci, ya ce da su, "Meyasa baku gyara komai a cikin haikalin ba? To yanzu kada ku ƙara ɗaukan kuɗi daga masu biyan harajinku, amma ku ɗauki wanda aka karɓa ku ba waɗanda za su yi gyaran haikalin."8Sai firistoci suka yarda cewa ba za su ƙara karɓar kuɗi daga wurin mutane domin gyaran haikali da kansu ba.
9A maimakon, Yeho'iada firist ya ɗauki mazubi ya yi masa huduwa a ƙasa, ya ajiye shi kusa da bagadin, daga gefen dama dai-dai inda mutane ke shiga gidan Yahweh. Sai firistoci da ke kula da ƙofar shiga haikalin suka zuba dukkan kuɗin da aka kawo gidan Yahweh.10Da zarar sun ga akwai kuɗi da yawa a cikin mazubin, sai marubuta na sarki da manyan firistoci su zo su zuba kuɗin a jakkuna sai su ƙirga kuɗin da aka samu a haikalin Yahweh.
11Suka ba da kuɗin da aka tattaro daga hannun mutane masu kula da haikalin Yahweh. Suka biya masu aikin katako da magina waɗanda suka yi aiki a haikalin Yahweh,12haka kuma masu sayo katakai da yankawa, da masu sassaƙa duwatsu, domin gyaran haikalin Yahweh, da kuma duk abin da ake bukatar a biya shi.
13Amma kuɗin da aka kawo cikin haikalin Yahweh ba a biya domin aikin yin kofin zinariya da fitilu da kwangiri da kakaki, ko kuma duk wani aiki na azurfa ba.14Sun bada kuɗin ga waɗanda suka yi aikin gyaran gidan Yahweh.
15Haka kuma, basu bukaci kuɗi domin su biya masu biyan ma'aikata ba, domin waɗannan mutanen suna da aminci.16Amma kuɗin baiko na hadayar laifi da kuma na hadayar zunubi ba a kawo su zuwa cikin haikalin Yahweh ba, domin na firistoci ne.
17Sai Hazayel sarkin Aram ya kai hari kan Gat ya kuma kame ta. Sai ya Hazayel ya juyo domin ya kawo hari Yerusalem.18Sai Yo'ash sarkin Yahuda ya ɗauke duk abubuwan da Yehoshafat da Yehoram da Ahaziya mahaifinsa da sarkunan Yahuda suka keɓe, da dukkan zinariya da aka samu a ɗakin ajiya na gidajen Yahweh da na gidan sarki ya aika da su wurin Hazayel sarkin Aram Sai Hazayel ya fita daga Yerusalem.
19Game kuma da sauran abubuwa game da sarki Yo'ash da duk abin da ya yi, ashe ba a rubuta su a cikin littafin ayukan sarakunan Yahuda ba?20Sai barorinsa suka tashi suka haɗa kai suka shirya maƙarƙashiya; suka kai hari ga Yo'ash a Bet Millo, a kan hanyar da ta gangara zuwa Silla.21Jozabad ɗan Shimeyet da Yehozabad ɗan Shomar, bayinsa suka kai masa hari, ya kuma mutu. Suka bizne Yo'ash tare da kakanninsa a birnin Dauda, Amaziya, ɗansa ya zama sarki a madadinsa.

13

1A shekara ta ashirin da uku na Yo'ash ɗan Ahaziya sarkin Yahuda, Yehoahaz ɗan Yehu ya fara mulki akan Isra'ila da Samariya; ya yi mulkin har tsawon shekaru goma. sha bakwai.2Ya kuwa yi abin mugunta a fuskar Yahweh da bin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra'ila ta yi zunubi; kuma Yehoahaz bai juya baya daga hakan ba.

3Fushin Yahweh ya yi ƙuna gãba da Isra'ila, sai ya ci gaba da bada su ga hannun Hazayel sarkin Aram da kuma ga hannun Ben Hadad ɗan Hazayel.4Saboda haka Yehoahaz ya yi kira ga Yahweh, sai Yahweh ya saurare shi domin ya ga danniyar da ake yi wa Isra'ila, yadda sarkin Aram ya ke zaluntarsu.5Don haka sai Yahweh ya ba Isra'ila maceci, sai suka kuɓuta daga ƙasar Aramiyawan, sai mutanen Isra'ila suka fara zama a gidajensu kamar yadda suke a dã.
6Duk da haka, ba su kauce daga zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa Isra'ila suka yi zunubi, kuma suka ci gaba a cikin su; kuma gunkiyar Asherah tana nan a Samariya.7Aramiyawan suka bar Yehoahaz da mahayan dawakai hamsin ne kawai da karusai goma da dakarai dubu goma, gama sarkin Aram ya halakar da su kamar ƙaiƙai a lokacin casa.
8Akan sauran zantuttukan game da Yehoahaz kuwa, da dukkan abin da ya yi da ikonsa, ba an rubuta su littafin tarihin sarakunan Isra'ila ba?9Sai Yehoahaz ya kwanta tare da kakaninsa, aka kuwa bizine shi a Samariya. Yohoash ɗansa ya zama sarkin da ya gaje shi.
10A shekara ta talatin da bakwai na Yo'ash sarkin Yahuda, mulkin Yohoash ɗan Yahoahaz ya fara kan Isra'ila a Samariya; ya yi mulki shekara goma sha shida.11Ya yi abin mugunta a fuskar Yahweh. Bai bar ko wani abu daga zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, ta yadda ya sa Isra'ila ta yi zunubi, amma ya yi tafiya cikinsu.
12A batun sauran zantuttukan da suka shafi Yohoash, da dukkan abin da ya yi, da ikonsa ta yadda ya yaƙi Amaziya sarkin Yahuda, ba an rubuta su cikin littafin tarihin sarakunan Isra'ila ba?13Yohoash ya kwanta tare da kakaninsa, sai Yerobowam ya zauna a kursiyinsa. An bizne Yohoash a Samariya tare da sarakunan Isra'ila.
14Sai Elisha ya yi rashin lafiya da ciwon da yasa ya mutu daga baya, don haka sai Yohoash sarkin Isra'ila ya zo gare shi ya yi kuka a kansa. Ya ce, "Babana, babana, karusan Isra'ila da mahayan dawakanta suna ɗaukan ka!"15Elisha yace masa, "Ɗauki baka da kibbau," sai Yo'ash ya ɗauki baka da wassu kibbau.16Elisha ya cewa sarkin Isra'ila, "Ka sa hannuwanka a bakan," sai ya sa hannuwansa a nan. Sai Elisha ya dafa hannuwansa a hannuwan sarkin.
17Elisha yace, "Buɗe tagar da ke wajen gabas," sai ya buɗe ta. Sa'annan Elisha yace, "Harba!", sai ya harba. Elisha yace, "Wannan kibiyar nasarar Yahweh ce, kibiyar nasara akan Aram, gama za ka kai wa Aramiyawan hari a Afek har sai ka yi kaca kaca da su."18Sai Elisha yace, "Ɗauki kibau," sai Yo'ash ya ɗauke su. Ya cewa sarkin Isra'ila, "Ka caki ƙasa da su," sai ya caki ƙasa sau uku, sa'annan ya tsaya.19Amma mutumin Allah ya yi fushi da shi ya ce, "Da ka bugi ƙasa sau biyar ko shida. Sa'annan da ka kai wa Aram hari har sai ka hallakar da ita, amma yanzu za ka kai wa Aram hari sau uku ne kawai."
20Sai Elisha ya mutu, kuma aka bizne shi. Sai gungun Mowabawa suka mamaye ƙasar a farkon shekara.21Sa'ad da suke bizne wani mutun, suka ga gungũn Mowabawa, sai suka jefar da gangar jikin cikin kabarin Elisha. Da zarar mutumin ya taɓi ƙasussuwan Elisha, sai ya farfaɗo ya miƙe tsaye da kafafunsa.
22Hazayel sarkin Aram ya muzguna wa Isra'ila dukkan kwanakin Yehoahaz.23Amma Yahweh ya yi alheri ga Isra'ila, ya kuma ji tausayin su ya kuma kula da su, saboda alƙawarinsa ga Ibrahim, Ishaku da Yakubu. Don haka Yahweh bai hallakar da su ba, haka kuma bai kore su daga gare shi ba.
24Hazayel sarkin Aram ya mutu, sai Ben Hadad ‌ɗansa ya gaji sarautarsa.25Yehoash ‌ɗan Yehoahaz ya karɓi biranen daga Ben Hadah ‌ɗan Hazayel wan‌ɗanda Yehoahaz mahaifinsa ya ƙwato ta yaki. Yehoash ya kai masa hari sau uku, kuma ya karɓe biranen Isra'ila.

14

1A shekara ta biyu ta Yehoash ɗan Yehoahaz, sarkin Isra'ila, Amaziya ɗan Yo'ash, sarkin Yahuda, ya fara mulki.2Yana shekara ashirin da biyar sa'ad da ya fara sarauta; ya yi mulki na tsawon shekara ashirin da tara a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Yehoaddan, ta Yerusalem.3Ya yi abin da ke da kyau a fuskar Yahweh, duk da haka ba kamar Dauda mahaifinsa ba. Ya yi dukkan abin da Yo'ash, mahaifinsa, ya yi.

4Amma ba a kawar da wuraren yin tsafi a tuddai ba. Mutane dai suka yi ta miƙa hadaya da ƙona turare a tuddan tsafi.5Sai ya zamana sa'ad da mulkinsa ya kafu sosai, sai ya kashe barorin da suka kashe mahaifinsa sarki.
6Duk da haka bai kashe 'ya'yan masu kisan ba; maimakon haka, ya yi aiki bisa ga abin da ke rubuce a shari'a, a cikin Littafin Musa, kamar yadda Yahweh ya umurta, cewa, "Ubanni bai wajaba a kashe su saboda "ya'yansu ba, ko kuma a kashe 'ya'yan saboda iyayensu ba. Maimakon haka, duk mutumin da ya yi laifi lallai ne a kashe shi domin nasa zunuban."7Ya kashe sojoji dubu goma na Idom a Kwarin Gishiri; ya kuma cafko Sela a yaƙi ya kira ta Yoktil, kuma haka ake kiranta har wa yau.
8Sa'an nan Amaziya ya aiko da manzanni ga Yehoash ɗan Yehoahaz ɗan Yehu sarkin Isra'ila, cewa, "Ka zo, mu sadu da juna ido da ido a yaƙi."9Amma Yehoash sarkin Isra'ila ya aike manzani su mayar da Amaziya sarkin Yahuda, cewa, "'Yar ƙaya da ke Lebanan ta aiko da saƙo ga itacen al'ul a Lebanan, cewa, 'Ki ba da ɗiyarki ga ɗa na don aure,' amma naman jeji a Lebanan ya wuce ta wurin ya tattaka ƙayar.10Hakika ka kai wa Idom hari, kuma zuciyarka ta ɗaga ka sama. Ka yi fahariya da nasararka, amma ka zauna a gida, gama donme zaka sawa kanka matsala ka faɗi, da kai da Yahuda tare da kai?"
11Amma Amaziya bai saurara ba. Saboda haka Yehoash sarkin Isra'ila ya kai hari kuma shi da Amaziya sarkin Yahuda sun sadu da juna ido da ido a Beth Shemesh, wadda ke ta Yahuda.12Isra'ila ta kãda Yahuda, kuma kowanne mutun ya gudu gida
13Yehoash sarkin Isra'ila, ya kamo Amaziya, sarkin Yahuda ɗan Yehoash ɗan Ahaziya, a Beth Shemesh. Ya zo Yerusalem ya rushe bangon Yerusalem daga Ƙofar Ifraim zuwa Ƙofar Kwana, mai nisan mita ɗari da tamanin.14Ya ɗauke dukkan zinariya da azurfa da dukkan abubuwan da aka samu a gidan Yahweh, da abubuwa masu daraja na fãdar sarki, tare da mutanen da aka ba da su jingina, sai ya koma Samariya.
15Game da sauran zantuttukan da suka shafi Yehoash kuwa, dukkan abin da ya yi da ikonsa da yadda ya yi yaƙi da Amaziya sarkin Yahuda, ba an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila ba?16Sa'an nan Yehoash ya yi barci tare da kakaninsa kuma aka bizne shi a Samariya tare da sarakunan Isra'ila, kuma Yerobowam, ɗansa, ya zama sarki a madadin sa.
17Amaziya ɗan Yo'ash, sarkin Yahuda, ya yi shekara goma sha biyar bayan mutuwar Yehoash ɗan Yehoahaz, sarkin Isra'ila.18Game da sauran zantuttuka da suka shafi Amaziya, ba an rubota su a littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?19Suka yi maƙarƙashiya gãba da Amaziya a Yerusalem, sai ya gudu zuwa Lakish. Ya gudu zuwa ga Lakishna, amma an aiko da maza su bishi har Lakish su kashe shi a wurin.
20Suka dawo da shi akan dawakai, sai aka bizne shi tare da kakaninsa a birnin Dauda.21Dukkan mutanen Yahuda suka ɗauki Azariya, wanda ke shekara goma sha shida, suka maida shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya.22Azariya ne wanda ya gina Elat ya maida ita ta Yahuda, bayan Sarki Amaziya ya kwanta da kakaninsa.
23A shekara ta goma sha biyar ta sarautar Amaziya ɗan Yo'ash sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yehoash sarkin Isra'ila ya fara sarauta a Samariya; ya yi mulki shekara arba'in da ɗaya.24Ya aikata mugunta a fuskar Yahweh. Bai kauce wa dukkan zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra'ila ta yi zunubi.25Ya maida iyakar Isra'ila daga Lebo Hamath zuwa Tekun Arabah, bisa ga bin umurnai na kalmar Yahweh, Allahn Isra'ila, wanda ya faɗa ta wurin bawansa Yona ɗan Amittai, annabin nan da ke daga Gat Hefa.
26Gama Yahweh ya ga azabar da Isra'ila ke ciki, kowa yana cikin tsananin wahala, da bawa da sakakke, kuma babu maceci don Isra'ila.27Saboda haka Yahweh ya ce ba zai shafe sunan Isra'ila daga ƙarƙashin sammai ba; maimakon haka, Ya cece su ta hannun Yerobowam ɗan Yehoash.
28Game da sauran zantuttukan da suka shafi Yerobowam, da dukkan abin da ya yi da ikonsa, da yadda ya yi yaƙi ya ƙwato Damaskus da Hamath, waɗanda ke na Yahuda a dã, domin Isra'ila, Ba an rubuta su a littafin abubuwan da suka faru da sarakunan Isra'ila ba?29Yerobowam ya kwanta da kakaninsa, tare da sarakunan Isra'ila, sai Zekariya ɗansa ya zama sarki a madadinsa.

15

1A shekara ta ashirin da bakwai ta sarautar Yerobowam, sarkin Isra'ila, Azariya ɗan Amaziya sarkin Yahuda ya fara mulki.2Azariya yana shekara goma sha shida sa'ad da ya fara mulki, kuma ya yi sarauta ta shekara hamsin da biyu a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya, kuma ita daga Yerusalem take.3Ya yi abin da ke dai-dai a idanun Yahweh, kamar yarda mahaifinsa Amaziya ya yi.

4Sai dai, wuraren tsafin kan tuddai ba a rusa su ba. Mutanen dai na miƙa hadaya da ƙona turare a saman tuddai.5Yahweh ya addabi sarkin da kuturta har zuwa ranar mutuwarsa kuma ya yi ta zama a gidan da aka ware ne. Yotam, ɗan sarki, ya shugabanci gidan ya kuma yi mulkin mutanen ƙasar.
6Game da sauran zantuttukan da suka shafi Azariya da dukkan abin da ya yi, ba an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?7Saboda haka Azariya ya yi barci tare da kakaninsa; su ka bizne shi tare da kakaninsa a birnin Dauda. Yotam, ɗansa ya zama sarki a madadinsa.
8A shekara ta talatin da takwas ta Azariya sarkin Isra'ila, Zekariya ɗan Yerobowam ya yi mulki a Isra'ila ta Samariya na wata shida.9Ya yi abin mugunta a fuskar Yahweh, kamar yadda mahaifansa suka yi. Bai kauce daga zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra'ila ta yi zunubi.
10Shallum ɗan Yabesh ya ƙulla wa Zekariya maƙarƙashiya, ya kai masa hari a Ibleam, ya kashe shi. Sai ya zama sarki a madadinsa.11Game da sauran zantuttukan da suka shafi Zekariya, An rubuta su a littafin abubuwan da suka faru da sarakunan Isra'ila.12Wannan ne batun da Yahweh ya faɗa wa Yehu, cewa, "Zuriyarka za su zauna a gadon sarautar Isra'ila har zuwa tsara ta huɗu." Abin da ya faru kenan
13Shullum ɗan Yabesh ya fara mulki a shekara ta talatin da tara na Azariya sarkin Yahuda, kuma ya yi mulki na wata ɗaya a Samariya.14Menahem ɗan Gadi ya tafi can daga Tirza zuwa Samariya. a wurin ya kai wa Shullum ɗan Yabesh hari, a Samariya. Ya kashe shi ya kuma zama sarki a madadinsa.
15Game da sauran zantuttuka da suka shafi Shallum da maƙarƙashiya da ya shirya, a rubuce suke a littafin tarihin sarakunan Isra'ila. Sa'an nan16Menahem ya kai hari a Tifsa da dukkan waɗanda ke wurin da iyakar wuraren Tirzah, saboda ba su ba shi zarafin shiga birnin ba. Sai ya kai mata hari ya kuma feɗe dukkan mata masu junabiyu a ƙauyen nan.
17A shekara ta talatin da tara ta Azariya sarkin Yahuda, Menahem ɗan Gadi ya fara mulki a kan Isra'ila, Ya yi mulkin shekara goma a Samariya.18Ya yi abin mugunta a fuskar Yahweh. Gama a dukkan rayuwarsa, bai kauce daga zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra'ila ta yi zunubi.
19Sa'an nan Ful sarkin Asiriya ya zo gãba da ƙasar, sai Menaham ya bai wa Ful talanti dubu na azurfa, saboda Ful ya taimaka da gudumawa domin masarautar Isra'ila ta ƙarfafa a hannunsa.20Manehen ya ƙarbi wannan kuɗin daga Isra'ila ta wurin neman awo hamsin na azurfa daga dukkan atajiri domin ya bai wa sarkin Asiriya. Don haka Sarkin Asiriya ya juya baya kuma bai zauna cikin ƙasar ba.
21Game da sauran zantuttukan da suka shafi Manahem, da dukkan abin da ya yi, ba a rubuce suke a litaffin tarihin sarakunan Isra'ila ba?22Sai Manahem ya yi barci tare da kakaninsa, kuma Fekahiya ɗansa ya zama sarki a madadinsa.
23A shekara ta hamsin ta Azariya sarkin Yahuda, Fekahiya ɗan Menahem ya fara mulki a Isra'ila cikin Samariya; ya yi mulki shekara biyu.24Ya yi abin mugunta a fuskar Yahweh. Bai juya daga zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ta wurin hakan ya sa Isra'ila ta yi zunubi.
25Fekahiya yana da hafsa mai suna Feka ɗan Remaliya, wanda ya ƙulla masa maƙarkashiya. Tare da mutane hamsin na Giliyad, Feka ya kashe Fekahiya da kuma Argob da Ariye a Samariya, a cikin sansanin hasumayar fadar sarki. Feka ya kashe Fekahiya ya kuma zama sarki a madadinsa.26Game da sauran zantuttuka da suka shafi Fekahiya da dukkan abin da ya yi, a rubuce suke a littafin tarihin sarakunan Isra'ila.
27A shekara ta hamsin da biyu na Azariya sarkin Yahuda, Fekah ɗan Remaliya ya fara mulki akan Isra'ila cikin Samariya; ya yi mulki shekara ashirin.28Ya yi abin mugunta a fuskar Yahweh. Bai kauce daga zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra'ila ta yi zunubi.
29A kwanakin Feka sarkin Isra'ila, Tiglat Filesa sarkin Asiriya ya zo ya ɗauki Ijon da Abel Bet Ma'aka da Janoya da Kedesh da Hazor da Giliyad da Galili da dukkan ƙasar Naftali. Ya ɗauki mutanen zuwa Asiriya.30Don haka Hosheya ɗan Elah ya shirya maaƙarƙashiya găba da Feka ɗan Remaliya. Ya kai masa hari ya kuma kashe shi. Sa'an nan ya zama sarki a madadinsa, a shekara ta ashirn ta yotam ɗan Uzziya.31Game da sauran zantuttukan da suka shafi Feka da dukkan abin da ya yi, a rubuce suke a littafin tarihin sarakunan Isra'ila.
32A shekara ta biyu ta Peka ɗan Remaliya, sarkin Isra'ila, Yotam ɗan Azariya, sarkin Yahuda ya fara mulki.33Yana da shekara ashirin da biyar a sa'ad da ya fara mulki; Ya yi mulki shekara goma sha shida a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Yerushah; Ita ɗiyar Zadok ce.
34Yotam ya yi abin da ke da kyau a fuskar Yahweh. Ya bi misalin dukkan abubuwan da mahaifisa Azariya ya yi.35Duk da haka, ba a ƙwato wuraren tsafin kan tuddai ba. Mutanen na yin hadaya da ƙona turare a samman tuddai, Yotam ya gina ƙofarta bisa ta gidan Yaweh.36Game da sauran zantuttukan da suka shafi Yotam, da dukkan abin da ya yi, ba a rubuta su a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?
37A kwanakin nan ne Yahweh ya fara aiko da Rezin sarkin Aram da Peka ‌ɗan Remaliya gaba da Yahuda.38Yotam ya kwanta da kakaninsa a birnin Dauda, kakansa. Sa'an nan Ahaz ‌ɗansa ya zama sarki a ma‌da‌dinsa.

16

1A shekara ta goma sha bakwai ta Feka ɗan Remaliya,2Ahaz ɗan Yotam sarkin Yahuda, ya fara mulki, kuma ya yi mulki shekara goma sha shida a Yerusalem. Bai yi abin da ke dai-dai a fuskar Yahweh Allahnsa ba, kamar yadda Dauda kakansa ya yi ba.

3Maimakon haka, ya yi tafiya a hanyar sarakunan Isra'ila; hakika, ya sa ɗansa a wuta domin hadaya ta ƙonawa, yana bin ayyukan ban ƙyama na al'ummai, waɗanda Yahwe ya fitar daga gaban mutanen Isra'ila.4Ya miƙa hadayu da kuma ƙona turare awurare bisa tuddai da ƙarƙashin kowanne koren Itace.
5Sa'an nan Rezin, sarkin Aram da Feka ɗan Remaliya, sarkin Isra'ila, ya zo Yerusalem ya kawo hari. Suka tunkari Ahaz, amma ba su iya mamayar sa ba.6A lokacin nan, Rezin sarkin Aram ya maido Elath domin Aram ya kori mazajen Yahuda daga Elat. Sa'an nan Aramiyawa suka zo gun Elat inda suka zauna har yau.
7Sai Ahaz ya aiki manzanni ga Tiglat Filesa sarkin Asiriya, cewa, "Ni baranka ne da ɗanka. Ka zo ka cece ni daga hannun sarkin Aram da hannun sarkin Isra'ila, waɗanda suka kawo mani hari."8Sai Ahaz ya ɗauki azurfa da zinariyan da aka tarar a gidan Yahweh da na cikin kayayyaki masu daraja na fãdar sarki ya aikar da su kyauta ga sarkin Asiriya.9Sa'an nan sarkin Asiriya ya saurare shi, kuma sarkin Asiriya ya farmaƙi Damaskus, ya mamaye ta, ya kuma ɗauke mutanenta ya kai su zaman bauta a Kir. Ya kuma kashe Rezin sarkin Aram.
10Sarki Ahaz ya tafi Damaskus ya sadu da Tiglat Filesa sarkin Asiriya. A Damaskus ya ga wani bagadi. Ya aika wa Yuriya firist irin fasalin bagaden da yanayinsa da zane domin dukkan aikin da ake bukata.11Don haka Yuriya firist ya gina bagaden da zai zama kamar tsarin da sarki Ahaz ya aiko daga Damaskus. Ya gama shi kafin sarki Ahaz ya dawo daga Damaskus.12Sa'ad da sarki ya zo daga Damaskus ya ga bagaden; sarkin ya kusanci bagaden ya kuma yi bayarwa akan sa
13Ya yi hadayarsa ta ƙonawar da hadayarsa ta hatsi, ya zubo hadayarsa ta sha, ya yayyafa jinin hadayarsa ta zumunci a bagaden.14Bagaden tagulla wanda ke gaban Yahweh - ya kawo shi daga gaban haikalin, daga tsakanin bagaden da haikalin Yahweh ya sa shi a gefen arewacin bagadensa
15Sai sarki Ahaz ya umurci Yuriya firist, cewa, "A babban bagaden ka ƙona baikon ƙonawa na safe da baikon hatsi na yamma, da kuma baikon na ƙonawa na sarki da baikon hatsinsa, da baikon na ƙonawa na dukkan mutanen ƙasar, da baikon hatsinsu da baikon shansu. Ka yayyafa jinin akan dukkan baiko na ƙonawa, da dukka jinin hadayar. Amma bagadin tagulla zai zama nawa domin neman shawara don jagoranci."16Yuriya firist kuwa ya yi abin da sarki Ahaz ya umurta.
17Sa'an nan sarki Ahaz ya ciro dakalan da darunan da suke bisansu; ya kuma ɗauke babban daron daga bijimin tagullar da ke ƙarƙashinsa ya sa shi a daɓen dutse.18Ya cire hanyar da aka killace ta Asabaci wanda aka gina a haikalin, tare da ƙofar dake waje ta shigar sarki zuwa haikalin Yahweh, saboda sarkin Asiriya.
19Game da sauran zantuttukan da suka shafi Ahaz da abin da ya yi, ba a rubuce suke cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?20Ahaz ya kwanta da kakaninsa aka kuma bizne shi tare da kakaninsa a birnin Dauda. Hezekiya ɗansa ya zama sarki a madadinsa.

17

1A shekara ta goma sha biyu ta Ahaz sarkin Yahuda, mulkin Hosheya ɗan Elah ya fara, ya yi mulki a Samariya akan Isra'ila na shekara tara.2Ya yi abin mugunta a fuskar Yahweh, duk da haka ba kamar sarakunan Isra'ila waɗanda suka gabace shi ba.3Shalmaneser sarkin Asiriya ya kai masa hari, kuma Hosheya ya zama baransa ya kawo masa haraji.

4Sa'an nan sarkin Asiriya ya gano cewa Hosheya na ƙulla maƙarƙshiya gãba da shi, don Hoshiya ya aiko manzanni ga So sarkin Masar; haka kuma, babu kyautar da ya miƙo wa sarkin Asiriya, kamar yadda ya saba yi shekara da shekara. Saboda haka sarkin Assiriya ya kulle shi ya ɗaure shi a kurkuku.5Sa'an nan sarkin Asiriya ya kai hari a ko'ina a ƙasar, ya kuma kai wa Samariya hari ya mamaye ta shekara uku.6A shekara ta tara ta Hosheya, sarkin Asiriya ya ɗauki Samariya ya kuma ɗauki Isra'ila zuwa Asiriya. Ya sa su a Halah, a harabar Kogin Gozan, da kuma cikin biranen Medeyawa.
7Mãmewar ta faru ne saboda mutanen Isra'ila sun yi zunubi ga Yahweh Allahnsu, wanda ya kawo su daga ƙasar Masar, daga ƙarƙashin hannun Fir'auna sarkin Masar. Mutanen suna bautawa waɗansu alloli ne8kuma suna tafiya cikin ayyukan al'umman da Yahweh ya kora daga mutanen Isra'ila, da kuma cikin ayyukan sarakunan Isra'ila da suka yi.
9Mutanen Isra'ila sun yi wa Yahweh Allahnsu abubuwan da ba dai-dai ba a asirce. Sun gina wa kansu manyan wurare a dukkan biranensu, daga hasumiya zuwa birni mai garu.10Suka kuma kafa ginshiƙai da sandunan Ashera a ko'ina bisan tudu da ƙarƙashin dukkan koren itace.
11A wurin suka ƙona turare cikin dukkan wurare masu bisa, kamar yarda al'ummai suka yi, waɗanda Yahweh ya fitar da su kafin su. Isra'ilawa sun aikata mugayen abubuwan da suka zuga Yahweh ga fushi,12sun bauta wa gumaka, irin waɗanda Yahweh ya ce masu, "Ba za ku yi wannan abin ba."
13Duk da haka Yahweh ya yi shaida ga Isra'ila da kuma ga Yahuda ta wurin kowanne annabi da kowanne mai gani, cewa, "Ku juyo daga hanyoyin mugunta ku tsare dokokina da farillaina, kuma ku yi hankali da tsare dukkan dokokin da na ummurce ubanninku, da waɗanda na aiko maku ta hanun barorina annabawa."
14Amma ba za su saurara ba; maiimakon haka suka taurare kamar ubanninsu waaɗnda ba su da aminci cikin Yahweh Allahnsu.15Suka ƙi dokokinsa da alƙawarin da ya yi da kakaninsu, da ummurnan alƙawarin da ya ba su. Suka bi ayyuka marasa amfani kuma su kansu suka zama marasa amfani. Suka bi al'umman arnan da ke kewaye da su, waɗanda Yahweh ya ummurce su kada su kwaikwaye su.
16Suka ƙyale dukkan dokokin Yahweh Allahnsu. Suka ƙera sifofin zubi na ƙarfe na 'yan muruƙa biyu domin su bauta masu. Suka yi sandan Ashera, kuma suka bautawa dukkan taurari na sama da Ba'al.17Suka sa 'ya'yansu maza da 'ya'yansu mata cikin wutan, suka yi duba da tsubbace tsubbace, suka sayar da kansu don su yi abin da ke mugu a fuskar Yahweh, kuma suka sa shi shi ya yi fushi.18Saboda haka Yahweh ya yi matuƙar fushi da Isra'ila ya cire su daga gabansa, Babu wanda aka bari ban da ƙabilar Yahuda ita ƙaɗai.
19Ko Yahuda ma ba su tsare dokokin Yahweh Allahnsu ba, amma maimakon haka suka bi abin da Isra'ila ta yi.20Sai Yahweh ya ƙi dukkan zuriyar Isra'ila; ya wahalshe su ya bada su ga hannun waɗanda za su ɗauki mallakarsu a matakin ganima, har sai da ya watsar da su daga fuskarsa
21Y a yago Isra'ila daga sarautar ta layin Dauda, suka kuma maida Yerobowam ɗan Nebat ya zama sarki. Yerobowam ya kawar da Isra'ila daga bin Yahweh ya sa suka aikata gagarumin zunubi.22Mutanen Isra'ila kuwa suka bi dukkan zunuban Yerobowam kuma ba su kauce daga yin su ba,23saboda haka Yahweh ya cire Isra'ila daga fuskarsa, kamar yadda ya faɗa ta wurin barorinsa annabawa cewa zai yi. Saboda haka aka ɗauke Isra'ila daga tasu ƙasar zuwa Asiriya, kuma haka yake har wannan rana
24Sarkin Asiriya ya kawo mutane daga Babila da Kutha da Avva da Hamat da Sefabayim, sai ya sa su a biranen Samariya a madadin mutanen Isra'ila. Suka mamaye Samariya suka zauna a biranenta.25Ya kasance a farkon zamansu a wurin ba su girmama Yahweh ba. Sai Yahweh ya aiko da Zakunan da suka kashe waɗansu daga cikinsu.26Sai suka yi magana da sarkin Asiriya, cewa, "Al'umman da ka ɗauke su ka sã a biranen Samariya ba su san ayyukan da allahn ƙasar ke buƙata ba. Saboda haka a aiko da zakuna a cikinsu, kuma, duba, zakunan na karkashe mutane a wurin saboda basu san ayyukan da allahn ƙasar ke buƙata ba
27Sa'an nan sarkin Asiriya ya ummurta, cewa, "Ɗauki ɗaya daga cikin firistocin wurin waɗanda ka kawo su daga wurin, kuma sai ya je ya zauna a wurin, ya kuma bari a koyar da su ayyukan da allan ƙasar ya sa a yi."28Sai ɗaya daga cikin firistocin da aka ɗauko daga Samariya ya zo ya zauna a Betel; ya koya masu yadda za su girmama Yahweh.
29Kowacce kabila sun yi alloli na kansu, kuma suka sa su a wuraren da Samariyawa suka yi - kowacce kabila a biranen da suke zama.30Mutanen Babila suka yi Succot Benot; mutanen Kuta suka yi Nergal; mutanen Hamat suka yi Ashima;31Avvitawa suka yi Nibhaz da Tartak. Sefavitawa suka ƙone 'ya'yansu a wuta ga Adrammelek da Anammelek, allolin Sefavitawa.
32Suka girmama Yahweh, kuma suka naɗa firistocin manyan wuraren daga cikinsu, waɗanda ke yin masu hadaya a masujadai na tuddan wuraren.33Suka girmama Yahweh suka kuma bauta wa alloli na kansu, bisa ga al'adar al'umman da aka kawar.
34Har wa yau suna ci gaba da al'adun dã. Basu girmama Yahweh, ko su bi farilla da umurni da doka, ko dokokin da Yahweh ya ba mutanen Yakubu - wanda ya kira Isra'ila ba -35kuma wanda Yahweh ya yi alƙawari ya kuma ummurce su, "Kada ku ji tsoron waɗansu alloli, ko ku russunar da kanku gare su, ko ku bauta masu ko ku yi masu hadaya.
36Amma Yahweh, wanda ya fito da ku daga ƙasar Masar da iko mai girma da dantse a ɗage, shi ne wanda za ku girmama; gare shi ne za ku yi ruku'u, kuma gare shi za ku yi hadaya.37Da Farillan da ummurnan da attaura da dokokin da ya rubuta domin ku, za ku tsare su har abada. Saboda kada ku ji tsoron waɗansu alloli,38kuma alƙawarin da na yi da ku, ba zaku mance ba; kuma ba za ku girmama waɗansu alloli ba.
39Amma Yahweh Allahnku shi ne wanda za ku girmama. Zai ƙuɓutar da ku daga ikon maƙiyanku."40Ba za su saurara ba, saboda sun ci gaba da yin abin da suke yi a baya.41Don haka al'umman sun ji tsoron Yahweh suka kuma bauta wa ƙerarrun sifofinsu, kuma 'ya'yansu suka yi hakan kuma - kamar yadda 'ya'yan 'ya'yansu suka yi. Suka ci gaba da yin abin da kakaninsu suka yi har wa yau.

18

1Yanzu a shekara ta uku na Hosheya ɗan Ela, sarkin Isra'ila, Hezekiya ɗan Ahaz, sarkin Yahuda ya fara mulki.2Yana da shekara ashirin da biyar sa'ad da ya fara mulki; ya yi mulki shekara ashirin da tara a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Abija; ita ɗiyar Zekariya ce.3Ya yi abin da ke dai-dai a fuskar Yahweh, ya na bin misalin dukkan abubuwan da Dauda, kakansa ya yi.

4Ya kawar da tuddan wurare, ya rusar da ginshiƙan dutse, ya farfashe sandan Ashera. Ya kakkarya tagullar macijin da Musa ya yi, saboda a kwanakin dã mutanen Isra'ila suna ƙona mata turare; a na kiran ta "Nehushtan."5Hezekiya ya dogara ga Yahweh, Allahn Isra'ila, saboda bayansa babu wani kamarsa a cikin sarakunan Yahuda, koma a cikin waɗanda suka gabace shi.
6Gama ya manne wa Yahweh. Bai daina binsa ba gama ya kiyaye dokokinsa, waɗanda Yahweh ya ummurci Musa.7Saboda haka Yahweh yana tare da Hezekiya, kuma duk inda ya je ya wadata. Ya yi wa sarkin Asiriya tawaye kuma bai bai bauta masa ba.8Ya kai wa Filistiyawa hari har Gaza da iyakar da ke kewaya, daga hasumiyar zuwa birni mai garu.
9A shekara ta huɗu na Hezekiya, wadda ke dai-dai da shekara ta bakwai ta Hosheya ɗan Elah sarkin Isra'ila, Shalmanesar sarkin Asiriya ya kawo wa Samariya hari ya mamaye su.10A ƙarshen shekaru uku suka ɗauke ta, a shekara ta shida na Hezekiya, wanda ke shekara ta tara ta Hosheya sarkin Isra'ila; a wannan hanyar kuwa aka kame Samariya.
11Sai sarkin Asiriya ya ɗauki Isra'la zuwa Asiriya ya sa su a Halah da kuma a kogin Habor a Gozan da biranen Medeyawa.12Ya yi wannan ne saboda ba su yi biyayya da muryar Yahweh Allahnsu ba, amma sun wofintar da ƙudurorin alkawarinsa, dukkan abin da Musa bawan Yahweh ya ummurta. Suka ƙi su ji ko su aikata shi.
13Sa'an nan a shekara ta goma sha huɗu ta Sarki Hezekiya, Senakerib sarkin Asiriya ya kai wa dukkan birane masu garu na Yahuda hari ya kuma danƙe su.14Saboda haka Hezekiya sarkin Yahuda ya aika wa sarkin Asiriya, wanda ke Lakish da kalma, cewa, "Na yi maka laifi. Ka janye daga gare ni. Duk abin da ka ɗora mani zan ɗauka." Sarkin Asiriya kuwa ya umarci Hezakiya sarkin Yahuda ya bada talanti ɗari uku na azurfa da talatin na zinariya masu yawa.15Sai Hezekiya ya ba shi dukkan azurfan da ke gidan Yahweh da na cikin ma'aji na fãdar sarki.
16Sa'an nan Hezekiya ya ciro zinariyar da ke ƙofofin haikalin Yahweh da kuma daga madogaran da aka kafa; ya ba da zinarin ga sarkin Assiriya.17Amma sarkin Asiriya ya shiryo gagarumin sojojinsa, Ya aiki Tartan da Rabsaris da babbar rundunar sojojin daga Lakish zuwa ga Sarki Hezekiya a Yerusalem. Suka yi tafiya ta hanyoyin su ka kai wajen Yerusalem. Suka nufi kududdufi na sama wurin kwanciyar ruwa, wanda ke a kan kwaruwa zuwa wurin wanki, suka tsaya ta wurin.18Sa'ad da suka yi kira ga Sarki Hezekiya, Eliyakin ɗan Hilkiya, wanda ke wakilin gidan da Shebna magatakarda da Yowa ɗan Asaf, mai rubutun rohoto suka je su sadu da su.
19Sai shugaban rundunar sojojin ya ce masu su faɗa wa Hezekiya abin da sarki mai girma, sarkin Asiriya, ya faɗa: "Mene ne masomin karfin halinka?20Kana faɗin kalmomi marasa amfani ne kawai, cewa akwai tarayya da ƙarfi domin yaƙi. Ga wa kake dogara? har da za ka tayar mani?21Duba, ka dogara ga sandan tafiya na raunannan ciyayin Masar, amma idan mutum ya manne mata, za ta haɗu da hannunsa ta soke shi. Wannan ne abin da Fir'auna sarkin Masar ya ke ga duk wanda ya dogara gare shi.
22Amma idan ka ce mani, 'Muna dogara ga Yahweh Allahnmu ne,' ba shi ne wanda Hezekiya ya ɗauke masa wuraren sama da bagaden ba, ya kuma cewa Yahuda da Yerusalem, 'Lallai sai kun yi sujada a gaban bagaden nan a Yerusalem'?23Yanzu dai, ina so in yi maka gudunmawa daga ubangijina sarkin Asiriya. Zan baka dawakai dubu biyu, idan za ka samar masu mahaya.
24Ta yaya zaka ma iya karawa da mafi ƙanƙantar shugaban sojojin ubangijina? Ka bada ƙarfinka ga Masar domin karusai da mahaya!25Na taɓa zuwa nan in yi yaƙi in hallka ta ba tare da Yahweh ba? Yahweh ya ce mani, 'Ka kai wa ƙasar nan hari ka hallaka ta."'
26Sa'an nan Eliyakim ɗan Hilkaya da Shebna da Yowa suka cewa shugaban rundunar, "In ka yarda ka yi magana da harshen Aramayik, don shi muka gane. Kada ka yi magana da mu da harshen Yahuda a kunnen mutanen da ke a bangon."27Amma shugaban rundunar ya ce masu, Ba maganar da ubangijina ya aike ni ga ubangijinku in faɗa kenan ba? Ba shi ya aiko ni wurin mazan da ke zaune a bangon, waɗanda za su ci kaãshinsu su kuma sha fitsarinsu tare da ku ba?"
28Sa'an nan shugaban rudunar sojojin ya tsaya ya yi kira da babbar murya a harshen Yahudawa, cewa, "Ku saurari maganar sarki mai girma, sarkin Asiriya.29Sarkin ya ce, 'Kar ka bar Hezekiya ya ruɗe ka, gama ba zai iya ya ƙubutar da kai daga ikona ba.30Kada ku yarda Hezekiya yasa ku dogara ga Allah, cewa, "Hakika Yahweh zai cece mu, kuma ba za a ba da wannan birnin ga hannun sarkin Asiriya ba.""
31Kada ku saurari Hezekiya, gama ga abin da sarkin Asiriya ya ce: 'Ku yi amana da ni ku kuma zo gare ni. Sa'an nan kowannen ku zai ci daga tasa kuringar inabi da itacen ɓaurensa ya kuma sha daga cikin randarsa.32Zaku yi haka har lokacin da zan zo in ɗauke ku in kaiku wata ƙasa mai kama da taku, ƙasar hatsi da sabon ruwan inabi, ƙasar gurasa da lambuna, ƙasar itatuwan zaitun da zuma, saboda ku rayu kar ku mutu.' Kada ka saurari Hezekiya sa'ad da yake ƙoƙarin rinjayarku, cewa, 'Yahweh zai cece mu.'
33Ko akwai wani daga cikin allolin mutanen da ya ceto su daga hanun sarkin Asiriya?34Ina allolin Hamat da Arfad? Ina allolin Sefabayim da Hena da Ivvah? Sun ceto Samariya daga hannuna ne?35A cikin allolin ƙasashe, akwai wani allahn da ya ceci ƙasarsa daga ikona? Ta yaya Yahweh zai ceci Yerusalem daga ikona?"
36Amma mutane suka yi shiru basu ce uffan ba, domin sarki ya bada umarni, "Kada ku amsa masa."37Sai Eliyakim ɗan Hikiya, wanda ke shugabantar gidan; Shebna magatakarda; da Yowa ɗan Asaf, mai ɗaukan rohoto, suka zo wurin Hezikiya da tufafinsu a yage, suka bada rahoto gare shi kan maganganun babban hafsan.

19

1Sai ya zamana sa'ad da sarki Hezekiya ya ji rohotonsu, ya yayyaga tufafinsa, ya rufe kansa da tsumma, ya je gidan Yahweh.2Ya aiki Eliyakim, wanda ke lura da gidan, da Shebna magatakarda, da dattawan firistoci, dukkan su saye da tufafin tsumma, ga annabi Ishaya ɗan Amoz.

3Suka ce masa, "Hezekiya ya ce, 'wannan ranar ta ƙunci da tsutawa da bankunya, gama 'ya'ya sun kai lokacin haifuwa amma babu ƙarfi domin haifar su.4Yana yiwuwa Yahweh Allahnka zai ji dukkan kalmomin shugaban rundunar, wanda sarkin Asiriya ubangijinsa ya aiko don ya jã da Allah, ya kuma tsauta wa kalmomin da Yahweh Allahnka ya ji. To ka ɗaga murya cikin addu'arka domin ragowar da ke nan har yanzu.""
5Saboda haka barorin sarki Hezekiya suka zo wurin Ishaya,6sai Ishaya ya ce masu, "Ku faɗawa shugabanku: 'Yahweh ya ce, "Kada ku ji tsoron kalmomin da kuka ji, waɗanda barorin sarkin Asiriya suka yi mani rashin kunya.7Duba, zan sa wani ruhu a cikinsa, sai ya ji wani rohoto ya koma zuwa ƙasarsa. Zan sa ya fãɗi ta takobi a nasa ƙasan.""'
8Sa'an nan shugaban rundunan ya komo ya tarar sarkin Asiriya yana yaƙi da Libna, gama ya ji wai sarkin ya tashi daga Lakish.9Sa'an nan Senakirib ya ji cewa Tirhaka sarkin Kush da Masar sun yi shiri su yaƙe shi, sai ya aiki manzanni kuma ga Hezekiya da saƙo:
10"Ku cewa Hezekiya sarkin Yahuda, 'Kada ka bar Allahnka wanda ka dogara gare shi ya ruɗe ka, cewa, "Ba zan ba da Yerusalem ga hannun sarkin Asiriya ba."11Duba, ka ji abin da sarkin Asiriya ya yi wa dukkan ƙasashe da ya hallakar da su sarai. To za ka kuɓuta?
12Allolin al'ummai sun kuɓutar da su ne, al'umman da ubannina suka hallakar wato Gozan da Haran da Rezef da mutanen Eden a Tel Assar?13Ina sarakunan Hamat da na Arfad da na biranen Sefabayim da Ivvah?"'
14Hezekiya ya karɓa wasiƙar daga manzannin ya karanta ta. Sai ya haura zuwa gidan Yahweh ya shinfiɗa ta a gabansa.15Sa'an nan Hezekiya ya yi addu'a a gaban Yahweh ya ce, '"Yahweh mai runduna, Allahn Isra'ila, Kai da ke zaune bisan kerubim, kai kaɗai ne Allah akan dukkan mulkokin duniya. Ka yi sammai da duniya.
16Ka kasa kunnenka, Yahweh, ka saurara. Ka buɗe idanuwanka Yahweh, ka gani, ka kuma ji kalaman Senakerib, waɗanda ya aiko don ya yi wa Allah mai rai ba'a.17A gaskiya, Yahweh, sarakunan Asiriya sun hallakar da al'ummai da ƙasashensu.18Suka sa allolinsu cikin wuta, gama su ba alloli ba ne amma aikin hannuwan mutane ne, katako da dutse kawai. Don haka Asiriyawan suka hallaka su.
19Yanzu, Yahweh Allahnmu, I na roƙe ka, ka cece mu, daga ikonsa, saboda dukkan mulkokin duniya su sani cewa kai, Yahweh, kai kaɗai ne Allah."
20Sa'an nan Ishaya ɗan Amoz ya aiko da saƙo ga Hezekiya, cewa, "Yahweh, Allahn Isra'ila ya faɗi, 'Saboda ka yi addu'a gare ni game da Senakerib sarkin Asiriya, Na ji ka.21Wannan ita ce maganar da Yahweh ya faɗa game da shi: "Budurwan nan ɗiyar Sihiyona ta rena ka tana kuma yi maka dariyar reni. Ɗiyar Yerusalem na girgiza maka kanta.22Wane ne ka saɓa wa ka kuma yi wa reni? Wanda kuma ka ɗaukaka muryarka ka ɗaga idanuwanka cikin taƙama gãba da shi? Gãba da Mai Tsarkin Isra'ila!
23Ta manzaninka ka saɓa wa Ubangiji, har ka ce, 'Tare da ɗumbin karusaina na kai duwatsu mafi tsawo, mafi tsawon tudddai ta Lebanan. Zan datse dogayen itatuwan sida da zaɓaɓɓun itatuwan Sifires a wurin. Zan shiga cikin manisancin kurminta, da dajinta da ya fi bada 'ya'ya.24Na gina rijiyoyi na kuma sha ruwan baƙuwar ƙasa. Na busar da dukkan kogunan Masar a ƙarƙashin tafin ƙafafuna.'
25Ba ka taɓa jin yadda na ƙudura shi da daɗewa ba, na kuma yi shi tun zamanin zamanai ba? Yanzu zan aiwatar da shi. Kana nan domin rage birane masu wadata su zama kufai.26Mazaunansu, masu ƙarancin ƙarfi, suna a warwatse, kuma an kunyata su. Su ganyaye ne a fili, koriyar ciyawa, ciyawa a rufi ko a fili, da aka ƙone kafin ta yi girma.
27Amma na san yadda kake zama a ƙasa da fitarka da shigarka, da tawayenka gãba da ni.28Saboda tayarwarka gãba da ni, kuma saboda taƙamarka ta kai kunuwana, zan sa ƙugiya a hancinka, da linzami a bakinka; zan komo da kai baya ta inda ka iso."
29Wannan zai zama alama a gare ka: wannan shekarar za ku ci abin da ke girma a jeji, a shekara ta biyu kuma, abin da ya fita daga nan. amma a shekara ta uku kuma dole ka shuka ka girba, ka shuka gonakin inabi ka ci 'ya'yan itatuwansu30Ragowar gidan Yahuda da suka rayu za su sake yin saiwa su yi "ya'ya.31Gama daga Yerusalem za a fito da ragowa, daga Tsaunin Sihiyona waɗanda suka tsira za su zo. Himmar Yahweh mai runduna za ta yi haka.
32Saboda haka Yahweh ya faɗi haka game da sarkin Asiriya: "Ba zai zo cikin birnin ko ya harba kibiya a nan ba. Ko kuwa ya zo gabansa da garkuwa ko ya gina sansani gãba da shi ba.33Ta hanyar da ya zo, ta nan kuma zai tafi; ba zai shiga wannan birnin ba - wannan furcin Yahweh ne."34Gama zan kãre wannan birnin in kuɓutar da shi, domin kaina da kuma domin bawana Dauda."'
35Sai ya zamana a daren nan da mala'ikan Yahweh ya je ya kai hari ga sansanin Asiriyawa, ya sa sojoji 185,000 suka mutu. Sa'ad da mazaje suka tashi da sassafe, sai ga gawawwaki kwance ko'ina.36Saboda haka Senakerib sarkin Asiriya ya bar Isra'ila ya tafi gida ya zauna a Nineba.37Bayan 'yan lokuta ƙaɗan, yayin da yake yin sujada a gidan allansa Nisrok, sai 'ya'yansa Adrammalek da Shareza suka kashe shi da takobi. Sa'an nan suka tsere zuwa ƙasar Ararat. Sai Esarhadon ɗansa ya zama sarki a madadinsa

20

1A kwanakin nan Hezekiya ya yi rashin lafiya har ya kusa da mutuwa. Saboda haka annabi Ishaya ɗan Amoz, ya zo gare shi, ya ce masa, "Yahweh ya ce, 'Ka shirya gidanka; gama zaka mutu, ba zaka rayu ba."'2Sa'an nan Hezekiya ya juya fuskarsa ga bango ya yi addu'a ga Yahweh yana cewa,3"In ka yarda Yahweh, ka tuna da yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da dukkan zuciyata, da kuma abubuwan masu kyau da na yi a fuskarka." Sai Hezekiya ya yi kuka.

4Kafin Ishaya ya fita cikin tsakiyar fãdar, maganar Yahweh ya zo gare shi, cewa,5"Ka juya baya, ka cewa Hezekiya, shugaban mutanena, 'Wannan shi ne abin da Yahweh, Allahn Dauda kakanka na asali, ya ce: "Na ji addu'arka, na ga hawayenka. Ina gab da warkar da kai a rana ta uku, kuma za ka haura zuwa gidan Yahweh.
6Zan ƙara shekaru goma sha biyar ga rayuwarka, zan kuɓutar da wannan birnin daga hannun sarkin Asiriya, kuma zan kare birnin nan domin kaina domin kuma bawana Dauda"""7Sai Ishaya yace, "Ka ɗauki curin ɓaure."Su ka yi haka suka sa a marurunsa, sai ya samI lafiya.
8Hezikiya ya cewa Ishaya, "Mene ne zai zama alamar cewa Yahweh zai warkar da ni, da kuma zai sa ni in je haikalin Yahweh a rana ta uku?"9Ishaya ya amsa, "Wannan ne zai zama alama dominka daga Yahweh, cewa Yahweh zai yi abin da ya faɗa. Inuwa ta yi gaba da taki goma, ko ta yi baya da taki goma?"
10Hezekiya ya amsa, "Abu mai sauki ne ga inuwa ta yi gaba da taƙi goma. A'a, bari Inuwa ta yi baya da taƙi goma."11Sai annabi Ishaya ya yi kira ga Yahweh, sai ya komo da inuwar taƙi goma baya, daga inda ta motsa a matakalin Ahaz.
12A lokacin nan Marduk-Baladan ɗan Baladan sarkin Babila ya aika da wasiƙu da kyautai ga Hezekiya, gama ya ji cewa Hezekiya ba shi da lafiya.13Hezekiya ya saurari wasiƙun nan, sai ya nuna wa manzaNnin dukkan fǎda da abubuwa masu daraja da azurfa da zinariya da kayan ƙanshi da mai, mai daraja da gidan ajiyar kayan yaƙi da dukkan abin da ke samuwa a gidajen ajiyarsa. Babu wani abu a gidansa, ko a mulkinsa, da Hezekiya bai nuãna masu ba.
14Sa'annan annabi Ishaya ya zo wurin sarki Hezekiya ya tambaye shi, "Mene ne waɗannan mazajen suka ce maka? Daga ina suka fito?" Hezekiya ya ce, "Sun zo daga ƙasa mai nisa ta Babila."15Ishaya ya tambaye shi, "Mene ne suka gani a gidanka?" Hezekiya ya amsa, "Sun ga kome a gidana. Babu wani abu cikin abubuwa masu daraja da ban nuna masu ba."
16Sai Ishaya ya cewa Hezekiya, "Ka saurari maganar Yahweh:17'Duba, ranakun na kusatowa da kowanne abu a fǎdarka, da abubuwan da kakaninka suka ajiye har zuwa yau, za a ɗauke su zuwa Babila. Babu abin da zai rage, inji Yahweh.18'Ya'yan da aka haifa maka waɗanda kai da kanka kake mahaifinsu - za a ɗauke su, zasu kuma zama bãbãni a fãdar sarkin Babila."'
19Sa'annan Hezekiya ya cewa Ishaya, "Maganar Yahweh da ka faɗa tana da kyau." Saboda yana tunanin, "Ba za a sami salama da zaman lafiya a kwanakina ba?"20Game da waɗansu zantuttuka da suka shafi Hezekiya, da dukkan ikonsa da yadda ya yi tafki da wuriyar ruwa, da yadda ya kawo ruwa cikin birnin - ba a rubuce suke cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?21Hezekiya ya yi barci tare da kakaninsa, sai Manasse ɗansa ya zama sarki a madadinsa.

21

1Manasse na da shekaru goma sha biyu sa'ad da ya fara mulki; ya yi mulki shekaru hamsin da biyar a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Hefziba.2Ya yi aikin mugunta a gaban Yahweh, kamar abubuwan banƙyama na al'umman da Yahweh ya kora a gaban mutanen Isra'ila.3Gama ya sake ginin wuraren bisa da Hezekiya mahaifinsa ya rurrushe, sai ya gina bagadi domin Ba'al, ya yi sandan Ashera, kamar yadda Ahab sarkin Isra'ila ya yi, ya kuma russuna wa dukkan tauraron sammai ya yi masu sujada.

4Manasse ya gina bagadai a cikin gidan Yahweh, ko da yake Yahweh ya ummurta, "A Yerusalem ne sunana zai kasance har abada."5Ya gina bagadi domin dukkan taurarin sammai a filayen ciki biyu da ke gidan Yahweh.6Ya sa ɗansa ya wuce ta wuta, ya yi sihiri da dubã da ma'amula da waɗanda ke magana da matattu da waɗanda ke magana da ruhohi. Ya yi mugunta da yawa a gaban Yahweh, yana sa shi yin fushi.
7Sarrafaffiyar siffa ta Ashera da ya yi, ya sata a gidan Yahweh. A game da wannan gidan ne Yahweh ya yi magana da Dauda da Suleimanu ɗansa; ya ce: "A wannan gidan da kuma Yerusalem ne, inda na zaɓa daga dukkan ƙabilun Isra'ila, da zan sa sunana har abada.8Ba zan sa ƙafafun Isra'ila su ƙara fita daga ƙasar da na ba kakanninsu ba, Idan har zasu kula su yi biyayya da dukkan abin da na ummurce su, su kuma bi dukkan dokokin da bawana Musa ya Ummurce su."9Amma mutanen ba su ji ba, Manasse kuma ya jagorance su ga yin aikin mugunta fiye da al'umman da Yahweh ya hallakar a gaban mutanen Isra'ila.
10Sai Yahweh ya yi magana ta wurin bayinsa annabawa, cewa,11"Saboda Manasse sarkin Yahuda ya yi waɗannan abubuwan banƙyama, ya kuma aikata mugunta fiye da dukkan abin da Amoriyawan da suke gabaninsa suka yi, ya kuma sa Yahuda ya yi zunubi da gumakansa,12don haka Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗi haka: Duba, Ina gab da kawo bala'i a Yerusalem da Yahuda wanda duk wanda ya ji abin, dukkan kunuwansa za su ƙaɗu.
13Zan miƙa a saman Yerusalem layin magwajin da zan gwada Samariya, da layin ma'aunin gwada gidan Ahab; Zan share Yerusalem fes-fes, kamar yadda mutum ke wanke kwano, yana share ta da kuma goge ta yana juya ta ko'ina.14Zan jefar da ragowar gãdona in ba da su ga hannun maƙiyansu. Za su zama waɗanda aka yi wa laifi da ganima ga dukkan makiyansu,15saboda sun yi abin mugunta a gabana, suka kuma zuga ni ga fushi, tun daga ranar da kakaninsu suka fito daga Masar, har yau."
16Haka kuma, Manasse ya zub da jinin adalai da yawa, har sai da ya cika Yerusalem daga gefe ɗaya zuwa wani gefen da mutuwa. Banda zunubin da ya sa Yahuda suka yi, sa'ad da suka yi mugunta a gaban Yahweh.17A game da sauran zantuttukan da ya shafi Manasse da dukkan abin da ya yi, da zunuban da ya aikata, ba a rubuta su cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?18Manasse ya yi barci tare da kakaninsa aka bizne shi a lanbun gidansa, a lanbun Uzza. Amon ɗansa ya zama saki a madadinsa.
19Amon na da shekaru ashirin da biyu sa'ad da ya fara mulki; ya yi mulki shekaru biyu a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Meshullemet; ita ɗiyar Haruz na Jotba ne.20Ya yi akin mugunta a gaban Yahweh, kamar yanda Manasse mahaifinsa ya yi.

21Amon ya bi dukkan hanyar da mahaifinsa ya yi tafiya ya kuma bauta wa gumakan da mahaifisa ya bauta wa, ya yi masu ruku'u.22Ya ƙi Yahweh, Allah na ubanninsa, bai kuma yi tafiya a hanyar Yahweh ba.23Barorin Amon suka shirya maƙarƙashiya gãba da shi suka kashe shi a cikin gidansa.
24Amma mutanen ƙasar suka kashe dukkan waɗanda suka yi wa sarki Amon maƙarƙashiya, sai suka maida Yosiya, ɗansa sarki a madadinsa.25Game da sauran zantuttukan da suka shafi Amon da abin da ya yi, ba a rubuce suke a littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?26Mutanen suka bizne shi a kabarinsa cikin lambun Uzza, sai Yosiya ɗansa ya zama sarki a madadinsa.

22

1Yosiya yana da shekaru takwas sa'ad da ya fara mulki; ya yi mulki shekaru talatin da uku a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Yedida (Ita ɗiyar Adayiya na Bozkat ce).2Ya yi abin da ya dace a gaban Yahweh. Ya yi tafiya a hanyar Dauda kakansa, bai kuma kauce mata zuwa dama ko hagu ba.

3Sai ya zamana a shekara ta goma sha takwas ta sarki Yosiya, ya aike Shafan ɗan Azaliya ɗan Mashullam, magatakarda, zuwa gidan Yahweh, cewa,4"Jeka wurin Hilkiya babban firist ka gaya masa ya ƙirga ƙuɗin da aka kawo cikin gidan Yahweh, wanda masu gadin haikali suka tara daga mutane.5A ba da shi ga hannun ma'aikatan da ke lura da gidan Yahweh, su ba ma'aikatan da ke gidan Yahweh domin su yi gyare-gyare a haikali.
6Su bada ƙuɗi ga kafintoci da magina, a kuma sayi katakon timba a buga dutse domin gyaran haikali."7Amma babu bukatar rohoton kashe kuɗin da aka ba su, saboda sun yi aiki da shi cikin aminci.
8Hilkiya babban firist ya cewa Shafan magatakarda, "Na sami littafin dokoki a gidan Yahweh." Sai Hilkiya ya ba da littafin ga Shafan, sai ya karanta shi.9Shafan ya je ya kai littafin gun sarki, ya kuma sanar da shi, cewa, "Barorinka sun kashe kuɗin da aka samu a haikali kuma sun ba da shi ga hannun ma'aikatan da ke shugabancin lura da gidan Yahweh."10Sa'annan Shafan magatakarda ya faɗa wa sarkin, "Hilkiya firist ya ba ni littafi." Sai Shafan ya karanta wa sarki.
11Sai ya zamana sa'ad da sarki ya ji kalmomin dokokin, sai ya yayyaga tufafinsa.12Sarkin ya ummurci Hilkiya firist da Ahikam ɗan Shafan da Akbor ɗan Mikayiya da Shafan magatakarda da Asayiya bawansa cewa,13"Ku je ku ji daga wurin Yahweh domina da mutanen da dukkan Yahuda, saboda kalmomin wannan littafin da aka samo. Gama fushin Yahweh a gare mu na da girma saboda kakanninmu ba su saurari kalmomin wannan littafin don yin biyayya game da dukkan abin da aka rubuta game da mu ba."
14Sa'an nan Hilkiya firist da Ahikam da Akbor da Shafan da Asayiya suka je wurin annabiya Hulda, matar Shallum ɗan Tikvah ɗan Harhas, mai tsaron ɗakin da ake ajiyan sutura (tana zaune a Yerusalem a yankin sabon birnin), sai suka yi magana tare da ita.15Ta ce masu, "Wannan ne abin da Yahweh, Allahn Isra'ila, ya faɗI: 'Gaya wa mutumin da ya aike ki gare ni,16Ga abin da Yahweh ya faɗi: 'Duba, zan auko da bala'i ga wannan wurin tare da mazaunansa, bisa ga dukkan abin da aka rubuta a littafin da sarkin Yahuda ya karanto.
17Saboda kun yashe ni kuka kuma ƙona turare ga waɗansu alloli, don su tsokane ni ga yin fushi da dukkan ayyukan da suka yi - don haka na fito da wutar hasalata gãba da wannan wurin, kuma ba za ta mutu ba."'18Amma ga sarkin Yahuda, Wanda ya aike ku ku nemi nufin Yahweh, ga abin da zaku ce masa: "Yahweh, Allah na Isra'ila ya faɗi haka: 'game da kalmomin da ka ji,19saboda zuciyarka ta yi taushi, ka kuma yi tawali'u a gaban Yahweh, sa'ad da ka ji abin da na faɗa gãba da wannan wurin da mazaunansa, akan yadda zasu zama kango da la'ana, saboda kuma ka yayyaga tufafinka ka yi kuka a gabana, Ni kuma na saurare ka - wannan furcin Yahweh ne.
20Duba, Zan tara ka ga kakanninka, kuma za a tara ka ga kabarinka cikin salama. Idanuwanka baza su ga dukkan masifun da zan auko da su akan wurin nan ba.""" Sai mazajen suka mayar da saƙon ga sarki.

23

1Sa'an nan sarki ya aiko da manzanni waɗanda suka tara masa dukkan dattawan Yahuda da Yerusalem.2Sai sarki ya haura zuwa gidan Yahweh da dukkan mazaunan Yahuda da Yerusalem da ke tare shi, da firistoci da annabawa da dukkan mutane, daga ƙanƙani zuwa babba. Sai ya karanta dukkan kalmomin littafin Alƙawarin da aka samu a gidan Yahweh a kunnuwansu.

3Sarkin ya tsaya a gefen ginshiƙi ya yi alƙawari ga Yahweh cewa zai bi Yahweh ya kiyaye dokokinsa, da ummurnansa da farillansa, da dukkan zuciyarsa da dukkan ransa, ya kuma ka'idantar da kalmomin alƙawarin da aka rubuta a wannan littafin. Saboda haka mutanen suka yarda su tsaya akan alƙawarin.
4Sa'an nan sarki ya ummurce Hilkiya babban firist da firistoci da ke ƙarƙashinsa da masu tsaron ƙofa su fitar da tasoshin da aka yi wa Ba'al da Ashera daga haikalin Yahweh, da dukkan taurarin sama. Ya ƙone su a bayan Yerusalem a filayen Kwarin Kidron, sa'an nan ya kwashe tokarsu zuwa Betel.5Ya kuma kawar da firistocin gumaka waɗanda sarakunan Yahuda suka naɗa don a ƙona turare a wuraren tuddai a biranen Yahuda da kewayen Yerusalem - waɗanda suka ƙona turare ga Ba'al, da rana da wata da duniyoyi da dukkan taurarin sama.
6Ya fitar da sandan Ashera daga haikalin Yahweh, wajen Yerusalem zuwa Kwarin Kidron ya ƙona shi a wurin. Ya buge ta har ga ƙura ya zubar da ƙurar cikin kaburburan talakawa.7Ya rusa ɗakunan karuwai matsafa waɗanda ke a haikalin Yahweh, inda matan ke saƙa tufafin Ashera.
8Yosiya ya fitar da dukkan firistoci daga biranen Yahuda ya ƙazantar da tuddan wuraren da firistoci ke ƙona turare, daga Geba zuwa Biyasheba. Ya rurrushe tuddan wuraren a kofofin da ke mashigin ƙofofin Yoshuwa (gwamnan birnin), a gefen hagu na ƙofar birnin.9Ko da shike ba a bar firistocin waɗannan tuddan wuraren su yi aiki a bagadin Yahweh a Yerusalem ba, sun ci gurasa mara yisti cikin 'yan'uwansu maza.
10Yosiya ya ƙazantar da Tofet, wanda ke cikin Kwarin Ben Hinom, saboda kar kowa ya sa ɗansa ko ɗiyarsa bi ta wuta a matsayin hadaya ga Molek.11Ya ɗauki dawakan da sarakunan Yahuda suka miƙa wa rana, Suna nan a wurin a ƙofar haikalin Yahweh kusa da ɗakin Natan-Melek shugaban shirayin da ke cikin farfajiya. Yosiya ya ƙona karusan rana.
12Sarki Yosiya ya rurrusa bagadan da ke bisa rufin benen Ahaz, waɗanda sarakunan Yahuda suka yi, da bagaden da Manasse ya yi a farfajiya biyu ta haikalin Yahweh. Yosiya ya rugurguza su ya jefar da su a Kwarin Kidron,13Sarkin ya rurrushe tuddan wuraren tsafi da ke gabashin Yerusalem kudu da dutsen hallaka wanda Suleman sarkin Isra'ila ya gina wa Ashtoret da ƙazantacciyar gunkiyar Sidoniyawa; don Kemosh, ƙazantaccen gunkin Mowab; kuma na Molek, da ƙazantaccen gunkin Amonawa.14Ya rurrushe ginshiƙai na dutse rugu-rugu ya kuma sassare sandunan Ashera sa'an nan ya rufe wuraren da ƙasussuwan mutane.
15Yosiya ya rurrushe bagadan da ke a Betel kakaf da wuri mai tudu da Yerobowam ɗan Nebat (wanda ya sa Isra'ila ta yi zunubi) ya gina. Ya kuma ƙona bagadin da wuri mai tudu, ya buge shi har ga ƙura, ya ƙona sandan Ashera.16Yayin da Yosiya ya dubi dukkan kewayen, sai ya gano kaburburan da ke kan tuddu, ya aika maza su kwaso ƙasusuwan daga kaburburan; sai ya ƙona su a bagadin, wanda ya ƙazantar da shi. Wannan bisa ga maganar Yahweh ce wadda mutumin Allah ya faɗa, mutumin da ya faɗi waɗannan abubuwan tuntuni.
17Sa'an nan ya ce, "Wanne kabari ne waccan da na gani?" Mutanen birnin suka gaya masa, "Waccan ne kabarin mutumin Allah da ya zo daga Yahuda, ya yi magana akan abubuwan nan da kayi gãba da bagaden Betel."18Sai Yosiya ya ce, ku bar shi kawai. Kada kowa ya motsa ƙasusuwansa, sai suka bar ƙasusuwansa tare da na annabin da yazo daga Samariya.
19Sa'an nan Yosiya ya cire dukkan gidajen wuraren kan tudu da ke a Samariya, wanda sarakunan Isra'ila su ka yi, da ya sa Allah ya yi fushi. Ya yi masu dai-dai da abin da aka yi a Betel.20Ya yayyanka dukkan firistocin tuddan wuraren akan bagadan sai ya ƙona ƙasusuwan mutane akan su. Sa'an nan ya koma Yerusalem.
21Sa'an nan Sarkin ya ummurci dukkan mutane cewa, "Ku kiyaye bikin Ƙetarewa ga Yahweh Allahnku, kamar yadda aka rubuta a Littafin Alƙawari."22Irin hidimar bukin nan ba a taɓa yinsa ba tun daga kwanakin da alƙalai suka yi mulkin Isra'ila, ko dukkan kwanakin sarakunan Isra'ila ko Yahuda.23Amma a shakara ta goma sha takwas ta sarki Yosiya an yi bikin wannan Ƙetarewa na Yahweh a Yerusalem.
24Yosiya kuwa ya kori dukkan mabiya waɗanda ke magana da matattu ko ruhohi. Ya kuma kori kawunan gidaje da gumaka da dukkan abubuwan banƙyama da ake gani a Yahuda da Yerusalem, saboda a ka'idantar da kalmomin dokokin da aka rubuta a littafin da Hilkiya firist ya samo a gidan Yahweh.25Kafin Yosiya, ba a yi wani sarki kamarsa, wanda ya juyo ga Yahweh da dukkan zuciyarsa da dukkan ransa da dukkan ƙarfinsa ba, wanda kuma ya bi dukkan dokokin Musa. Ba a kuwa yi wani sarki kamar Yosiya ba a bayansa.
26Duk da haka, Yahweh bai juya baya daga zafin fushinsa ba, wanda ya yi gãba da Yahuda saboda dukkan abubuwan da Manasse ya yi na sashi shi ya yi fushi.27Saboda haka Yaweh ya ce, "Zan kuwa kawar da Yahuda daga fuskata, kamar yadda na tsige Isra'ila, zan kuma jefar da birnin da na zaɓa, Yerusalem, da kuma gidan da nace, 'Sunana zai kasance a wurin.'"
28Game da sauran zantuttukan da suka shafi Yosiya da dukkan abubuwan da ya yi, ba a rubuce suke a littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?29A kwanakinsa, Fir'auna Neko, sarkin Masar, ya je yaƙi da sarkin Asiriya a kogin Yuferatis. Sarki Yosiya ya je ya sami Neko a yaƙi, sai Neko ya kashe shi a Megiddo.30Sai baran Yosiya ya ɗauke shi a karusa daga Megiddo, ya taho da shi Yerusalem ya bizne shi a nasa kabarin. Sa'an nan Mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoahaz ɗan Yosiya, suka shafa masa mai, suka mai da shi sarki a madadin mahaifinsa.
31Yehoahaz yana da shekaru ashirin da uku lokacinin da ya fara mulki, ya yi mulkin shekaru uku a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Hamutal; ita ɗiyar Irmiya na Libna ne,32Yehoahaz ya yi aikin mugunta a gaban Yahweh, kamar dukkan yadda kakaninsa suka yi.33Fir'auna Neko ya ɗaure shi a Ribla, a ƙasar Hamat, saboda kar ya yi mulkin Yerusalem. Sa'an nan Neko ya yi wa Isra'ila tarar talanti ɗari na azurfa da talanti ɗaya na zinariya.
34Fir'auna Neko ya sa Eliyakim ɗan sarki Yosiya ya zama sarki a madadin mahaifinsa, sai ya canza masa suna zuwa Yehoiakim. Amma ya ɗauki Yehoahaz zuwa Masar har Yehoahaz ya mutu a can.35Yehoiakim ya biya azurfa da zinariya ga Fir'auna. Don ya iya yin yadda Fir'auna yake so, Yehoiakim ya sa ƙasar biyan haraji kuma ya tilasta kowanne mutum daga cikin mutanen ƙasar ya biya da azurfa da zinariya bisa ga yanayin tsarinsu.
36Yehoiakim yana da shekara ashirin da biyar sa'ad da ya fara mulki, kuma ya yi mulki na shekara goma sha ɗaya a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Zebida ɗiyar Fediya na Ruma.37Yehoiakim ya yi akin mugunta a fuskar Yahweh, kamar yadda kakaninsa suka yi.

24

1A kwanakin Yehoiakim, Nebukadnezza sarkin Babila ya kai wa Yahuda hari; Yehoiakim ya zama bawansa na shekaru uku. Sa'an nan Yehoiakim ya juya ya tayar wa Nebukadnezza.2Yahweh ya aiko da Yehoiakim, maharan Kaldiyawa da Aramiyawa da Mowabawa da Amoniyawa, ya aike su gãba da Yahuda su hallakar da shi. Wannan ya zo dai-dai ne da maganar Yahweh da aka faɗa ta barorinsa annabawa.

3Hakika ta bakin Yahweh ne wannan ya zo ga Yahuda, ya cire su daga fuskarsa, saboda laifofin Manasse, dukkan abin da ya yi,4kuma saboda zub da jinin bayin Allah da ya yi, gama ya cika Yerusalem da jinin adalai, Yahweh bai yi niyar gafarta hakan ba.
5Game da sauran zantuttukan da suka shafi Yehoiakim, da dukkan abubuwan da ya yi, ba a rubuce suke a littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?6Yehoiakim ya yi barci tare da kakaninsa, sai Yehoiacin ɗansa ya zama sarki a madadinsa.
7Sarkin Masar bai sake fita ƙasarsa ya kai wa wani hari ba, saboda sarkin Babila ya ƙwato dukkan ƙasashen da ke ƙarƙashin sarkin Masar, daga rafin Masar har zuwa kogin Yuferatis.
8Yehoiacin ya na da shekaru goma sha takwas yayin da ya fara mulki a Yerusalem; ya yi mulkin wata uku a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Nehushta; ɗiyar Elnatan na Yerusalem.9Ya yi aikin mugunta a gaban Yahweh; ya yi dukkan abubuwan da mahaifinsa ya yi.
10A lokacin nan ne sojojin Nebukadnezza sarkin Babila suka kai wa Yerusalem hari, suka kewaye birnin da yaƙi,11Nebukadnezza ya zo birnin yayin da sojojinsa ke kewaye da shi,12sai Yehoiacin sarkin Yahuda ya je ya tari sarkin Babila, shi da mahaifiyarsa da barorinsa da 'ya'yansa da hafsoshinsa. Sarkin Babila ya kama shi a shekara ta goma sha takwas ta mulkinsa.
13Nebukadnezza ya ɗauki dukkan abubuwa masu daraja na gidan Yahweh, da waɗanda ke fãdar sarki. Ya farfashe dukkan tasoshin zinariyar da sarki Suleman ya yi a haikalin Yahweh, kamar yadda Yahweh ya ce zai faru.14Ya ɗauki 'yan zuwa zaman talala daga dukkan Yerusalem, da dukkan shugabanin da dukkan mayaƙa da kamammu dubu goma da dukkan 'yan fasaha da maƙera. Babu wanda aka bari sai fakirai na ƙasar.
15Nebukadnezza ya ɗauki Yehoiacin zuwa zaman talala a Babila. da kuma mahaifiyar sarki da matansa da hafsoshi da manyan mazajen ƙasar. Ya ɗauke su zuwa zaman talala daga Yerusalem zuwa Babila.16Dukkan mayaƙa dubu bakwai da masu sana'a da maƙera dubu ɗaya dukkansu ƙarfafa ne da suka isa zuwa yaƙi - sarkin Babila ya kawo waɗannan mutanen ga zaman talala a Babila.17Sarkin Babila ya sa Mataniya, ɗan'uwan mahaifin Yehoiacin, ya zama sarki a madadinsa ya kuma canza masa suna zuwa Zedekiya.
18Zedekiya yana da shekaru ashirin da ɗaya yayin da ya fara mulki; ya yi mulki shekaru goma sha ɗaya a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Hamutal; ita ɗiyar Irmiya na Libna ne.19Ya yi aikin mugunta a gaban Yahweh; ya yi dukkan abin da Yehoiakim ya yi.20Ta dalilin fushin Yahweh ne, dukkan waɗannan abubuwan suka faru a Yerusalem da Yahuda, har sai ya kore su daga gare shi. Sa'an nan Zedekiya ya yi tayar da gãba da sarkin Babila.

25

1Sai ya zamana a shekara na tara a mulkin Zedekiya, a wata na goma, a rana ta goma ga watan, Nebukadnezza sarkin Babila ya zo da dukkan sojojinsa gãba da Yerusalem. Ya yi sansani kusa da ita, ya gina kagarai kewaye da ita.2Saboda haka aka kewaye birnin da yaƙi har shekara goma sha ɗaya na mulkin Zedekiya.3A rana ta tara na watan huɗu na shekarar, yunwa ta yi tsanani a birnin har babu abinci domin mutanen ƙasar.

4Sa'an nan aka shigo birnin, sai dukkan masu yaƙin suka gudu ta ƙofar dake tsakanin katangu biyu, ta lambun sarki, ko da shike Kaldiyawa suna kewaye da birnin. Sarki ya yi ta wajen Araba.5Amma sojojin Kaldiyawa suka yi fakon sarki Zedekiya har suka mamaye shi a filayen kwarin Kogin Yodan kusa da Yeriko. Dukkan sojinsa kuwa suka warwatsu daga gare shi.
6Suka kamo sarkin suka kai shi gun sarkin Babila a Ribla, inda aka yanke masa hukunci.7Game da 'ya'yan Zedekiya maza kuwa, an yayyanka su a gabansa. Sa'annan ya ƙwaƙule masa idanunsa, ya ɗaure shi da sarƙa ta tagulla, ya kai shi Babila.
8Yanzu kuwa a wata na biyar, a rana ta bakwai ga watan, wanda ke a shekara ta goma sha tara ta mulkin Nebukadnezza sarkin Babila, Nebuzaradan, baran sarkin Babila da kuma shugaban masu gadin sarki, ya zo Yerusalem.9Ya ƙona gidan Yahweh da fãdar sarki da dukkan gidajen Yerusalem; ya kuma ƙone dukkan manyan gine-ginen birnin.10Game da garun kewaye da Yerusalem kuwa, dukkan sojojin Babilan da ke ƙarƙashin shugaban sun rurrushe su.
11Game da sauran mutanen da aka bari a birnin da waɗanda suka tafi wurin sarkin Babila, da sauran ragowar mutanen - Nebuzaradan, shugaban masu gadin sarki, ya ɗauke su zuwa zaman talala.12Amma shugaban masu gadin sarki ya bar waɗansu matalautan ƙasar su ci gaba da aikin lambuna da filaye.
13Game da ginshiƙan tagulla da ke gidan Yahweh, da dakalansu da takwanniyar ruwa da ke cikin gidan Yahweh, Kaldiyawa sun ragargaza su su ka kuma ɗauke tagullan su ka kai su Babila.14Kaldiyawan kuma su ka kwashe tukwane da manyan cokula da hantsuka da cokula da dukkan tasoshin tagulla waɗanda firistoci ke aiki da su a haikali - Kaldiyawa sun tafi da su dukka.15Tukwanen da ake amfani da su domin cire tokar bagaden darurruka da aka yi da zinariya da azurfa - shugaban masu gadin sarkin ya kwashe su dukka ya tafi da su.
16Ginshiƙan biyu kuwa da takwanniyar ruwa da dakalan da Suleman ya yi domin gidan Yahweh suna ƙunshe da tagulla da yawa da ba a iya aunawa.17Tsawon ginshiƙi na farkon kamu goma sha takwas ne. dajiyar tagulla akan ginshiƙin kamu uku ne, wadda aka kewaye da raga da rumman, kuma dukka da tagulla aka yi su. Ɗaya ginshiƙin da ragarsa na dai-dai da ta farkon.
18Shugaban masu gadin sarkin ya ɗauki Serayiya babban firist da Zefaniya da firist na biyun da mutun uku masu tsaron ƙofa.19Daga birnin kuwa ya ɗauki waɗansu manyan sojoji da mashawartan sarki guda biyar waɗanda ba a tafi da su ba duk ya kamo ya tsare su don kada su gudu. Ya kuma kamo babban sojan da ke shugabancin ɗaukan sojoji aiki, tare da mutum sitin kuma da ke cikin birnin.
20Sa'an nan Nebuzaradan, shugaban masu gadin sarki, ya ɗauko su ya kai wa sarkin Babilan a Ribla.21Sarkin Babila ya kashe su a Ribla a ƙasar Hamat. Ta haka Yahuda ya bar ƙasarsa zuwa zaman bauta.
22Game da mutanen da suka rage a ƙasar Yahuda, waɗanda Nebukadnezza sarkin Babilan ya bari, ya sa Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, shugabancin su,23Yanzu kuwa da dukkan shugabanin sojojin, su da mazajensu, suka ji sarkin Babila ya maida Gedaliya gwamna, sai suka je wurin Gedaliya a Mizpa. Waɗannan mazajen su ne Isma'il ɗan Netaniya da Yohanan ɗan Kariya da Serayiya ɗan Tanhumet Banetofate da Ya'azaniya ɗan Ma'akatite - su da mazajensu.24Gedaliya ya yi amana da su da mazajensu, ya ce da su, "Kada ku ji tsoron shugabanin Kaldiyawa. Ku zauna a ƙasar ku yi wa sarkin Babilan hidima, kuma kome zai yi maku kyau."
25Amma ya zamana dai a watan bakwai Isma'il ɗan Netaniya ɗan Elishama, daga iyali mai martaba, ya zo ya da mutum goma ya kai wa Gedaliya hari. Gedaliya ya mutu, tare da mutum goma na Yahuda da Babilonawan da ke tare da shi a Mizfa.26Sa'an nan dukkan mutanen, daga mafi ƙanƙanta zuwa masu muhiminci, da dukkan shugabani sojojin, suka tashi suka tafi Masar, saboda suna tsoron Babilonawan.
27Ya zamana daga baya a shekara ta talatin da bakwai na zaman talalar Yahoiacin sarkin Yahuda, a wata na goma sha biyu, sai Awel Marduk sarkin Babilan ya saki Yahoiacin sarkin Yahuda daga kurkuku. Wannan ya faru ne a shekarar da Awel- Marduk ya fara mulki.
28Ya yi maganar kirki da shi ya kuma ba shi wurin zaman da ya fi na waɗansu sarakunan da ke tare da shi a Babila.29Awel-Marduk ya cire wa Yahoiacin tufafin kurkuku, har Yahoiacin ya ci gaba da liyafa a teburin sarki dukkan rayuwarsa.30Ana kuwa biyansa albashin abinci dukkan kwanakin rayuwarsa.

Littafin tarihi na ɗaya

1

1Adamu, Set, Enosh,2Kenan, Mahalalel, Yared,3Enok, Metusela, Lamek.4'Ya'yan Nuhu su ne Shem, Ham da Yafet.

5'Ya 'yan Yafet su ne Gomer, Magog, Madai, Yaban, Tubal, Meshek, Tiras.6'Ya'yan Gomer su ne Ashkenaz, Rifat da Togarma.7'Ya 'yan Yaban su ne Elisha, Tarshish, Kitiyawa, da Rodanawa.
8'Ya'yan Ham su ne Kush, Masar, Fut da Kan'ana.9'Ya'yan Kush su ne Seba, Habila, Sabta, Ra'ama da Sabteka.10'Ya'yan Ra'ama su ne Sheba da Dedan. Kush ya zama mahaifin Nimrod, wanda shi ne ya fara zama jarumi a duniya.
11Masar ya zama mahaifin mutanen Ludawa, da Anamawa, da Lehabawa, da Naftuhawa, da12Fatrusawa, da Kasluhawa (daga wannan tushen Filistiyawa suka fito), da Kaftorawa.
13Kan'ana ya zama mahaifin Sidon, ɗan farinsa, da kuma Hitiyawa.14Shi ne ya zama kakan Yebusawa, Amoriyawa, Girgashawa,15Hibiyawa Arkiyawa, Siniyawa da16Arbiyawa, Zemarawa, da Hamatawa.
17'Ya'yan Shem su ne Elam, Ashur, Arfazad, Lud, Aram, Uz, Hul, Geter, da Meshek,18Arfazad shi ne ya zama mahaifin Shela, Shela kuma ya zama mahaifin Eber.19Eber na da 'ya'ya biyu. Sunan ɗayan Feleg, gama a zamaninsa ne duniya ta rabu. Sunan ɗan'uwansa Yoktan.
20Yoktan ya zama mahaifin Almodad, Shelef, Hazamavet, Yera,21Hadoram, Uzal, Dikla,22Obal, Abimayel, Sheba,23Ofir, Habila, da Yobab, duk waɗannan daga zuriyar Yoktan ne.
24Shem, Arfazad, Shelah,25Eber, Feleg, Rewu,26Serug, Nahor, Tera,27Abram shi ne Ibrahim.
28'Ya'yan Ibrahim su ne Ishaku da Isma'il.29Waɗannan su ne 'ya'yansu:‌ Ɗan farin Isma'il Nebayot ne, sa'an nan Kedar, Adbeel, Mibsam,30Mishma, Duma, Massa, Hadad, Tema,31Yetur, Nafish, da Kedema. Waɗannan su ne 'ya'yan Isma'il.
32'Ya'yan Ketura, ƙwarƙwarar Ibrahim su ne Zimran, Yokshan, Medan, Midiyan, Ishbak da Shuwa. 'Ya'yan Yokshan su ne Sheba da Dedan.33'Ya'yan, Midiyan su ne Efa, Efer, Hanok, Abida, da Elda'ah. Dukkan waɗannan zuriyar Ketura ne.
34Ibrahim ya zama mahaifin Ishaku. 'Ya'yan Ishaku su ne Isuwa da Isra'ila.35'Ya'yan Isuwa su ne Elifaz, Ruwel, Yewush, Yalam, da Kora.36'Ya'yan Elifaz su ne Teman, Omar, Zefo, Gatam, Kenaz, Timna da Amalek.37'Ya'yan Ruwel su ne Nahat, Zera, Shamma, da Mizza.
38'Ya'yan Seyir su ne Lotan, Shobal, Zibiyon, Ana, Dishon, Ezer, da Dishan.39'Ya'yan Lotan su ne Hori da Homam, Timna 'yar'uwar Lotan ce.40'Ya'yan Shobal su ne Alban, Manahat, Ebal, Shefo, da Onam. 'Ya'yan Zibiyon su ne Aiya da Ana.
41‌Ɗan Ana shi ne Dishon. 'Ya'yan Dishon su ne Hemran, Eshban, Itran, da Keran.42'Ya'yan Ezer su ne Bilhan Za'aban, Ya'akan da Akan. 'Ya'yan Dishan su ne Uz da Aran.
43Waɗannan su ne sarakunan da suka yi mulki a ƙasar Idom kafin wani sarki ya yi mulki bisa Isra'ilawa. Bela ɗan Beyor, sunan birninsa Dinhaba ne.44Da Bela ya mutu, Yobab ɗan Zera na Bozra ya yi mulki a gurbinsa.45Da Yobab ya mutu, Husham na ƙasar Temanawa ya yi mulki a gurbinsa.
46Da Husham ya mutu, Hadad ɗan Bedad, wanda ya ci Midiyan a ƙasar Mowab, ya yi sarauta a gurbinsa. Sunan birninsa Avit.47Da Hadad ya mutu, Samla na Masreka ya yi sarauta a gurbinsa.48Da Samla ya mutu, Shawul na Rehobot wadda a kan kogin ya yi sarauta a gurbinsa.
49Da Shawul ya mutu, Ba'al-Hanan ɗan Akbor ya yi mulki a gurbinsa.50Ba'al-Hanan ɗan Akbor ya mutu, Hadar ya yi mulki a gurbinsa. Sunan birninsa Fawu. Sunan matarsa Mehetabel ce ɗiyar Matred ɗiyar Me Zahab.
51Hadad ya mutu, shugaban iyalin Idom su ne Timna, Alba, Yetet,52Ohalibama, Elah, Finon,53Kenaz Teman, Mibza,54Magdiyel, da Iram. Waɗannan su ne shugabannin a Idom.

2

1Waɗanan su ne 'ya'yan Isra'ila maza: Ruben, Simiyon, Lebi, Yahuda, Issaka, Zebulun,2Dan, Yosef, Benyamin, Naftali, Gad da Asha.

3'Ya'yan Yahuda su ne Er, Onan, da Shela, waɗanda ɗiyar Shuwa ta haifa masa Bakan'aniye. Er ɗan farin Yahuda, mugu ne a gaban Yahweh, sai Yahweh ya kashe shi.4Tama, surukarsa, ta haifa masa Ferez da Zara. Yahuda yana da 'ya'ya biyar maza.
5'Ya'yan Ferez su ne Hezron da Hamul.6'Ya'yan Zera su ne Zimri, Etan, Heman, Kalkol, da Darda su biyar cur‌.7‌Ɗ‌an Karmi shi ne Akar, wanda ya kawo matsala ga Isra'ila lokacin da ya saci abubuwan da aka keɓe domin Yahweh.‌8Ɗan Etan shi ne Azariya.
9'Ya'yan Hezron su ne Yeramil, Ram, Kaleb.10Ram ya zama mahaifin Aminadab, Aminadab ya zama mahaifin Nashon, shugaba ne cikin zuriyar Yahuda.11Nashon ya zama mahaifin Salmon, Salmon ya zama mahaifi Bo'aza.12Bo'aza ya zama mahaifin Obed, Obed ya zama mahaifin Yesse.
13Yesse ya zama mahaifin ɗan farinsa Eliab, Abinadab na biyu, Shimeya na uku,14Netanel na huɗu, Raddai na biyar,15Ozem na shida, sai Dauda na bakwai.
16'Yan'uwansu mata su ne Zeruyiya da Abigel. 'Ya'yan Zeruyiya su ne Abishai, Yoab da Asahel, su uku.17Abigel ta haifi Amasa, mahaifinsa Yeter ne Ba'isma'ile.
18Kaleb ɗan Hezron ya haifi 'ya'ya daga matarsa Azuba, da kuma Yeriyot. 'Ya'yansa maza su ne Yesher, Shobab, da Ardon.19Azuba ta mutu, sai Kaleb ya auro Efrat, wacce ta haifa masa Hur.20Hur ya zama mahaifin Uri, Uri kuma ya zama mahaifin Bezalel.
21Daga baya Hezron (da ya cika shekaru sittin) ya auri ɗiyar Makir, mahaifin Giliyad. Ita ta haifa masa Segub.22Segub ya zama mahaifin Yayir, wanda ya mallaki birane ashirin da uku a ƙasar Giliyad.
23Geshur da Aram suka ci garin Yayir da Kenat, har da garuruwa sittin na kewaye. Duk waɗannan mazauna zuriyar Makir ne, mahaifin Giliyad.24Bayan mutuwar Hezron, Kaleb ya kwana da Efrata, matar Hezron mahaifinsa. Ta haifa masa Ashhur, mahaifin Tekowa.
25'Ya'yan Yeramil, ɗan farin Hezron, su ne Ram ɗan fari, Buna, Oren, Ozem, da Ahija.26Yeramil ya na da wa ta mata, wadda ta ke da suna Atara. Ita ce uwar Onam.27'Ya'yan Ram, ɗan farin Yeramel, su ne Ma'az, Yamin, da Eker.28'Ya'yan Onam su ne Shammai da Yada. 'Ya'yan Shammai su ne Nadab da Abishur.
29Sunan matar Abishur Abihel ne, ta kuma haifa masa Ahban da Molid.30'Ya'yan Nadab su ne Seled da Affayim, amma Seled ya mutu ba shi da 'ya'ya,31'Ɗan Affayim kuwa Ishi ne.‌ Ɗan Ishi shi ne Sheshan.‌ Ɗan Sheshan shi ne Ahlai.32'Ya'yan Yada, ɗan'uwan Shammai, su ne Yeter da Yonatan. Yeter ya mutu ba shi da 'ya'ya.33'Ya'yan Yonatan su ne Felet da Zaza. Waɗannan su ne zuriyar Yeramil.
34Sheshan ba shi da 'ya'ya maza, sai dai mata. Sheshan ya na da bawa, Bamasare, mai suna Yarha.35Sai Sheshan ya ba baransa Yarha ɗiyarsa ta zama matarsa. Ita ce ta haifa masa Attai.
36Attai ya zama mahaifin Natan, Natan ya zama mahaifin Zabad.37Zabad ya zama mahaifin Eflal, kuma Eflal ya zama mahaifin Obed.38Obed ya zama mahaifin Yehu, kuma Yehu ya zama mahaifin Azariya.
39Azariya ya zama mahaifin Helez, Helez ya zama mahaifin Eleyasa.40Eleyasa ya zama mahaifin Sismai, Sismai kuma ya zama mahaifin Shallum.41Shallum ya zama mahaifin Yekamiya, Yekamiya kuma ya zama mahaifin Elishama.
42'Ya'yan Kaleb, ɗan'uwan Yeramil, su ne Mesha ɗan farinsa, wanda shi ne mahaifin Zif.‌ Ɗansa na biyu, Maresha, shi ne mahaifin Hebron.43'Ya'yan Hebron su ne Kora, Taffuwa, Rekem, da Shema.44Shema ya zama mahaifin Raham, mahaifin Yorkiyam. Rekem ya zama mahaifin Shammai.
45‌Ɗan Shammai kuwa shi ne Mawon, Mawon shi ne mahaifin Bet Zur.46Efah, ƙwarƙwarar Kaleb, ta haifi Haran, Moza, da Gazez. Haran ya zama mahaifin Gazez.47'Ya'yan Yahdai su ne Regem, Yotam, Geshan, Felet, Efah da Sha'af.
48Ma'aka, ƙwarƙwarar Kaleb, ta haifi Sheber da Tirhanah.49Ita ce kuma mahaifiyar Sha'af mahaifin Madmanna, Sheva mahaifin Makbena da mahaifin Gibeya.‌ Ɗiyar Kaleb ita ce Aksah. Waɗannan su ne zuriyar Kaleb.
50Wàɗannan su ne 'ya'yan Hur, ɗan farinsa daga Efrata: Shobal mahaifin Kiriyat Yerim,51Salma mahaifin Betlehem da kuma Haref mahaifin Bet Gader.
52Shobal mahaifin Kiriyat Yerayim yana da zuriya: Harowe, rabin jama'ar Manahatawa,53da kuma iyalin Kiriyat Yerayim: na Itirawa da na Futiyawa, da na Shumatawa da Mishrayawa. Daga waɗannan ne Zoratawa da Eshtawolawa suka fito.
54Waɗannan su ne dangogin Salma: Betlehem, Netofatawa, Atrot Bet Yowab, da rabin Manahatawa - Zoritawa,55dangogin marubuta waɗanda suka zauna a Yabez: Tiratawa, Shimiatawa, da Sukatawa. Waɗannan su ne Kenitawa zuriyar da suka fito daga Hammat, kakan Rekabawa.

3

1Waɗannan su ne 'ya'yan Dauda da aka haifa masa a Hebron: ɗan fari shi ne Amnon, ta wurin Ahinowam daga Yezriyel; na biyun shi ne Daniyel, ta wurin Abigel daga Karmel;2na ukun shi ne Absalom, wanda uwarsa ita ce Ma'aka, ɗiyar Talmai sarkin Geshur. Na huɗun shi ne Adonijah ɗan Haggit;3na biyar shi ne Shefatiya ta wurin Abital; na shida shi ne Itreyam ta wurin Egla matarsa.

4Waɗannan shida aka haifa wa Dauda a Hebron, inda ya yi sarauta shekaru bakwai da wata shida. Sa'an nan ya yi sarauta a Yerusalem shekaru talatin da uku.5Waɗannan 'ya'ya maza huɗu ta wurin Batsheba ɗiyar Ammiyel aka haifa masa su a Yerusalem: Shamuwa, Shobab, Natan, da Suleman.
6Wasu 'ya'ya maza na Dauda su ne: Ibhar, Elishuwa, Elifelet,7Nogah, Nefeg, Yafiya,8Elishama, Eliyada da Elifelet.9Waɗannan su ne 'ya'yan Dauda maza, banda 'ya'yan da ƙwaraƙwarai suka haifa masa. Tamar 'yar'uwarsu ce.
10‌Ɗan Suleman shi ne Rehobowam. Ɗ‌an Rehobowam shi ne Abiya.‌ Ɗan Abiya shi ne Asa. Ɗan Asa shi ne Yehoshafat.11Ɗan Yehoshafat shi ne Yehoram.‌ Ɗan Yehoram shi ne Ahaziya.‌ Ɗan Ahaziya shi ne Yo'ash.‌12Ɗan Yo'ash shi ne Amaziya, ‌Ɗan Amaziya shi ne Azariya. ‌Ɗan Azariya shi ne Yotam.
13‌Ɗan Yotam shi ne Ahaz.‌ Ɗan Ahaz shi ne Hezekiya. ‌Ɗan Hezekiya shi ne Manasse. ‌Ɗ‌an14Manasse shi ne Amon. ‌Ɗan Amon shi ne Yosiya.
15Ga 'ya'yan Yosiya na farkon shi ne Yohanan, ɗansa na biyu Yaho'iakim, ɗansa na uku Zedekiya, ɗansa na huɗu Shallum.16'Ya'yan Yeho'akim su ne Yeho'iacin da Zedekiya.
17'Ya'yan Yaho'iacin, ɗan bautar talala, su ne Sheltiyal,18Malkiram, Fedayiya, Shenazza, Yekamiya, Hoshama da Nedabiya.
19'Ya'yan Fedayiya su ne Zerubabel da Shimei. ‌'Ya'yan Zerubabel su ne Meshullam da Hananiya; Shelomit 'yar'uwarsu ce.20Wasu 'ya'yansa maza biyar kuwa su ne Hashuba, Ohel, Berekiya, Hasadiya, Yushab-Hesed.21'Ya'yan Hananiya su ne Felatiya da Yeshayiya. ‌‌Ɗansa shi ne Refayiya, waɗansu sauran zuriyoyin su ne Arnan, Obadiya, da Shekaniya
22‌Ɗan Shekaniya shi ne Shemayiya. 'Ya'yan Shemayiya su ne Hattush, Igal, Bariya, Niyariya, da Shafat.23'Ya'yan Niyariya guda uku su ne Eliyonai, Hizkiya, da Azrikam.24'Ya'yan Eliyonai su bakwai ne su ne Hodabiya, Eliyashib, Felayiya, Akkub, Yohanan, Delayiya da Anani.

4

1'Zuriyar Yahuda su ne Ferez, Hezron, Karmi, Hur da Shobal.2Shobal shi ne mahaifin Reyayiya. Reyayiya shi ne mahaifin Yahat. Yahat shi ne mahaifin Ahumai da Lahad. Waɗannan su ne dangogin Zoratawa.

3Waɗannan su ne kakannin dangogin da ke cikin birnin Itam: Yezriyel, Ishma, da Idbash. Sunan 'yar'uwarsu Hazzelelfoni.4Feniyel shi ne kakan dangoginn da ke cikn birnin Gedor. Ezer shi ne na asalin dangogin da ke cikin Hushah. Waɗannan su ne zuriyar Hur, ɗan farin Efrata kuma shi ne asalin Betlehem.
5Ashur mahaifin Tekowa ya na da mata biyu, Helah da Na'arah.6Na'arah ta haifa masa Ahuzzam, Hefa, Temeni, Hahashtari. Waɗannan su ne 'ya'yan Na'arah.7'Ya'yan Helah su ne Zeret, Zohar, Itnan,8da Koz wanda ya zama mahaifin Anub da Hazzobeba, da dangogin zuriyar da suka fito daga Ahahel ɗan Harum.
9Yabez ya sami girmamawa fiye da 'yan'wansa. Mahaifiyarsa ta kira shi Yabez. Ta ce, "Domin na haife shi cikin azaba."10Yabez ya kira bisa sunan Yahweh na Isra'ila ya ce, "Idan da za ka albarkace ni da gaske, ka faɗaɗa mani iyakata, hannunka ya kasance tare da ni. Idan ka yi haka ka kare ni daga cuta, domin in 'yantu daga azaba!" Sai Yahweh ya amsa addu'arsa.
11Kaleb ɗan'uwan Shuhah shi ne mahaifin Mehir, wanda shi ne mahaifin Eshton.12Eshton shi ne mahaifin Bet Rafa, Faseya, da Tehinna, wanda shi ne mahaifin Ir Nahash. Waɗannan su ne mutanen da suka zauna a Reka.
13'Ya'yan Kenaz su ne Otniyel da Serayiya. 'Ya'yan Otniyel su ne Hatat da Meyonotai.14Meyonotai ya zama mahaifin Ofra, Serayiya ya zama mahaifin Yowab wanda ya kafa Ge-Harashim, mutanen masassaƙa ne.15'Ya'yan Kaleb 'ɗan Yefune su ne Iru, Elah da Na'am.‌ Ɗ‌an Elah shi ne Kenaz.16'Ya'yan Yehallelel su ne Zif, Zifa, Tiriya da Asarel.
17'Ya'yan Ezrah su ne Yeter, Mered, Efer, da Yalon. Matar Mered Bamasariye ta haifi Miriyam, Shammai, da Ishba, wanda shi ne mahaifin Estemowa.18Waɗannan su ne 'ya'yan Bitiya, ɗiyar Fir'auna, wadda Mered ya aura. Matar Mered Bayahude ta haifi Yarid, wanda shi ne mahaifin Gedor; Haba, wanda ya zama mahaifin Soko; da Yekutiyel, wanda shi ne ya zama mahaifin Zanowa.
19Matar Hodiya 'yar'uwar Naham, tana da 'ya'ya maza biyu, ɗaya daga cikinsu ya zama mahaifin Keila Bagarme.‌ Ɗayan kuwa shi ne Eshtamowa Bamaakate.20'Ya'yan Shimon su ne Amon, Rinna, Ben-Hanan da Tilon. 'Ya'yan Ishi su ne Zohet da Ben-Zohet.
21Zuriyar Shela ɗan Yahuda su ne Er mahaifin Leka, La'ada mahaifin Maresha da dangogin da ke sana'ar linin a Bet Ashbiya,22Yokim, mutanen Kozeba, da Yo'ash da Saraf, da ya yi mulki a Mowab da Yashubi Lehem. (Wannan labari daga daɗaɗen rubutu ne.)23Waɗannan su ne maginan tukwane da suka zauna a Netayim da Gedera, suka yi wa sarki aiki.
24Zuriyar Simiyon su ne Nemuyel, Yamin, Yarib, Zera da Shawul.25Shallum ɗan Shawul ne, Mibsam ɗan Shallum ne, kuma Mishma ɗan Mibsam ne.26Zuriyar Mishma su ne ɗansa Hamuyel, Zakur jikansa da Shimei tattaɓa kunnensa.
27Shimei yana da 'ya'ya goma sha shida da 'ya'ya mata shida. Ɗan'uwansa bai haifi 'ya'ya da yawa ba, saboda haka dangoginsu ba su yi yawa kamar mutanen Yahuda ba.28Su ka zauna a Biyasheba, Molada, da kuma Hazar Shuwal.
29Sun kuma zauna a Bilha, Ezem, Tolad,30Betuwel, Horma, Ziklag,31Bet Markabot, Hazar Susim, Bet Biri, da Sha'arayim. Waɗannan su ne biranensu har ya zuwa mulkin Dauda.
32‌Ƙauyukansu biyar su ne Itam, Ain, Rimmon, Token, da Ashan,33da dukkan ƙauyukan da ke kewaye har zuwa Baalat. Waɗannan su ne mazauninsu, kuma suka adana tarihin zuriyarsu a rubuce.
34Shugabannin dangi su ne Meshobab, Yamlek, Yosha ɗan Amaziya,35Yowel, Yehu ɗan Yoshibiya ɗan Serayiya ɗan Asiyel,36Eliyonai, Ya'akoba, Yeshohaiya, Asayiya, Adiyel, Yesimiyel, Binayiya37da Ziza ɗan Shifi ɗan Allon ɖan Yedayiya ɗan Shimri ɗan Shemayiya.38Waɗannan da aka ambata da sunaye shugabanni ne cikin dangoginsu, dangoginsu kuma su ka ƙaru ainun.
39Su ka tafi kusa da Gebor, yamma da kwari, domin su nemi makiyaya saboda garkunansu.40Suka kuwa sami makiyaya mai dausayi. ‌Ƙasar mai girma ce, ba fitina ga kuma salama. Dã Hamawa suka zauna a wurin.41Waɗannan da aka lisafta da sunaye sun zo ne a zamanin Hezekiya sarkin Yahuda, suka hari mazaunin Hamawa da na Mewunawa, waɗanda su ke a wurin. Suka hallakar da su gaba ɗaya suka gãje wurin sabili da sun sami makiyaya mai dausayi domin garkunansu.
42Mutane ɗari biyar daga kabilar Simiyon su ka tafi Tsaunin Seyir, tare da shugabaninsu Felatiya, Niyeriya, Refayiya, da Uzziyel 'ya'yan Ishi.43Suka ci sauran Amelikawa 'yan gudun hijira, suka zauna a can har zuwa yau.

5

1'Ya'yan Ruben ɗan farin Isra'ila - Ruben shi ne ɗan farin Isra'ila, amma aka ba da girman ɗan farinsa ga 'ya'yan Yosef ɗan Isra'ila domin Ruben ya ƙazantar da gadon mahaifinsa. Saboda haka ba a lisafta shi a matsayin ɗan fãri ba.2Yahuda shi ne mafi ƙarfi cikin 'ya'uwansa, shugaba kuma zai fito da ga cikinsa. Amma albarkar ɗan fari na Yosef ne -3'ya'yan Ruben ɗan farin Isra'ila su ne Hanok, Fallu, Hezron da Karmi.

4Waɗannan su ne zuriyar Yowel: ‌Ɗan Yowel shi ne Shemayiya. ‌Ɗan Shemayiya shi ne Gog. ‌Ɗan Gog shi ne Shimei.5‌Ɗan Shimei shi ne Mika. ‌Ɗan Mika shi ne Reyayiya. ‌Ɗan Reyayiya shi ne Ba'al.6‌Ɗan Ba'al shi ne Bira, wanda Tilgat Filesa sarkin Asiriya ya kai su bautar talala. Bira shugaba ne cikin kabilar Ruben.
7Waɗannan su ne 'yan'uwan Bira cikin dangoginsu ga yadda aka lisaftasu cikin rubutun tarihin asali: Yeyel shi ne babba, Zekariya, da8Bela ɗan Azaz ɗan Shema ɗan Yowel. Suka zauna a Arowa, har can nesa da Nebo da Ba'al Meyon,9daga gabas kuma har zuwa goshin jejin da ya miƙe zuwa Kogin Yuferatis. Wannan ya zama haka domin suna da garken dabbobi da yawa a ƙasar Giliyad.
10A zamanin Saul, kabilar Ruben ta faɗa wa Hagarawa ta ci su. Suka zauna a rumfunan Hagarawa a dukkan ƙasar da ke gabashin Giliyad.
11'Yan kabilar Gad suka zauna kusa da su, a cikin ƙasar Bashan har zuwa Saleka.12Shugabanninsu su ne Yowel, wanda shugaba ne, da Shafan shi ma wani shugaba ne, da Yanai da Shafat a Bashan.13'Yan'uwansu ta wurin iyalan mahaifisu su ne Mika'el, Meshulam, Sheba, Yorai, Yakan, Ziya, da Eber - su bakwai cur.
14Waɗannan mutane da aka ambata a baya su ne zuriyar Abihal, Abihal ɗan Huri ne, Huri ɗan Yarowa ne. Yarowa ɗan Giliyad ne. Giliyad ɗan Mika'el ne. Mika'el ɗan Yeshishai ne. Yeshishai ɗan Yahdo ne. Yahdo ɗan Buz ne.15Ahi ɗan Abdiyel ɗan Guni, shugaba ne a iyalin mahaifinsa.
16Sun zauna a Giliyad, da Bashan da cikin garuruwanta da kuma cikin dukkan makiyayan ƙasar Sharon har zuwa goshin iyakarta.17An rubuta waɗannan dukka bisa ga tarihin asali a kwanakin Yotam sarkin Yahuda da kuma Yerobowam sarkin Isra'ila.
18Rubenawa da Gadawa, da rabin kabilar Manasse su na da jarumawa dubu arba'in da hudu gwanayen mayaƙa, ɗauke da garkuwa da takobi da masu harbi da baka.19Suka kai hari ga Hagarawa, Yetur, Nafish, da Nodab.
20Suka sami taimakon yin yaƙi da abokan gabarsu daga Mai iko dukka. Da haka ne, su ka ci Hagarawa da dukkan waɗanda ke tare da su. Wannan ya faru domin Isra'ilawa sun yi kuka ga Allah cikin yaƙin, ya kuma sauraresu domin sun dogara gareshi.21Suka washe dabbobinsu, tare da raƙuma dubu hamsin, tumaki 250,000, jakai dubu biyu, da mazaje 100,000.22Sabili da Allah ya yi yaƙi domin su, suka kashe maƙiyansu da yawa. Suka zauna a ƙasarsu har lokacin zuwa bautar talala.
23Rabin kabilar Manasse suka zauna a ƙasar Bashan har zuwa Ba'al Harmon da Senir (wato Tsaunin Harmon).24Waɗannan su ne shugabannin gidajen ubanninsu: Efer, Ishi, Eliyel, Azriyel, Irmiya, Hodabiya, da Yadiyel. Waɗannan ƙarfafa ne kuma jarumawan mutane ne, shahararrun mutane, shugabannin gidajen ubanninsu.
25Amma suka yi rashin aminci ga Allahn kakanninsu. A maimako, sai suka yi sujada ga allolin mutanen ƙasar, waɗanda Allah ya hallakar a gabansu.26Allah na Isra'ila ya zuga Ful sarkin Asiriya (ana kiransa Tilgat Filesa sarkin Asiriya). Ya kwashe waɗannan zuwa bautar talala Rubenawa, da Gadawa da rabin kabilar Manasse. Ya kawo su Halah, Habor, Hara, har kuma ya zuwa kogin Gozan, in da suke zaune har wa yau.

6

1'Ya'yan Lebi su ne Geshon, Kohat, da Merari.2'Ya'yan Kohat su ne Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel.3'Ya'yan Amram su ne Haruna, Musa da Miriyam. 'Ya'yan Haruna su ne Nadab, Abihu, Eliyeza da Itama.

4Eliyeza ya zama mahaifin Finehas sai kuma Finehas ya zama mahaifin Abishuwa.5Abishuwa ya zama mahaifin Bukki. Sai Bukki ya zama mahaifni Uzzi.6Uzzi ya zama mahaifin Zerahiya, Zerahiya yazama mahaifni Merayot.
7Merayot ya zama mahaifni Amariya, Amariya ya zama mahaifni Ahitub.8Ahitub ya zama mahaifin Zadok, Zadok ya zama mahaifin Ahima'az.9Ahima'az ya zama mahaifin Azariya, Azariya ya zama mahaifin Yohanan.
10Yohanan ya zama mahaifin Azariya wanda ya yi hidima a haikalin da Suleman ya gina a Yerusalem.11Azariya ya zama mahaifin Amariya kuma Amariya ya zama mahaifin Ahitub.12Ahitub ya zama mahaifin Zadok, Zadok ya zama mahaifin Shallum.
13Shallum ya zama mahaifin Hilkiya, Hilkiya ya zama mahaifin Azariya.14Azariya ya zama mahaifin Serayiya, sai kuma Serayiya ya zama mahaifin Yozadak.15Aka kama Yozadak aka tafi da shi a tsare lokacin da Yahweh ya aika Yahuda da Yerusalem bautar talala ta hannun Nebukadnezza.
16'Ya'yan Lebi su ne Gashom, Kohat, da Merari.17'Ya'yan Gashom su ne Libni, da Shimei.18'Ya'yan Kohat su ne Amram, Izar, Hebron da Uzziyel.
19'Ya'yan Merari su ne Mali da Mushi. Waɗannan ne suka zama kabilar Lebiyawa bisa ga gidajen ubanninsu.20Zuriyar Gershon ya soma da ɗansa Libni ɗan LIbni kuwa Yahat ne.‌ Ɗansa kuwa Zimma ne.‌21Ɗansa Yohat ne.‌ Ɗansa Iddo ne.‌ Ɗansa Zera ne.‌ Ɗansa Yeyaterai ne.
22Zuriyar Kohat: ‌Ɗansa shi ne Aminadab.‌ Ɗansa kuwa shi ne Kora.‌ Ɗansa shi ne Assir.‌23Ɗansa shi ne Elkana. Ɗansa shi ne Abiyasaf. ‌Ɗansa shi ne Assir.24Ɗansa shi ne Tahat. Ɗansa shi ne Uriyel. Ɗansa shi ne Uzziya. ‌Ɗansa shi ne Shawul.
25'Ya'yan Elkana su ne Amasai, Ahimot, da wani ɗa kuma da aka kira Elkana.;26Ɗansa shi ne Zofai.‌ Ɗansa shi ne Nahat.‌27Ɗansa shi ne Eliyab.‌ Ɗansa shi ne Yeroham.‌ Ɗansa shi ne Elkana.
28'Ya'yan Sama'ila su ne ɗan farinsa Yowel, da Abiya na biyu.29‌Ɗan Merari shi ne Mahli.‌ Ɗansa shi ne Libni. ‌Ɗansa shi ne Shimei.‌ Ɗ‌ansa shi ne Uzza.‌30Ɗansa shi neShimeya.‌ Ɗansa shi ne Haggiya.‌ Ɗansa shi ne Asayiya.
31Waɗannan su ne sunayen mutanen da Dauda ya sa su bisa hidimar waƙa a haikalin Yahweh, bayan da akwatin alƙawari ya sami hutawa a wurin.32Suka yi hidima ta wurin waƙoƙi a gaban rumfar sujada, rumfar taruwa, har sai da Suleman ya gina haikalin Yahweh a Yerusalem. Suka aiwatar da hidimarsu bisa ga umarnin da aka ba su.
33Waɗannan su ne suka yi hidima da 'ya'yansu. Daga dangogin Kohatawa aka sami Heman mawaƙi. Ga kakanninsa idan an koma lokacin baya: Heman ɗan Yowel ne. Yowel ɗan Sama'ila ne.34Sama'ila ɗan Elkana ne. Elkana ɗan Yeroham ne. Yeroham ɗan Eliyel ne. Eliyel ɗan Towa ne.35Towa ɗan Zuf ne. Zuf ɗan Elkana ne. Elkana ɗan Mahat ne. Mahat ɗan Amasai ne. Amasai ɗan Elkana ne.
36Elkana ɗan Yowel ne. Yowel ɗan Azariya ne. Azariya ɗan Zefaniya ne.37Zefaniya ɗan Tahat ne. Tahat ɗan Assir ne. Assir ɗan Ebiyasaf ne. Ebiyasaf ɗan Kora ne.38Kora ɗan Izar ne. Izar Kohat ne. Kohat ɗan Lebi ne. Lebi ɗan Isra'ila ne.
39Abokin Heman Asaf ne, shi ya tsaya a hannun damarsa. Asaf ɗan Berekiya ne. Berekiya ɗan Shimeya ne.40Shimeya ɗan Mika'el ne. Mika'el ɗan Ba'asiya ne. Ba'asiya ɗan Malkiya ne.41Malkiya ɗan Etni ne. Etni ɗan Zera ne. Zera ɗan Adaya ne.42Adaya ɗan Itam ne. Itam ɗan Zimma ne. Zimma ɗan Shimei ne.43Shimei ɗan Yahat ne. Yahat ɗan Geshon ne. Geshon ɗan Lebi ne.
44A hannun hagun Herman akwai abokansa su ne "ya'ya Merari. Su ne waɗannan Etan ɗan Kishi. Kishi ɗan Abdi ne. Abdi ɗan Malluk ne.45Malluk ɗan Hashabiya ne. Hashabiya ɗan Amaziya ne. Amaziya ɗan Hilkiya ne.46Hilkiya ɗan Amzi ne. Amzi ɗan Bani ne. Bani ɗan Shemer ne.47Shemer ɗan Mahli ne. Mahli ɗan Mushi ne. Mushi ɗan Merari ne. Merari ɗan Lebi ne.
48Aka ba abokan aikinsu Lebiyawa dukkan hidimar rumfar sujada, gidan Yahweh.
49Haruna da 'ya'yansa suka yi hidimar miƙa baye-baye bisa bagadi domin baye-bayen ƙonawa; da kuma baiko bisa bagadin turare domin dukkan aiki a wuri mafi tsarki. Waɗannan baye-baye suka yi kaffara domin Isra'ila, bisa ga dukkan abin da bawan Allah Musa ya umurta.
50Zuriyar Haruna kenan bi da bi: Ɗan Haruna shi ne Eliyeza.‌ Ɗan Eliyeza shi ne Fenihas.‌ Ɗan Fenihas shi ne Abishuwa.‌51Ɗan Abishuwa shi ne Bukki.‌ Ɗan Bukki shi ne Uzzi.‌ Ɗan Uzzi shi ne Zerahiya.‌52Ɗan Zerahiya shi ne Merayot‌. Ɗan Merayot shi ne Amariya.‌ Ɗan Amaraiya shi ne Ahitub.‌53Ɗan Ahitub shi ne Zadok.‌ Ɗan Zadok shi ne Ahima'az.
54Ga wuraren da aka ba zuriyar Haruna su zauna, wato, zuriyar Haruna waɗanda ke daga dangin Kohatawa (rabo na fari nasu ne).55Aka ba su Hebron a ƙasar Yahuda da kuma makiyayarta,56amma jejin birnin da ƙauyukansa aka ba Kaleb ɗan Yefunne.
57Aka ba zuriyar Haruna: Hebron (birnin mafaƙa), da Libna da makiyayarta, Yattir, Estomawa da makiyayarta,58Hilen da makiyayarta, da Debir da makiyayarta.
59Aka ba zuriyar Haruna: Ashan da makiyayarta, Yutta da Bet Shemesh da makiyayarta;60daga kabilar Benyamin aka ba su Geba da makiyayarta, Alemet da makiyayarta, da Anatot da makiyayarta. Dukkan biranen iyalen Kohat guda goma sha uku ne.
61Ga sauran zuriyar Kohat ta wurin kuri'a aka ba su birane goma daga rabin kabilar Manasse.62Ga zuriyar Gershon a cikin dangoginsu da bam da bam aka ba su birane goma sha uku daga cikin kabilar Issaka, Asha, Naftali, da rabin kabilar Manasse a Bashan.
63Aka ba zuriyar Merari birane goma sha biyu dangi bayan dangi, daga kabilar Ruben, Gad da Zebulun.64Sai mutanen Isra'ila suka bada waɗannan birane da makiyayarsu ga Lebiyawa.65Aka ba su ta wurin ƙuri'a garuruwan da aka zana a baya daga kabilun Yahuda, Simiyon da Benyamin.
66Ga wasu dangogin Kohatawa aka bada birane daga gundumar Ifraim.67Aka basu: Shekem (birnin mafaƙa) da makiyayarta a ƙasar duwatsu ta Ifraim, Gezer da makiyayarta,68Yokmiyam da makiyayarta, Bet Horon da makiyayarta,69Aijalon da makiyayarta, da Gat Rimmon da makiyayarta.
70Rabin kabilar Manasse suka ba Kohatawa: Aner da makiyayarta da Bileyam da makiyayarta. Waɗannan suka zama mallaƙar sauran dangogin Kohatawa.
71Zuriyar Geshon daga dangogin rabin kabilar Manasse, aka ba Golan a Bashan da makiyayarta da Ashtarot da makiyayarta.72Kabilar Issaka ta ba zuriyar Geshon: Kedesh da makiyayarta, Daberat da makiyayarta,73Ramot da makiyayarta, da Anem da makiyayarta.
74Daga kabilar Asha Issaka ta karɓi: Mashal da makiyayarta, Abdon da makiyayarta,75Hukok da makiyayarta, da Rehob da makiyayarta.76Suka karɓa daga kabilar Naftali: Kedesh a Galili da makiyayarta, Hammon da makiyayarta, Kiriyatayim da makiyayarta.
77Ga sauran zuriyar Merari aka ba su daga kabilar Zebulun: Yokheyam, Kartah, Rimmono da makiyayarta da Tabor da makiyayarta;78daga na kabilar Ruben a hayin Yodan a Yeriko, a gabashin kogin: Beza a cikin jeji da makiyayarta, Yahza da makiyayarta,79Kedemot da makiyayarta, da Mefa'at da makiyayarta.
80Daga kabilar Gad, Lebiyawa suka karɓi: Ramot a Giliyad da makiyayarta, Mahanayim da makiyayarta,81Heshbon da makiyayarta, da Yazer da makiyayarta.

7

1'Ya'yan Issaka huɗu su ne: Tola, Fuwa, Yashub, da Shimron.2'Ya'yan Tola su ne; Uzzi, Refayiya, Yeriyel, Yahmai, Ibsam, da Sama'ila. Su ne shugabannin gidajen ubanninsu, daga zuriyar Tola an lissafa su cikin jarumawa a zamanin su. Sun kai mutum 22,600 a cikin zamanin Dauda.3Dan Uzzi shi ne Izrahiya. 'Ya'yansa su ne Mika'el, Obadiya, Yowel da Ishiya, dukkansu biyar ɗin shugabannin zuriya ne.

4Tare da su kuma suna da taron rundunar yaƙi zambar talatin da shida, bisa ga tsarin dake na dangogin kakanninsu, gama suna da mata yawa da 'ya'ya.5'Yan'uwansu, mayaƙan mutane daga dukkan kabilar Issaka, suna da jarumawa dubu tamanin da bakwai, bisa ga lissafin tarihin asalinsu.
6'Ya'yan Benyamin uku su ne Bela, Beker, da Yediyayel.7'Ya'yan Bela guda biyar su ne Ezbon, Uzzi, Uzziyel, Yerimot, da Iri. Su sojoji ne kuma shugabannin gidajen ubanninsu. Mutanen su sun kai 22,034 mayaƙan mutane, bisa ga jerin lissafin dangogin kakanninsu.
8'Ya'yan Beka su ne Zemirah, Yo'ash, Eliyeza, Eliyonai, Omri, Yeremot, Abijah, Anatot, da Alemet. Dukkan waɗannan 'ya'yansa ne.9Lissafin dangoginsu yakai 20,200 shugabannin gida idajen ubanninsu kuma jarumawa.10Ɗan Yediyel shi ne Bilhan. 'Ya'yan Bilhan su ne Yewush, Benyamin, Ehud, Kena'ana, Zetan, Tarshish, da Ahishaha.
11Dukkan waɗannan 'ya'yan Yediyayel. Jerinsu cikin zuriyarsu sun kai 17,200 shugabannin gidajen ubanninsu kuma mayaƙa maza da su ka cancanci hidimar soja.12(Shuffitawa da Huffitawa 'ya'yan Ir, da Hushitawa ɗan Aher ne.)
13'Ya'yan Naftali su ne Yahziyel, Guni, Yezer, da Shillem. Waɗannan su ne jikokin Bilha.
14Manasse ya na da ɗa mai suna Asriyel, wanda ƙwarƙwararsa Ba'aramiye ta haifa. Ta kuma haifi Makir, mahaifin Giliyad.15Makir ya ɗauko mace daga wurin Huffitawa da Shuffitawa. Sunan 'yar'uwarta shi ne Ma'aka. Wata zuriyar Manasse kuma shi ne Zelofihad, wanda 'ya'yansa mata ne kaɗai.16Ma'aka matar Makir, ta haifa masa ɗa ta kira shi Feresh. Sunan ɗan'uwansa kuma shi ne Sheresh, 'ya'yansa kuma Ulam da Rakem.
17'‌Ɗ‌an Ulam kuma shi ne Bedan. Waɗannan su ne zuriyar Giliyad ɗan Makir ɗan Manasse.18'Yar'uwar Giliyad Hammoleket ta haifi Ishhod, Abiyeya, da Mahla.19'Ya'yan Shemida su ne Ahiyan, Shekem, Likhi, da Aniyam.
20Zuriyar Ifraim su ne kamar haka: ɗan Ifraim shi ne Shutela. ‌Ɗ‌an Shutela shi ne Bered. Ɗan Bered shi ne Tahat. Ɗan Tahat shi ne Eleyada. Ɗan Eliyada shi ne Tahat.21Ɗan Tahad shi ne Zabad. Dan Zabad shi ne Shutela. (Ezer da Eleyad mutanen Gat ne suka kashe su, mutanen da aka haifa cikin ƙasar, lokacin da suka je su sace masu shanunsu.22Ifraim mahaifinsu ya yi makoki dominsu kwanaki da yawa, 'ya'uwansa kuma suka zo don su ta'azantar da shi.
23Ya kwana da matarsa. Sai ta yi ciki ta haifi ɗa. Ifraim ya kira shi Beriya, saboda masifa ta zo wa iyalinsa.)24‌Ɗ‌iyarsa ita ce Sheerah, wadda ta gina Runtse da Sama Bet Horon da Uzzen Sheerah.
25‌Ɗansa shi ne Refha. ‌Ɗan Refha shi ne Reshef. ‌Ɗ‌an Reshef shi ne Tela.‌ Ɗ‌an Tela shi ne Tahan. ‌Ɗan Tahan shi ne Ladan.26‌Ɗ‌an Ladan shi ne Ammihud. ‌Ɗan Ammihud shi ne Elishama.27‌Ɗ‌an Elishama shi ne Nun. ‌Ɗan Nun shi ne Yoshuwa.
28Mallakarsu da mazaunansu Betel ne da ƙauyukansu na kewaye. Suka miƙa ta gabashi zuwa Na'aran da yammaci zuwa Gezar da ƙauyukansu, zuwa Shekem da ƙauyukansu zuwa Ayyah da ƙauyukansu.29Akan iyaka da Manasse su ne Bet Shan da ƙauyukansu, Ta'anak da ƙauyukansu Megiddo da ƙauyukansu, da Dor da ƙauyukansu. A cikin waɗannan garuruwa zuriyar Yosef ɗan Isra'ila suke zaune.
30'Ya'yan Asha su ne Imna, Ishba, Ishbi, da Beriya. Serah 'yar'uwar su ce.31'Ya'yan Beriya su ne Heber da Malkiyel, shi ne mahaifin Birza'it.32'Ya'yan Heber su ne Yaflet, Shomer da Hotman. Shuwa 'yar'uwarsu ce.
33'Ya'yan Yaflet su ne Fasak, Bimhal, da Ashbat. Waɗannan su ne 'ya'yan Yaflet.34Shomer, ɗan'uwan Yaflet, yana da 'ya'ya kamar haka: Roga, Hubba, da Aram.35‌Ɗ‌an'uwan Shemer, wato Helem, yana da 'ya'ya kamar haka: Zofa, Imna, Shelesh, da Amal.
36'Ya'yan Zofa su ne Suwa, Harnefa, Shuwal, Beri, Imrah,37Bezer, Hod, Shamma, Shilsha, Itran, da Beera.38'Ya'yan Yeter su ne Yefunne, Fisfa, da Ara.
39'Ya'yan Ulla su ne Ara, Hanniyel, da Riziya.40Duk waɗannan zuriyar Ashar ne. Su ne kakannin dangogi, shugabannin gidajen ubanninsu, fitattun mutane, mayaƙan mutane, sarakuna a cikin shugabanni. Sun kai su dubu ashirin da shida mazaje da suka cancanta domin yin hidimar aikin soja, bisa ga jerin lissafinsu.

8

1'Ya'yan Benyamin biyar su ne Bela ɗan farinsa, Ashbel, Aharan,2Nohah, da Rafa.3'Ya'yan Bela su ne Adda, Gera, Abihud,4Abishuwa, Na'aman, Ahowa,5Gera, Shefufan, da Huram.

6Waɗannan su ne zuriyar Ehud shugabannin gidajen ubanninsu domin mazaunan Geba, waɗanda aka tilasta masu su tafi Manahat:7Na'aman, Ahiyah, da Gera. Na ƙarshen, Gera, ya jagorance su cikin tafiyarsu. Shi ne mahaifin Uzza da Ahihud.
8Shaharayim ya zama mahaifni 'ya'ya cikin ƙasar Mowab, bayan ya saki matansa Hushim da Ba'ara.9Ta wurin matarsa Hodesh, Shaharayim ya zama mahaifin Yobab, Zibiya, Mesha, Malkam,10Yewuz, Shakiya, da Mirma. Waɗannan su ne 'ya'yansa, shugabanni cikin gidajen ubanninsu.11Ya rigaya ya zama mahaifin Abitub da Elfa'al ta wurin Hushim.
12'Ya'yan Elfa'al su ne Eber, Misham, da Shemed (wanda ya gina Ono da Lod tare da ƙauyukan da ke kewaye da su).13Akwai kuma Beriya da Shema. Su ne shugabannin zuriyar da suke zama cikin Aijalon, waɗanda suka kori mazaunan Gat.
14Beriya yana da waɗannan 'ya'ya: Ahio, Shashak, Yeremot,15Zebadiya, Arad, Eder,16Mika'el, Ishfa, da Yoha.17Elfa'al yana da waɗannan 'ya'yan: Zebadiya, Meshullam, Hizki,18Heber, Ishmerai, Izliya, da Yobab.
19Shimei yana da waɗannan 'ya'yan: Yakim, Zikri, Zabdi,20Eliyenai, Zilletai, Eliyel,21Adayiya, Berayiya, da Shimrat.
22Shashak yana da waɗannan 'ya'yan: Ishfan, Eber, Eliyel,23Abdon, Zikri, Hanan,24Hananiya, Elam, Antotijah,25Ifdeyiya, da Fenuwel.
26Yeroham na da waɗannan 'ya'yan: Shamsherai, Shehariya, Ataliya,27Ya'areshiya, Iliya da Zikri.28Waɗannan su ne shugabannin gidajen ubanninsu da suka zauna cikin Yerusalem.
29Yeyil, mahaifin Gibiyon, sunan matarsa ita ce Ma'aka, ya zamna cikin Gibiyon.30‌'Ɗan farinsa shi ne Abdon, sai Zur, Kish, Ba'al, Nadab,31Gedor, Ahiyo, da Zeker.
32Wani daga cikin 'ya'yan Yeyil shi ne Miklot, wanda ya zama mahaifin Shimeya. Sun zauna kusa da 'yan'uwansu cikin Yerusalem.33Ner shi ne mahaifin Kish. Kish shi ne mahaifin Saul. Saul shi ne mahaifin Yonatan, Malki-Shuwa, Abinadab, da Esh-Ba'al.34'‌Ɗan Yonatan shi ne Merib-Ba'al. Merib-Ba'al shi ne mahaifin Mika.
35'Ya'yan Mika su ne, Fithon, Melek, Tareya, da Ahaz.36Ahaz ya zama mahaifin Yehoada. Yehoada shi ne mahaifin Alemet, Azmabet da Zimri, Zimri shi ne mahaifin Moza.37Moza shi ne mahaifin Bineya. Bineya shi ne mahaifin Rafa. Rafa shi ne mahaifin Eliyasa. Eliyasa shi ne mahaifin Azel.
38Azel yana da 'ya'ya shida: Azrikam, Bokeru, Ishmail, Sheyariya, Obadiya, da Hanan. Dukkan waɗannan 'ya'yan Azel ne.39'Ya'yan Eshek, da ɗan'uwansa, su ne Ulam ɗan farinsa, Yewush na biyu, da Elifelet na uku.40'Ya'yan Ulam mayaƙa ne da maharba. Suna da 'ya'ya da jikoki da yawa, jimillarsu 150. Dukkan waɗannan daga zuriyar Benyamin suke.

9

1Haka dukkan Isra'ila aka rubuta su bisa ga tarihin asalinsu. An rubuta su cikin littafin sarakunan Isra'ila. Amma game da Yahuda, an ɗauke su zuwa bauta cikin Babila saboda zunubinsu.2Na farko da suka zauna cikin biranensu su ne waɗansu Isra'ilawa, firistoci, Lebiyawa da bayin haikali.3Waɗansu zuriyar Yahuda, Benyamin, Ifraim, da Manasse sun zauna cikin Yerusalem.

4Waɗanda suka zauna sun haɗa da Utai ɗan Ammihud ɗan Omri ɗan Imri ɗan Bani, ɗaya daga cikin zuriyar Ferez ɗan Yahuda.5A cikin Shelonawa su ne Asayiya ɗan fari da 'ya'yansa kuma.6A cikin zuriyar Zera akwai Yewuel. Yawan zuriyarsu ta kai 690.
7Daga zuriyar Benyamin akwai Sallu ɗan Meshullam ɗan Hodabiya ɗan Hassenuya.8Akwai kuma Ibneyiya ɗan Yeroham; Elah ɗan Uzzi ɗan Mikri; da Meshullam ɗan Shefatiya ɗan Rewuel ɗan Ibnijah.9'Yan'uwansu da ke rubuce cikin tarihin asalinsu sun kai 956. Dukkan waɗannan mutanen shugabanni ne cikin zuriyar kakanninsu.
10Firistoci su ne Yedayiya, Yeho'iarib, da Yakin.11Akwai kuma Azariya ɗan Hilkiya ɗan Meshullam ɗan Zadok ɗan Meraiyot ɗan Ahitub, shugaba a cikin gidan Allah.
12Akwai Adayiya ɗan Yeroham ɗan Fashur ɗan Malkijah. Akwai kuma Ma'asai ɗan Adiyel ɗan Yahzera ɗan Meshullam ɗan Meshillemit ɗan Immer.13'Yan'uwansu, da suke shugabanni cikin gidajen kakanninsu, sun kai 1,760. Mutane ne da suka iya aiki cikin gidan Allah.
14A wajen Lebiyawa, akwai Shemaiya ɗan Hasshub ɗan Azrikam ɗan Hashabiya, daga zuriyar Merari.15Akwai kuma Bakbakkar, Heresh, Galal, da Mattaniya ɗan Mika ɗan Zikri ɗan Asaf.16Akwai kuma Obadiya ɗan Shemaiya ɗan Galal ɗan Yedutun; and Berekiya ɗan Asa ɗan Elkana, wanda ya zauna a ƙauyukan Netofatawa.
17Matsaran ƙofa su ne Shallum, Akkub, Talmon, Ahiman, da zuriyarsu. Shullam shi ne shugabansu.18Dã suna tsaro a ƙofar sarki ta wajen gabas domin sansanin zuriyar Lebi.19Shallum ɗan Kore ɗan Ebiyasaf, wanda a matsayinsa na ɗan Kora, da 'yan'uwansa daga gidan mahaifinsa, su Korawa, suna bisa aikin hidima, su na kula da ƙofar rumfa, kamar yadda kakanninsu suka kula da sansanin Yahweh, suna kuma tsaron wurin shiga.
20Finehas ɗan Eliyeza shi ne shugabansu a dã, Yahweh kuma yana tare da shi.21Zekariya ɗan Meshelemiya shi ne mai tsaron ƙofar shiga haikali, "rumfar taruwa."
22Dukkan waɗanda aka zaɓe su matsaran ƙofofi sun kai 212. An rubata sunayensu cikin lissafin mutane cikin ƙauyukansu. Dauda da Sama'ila mai gani sun sanya su cikin muƙamansu na amana.23Da su da 'ya'yansu sun kula da ƙofofin gidan Yahweh, wato rumfar sujada.24An sanya matsran ƙofofi a dukkan kusurwoyi huɗu, wajen gabas, yamma, arewa, da kudu.
25'Yan'uwansu, da ke zaune a ƙauyukansu, sun zo domin kewayawa na kwana bakwai, a juyi.26Amma shugabannin matsara huɗu, wato Lebiyawa, an sanya su kula da ɗakuna da ɗakunan ajiya cikin gidan Allah.27Sukan tsaya dukkan dare a wurarensu kewaye da gidan Allah. Domin suke da haƙƙin kula da shi. Za su buɗe shi kowacce safiya.
28Waɗansun su suna kula da kayan haikali; suna ƙirga su yayin da aka kawo su ko aka fitar da su.29Waɗansu kuma an sanya su kula da abubuwa masu tsarki, kayayyaki, da kayan da aka tanada, waɗanda sun haɗa da gari mai laushi, ruwan inabi, mai, da turaren ƙonawa, da kayan yaji.
30Waɗansu 'ya'yan firistoci sukan haɗa kayan yaji.31Mattitiya, ɗaya daga cikin Lebiyawa wanda ɗan fari ne a wurin Shallum Korahiye, shi ne ke ɗauke da nawayar shirya gurasa domin baye-baye.32Waɗansu 'yan'uwansu, zuriyar Kohatawa, su ne masu kula da yin gurasa, su shirya kowacce Asabaci.
33Mawaƙa da shugabannin gidajen ubannin Lebiyawa sun zauna cikin ɗakuna a wuri mai tsarki lokacin da ba su da wani aiki, domin dole su aiwatar da nasu ayyuka dare da rana.34Waɗannan shugabannin gidajen ubannin cikin Lebiyawa ne, kamar yadda ya ke a jere cikin rubutaccen tarihin asalinsu. Suna zama cikin Yerusalem.
35Mahaifin Gibiyon, Yeyiyel, sunan matarsa itace Ma'aka, ya zauna cikin Gibiyon.36'Dan farinsa shi ne Abdon, ɗansa shi ne Zur, Kish, Ba'al, Ner, Nadab,37Gedor Ahiyo, Zekariya da Miklot.
38Miklot shi ne mahaifin Shimeyam. Sun zauna kusa da 'yan'uwansu cikin Yerusalem.39Ner shi ne mahaifin Kish. Kish mahaifin Saul. Saul mahaifin Yonatan, Malki-Shuwa, Abinadab, da Esh-Ba'al.40‌Ɗan Yonatan shi ne Merib-Ba'al. Merib-Ba'al shi ne mahaifin Mika.
41'Ya'yan Mika su ne Fithon, Melek, Tareya, da Ahaz.42Ahaz shi ne mahaifin Yada. Yada shi ne mahaifin Alemet, Azmabet, da Zimri. Zimri shi ne mahaifin Moza.43Moza shi ne mahaifin Bineya. Bineya shi ne mahaifin Refayiya. Refayiya shi ne mahaifin Eliyasa. Eliyasa shi ne mahaifin Azel.44'Ya'yan Azel shida su ne Azrikam, Bokeru, Ishma'el, Sheyariya, Obadiya, da Hanan. Waɗannan su ne 'Ya'yan Azel.

10

1Yanzu fa Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra'ila. Kowanne mutumin Isra'ila ya gudu daga gaban Filistiyawa su ka faɗi matattu a kan Tsaunin Gilbowa.2Filistiyawa suka runtumi Saul da ɗansa kusa kusa. Filistiyawa suka kashe Yonatan, Abinadab, da Malki-Shuwa, 'ya'yansa.3Yaƙi ya tsananta gãba da Saul ƙwarai, maharba kuma sun cim masa, kuma suka yi masa rauni.

4Daga nan sai Saul ya ceda mai ɗaukar masa makamai, "Ka zare takobinka ka kashe ni da ita. In ba haka ba, waɗannan marasa kaciyar za su zo su zage ni." Amma mai ɗaukar makamansa yaƙi, domin yana jin tsoro ƙwarai. Sai Saul ya ɗauki takobinsa ya faɗi a kanta.
5Sa'ad da mai ɗaukar makamansa ya ga Saul ya mutu, shi ma sai ya faɗi a kan takobinsa ya mutu.6Da haka Saul ya mutu, da 'ya'yansa uku. Dukkan iyalin gidansa suka mutu tare.
7Sa 'ad da kowanne mutum a Isra'ila da ke cikin kwari yaga cewa sun gudu, kuma Saul da 'ya'yansa sun mutu, sai suka bar biranensu suka gudu. Daga nan sai Filistiyawa suka zo suka zauna cikinsu.8Ya zama kuwa washegari, sa'ad da Filistiyawa suka zo su ɗauki kayan matattu, sun tarar da Saul da 'ya'yansa matattu a Tsaunin Gilbowa.
9Suka tuɓe shi suka ɗauki kansa da kayan yaƙinsa. Suka aikar da saƙo ko'ina cikin Filisitaya a kuma kai labarin ga gumakansu da mutane.10Suka sa kayan yaƙinsa cikin haikalin allolinsu, suka kafe kansa a gidan Dagon.
11Sa'ad da dukkan mutanen Yabesh Giliyad suka ji dukkan abin da Filistiyawa suka yi wa Saul,12dukkan maza mayaƙa su ka je suka ɗauki jikin Saul da na 'ya'yansa, suka kawo su Yabesh. Suka bizne ƙasusuwansu ƙarƙashin itacen rimi cikin Yabesh suka yi azumi kwana bakwai.
13Saul ya mutu saboda ya yi rashin amincin ga Yahweh. Bai yi biyayya ga umarnan Yahweh ba, amma ya nemi shawara a wurin wata mai yin magana da matattu.14Bai nemi shawara daga wurin Yahweh ba, shi yasa Yahweh ya kashe shi ya mayar da mulkin ga Dauda ɗan Yesse.

11

1Daga nan si dukkan Isra'ila suka zo wurin Dauda a Hebron suka ce, "Duba, mu ƙashinka da namanka ne.2Cikin kwanakin dã, lokacin da Saul ya ke sarki a bisanmu, kai ne ka ke jagorancin mutanen Isra'ila. Yahweh Allahnka ya ce maka, 'Za ka yi kiwon mutanena Isra'ila, kuma zaka zama mai mulki bisan mutanena Isra'ila.""3Dukkan dattawan Isra'ila suka zo wurin sarki a Hebron, Dauda ya yi alƙawari da su gaban Yahweh. Suka ƙeɓe Dauda sarki a bisan Isra'ila. Ta haka maganar Yahweh wadda Sama'ila ya furta ta zama gaskiya.

4Dauda da dukkan Isra'ila suka je Isra'ila (wato, Yebus). Yebusawa mazaunan ƙasar, su na can.5Mazaunan Yebus suka ce da Dauda, "Ba za ka zo nan ba."6Amma Dauda ya ci kagarar Sihiyona, wato, Birnin Dauda. Dauda ya ce, "Duk wanda ya fara bugun Yebusawa zai zama shugaban yaƙi." Yowab ɗan Zeruya ya fara kai hari, aka mai she shi ya zama shugaba.
7Daga nan Dauda ya fara zama cikin kagara. Sai suka kira ta birnin Dauda.8Ya gina garu kewaye da birnin daga Millo da baya zuwa kewayan bangon. Yowab ya gina sauran birnin.9Dauda ya zama babba ya ƙasaita saboda Yahweh mai runduna yana tare da shi.
10Wɗannan su ne shugabanni ƙarƙashin Dauda, waɗanda su ka taimaki mulkin Dauda ya zama da karfi, tare da dukkan Isra'ila, suka sa shi ya zama sarki, da biyayya da maganar Yahweh game da Isra'ila.11Waɗannan su ne jerin ƙwararrun sojojin Dauda: Yashobeyam, ɗan Bahakmonite, shi ne hafsan ofisoshi. Ya kashe mutum ɗari uku da mashin sa a lokaci ɗaya.
12Bayan sa sai Eliyeza ɗan Dodo, Ba'ahohite, ɗaya daga cikin jarumawan nan uku.13Yana tare da Dauda a Fas Dammim, a wurin Filistiyawa suka taru domin yaƙi, inda akwai yankin ƙasa mutane kuma suka gudu daga gaban Filistiyawa.14Suka tsaya a tsakiyar filin. Suka kãre shi suka kuma kashe Filistiyawa da yawa Yahweh kuma ya cece su da babbar nasara.
15Daga nan mutum uku cikin talatin suka tafi wurin Dauda cikin dutse, a kogon Adullam. Mutanen Filistiyawa suka yi sansani a cikin Kwarin Refayim.16A lokacin nan Dauda yana cikin kagara, a kogo, yayin da Filistiyawa suka kafa sansanin su a Betlehem.17Dauda ya ji ƙishin ruwa sai ya ce, "Da ma wani zaya bani ruwa in sha daga rijiyar da ke a Betlehem, rijiyar dake a bakin ƙofa!"
18Sai jarumawan nan uku suka kụtsa cikin rundunar Filistiyawa suka ɗebo ruwa daga cikin rijiyar Betlehem, rijiyar da ke bakin ƙofa. Suka ɗauko ruwan suka kawo wa Dauda, amma yaƙi shan sa. Maimakon haka, ya tsiyaye shi ga Yahweh.19Sai ya ce, "Yahweh, ya nisantarda wannan daga gare ni, da zan sha wannan ruwan. Zan sha jinin mutane waɗanda su ka sadaukar da rayukansu?" Saboda sun sa ran su cikin haɗari, Dauda ya ƙi shan ruwan. Wannan shi ne abin da jarumawan nan uku suka yi.
20Abishai ɗan'uwan Yowab, shugabane na jarumawan uku. Ya taɓa amfani da mãshin sa ya kashe mutum ɗari uku. An faɗe shi cikin su ukun nan.21A cikin ukun ɗin ya sami girmamawa riɓi biyu har ya zama shugabansu. Ko da shike baya ɗaya daga cikin su.
22Benaiya ɗan Yeho'iada ya zama da ƙarfi daga Kabzeel wanda ya yi manyan abubuwa. Ya kashe 'ya'ya biyu na Ariyel mutumin Mowab. Ya kuma sauka cikin rami ya kashe zaki lokacin sanyin dusar ƙanƙara.23Har ya kashe Bamasare, tsawon mutumin ya kai kamu biyar. Bamasaren yana da babban mãshi misalin itacen sãƙa amma ya je wurin sa da sanda kawai. Ya fizge mãshin daga hanun Bamasaren ya kashe shi da mãshinsa.
24Benaiya ɗan Yeho'iada ya yi waɗannan ayyuka, an sanya sunansa tare da jarumawan uku.25An mutunta shi fiye da sojojin nan talatin gaba ɗaya, amma ba kamar ƙwararrun sojojin nan uku ba. Duk da haka Dauda ya sanya shi shugaba akan matsaransa.
26Jarumawan mutanen su ne: Asahel ɗan'uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo na Betlehem,27Shammot Baharore, Helek Bafelone,28Ira ɗan Ikkesh Batekoye, Abiyeza Ba'anatote,29Sibbekai Bahushate, Ilai Ba'ahohite.
30Maharai Banetofate, Heled ɗan Baanah Banetofate,31Ittai ɗan Ribai na Gibiya na zuriyar Benyamin, Benaiya Bafiratone,32Hurai na kwarurrukan Ga'ash, Abiyel Ba'arbate,33Azmabet Baharume, Eliyaba Basha'albone,
34'ya'yan Hashem Bagizoniye, Yonatan ɗan Shagi Baharare,35Ahiyam ɗan Sakar Baharare, Elifal ɗan Ur,36Hefar Bamekarate, Ahija Bafelone,37Hezro Bakarmele, Na'arai ɗan Ezbai,
38Yowel ɗan'uwan Natan, Mibhar ɗan Hagri,39Zelek Ba'moniye, Naharai Baberote (mai ɗaukar wa Yowab makamai ɗan Zeruyiya)40Ira Ba'itriye, Gareb Ba'itriye,41Yuriya Bahitte, Zadab ɗan Ahlai,
42Adina ɗan Shiza Barubeniye (shugaban Rubenawa) da mutum talatin tare dashi,43Hanan ɗan Ma'aka da Yoshafat Bamitiniye,44Uzziya Ba'ashterate, Shama da Yeyiyel 'ya'yan Hotam Ba'arowaye,
45Yediyayel ɗan Shimri, Yoha (ɗan'uwansa Batize),46Eliyel Bamahabe, Yeribai da Yoshabiya 'ya'yan Elna'am, Itma Bamowabe,47Eliyel, Obed, da Ya'asiel Bamezobate.

12

1Waɗannan su ne waɗanda suka zo wurin Dauda a Ziklag, tun lokacin da bai iya tsayawa gaban Saul ɗan Kish ba. Suna cikin sojoji, mataimakan sa a cikin yaƙi.2Maharban baka ne kuma sukan harba ta dama da hagu sukan jefa dutse da majaujawa wajen harbin kibiya da baka. Su mutanen Benyamin ne, mutanen kabilar Saul.

3Sarki shi ne Ahiyaza, sai Yowash, dukkan su 'ya'yan Shema'ah Bagibeyate. Akwai Yeziyel da Felet, 'ya'yan Azmebet. Akwai kuma Berakah, Yehu Ba'anatote,4Ishmaiya Bagibiyone, sojane cikin talatin ɗin (Kuma shugaban talatin ɗin); Irmiya, Yahaziyel, Yonanan, Yozabad Bagaderate.
5Eluzai, Yerimot, Beyaliye, Shemariya, Shefatiya Baharufiye,6Koratawa, Elkana, Isshiya, Azarel, Yoyezar, Yashobeyam, da7Yowela da Zebadiya, 'ya'yan Yeroham na Gedor.
8Waɗansu Gadawa su ka haɗu da Dauda a kagara cikin jeji. Su jarumawa ne, Horarru domin yaƙi, waɗanda sun iya garkuwa da mashi; fuskokinsu kamar na zakuna. Sauri gare su kamar bareyi a kan duwatsu.
9Akwai Ezer shugaba, Obadiya na biyu, Eliyab na uku,10Mishmanna na huɗu, Irmiya na biyar,11Attai na shida, Eliyel na bakwai,12Yonatan na takwas, Elzabad na tara,13Irmiya na goma, Makbannai na sha ɗaya.
14Waɗannan 'ya'yan Gad shugabannin runduna ne. ƙaraminsu shi ke jagorancin ɗari, babbansu shi ke jagorancin dubbai.15Sun ƙetare Yodan cikin wata na fari, sa'ad da ya yi ambaliya ya kori dukkan waɗanda suke zama cikin kwarurruka, dukka da na wajen gabas da na wajen yamma.
16Waɗansu mutanen Benyamin da na Yahuda suka zo kagara wurin Dauda.17Dauda ya fita domin ya tarye su ya yi masu jawabi yace: "Idan kun zo wurina da salama ku taimakeni, za ku iya haɗa hannu da ni. Amma idan kun zo ne domin ku bashe ni ga abokan gãba ta, bari Allah na kakanninku ya gani ya tsauta maku, gama ban yi wani abin da ba dai-dai ba."
18Sa'an nan sai Ruhu ya sauko kan Amasai, wanda ya ke shugaban talatin ɗin. Amasai ya ce, "Mu na ka ne, ya Dauda. Wajen ka mu ke, ya ɗan Yesse. Salama, bari salama ta kasance ga duk wanda ya taimakeka. Bari salama ta kasance ga masu taimakonka, gama Allahnka ya na taimakonka." Daga nan Dauda ya karɓe su ya sa su zama shugabanni akan jama'arsa.
19Waɗansu daga Manasse ku ma suka koma wajen Dauda sa'ad da ya zo tare da Filistiyawa domin ya yi yaƙi da Saul. Duk da haka ba su taimaki Filistiyawa ba, saboda shugabannin Filistiyawa sun tuntuɓi junansu sa'an nan suka sallame shi. Suka ce, "Zai koma wajen ubangidansa Saul zai jawo haɗari ga rayukanmu."20Da ya je Ziklag, mutanen Manasse da su ka haɗa hannu da su su ne Adna, Yozabad, Yediyayel, Mika'el, Yozabad, Elihu, da Zilletai, shugabanni na dubbai na Manasse.
21Sun taimaki Dauda yaƙi da taron mahara, gama su jarumawa ne. Daga baya su ka zama shugabanni cikin runduna.22Yau da gobe, mutane suka yi ta zuwa wurin Dauda domin su taimake shi, har aka sami babbar rundunar soja, kamar rundunar sojojin Allah.
23Wannan shi ne lissafin sojoji masu makamai domin yaƙi, waɗanda suka zo wurin Dauda a Hebron, domin su juyar da mulkin Saul zuwa gare shi, domin tabbatar da maganar Yahweh.24Daga Yahuda waɗanda suke ɗauke da garkuwa da mãshi sun kai 6,800, a shirye domin yaƙi.25Daga zuriyar Simiyon sun kai jarumawa 7,100
26Daga zuriyar Lebiyawa sun kai mayaƙa 4,600.27Yehoyada shi ne shugaban zuriyar 'ya'yan Haruna tare da shi akwai mutum 3,700.28Tare da Zadok saurayi, ƙaƙƙarfa, mutum mai ƙarfin hali, sun kai shugabanni ashirin da biyu daga iyalin mahaifinsa.
29Daga Benyamin, kabilar Saul, sun kai dubu uku. Yawancinsu suka zama da biyayya ga Saul har zuwa lokacin nan.30Daga Ifraim sun kai mayaƙa 20,800, suna cikin gidajen mahaifansu.31Daga rabin kabilar Manasse akwai mutane dubu goma sha takwas waɗanda suka zo domin su naɗa Dauda sarki.
32Daga Issaka, akwai shugabanni ɗari biyu masu gane zamanai sun san abin da ya kamata Isra'ila su yi. Dukkan 'yan'uwansu suna ƙarƙashin mulkinsu.33Daga Zebulun akwai mayaƙa dubu hamsin, shiryayyu domin yaƙi, da dukkan makaman yaƙi, a shirye suke suyi biyayya da zuciya ɗaya.
34Daga Naftali akwai shugabanni dubu, tare da su kuma mutum dubu talatin da bakwai tare da garkuwa da mãsu.35Daga Danawa akwai mutane 28,600 shiryayyu domin yaƙi.
36Daga Asha akwai mutane dubu arba'in shiryayyu domin yaƙi.37Daga ɗaya ƙetaren Yodan, daga Rubenawa, Gadawa, da rabin kabilar Manasse, akwai mutane 120,000 shirye domin kowanne irin yaƙi.
38Dukkan waɗannan sojojin, shiryayyu ne domin yaƙi, sun zo Hebron da tsayayyar manufa wato su naɗa Dauda sarki bisa Isra'ila.39Dukkan sauran Isra'ila kuma sun amince ya zama sarki. Suna can tare da Dauda kwana uku, suna ci da sha, gama 'yan'uwansu sun aike su da guzuri.40Har yanzu kuma, waɗanda ke kusa da su, kamar su Issaka da Zebulun da Naftali, sun kawo abinci akan jakuna da raƙuma, alfadarai, da shanu, guzurin gari, kauɗar 'ya'yan ɓaure, ruwan inabi, mai, shanu, da tumaki, gama Isra'ila tana murna.

13

1Dauda ya tuntuɓi shugabanni na mutum dubbai da na ɗaruruwa, tare ta kowanne shugaba.2Dauda ya ce da dukkan taron Isra'ila, "Idan kun ga ya yi maku kyau, idan kuma wannan ya zo ne daga wurin Yahweh Allahnmu, bari mu aika da 'yan saƙo ko'ina ga 'yan'uwanmu, waɗanda suka rage cikin dukkan lardunan Isra'ila, ga Firistoci da Lebiyawa waɗanda suke cikin garuruwansu. Bari a sanar da su cewa su haɗa kai da mu.3Bari mu kawo akwatin Allahnmu gare mu, gama ba mu nemi nufinsa a cikin kwanakin mulkin Saul ba."4Dukkan taron jama'a suka yarda da waɗannan abubuwa, saboda ya yi dai-dai a idanun dukkan mutane.

5Dauda fa ya tara dukkan Isra'ila tare, daga Shihor Kogi a cikin Masar zuwa Lebo Hamat, domin kawo akwatin Allah daga Kiriyat Yeyarim.6Dauda da dukkan Isra'ila suka hau zuwa Baalah, wato Kiriyat Yeyarim, wanda ke na Yahuda, domin daga can za a ɗauko akwatin Allah, wanda ake kira da sunan Yahweh, wanda ya ke zaune yana mulki akan Kerubim
7Sai suka sanya akwatin Allah akan sabon keken shanu. Sun fito da shi daga gidan Abinadab. Uzza da Ahiyo suna kula da keken shanun.8Dauda da dukkan Isra'ila suna murna a gaban Allah da dukkan ƙarfinsu. Suna waƙa da garayu da molaye, kugenni, da kakaki
9Sa'ad da suka zo masussukar Kidon, Uzza ya miƙa hannunsa domin ya riƙe akwatin, saboda shanun sun yi tuntuɓe.10Daga nan fushin Yahweh ya yi ƙuna akan Uzza, Yahweh ya kashe shi domin Uzza ya miƙa hannunsa ya taɓa akwatin. Ya mutu a wurin a gaban Allah.11Dauda ya yi fushi saboda Yahweh ya abkawa Uzza. Ana kiran wannan wurin Ferez Uzza har wa yau.
12Dauda ya ji tsoron Allah a wannan rana. Ya ce, "Ya ya zan kawo akwatin Allah in dawo da shi gidana?"13Dauda bai gusar da akwatin zuwa birnin Dauda ba, amma ya sa shi a gefe cikin gidan Obed Idom Bagittiye.14Akwatin Allah ya kasance cikin gidan Obed Idom har wata uku. Yahweh ya albarkaci gidansa da dukkan abin da ya mallaka.

14

1Daga nan Hiram sarkin Taya ya aika da 'yan saƙo wurin Dauda, da itatuwan Sida, kafintoci da magina. Su ka gina masa gida.2Dauda kuwa ya sa ni Yahweh ya tabbatar da shi zama sarki akan Isra'ila, kuma mulkinsa zai ɗaukaka sama domin taimakon mutanensa Isra'ila.

3A cikin Yerusalem, Dauda ya auri waɗansu mata, ya zama mahaifin waɗansu 'ya'ya maza da 'ya'ya mata.4Waɗannan su ne 'ya'yan da aka haifa masa cikin Yerusalem: Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,5Ibha, Elishuwa, Elfelet,6Noga, Nefeg, Yafiya,7Elishama, Biliyada, da Elifelet.
8Sa'ad da Filistiyawa su ka ji cewa an keɓe Dauda ya zama sarki bisa Isra'ila, dukka suka fita suna neman sa. Amma Dauda ya ji labarin sai ya fita ya yi yaƙi da su.9Filistiyawa sun rigaya sun kawo hari cikin kwarin Refayim.
10Daga nan Dauda ya nemi taimako a wurin Allah. Ya ce, "Ko zan iya kai wa Filistiyawa hari? Za ka bani nasara akan su?" Yahweh ya ce masa, "Kai masu hari, gama lallai zan ba she su gare ka."11Sai suka zo Ba'al Ferazim, a can ya yi nasara da su. Ya yaba ya ce, "Yahweh ya fasa abokan gãbata ta hannuna, kamar fasuwar ambaliyar ruwa." Sunan wannan wurin ya zama Ba'al Ferazim.12Filistiyawa suka bar allolinsu a wurin, Dauda kuma ya umarta a ƙone su.
13Filistiyawa suka sake kai hari a cikin kwari.14Dauda ya sake neman taimako a wurin Allah. Allah ya ce masa, ba za ka kai hari ta gabansu ba, amma ka kewaye su ta itatuwan balsam sai ka kai masu hari ta baya."
15Sa'ad da ka ji motsin tafiya cikin iska ta itatuwan balsam, daga nan sai ka kai hari da ƙarfi. Ka yi haka gama Allah ya rigaya ya tafi a gabanka domin ya bugi rundunar Filistiyawa."16Dauda ya yi kamar yadda Allah ya umarce shi. Ya ci nasara da rundunar Filistiyawa tun daga Gibiyon har zuwa Gezar.17Daga nan sunan Dauda ya bazu zuwa ko'ina cikin dukkan ƙasashe, Yahweh kuma ya sa dukkan ƙasashe su ji tsoron sa.

15

1Dauda ya gina wa kansa gidaje a cikin birnin Dauda. Ya shirya rumfa saboda akwatinin Yahweh inda a ka ajiye shi.2Sa'an nan Dauda yace, "Lebiyawa ne kaɗai za su ɗauki akwatin Yahweh, domin su aka zaɓa su ɗauki akwatin Yahweh, su yi masa hidima har abada."3Sa'an nan Dauda ya tattara dukkan Isra'ila a Yerusalem domin a kawo akwatin Yahweh wurin da ya shirya masa.

4Dauda ya tattara zuriyar Haruna da Lebiyawa.5Daga zuriyar Kohat akwai shugaba wato Yuriyel, da 'yan'uwansa mutum 120.6Daga zuriyar Merari akwai shugaba wato Asayiya, da 'yan'uwansa mutum 220.
7Daga zuriyar Geshon akwai shugaba wato Yowel, da 'yan'uwansa mutum 130.8Daga zuriyar Elizafan, akwai shugaba wato Shemaiya, da 'yan'uwansa mutum 200.9Daga zuriyar Hebron akwai shugaba wato Eliyel, da 'yan'uwansa mutum tamanin.10Daga zuriyar Yuziyel akwai shugaba wato Amminadab da 'yan'uwansa mutum 112.
11Dauda ya kira Zadok da Abiyata firistoci da Lebiyawa wato su, Yuriyel da Asayiya da Yowel da Shemaiya da Eliyel da Amminadab.12Ya ce da su, "Ku ne shugabannin Lebiyawa. Ku tsarkake kanku, ku da 'yan'uwanku domin ku kawo akwatin Yahweh, Allah na Isra'ila a wurin da na shirya domin sa.
13Ba ku ne ku ka ɗauke shi da farko ba. Shi ya sa Ubangiji Yahweh ya yi fushi da mu domin ba mu bi farillansa ba."14Sai firistoci da Lebiyawa suka tsarkake kansu domin su iya ɗauko akwatin Yahweh, Allah na Isra'ila.15Haka Lebiyawa suka ɗauko akwatin Yahweh, Allah na Isra'ila, a bisa kafaɗunsu da sandunan, kamar yadda Musa ya umurta - suna bin ka'idojin da aka shimfiɗa a maganar Yahweh.
16Dauda ya yi magana da shugabannin Lebiyawa su sa 'yan'uwansa su zama mawaƙa, da kayan waƙoƙi, wato su garayu da molaye da kugenni, suna kaɗa su da ƙara sosai suna tada muryoyinsu suna murna.17Sai Lebiyawa suka naɗa Heman ɗan Yowel da wani cikin 'yan'uwansa, wato Asaf ɗan Berekiya. Daga cikin 'yan'uwansu, wato daga zuriyar Merari suka naɗa Itam ɗan Kushaiya.18Tare da su akwai 'yan'uwansu aji na biyu: wato su Zekariya da Ya'aziyel da Shemiramot da Yehiyel da Unni da Eliyab da Benaiya da Ma'aseiya da Mattitiya da Elifelehu da Miknaiya da Obed Idom da Yehiyel masu tsaron ƙofa.
19Mawaƙan suka zaɓi Heman da Asaf da Itam su zama masu kaɗa kugenni masu ƙara na tagulla.20Zekariya da Aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ma'sseiya da Benaiya su ne masu kiɗan girayu, da aka shirya wa Alamot.21Mattitiya da Elifelehu da Mikneiya, Obed Idom, Yeyiyel da Azaziya suka bi da hanya tare da kiɗin girayu da aka shirya wa Sheminit.
22Kenaniya, shugaban Lebiyawa shi ne kuma shugaban mawaƙa saboda shimai koyar da waƙa ne.23Berekiya da Elkana su ne masu tsaron akwati.24Shebaniya, Yoshafat, Netanel, Amasai, Zekariya, Benaiya da Eliyeza, firistoci, su ne masu busa ƙaho a gaban akwatin Yahweh. Obed Idom da Yehiyel kuma su ne masu tsaron akwatin Yahweh.
25Sai Dauda da dattawan Isra'ila da shugabannin dubbai suka tafi don su ɗauko akwatin alƙawarin Yahweh daga gidan Obed Idom da murna.26Sa'an nan, Yahweh ya taimaki Lebiyawan da suka ɗauko akwatin alƙawarin Yahweh, suka miƙa hadaya ta bijimai bakwai da raguna bakwai.
27Dauda ya sa riga ta linin, haka kuma Lebiyawan da suka ɗauki akwatin da mawaƙa da Kenaniya shugaban mawaƙan. Dauda kuma yana saye da falmara ta linin.28Haka dukkan Isra'ila suka kawo akwatin alƙawarin Yahweh da shewa ta farinciki, da ƙarar ƙahonni da kugenni da girayu da molaye.
29Amma sa'ad da akwatin alƙawarin Yahweh ya shigo birnin Dauda, Mika'el ɗiyar Saul ta leƙa ta taga. Sai ta ga sarki Dauda yana rawa yana jin daɗi. Sai ta rena shi a cikin zuciyarta.

16

1Su kawo akwatin Yahweh suka sa shi a tsakiyar rumfar da Dauda ya kafa domin sa. Sa'an nan suka yi baye-baye na ƙonawa da baye-baye na zumunta a gaban Yahweh.2Sa'ad da Dauda ya gama yin hadayu na ƙonawa da baye - baye na zumunta, ya sa wa mutanen albarka a cikin sunan Yahweh.3Ya ba kowanne mutum namiji da mace dunƙulen gurasa da yankan nama da curin kauɗar inabi.

4Dauda ya sa waɗansu cikin Lebiyawa su yi hidima a gaban akwatin Yahweh, su yi farinciki da godiya su yi yabo ga Yahweh, Allah na Isra'ila.5Waɗannan Lebiyawa su ne Asaf, shi ne shugabansu da Zekariya, Yaaziyel, Shemiramot, Yehiyel, Mattitiya, Eliyab, Benaiya, Obed Idom da Yeyiyel. Waɗanna su ne za su kiɗa girayu da molaye. Asaf shi ne zai kiɗa kugenni da ƙara sosai.6Benaiya da Yahaziyel firistoci su ne za su yi ta busa ƙahonni, a gaban akwatin alƙawari na Allah.
7A wannan rana Dauda ya fara sa Asaf da 'yan'uwansa su rera wannan waƙa ta godiya ga Yahweh.8Ku yi godiya ga Yahweh, ku kira bisa sunansa, ku sanar da ayyukansa a cikin al'ummai.9Ku rera gare shi, ku rera yabbai gare shi, ku faɗi dukkan ayyukansa na mamaki.
10Ku yi fahariya cikin sunansa mai tsarki; bari zuciyar waɗanda suke neman Yahweh ta yi murna.11Ku nemi Yahweh da ƙarfinsa; ku nemi kasancewarsa a kullun.
12Ku tuna aiyukan ban mamakin da ya yi, da al'ajibansa da dokokin bakinsa,13ku zuriyar Isra'ila bayinsa da ku mutanen Yakubu, zaɓaɓɓunsa.14Shi ne Yahweh, Allahnmu, dokokinsa suna cikin dukkan duniya.
15Ku tsare alƙawarinsa a zukatanku har abada da maganar da ya umurta ga dubun tsararraki.16Yakan tuna alƙawarin da ya yi da Ibrahim da wa'adin da ya yi wa Ishaku.17Wannan shi ne ya tabbatar wa Yakubu ya zama ka'ida, ga Isra'ila kuma alƙawari na har abada.18Ya ce, "Zan ba ku ƙasar Kan'ana a matsayin rabonku na gădo."
19Lokacin da ba su da yawa, 'yan ƙalilan, kuma baƙi a cikin ƙasar.20Suka yi yawo daga wannan al'umma zuwa waccan, daga wannan mulki zuwa wani.21Bai yarda wani ya tsanance su ba; ya ma hori sarakuna saboda su.22Ya ce, "Kada ku taɓa shafaffuna, kada ku cuci annabawana."
23Ku rera ga Yahweh, ku duniya dukka, ku yi shelar cetonsa kowacce rana.24Ku shaida ɗaukakarsa a cikin al'ummai, ayyukansa na mamaki a cikin dukkan al'immai.
25Gama Yahweh mai girma ne, a yabe shi ƙwarai, a ji tsoron sa fiye da dukkan alloli.26Gama dukkan alloli na al'ummai gumaka ne, Amma Yahweh, shi ne ya hallicci sammai.27Daraja da martaba na tare da shi. Iko da farinciki na wurinsa.
28Ku bayar ga Yahweh, ku kabilun duniya, ku bayar da daraja da iko ga Yahweh!29Ku ba Yahweh darajar da ta dace da sunansa. Ku kawo masa baiko ku zo gabansa. Ku durƙusa ga Yahweh a cikin martabarsa mai tsarki.
30Ku yi rawar jiki a gabansa ku duniya dukka. Duniya ta kahu, ba za ta iya girgiza ba.31Bari sammai su yi murna, bari duniya ta yi farinciki, a cikin al'ummai bari su ce, "Yahweh ne ya ke mulki."
32Bari teku ya yi ruri, abin da ya ke cika shi kuma ya yi sowa ta farin ciki. Bari filaye su yi farinciki tare da dukkan abin da ke cikin su.33Bari itatuwan da ke cikin jeji su yi sowa ta farinciki a gaban Yahweh, gama yana zuwa domin ya hukunta duniya.
34A yi godiya ga Yahweh, gama nagari ne shi, alƙawarinsa na jinƙai ya tabbata har abada.35Sai ku ce, "Ka cece mu, ya Allah na cetonmu. Ka tattara mu, ka kuɓutar da mu daga sauran al'ummai, domin mu ba da godiya ga sunanka mai tsarki da ɗaukaka cikin yabonka."
36A yi yabo ga Yahweh, Allah na Isra'ila har abada abadin. Dukkan mutane suka ce, "Amin" yabo ga Yahweh.
37Sai Dauda ya bar Asaf da 'yan'uwansa a gaban akwatin alƙawari na Yahweh, su yi ta yin hidima a gaban akwatin, dai-dai da buƙatar kowacce rana.38Obed Idom haɗe da 'yan'uwan nan sittin da takwas. Obed Idom ɗan Yedutun tare da Hosah su ne masu tsaron ƙofa.39Zadok da abokan aikinsa firistoci kuma suka yi hidima a rumfar Yahweh a can tudun Gibiyon.
40Su riƙa miƙa baye-baye na ƙonawa a kan bagadi babu fasawa safe da yamma, bisa ga abin da ke rubuce a cikin shari'ar Yahweh, wadda ya ba Isra'ila umarni.41Heman da Yedutun su na tare da su da kuma waɗanda a ka kira sunayensu a ka zaɓe su, su ba da godiya ga Yahweh saboda alƙawarinsa da amincinsa sun tabbata har abada.
42Heman da Yedutun su ne za su lura da waɗanda za su busa ƙahonni da kugenni da sauran kayan kiɗin da a ke amfani da su lokacin da a ke rera waƙoƙi na saduda. 'ya'yan Yedutun su na tsaron ƙofa.43Daga nan dukkan jama'a su ka koma gidajensu, Dauda kuma ya koma gida domin ya sa wa mutanensa albarka.

17

1Ya zama bayan da sarki ya kimtsa a gidansa, sai ya ce da annanbi Natan, "Duba ni ina zaune a cikin gidan sida, amma akwatin alƙawarin Yahweh yana zaune a rumfa."2Natan yace da Dauda, "Ka yi abin da ya ke a zuciyarka, gama Yahweh yana tara da kai."

3Amma a wannan daren maganar Yahweh ta zo wurin Natan, cewa,4"Je ka, ka gaya wa Dauda bawana, 'ga abin da Yahweh ya ce: 'Kai ba za ka gina mani gidan da zan zauna ba.5Gama ba a gida ni ke zama ba tun daga ran da na kawo Isra'ila har zuwa yau. Sai dai a rumfa na ke zama da rumfar sujada a wurare dabam-daban.6A cikin dukkan wuraren da na zaga cikin Isra'ila, na taɓa yi wa wani cikin shugabannin da na sa, cewa, "Me ya sa ba ka gina mani gida na sida ba?""'
7To yanzu, ka gaya wa bawana Dauda, 'Ga abin da Yahweh mai Runduna ya ce: Na ɗauko ka daga wurin kiwo, daga bin tumaki, domin ka yi mulkin jama'ata Isra'ila.8Ina tare da kai dukkan inda ka tafi, na kuma datse dukkan maƙiyanka daga gabanka, kuma zan sa ka yi suna, kamar sunan waɗanda suke manya a duniya.
9Zan zaɓi wuri domin jama'ata Isra'ila, domin su zauna a wuri na kansu, don kada su ƙara samun tashin hankali. Mutane masu mugunta ba za su ƙara musguna masu yadda suka yi a dã ba,10kamar yadda su ka yi sa'ad da na umurci alƙalai su shugabanci jama'ata Isra'ila. Zan ladabtar da dukkan maƙiyanka. Har yanzu, ina gaya ma ka, Ni Yahweh, zan gina maka gida.
11Za ya zama idan kwankinka suka cika da za ka tafi wurin ubanninka, zan tada zuriyarka a bayanka, wani daga cikin zuyarka, zan kafa masarautarsa.12Shi zai gina mani gida, kuma zan kafa kursiyinsa har abada.
13Zan zama uba a gare shi, shi kuma zai zama ɗana. Ba zan ɗauke alƙawarin amincina daga gare shi ba kamar yadda na ɗauke daga wurin Saul, wanda ya yi mulki kafin ka.14Zan ɗora shi bisa gidana cikin masarautata har abada, kursiyinsa kuma zai tabbata har abada.'"15Natan ya yi magana da Dauda, ya baiyana masu dukkan waɗannan maganganu, ya kuma gaya masa game da wahayin gabaɗaya.
16Sai Dauda ya shiga ciki ya zauna a gaban Yahweh; ya ce, "Wanene ni, Ubangiji Yahweh, menene kuma iyalina, da ka kawo ni a wannan matsayi?17Gama wannan ƙaramin abu ne a wurin ka Yahweh. Ka yi magana a kan iyalin bawanka game da babban lokaci mai zuwa, ka kuma nuna wa bawanka tsararraki na gaba, Allah Yahweh.18Ni Dauda, me kuma zan ce da kai? Ka ɗaukaka bawanka. Gama ka darajanta bawanka sosai.
19Yahweh, saboda bawanka, kuma domin ka cika nufinka, ka yi wannan babban abu na baiyana ayyukanka masu girma.20Yahweh, ba wani kamar ka, kuma ba wani Allah ban da kai, kamar yadda mu ke ji koyaushe.21Gama ina wata al'umma kamar jama'arka Isra'ila, waɗanda ka kuɓutar daga Masar domin su zama mutanenka, su yi suna domin ka ta wurin aiyukanka masu girma da ban razana? Ka kori al'ummai daga gaban mutanenka, waɗanda ka kuɓutar daga Masar.
22Ka sa Isra'ila sun zama mutanenka har abada, kuma kai, Yahweh ka zama Allahnsu.23To yanzu, Yahweh, ka bari alƙawarin da ka yi game da bawanka da iyalinsa ya tabbata har abada. Ka yi kamar yadda ka ce.24Sunanka ya tabbata har abada ya yi girma domin mutane su ce, 'Yahweh mai Runduna shi ne Allah na Isra'ila,' gidana kuma ni, Dauda ya tabbata a gabanka har abada.
25Gama kai, Allahna, ka baiyanawa bawanka za ka gina gida domin sa. Shi ya sa ni bawanka, na sami ƙarfin in yi addu'a zuwa gare ka.26To yanzu, Yahweh, kai Allah ne, ka kuma yi wannan kyakkyawan alƙawari ga bawanka:27Gama ya gamshe ka, ka albarkaci gidan bawanka ya kasance a gabanka har abada. Kai Yahweh, kai ne ka albarkace shi, kuma zai zama mai albarka har abada."

18

1Bayan wannan sai Dauda ya kai wa Filistiyawa hari kuma ya yi nasara a kan su. Ya ƙwace Gat da ƙauyukanta daga ƙarƙashin mulkin Filistiyawa.2Daga nan ya yi nasara da Mowab, Mowabawa suka zama bayin Dauda suka biya haraji gare shi.

3Sa'an nan Dauda ya yi nasara da Hadadezer sarkin Zoba a Hamat, sa'ad da Hadadezer ya ke tafiya domin ya kafa mulkinsa a Kogin Yuferatis.4Dauda ya ƙwace masa karusai dubu da mahaya dawaki dubu bakwai da sojojin ƙasa dubu ashirin. Dauda ya yaiyanke jijiyoyin gwuiwoyin dukkan dawakan da ke jan karusai, amma ya rage waɗanda za su ja karusai ɗari.
5Sa'ad da Aramiyawan Damaskus suka zo domin su taimaki Hadadezar sarkin Zoba, Dauda ya kashe mutanen Aramiyawa dubu ashirin da biyu.6Sai Dauda ya kafa zangon sojoji a Aram ta Damaskus. Aramiyawa suka zama bayinsa suka kawo masa gaisuwa. Dukkan inda Dauda ya je, Yahweh yana ba shi nasara.
7Dauda ya ɗauko garkuwowin zinari waɗanda bayin Hadadezar ke ɗauke da su ya kawo su Yerusalem.8Dauda ya ɗauko tagulla da yawa daga Tibhat da Kun biranen Hadadezar. Da wannan tagullar ne Suleman ya yi "Teku" na tagulla da ginshiƙai da sauran kayan aiki na tagulla.
9Sa'ad da Tou sarkin Hamat ya ji labarin Dauda ya yi nasara da dukkan sojojin Hadadeza sarkin Zoba,10Sai Tou ya aika ɗansa Hadoram ya je ya gaida sarki Dauda ya sa masa albarka, saboda Dauda ya yi yaƙi da Hadadeza kuma ya yi nasara da shi, saboda Tou ya yi yaƙi da Hadadeza. Kuma Tou ya aika Dauda abubuwa daban-daban na zinariya da azurfa da tagulla.11Sarki Dauda ya keɓe waɗannan kaya ga Yahweh tare da dukkan azurfa da zinariyar da ya samo daga dukkan al'ummai: wato Idom, Mowab, da mutanen Ammon da Filistiyawa da Amelikawa.
12Abishai ɗan Zeruyiya ya kashe Idomawa dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.13Ya kafa zangon sojoji a Idom, dukkan Idomawa suka zama bayin Dauda. Yahweh ya ba Dauda nasara a dukkan inda ya je.
14Dauda ya yi mulkin dukkan Isra'ila, kuma ya yi gaskiya da adalci ga dukkan mutane.15Yowab ɗan Zeruyiya shi ne shugaban sojoji, Yehoshafat ɗan Ahilud kuma shi ne marubuci.16Zadok ɗan Ahitub da Ahimelek ɗan Abiyata su ne firistoci, Shabsha ne marubuci.17Benaiya ɗan Yehoiada shi ne shugaban Keretawa da Feletiyawa, 'ya'yan Dauda kuma su ne manyan masu ba da shawara.

19

1Daga baya sai Nahash, sarkin mutanen Amon, ya mutu, ɗansa ya gaje shi.2Dauda yace, "Zan yi mutunci ga Hanum ɗan Nahash, saboda mahaifinsa ya nuna mutunci gare ni." Sai Dauda ya aika manzanni su yi masa gaisuwa game da mahaifinsa. Bayin Dauda suka shiga ƙasar Ammoniyawa suna je wurin Hanum domin su yi masa gaisuwa.3Amma sarakunan Ammoriyawa suka ce da Hanum, "Ka na tsammani Dauda girmama mahaifinka ya ke yi da ya aiko mutane su yi maka gaisuwa? Ba leƙen asiri ya kawo su domin su duba ƙasar nan da nufin su kaɓantar da ita ba?"

4Sai Hanun ya kama bayin Dauda ya yi masu aski, ya yayyanke rigunansu har zuwa kwankwaso sa'an nan ya sallame su.5Sa'ad da suka yi wa Dauda bayani ya aika a ka tarbe su, saboda sun kunyata ƙwarai. Sarki yace da su, "Ku tsaya a Yeriko sai gemunanku sun fito, sa'an nan ku dawo."
6Da Ammoniyawa suka ga sun maida kansu abin ƙyama ga Dauda, Hanun da Ammoniyawa suka aika da dubban awon azurfa domin su gaiyato karusan Arameyawa da mahaya dawaki daga Nahariyam da Ma'aka da Zoba.7Su ka gaiyato karusai dubu talatin da biyu tare da sarkin Ma'aka da mutanensa, waɗanda suka zo suka yi zango kusa da Medeba. Ammoniyawa suka tattaro daga biranensu, suka fito domin a yi yaƙi.
8Da Dauda ya ji haka, sai ya aiki Yowab tare da dukkan sojojinsa su je su same su.9Mutanen Ammon su ka fito suka ja layi a ƙofar birni domin yaƙi, su kuma sarakunan da suka zo suka zauna cikin fili su kaɗai.
10Lokacin da Yowab ya ga layin yaƙi na fuskantar sa gaba da baya, daga cikin mutanen Isra'ila ya zaɓi waɗansu gwanayen yaƙi ya shirya su, domin su kara da Arameyawa.11Sauran sojojin kuma ya ba da su ga Abishai ɗan'uwansa, domin ya sa su kara da sojojin Ammon.
12Yowab yace, "Idan Arameyawa suka fi ƙarfi na, to kai Abishai, sai ka kuɓutar da ni. Amma idan sojojin Ammoniyawa suka fi ƙarfin ka to, ni zan zo in kuɓutar da kai.13Ka ƙarfafa, bari mu yi ƙarfin hali saboda mutanenmu kuma saboda biranen Allahnmu, gama Yahweh zai yi abin da ya gamshe shi."
14Sai Yowab da sojojinsa suka nausa domin su yi yaƙi da sojojin Arameyawa, waɗanda aka tilasta wa su gudu a gaban sojojin Isra'ila.15Sa'ad da sojojin Ammon suka ga Arameyawa sun gudu, suma sai suka gudu daga wurin Abishai ɗan'uwan Yowab suka koma cikin birni. Daga nan Yowab ya koma daga wurin mutanen Ammon ya kuma koma Yerusalem.
16Lokacin da Arameyawa suka ga Isra'ilawa sun yi nasara a kansu, sai suka nemi taimako daga ƙetaren Kogin Yuferatis, tare da Shofak shugaban sojojin Hadadeza.17Sa'ad da Dauda ya ji haka, sai ya tattara dukkan Isra'ila, suka haye Yodan, suka je wurin su. Ya shirya sojoji domin su yi yaƙi da Arameyawa, suka kuwa yi faɗa da shi.
18Arameyawa suka gudu daga gaban Isra'ila, Dauda kuwa ya kashe sojojin karusan Arameyawa dubu bakwai da sojojin ƙasa dubu arba'in. Ya kuma kashe Shofak shugaban sojojin.19Da dukkan sarakuna, wato bayin Hadadeza suka ga Isra'ila sun ci nasara a kan su, suka nemi salama da Dauda suka bauta masa. Sai ya zama mutanen Aram ba su ƙara marmarin su taimaka wa Amoniyawa ba.

20

1Da lokaci ya yi sa'ad da sarakuna su kan tafi yaƙi, sai Yowab ya jagoranci sojoji suka je suka ragargaza ƙasar Amoniyawa. Ya ja daga a Rabba. Dauda kuma na Yerusalem. Yowab ya kai wa Rabba hari, ya yi nasara a kanta.

2Dauda ya ɗauke rawanin sarkinsu daga kansa, sai ya tarar ya kai nauyin awo ɗaya na zinariya, kuma da duwatsu masu daraja a cikin sa. A ka ɗora rawanin a kan Dauda, kuma ya kawo ganima mai yawa daga birnin.3Ya fito da mutanen daga cikin birni ya tilasa su yi aiki da zartuna da ƙarafa masu tsini na aiki da gatura. Dauda ya sa dukkan mutanen da ke cikin biranen Ammon su yi wannan aikin. Daga nan Dauda da dukkan sojojin suka dawo Yerusalem.
4Bayan wannan sai ya zama yaƙi ya ɓarke a Gezer da Filistiyawa. Sibbekai Bahushate ya kashe Siffai, wani daga cikin kabilar Refiyam, daga nan sai a ka ladabtar da Filistiyawa.5Sai ya zama a wani yaƙi kuma da Filistiyawa a Gob, Elhanan ɗan Ya'ir mutumin Betlehem ya kashe Lahmi ɗan'uwan Goliya mutumin Gat, wanda makamin mãshinsa ya yi kamar turken masaƙa.
6A wani yaƙin kuma a Gat, a ka sami wani mutum mai tsawo ƙwarai, wanda ya ke da yatsu shida a kowanne hannunsa da kuma yatsu shida a kowacce ƙafarsa. shi ma daga Refiyam ya ke.7Da ya yi wa sojojin Isra'ila ba'a, Yehonadab ɗan Shemiya ɗan'uwan Dauda ya kashe shi.8Waɗannan zuriyar Refiyam na Gat ne, suka kashe su da hannuwan Dauda da sojojinsa.

21

1Wani magafcin Isra'ila ya taso ya iza Dauda ya ƙidaya mutanen Isra'ila.2Sai Dauda yace da Yowab da manyan sojoji, "Ku je ku ƙidaya mutanen Isra'ila tun daga Biyasheba har zuwa Dan, ku kawo mani rahoto, domin in san yawansu."3Sai Yowab ya ce, "Dama Yahweh ya sa sojojinsa su fi haka yawa sau ɗari. Amma shugabana sarki, dukkan su ba bauta maka su ke yi ba? Me ya sa shugabana ya ke so a yi haka? Yaya za a kawo laifi a Isra'ila?"

4Amma maganar sarki ta rinjayi Yowab. To, sai Yowab ya fita ya zagaya dukkan Isra'ila. Daga nan ya dawo Yerusalem.5Yowab ya kawo wa Dauda rahoton yawan sojoji. A Isra'ila masu zarar takobi su ne 1,100,000. A Yahuda kaɗai akwai sojoji 470,000.
6Amma ba a ƙidaya Benyamin da Lebi tare da su ba, saboda Yowab bai ji daɗin maganar da sarki ya yi ba.7Yahweh bai ji daɗin wannan aikin ba, saboda haka sai ya buga Isra'ila.8Dauda ya ce da Yahweh, "Na yi zunubi mai girma da na yi haka. Yanzu, ka ɗauke zunubin bawanka gama na yi wauta ƙwarai."
9Yahweh yace da Gad, annabin Dauda,10"Je ka ka ce da Dauda, 'Ga abin da Yahweh yace, ina ba ka zaɓi guda uku, sai ka zaɓi ɗaya daga cikin su."
11Sai Gad ya je wurin Dauda ya ce da shi, "Ga abin da Yahweh ya ce, 'Ka zaɓi ɗaya cikin waɗannan:12yunwa ta shekaru uku ko wata uku na ƙanƙanci a hannun abokan gãbarka ko kuwa Yahweh ya bi ka da takobinsa har kwana uku, wato annoba ta afko cikin ƙasar, mala'ikan Yahweh ya bi ko'ina cikin ƙasar Isra'ila yana ta hallaka mutane.' To yanzu, sai ka yi tunani ka ba ni amsar da zan kai wa wanda ya aiko ni."
13Sai Dauda yace da Gad, "Ina cikin babbar damuwa! Gara in faɗa cikin hannun Yahweh da in faɗa cikin hannun mutum, gama jinƙansa yana da yawa ƙwarai."14Sai Yahweh ya aiko da annoba a ƙasar Isra'ila, har mutum dubu saba'in suka mutu.15Sa'an nan Yahweh ya aiko mala'ika ya hallaka Yerusalem. Yana kusa da ya hallaka ta, sai Yahweh ya canza niyyarsa. Ya ce da mala'ikan mai hallakarwa, "Ya isa! Ka mayar da hannunka."A wannan lokacin, mala'ikan Yahweh yana tsaye masussukar Ornan Bayebushe.
16Dauda ya tada ido, ya ga mala'kan Yahweh yana tsaye tsakanin sama da ƙasa, da takobi a zare cikin hannunsa ya ɗaga shi a kan Yerusalem. Sai Dauda ya ce da dattawa, ku sa tufafin makoki, ku kwanta da fuskokinku a ƙasa.17Dauda ya ce da Yahweh, "Ba ni ne na ba da umarnin a ƙidaya sojoji ba? Ni ne na yi wannan aikin mugunta, amma waɗannan tumaki, me suka yi? Yahweh Allahna! Ka sa hannunka ka buga ni, ni da iyalina, amma kada ka bari annobar ta zauna a kan mutanenka."
18Sai mala'ikan Yahweh ya umurci Gad ya ce da Dauda, Dauda ya je ya ginawa Yahweh bagadi a masussukar Ornan Bayebushe.19Sai Dauda ya tafi ya yi kamar yadda Gad ya dokace shi a cikin sunan Yahweh.20Lokacin da Ornan ke sussukar alkama, sai ya juya ya ga mala'ikan. Sai shi da 'ya'yansa su huɗu, suka ɓoye kansu.
21Lokacin da Dauda ya zo wurin Ornan, sai Ornan ya duba ya ga Dauda. Sai ya bar wurin sussukar ya faɗi da fuskarsa a ƙasa a gaban Dauda.22Sa'an nan Dauda ya ce da Onan, "Ka sayar mani da wannan masussuka domin in gina wa Yahweh bagadi. Zan biya gaba ɗaya domin a cire annobar daga cikin jama'a."
23Ornan ya ce da Dauda, "Ka ɗauke ta kamar taka ce, ya shugabana sarki. Ka yi abin da ka ga dama da ita. Duba, zan ba ka bijimaina domin hadaya ta ƙonawa, sandunan fyaɗi kuma ka yi makamashi da su, alkama kuma domin hadaya ta tsaba, zan ba ka su dukka."24Sarki Dauda yace da Ornan, "A'a gara dai in saya in biya. Ba zan ɗauki kayanka in yi hadaya ta ƙonawa ga Yahweh ba, ba tare da ya shafe ni da komi ba."
25Sai Dauda ya sayi wurin a bakin zinariya awo ɗari shida.26Sai Dauda ya gina wa Yahweh bagadi a wurin, ya miƙa baye-baye na ƙonawa da baye-baye na zumunta. Ya yi kira ga Yahweh, ya kuwa amsa masa da wuta daga sama a kan baye-baye na ƙonawar.27Sa'an nan Yahweh ya umurci mala'ikan, mala'ikan kuma ya mayar da takobinsa cikin kubenta.
28Da Dauda ya ga Yahweh ya amsa masa a masussukar Ornan Bayebushe, sai ya yi hadayar a wurin nan take.29A wannan lokaci wurin taruwa na Yahweh wanda Musa ya yi a cikin Jeji da bagadi domin baye-baye na ƙonawa suna can kan tudun Gibiyon.30Duk da haka, Dauda ba zai iya zuwa can domin ya nemi nufin Yahweh ba, saboda yana jin tsoron takobin mala'kan Yahweh.

22

1Sai Dauda yace, "A nan gidan Yahweh Allah zai kasance, tare da bagadin ƙona baye-baye na Isra'ila."2Sai Dauda ya umurci bayinsa su tattaro baƙin da ke zaune a ƙasar Isra'ila. Ya sa su zama masu sassaƙo duwatsu, su sassaƙo tubulan duwatsu waɗanda za a gina gidan Yahweh da su.

3Dauda kuma ya ba da ƙarafa masu tarin yawa domin a yi ƙusoshi saboda ƙofofi da ƙyamarensu da tagulla. Ya kuma ba da tagulla mai yawan da ba za a iya aunawa ba,4da itacen sida fiye da yadda za a iya ƙirgawa. (Sidoniyawa da mutanen Taya suka kawo wa Dauda gumaguman sida da yawa domin ya ƙidaya.)5Dauda ya ce ɗana Suleman yaro ne, bai ƙware ba tukuna, kuma gidan da za a gina wa Yahweh dole ne ya zama mai daraja sosai, domin ya zama da daraja ya yi suna a dukkan ƙasashe. Saboda haka zan yi shiri domin gininsa." Saboda haka, Dauda ya yi gagarimin shiri kafin mutuwarsa.
6Sai ya kira Suleman ɗansa ya umurce shi ya gina gida saboda Yahweh, Allah na Isra'ila.7Dauda yace da Suleman, "Ɗana, na yi niyya ni da kaina in gina gida saboda sunan Yahweh, Allahna.8Amma Yahweh ya zo wuri na ya ce, 'Ka yi yaƙe-yaƙe da yawa ka zubar da jini. Ba za ka gina gida domin sunana ba, domin ka zubar da jini da yawa bisa ƙasa a idanuna.
9Duk da haka, za ka sami ɗa wanda zai zama mutum mai salama. Zan ba shi hutawa daga dukkan maƙiyansa a kowanne sashi. Sunansa zai zama Suleman, kuma zan ba da salama da kwanciyar rai ga Isra'ila a kwanakinsa.10Shi ne zai gina mani gida, zai zama ɗa a gare ni, ni kuma zan zama mahaifinsa. Zan tabbatar da kursiyin mulkinsa bisa Isra'ila har abada.'
11To yanzu, ɗana, Yahweh ya kasance tare da kai ya ba ka nasara. Za ka ginawa Yahweh Allahnka gida kamar yadda ya ce.12Bari Yahweh ya ba ka fahimi da hangen gaba, domin ka yi biyayya da dokar Yahweh Allahnka, sa'ad da ya ɗora ka bisa shugabancin Isra'ila.13Za ka yi nasara idan ka lura ka yi biyayya da farillai da dokokin da Yahweh ya ba Musa game da Isra'ila. Ka ƙarfafa, ka yi ƙarfin zuciya, kada ka karaya.
14Yanzu ka duba, na yi baban ƙoƙari, na yi tanaji domin gidan Yahweh, zinariya awo 100,000, azurfa awo milyan ɗaya, da tagulla da ƙarafa masu tarin yawa. Na kuma tanaji katako da dutse. Na sani dole sai ka ƙara a kan su.
15Kana da ma'aikata da yawa: masu sassaƙar dutse da magina da kafintoci da ƙwararru ga aikin hannu da yawa a kowanne fanni,16waɗanda za su iya yin aiki da zinariya da azurfa da tagulla da ƙarafa. Sai ka fara aiki, Yahweh ya kasance tare da kai."
17Dauda kuma ya dokaci dukkan dattawan Isra'ila su taimaki ɗansa Suleman, da cewa,18"Yahweh Allahku yana tare da ku, kuma ya ba ku salama a kowanne sashi, ya ba da mazauna yankin cikin hannuna. An ladabtar da yankin a gaban Yahweh da mutanensa.19Sai ku nemi Yahweh Allah da dukkan zuciyarku da ranku. Sai ku tashi tsaye ku gina wuri mai tsarki na Yahweh Allah. Sa'an nan ne za ku iya kawo akwatin alƙawari na Yahweh tare da abubuwan da ke na Yahweh a cikin gidan da a ka gina domin sunan Yahweh."

23

1Sa'ad da Dauda ya tsufa, yana kusa da ƙarshen rayuwarsa, sai ya naɗa ɗansa Suleman ya zama sarkin Isra'ila.2Ya tattara dukkan shugabannin Isra'ila, tare da firistoci da Lebiyawa.3Lebiyawa kuwa masu shekaru talatin da ma sama da haka, aka kidaya su, sun kai jimillar dubu talatin da takwas.

4'"Dubu ashirin da huɗu daga cikin su za su yi hidimar gidan Yahweh, sai kuma dubu shida za su zama ma'aikata da alƙalai.5Dubu huɗu kuwa za su zama matsara ƙofofi da dubu huɗu kuma za su zama masu yabon Yahweh da kayayyakin bushe-bushe da kaɗe-kaɗe waɗanda za su yi yabo," Dauda ya ce.6Ya raba su kashi kashi bisa ga 'ya'yan Lebi: Geshon, da Kohat da Merari.
7Daga zuriyar kabilar Geshon, akwai Ladan da Shimei.8Akwai 'ya'ya maza uku na Ladan: su ne Yehiyel shi ne shugaba da Zetam da Yowel.9Akwai 'ya'ya uku maza na Shimei, su ne Shelomit da Heziyel da Haran. Waɗannan su ne shugabannin kabilar Ladan.
10Akwai 'ya'ya huɗu maza na Shimei, su ne Yahat, Ziza, Yewush da Beriya.11Yahat shi ne babba, Ziza shi ne na biyu, amma Yewush da Beriya ba su da 'ya'ya maza da yawa, saboda haka sai aka ɗauke su a matsayin kabila ɗaya tare da yin ayyuka iri ɗaya.
12Akwai 'ya'ya maza huɗu na Kohat su ne Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel.13Waɗannan 'ya'ya maza na Amram su ne Haruna da Musa. Haruna aka zaɓa aka kuma ƙeɓe shi domin ya tsarkake abubuwa mafi tsarki, shi da kabilarsa su riƙa ƙona turare a gaban Yahweh, su yi masa hidima, su riƙa sa albarka da sunansa har abada.14Amma Musa mutumin Allah, da 'ya'yansa maza aka ɗauke su a matsayin Lebiyawa.
15'Ya'yan Musa maza kuwa su ne Geshon da Eliyeza.16A zuriyar Geshon Shebayel ne babban ɗansa.17Zuriyar Eliyeza Rehabiya ne ɗansa. Eliyeza ba shi da 'ya'ya maza, amma Rehabiya na da zuriya mai yawa.18Ɗan Izhar shi ne Shelomit na shugaba.
19Zuriyar Hebron su ne Yeriya, babbansu, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da kuma Yekameyam na huɗu.20'Ya'yan Uzziyel maza kuwa su ne Mika ne babban da Ishija na biyu.
21'Ya'yan Merari maza su ne Mali da Mushi. 'Ya'yan Mali maza su ne Eliyeza da Kish.22Eliyeza kuwa ya rasu ba shi da ko 'ya'ya maza. Yana da 'ya'ya mata ne kaɗai.23'Ya'ya maza na Kish ne suka aure su. 'Ya'yan Mushi uku maza su ne Mali, Eder da Yerimot.
24Waɗannan su ne zuriyoyin Lebiyawa bisa ga dangoginsu. Su ne shugabannin, da aka lasafta aka jera su bisa ga sunaye, su ne dangogin da suka yi hidimar aiki a cikin gidan Yahweh, daga shekaru ashirin zuwa gaba.25Gama Dauda ya ce, '"Yahweh, Allah na Isra'ila, ya ba da hutu ga sauran mutanensa. Ya mai da gidansa a Yerusalem har abada.26Lebiyawa ba sauran bukatar ɗauka rumfar sujada tare da kayayyakin yin aiki a cikinta."
27Gama bisa ga maganar Dauda ta ƙarshe aka kiɗaya Lebiyawa, daga mai shekaru ashirin zuwa gaba.28Aikinsu kuwa shi ne su taimaki zuriyar Haruna gudanar da aiki cikin gidan Yahweh. Su kula da farfajiyoyi da ɗakuna, da tsabtace tsarkakan dukkan abubuwa da su ke na Yahweh, da sauran ayyuka a cikin gidan Allah.29Za su kuma ɗauki nauyin kula da wajen gurasar ajiyewa da lallausan gari na baiko na gari, da waina marar gami da soyayyun baye-baye, baye-bayen da ka gauraya da mai, da dukkan ma'aunan nauyi da girma abubuwa.
30Suna kuma tsaye a kowacce safiya don su yi godiya da yabon Yahweh. Suna riƙa yin wannan da maraice31da duk lokacin baikon ƙonawa suna miƙa wa Yahweh, a ranakun Asabaci da lokacin tsayuwar sabon wata da bikin ƙayyadaddun idodi. Akwai adadin lambar da za a sa bisa ga ka'ida, kullum za su bayyana a gaban Yahweh.
32Su ne za su riƙa lura da rumfar taruwa, da wuri mai tsarki, za su kuma taimaki abokansu, zuriyar Haruna hidima cikin gidan Yahweh.

24

1Ga yadda aka raba aiki bisa ga zuriyar Haruna su ne: Nadab, Abihu, Eliyeza da kuma Itama.2Nadab da Abihu sun riga mahaifinsu mutuwa. Ba su da 'ya'ya, saboda haka Eliyeza da Itama suka shiga aikin firistoci.3Dauda, tare da Zadok, zuriyar Eliyeza da Ahimelek, da zuriyar Itama, sun karkasa su bisa ga ayyukansu na matsayin firistoci.

4Akwai manyan mutane da yawa a zuriyar Eliyeza fiye da zuriyar Itama, sai suka karkasa zuriyar Eliyeza zuwa kashi goma sha shida. Sun yi wannan bisa ga shugaban dangogi da kuma bisa ga zuriyar Itamar. Waɗannan rabe rabe guda takwas ne adadinsu, bisa ga dangoginsu.5Suka karkasa su ta hanyar ƙuri'a, domin akwai ma'aikatan wuri mai tsarki da kuma ma'aikata na Allah daga zuriyar Eliyeza da kuma zuriyar Itama.
6Shemaiya ɗan Netanel marubuci, Balabe, ya rubuta sunayensu a gaban sarki da ma'aikata, Zadok firist, da Ahimelek ɗan Abiyata, da shugabannin firistoci da iyalan Lebiyawa. An sami dangi ɗaya ta wurin ƙuri'a daga zuriyar Eliyeza, an sake samun ɗaya daga zuriyar Itama.
7‌Ƙuri'a ta farko ta je ga Yehoyarib, ta biyu ga Yedayiya,8ta uku ga Harim, ta huɗu ga Seyorim,9ta biyar ga Malkija, ta shida ga Mijamin,10ta bakwai ga Hakkoz, ta takwas ga Abija,
11Na tara Yeshuwa, ta goma ga Shekaniya,12ta goma sha ɗaya ga Eliyashib, ta goma sha biyu ga Yakim,13ta goma sha uku ga Huffa, ta goma sha huɗu ga Yeshebeyab,14Ta goma sha biyar ga Bilga, ta goma sha shida ga Immer,
15Ta goma sha bakwai ga Hezir, ta goma sha takwas ga Haffizzez,16ta goma sha tara ga Fetahiya, ta ashirin ga Yehezkel,17ta ashirin da ɗaya ga Yakin, ta ashirin da biyu ga Gamul,18ta ashirin da uku ga Delaiya, da kuma ta ashirin da huɗu ga Ma'aziya.
19Wannan shi ne tsarin aikinsu, idan sun zo hidima cikin gidan Yahweh, bisa ga ka'idar da kakansu Haruna ya ba su, kamar yadda Yahweh, Allah na Isra'ila ya umarce shi.
20Waɗannan su ne sauran Lebiyawa, 'ya'ya maza na wajen Amram, shi ne Shubawel; 'Ya'ya maza na Shubawel da Yedaiya.21'Ya'ya maza na Rehabiya shi ne Ishija shugaba.22Na wajen Izharawa: shi ne Shelomit; na wajen Shelomit: shi ne Yahat.
23'Ya'ya maza na wajen Hebron Yeriya ne shugaba, Amariya na biyu, da Yahaziyel na uku, da Yekameyam na huɗu.24'Ya'ya maza zuriyar Uzziyel ya haɗa da Mika. Zuriyar Mika ta haɗa da Shamir.25Ɗan'uwan Mika shi ne Ishija. 'Ya'ya maza ya haɗa da Zekariya.
26'Ya'ya maza na Merari su ne Mali da Mushi. Ɗan Yaaziya shi ne Beno.27'Ya'ya maza na Merari su ne Yaaziya: Beno, Shoham, Zakkur da Ibri.28'Ya'ya maza na Mali su ne Eliyeza, wanda ba shi da 'ya'ya maza.
29'Ya'ya maza na Kish, ɗan Kish, shi ne Yerameyel.30'Ya'ya maza na Mushi su ne Mali, Eder da Yerimot. Waɗannan su ne Lebiyawa bisa ga iyalansu.31Waɗannan mutane su ne ke shugabatar kowanne gidan uba da kowane ɗan 'yan'uwansu, aka jefa ƙuri'a a gaban sarki Dauda da Zadok da kuma Ahimelek, tare da shugabanni na kowanne iyalan firistoci da Lebiyawa. Suka jefa ƙuri'a kamar yadda zuriyar Haruna suka yi.

25

1Dauda da shugabannin Lebiyawa sun zaɓi waɗansu don aiki suna cikin 'ya'yan Asaf maza da na Heman da na Yedutun. Waɗannan mutane za su yi annabci da waɗannan kayayyakin bushe bushe irin su garayu da molaye da kuge. A nan ga adadin mutanen da suka yi wannan aikin:2Daga 'ya'yan Asaf maza, su ne Zakkur, Yosef, Netaniya da Asharela, Asaf mahaifinsu ne ya ke bi da su, shi ne kuma wanda ya ke waƙa a ƙarƙashin sarki.3Daga 'ya'yan Yedutun maza su ne Gedaliya, Zeri da Yeshayiya, Shimei, Hashabiya da Mattitiya, dukka su shida ne, mahaifinsu Yedutun ne ke kula da su, shi ne kuma mai raira waƙoƙi da garaya don godiya da yabon Yahweh.

4Daga 'ya'yan Heman maza kuwa akwai Bukkiya, Mattaniya, Uzziyel, Shebuwel, Yerimot, Hananiya, Hanani, Eliyata, Giddalti, Romamti-Ezer, Yoshbekasha, Malloti, Hotir da kuma Mahaziyot.5Dukkan waɗannan 'ya'ya maza ne na Heman annabin sarki. Allah ya ba Heman 'ya'ya maza goma sha huɗu da kuma 'ya'ya mata uku don ya girmama shi.
6Dukkan waɗannan suna ƙarƙashin mahaifinsu. Su mawaƙan gidan Yahweh ne, tare da kaɗa kuge da molaye da garayu kamar yadda suke aiki cikin gidan Allah. Asaf da Yedutun da Heman suna ƙarƙashin umarnin sarki.7Su da 'yan'uwansu maza horarru ne sun kuma ƙware da mawaƙa ga Yahweh jimillarsu kuwa ita ce 288.8Suka jefa ƙuri'u don ayyukansu, dukka suna kama da juna, haka ma ya ke ga yaro da babba da malami da ɗalibi.
9Yanzu game da 'ya'yan Asaf maza; ƙuri'a ta farko ta faɗa a kan iyalin Yosef; ta biyu ga iyalin Gedaliya, jimilla mutane goma sha biyu ne;10ta uku ta faɗa a kan Zakkur, da 'ya'yansa da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne,11ta hudu ta faɗa ga Izri, 'ya'yansa da danginsa jimilla mutane goma sha biyu ne;12ta biyar ta faɗa ga Netaniya, 'ya'yansa maza da danginsa jimilla mutane goma sha biyu ne;
13ta shida ta faɗa ga Bukkiya, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;14ta bakwai ta faɗa ga Yesarela, 'ya'yansa maza da danginsa jimilla mutane goma sha biyu na;15ta takwas ta faɗa ga Yeshayiya, 'ya'yansa dandinsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;16ta tara ta faɗa ga Mattaniya, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;
17ta goma ta fada ga Shimei, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;18ta goma sha ɗaya ta faɗa ga Azarel, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;19ta goma sha biyu ta faɗa ga Hashabiya, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;20ta goma sha uku ta faɗa ga Shubayel, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;
21ta goma sha hudu ta faɗa ga Mattitiya, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;22ta goma sha biyar ta faɗa ga Yerimot, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;23ta goma sha shida ta faɗa ga Hananiya, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;24ta goma sha bakwai ta faɗa ga Yoshbekasha, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;
25ta goma sha takwas ta faɗa ga Hanani, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;26ta goma sha tara ta faɗa ga Malloti, 'ya'yansa da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;27ta ashirin ta faɗa ga Eliyata, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;28ta ashirin da ɗaya ta faɗa ga Hotir, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;
29ta ashirin da biyu ta faɗa ga Giddalti, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;30ta ashirin da uku ta faɗa ga Mahaziyot, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;31sai ta ashirin da huɗu ta faɗa ga Romamti-Ezer, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne.

26

1A nan ga yadda aka raba masu tsaron ƙofofi: Daga Koratawa, Meshelemiah ɗan Kore ne, zuriyar Asaf.2Meshelemiya yana da 'ya'ya maza: Zekariya ne ɗan fari, Yediyayel ne na biyu, Zebadiya na uku, Yatniyel na huɗu,3Elam na biyar, Yehohanan na shida, Eliyehoyenai ne ɗa na bakwai.

4Obed Idom da 'ya'ya maza su ne, na fari shi ne Shemaiya, na biyu Yehozabad, na uku Yowa, na huɗu Sakar, na biyar Netanel, shida5Ammiyel, na bakwai Issaka, na takwas Fiyuletai, gama Allah ya sa wa Obed Idom albarka.6Shemaiya shi ne ɗan farin Obed Idom ya haifi 'ya'ya maza waɗanda suka yi shugabancin iyalansu; su jarumawan mutane ne.
7'Ya'yan Shemaiya maza su ne Otni, Refayel, Obed, Elzabad. Danginsa Elihu da Shemakiya suma jaruman mutane ne.8Dukkan waɗannan kabilun Obed Idom. Su da 'ya'yansu maza da dangoginsu jarumai ne masu ƙarfi da gwaninta na yin hidima. Akwai mutane sittin da biyu da suke da dangantaka da Obed Idom.9Meshelemiya yana da 'ya'ya maza da 'yan'uwa, mutane ne masu ƙarfi da gwaninta, su dukka goma sha takwas ne.
10Hosa, yana cikin zuriyar Merari, yana da 'ya'ya maza, Shimri shugaba (ko da ya ke ba shi ne ɗan fari ba, duk da haka maihaifinsa ya maishe shugaba).11Hilkiya shi ne na biyu, da Tabaliya na uku da Zekariya na huɗu. Dukkan 'ya'yan Hosa maza da 'yan'uwansa su goma sha uku ne.
12Waɗannan su ne rabe rabe na masu tsaron ƙofa, bisa ga shugabanninsu, da ayyuka, kamar iyalansu, da za su yi hidima a gidan Yahweh.13Sai suka jefa kuri'a yaro da babba bisa ga iyalansu, don kowacce ƙofa.14Sai ƙuri'ar ƙofar gabas, ta faɗo a kan Shelemiya. Suka kuma jefa ƙuri'a don ɗansa Zekariya, mai ba da shawara mai ma'ana, sai ƙuri'arsa ta fito don ƙofar arewa.
15An sa Obed Idom ƙofar kudu, an kuma sa 'ya'yansa maza lura da ɗakunan ajiya.16Shuffin da Hosa an sa su a ƙofa ta yamma tare da Shalleket, a kan hanyar da ta haura. Aka tabbatar da masu tsaron kowanne iyali.
17A gefen gabas akwai Lebiyawa shida, a gefen arewa a rana ta huɗu, a gefen kudu a rana ta huɗu, an kuma sa biyu biyu a ɗakunan ajiya.18A ɗakin shari'a da ke yamma akwai masu tsaro huɗu, a hanya guda huɗu, biyu kuma a ɗakin shari'a.19Yadda aka raba masu tsaron ƙofofin kenan. Suna cike da zuriyoyin Kora da Merari.
20A cikin Lebiyawa, Ahijah ne mai kula da ma'ajin gidan Allah, da ma'ajin abubuwa da ke na Yahweh.21Zuriyar Ladan, daga zuriyar Geshon ta wurinsa da waɗanda suke shugabannin iyalan Ladan Bageshone, su ne Yehiyeli,22da 'ya'yansa maza Zetam da Yowel ɗan'uwansa, su ne ke kula da ɗakunan ajiyar gidan Yahweh.
23Akwai kuma masu tsaro da aka ɗauko daga kabilar Amram, da Izhar da Hebron da kuma Uzziyel.24Shubayel ɗan Geshom ɗan Musa, shi ne babban jami'in ɗakunan ajiya.25Danginsa daga kabilar Eliyeza su ne ɗansa Rehabiya, Yeshayiya ɗan Rehabiya, Yoram ɗan Yeshabiya, Zikri ɗan Yoram, da kuma Shelomit ɗan Zikri.
26Shelomit da 'yan'uwansa ne ke lura da dukkan gidajen ajiya da abubuwan da ke na Yahweh, wanda Dauda sarki, da iyalin shugabanni, da shugabannin sojoji na dubu dubu na ɗari ɗari da kuma shugabannin sojojin da aka keɓe.27Su ne kuma aka keɓe don kula da ganimar yaƙe-yaƙe domin kuma gyaran gidan Yahweh.28Su ne kuma masu lura da kowane irin abubuwa da aka keɓe ga Yahweh ta wurin annabi Sama'ila, da Saul ɗan Kish da Abner ɗan Ner da Yowab ɗan Zeruyiya. Kowanne abu da aka keɓe ga Yahweh yana ƙarƙashin kulawar Shelomit da 'yan'uwansa.
29Zuriyar Izhar da Kenaniya tare da 'ya'yansa maza su ne aka danƙa wa al'amuran sasantawa na Isra'ila. Su ne shugabanni da alƙalai.30Zuriyar Hebron da Hashabiya haɗe da 'yan'uwansa, 1700 gwanayen mutane ne, su ne masu lura da ayyukan Yahweh da na sarki. Suna wajen yammacin Yodan.
31Daga zuriyar Hebron, Yeriya shi ne shugaban zuriyarsa, bisa ga asalin iyalansu. A shekara ta arba'in ta sarautar Dauda sun bincika, aka tarar akwai ƙarfafan mutane, jarumawa a Yazer ta Giliyad.32Yeriya yana da 'yan'uwa har 2,700, waɗanda suke gwanaye shugabannin iyali. Dauda ya maida su masu lura da kabilar Ruben da ta Gad da kuma rabin kabilar Manasse, domin kowane abu da ke na Allah da kuma al'amuran sarki.

27

1Wannan shi ne lissafin iyalin shugabannin Isra'ila, shugabannin sojoji na dubu dubu da ɗari ɗari, har da rudunar sojoji waɗanda suke yi wa sarki aiki ta hanyoyi dabam dabam. Kowace runduna za ta yi aiki wata wata har ƙarshen shekara. Kowanne kashi na da mutane dubu ashirin da huɗu.2A kowane kashi a wata na farko, shi ne na Yashobeyam ɗan Zabdiyel. A cikin kashinsa akwai mutane dubu ashirin da huɗu.3Yana cikin zuriyar Pezer, shi ne kuma mai lura da dukkan shugabannin sojoji a watan farko.

4Bisa ga kashi wata na biyu shi ne Dodai, daga kabilar zuriya daga Ahoya. Miklot shi ne na biyu a jerin. A cikin rabonsa akwai mutane dubu ashirin da huɗu.5Shugaban ruduna a wata na uku shi ne Benaiya ɗan Yehoiada, firist ne kuma shugaba. A cikin rabonsa akwai mutane dubu ashirin da huɗu.6Wannan shi ne Benaiya wanda shi ne shugaba a cikin talatin, da kuma bisa ga talatin. Ammizabad ɗansa mana cikin rabonsa.
7Shugaban sojoji a wata na huɗu shi ne ɗan'uwan Asahel Yowab. Ɗansa Zebadiya ya zama shugaba a madadinsa. A cikin rabonsa akwai mutane dubu ashirin da huɗu.8Shugaba na watan biyar shi ne Shamhut, a zuriyar Izra. A cikin rabonsa akwai mutane dubu ashirin da huɗu.9Shugaba na watan shida shi ne Ira ɗansa Ikesh, daga Tekowa. A cikin rabonsa akwai mutane dubu ashirin da huɗu.
10Shugaba na watan bakwai shi ne Helez Bafelone, daga mutanen Ifraim. Rabonsa mutane dubu ashirin da huɗu ne.11Shugaba na watan takwas shi ne Sibbekai Bahushate, daga kabilar zuriya daga Zera. Rabonsa mutane dubu ashirin da huɗu ne.12Shugaba na watan tara shi ne Abiyeza Ba'anatot, daga kabilar Benyamin. Rabonsa mutane dubu ashirin da huɗu ne.
13Shugaba na watan goma shi ne Maharai daga birnin Netofa, daga dangin zuriya daga Zera. Rabonsa mutane dubu ashirin da huɗu ne.14Shugaba na watan goma sha ɗaya shi ne Benaiya daga birnin Firaton, daga kabilar Ifraim. Rabonsa mutane dubu ashirin da huɗu ne.15Shugaba na watan goma sha biyu shi ne Heldai daga birnin Netofa, daga dangin zuriya daga Otniyel. Rabonsa mutane dubu ashirin da huɗu ne.
16Waɗannan su ne shugabannin kabilun Isra'ila: Ga kabilar Ruben, Eliyeza ɗan Zikri shi ne shugaba. Ga kabilar Simiyonn, Shefatiya ɗan Ma'aka shi ne shugaba.17Ga kabilar Lebi, Hashabiya ɗan Kemuwel shi ne shugaba, Zadok shi ne jagora na zuriyar Haruna.18Ga kabilar Yahuda, Elihu, ɗaya daga cikin 'yan'uwan Dauda, shi ne shugaba. Ga kabilar Issaka, Omri ɗan Mika'el shi ne shugaba.
19Ga kabilar Zebulun, Ishamaiya ɗan Obadiya shi ne shugaba. Ga kabilar Naftali, Yerimot ɗan Azriyel shi ne shugaba.20Ga kabilar Ifraim, Hosheya ɗan Azaziya shi ne shugaba. Ga rabin kabilar Manasse, Yowel ɗan Fedaiya shi ne shugaba.21Ga rabin kabilar Manasse a Gileyad, Iddo ɗan Zekariya shi ne shugaba. Ga kabilar Benyamin, Ya'asiyel ɗan Abner shi ne shugaba.22Ga kabilar Dan, Azarel ɗan Yeroham shi ne shugaba. Waɗannan su ne shugabannin kabìlun Isra'ila.
23Dauda bai ƙidaya waɗanda shekarunsu ba su kai ashirin ba ko kuma yara, gama Yahweh ya yi alƙawarin zai sa mutanen Isra'ila su yi yawa kamar taurarin sammai.24Yowab ɗan Zeruya ne ya fara ƙidayar mutanen nan, amma bai gama ba. Sai hukunci mai zafi ya sami Isra'ila saboda wannan. Wannan ƙidayar ba a rubuta ta ba cikin Tarihin Sarki Dauda ba.
25Azmabet ɗan Adiyel shi ne mai lura da ma'ajin sarki. Yonatan ɗan Uzziya shi ne mai kula da ɗakin ajiya a filaye da kuma cikin birane, har da ƙauyuka da kagaran hasumiyoyi.26Ezri ɗan Kelub shi ne mai lura da gonaki, da waɗanda suke huɗa a ƙasar.27Shimei Baramate shi ne mai kula da gonakin inabi da Zabdi Bashifime shi ne mai lura da itatuwan zaitun da inda ake ajiye kwalaben shaye-shaye.
28Ga itatuwan zaitun da na ɓaure waɗanda suke a kwari shi ne Ba'al-Hanan daga Geder, kuma ɗakin ajiyar man shi ne Yowash.29Bisa ga garken shanu a Sharon shi ne Shitrai, daga Sharon kuma bisa ga garken shanu da ke cikin kwari shi ne Shafat ɗan Adlai.
30Bisa ga rakuma shi ne Obil Ba'isma'ile, kuma bisa ga jakuna mata shi ne Yedaiya daga Meronot. Bisa ga tumaki shi ne Yaziz Bahagire.31Yazia Bahagire shi ne mai lura da garken. Dukkan waɗannan su ne masu lura da dukiyar sarki Dauda.
32Yonatan, kawun Dauda, shi ne mai ba da shawara, tun da shi mutum ne mai ganewa shi ne kuma magatakarda. Yehiyel ɗan Hakmoni shi ne mai kula da 'ya'yan sarki.33Ahitofel shi ne mai ba sarki shawara, Hushai daga mutanen Arkite su ne masu shawara na jikin sarki.34Ahitofel ɗan Benaiya an ba da makaminsa ga Yehoiada ɗan Benaiya ta wurin Abiyata. Yowab shi ne babban shugaban sojojin sarki.

28

1Dauda ya tara dukkan shugabannin Isra'ila a Yerusalem: shugabannin kabilu da shugabannin kungiyoyi da ke yi wa sarki hidima a cikin shirin aikinsa, shugabannin dubu dubu da ɗari ɗari da manajoji bisa dukkan dukiya da mallakar sarki da 'ya'yansa da kuma fãdawa da mutane mayaƙa, tare da waɗanda suka zama mafiya fasaha.

2Sai sarki Dauda ya mike tsaye ya ce, "Ku saurare ni, 'yan'uwana da jama'ata. Na yi niyya in gina haikalin akwatin alƙawari na Yahweh; wurin zaman zatin Allahnmu, na kuma riga na yi shirin ginin.3Amma Allah ya ce da ni, 'Ba za ka gina mani haikali da sunana ba, domin kai mutum ne mayaƙi, ka kuma zubar da jini.'
4Duk da haka Yahweh, Allah na Isra'ila, ya zaɓe ni daga dukkan iyalin mahaifina, in zama sarkin Isra'ila har abada. Shi ne ya zaɓi kabilar Yahuda da kuma gidan mahaifina, daga cikin dukkan 'ya'ya maza na mahaifina, shi ne ya zaɓe ni in zama sarkin Isra'ila.5Daga 'ya'ya maza da yawa Yahweh ya ba ni, ya zaɓe Suleman, ɗana, ya zauna a kan gãdon sarautar mulkin Yahweh, bisa Isra'ila.
6Ya ce da ni, 'Suleman ɗanka ne zai gina mani gida da farfajiyoyina, gama na zaɓe shi ya zama ɗa a gare ni, ni kuwa zan zama uba a gare shi.7Zan tabbatar da mulkinsa har abada, idan ya tsaya da gaske ya yi biyayya da dokokina da kuma ka'idodina.'
8Saboda haka yanzu, a gaban dukkan Isra'ila, wannan taron Yahweh, da kuma gaban Allahnmu, dukkan ku dole ku kiyaye kuma yi ƙoƙari ku bi dukkan umarnan Yahweh Allahnku. Ku yi wannan don ku mallaki wannan ƙasar mai kyau, ku zauna a cikin ta a matsayin gãdo ga 'ya'yanku a bayanku har abada.
9Amma kai, ɗana Suleman, ka yi biyayya da Allah na mahaifinka, ka bauta masa da dukkan zuciyarka da kuma yardar rai. Ka yi wannan gama Yahweh mai binciken dukkan zukata ne, ya kuma san kowanne irin nufi da tunanin kowanne mutum. Idan ka neme shi, zaka same shi, amma idan ka rabu da shi, shi ma zai yi watsi da kai har abada.10Ka lura da cewa Yahweh ya zaɓe ka domin ka gina wannan rumfa mai tsarki. Ka yi ƙarfi, ka kama yi aiki."
11Sa'an nan Dauda ya ba ɗansa Suleman tsarin ginshiƙan ƙofar haikalin, da gine-ginen haikali da ɗakunan ajiya da benaye da ɗakunan ciki da ɗakunan inda ake gafarta zunubi.12Ya ba shi tsarin da ya zãna domin farfajiyoyin gidan Yahweh, da dukkan kewayen ɗakunan, da ɗakunan ajiya na gidan Allah, da ma'ajiyai domin abubuwan da ke na Yahweh.
13Ya kuma ba shi ƙa'idodin domin rarraba firistoci da Lebiyawa, da dukkan hidimar da za a yi a gidan Yahweh, domin kowanne aiki na cikin gidan Yahweh.14Ya fayyace nauyin santulan zinariya domin kowanne irin aiki, nauyin santulan azurfa domin kowanne irin aiki.15Nauyin zinariya domin dukkan kayayyakin zinariya, sun haɗa da kowanne alkuki da fitilunsa da fitilar zinariya, nauyin ma'aunin kowacce fitila da maɗori, nauyin ma'aunin kowacce azurfa domin kowanne maɗorin fitila, bisa ga yadda za'a yi amfani da kowanne maɗorin fitila a cikin sujada.
16Ya ba da ma'aunin zinariya da za a yi teburorin gurasar ajiyewa don kowanne teburi, da kuma ma'aunin azurfa don teburorin azurfa.17Ya bada ma'aunin zinariya tsantsa wadda za a yi cokula masu yatsu domin nama da daruna da kofuna da kwanoni da da ma'auni na yawan azurfa da za a yi kwanoni da ita.
18Ya bada ma'aunin zinariya tsantsa wadda za a yi bagaden ƙona turare da ita, da kuma zinariya da za a yi tsarin kerubobin da za su miƙa fikafikansu su rufe akwatin alƙawarin Yahweh.19Dauda ya ce, "Na sa dukkan wannan a rubuce ne kamar yadda Yahweh ya umarce ni, ya kuma ba ni don in fahimci fasalin aikin filla-filla."
20Dauda ya ce da ɗansa Suleman, "Ka yi ƙarfi da jaruntaka. Ka yi aikin. Kada ka ji tsoro ko ka karai, gama Yahweh Allah, Allahna, na tare da kai. Ba zai bar ka ba ko ya ƙyale ka har sai ka gama dukkan aikin hidimar haikalin Yahweh.21Duba ga, karkasuwar firistoci da Lebiyawa na nan domin yin dukkan hidima a haikalin Allah. Za su kasance tare da kai, tare kuma da dukkan gwanayen mutanen da suka yarda su taimake ka a cikin aikin da yadda za a yi hidimar. Shugabanni da dukkan mutane na shirya su bi umarninka."

29

1Sarki Dauda yace da dukkan taron, "Ɗana Suleman, wanda shi kaɗai Allah ya zaɓa, sai dai saurayi ne, kuma ba shi da ƙwarewa, kuma aikin babba ne. Gama haikalin ba na mutum ba ne, amma na Yahweh Allah ne.2A halin yanzu dai na riga na yi iyakacin ƙoƙarina, har na tanada waɗannan abubuwa saboda haikalin Allahna. Na ba da zinariya saboda abubuwa na zinariya, azurfa saboda abubuwa na azurfa, tagulla saboda abubuwa na tagulla, ƙarfe saboda abubuwa na ƙarfe, itace kuwa saboda na itace. Na kuma ba da duwatsu da yawa masu daraja, da masu launi iri-iri -da kowaɗanne irin duwatsu masu daraja - da duwatsu a yalwace.

3Yanzu, saboda ƙaunar da na ke da ita ta gidan Allahna, shi ya sa na bada zinariyata da azurfata don wannan aiki. Ina ƙara yin wannan dukka don in shirya wannan haikali mai tsarki,4na bada zinariya tsantsa talanti dubu uku daga Ofir, azurfa tsantsa talanti dubu bakwai, domin yin ado a bangon ginin.5Na bada zinariya saboda abubuwa da abin da za ayi da zinariya, azurfa saboda abubuwan da za a yi na azurfa, da dukkan irin abubuwa da kafintoci za su yi. Wane ne kuma ya ke da niyyar bayarwa domin Yahweh yau, ya kuma ba da kansa gare shi?
6Sai aka yi bayarwar yardar rai bisa ga shugabannin iyalan kakanni da shugabannin kabilun Isra'ila da shugabannin dubbai da ɗaruruwa da kuma shugabannin da suke yi wa sarki aiki.7Suka bada saboda hidimar gidan Allah talanti dubu biyar da darik dubu goma na zinariya, da talanti dubu goma na azurfa da dubu goma sha takwas na tagulla da kuma talanti 100,000 na ƙarfe.
8Waɗanda suke da duwatsu masu daraja sun bada su cikin taskar gidan Yahweh, a ƙarƙashin kulawar Yehiyel, zuriyar Gashon.9Mutane suka yi murna domin waɗannan baye-baye na yardar rai, gama sun bayar da zuciya ɗaya ga Yahweh. Sarki Dauda kuma ya yi murna ƙwarai.
10Dauda ya albarkaci Yahweh a gaban dukkan taron, ya ce, "Yabo naka ne, Yahweh, Allah na kakanmu Isra'ila, har abada abadin.11Naka ne, Yahweh, girma da iko da daraja da nasara da ɗaukaka. Gama dukkan abin da ke cikin sammai da duniya naka ne. Naka ne mulki, Yahweh, kai ne maɗaukaki mai mulki a bisa komai.
12Dukkan wadata da ɗaukaka suna zuwa daga gare ka, kai ka ke mulki bisa dukkan mutane. A hannunka iko da ƙarfi su ke. Kai ne ka ke da ƙarfi da iko ka sa mutane su yi girma, ka kuma bada ƙarfi ga kowane mutum.13Yanzu, ya Allahnmu, muna gode maka muna kuma yabon sunanka mai daraja.
14Amma wãne ni, ko kuma mutanena da za mu iya kawo waɗannan abubuwa da yardar rai? Gama dukkan abubuwan nan sun zo daga gare ka ne, mu kuma muka ba ka abin da ke naka.15Gama mu bãƙi ne, matafiya kuma a gabanka, kamar kakanninmu. Kwanakinmu a duniya kamar inuwa ne, ba mu da begen dauwama a duniya.
16Yahweh Allahnmu, dukkan wannan dukiya da muka tattara domin mu gina haikali saboda ɗaukakar sunanka mai tsarki - sun zo daga gare ka ne kuma naka ne. Na kuma sani, ya Allahna, ka kan gwada zuciya, kana jin daɗin abin da ke nagari.17Amma ni, bisa ga amincewar zuciyata, da yardar rai, na miƙa maka dukkan waɗannan abubuwa, yanzu ina dubawa da murna ganin mutanenka waɗanda suke nan da yardar su suka kawo maka kyautai.
18Yahweh, Allah na Ibrahim da Ishaku da Isra'ila-kakanninmu - ka ajiye wannan har abada a cikin tunanin zukatan mutanenka. Ka bi da zukatansu zuwa gare ka.19Ka ba ɗana Suleman cikakkiyar zuciyar sha'awar kiyaye umarnanka da alƙawarin ka'idodi da dokokinka, domin ya aikata dukka waɗannan shirye-shirye na gina haikali wanda na riga na yi tanaji dominsa."
20Dauda ya ce da dukkan taron, "Yanzu sai ku albarkaci Yahweh, Allahnku." Dukkan taron kuwa suka albarkaci Yahweh, Allah na kakaninsu, suka rusuna da kawunsu suka yi sujada ga Yahweh suka kuma sunkuyar da kansu a gaban sarki.21Washegari, sai suka miƙa wa Yahweh hadayu da hadayun ƙonawa gare shi. Sun miƙa bijimai dubu ɗaya, da raguna dubu ɗaya da kuma 'ya'yan tumakai dubu ɗaya, tare da hadayunsu na sha da hadayu masu yawan gaske domin dukkan Isra'ila.
22A wannan rana, sun ci, sun sha a gaban Yahweh tare da bayyana murna da yabo. Sai suka sake naɗa Suleman ɗan Dauda, sarki a karo na biyu, suka shafa masa man keɓewa tare da ikon Yahweh ya zama mai mulki. Suka kuma keɓe Zadok don ya zama firist.23Sai Suleman ya zauna a kan gadon sarauta na Yahweh maimakon Dauda mahaifinsa. Ya yi wadata, kuma dukkan Isra'ila suka yi biyayya da shi.
24Dukkan shugabanni da sojoji da 'ya'yan sarki suka yi alƙawari za su yi wa sarki Suleman biyayya.25Yahweh kuwa ya ɗaukaka Suleman ƙwarai da gaske a gaban dukkan Isra'ila, ya ba shi babban iko fiye da wani sarki kafin shi a Isra'ila.
26Dauda ɗan Yesse ya yi mulki bisa dukkan Isra'ila.27Dauda ya yi mulki a Isra'ila har shekaru arba'in. Ya yi mulki a Hebron shekaru bakwai, sa'an nan ya yi mulki shekaru talatin da uku a Yerusalem.28Ya rasu da kyakkyawan tsufa, bayan ya ji daɗin rayuwa mai tsawo, da arziki da daraja. Suleman ɗansa ya gaje shi.
29Abubuwan da sarki Dauda ya yi suna rubuce a cikin tarihin annabi Sama'ila, da annabi Natan da annabi Gad.30Abubuwan da ke rubuce su ne ayyukansa da mulkinsa, abubuwan da ya kammala da kuma waɗanda suka shafe shi da Isra'ila da dukkan mulkokin sauran ƙasashe.

Littafin tarihi na biyu

1

1Aka ƙarfafa Suleman ɗan Dauda a cikin mulkinsa, Yahweh Allahnsa na tare da shi ya kuma sa shi ya zama da iko sosai.

2Suleman ya yi magana da dukkan Isra'ila, hafsoshi dubu-dubu dana ɗari-ɗari, da mahukunta da dukkan sarakuna a Isra'ila, da shugabannin gidajen ubanni.3Suleman da dukkan taro suka tafi babban tudu a Gibiyon, domin a can ne rumfar taruwa ta Allah take, wadda Musa bawan Yahweh ya yi a cikin jeji.4Amma Dauda ya kawo akwatin alƙawari na Allah daga Kiriyat Yerim zuwa wurin da ya keɓe dominsa. Domin ya kafa mata rumfa a Yerusalem,5Bugu da ƙari bagadin jan ƙarfen da Bezalel ɗan Uri ya yi yana wurin a gaban rumfar taruwa ta Yahweh; Suleman da dukkan taron suka tafi wurinta.
6Suleman ya tafi can wurin bagadi na tagulla a gaban Yahweh, wadda take a rumfar taruwa, ya miƙa baye-bayen ƙonawa guda dubu a kansa.7Allah ya bayyana ga Suleman a wannan dare ya cemasa, "ka tambaya! Me zan baka?"
8Suleman ya ceda Allah, '"Ka nuna babban amintaccen alƙawari ga Dauda mahaifina, kuma ka maida ni sarkin mutanensa a madadin sa.9Yanzu, Yahweh Allah, sai ka cika alƙawarin da kayi wa mahaifina Dauda, domin ka maida ni sarki kan mutane masu ɗumbin yawa kamar ƙasa.10Yanzu sai ka bani hikima da ilimi domin in iya jagorancin mutanen nan, domin wane ne zai iya yiwa mutanenka hukunci, su da keda yawa sosai?"11Allah ya ceda Suleman, "Saboda wannan ne yake zuciyarka, kuma domin baka roƙi wadata ba, ko kuɗi, ko girma, ko kuma ran waɗanda ke ƙinka, ko kuma tsawon ranka ba, amma ka roƙi hikima da ilimi domin kanka, domin ka iya mulkin mutanena, waɗanda na maishe ka sarki a kansu, to wannan shi ne abin da zan yi.
12Yanzu zan baka hikima da ilimi. Hakannan zan baka arziki da wadata da girma, da ba a taɓa samun sarki kamarka a baya ba, ba kuma za a samu a bayan ka ba."13To sai Suleman ya komo Yerusalem wuri mai tudu da kea Gibiyon, daga wurin rumfar taruwa; ya yi sarauta akan Isra'ila.
14Suleman ya tattara karusai da mahayan dawakai, yana da karusai 1,400 da mahayan dawakai dubu goma sha biyu waɗanda yasa a biranen karusai da kuma tare da shi sarki, a Yerusalem.15Sarki ya samar da zinariya da azurfa birjik kamar duwatsu a Yerusalem, ya kuma samar da itacen sida sosai kamar itacen ɓaure da ke cikin kwaruruka.
16Game da sayo dawakai daga Masar da Kuye domin Suleman, fatakensa ne suka sayo su daga Kuye cikin rahusa.17Suka sayo karusa daga Masar a awo ɗari shida na zinariya, da kuma doki akan shekel 150. Suka kuma sayar da wasu ga sarakunan Hitiyawa da Aremiyawa.

2

1Suleman kuma ya bada umarni domin ginin gida saboda sunan Yahweh da kuma gina fãda domin masarautarsa.2Suleman yasa mutune dubu saba'in su kwaso kayayyaki, mutane dubu tamanin masu saran duwatsu a cikin tsaunuka, da kuma mutane dubu 3,600 su dinga kula da su.3Suleman ya aika da saƙo zuwa sarki Hiram na Taya cewa "Kamar yadda ka yi ga mahaifina Dauda, kana aiko masa da itacen sida domin ya gina gidan da zai zauna, to sai kayi mani haka.

4Duba ina gab da gina gida saboda sunan Yahweh Allahna, in keɓe shi dominsa, in ƙona turare mai ƙamshi a gabansa, in kuma kawo gurasa ta kasancewarsa da kuma hadaya ta ƙonawa safe da yamma, da ranakun asabarci da sabobbin watanni, da kuma ayyanannun bukukuwa domin Yahweh Allahnmu. Wannan na har abada ne, domin Isra'ila.5Gidan da zan gina zai zama da girma sosai, domin Allahnmu mai girma ne fiye da dukkan wasu alloli.
6Amma wane ne zai iya gina gida domin Allah, da yake duniya da dukkan sammai da kansu basu ishe shi ba? Wane ni da zan gina masa gida, ba sai dai kawai in ƙona masa hadaya ba?7To sai ka aiko mani da mutum da ya ƙware a aikin zinariya, azurfa, tagulla, jan ƙarfe, da shunayya, da ja, da shuɗin u'lu, mutum wanda ya iya dukkan ingantattatu sassaƙa. Zai kasance tare da ƙwararrun mutane waɗanda ke tare da ni a Yahuda da Yerusalem, wanda Dauda mahaifina ya yi tanadi.
8Ka aiko mani da itacen sida dana sifires da algun daga Lebanon. Duba barorina zasu tafi tare da barorinka,9domin a samar da katakai sosai, domin gidan da nake shirin ginawa zai zama babba da kuma ban mamaki.10Duba zan ba barorinka mutanen da zasu saro katakan, da kuma awo dubu ashirin na niƙaƙƙiyar alkama, da awo dubu ashirin na sha'ir, da salkunan ruwan inabi dubu ashirin, da kuma santulan mai guda dubu ashirin."
11Sai Hiram, sarkin Taya ya amsa a rubuce ya aika wa Suleman: "Saboda Yahweh yana ƙaunar mutanensa, sai ya naɗa ka sarki a kansu."12Bugu da ƙari Hiram yace, "Albarka ta tabbata ga Yahweh, Allah na Isra'ila, wanda ya hallici sama da duniya, wanda ya ba sarki Dauda ɗa mai hikima, da baiwa da kirki da fahimi, wanda zai gina gida domin Yahweh, da kuma fãda domin kansa.
13Yanzu na aiko da mutum mai fasaha, da baiwa da fahimi, shi ne Huram-Abi.14Shi ɗan wata mata ne a cikin 'ya'yan Dan. Mahaifinsa ya zo ne daga Taya. Shi ƙwararre ne a aikin zinariya da azurfa, da tagulla, da baƙin ƙarfe, da duwatsu, da katakai, da shunayya, da shuɗi, da jan ulu, da lilin mai kyau. Hakannan kuma ƙwararre ne a fannin kowacce irin sassaƙa da zãne. Sai a samar masa wuri a cikin mutanenka ƙwararru da keyi maka aiki, da kuma na shugabana, Dauda, mahaifinka.
15Yanzu kuma da alkama da riɗi, da maida ruwan inabi, wanda shugabana ya yi magana, sai ya aiko da waɗannan abubuwan ga bayinsa.16Zamu saro katako daga Lebanon, gwargwadon yawan katakon da kake bukata. Zamu kawo maka har zuwa tekun Yoffa, sai ka ɗauke su zuwa Yerusalem."
17Suleman ya ƙirga dukkan baƙi da kea ƙasar Isra'ila, ya bi irin fasahar da Dauda mahaifinsa ya mora, ya ƙirga su aka sami mutum 153,600.18Yasa dubu saba'in daga cikinsu su suke ɗaukar kaya, dubu tamanin kuma masu saro katako a kan duwatsu, sai 3,600 su zama masu duba aikin da kuma sa mutanen suyi aikin

3

1Sai Suleman ya fara gina gidan Yahweh a Yerusalem akan Tsaunin Moriya, inda Yahweh ya bayyana ga Dauda mahaifinsa. Ya shirya wurin da Dauda ya tsara dominsa, a masussukar Ornan na Yebusiya.2Ya fara ginin a rana ta biyu ta watan, a shekara ta huɗu ta mulkinsa.3Wannan shi ne fasalin ginshiƙin da Suleman ya kafa domin gidan Allah. ya yi amfani da tsohon salon awo, tsawonsa kamu sittin ne, sai faɗinsa kamu ashirin ne.

4Awon harabar daga gaban gidan ya kai kamu ashirin, dai-dai da faɗin ginin. Tsayinsa kuma kamu ashirin ne, Suleman kuma ya dalaye cikin ginin da tsantsar zinariya.5ya yi wa rufin ainihin cikin harabar ado da sifires, waɗanda ya dalaye da zinariya mai kyau, waɗanda ya sassaƙa da itatuwan dabino da sarƙoƙi.
6ya yi wa gidan ado da duwatsu masu daraja; zinariyar an samo ta ne daga Farbayim.7Hakannan ya yi daɓen ƙasa da bango, da ƙofofin da zinariya; da sassaƙaƙƙun kerubim a jikin bangayensa.
8Ya gina wuri mafi tsarki. Tsawonsa ya kai awo ashirin dai-dai da faɗin ginin, haka kuma faɗin gidan shi ma kamu ashirin ne. Ya shafe shi da tsantsar zinariya dai-dai da yawan talanti dubu ɗari shida.9Nauyin awon ƙusa ya kai awo hamsin na zinariya. Ya shafe shi har sama da zinariya.
10Ya yi siffofin kerubim guda biyu domin wuri mafi tsarki; masu aikin sassaƙa suka dalaye su da zinariya.11Faɗin fuka-fukan kerubobin kamu ashirin ne tsawonsu gaba ɗaya; Fuffuken kerub ɗin ya kai awo biyar a tsawo, wanda ya kai har bangon ɗakin; shi ma ɗaya fuffuken kamu biyar ne, yana taɓa fuffuken ɗaya kerub ɗin na farko.12Fuffuken ɗaya kerub ɗin ma kamu biyar ne, ya kai har bangon ɗakin; ɗayan fuffuken ma kamu biyar ne, yana taɓa fuffuken kerub na farko.
13Fuka-fukan waɗannan kerubobin sun kai faɗin awo ashirin. Kerubobin suka tsaya kan ƙafafunsu, fuskokinsu na fuskantar babban ɗakin taron.14Ya mayar da labulen shuɗi, da shunayya, da jan ulu, ya sassaƙa zãnen kerubobi a kansa.
15Hakannan Suleman ya kafa ginshiƙai guda biyu kowanne tsawonsa ya kai kamu talatin da biyar a tsawo, domin a gaban, abubuwan da kekansu sun kai kamu biyar na tsawo.16Ya yi sarƙoƙi domin ginshiƙan ya kuma dora su a kansu; hakannan yasa turaren ƙanshi ya haɗa su a jikin sarƙar.17Ya kafa ginshiƙan a gaban haikalin, ɗaya daga hannun hagu, ɗaya kuma daga hannun dama, yasa wa ginshiƙan hannun dama suna Yakin, na hannun hagun kuma Bo'aza.

4

1Hakanan ya yi bagadi na tagulla; tsawonsa kamu hamsin ne, faɗinsa kuma kamu ashirin ne, tsawonsa kuma goma ne.2Hakannan ya yi wani kewayayyen tafki na ƙarfe, kamu goma daga baki zuwa baki. Tsawonsa kamu biyar ne, tafkin kuma a kewaye kamu talatin ne.3A ƙarƙashin bakin tafkin akwai bijimai kewaye, kowanne awo goma, aka yi zuɓin ɗaya tare da tafkin sa'ad da aka yi zuɓin tafkin kansa.

4Babban madatsar da ake kira "Tafkin" aka ɗora shi bisa bijimai goma sha biyu, uku na fuskantar arewa, uku yamma, uku kudu, uku kuma gabas. Aka ɗora "Tafkin" a bisansu kuma gadon bayansu na fuskantar ciki.5"Bangajin" ya yi kaurin damtsen hannu, kuma aka goge bakinsa kamar bakin kofi, kamar buɗewar fure. "Tafkin" yana ɗaukar kimanin garwa dubu uku ta ruwa.6Hakannan ya yi tafkuna goma domin wankin abubuwa; yasa biyar daga ɓangaren kudu, biyar kuma daga arewa; za a dinga wanke kayayyakin miƙa baiko na ƙonawa a cikinsu. Babban madatsar da aka fi sani da "Tafki" firistoci ne suke amfani da ita domin wanke-wanke.
7ya yi sandunan zinariya na ajiye fitilu guda goma kuma an tsara su ne kamar yadda aka umarta; ya ajiye su a cikin haikali, biyar a hannun dama biyar a hannun hagu.8ya yi tebura goma yasa su a cikin haikalin, biyar a bangon dama, biyar a bangon hagu. Ya yi kwanonin na zinariya guda ɗari.
9Bugu da ƙari ya yi harabar firistoci, da babbar haraba da kuma ƙofofi domin harabar ya kuma dalaye ƙofofinsu da tagulla.10Ya ajiye madatsar da aka sani da "Tafki" a gefen gabas na haikalin, daga gabas kuma na haikalin, yana fuskantar kudu.
11Huram ya yi tukwanen, cebura na ƙarfe da kwanoni na yayyafa ruwa. Da haka Huram ya kammala aikin da ya yi wa Suleman a cikin gidan Allah:12ginshiƙai guda biyu, gammunan biyu masu fasalin kwano da kebisa ginshiƙin biyu, tsare-tsaren aikin ado biyu da aka yi domin rufe gammunan biyu masu fasalin kwano waɗanda ke bisa ginshiƙan.13Ya kuma yi siffofin ruman guda ɗari huɗu domin suturta waɗannan kayayyakin: ya kawo dozin biyu na kayan kyalli domin a adana bangazan da kekan ginshiƙan.
14Hakannan ya yi matokarai domin kawo tafkunan su zauna a matokaran;15tafki ɗaya bijimai sha biyu a ƙarƙashinsa,16Hakannan da tukwanen, da ceburan, cokulan nama masu yatsu, da dukkan sauran kayayyaki da Huram-Abi ya ƙera daga gogaggiyar tagulla domin Sarki Suleman, domin gidan Yahweh.
17Sarki ya ajiye su a filin Yodon filin yumɓu tsakanin Sukkot da Zaretan.18Da haka Suleman ya yi dukkan waɗannan kayyayaki cikin babbar yalwa. Hakika ba a san nauyin tagullar da aka yi aiki da ita ba.
19Suleman ya yi dukkan kayan ƙawa da kecikin haikalin Allah da kuma bagadi na zinariya, da kuma teburi inda ake ajiye gurasa;20Sandunan ajiye fitilu da fitilun da aka yi domin ƙona hadaya a gaban ɗakin ƙurya - waɗannan anyi su da tsantsar zinariya ne;21Hakannan furannin, da fitilun bangazan, da cokulan da abin ƙona turare duk da zinariya tsantsa, aka yi su.
22Haka kuma abin gyara fitilu, da cokula, da bangazai da abin ƙona turare duk da tsantsar zinariya aka yi su. Game kuma da ƙofar gidan, da ƙofofinsu na ciki zuwa wuri mafi tsarki da kuma ƙofofin gidan, dake, na haikalin, duk da zinariya aka yi su.

5

1Bayan Suleman ya kammala waɗannan ayyukan domin gidan Yahweh, Suleman ya kawo kayayyakin da Dauda mahaifinsa ya keɓe saboda wannan dalilin, haɗe da zinariya da azurfa, da dukkan kayayyakin ado - ya ajiye su a ma'ajin gidan Allah.

2Daga nan Suleman ya tattaro dukkan dattawan Isra'ila, da dukkan shugabannin kabilu, da shugabannin iyalai na mutanen Isra'ila, a Yerusalem domin su kawo akwatin alƙawari na Yahweh daga birnin Dauda, wato Sihiyona.3Dukkan mutanen Isra'ila suka tattaru a gaban sarki a wurin bikin, wanda aka yi a wata na bakwai.
4Dukkan dattawan Isra'ila suka zo, Lebiyawa kuma suka ɗauko akwatin alƙawari.5Suka kawo akwatin, da rumfar taruwa, da dukkan kayayyakin da kecikin rumfar. Sai firistoci waɗanda ke daga kabilar Lebiyawa suka kawo waɗannan abubuwa6Sarki Suleman da dukkan taron mutanen Isra'ila suka taru a gaban akwatIn, suka yi hadaya da shanu har da ba za'a iya ƙirgawa ba.
7Sai firistoci suka kawo akwatin alƙawari na Yahweh a wurinsa, a can ɗaki na ƙurya na gidan, zuwa wuri mafi tsarki, a ƙarƙashin fuka-fukan kerubim.8Domin kerubim sun buɗe fuka-fukansu a kan wurin akwatin sun kuma rufe akwatin da kuma sanduna da aka ɗauko shi da su.
9Sandunan suna da tsawo sosai ana ganin ƙarshensu daga wuri mai tsarki a gaban ɗaki na can ciki, amma ba za a iya ganinsu daga waje ba. Suna nan a wurin har ya zuwa yau.10Ba komai a cikin akwatin sai allunan guda biyu da Musa ya saka a Tsaunin Horeb, a lokacin da Yahweh ya ƙulla alƙawari da Isra'ila, bayan sun fito daga Masar.
11Sai ya zamana bayan firistoci sun fito daga wuri mai tsarki. Dukkan firistocin da kewurin suka tsarkake kansu ga Yahweh, basu bi tsarinsu na rabe-rabensu ba.12Hakannan Lebiyawa da kemawaƙa, dukkansu har da Asaf da Heman da Yedutun da 'ya'yansu da 'yan'uwansu suka yi ado da kaya masu kyau suna kaɗa molo da garayu, da goge, sarewa, suna tsaye a gabas da bagadin. Tare da su akwai firistoci 120 suna hura kakakai.
13Sai ya zamana da masu hura kakakin da mawaƙan suna waƙa tare, suna fitar da murya ɗaya domin yabo da godiya ga Yahweh. Sun tada muryoyinsu da kakakinsu da molonsu da kayan kaɗe-kaɗensu, suka kuma yabi Yahweh. Suka rera waƙa cewa, "Domin shi managarci ne domin alƙawarinsa mai aminci ya tabbata har abada." Daga nan sai gidan, wato gidan Yahweh, ya cika da girgije.14Firistoci basu iya tsayawa suyi hidima ba saboda girgijen, domin daukakar Yahweh ta cika gidan.

6

1Daga nan sai Suleman ya ce"Yahweh ya cezai zauna a cikin duhu baƙi ƙirin,2amma na gina maka wurin zama mai dacewa, wurin da zaka zauna har abada."3Bayan wannan sai sarki ya juya ya albarkaci dukkan taron mutanen Isra'ila a lokacin da taron Isra'ila ke tsaye.

4ya ce dãma a yabi Yahweh na Isra'ila, wanda ya yi magana da mahaifina Dauda, ya kuma cika shi da hannunsa, cewa,5'Tun daga ranar dana fito da mutanena daga ƙasar Masar, ban zaɓi wani wuri a cikin dukkan kabilun Isra'ila domin in gina gida saboda sunana a can ba. Ban kuma zaɓi wani mutum ya zama sarkin mutanena Isra'ila ba.6Duk da haka na zaɓi Yerusalem, domin sunana ya kasance a can, na kuma zaɓi Dauda ya zama sarkin mutanena Isra'ila,'
7To a cikin zuciyar mahaifina Dauda ya ƙudurta ya gina gida domin Yahweh Allah na Isra'ila.8Amma Yahweh ya cewa Dauda mahaifina in har ka ƙudurta ka gina gida domina ka kyauta daka sa wannan a zuciyarka.9Duk da haka ba kaine zaka gina gidan ba; amma ɗanka ne, wanda zai fito daga tsatsonka, shi ne zai gina gida domin sunana.'
10Yahweh ya cika maganar da ya faɗa, domin ina tsayawa a maimakon Dauda mahaifina, na kuma zauna a kan gadon sarautar Isra'ila, kamar yadda Yahweh ya alƙawarta. Na kuma gina gida domin sunan Yahweh, Allah na Isra'ila.11Na ajiye akwatin alƙawari a can, wanda shi ne alƙawarin Yahweh, wanda ya yi da mutanen Isra'ila."
12Suleman ya tsaya a gaban bagadi na Yahweh a gaban dukkan taron Isra'ilawa ya buɗe hannuwansa.13Domin ya yi dakali na tagulla, tsawo kamu biyar, fãɗi kamu biyar, bisansa kamu biyar. Ya ajiye shi a tsakiyar harabar haikalin. Ya tsaya a kansa ya kuma durƙusa a gaban dukkan taron Isra'ila, daga nan sai ya buɗe hannuwansa zuwa sammai.
14Yace, "Yahweh, Allah na Isra'ila, ba wani Allah kamarka a sama ko a ƙasa, wanda ke cika alƙawari da madawwamiyar ƙauna ga bayinka da suka yi tafiya a gabanka da dukkan zuciyarsu;15kai wanda ka riƙe alƙawari da bawanka Dauda mahaifina, abin daka alƙawarta masa. I, kayi magana da bakinka ka kuma cikata da kanka kamar yadda ya ke a yau.
16Yanzu Yahweh, Allah na Isra'ila, sai ka cika abin daka alƙawarta wa bawanka Dauda mahaifina, lokacin da kace 'Baza ka taɓa rasa wani mutun a gabana da zai zauna a kan gadon sarautar Isra'ila ba, in dai zuriyarka suka lura suyi tafiya bisa shari'ata, kamar yadda kayi tafiya a gabana.'17Yanzu, Yahweh, Allah na Isra'ila, ina roƙonka cewa ka tabbatar da alƙawarin da kayi wa bawanka Dauda.
18Amma ko Allah zai yi rayuwa da mutum a duniya? duba, duniya ma kanta da sama basu isheka ba, balle kuma wannan haikalin dana gina!19Amma duk da haka ina roƙo ka girmama wannan addu'a ta bawanka, da kuma roƙonsa Yahweh Allahna; ka ji addu'a da kuma kukan da bawanka ke yi a gabanka.20Dama idanunka da kunnuwanka su kasance a buɗe rana da dare ga wannan haikalin. Wurin da kayi alƙawarin sa sunanka. Dama ka saurari addu'ar bayinka da zasu yi a wannan wurin.
21To sai ka saurari roƙe-roƙen bawanka da mutanenka Isra'ila a lokacin da suka yi addu'a suna fuskantar wannan wuri. I, ka saurara daga wurin da kake zaune, daga sammai kuma bayan ka saurara, ka yi gafara.
22In mutun ya yi laifi gãba da ɗan'uwansa in an bukace shi da ya rantse a gaban bagadinka a wannan gida,23to sai kaji daga sammai ka kuma hukunta bayinka, kayi wa mugu sakaiya, ka kuma ɗora masa hakinsa a kansa. Ka kuma shaida mai adalci mara laifi, ka bashi ladar aikinsa na adalci.
24A lokacin da aka ci nasara kan mutanenka Isra'ila ta hannun maƙiya saboda sunyi maka zunubi, in sun juyo wurinka, suka kuma furta sunanka, suka yi addu'a, suka roƙi gafara a gabanka a wannan wuri-25to ina roƙo kaji daga sammai ka gafarta zunubin mutanenka Isra'ila; ka komo da su ƙasar daka basu, su da kakaninsu.
26Idan sammai suka rufe kuma aka sami fãri saboda mutane sun yi maka zunubi - in sun yi addu'a suna fuskantar wannan wuri, suka furta sunanka, suka kuma juyo daga zunubinsu bayan ka hore su -27to sai kaji su a sama ka gafarta zunubin bayinka da mutanenka Isra'ila, lokacin daka bi da su ta hanya mai kyau da zasu bi. Ka aiko da ruwan sama a kan ƙasarka, wadda ka ba mutanenka gãdo.
28Ko kuma ace ana yunwa a ƙasar, ko kuma akwai cuta, ko annoba, ko darɓa, ko funfuna; ko kuma ace a kwai magafta da suka kawo hari a ƙofofin birnin ƙasar, ko kuma wata masifa ta afko wa ƙasar ko rashin lafiya_29ko kuma ace an yi adduo'i da roƙe-roƙe ta wurin mutum ɗaya ko kuma dukkan mutanenka Isra'ila-ko kuma na sane da annobar da kuma baƙincikin a zuciyarsa lokacin da ya buɗe hannuwansa yana fuskantar wannan haikali.30sai ka saurara daga sama, a wurin da kake zama; ka gafarta ka kuma sãka wa kowanne mutum gwargwadon aikinsa; ka san zuciyarsa, domin kai kaɗai ne kasan zukatan mutane.31Kayi wannan domin su ji tsoronka, domin suyi tafiya bisa tafarkunka a cikin dukkan kwanakin da suke a wannan ƙasa daka ba kakaninsu.
32Game kuma da băƙi da ba mutanenka Isra'ila ba, amma saboda girman sunanka, da hannunka mai iko, da kuma damtsenka daka miƙa - suka zo suka yi addu'a suna fuskantar wannan wuri,33to ina roƙo ka saurara daga sama, wurin da kake zama, ka kuma yi duk abin da băƙin suka roƙe ka, domin dukkan mutanen duniya su san sunanka su kuma ji tsoronka, kamar mutanenka Isra'ila, domin kuma su san wannan gidan dana gina ana kiransa da sunanka.
34Ko kuma in mutanenka suka tafi yaƙi gãba da maƙiyansu, ta kowacce hanya da zaka aike su, sai kuma suka yi addu'a gare ka suna fuskantar wannan birni daka zaɓa, suna kuma fuskantar wannan wuri dana gina domin sunanka.35To sai ka saurari addu'arsu da roƙonsu ka taimake su daga sammai.
36Ko kuma in sunyi maka zunubi_ tunda ya ke ba wanda baya yin zunub i- ko kuma in kayi fushi da su ka kuma miƙa su ga maƙiya, domin maƙiya su kwashe su su kaisu bauta a ƙasarsu, ko kusa ko nesa.37Daga nan a misali in sun gane cewa suna ƙasar bauta, kuma a misali in sun tuba suka kuma nemi tagomashi daga wurinka a ƙasar da suke bauta. A misali kuma idan suka ce, 'Mun yi wauta mun yi zunubi. Mun yi halin mugunta.'38A misali idan suka juyo gare ka da dukkan zuciyarsu da ransu a ƙasar da suke bauta, inda suka ɗauke su a matsayin bautar talala, a misali kuma in sun yi addu'a suna fuskantar ƙasarsu, wadda ka ba kakaninsu, da kuma birni daka zaɓa, da kuma gidan da na gina domin sunanka.39Daga nan sai kaji addu'oinsu da roƙe-roƙensu ka kuma taimake su, daga sammai a wurin da kake zama ka taimaki al'amarinsu. Ka gafarta wa mutanenka, da suka yi maka zunubi.
40Yanzu, Allahna, ina roƙonka, ka buɗe idanunka, ka kuma sa kunnuwanka suji addu'ar da za a yi a wannan wuri.41Yahweh Allah, sai ka tashi daga wurin hutawarka, kai da akwatin ƙarfinka. Yahweh kasa firistocinka su rufa da cetonka, ka kuma sa tsarkakanka suyi murna kan alheranka.42Yahweh Allah, kada ka juyar da fuskar keɓaɓɓunka daga wurinka. Ka tuna da abubuwan daka alƙawarta na yin aminci ga bawanka Dauda."

7

1Da Suleman ya gama addu'a sai wuta ta sauko daga sama ta cinye baye-baye na ƙonawa da hadayu, sai ɗaukakar Yahweh ta cika gidan.2Firistoci basu iya samun damar shiga gidan Yahweh ba, saboda ɗaukakarsa ta cika gidansa.3Duk mutanen Isra'ila sun ga yadda wutar tazo daga sama ɗaukakar Yahweh kuma ta sauko a kan gidan, sai suka sunkuyar da kawunansu ƙasa a kan keɓaɓɓen dutse na sujada suka bada godiya ga Yahweh. Suka ce, "Domin shi nagari ne, domin alƙawarin amincinsa ya tabbata har abada."

4Sai sarki da dukkan mutanen suka miƙa hadaya ga Yahweh.5Sarki Suleman ya miƙa hadayar bijimai dubu ashirin, da tumaki da awaki 120,000. Sai sarki da dukkan mutanen suka keɓe gidan Allah.6Sai firistoci suka tsaya, kowanne ya tsaya a inda ya ke hidima, hakannan Lebiyawa suna ɗauke da kayan kiɗa na Yahweh, wanda sarki Dauda ya yi domin ya riƙa yin godiya ga Yahweh ta wurin waƙa, "Domin alƙawarin amincinsa ya tabbata har abada." Sai dukkan firistoci suka hura kãkãki a gabansu, kuma sai dukkan Isra'ila suka miƙe tsaye.
7Sai Suleman ya keɓe tsakiyar haikalin a gaban gidan Yahweh. A can ya miƙa baye-baye ta ƙonawa da kuma kitse na baye-baye na zumunci, domin wannan bagadi na tagulla da ya yi ya gaza ɗaukar baye-baye na ƙonawa, baye-baye ta hatsi, da kitsen.
8Sai Suleman da ya yi bukin a wancan lokacin har na kwana bakwai tare kuma da dukkan Isra'ilawa, babban taro ne tun daga Lebo Hamat har zuwa iyakar Masar.9A rana ta takwas suka yi taron murna domin sun yi taron keɓe bagadi na kwana bakwai.10A rana ta ashirin da uku a wata na bakwai, Suleman ya sallami taron mutanen suka koma gidajensu da murna da farin ciki saboda alheran Yahweh daya nuna ga Dauda da Suleman da kuma Isra'ila, mutanensa.
11Da haka Suleman ya kammala gidan Yahweh da kuma gidansa. Duk abin da yazo zuciyar Suleman game da gidan Yahweh da kuma gidansa ya yi su dukka.12Sai Yahweh ya bayyana ga Suleman da dare ya kuma ce da shi, "Na ji addu'arka na kuma zaɓi wannan wurin domin kaina domin ya zama gidan miƙa hadaya.
13A misali da ace na rufe sammai domin kada ayi ruwa, ko kuma in umarci fări su cinye ƙasar, ko kuma idan na aiko da cuta cikin mutanena,14To indan mutanena da ake kira da sunana, zasu yi tawali'u su yi addu'a, su biɗi fuskata, su kuma juya daga mugayen hanyoyinsu, to zan ji daga sama, zan kuma gafarta zunubinsu, in kuma warkar da ƙasarsu.15Yanzu idanuna zasu zama a buɗe kunnuwana kuma zasu ji addu'o'in da za ayi a wannan wurin.
16Domin yanzu na zaɓa na kuma keɓe wannan gida domin sunana ya kasance a wurin har abada. Idanuna da zuciyata zasu kasance a can kullum.17Kai kuma in zaka yi tafiya a gabana kamar yadda mahaifinka Dauda ya yi, ka kuma yi biyayya da duk abin da na umarce ka ka kuma kiyaye sharuɗana da farillaina,18To zan kafa gadon sarautarka, kamar yadda na faɗa a alƙawarina da Dauda mahaifinka, lokacin da nace, 'Ba za a taɓa rasa wani daga cikin zuriyarka ba wanda zai yi mulki a Isra'ila.'
19Amma in ka juya, kayi watsi da farillaina da dokokina dana sa a gabanka, kuma idan ka juya ka bautawa gumaka ka russuna masu,20To zan tunɓuke su daga ƙasar dana basu. Wannan gidan kuma dana keɓe domin kaina zan kawar da shi daga gare ni, zan kuma maida shi abin habaici da ba'a ga dukkan al'ummai.
21Koda ya ke wannan haikalin ya ƙayatu yanzu, duk wanda ya wuce ta gefensa zai razana ya yi tsaki. Zasu ce 'Me yasa Yahweh ya yi haka ga wannan gida da kuma wannan ƙasa?'22Sauran zasu amsa suce saboda sun yashe da Yahweh Allahnsu ne, wanda ya fito da kakanninsu daga ƙasar Masar, sai kuma suka kakkafa waɗansu gumaku suka russuna masu suka yi masu sujada. Shi yasa Yahweh ya aukar masu da duk wannan masifa."'

8

1Sai ya kasance a karshen shekaru ashirin da Suleman ya gina gidan Yahweh da kuma gidansa,2sai Suleman ya sake gina garuruwan da Hiram ya bayar gare shi, ya kuma zaunar da mutanen Isra'ila a cikinsu.

3Sai Suleman ya kai wa Hamatzoba hari ya kuma cinye ta.4Ya gina biranen ajiya a cikin hamada, da dukkan birane ƙayatattu da ya gina a Hamat.
5Haka kuma sai ya gina Bet Horon na Sama da Bet Horon na Ƙasa, birane masu tsaro mai ƙarfi tare da katangai, ƙofofi, da ƙyamare.6Ya gina Balat da dukkan biranen ma'aji da ya mallaka, da dukkan biranem domin karusansa da kuma biranen domin mahayansa, kuma ko mene ne ya yi niyar ginawa domin jin daɗinsa a cikin Yerusalem, cikin Lebanon, da kuma cikin dukkan ƙasashen da keƙarƙashin mulkinsa.
7Amma game da dukkan mutanen da aka rage na wajen su Hittiyawa, da Amoriyawa, da Feriziyawa, da Hibiyawa, da kuma Yebusiyawa, waɗanda ba daga Isra'ila suke ba,8zuriyarsu da aka bari a bayansu cikin ƙasar, waɗanda mutanen Isra'ila basu hallakar ba - Suleman ya maishe su masu aikin tilas, haka suke har wa yau.
9Duk da haka, Suleman bai ɗora wa jama'ar Isra'ila aikin tilas ba. A maimakon haka, suka zama sojojinsa, kwamandojinsa, da hafsoshinsa, da kuma kwamandojin karusan jarumawansa da kuma mahaya dawakansa.10Waɗannan kuma su ne manyan hafsoshin masu tafiyar da al'amuran masu kula waɗanda ke na Sarki Suleman, 250 ne suke, waɗanda suka kula da mutanen da suka yi aiki.
11Sai Suleman ya fito da ɗiyar Fir'auna daga birnin Dauda zuwa gidan da ya gina mata, gama yace, "Matata bazata zauna a gidan Dauda sarkin Isra'ila ba, domin duk inda akwatin alƙawarin Yahweh ya shiga mai tsarki ne."
12Sai Suleman ya miƙa baye-baye na ƙonawa ga Yahweh a bisa bagadin Yahweh daya gina a gaban Haikalin.13Ya miƙa hadayu kamar yadda ya wajaba cikin shirin kowacce rana; ya miƙa su, yana koyi da yadda aka shimfiɗa su a cikin umurnan Musa, a ranakun Asabaci, sabobbin watanni, da kuma kafaffun bikin sau uku kowacce shekara: Bikin Gurasa Mara Gami, Bikin Mako, da kuma Bikin Bukkoki.
14Bisa ga dokokin mahaifinsa Dauda, Suleman ya naɗa ƙungiyoyin firistoci ga aikinsu, Lebiyawa kuma ga matsayinsu, domin suyi yabo ga Allah su kuma yi hidima a gaban firistoci, kamar yadda ya wajaba a kowacce rana. Ya kuma sa matsaran ƙofofi bisa ga tsarinsu a kowacce ƙofa, gama Dauda, mutumin Allah, ya umarta wannan.15Waɗannan mutane basu kauce daga dokokin sarki ga firistoci da Lebiyawa ba game da kowanne al'amari, ko game da ɗakunan ajiya.
16Dukkan aikin da Suleman ya umartar aka gama, daga ranar da aka kafa harsashen gidan Yahweh har aka gama shi. Gidan Yahweh ya kammalu.
17Sai Suleman ya tafi Eziyon Geba daga nan zuwa Elat a gaɓar teku, a ƙasar Idom.18Sai Hiram ya aika mashi da jirage da hafsoshinsa suka umarta, mazajen da suka ƙware a sha'anin teku, kuma tare da bayin Suleman suka tafi Ofir suka kuma ɗauka daga nan talanti 450 na zinariya suka kawo wurin Sarki Suleman.

9

1Da sarauniyar Sheba taji game da girman Suleman, sai tazo Yeruslem domin ta gwada shi da tambayoyi masu wuya. Ta zo da doguwar tawaga, tare da raƙuma ɗauke da kayayyakin ƙamshi, zinariya mai yawa, da kuma duwatsu masu daraja dayawa. Da ta iso wurin Suleman, sai ta gaya masa dukkan abin da kecikin zuciyarta.2Suleman ya bata amsar dukkan tambayoyinta; babu komai mai wuya ga Suleman; babu tambayar da bai bada amsar ta ba.

3Da sarauniyar Sheba ta ga hikimar Suleman da kuma fãdar da ya gina,4abincin teburinsa, da yanayin zaman bayinsa, aikin bayinsa da kuma tufafinsu, har da masu ba shi abin sha da irin tufafinsu, da kuma baye-baye na ƙonawa daya miƙa a gidan Yahweh, sai kuma babu sauran hanzari a cikinta.
5Ta cewa sarkin, "Gaskiya ne, labarin da naji cikin ƙasata game da maganganunka da hikimarka.6Ban yarda da abin da naji ba har sai da nazo nan, kuma da idanuwana na gani. Ko rabi ba a gaya mani ba game hikima da wadatarka! Ka zarce girman da naji game da kai.
7Mutanenka masu albarka ne, bayinka kuma waɗanda ke tsayawa gaban ka koyaushe masu albarka ne, domin suna sauraran hikimarka.8Mai albarka ne Yahweh Allahnka, wanda ya ke jin daɗinka, wanda ya ɗora ka a bisa kursiyinsa, ka zama sarki domin Yahweh Allahnka. Domin Allahnka na ƙaunar Isra'ila, domin ya kafa su har abada, ya maishe ka sarki bisansu, domin ka aikata gaskiya da adalci!"
9Sai ta ba sarki talanti 120 na zinariya da kayan ƙamshi mai yawa da kuma duwatsu masu daraja. Babu kayan ƙamshi mai yawa haka kamar wannan da sarauniyar Sheba ta ba Sarki Suleman da aka ƙara kawo masa kuma.
10Bayin Hiram da bayin Suleman, waɗanda suka kawo zinariya daga Ofir, sun kawo kuma katakon algum da duwatsu masu daraja.11Da katakan algum ɗin, sarki ya yi matakalai na gidan Yahweh da kuma domin fadarsa, har kuma da garayu da molaye domin mawaƙa. Ba a taɓa ganin irin wannan katakon a ƙasar Yahuda ba.12Sarki Suleman ya ba sarauniyar Sheba dukkan abin da ta tambaya; ya bata fiye da abin da ta kawo wa sarki. Sai ta tafi ta koma ƙasarta, ita da bayinta.
13Yanzu nauyin zinariyan da yazo wurin Suleman a cikin shekara ɗaya talanti 666 na zinariya ne,14ban da zinariyar da 'yan kasuwa da fatake suka kawo. Dukkan sarakunan Arabiya da gwamnoni a cikin ƙasar suka kawo zinariya da azurfa ga Suleman.
15Sarki Suleman ya yi manyan garkuwoyi guda ɗari biyu na bugaggar zinariya. Awo ɗari shida na zinariya ne ya shiga kowacce ɗaya.16Ya kuma yi garkuwoyi na bugaggar zinariya guda ɗari uku. Minas uku na zinariya ne ya shiga kowacce garkuwa; sarki ya ajiye su a cikin Gida na Jejin Lebanon.
17Sa'an nan sarki ya gina babban kursiyi na hauren giwa ya kuma dalaye ta da zinariya mafi kyau.18Da akwai matakalai guda shida na hawan kursiyin, kuma da kujeran ɗora ƙafa harɗe da mazamnin sarautar. A kowanne ɓangaren kursiyin akwai abin ɗora hannu da zakuna biyu tsaye kusa da kowannen su.
19Zakuna goma sha biyu suna tsaye a matakalun, ɗaya a kowanne gefe na matakalai shidan. Babu wata masarautar da keda irin wannan kursiyin.20Dukkan abubuwan shan ruwan Sarki Suleman na zinare ne, kuma dukkan moɗayen shan ruwa da kea Gida na Jejin Lebanon duk na zallar zinare ne. Babu wadda suke daga azurfa domin azurfa ba abin daraja bane a kwanakin Suleman.21Sarkin yana da jiragen ruwa masu tafiya cikin teku, tare da jiragen na Hiram. Sau ɗaya a shekara uku jiragen sukan tafi su kawo zinariya, azurfa, da kuma hauren giwa, da manyan birai, da ɗawisu.
22Saboda haka sarki Suleman yafi dukkan sarakunan duniya arziki da kuma hikima.23Dukkan sarakunan duniya suka nemi su ga Suleman domin su saurari hikimarsa, wadda Allah yasa cikin zuciyarsa.24Waɗanda suka kawo ziyara suka zo masa da kyautai, kayayyaki na azurfa dana zinariya, riguna, kayan yaƙi, da kayan ƙanshi, da kuma dawakai da alfadarai, shekara bayan shekara.
25Suleman yana da ɗakunan dawakai har dubu huɗu da karusai, da mahayan dawakai dubu sha biyu, waɗanda ya sanya su cikin birnin karusai tare da shi kuma a cikin Yerusalem.26ya yi mulki bisa dukkan sarakuna daga Kogin Yufiretis zuwa ƙasar Filistiyawa, zuwa iyakar Masar.
27Sarkin yana da azurfa cikin Yerusalem, yawansu kamar duwatsun ƙasa. Ya maida itacen sida kamar itacen durumi mai yawa da suke ƙauyuka.28Aka kawo wa Suleman dawakai daga Masar da kuma daga dukkan ƙasashe.
29Game da waɗansu batutuwa game da Suleman, farko da ƙarshe, ba an rubuta su cikin Tarihi na Nathan annabi ba, cikin Annabci Ahiya Ba-shiloni, kuma a cikin Wahayin Iddo Mai duba (wanda ya sami labari game da Yerobowam ɗan Nebat)?30Suleman ya yi mulki cikin Yerusalem bisa dukkan Isra'ila har shekara arba'in.31Ya yi barci tare da kakanninsa kuma mutanen suka binne shi a cikin birnin Dauda mahaifinsa. Rehobowam, ɗansa, ya zama sarki a madadinsa.

10

1Rehobowam ya tafi Shekem, gama dukkan Isra'ila na zuwa Shekem domin a naɗa shi sarki.2Da Yerobowam ɗan Nebat ya ji wannan (domin yana cikin Masar, inda ya guje wa sarki Suleman), sai ya dawo daga Masar.

3Sai suka aika aka kirawo shi, kuma Yerobowam da dukkan Isra'ila suka zo; suka yi magana da Rehobowam suka kuma ce,4"Mahaifinka yasa karkiyarmu da wuya. Yanzu kuwa, kasa aikin mahaifinka mai wuya ya zama da sauƙi, ka kuma sauƙaƙa karkiya mai nauyin da ya ɗora mana, mu kuma mu bauta maka."5Sai Rehobowam yace masu, "Ku komo gare ni bayan kwana uku." Sai mutanen suka tafi.
6Sai sarki Rehobowam ya nemi shawara a wurin dattawa waɗanda suka tsaya a gaban Suleman mahaifinsa sa'ad da ya ke raye; yace, "Ta yaya zaku shawarce ni in bada amsa ga waɗannan mutanen?"7Suka yi magana da shi suka ce, "Idan kayi alheri ga waɗannan mutanen ka kuma kyauta masu, ka kuma faɗi masu maganganun alheri, sa'annan zasu zama bayin ka koyaushe."
8Amma Rehobowam ya yi watsi da shawarar da dattawan suka bashi, amma ya nemi shawara daga matasa waɗanda suka girma tare dashi, waɗanda suka tsaya gabansa.9Yace masu, "Wacce shawara zaku bani, domin mu amsa ma mutanen da suka yi magana da ni suka ce, 'Ka rage mana nauyin karkiyar da mahaifinka ya ɗora mana'?"
10Samarin da suka yi girma tare da Yerobowam suka yi magana dashi, cewa, "Ga yadda zaka yi magana da mutanen da suka ce maka mahaifinka Suleman yasa ƙarkiyarsu tayi nauyi, amma wai dole kasa ta zama da sauƙi. Ga abin da zaka ce masu, 'Ɗan ƙaramin yatsana yafi ƙugun mahaifina kauri.11Don haka yanzu, ko da ya ke mahaifina ya tsananta maku da karkiya mai nauyi, ni zan daɗa bisa karkiyarku. Mahaifina ya hore ku da bulala, amma ni zan hore ku da kunnamai."
12Sai Yerobowam da dukkan mutanen suka zo wurin Rehobowam a rana ta uku, kamar yadda sarki ya faɗi, "Ku dawo wurina a rana ta uku."13Sai Rehobowam ya yi masu magana da zafi, ya yi banza da shawarar dattawan.14ya yi masu magana bisa ga shawarar Samarin, cewa, "Mahaifina yasa ƙarkiyarku tayi nauyi, amma zan daɗa bisanta. Mahaifina ya yi maku horo da bulala, amma ni zanyi maku horo da kunamai."
15Sarki kuwa bai saurari mutanen ba, gama al'amari ne wadda ke faruwa yadda Allah ya shirya, domin Yahweh ya aiwatar da maganarsa wadda Ahiya Bashilone ya faɗi ga Yerobowam ɗan Nebat.
16Lokacin da dukkan Isra'ila suka ga cewa sarki bai saurare su ba, sai mutanen suka amsa masa suka ce, "Wanne rabo muke da shi a cikin Dauda? Bamu da gãdo a cikin ɗan Yesse! Kowannenku ya koma ga rumfarsa, Isra'ila. Yanzu ka kula da naka gidan, Dauda." Sai dukkan Isra'ila suka koma rumfunansu.
17Amma game da mutanen Isra'ila waɗanda ke zaune cikin biranen Yahuda, Rehobowam ya yi mulki bisansu.18Sai sarki Rehobowam ya aiki Adoniram, wanda ke lura da aikin tilas, amma mutanen suka jejjefe shi da duwatsu har ya mutu. Sarki Rehobowam ya tsere da sauri cikin karusansa zuwa Yerusalem.19Don haka Isra'ila ke tayarwa gãba da gidan Dauda har wa yau.

11

1Da Rehobowam ya isa Yerusalem, ya tattaro gidan Yahuda da Benyamin, 180,000 zaɓaɓɓun mutane waɗanda suke sojoji, suyi yaƙi gãba da Isra'ila, su maido da masarautar ga Rehobowam.

2Amma maganar Yahweh tazo wa Shamayya mutumin Allah, cewa,3"Ka cewa Rehobowan ɗan Suleman, sarkin Yahuda, da dukkan Isra'ila cikin Yahuda da Benyamin,4Yahweh ya faɗi wannan, "Kada ku kai hari ko kuyi yaƙi gãba da 'yan'uwanku. Kowanne dole ya koma ga nasa gidan, domin na sanya wannan ya faru."'" Sai suka yi biyayya da maganganun Yahweh suka kuma juya baya daga harin Yerobowam.
5Rehobowam ya zauna cikin Yerusalem ya kuma gina birane domin tsaro.6Ya gina Betlehem, Itam, Tekoya,7Betzur, Soko, Adullam,8Gat, Maresa, Zif,9Adorayim, Lakish, Azeka,10Zora, Ayyalon, da kuma Hebron. Waɗannan tsararrun birane ne cikin Yahuda da Benyamin.
11Ya ƙarfafa wuraren tsaronsu ya sanya ofisoshi a cikinsu, tare da tanadin abinci, da mai, da inabi.12Ya sanya garkuwoyi da mãsu a cikin dukkan biranen ya kuma maida su masu ƙarfi sosai. Haka Yahuda da Benyamin suka zama nasa.
13Firistoci da Lebiyawa daga cikin dukkan Isra'ila suka ƙetara zuwa gare shi daga cikin kan iyakokinsu.14Domin Lebiyawan suka bar gonakinsu na noma da kiwo da kaddarorinsu domin su zo Yahuda da Yerusalem, domin Yerobowam da 'ya'yansa maza sun kore su, don kada su sake aiwatar da ayyukan firistoci domin Yahweh.15Yerobowam ya naɗa wa kansa firistoci domin wuraren masujadai da kuma gumakan akuya da na maraƙi da ya yi.
16Mutane daga dukkan kabilun Isra'ila suka biyo shi, waɗanda suka tsaida zukatansu su biɗi Yahweh, Allah na Isra'ila; suka zo Yerusalem suyi hadaya ga Yahweh. Allahn Ubanninsu.17Sai suka ƙarfafa masarautar Yahuda suka kuma sa Rehobowam ɗan Suleman ya yi ƙarfi lokacin shekaru uku, suka kuma yi tafiya shekaru uku cikin hanyar Dauda da Suleman.
18Rehobowam ya ɗaukar wa kansa mata: Mahalat, ɗiyar Yerimot, ɗan Dauda, da Abihayil, ɗiyar Eliyab, ɗan Yesse.19Ta haifa masa 'ya'ya maza: Yewush, Shemariya, da Zaham.
20Bayan Mahalat, Rehobowam ya ɗauki Ma'aka, ɗiyar Absalom; ta haifa masa Abiya, Attai, Ziza, da Shelomit.21Rehobowam yana ƙaunar Ma'aka, ɗiyar Absalom, fiye da dukkan matansa da ƙwaraƙwaransa (ya ɗauki mata sha takwas da ƙwaraƙwarai sittin, ya kuma zama mahaifin 'ya'ya maza ashirin da takwas da 'ya'ya mata sittin).
22Rehobowam ya naɗa Abiya ɗan Ma'aka ya zama basarake, shugaba a tsakanin 'yan'uwansa; yana tunanin maida shi sarki.23Rehobowam ya yi mulki da hikima; ya baza dukkan 'ya'yansa maza cikin dukkan ƙasar Yahuda da Benyamin zuwa kowanne tsararren birni. Ya kuma basu abinci a yalwace ya kuma nemo mataye da yawa domin su.

12

1Sai ya kasance, da mulkin Rehobowam ya kafu ya kuma yi ƙarfi, sai ya watsar da shari'ar Yahweh - da dukkan Isra'ila tare da shi.

2Ya faru a shekara ta biyar na sarki Rehobowam, Shishak, sarkin Masar, yazo gãba da Yerusalem, saboda mutanen sun yi rashin aminci ga Yahweh.3Yazo da karusai ɗari sha biyu da mahaya dawakai dubu sittin. Sojoji babu iyaka suka zo tare da shi daga Masar: Libiyawa, Sukkiyawa, da Kushiyawa.4Ya ƙwaci tsararrun birane da kena Yahuda ya kuma zo Yerusalem.
5Yanzu Shemayya annabi yazo wurin Rehobowam da shugabannin Yahuda da suka tattaru tare a Yerusalem saboda Shishak. Shemayya yace masu, "Wannan ne abin da Yahweh ya faɗa: Kun yashe ni, don haka nima na bayar daku cikin hannun Shishak."6Daga nan shugabannin Isra'ila da sarki suka ƙasƙantar da kansu suka kuma ce, "Yahweh mai adalci ne."
7Da Yahweh yaga cewa sun ƙasƙantar da kansu, maganar Yahweh tazo ga Shemayya, cewa, "Sun ƙasƙantar da kansu. Ba zan rusa su ba; zan ƙubutar da su na wani matsayi, fushina kuma ba zai zubo bisa Yerusalem ta hannun Shishak ba.8Duk da haka, zasu zama bayinsa, domin su fahimci bambanci tsakanin yi mani bauta da kuma bauta wa shugabannin sauran ƙasashen."
9Sai Shishak sarkin Masar yazo gãba da Yerusalem ya kuma ɗauke taskokin cikin gidan Yahweh, da taskokin cikin gidan sarki. Ya ɗauke komai da komai; ya ɗauke garkuwoyi ta zinariya da Suleman ya yi.10Sarki Rehobowam ya yi garkuwoyi na tagulla a mamadinsu ya miƙa su kuma cikin hannuwan ofisoshin tsaro, waɗanda ke tsaron ƙofofin zuwa gidan sarki.
11Sai ya kasance duk sa'ad da sarki ya shiga gidan Yahweh, matsaran zasu ɗauke su; daga nan zasu maido da su cikin gidan tsaro.12Da Rehobowam ya ƙasƙantar da kansa, fushin Yahweh ya juya daga gare shi, domin kada a lalatar da shi ɗungun; baya da haka, akwai sauran wasu abubuwan nagarta da ake samu cikin Yahuda.
13Sai sarki Rehobowam yasa sarautarsa tayi ƙarfi a Yerusalem, haka kuma ya yi mulki. Rehobowam na da shekaru arba'in da ɗaya sa'ad da ya fara mulki, ya kuma yi mulki shekaru sha bakwai a Yerusalem, birnin da Yahweh ya zaɓa daga dukkan kabilun Isra'ila saboda yasa sunansa a wurin. Sunan mahaifiyarsa Na'ama, Ba'ammoniya.14Ya aikata abin da ke mugunta, saboda bai kafa zuciyarsa ba domin ya biɗi Yahweh.
15Sauran al'amura kuwa game da Rehobowam, farko da ƙarshe, ba a rubuce suke ba a cikin rubuce-rubucen Shemayya annabi da Iddo mai dubawa, waɗanda kuma suke da lissafe - lissafen asaloli da ci gaba da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam?16Rehobowam ya yi barci da kakanninsa aka kuma binne shi cikin birnin Dauda; Abiya ɗansa ya zama sarki a gurbinsa.

13

1A cikin shekara ta sha takwas ta sarki Yerobowam, Abiya ya fara mulki bisa Yahuda.2ya yi mulki shekaru uku a Yerusalem; sunan mahaifiyarsa Ma'aka, ɗiyar Yuriyel na Gibiya. Aka yi yaƙi tsakanin Abiya da Yerobowam.3Abiya ya tafi cikin yaƙin da mayaƙa ƙarfafa, sojoji masu ƙarfin hali, zaɓaɓɓun mutane 400,000. Yerobowam yaja dagar yaƙi gãba da shi tare da zaɓaɓɓun mutane 800,000, ƙarfafa, sojoji masu ƙarfin hali.

4Abiya ya tsaya a tsaunin Zemarayim, wanda ke ƙasar tudu ta Ifraim, ya kuma ce, "Ku saurare ni, Yerobowam da dukkan Isra'ila!5Baku san cewa Yahweh, Allah na Isra'ila, ya bayar da mulki bisa Isra'ila ga Dauda ba har abada, gare shi da 'ya'yansa bisa tsararren alƙawari?
6Duk da haka Yerobowam ɗan Nebat, bawan Suleman ɗan Dauda, ya tashi da tawaye gãba da ubangijinsa.7Mutane marasa amfani, ƙasƙantattun jama'a, suka tattaru gare shi. Sun zo gãba da Rehobowam ɗan Suleman, duk da cewa Rehobowam yaro ne kuma bai da ƙwarewa kuma ba zai iya tsayayya da su ba.
8Yanzu kunce wai zaku iya ƙin ikon mulkin Yahweh cikin hannun zuriyar Dauda. Ku mayaƙa ne masu yawa, tare daku kuma akwai maruƙan zinariya da Yerobowam ya yi a matsayin alloli dominku.9Ba ku kuka kori firistocin Yahweh, zuriyar Haruna, da Lebiyawa ba? Ba kun naɗa wa kanku firistoci bisa ga ɗabi'ar mutanen sauran ƙasashe ba? Duk wanda yazo ya keɓe kansa da ɗan maraƙi da raguna bakwai zai zama firist na abubuwan da ba alloli ba.
10Amma mu kam, Yahweh ne Allahnmu, kuma bamu yashe shi ba. Muna da firistoci, zuriyar Haruna, suna bautar Yahweh, da Lebiyawa, waɗanda ke kan aikinsu.11Kowacce safiya da maraice suna ƙona wa Yahweh baye-baye na ƙonawa da turaren ƙamshi. Suna kuma shirya gurasar miƙawa a bisa tsastsarkan teburi; suna kuma lura da mazaunin fitila na zinariya tare da fitilunsu, domin su riƙa ci kowacce safiya. Muna kiyaye dokokin Yahweh, Allahnmu, amma kun yashe shi.
12Duba, Allah yana tare da mu a bisa kanmu, kuma firistocinsa suna nan tare da kãkãki domin su busa ƙara gãba daku. Mutanen Isra'ila, kada kuyi faɗa gãba da Yahweh, Allah na kakanninku, domin baza kuyi nasara ba."
13Amma Yerobowam ya shirya kwanto a bayansu; mayaƙansa suna gaban Yahuda, masu kwanton kuma a bayansu.14Da Yahuda suka waiga baya, duba, yaƙin yana gabansu kuma yana bayansu. Suka yi kuka ga Yahweh, firistocin kuma suka busa kãkãki.15Dagana mutanen Yahuda suka yi kuwwa; yayin da suka yi kuwwar, sai Allah ya mazge Yerobowam da dukkan Isra'ila a gaban Abiya da Yahuda.
16Mutanen Isra'ila suka guje daga gaban Yahuda, Allah kuma ya bayar da su cikin hannun Yahuda.17Abiya da mayaƙansa suka kashe su da babban yanka; zaɓaɓɓun mutane 500,000 na Isra'ila suka fãɗi matattu.18Ta wannan hanya, mutanen Isra'ila aka kayar da su a wannan lokaci; mutanen Yahuda suka yi nasara saboda sun dogara ga Yahweh, Allah na kakanninsu.
19Ya runtumi Yerobowam; Ya ɗauke birane daga gare shi: Betel da kauyukanta, Yeshana da ƙauyukanta, da Efron da ƙauyukanta.20Yerobowam bai taɓa sake samun iko ba a lokacin kwanakin Abiya; Yahweh ya buge shi, kuma ya mutu.21Amma Abiya ya zama cike da iko; ya ɗaukar wa kansa mata sha huɗu ya kuma zama mahaifin 'ya'ya maza ashirin da biyu da 'ya'ya mata sha shida.22Sauran ayyukan da Abiya ya aiwatar, ɗabi'arsa da maganganunsa an rubuta a cikin taƙaitaccen labarin Annabi Iddo.

14

1Abiya ya yi barci tare da kakanninsa, aka kuma bizne shi a cikin birnin Dauda. Asa, ɗansa, ya zama sarki a gurbin sa. A kwanakin sa ƙasar ta kasance shiru na shekaru goma.2Asa ya yi abin da kemai kyau da dai-dai a idanun Yahweh Allahnsa,3domin ya ɗauke bãƙin bagadai da wuraren tuddai. Ya farfasa ginshiƙan dutse ya kuma datse kafe-kafen Astarot.4Ya dokaci Yahuda su biɗi Yahweh, Allah na kakanninsu, su kuma aiwatar da shari'ar da dokokin.

5Haka kuma ya ɗauke wuraren tuddai da bagadan turare daga dukkan biranen Yahuda. Masarautar ta sami hutawa a ƙarƙashin sa.6Ya gina tsararrun birane a Yahuda, domin ƙasar ta kasance shiru, kuma ba shi da yaƙi a waɗannan shekaru, saboda Yahweh ya ba shi salama.
7Domin Asa ya cewa Yahuda, "Bari mu gina waɗannan birane muyi katangai kewaye da su, da hasumiyoyi, da ƙofofi, da ƙarafuna; ƙasar har wayau tamu ce, saboda mun biɗo Yahweh Allahnmu. Mun biɗo shi, kuma ya bamu salama ta kowanne gefe." Sai suka yi gini kuma suka yi nasara.8Asa na da mayaƙa da ke ɗaukar garkuwoyi da mãsu; daga Yahuda yana da mutane 300,000, daga kuma Benyamin, mutane 280,000 waɗanda ke ɗauke da garkuwoyi suna kuma jan bakkuna. Dukkan waɗannan ƙarfafa ne, mutane masu ƙarfin hali.
9Zera Bakushe yazo gãba da su tare da mayaƙa sojoji miliyan ɗaya da karusai ɗari uku; yazo Maresha.10Daga nan Asa ya fita domin ya gamu da shi, suka kuma kafa dãgar yaƙi a kwarin Zefata a Maresha.11Asa ya yi kuka ga Yahweh, Allahnsa, ya kuma ce, "Yahweh, babu wani sai kai da zai taimaki wanda ba shi da ƙarfi yayin da ya ke fuskantar masu yawa. Ka taimake mu, Yahweh Allahnmu, domin mun dogara gare ka, kuma a cikin sunanka munzo gãba da wannan babban taro. Yahweh, kai ne Allahnmu; kada ka bar mutum ya yi nasara da kai."
12Yahweh ya buge Kushiyawa a gaban Asa da Yahuda; Kushiyawa suka tsere.13Asa da sojojin da ketare da shi suka runtume su zuwa Gera. Kushiyawa da yawa suka fãɗi yadda basu iya murmurowa ba, domin an lalatar da su gaba ɗaya a gaban Yahweh da mayaƙansa. Mayaƙan suka kwashe ganima mai yawa.
14Mayaƙan suka hallakar da dukkan ƙauyukan da ke kewaye da Gera, domin fargaban Yahweh ya sauko bisa dukkan mazaunansu. Mayaƙan suka washe dukkan ƙauyukan, kuma akwai ganima da yawa a cikin su.15Mayaƙan kuma suka hallakar da rumfar zaman makiyaya mayawata; suka kwashe ganimar tumaki masu yawa, tare da raƙuma, sa'an nan suka koma Yerusalem.

15

1Ruhun Allah yazo bisa Azariya ɗan Oded.2Ya fita ya sami Asa ya kuma ce masa, "Ka saurare ni, Asa, da dukkan Yahuda da Benyamin: Yahweh yana tare da kai, yayin da kake tare da shi. Idan ka biɗe shi, zaya samu gare ka; amma idan ka yashe shi, zai yashe ka.

3Yanzu lokaci mai tsawo, Isra'ila basu tare da Allah na gaskiya, babu firist mai koyarwa, babu kuma shari'a.4Amma idan a cikin ƙuncinsu suka juya ga Yahweh, Allahnsu, suka kuma biɗe shi, sai ya samu a gare su.5A waɗannan lokuta babu salama ga wanda ya yi tafiyarsa zuwa wani wuri, ko wanda ya yi tafiya zuwa nan; maimako, manyan matsaloli na bisa dukkan mazauna ƙasashen.
6Aka karya su gutsu-gutsu, al'umma gãba da al'umma, birni kuma gãba da birni, domin Allah ya azabtar da su da dukkan wahalu iri - iri.7Amma ka ƙarfafa, kada kuma ka bar hannunka ya zama kasasshe, domin aikin ka zai sami sakamako."
8Sa'ad da Asa yaji waɗannan maganganu, anabcin Oded annabi, sai ya yi ƙarfin hali ya kori ƙazantattun abubuwa daga dukkan ƙasar Yahuda da Benyamin, daga kuma biranen da ya kame daga ƙasar tudu ta Ifraimu, ya kuma sake gina bagadin Yahweh, wanda ke gaban rumfar gidan Yahweh.9Ya tattaro dukkan Yahuda da Benyamin, da waɗanda ke zama tare da su - mutane daga na Ifraim da Manasse, daga kuma Simiyon. Domin sunzo daga Isra'ila zuwa gare shi babban taro, da suka ga cewa Yahweh Allahnsa na tare da shi.
10Sai suka tattaru tare a Yerusalem a cikin wata na uku, a cikin shekara ta sha biyar na mulkin Asa.11Suka yi hadaya ga Yahweh a wannan rana daga cikin ganimar da suka kawo: shanu ɗari bakwai da tumaki da awaki dubu bakwai.
12Suka shiga cikin alƙawari su biɗi Yahweh, Allah na kakanninsu, da dukkan zuciyarsu kuma da dukkan ransu.13Suka yarda da cewa duk wanda ya ƙi ya biɗi Yahweh, Allah na Isra'ila, za a kashe shi, ko da ƙarami ne ko babba, ko namiji ko mace.
14Suka yi rantsuwa ga Yahweh da babbar murya, tare da sowa, kuma da kãkãki da ƙahonni.15Dukkan Yahuda suka yi farinciki da alƙawarin, domin sun yi rantsuwa da dukkan zuciyarsu, suka kuma biɗi Allah da dukkan buƙatunsu, kuma ya samu a gare su. Yahweh ya basu salama a dukkan kewayensu.
16Ya kuma cire Ma'aka, kakarsa, daga zama sarauniya, domin tayi ƙazantaccen siffa daga wani ƙarfen Ashera. Asa ya datse ƙazantaccen siffar, ya niƙe shi zuwa turɓaya ya kuma ƙone shi a magudanar Kidron.17Amma bisan wurare ba a ɗauke su ba daga Isra'ila. Duk da haka Asa ya sadaukar da zuciyarsa gaba ɗaya dukkan kwanakinsa.
18Ya kawo cikin gidan Allah abubuwan mahaifinsa da abubuwansa wanda ke na Yahweh: Kayayyakin azurfa da zinariya.19Babu sauran yaƙi kuma har shekara talatin da biyar na mulkin Asa.

16

1Cikin shekara ta talatin da shida na mulkin Asa, Ba'asha, sarkin Isra'ila, ya nuna tsageranci gãba da Yahuda ya kuma gina Rama, domin kada ya bar wani ya tashi ko ya tafi ƙasar Asa, sarkin Yahuda.

2Daga nan Asa ya fito da azurfa da zinariya daga ɗakunan ajiya na cikin gidan Yahweh da gidan sarki, ya kuma aika su ga Ben Hadad sarkin Aram, wanda ke zama a Damaskus. Yace,3"Bari alƙawari ya kasance tsakani na da kai, kamar yadda ya kasance tsakanin mahaifi na da mahaifin ka. Duba, na aiko maka da azurfa da zinariya. Ka karya alƙawarinka da Ba'asha, sarkin Isra'ila, saboda ya rabu da ni."
4Ben Hadad ya saurari sarki Asa ya kuma aika da shugabannin mayaƙansa gãba da biranen Isra'ila. Suka kai hari ga Iyon, Dan, Abelmayim, da dukkan biranen ajiya na Naftali.5Sai ya kasance da Ba'asha yaji wannan, sai ya dena ginin Rama, ya kuma bar aikinsa ya tsaya.6Daga nan Asa sarki ya ɗauki dukkan Yahuda tare da shi. Suka ɗauke duwatsu da katakai daga Rama wanda Ba'asha ke ginin birnin da su. Daga nan nan sarki Asa ya ɗauki waɗannan kayan gini ya yi amfani da su ya gina Geba da Mizfa.
7A wannan lokaci Hanani mai gani ya tafi wurin Asa, sarkin Yahuda, ya kuma ce ma shi, "Saboda ka dogara ga sarkin Aram baka kuma dogara ga Yahweh Allahnka ba, mayaƙan sarkin Aram sun kuɓuce daga hannunka.8Kushiyawa da Libiyawa ba manyan mayaƙa ba ne, tare da karusai masu yawa da mahaya dawakai? Duk da haka, saboda ka dogara ga Yahweh, ya baka nasara a bisansu.
9Gama idanun Yahweh na dubawa ko'ina cikin dukkan duniya, domin ya nuna kansa mai karfi a madadin waɗanda zukatansu ke shiryayyu zuwa gare shi. Amma ka aikata wawanci a cikin wannan al'amari. Daga yanzu zuwa nan gaba, zaka sami yaƙi."10Daga nan Asa ya fusata da mai ganin; ya sanya shi cikin kurkuku, domin ya yi fushi da shi game da wannan al'amari. A dai-dai wannan lokacin kuma, Asa ya tsananta wa wasu daga cikin mutanen.
11Duba, ayyukan Asa, daga farko zuwa karshe, duba, an rubuta su cikin littafin sarakunan Yahuda da Isra'ila.12A cikin shekara ta talatin da tara na mulkinsa, Asa ya kamu da cuta a ƙafafunsa; cutarsa kuwa ta yi tsanani sosai. Duk da haka, bai nemi taimako ba daga Yahweh, amma daga masu magani kaɗai.
13Asa ya yi barci tare da kakanninsa; ya mutu a shekara ta arba'in da ɗaya na mulkinsa.14Suka bizne shi a nasa kabarin, wanda ya haƙa domin kansa a cikin birnin Dauda. Aka kwantar da shi cikin maɗauki da ke cike da ƙanshi mai daɗi da kayan ƙanshi daban-daban da ƙwararrun masu haɗa turare suka haɗa. Daga nan suka haɗa babbar wuta domin girmama shi.

17

1Yehoshafat ɗan Asa ya zama sarki a gurbinsa. Yehoshafat ya ƙarfafa kansa gãba da Isra'ila.2Ya sanya 'yan doka a cikin dukkan ƙarfafan biranen Yahuda, ya kuma kafa sansanai a cikin ƙasar Yahuda da cikin biranen Ifraim, waɗanda Asa mahaifinsa ya kame.

3Yahweh yana tare da Yehoshafat saboda ya yi tafiya cikin hanyoyin farko na mahaifinsa Dauda, bai kuma biɗi ba'aloli ba.4Maimako, ya dogara ga Allah na mahaifinsa, ya kuma yi tafiya cikin dokokinsa, ba bisa ga ɗabi'ar Isra'ila ba.
5Sai Yahweh ya tabbatar da mulkin a hannunsa; dukkan Isra'ila suka kawo haraji ga Yehoshafat. Yana da dukiya da daraja a yalwace.6Zuciyarsa ya sadaukar ga hanyoyin Yahweh. Ya cire wuraren tuddai da kafe-kafen Ashera daga Yahuda.
7A cikin shekara uku na mulkinsa ya aika da ofisoshinsa Benhayin, Obadiya, Zakariya, Netanel, da Mikaya, su koyar a cikin biranen Yahuda.8Tare da su kuma akwai Lebiyawa: Shemayya, Nataniya, Zebadiya, Asahel, Shemiramot, Yehonatan, Adoniya, Tobiya, da Tobadoniya; tare da su kuma akwai firistoci Elishama da Yehoram.9Suka koyar a Yahuda, suna da littafin shari'ar Yahweh tare da su. Suka yi yawo cikin dukkan biranen Yahuda suka kuma yi koyarwa a cikin mutanen.
10Fargabar Yahweh ya sauko bisa dukkan masarautun ƙasashen da kekewaye da Yahuda, har da ba su iya yaƙar Yehoshafat ba.11Wasu daga cikin Filistiyawa suka kawo kyautai ga Yehoshafat, da azurfa a matsayin haraji. Larabawa kuma suka kawo masa garkuna, raguna 7,700, da awaki 7,700.
12Yehoshafat ya zama cike da iko sosai. Ya gina tsararrun birane da wuraren ajiya a Yahuda.13Yana da kayan biyan buƙatu masu yawa a cikin biranen Yahuda, da sojoji - ƙarfafa, mutane masu ƙarfin hali - a Yerusalem.
14Ga lissafinsu an tsãra bisa ga sunayen gidajen ubanninsu: Daga Yahuda, shugabannin dubbai; Adna shugaba, tare da shi kuma mutanen yaƙi 300,000;15gaba da shi kuma Yehohanan shugaba, tare da shi kuma mutane 280,000;16gaba da shi kuma Amasiya ɗan Zikri, wanda ya miƙa kansa ya bautawa Yahweh da yardan ransa; tare da shi kuma mutanen yaƙi 200,000.
17Daga Benyamin: Eliyada cike da iko mutum mai ƙwazo, tare da shi kuma 200,000 shiryayyu da bakkuna da garkuwoyi;18gaba da shi kuma Yehozabad, tare da shi kuma 180,000 a shirye shiryayyu domin yaƙi.19Waɗannan ne waɗanda suka bauta wa sarki, baya ga waɗanda sarki ya sanya a tsararrun birane a cikin dukkan Yahuda.

18

1Yanzu Yehoshafat yana da dukiya da yawa da kuma girma; sai ya haɗa kai da Ahab ta wurin miƙa ɗaya daga cikin iyalinsa ya auri 'yarsa.2Bayan 'yan shekaru sai ya tafi wurin Ahab a Samariya. Ahab ya yanyanka tumaki da shanu masu yawa dominsa da kuma mutanensa da ketare da shi. Ahab yasa shi ya kai wa Ramot Giliyad hari tare da shi.3Ahab sarkin Isra'ila yace da Yehoshafat, sarkin Yahuda, "Ko za ka bini zuwa Ramot Giliyad?" Yehoshafat ya amsa masa, ni kamar ka ne, mutanena kuma kamar mutanenka ne; zamu kasance tare da kai a cikin yaƙin."

4Sai Yehoshafat yace da sarkin Isra'ila, "Na roƙe ka ka fara neman maganar Yahweh domin amsarka."5Daga nan sai sarki ya tattara dukkan annabawa tare har su ɗari huɗu sai yace da su, "Ko ma iya zuwa Ramot Gileyad yaƙi, ko kuwa kada mu je?" Suka ce, "Ka kai hari, domin Allah zai bada ita a hannun sarki."
6Amma Yehoshafat yace, "Babu wani annabin Yahweh da ba shi nan da zamu nemi shawara?"7Sarkin Isra'ila ya cewa Yehoshafat, "Har yanzu akwai wani da zamu nemi shawarar Yahweh, shi ne Mikaiya ɗan Imla, amma ina ƙinsa domin bai taɓa yi mini wani anabci mai kyau ba, amma kullum na mugunta ne." Amma Yehoshafat yace, "Bai kamata sarki ya faɗi haka ba."8Sai sarkin Israila ya kira hafsa yace, "Ka yi hanzari ka kawo Mikaiya ɗan Imla."
9To Ahab sarkin Isra'ila da Yehoshafat sarkin Yahuda na zaune a kujerar mulki kowannensu ya yi adonsa na sarauta a filin Allah a ƙofar shiga Yerusalem, kuma dukkan annabawa na zaune a gabansu.10Sai Zedekiya ɗan Kena'ana ya yi wa kansa ƙaho na ƙarfe ya ce"Yahweh ya faɗi wannan. Da wannan zaka rarraki Aremiyawa har sai an haɗiye su.11Duk annabawan suka yi annabci iri ɗaya suna cewa ka kai hari kan Ramot Gileyad kayi nasara, gama Yahweh ya bayar da ita a hannun sarki."
12Manzon da aka aika wurin Mikaiya ya yi magana da shi yace, "Duba, dukkan annabawa sun faɗi maganganu masu kyau game da sarki. Ina roƙonka kaima maganarka ta zama kamar tasu, ka faɗi abubuwa masu kyau."13Mikaiya ya amsa, "Na rantse da Yahweh abin da Allah ya faɗi shi zan faɗa."14Sa'ad da yazo wurin sarki, sarki ya ceda shi, "Mikaiya, ma iya zuwa Ramot Gileyad yaƙi, ko a'a?" Mikaiya ya amsa masa, "Ka kai hari ka kuma yi nasara! Domin zata zama babbar nasara."
15Sai sarki ya ceda shi, "Har sau nawa zan buƙace ka da ka rantse ka faɗa mini gaskiya da sunan Yahweh?"16To sai Mikaiya yace, "Na ga dukkan Isra'ila a warwatse a kan tuddai, kamar tumakin da basu da makiyayi, Yahweh kuma yace, 'Waɗannan basu da makiyayi. Bari kowanne mutum ya koma gidansa cikin salama.'"
17To sai sarkin Isra'ila ya ceda Yehoshafat, "Ashe ban faɗa maka cewa ba zai yi annabci mai kyau game da ni ba, amma sai na masifa?"18Sai Mikaiya ya ce yanzu dukkan ku sai ku ji maganar Yahweh: Na ga Yahweh zaune kan kursiyinsa, kuma dukkan rundunar sama na tsaye a gefen damansa da hagunsa.
19Yahweh yace, Wane ne zai yaudari Ahab, sarkin Isra'ila, domin ya haura ya faɗi a Ramot Gileyad?' Wannan ya ce haka wani kuma ya ce wancan.
20Daga nan sai wani ruhu ya sauko daga wurin Yahweh yace, 'zan ruɗe shi. 'Yahweh ya ceda shi ta yaya?'21Sai ruhun ya amsa, 'Zan je in zama ruhun ƙarya a bakin annabawansa dukka. Yahweh ya amsa, 'Zaka ruɗe shi, kuma zaka yi nasara. To yanzu sai ka tafi ka yi haka.'
22Yanzu duba, Yahweh yasa ruhun ƙarya a bakin annabawan nan naka, Yahweh kuma ya umarta masifa dominka."
23Sai Zedekiya ɗan Kena'aya, yazo gaba, ya mari Mikaiya a kunci, yace, "Ta wacce hanya Ruhun Yahweh ya barni har ya yi magana da kai?"24Mikaiya yace, "Duba za ka san haka a waccan ranar, lokacin da ka shiga lungun ɗaki domin ka ɓuya."
25Sarkin Isra'ila ya ceda wanɗansu bayi, "Ku je ku kama Mikaiya ku kai shi wurin Amon gwamnan birnin, da kuma Yowash, ɗana.26kuce da shi, 'Sarki ya ceka sa wannan mutum a kurkuku ka kuma ciyar da shi da 'yar gurasa da ɗan ruwa, har sai na dawo lafiya.'"27Sai Mikaiya ya cein har ka dawo lafiya to ba Yahweh ne ya yi magana ta wurina ba." Ya ƙara da cewa, dukkan ku mutane ku ji wannan."
28To sai Ahab, sarkin Isra'ila, da Yehoshafat, sarkin Yahuda, suka tafi yaƙi a Ramot Gileyad.29Sarkin Isra'ila ya ceda Yehoshafat, "Zan yi ɓadda kama in tafi yaƙin, amma kai sai ka sa rigunanka na sarauta." Sai sarkin Isra'ila ya yi ɓadda kama suka tafi yaƙin.30Shi kuma sarkin Aram ya bada umarni ga shugaban mayaƙan karusai cewa "Kada ya hari ƙananan mayaƙa sai dai sarkin Isra'ila kaɗai."
31Sai ya kasance bayan shugaban mayaƙan ya ga Yehoshafat sai yace, "Wancan sarkin Isra'ila ne." Sai suka juya domin su kai masa hari, amma Yehoshafat ya ƙwala ihu, Yahweh kuma ya taimake shi. Allah ya juyar da su daga binsa.32Bayan da shugabannin yaƙin suka gane ba sarkin Isra'ila bane sai suka juya suka dena fafararsa.
33Amma wani mutum ya ciro bakansa ya yi harbi a iska sai ya bugi sarkin Isra'ila a mahaɗar makamansa. Sai Ahab ya ceda mai tuƙa karusarsa, ka juya ka fitar da ni daga filin dãga, domin na sami mummunan rauni sosai."34Yaƙi ya yi zafi sosai a wannan rana, ana kuma riƙe da sarkin Isra'ila a cikin karusarsa da kefuskantar Aremiyawa har yamma. Can kusan faɗuwar rana, sai ya mutu.

19

1Yehoshafat sarkin Yahuda ya koma gidansa a Yerusalem lafiya.2Sai Yehu ɗan Hanani, mai duba yaje ya tare shi ya cewa sarki Yehoshafat, "Ko zaka dinga taimakon mugaye? Ko zaka ƙaunaci maƙiyan Yahweh? Domin wannan, fushi daga Yahweh na kanka.3Duk da haka akwai 'yan waɗansu halaye nagari a cikinka, domin kã kawar da sandunan Ashera daga ƙasar, ka kuma sa zuciyarka ga neman Allah."

4Yehoshafat ya zauna a Yerusalem; ya kuma sake yin tafiya cikin mutanen Biyarsheba zuwa ƙasar duwatsu ta Ifiraimu ya kuma komo da su ga Yahweh, Allah na ubanninsu.5Ya sa mahukunta a cikin ƙasar a cikin dukkan tsararrun biranen Yahuda, daga birni zuwa birni.
6ya ceda mahukuntan, "Ku yi la'akari da abin da zaku yi, domin ba saboda mutum kuke yin hukuncin ba, amma saboda Yahweh; yana tare daku a cikin zartar da hukunci.7Yanzu dai, sai ku bar tsoron Yahweh ya zauna a bisanku. Ku yi hankali a lokacin da kuke yin hukunci, domin babu laifofi ga Yahweh Allahnmu, kuma babu wata tara ko karɓar rashawa."
8Bugu da ƙari, a Yerusalem Yehoshafat ya naɗa waɗansu daga cikin Lebiyawa da firistoci da waɗansu shugabannin kakanni na gidajen Isra'ila, da su gudanar da hukunci domin Yahweh, da kuma sasanta saɓani. Suka zauna a Yerusalem.9Ya umarce su, da cewa, "Dole ku yi hidima cikin girmamawa ga Yahweh, da kuma aminci, da kuma dukkan zuciyarku.
10Duk inda akwai wani saɓani da ya zo gare ku daga ɗan'uwa da kezaune a birninsu, ko dai game da zubar da jini, ko game da dokokin da aka umarta, da sharuɗa da farillai, dole ku gargaɗe su kada su zama da laifi a gaban Yahweh, ko kuma fushi ya sauko maku daku da "yan'uwanku. Wannan zaku yi kuma ba zaku zama da laifi ba.
11Duba, Amariya babban firist shi ne shugabanku a kan dukkan al'amuran Yahweh. Zebadiya ɗan Isma'ila, shugaban gidan Yahuda, shi ne ke da ragamar duk abin da ya shafi sarki. Hakannan Lebiyawa zasu zama hafsoshi suna yi maku hidima. Ku yi ƙarfin hali ku kiyaye dokokin ku, Bari Yahweh kuma ya kasance da masu aikata nagarta."

20

1Sai ya kasance bayan wannan, sai mutanen Mowab da Ammon, da waɗansu Meyunawa suka kawo wa Yehoshafat yaƙi.2Sai waɗansu suka faɗa wa Yehoshafat cewa, "Babbar runduna na zuwa găba da kai daga hayin Mataccen Teku, daga Idom. Duba suna nan a Hazezon Tamar," wato Engedi.

3Sai Yehoshafat ya tsorata ya kuma ƙudurta ya nemi Yahweh. ya yi shelar azumi a cikin dukkan Yahuda.4Yahuda ta taru domin neman Yahweh; Suka zo su nemi Yahweh daga dukkan biranen Yahuda.
5Yehoshafat ya miƙe a cikin taron mutanen Yahuda da Yerusalem, a gidan Yahweh, a gaban sabon harabar.6ya ce"Yahweh Allah na ubanninmu, ba kai bane Allah a sama? Ba kai bane mai mulkin dukkan mulkokin al'ummai? Ƙarfi da iko naka ne, domin haka ba wanda zai iya yin tsayayya da kai.7Allahnmu ashe ba kai ka kori mazaunan wannan ƙasa ba daga gaban mutanen ka Isra'ila, ka kuma bada ita har abada ga zuriyar Ibrahim?
8Sun zauna a cikinta suka gina maka wuri mai tsarki a cikinsa da sunanka cewa,9'In wata masifa ta taso a kanmu - ko takobin hukunci, ko cuta, ko yunwa - zamu tsaya a gaban wannan gida, da kuma gabanka (domin sunanka na a cikin wannan gida), kuma zamu yi kuka zuwa gare ka a cikin ƙuncinmu, zaka kuma jimu ka kuma cece mu.'
10Duba yanzu, ga mutanen Ammon, da Mowab, da Tsaunin Seyir waɗanda baka bari mu hallakar da su ba a lokacin da suka fito daga ƙasar Masar; a maimakon haka, Isra'ila suka juya daga wurinsu basu kuma hallaka su ba.11Dubi yadda suke sãka mana; suna tafe domin su kore mu daga ƙasar da ka bamu gãdo.
12Allahnmu, ba zaka hukunta su ba? Domin bamu da ikon yin yaƙi da wannan babbar rundunar da kezuwa domin su yaƙe mu. Ba mu san abin da zamu yi ba, amma mun zuba ido gare ka."13Dukkan Yahuda suka tsaya a gaban Yahweh, duk da ƙananansu da matayensu, da yaransu.
14To a cikin tsakiyar tattaruwar, sai Ruhun Yahweh ya zo kan Yahaziyel, ɗan Zakariya, ɗan Benaiya, ɗan Yeyel, ɗan Mataniya, Balebi, ɗaya daga cikin 'ya'yan Asaf.15Yahaziyel yace, "Ku saurara, ku dukkan Yahuda da mazaunar Yerusalem, da sarki Yehoshafat. Wannan shi ne abin da Yahweh ya faɗa maku, ' Kada kuji tsoro; kada ku karaya saboda girman wannan babbar rundunar, domin yaƙin ba naku bane na Allah ne.
16Dole ne kuje ku yaƙe su gobe. Duba suna zuwa ta mashigin Ziz. Zaku same su a ƙarshen kwari kafin hamadar Yeruwel.17Ba zaku bukaci ku yi faɗa ba a wannan yaƙin. Ku tsaya a wurarenku, ku tsaya ku jira, ku ga ceton Yahweh tare daku, Yahuda da Yerusalem. Kada ku tsorata ko ku karaya. Kuje ku hare su gobe, domin Yahweh yana tare daku.'"
18Yehoshafat ya sunkuyar da kansa ƙasa. Dukkan Yahuda da mazauna Yerusalem suka faɗi a gaban Yahweh, suna yi masa sujada.19Da Lebiyawa, na zuriyar Kohatiyawa, suka miƙe suka yabi Yahweh, Allah na Isra'ila, da babbar murya.
20Da sassafe suka tashi suka tafi hamadar Tekowa. A lokacin da suka fita, Yehoshafat ya tashi tsaye yace, "Ku saurare ni Yahuda da ku mazauna Yerusalem! Ku dogara ga Yahweh Allahnku, zaku sami kafuwa. Ku dogara ga annabawansa, zaku yi nasara."21Bayan da ya tuntuɓi mutane, sai ya naɗa waɗanda zasu raira yabo ga Yahweh su ba shi waƙar yabo domin ɗaukakarsa mai tsarki, a lokacin da suka tafi suna tunkarar sojoji, suka ce, "Ku yi godiya ga Yahweh, domin alƙawarin amincinsa ya tabbata har abada."
22Sa'ad da suka fara waƙar yabo, sai Yahweh yasa masu kwanto gãba da mutanen Ammon, da Mowab, da Tsaunin Seyir waɗanda ke zuwa domin su kawo hari ga Yahuda, aka yi nasara da su.23Domin mutanen Ammon da Mowab suka fita suka yaƙi mazaunan Tsaunin Seyir, suka karkashe su suka hallakar da su. Bayan sun hallaka mazaunan Tsaunin Seyir. Sai duk suka taimaka wajen hallaka junansu.
24Sa'ad da Yahuda suka zo su dudduba hamada sai suka dubi sojojin. Duba, sun fãɗi ƙasa matattu; ba wanda ya tsira.
25Yehoshafat da dukkan mutanensa suka zo domin su kwashi ganima daga gare su, sai suka sami kayayyakin da aka yi watsi da su, da tufafi, da abubuwa masu daraja, waɗanda suka ɗebar wa kansu, fiye da yadda zasu iya ɗauka. Ya ɗauke su kwana uku kafin su iya kwashe ganimar, domin akwai ta birjik.26A rana ta huɗu sai suka taru a kwarin Beraka. A can suka yabi Yahweh, domin haka ake kiran sunan wurin "Kwarin Beraka" har ya zuwa yau.
27Daga nan sai suka juya, dukkan mutanen Yahuda da na Yerusalem, Yehoshafat kuma yana yi masu jagora, suka sake koma Yerusalem da farinciki, domin Yahweh ya sake sa su suyi murna a kan maƙiyansu.28Suka zo Yerusalem zuwa gidan Yahweh da garayu, da molo, da kãkãki.
29Razanar Allah ta kama dukkan mulkokin al'ummai sa'ad da suka ji Yahweh ya yaƙi maƙiyan Isra'ila.30Ta haka mulkin Yehoshafat ya zama da kwanciyar hankali, domin Allahnsa ya ba shi salama a dukkan yankunansa.
31Yehoshafat ya yi mulkin Yahuda: Yana da shekaru talatin da biyar a lokacin da ya fara sarauta, ya kuma yi mulkin Yerusalem na tsawon shekaru ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa Azuba, 'yar Shilhi.32ya yi tafiya bisa tafarkin Asa, mahaifinsa, bai kuma juya ya barsu ba; ya yi abin da keda kyau a gaban Yahweh.33Duk da haka, ba a ɗauke wuraren tuddai ba. Mutanen basu juyar da zukatansu ga Allah na kakanninsu ba.
34A kan kuma sauran abubuwa game da Yehoshafat, farko da ƙarshe, duba an rubuta su a cikin tarihin Yehu ɗan Hanani, wanda aka rubuta a cikin littafin sarakunan Isra'ila.
35Bayan wannan Yehoshafat, sarkin Yahuda, ya haɗa kai da Ahaziya, sarkin Isra'ila, wanda ya yi aikin ƙeta sosai.36Ya haɗa kai da shi domin ya yi jiragen ruwa domin zuwa Tarshish. Sun kafa jiragen a Eziyon Geba.37Daga nan sai Eliyeza ɗan Dodabahu na Maresha, ya yi annabci gãba da Yehoshafat; ya ce"Saboda ka haɗa kanka da Ahaziya, Yahweh ya rushe ayyukanka." Sai aka ragargaje jiragen domin kada a iya tafiya.

21

1Yehoshafat ya yi barci tare da kakanninsa aka binne shi tare da su a birnin Dauda; Yehoram, ɗansa, ya zama sarki a madadin sa.2Yehoram na da 'yan'uwa, ga 'ya'yan Yehoshafat: Azariya, Yehiyel, Zekariya, Azariyahu, Mika'ilu da Shefatiya. Dukkan waɗannan 'ya'yan Yehoshafat ne sarkin Isra'ila.3Mahaifinsu ya basu kyautar zinariya da azurfa masu ɗumbin yawa da sauran kayayyaki masu daraja, da ƙayatattun birane a Yahuda, amma sai ya bada gadon sarauta ga Yehoram, saboda shi ne ɗan fari.

4To lokacin da Yehoram ya gãji mahaifinsa a sarauta ya kuma kafa kansa sosai a matsayin sarki, sai ya karkashe dukkan 'yan'uwansa da takobi, haka kuma da shugabannin Isra'ila da ban da ban.5Yehoram na da shekaru talatin da biyu lokacin da ya fara mulkin, ya kuma yi mulki a Yerusalem na tsawon shekaru takwas.
6ya yi tafiya bisa tafarkin sarakunan Isra'ila, kamar yadda gidan Ahab ya yi, domin ya auri ɗiyar Ahab ta zama matarsa sai ya yi mugun abu a gaban Yahweh.7Duk da haka Yahweh bai so ya hallakar da gidan Dauda ba saboda alƙawarin da ya yi da Dauda; ya yi alƙawarin cewa kullum zai ba da rai a gare shi da kuma zuriyarsa.
8A kwanakin Yehoram, Idom ta ɓalle daga mulkin Yahuda, suka kuma naɗawa kansu sarki.9Daga nan sai Yehoram da jarumawansa suka ƙetara da karusansa. Da duhu ya tashi ya yaƙi Idomawan da suka kewaye shi da dukkan jarumawan karusansa.10Ta haka Idom ta ci gaba da tayar wa Yahuda har wa yau. Libna ita ma sai ta tayar a lokaci guda, domin Yehoram ya rabu da Yahweh, Allah na kakanninsa.
11Haka kuma, Yehoram ya gina manyan wurare a duwatsun Yahuda yasa mazaunan Yerusalem su yi rayuwa kamar karuwai, ya kuma karkatar da Yahuda.
12Wasiƙa daga annabi Iliya ta zo ga Yehoram. Cewa, "Wannan shi ne abin da Yahweh, Allah na Dauda mahaifinka, ya ce: Saboda baka yi tafiya bisa tafarkin Yehoshafat mahaifinka ba, baka kuma bi tafarkin Asa sarkin Yahuda ba,13amma ka bi tafarkin sarakunan Isra'ila, ka kuma sa Yahuda da mazauna Yerusalem su zama kamar karuwai, kamar yadda gidan Ahab suka yi-saboda kuma ka kashe 'yan'uwanka a cikin iyalin mahaifinka ko mariƙa takobi da suka fi ka shahara-14Duba, Yahweh zaya kawo wa mutanenka da matanka da 'ya'yanka da mallakarka babbar annoba.15Kai kuma da kanka ka zama da matsananciyar cuta saboda cutar da kecikin hanjinka, har sai hanjinka ya fito waje saboda cutar, kwana bayan kwana."
16Yahweh ya tayar da ruhun Filistiyawa da na Larabawa gãba da Yehoram waɗanda ke kusa da Kush.17Suka kawo wa Yahuda hari, suka washe ta, suka kwashe dukkan wadatarta da suka samu a gidan sarki. Suka kuma kwashe 'ya'yansa da matansa. Basu bar masa ko ɗa ɗaya ba sai dai Yehowahaz, ƙaramin ɗansa.
18Bayan duk waɗannan, Yahweh ya buge shi a hanjinsa da cuta mara warkewa.19Sai ya kasance a lokacin a ƙarshen shekaru biyu, sai hanjinsa ya fito saboda rashin lafiyarsa, sai ya mutu ta wurin matsananciyar cuta. Mutanensa basu yi wata wata domin girmama shi ba kamar yadda suke yi wa kakanninsa.20Ya fara sarauta a lokacin da yake da shekaru talatin da biyu; ya yi mulkin Yerusalem na tsawon shekaru takwas, sai ya mutu ba tare da makoki ba. Suka binne shi a birnin Dauda, amma ba a maƙabartar sarakuna ba.

22

1Mazauna Yerusalem suka naɗa Ahaziya sarki, wato ƙaramin ɗan Yehoram sarki, a madadinsa, domin rundunonin Larabawa sun kashe dukkan manyan 'ya'yansa. Domin haka Ahaziya ɗan Yehoram sarkin Yahuda ya zama sarki.2Ahaziya na da shekaru ashirin da biyu a lokacin da ya fara sarauta; ya yi mulkin Yerusalem shekara ɗaya. Sunan mahaifiyarsa Ataliya; ita 'yar Omri ce.3Shi ma ya bi tafarkin Ahab domin mahaifiyarsa ce ke ba shi shawara a cikin yin ayyukan mugunta.

4Ahaziya ya yi abin mugunta a gaban Yahweh, kamar yadda gidan Ahab suka yi, domin su ne mashawartansa bayan mutuwar mahaifinsa zuwa hallakarsa.5Hakanan ya bi shawararsu; ya yi tafiya tare da Yerom ɗan Ahab, sarkin Isra'ila, domin su kai hari ga Hazzaiyel, sarkin Aram, a Ramot Gileyad. Aremiyawa suka yi wa Yoram rauni. `
6Yoram ya komo domin ya warke daga raunukan da suka ji masa a Rama, lokacin da ya fita ya yi yaƙi da Hazeyel, sarkin Aram. Domin haka Ahaziya ɗan Yehoram sarkin Yahuda ya tafi can Yezril domin ya ga Yoram ɗan Ahab, domin an raunata Yoram.
7To an kawo hallakar Ahaziya daga Allah a ziyarar da Ahaziya ya kai wa Yoram. A lokacin da ya isa, sai ya tafi tare da Yehoram domin su kai hari ga Yehu ɗan Nimshi, wanda Yahweh ya zaɓa ya hallakar da gidan Ahab.8A lokacin da Yehu ke aiwatar da hukuncin Allah a kan gidan Ahab, sai ya tarar da shugabannin Yahuda da kuma 'ya'yan ɗau'uwan Ahaziya suna yi wa Ahaziya hidima. Sai Yehu ya kashe su.
9Yehu ya nemi Ahaziya, suka kama shi yana ɓoye a Samariya, sai suka kawo shi wurin Yehu, suka kashe shi. Sai suka binne shi, domin sun ce, "Shi ɗan Yehoshafat ne, wanda ya nemi Yahweh da dukkan zuciyarsa." Domin haka gidan Ahaziya ba shi da sauran iko yin sarautar mulkin.
10Yanzu bayan Ataliya, ta ga cewa ɗanta ya mutu, sai ta tashi ta kashe dukkan 'ya'yan sarauta a cikin gidan Yahuda.11Amma Yehosheba, ɗiyar sarki, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya a asirce ta ware shi da ban da sauran 'ya'ya maza na sarki waɗanda ake shirin kashewa. Ta sa shi da kuma mai renon shi a ɗakin kwana. Da haka Yehosheba 'yar sarki Yehoram, matar Yehoida firist (domin ita 'yar'uwar Ahaziya ce) sai ta ɓoye shi daga Ataliya domin kada Ataliya ta kashe shi.12Yana tare da su a gidan Allah har tsawon shekaru shida, bayan Ataliya ta yi mulkin ƙasar.

23

1A shekara ta bakwai, Yehoyida ya nuna ƙarfinsa ya shiga alƙawari da shugabannin ɗari-ɗari, Azariya ɗan Yeroham, da Isma'ila ɗan Yehohanan, da Azariya ɗan Obed, Ma'asiya ɗan Adayiya, da Elishafat ɗan Zikri.2Suka zazzaga Yahuda suka tattara Lebiyawa daga dukkan biranen Yahuda, da kuma shugabannin kabilu na gida-gidan Isra'ila sai suka zo Yerusalem.3Dukkan taron mutanen suka yi alƙawari da sarki a gidan Allah. Yehoyida ya ce da su, Duba ɗan sarki ne zai yi mulki, kamar yadda Yahweh ya faɗi game da zuriyar Dauda.

4Wannan ne abin da dole zaku yi: kashi uku na firistoci da Lebiyawa da suka zo yin hidima a ranar Asabar, zasu zama masu tsaro a ƙofofi.5Kashi uku kuma su tsaya a fadar sarki, kashi uku kuma a wurin da aka kafa harsashin ƙofa. Dukkan mutane zasu kasance a harabar gidan Yahweh.
6Kada ku bar kowa ya shiga haikalin Yahweh sai dai firistoci da Lebiyawan da keyin hidima kai ɗai. Zasu shiga domin an keɓe su, amma sauran dole ne su yi biyayya da umarnin Yahweh.7Dole ne Lebiyawa su kewaye sarki, kowanne na riƙe da makami a hannunsa. Duk wanda ya shigo gidan kuma sai a kashe shi. "Ku tsaya wurin sarki a lokacin da ya shigo da kuma lokacin da ya fita."
8To sai Lebiyawa da dukkan Yahuda suka yi kamar yadda Yehoyida firist ya umarta. Kowannen su ya ɗauki mutanensa, masu zuwa domin su yi hidima a ranar Asabar, da kuma waɗanda ba zasu yi hidima a ranar Asabar ba, domin Yehoyida firist bai sallami kowacce runduna ba tukuna.9Sai Yehoyida firist ya kawo masu da manya da ƙananan garkuwoyi da sarki Dauda ya ajiye a gidan Allah ya ba kwamandojin.
10Yehoyida ya sanya dukkan sojojin, kowanne mutum da makaminsa a hannusa, daga sashen dama na haikalin zuwa sashen hagu na haikalin, kusa da bagadin da kuma haikalin, zagaye da sarkin.11Sai suka fito da ɗan sarki suka sa masa rawani suka kuma bashi kundin dokoki na alƙawari, suka naɗa shi sarki daga nan sai Yehoyida firist da 'ya'yansa suka keɓe shi ya zama sarki suka ce, "Ranka ya daɗe sarki."
12Lokacin da Ataliya ta ji hayaniyar mutanen suna yabon sarki sai ta zo cikin mutane ta shiga haikalin,13ta na dubawa sai ga sarki tsaye kan dakalin sarauta riƙe da sandar sarauta a ƙofar shiga, ga kuma kwamandoji da masu hura kakaki kewaye da sarki. Dukkan mutanen ƙasar na murna suna busa kakaki, mawaƙa suna kaɗa kayan kaɗe-kaɗe suna kuma bida waƙoƙin yabo. Sai Ataliya ta keta tufafinta tana cewa, "Cin amana! Cin amana!"
14Daga nan sai Yehoyida ya ce da kwamandojin ɗari-ɗari su zo su fito da ita a kashe ta da takobi tare da duk waɗanda suka biyo ta. domin firist ya ce, "Kada ku kashe ta a cikin gidan Yahweh".15To sai suka buɗa mata hanya ta bi ta Ƙofar Doki zuwa gidan sarki a can suka kashe ta.
16To sai Yehoaida da sarki da dukkan mutanen suka yi alƙawari cewa za su zama mutanen Yahweh.17Sai dukkan mutanen suka tafi gidan Ba'al suka rushe shi, suka ɓaɓɓalle bagadin Ba'al da kuma gunkinsa. Suka kashe matan firist na Ba'al a gaban waɗanan bagadan.
18Yehoyida ya zaɓi shugabannin haikalin Yahweh ta wurin jagorancin firistoci, da ke Lebiyawa waɗanda Dauda ya sa domin su yi hidima a gidan Yahweh, domin su miƙa hadaya ta ƙonawa ga Yahweh tare da farinciki kamar yadda Dauda ya yi umarni, kamar yadda ya ke a rubuce a shari'ar musa.19Yehoyida ya sa 'yan tsaro a ƙofar haikalin Yahweh, domin kada duk wani marar tsarki ta kowanne fanni ya shiga.
20Yehoyida ya kwashi kwamandoji da mutane ma su daraja da gwamnoni tare da shi da dukkan mutanen ƙasar. Ya kawo sarki daga gidan Yahweh, mutane suka shiga ta babbar ƙofa zuwa gidan sarki daga gidan suka zaunar da sarki akan gadon sarauta.21domin haka dukkan mutanen ƙasar suka yi murna birnin kuma ya sami kwanciyar hankali. Ataliya kuma aka kashe ta da takobi.

24

1Yowash yana da shekaru bakwai lokacin da ya fara mulki, ya yi mulki na tsawon shekaru arba'in a Yerusalem, sunan mahaifiyarsa Zibiya, daga Biyasheba.2Yoash ya yi abin da kenagari a gaban Yahweh a dukkan kwankin Yehoyida, firist.3Yehoyida ya aura masa mata biyu, sai ya zama uba na 'ya'ya maza da mata.

4Bayan wannan Yowash ya yanke shawarar gyara gidan Yahweh.5Sai ya tara firistoci da Lebiyawa ya ce da su, "Kowacce shekara sai ku je cikin dukkan biranen Yahuda ku tattaro kuɗin da za a gyara gidan Allahnku daga dukkan mutanen Isra'ila. Ku tabbata kun fara yanzu." Lebiyawa basu yi komai ba da farko.
6Sai sarki ya kirawo Yehoyida babban firist ya ce da shi, "Meyasa baka bukaci Lebiyawa su kawo haraji daga Yahuda da kuma Yerusalem ba kamar yadda Musa bawan Yahweh da kuma taron Isra'ila suka yi ba domin rumfar alƙawarin dokoki ba?"7Domin 'ya'ya maza na Ataliya wannan muguwar mata, sun rushe gidan Allah suka kuma kwashe dukkan kayayyaki masu tsarki na gidan Yahweh suka kai suka bayar ga Ba'al.
8To sai sarki ya umarta, suka yi taska suka sa ta daga wajen ƙɔfar shiga gidan Yahweh.9Sai suka yi shela a cikin dukkan Yahuda da Yerusalem domin mutane su biya haraji domin gidan Yahweh harajin da Musa bawan Allah ya sa wa Isra'ila a jeji.10Dukkan shugabanni da dukkan mutane suka yi murna suka kawo kuɗi suka sa a taska har sai da suka cika ta.
11To bayan an kawo taskar wurin fadawan sarki ta hannun Lebiyawa duk lokacin da suka ga taskar ta cika da kuɗi sosai a cikinta, marubutan sarki da manyan firistoci su kan zo, su ɗauke ta su kwashe sai su mayar da ita wurin da ta ke. Haka suka dinga yi kowacce rana, suka dinga tara kuɗaɗe masu yawa.12Sai sarki da Yehoyida suka ba da kuɗaɗen ga masu yin aikin hidima a gidan Yahweh. Waɗannan mutanen suka yi hayar masu aikin dutse da masu aikin katako domin su komo da gidan Yahweh, haɗe da masu aikin ƙarfe da tagulla.
13To sai ma'aikatan, suka gudanar da aikin ta hannuwansu; suka tayar da gidan Yahweh suka komar da shi kamar yadda ya ke da farko, suka kuma ƙarfafa shi.14Bayan sun gama sai suka mayar da sauran kuɗin ga sarki da kuma Yehoyida. Wannan kuɗin da shi aka yi aikin kujerun gidan Yahweh, da kayayyaki wanda aka mora domin karɓar baiko- cokula da kayayyaki na zinariya da azurfa. Suka yi ta miƙa baye-baye na ƙonawa a gidan Yahweh a dukkan kwanakin Yehoyida.
15Yehoyida ya tsufa yana da cikkakun kwanaki, ya mutu yana da shekaru 130.16Suka binne shi a birnin Dauda a cikin sarakuna, saboda ya yi abu mai kyau a Isra'ila, a gaban Allah da kuma gidan Allah.
17To yanzu kuma bayan mutuwar Yehoyida, mutanen Yahuda suka zo domin su nuna karramawa ga sarki. Sai sarki ya saurare su.18Suka yi watsi da gidan Yahweh, Allah na kakanninsu suka bautawa gumakan Ashera da siffofinta. Fushin Allah ya auko kan Yahuda da Yerusalem saboda wannan aikin na su mara dacewa.19Duk da haka ya aiko annabawa gare su domin su sake komo da su gare shi, annabawan suka ce Yahweh na gãba da mutanen, amma suka ƙi saurara.
20Sai Ruhun Allah ya zo kan Zakariya ɗan Yehoyida, firist; Zakariya ya miƙe a sama da mutanen ya ce da su, "Allah ya faɗi wannan: Me yasa ku ke aikata laifofi ga dokokin Yahweh, domin kada ku azurta? Da yake kun yi watsi da Yahweh, shima ya yi watsi da ku.21"Amma suka yi masa maƙarƙarshiya; sarki ya umarta a jejjefe shi da duwatsu a dandalin gidan Yahweh.22Ta irin wannan hali Yowash, sarki, ya jahilci kirkin da Yehoyida mahaifin Zakariya ya yi masa. A memakon haka ya kashe ɗan Yehoyida. Lokacin da Zakariya ke mutuwa ya faɗi cewa, "Dãma Yahweh ya ga wannan ya kuma sa ka bada lissafi."
23To bayan kusan ƙarshen shekara, sai sojojin Aram suka tasarwa Yowash. Suka zo Yahuda da Yerusalem; suka kashe dukkan shugabannin mutane suka kuma kwashe dukkan ganimarsu zuwa ga sarkin Damaskus.24Sojojin Armeniyawa kuma suka zo da ƙaramar rundunar soja, amma Yahweh ya ba su nasara kan babbar rundunar soja, domin Yahuda ta yi watsi da Yahweh na kakanninsu. Allah na kakanninsu. Da haka Armeniyawa suka kawo hukunci a kan Yowash.
25A lokacin da Armeniyawa suka fice, an yi wa Yowash mummunan rauni. Bayinsa suka yi masa maƙarƙashiya saboda ya kashe Zakariya ɗan Yehoyida, firist. Suka kashe shi a kan gadonsa; suka binne shi a birnin Dauda, amma ba a maƙabartar sarakuna ba.26Waɗannan su ne mutanen da suka yi masa maƙarƙashiya: Zabad ɗan Shimeyat mace Ba'ammoniya, da Yehozabad ɗan Shimrit, mace Bamowabiya.
27To lissafin 'ya'yansa, da kuma annabci mai muhimmanci da aka yi a kansa, da kuma sake gina haikalin Allah, duba an rubuta su a cikin Littafin shashi akan sarakuna. Sai Amaziya ɗansa, ya zama sarki a madadinsa.

25

1Amaziya yana da shekaru ashirin da biyar a lokacin da ya fara sarauta; ya yi sarauta ta shekaru ashirin da tara a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddan ta Yerusalem.2ya yi abin da kemai kyau a gaban Yahweh, amma ba da cikakkiyar miƙa zuciya ba.

3Sai ya zamana nan da nan bayan mulkinsa ya kafu sai ya kashe bayin da suka kashe mahaifinsa, sarki.4Amma bai kashe 'ya'yan waɗanda suka yi kisan kan ba. Amma ya yi kamar yadda aka rubuta cikin shari'ar Musa, kamar yadda Yahweh ya umarta, "Dole ne iyaye ba zasu taɓa mutuwa ba saboda 'ya'ya, ko 'ya'ya su mutu saboda iyayensu ba, a maimakon haka, kowa zai ɗauki alhakin zunubinsa."
5Bugu da ƙari, Amaziya ya tattara mutanen Yahuda ya yi masu ƙidaya bisa ga kabilar kakanninsu, a ƙarƙashin jagorancin shugabannin dubu-dubu da na ɗari-ɗari da dukkan Yahuda da Benyamin. Ya ƙirga su daga 'yan shekaru ashirin zuwa sama, ya sami mutane kusan 300,000 zaɓaɓɓu domin yaƙi waɗanda zasu iya riƙe mashi da garkuwa.6Hakannan ya yi hayar mayaƙa 100,000 daga Isra'ila akan kuɗi azurfa ɗari ɗaya.
7Amma sai mutumin Allah ya zo gunsa ya ce masa "Sarki kada ka bari mutanen Israi'la domin Yahweh ba ya tare da Isra'ila - ba ko ɗaya daga cikin mutanen Ifiraimu,8Amma ko dama a ce kana da ƙarfi na yi yin yaƙin Ubangiji zai rikirtar da kai a gaban maƙiya, domin Yahweh ya na da ikon taimako yana kuma da ikon rushewa."
9Amaziya ya ce da mutumin Allah, "Amma me za muyi da talanti ɗari dana ba sojojin Isra'ila?" Mutumin Allah ya amsa da cewa "Yahweh zai iya baka fiye da wannan."10To sai Amaziya ya rarraba sojojin da suka zo daga Ifiraimu; ya sake aika su gida. Fushinsu ya yi zafi sosai a kan Yahuda, suka koma gida da matsanancin fushi.
11Amaziya ya yi ƙarfin hali har ya tafi da mutanensa zuwa Kwarin Gishiri; a can ya karkashe sojojin Seyir guda dubu goma.12Sojojin Yahuda kuma suka kama sojoji duba goma da ransu. Suka kai su can ƙonƙolin tsauni suka tutturo su ƙasa duk suka kakkarye.
13Amma sojojin da Amaziya ya komar da su domin kada su je yaƙi tare da shi, suka je suka kai hari a Yahuda daga Samariya har zuwa Betahoron. Suka kashe mutane dubu uku suka kuma kwashi ganima mai yawa.
14Sai ya zamana, bayan Amaziya ya dawo daga kisan Idomawa, sai ya kwaso allolin Seyir ya maida su allolinsa. Ya russuna masu ya kuma ƙona masu turare.15Domin haka fushin Yahweh ya yi ƙuna a kan Amaziya. Ya aika masa da saƙo ta hannun annabi cewa, "Meyasa ka je ka tuntuɓi allololin da basu iya ceton mutanensu daga hannunka ba?"
16To lokacin da annabin keyi masa magana, sarki ya ce da shi, "Ko mun maida kai mashawarcin sarki ne? Ka bari! donme za a kashe ka?" Daga nan sai annabin ya bari ya ce na sani Allah ya yi ƙudiri na hallakar da kai saboda ka yi waɗannan abubuwa ba ka kuma ji shawarata ba."
17To sai Amaziya sarkin Yahuda ya tuntuɓi mashawartansa ya aika da 'yan saƙo zuwa ga Yehowash ɗan Yehoyahaz ɗan Yehu, sarkin Isra'ila, cewa, "Ka zo mu sadu da juna fuska da fuska a cikin yaƙi."
18Amma Yehowash sarkin Isra'ila ya aika da 'yan saƙo ga Amaziya sarkin Yahuda, cewa, "Ɗan ƙaramin sassabe da kea Lebanon ya aika da saƙo ga itacen sida a Lebanon, cewa, "Ka bada 'yarka ga ɗana a matsayin mata; amma sai dabbar daji a Lebanon ta zo ta tattake ɗan sassaben.19Ka kuma ce, duba na rugurguje Idom; amma zuciyarka ta kumburaka. Ka yi taƙama da ɗaukakarka, amma ka tsaya a gida, gama donme zaka jawo wa kanka masifa da faɗuwa, kai da Yahuda tare da kai?"
20Amma Amaziya ba zai saurara ba, domin wannan al'amarin daga Allah ne, domin ya miƙa Yahuda ga hannun maƙiyanta, domin sun nemi shawara daga allolin Idom.21To sai Yowash sarkin Isra'ila ya kai hari; shi da Amaziya, sarkin Yahuda, suka gamu fuska da fuska a Betshemesh, wadda take mallakar Yahuda.22A ka ragargaza Yahuda a idon Isra'ila kowa kuma ya tsere gida.
23Yehowash, sarkin Isra'ila, ya kame Amaziya ɗan Yehowash ɗan Ahaziya, sarkin Yahuda, a Betshemesh. Ya kawo shi Yerusalem daga Ifiraimu ya kuma rushe ganuwar Yerusalem daga ƙofar Ifiraimu zuwa kusurwar ƙofar, tsawon kamu ɗari huɗu ne.24Ya kwashe dukkan zinariya da duk abubuwan da ya iske a gidan Allah da Obida da Idom, da kuma abubuwa masu daraja na gidan sarki, tare da kamammun yaƙi, sai ya koma Samariya.
25Amaziya ɗan Yowash Sarkin Yahuda ya yi mulki na tsawon shekaru sha biyar yana mulkin Yahuda bayan mutuwar Yehoyash, ɗan Yehoyahaz, sarkin Isra'ila.26Game da sauran ayyukan Amaziya na farko da na ƙarshe duba an rubuta su a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda da Isra'ila.
27Yanzu tun daga lokacin da Amaziya ya juya wa Yahweh baya, sai suka fara shirya masa maƙarƙashiya a Yeruslem. Sai ya gudu zuwa Lakish suka kashe shi a can.28Suka komo da shi a kan dawakai suka binne shi a maƙabartar kakanninsa a birnin Yahuda.

26

1Dukkan mutanen Yahuda suka ɗauki Uziya lokacin ya na ɗan shekara sha shida suka naɗă shi sarki a madadin babansa Amaziya.2Shi ne wanda ya sake gina Ilat ya sake komo da ita Yahuda. Bayan wannan sai ya mutu tare da kakanninsa.3Uziya yana da shekara sha shida lokacin da ya fara sarauta. ya yi mulki na tsawon shekaru hamsin da biyu a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya; ita daga Yerusalem ce.

4ya yi abin da kemai kyau a gaban Yahweh, ya bi misalin mahaifinsa, Amaziya, ta kowanne abu.5Yasa kansa ga tafarkin neman Allah a kwanakin Zakariya, wanda ya bashi dokoki na yin biyayya ga Allah. Da yake ya nemi Yahweh sai Yahweh ya wadata shi.
6Sai Uziya ya fita ya je ya yi yaƙi da Filistiyawa, ya rushe ganuwar birnin Gat da Yamna da ta Ashdod; ya gina birane a ƙasar Ashdod da` kuma cikin Filistiyawa.7Allah ya taimake shi gãba da Filistiyawa da Larabawan da suka zauna a Gurba'al da kuma Maunayawa.8Ammoniyawa kuma su ka biya haraji ga Uziya ƙarfinsa kuma ya kai har Masar, domin yana ƙara samun iko sosai.
9Bugu da ƙari kuma Uziya ya gina hasumiya a Yerusalem akan Ƙofar Kwana, a Ƙofar Kwari, ya kuma ƙayata su.10Ya kuma gina hasumiyar tsaro a jeji ya kuma haƙa rijiyoyi da yawa domin yana da dabbobi masu yawa a kwarurruka da kuma a saura. Yana da manoma da masu kula da itatuwan inabi a ƙasa mai duwatsu da kuma a filaye masu 'ya'yan itatuwa, domin ya ƙaunaci aikin gona sosai.
11Kuma Uziya yana da mayaƙan sojoji da kezuwa yaƙi a ƙungiyance bisa yadda aka rarraba su bisa ga yawansu yadda Yeyil marubuci da Ma'asiya, hafsa, ƙarƙashin ikon Hananiya ɗaya daga ciki kwamandojin sarki.12Dukkan yawan shugabannin mayaƙa na kabilu shi ne 2600.13A karƙashin ikonsu kuma akwai soja guda 307,500 da keyin yaƙi da iko mai ƙarfi domin su taimaki sarki yaƙi da maƙiya.
14Uziya ya shirya su - domin su zama da dukkan garkuwoyi suturun yaƙi da kwari da kibaw da duwatsun majajjawa.15A Yerusalem ya yi masu aikin ƙira da mutane masu fasaha suka samar su kasance a kan hasumiyoyin da kuma filayen dãga, domin su dinga harba kibiyoyi da kuma manyan duwatsu. Ikonsa ya kai har ƙasashe masu nisa, domin ya sami taimako sosai har sai da ya zama da iko sosai.
16Amma bayan Uziya ya sami iko sosai sai zuciyarsa ta kumbura domin haka ya yi abin da ba shi da kyau; ya yi wa Yahweh Allahnsa zunubi, domin ya tafi gidan Yahweh domin ya ƙona turare akan bagadin ƙona turare.17Sai Azariya firist ya bi shi tare da shi kuma akwai firistocin Yahweh guda tamanin, waɗanda mutane ne masu ƙarfin hali.18Suka yi tsayayya da sarki Uziya, suka ce da shi, "Uziya ba aikinka bane ka ƙona turare, amma aikin firistoci ne, 'ya'yan Haruna waɗanda aka keɓe su ƙona turare. Ka fita daga wuri mai tsarki, domin kana da rashin aminci kuma Yahweh Allah ba zai girmamaka ba"
19Sai Uziya ya yi fushi. yana riƙe da sandan tasar ƙona turare a hannunsa. Lokacin da yake fushi da firistoci, sai kuturta ta kama shi a goshi a gaban firistocin a gidan Yahweh, a gefen bagadin ƙona turare.20Sai Azariya da dukkan firistoci suka duba, sai, suka ga ya zama kuturu a goshinsa. Sai suka yi sauri suka fitar da shi daga can. Hakika, shima ya gaugauta fita, domin Yahweh ya buge shi.
21Sarki Uziya ya zama kuturu har ya zuwa randa ya mutu, ya kuma zauna a keɓaɓɓen gida saboda ya zama kuturu, domin an fitar da shi daga gidan Yahweh. Ɗansa, Yotam, ya zama mai kula da gidan sarki, ya kuma yi mulkin mutanen ƙasar.
22Game kuma da sauran abubuwa akan Uziya farko da ƙarshe, an rubuta su a cikin abin da annabi Ishaya ɗan Amoz ya rubuta.23Sai Uziya ya yi barci tare da kakanninsa aka binne shi a maƙabartar sarakuna, domin sun ce, "Shi kuturu ne." Yotam, ɗansa, ya zama sarki a madadinsa.

27

1Yotam yana da shekaru ashirin da biyar lokacin da ya fara mulki; ya yi mulki na shekaru sha shida a Yerusalem, sunan mahaifiyarsa Yerusha; ita ɗiyar Zadok ce.2Ya yi abin da kemai kyau a idon Yahweh, ya bi gurbin mahaifinsa Uziya ta kowanne abu. Ya kuma ƙi shiga wuri mai tsarki na Yahweh, amma duk da haka mutane basu daina aikin mugunta ba.

3Ya gina ƙofar sama ta gidan Yahweh, akan tsaunin Ofel kuma ya yi gine-gine masu yawa.4Ya kuma yi gine-gine a ƙasa mai duwatsu ta Yahuda, a cikin daji kuma ya gina tsararrun wurare da hasumiyoyi.
5Ya kuma yi yaƙi da mutanen Amon ya kuma cinye su. A wannan shekarar, dai mutanen Amon suka bashi talanti ɗari na zinariya, da awo goma na alkama, da awo goma na riɗi, haka mutanen Amon suka riƙa ba shi a shekara ta biyu da ta uku.
6Sai Yotam ya zama da iko sosai saboda ya yi tafiya da ƙarfi tare da Yahweh Allahnsa.7Game kuma da sauran abubuwa game da Yotam, da dukkan yaƙe-yaƙensa, duba, an rubuta su a cikin littafin sarakunan Isra'ila da Yahuda.
8Yana da shekaru ashirin da biyar a lokacin da ya fara mulki, ya yi mulki a Yerusalem na tsawon shekaru sha shida.9Yotam ya yi barci tare da kakanninsa, aka binne shi a birnin Dauda. Ahaz, ɗansa, ya gaje shi a sarauta.

28

1Ahaz na da shekaru ashirin ne sa'ad da ya fara mulki, kuma ya yi mulki na shekara goma sha shida a Yerusalem. Bai yi abin da ke dai-dai a fuskar Yahweh ba, kamar yadda Dauda kakansa ya yi,2Maimakon haka, ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra'ila; ya kuma ƙera zubin ƙarfe domin Ba'al.

3Bugu da ƙari, ya ƙona turare a ƙwarin Ben Hinnom kuma yasa 'ya'yansa cikin wuta, bisa ga ayyukan ɓautar gumaka na mutanen da Yahweh ya kora daga ƙasarsu kafin mutanen Isra'ila.4ya yi hadaya da ƙona turare a wuraren bisa da kan tuddai da ƙarƙashin kowanne koren itace.
5Saboda haka Yahweh Allahn Ahaz, ya bada shi ga hannun sarkin Aram. Aramiyawan suka buge shi kuma suka ɗauke daga gare shi gagarumin taron ɗaurarru, aka tafi da su Damaskus. Ahaz ma aka bada shi ga hannun sarkin Isra'ila wanda ya buge shi da mummunar kisa.6Gama Pekah ɗan Remaliya a rana ɗaya, ya kashe sojoji Yahuda 120,000, dukkansu maza masu ƙarfin hali ne, saboda sun yashe da Yahweh, Allahn kakanninsu.
7Zikiri, mutum mai ƙarfi daga Ifraimu, ya kashe Ma'asiyya ɗan sarki, Azirikam, shugaban făda da Elkana, wanda ke bin sarki a muƙami.8Mayaƙan Isra'ila sun ɗauki kãmammu daga danginsu mata 200,000 da 'ya'ya maza da mata. Suka kuma kwaso ganima da yawa, wadda suka komo da su Samariya.
9Amma akwai wani annabin Yahweh a wurin, sunansa Oded. Ya je ya sadu da mayaƙan da kezuwa Samariya. Ya ce masu, "Saboda Yahweh, Allahn kakanninku, na fushi daYahuda, ya bada su ga hannun ku. Amma kuka yanka su cikin harzuƙan da ta kai samma.10Yanzu kun yi niyar ku ajiye maza da matan Yahuda da Yerusalem kamar bayinku. Amma ba ku da laifin zunubanku ga Yahweh Allahnku?11To yanzu, ku saurare ni: Ku mayar da kamammun, waɗanda kuka ɗauko cikin naku 'yan'uwan, gama zafin fushin Yahweh na kanku."
12Sa'annan waɗansu shugabannin mutanen Ifraimu- Azariya ɗan Yohanan da Berakiya ɗan Meshilemot da Yehizkiya ɗan Shallum da Amasa ɗan Hadlai, suka taso gãba da waɗanda suka dawo daga yaƙin.13Suka ce da su, "Kada ku kawo kamammun nan, gama kunyi niyar wani abu da zai kawo wa kanmu zunubi ga Yahweh, ya kuma ƙara a kan zunubanmu da laifofinmu, gama laifofinmu na da yawa, kuma akwai fushi mai zafi a kan Isra'ila."
14Sai mayaƙan suka bar kamammun da ganimar a gaban shugabannin da dukkan taron.15Mutanen da aka kira sunansu suka tashi suka ɗauki kãmammun, suka suturad da dukkan waɗanda ke a tsirance cikinsu tare da ganimar. Suka suturad da su suka basu takalma. Suka basu abinci su ci su sha. Suka yi jinyar masu raunuka kuma suka sa masu rauni a kan jakuna. Suka komo da su ga iyalansu a Yeriko, (wadda ake kira Birnin Dabino). Sa'annan suka koma Samariya.
16A wancan lokacin sarki Ahaz ya aiki manzanni zuwa sarakunan Assiriya domin neman su taimake shi.17Gama Idomawa sun sake kawo wa Yahuda hari, suna ɗaukar kamammu suna tafiya da su.18Filistiyawa kuma sun mamaye biranen da keƙwararru da na Negev ta Yahuda. Suka ɗauki Beth Shemesh, da Aijalon, da Gederot, da Soko tare da ƙauyukanta, da Timna tare da ƙauyukanta, da kuma Gimzo tare da ƙauyukanta. Suka tafi su zauna a wuraren.
19Gama Yahweh ya ƙasƙantar da Yahuda saboda Ahaz, sarkin Isra'ila; domin ya yi mugunta a Yahuda kuma ya yi wa Yahweh zunubi mai nauyi.20Tiglat Filesar, sarkin Assiriya, ya zo wurinsa ya dame shi maimakon ya ƙarfafa shi.21Domin Ahaz ya ɗebo kaya daga gidan Yahweh da gidajen sarki da shugabanni, ya bada abubuwa masu daraja ga sarakunan Assiriya. Amma yin hakan bai sa yaci riba ba.
22Wannan sarki Ahaz kuma ya yi zunubi ƙwarai ga Yahweh a lokacin wahalarsa.23Gama ya yi wa allolin Damaskus hadaya, allolin da suka kada shi. Ya ce, "Saboda allolin sarakunan Aram sun taimaka masu, zan yi masu hadaya, don su taimake ni." Amma su suka zama masa dalilin lalacewa da dukkan Isra'ila.
24Ahaz ya tattara kayan ɗaki na gidan Allah ya datse su gunduwa-gunduwa. Ya ƙulle kofofin gidan Yahweh sai ya yi wa kansa bagadai a dukkan lungunan Yerusalem.25A kowanne birni a Yahuda ya yi wuraren tuddai na ƙone hadaya ga waɗansu alloli. Ya harzuƙa Yahweh, Allahn kakaninsa, ga fushi.
26Yanzu sauran aikinsa, da dukkan hanyoyinsa, na farko dana karshe, Duba, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuda da Isra'ila.27Ahaz ya kwanta da kakanninsa, kuma suka binne shi a birnin, a Yerusalem, amma ba su kawo shi cikin hurumin sarakunan Isra'ila ba. Hezekiya, ɗansa, ya zama sarki a madadinsa.

29

1Hezekiya ya fara mulki a sa'ad da yake da shekaru ashirin da biyar da haifuwa; ya yi mulki shekara ashirin da tara a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Abijah; ita ɗiyar Zakariya ce.2Ya yi abin da ke dai-dai a fuskar Yahweh kamar yadda mahaifinsa Dauda ya yi.

3A shekara ta farko na mulkinsa, A wata na farko, Hezekiya ya ɓuɗe ƙofofin Gidan Yahweh ya gyaggyara su.4Ya kawo firistoci da Lebiyawa, ya tattaro su a farfajiyar gefen gabas.5ya ce da su, "Ku saurare ni, ku Lebiyawa! Ku keɓe kanku, ku kuma keɓe gidan Yahweh, Allahn kakanninku, ku cire ƙazamci daga wuri mai tsarki.
6Gama kakanninmu sun kauce daga hanya suka yi mugun abu a fuskar Yahweh Allahnmu; suka yashe shi, suka juye fuskarsu daga wurin da Yahweh ke zamne, kuma suka juya ma wurin baya.7Haka kuma suka kukkulle ƙofofin rumfuna suka kakkashe wutan fitilun; basu ƙona turare ko miƙa baye-baye na ƙonawa a wuri mai tsarki ga Allah na Isra'ila ba.
8Saboda haka fushinYahweh ya faɗo wa Yahuda da Yerusalem, kuma yasa suka zama abin razana da tsoro da ba'a, kamar yadda ku ke gani da idanunku.9Wannan shi yasa ubaninmu suka faɗi ta kaifin takobi, kuma 'ya'ya mazanmu da 'ya'ya matanmu da matayenmu suke cikin bautar talala.
10Yanzu kuwa yana zuciyata in yi alƙawari da Yahweh, Allah na Isra'ila, saboda zafin fushinsa ya juya daga auko mana.11'Ya'yana maza kada ku zama da ragwanci yanzu, gama Yahweh ya zaɓe ku ku tsaya a gabansa, kuyi masa sujada, ku kuma zama barorinsa ku ƙona turare."
12Sa'annan Lebiyawa suka tashi: Mahat ɗan Amasai da Yowel ɗan Azariya, na mutanen Kohatawa; da mutanen Merari, wato Kish ɗan Abdi, da Azariya ɗan Yahalelel; da Gershonawa, wato Yowa ɗan Zimma, da Iden ɗan Yowa;13na 'ya'yan Elizafan, Shimri da Yewuyel; dana 'ya'yan Asaf wato Zekariya da Mataniya;14na 'ya'yan Heman, Yehuwel da Shimei; da na 'ya'yan Yedutun wato Shemayya da Uziyel.
15Suka tattara 'yan'uwansu maza suka tsarkake kawunansu, sai suka shiga ciki, kamar yadda sarki ya umarta, biye da maganar Yahweh, a tsabtace gidan Yahweh.16Firistocin suka je cikin gidan Yahweh domin su tsabtace shi suka fitar da dukkan kazamtar da suka samo a haikalin Yahweh, suka zuba a harabar gidan. Sai Lebiyawa suka kwashe ta suka kai waje zuwa rafin Kidron.17Sai suka fara aikin tsarkakewa a rana ta fari a watan ɗaya. A rana ta takwas ga wata suka kai shirayin Yahweh da aikin, Sa'annan bayan kwana takwas kuma suka tsarkake gidan Yahweh. A ranar sha shida ga watan ɗaya suka gama.
18Sai suka tafi wurin sarki Hezekiya, a cikin fada, suka ce, "Mun tsabtace haikalin Yahweh dukka da bagadin baye-bayen ƙonawa tare da dukkan tasoshi, da kayayyaki, da teburan gurasar kasancewa, da dukkan kayayyakin da suke ciki.19Saboda haka muka shirya muka kuma tsarkake dukkan kayayyakin da sarki Ahaz ya lalatar sa'ad da ya yi aikin rashin aminci a lokacin da yake mulki. Duba, su na nan a gaban bagadin Yahweh."
20Sa'annan sarki Hezekiya ya tashi da sassafe ya tattara shugabanin birnin; ya haura can zuwa gidan Yahweh.21Suka kawo bijimai bakwai da raguna bakwai da 'yan raguna bakwai da bunsura bakwai a matsayin baikon zunubi masarauta da wuri mai tsarki, domin kuma Yahuda. Sai ya umarci firistioci, wato 'ya'yan Haruna maza, su miƙa su a kan bagadin Yahweh.
22Sai suka yanka bijiman, firistoci suka karɓi jinin suka yayyafa a bagadin. Suka yanka ragunan suka yayyafa jinin a bagadin; hakanan kuma suka yanka 'yan ragunan suka yayyafa jinin a bagadin.23Suka kawo bunsuran yin hadaya domin zunubi a gaban sarki da taron jama'a; suka ɗora hannuwansu a kansu.24Sai firistoci suka yankasu suka yi hadaya domin zunubi da jinin a bagadin domin ayi kafara saboda dukkan Isra'ila, gama sarki ya umarta ayi baiko na ƙonawa da baiko domin zunubi saboda dukkan Isra'ila.
25Sai Hezekiya ya sanya Lebiyawa a gidan Yahweh tare da kuge da molaye da garayu. Suka jerasu bisa ga umarnin Dauda, da na Gad, mai gani na sarki, da annabi Nathan, gama umarnin daga wurin Yahweh ya zo ta wurin annabawansa.26Lebiyawa suka tsaya da kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe na Dauda, firistoci kuwa suna rike da ƙahonni.
27Sai Hezekiya ya bada umarni a miƙa baiko na ƙonawa a bisa bagadin. Sa'ad da aka fara miƙa hadaya ta ƙonawa sai waƙa ga Yahweh ma ta fara tasowa tare da busa ƙaho da sauran kayan kiɗe-kiɗe dana bushe- bushe na Dauda sarkin Isra'ila.28Dukkan taron suka yi sujada. mawaƙa suka raira waƙa, masu ƙahonni su ka yi ta busawa; Aka yi ta yin haka har lokacin da aka gama miƙa hadayar ƙonawa.
29Bayan da aka gama yin hadaya ta ƙonawa, sai sarki, tare da dukkan waɗanda suke tare da shi, suka sunkuya suka yi sujada.30Bugu da ƙari, sarki Hezekiya, tare da shugabanin suka umarci Lebiyawa su raira waƙar yabo ga Yahweh da kalmomin Dauda da na Asaf mai gani. Suka raira wakokin yabo tare da murna, suka sunkuya suka yi sujada.
31Sai Hezekiya ya ce, "yanzu dai kun tsarkake kanku ga Yahweh. Sai ku zo kusa ku kawo hadayu da sadakoki na godiya a cikin gidan Yahweh. Sai taron suka kawo hadayu da sadakoki na godiya, kuma dukkan waɗanda suka yi niya sun kawo hadayan ƙonawa.
32Jimilar hadayu na waɗanda taron suka kawo su ne bijimai saba'in da raguna ɗari da 'yan raguna ɗari biyu. waɗannan duka kuwa don hadaya ne ta ƙonawa ga Yahweh.33Tsarkakakkun baye-bayen kuwa bijimai ɗari shida da tumaki dubu uku ne.
34Amma firistocin kima ne don haka suka kasa feɗe dukkan dabbobin da za a miƙa su baye-baye na ƙonawa, sai 'yan'uwansu, Lebiyawa, suka taimake su har aka gama aikin kamin sauran firistoci su sami damar tsarkake kansu. gama Lebiyawan su na la'akari da tsarkake kansu fiye da firistocin.
35Bugu da ƙari, akwai hadayu masu yawa na ƙonawa da aka yi; suka aikatu da kitse na hadaya ta salama, akwai kuma hadaya ta sha don kowacce hadaya ta ƙonawa. Da haka aka maido da hidimar gidan Yahweh.36Hezekiya ya ji daɗi, haka ma dukkan jama'a suka yi murna saboda abin da Allah ya yi wa jama'a, gama farat ɗaya aka yi aikin.

30

1Hezikiya ya aiko da saƙo ga dukkan Isra'ila da Yahuda, ya kuma rubutawa Manasa da Ifraimu wasiƙu, da cewa su zo gidan Yahweh a Yerusalem, su yi Idin ‌Ƙetarewa ga Yahweh, Allah na Isra'ila,2Gama sarkin, da shugabaninsa da dukkan taron jama'a sun gana tare, cewa sun shirya su yi Idin ‌Ƙ‌etarewa a wata na biyu.3Ba su iya yinsa a lokacin da aka saba yi ba, saboda babu firistocin da suka tsarkake kansu, kuma mutane ba su tattaro kansu gaba ɗaya zuwa Yerusalem ba.

4Wannan shirin kuwa ya yi dai-dai a idanuwan sarki da dukkan taron jama'a.5Saboda haka suka yarda su yi shelar umarnin a ko'ina a Isra'ila daga Biyarsheba zuwa Dan, cewa mutanen su zo su yi bikin Idin ‌Ƙ‌etarewa ga Yahweh, Allahn Isra'ila, a Yerusalem. Domin sun lura ba su taɓa yin sa da mutane da yawa ba, bisa ga abin da kea rubuce.
6Sai masu kai saƙo suka tafi da wasiƙu daga sarki da shugabaninsa zuwa ga dukkan Isra'ila da Yahuda, da umarnin sarkin, Suka ce ku mutanen Isra'ila, ku juyo ga Yahweh, Allahn Ibrahim da Ishaku da Iara'ila. Saboda shi ma ya sake juyowa ga ragowarku da kuka kuɓuta daga hannun sarkin Assiriya.
7Kada ku zama kamar kakaninku ko 'yan'uwanku maza, waɗanda suka kauce daga Yahweh, Allahn kakaninsu, har yasa ya bar su ga hallaka, kamar yadda kuka gani.8Yanzu kuwa kada kuyi taurin kai, kamar yadda kakaninku suka yi, ku miƙa kanku ga Yahweh, ku kuma zo wurinsa mai tsarki, wadda ya tsarkake har abada, kuyi sujada ga Yahweh Allahnku, saboda zafin fushinsa zai kauce daga aukowa maku.9Gama idan kuka juya baya ga Yahweh, 'yanuwanku maza da yaranku zasu sami tagomashi a gaban waɗanda suka tafi da su a matsayin kamammu, kuma zasu dawo wannan ƙasar. Gama Yahweh Allahnku mai alheri da jinkai ne kuma ba zai juya fuskarsa daga gare ku ba idan kun juyo zuwa gare shi."
10Sai manzanin suka wuce daga birni zuwa birni a dukkan lardin Ifraimu da Manasa, har zuwa Zabulun, amma mutanen suka yi masu dariya da ba'a.11Ko da yake, waɗansu mutanen Asha da Manasa da Zabulun suka yi tawali'u suka zo Yerusalem.12Hannun Allah kuma ya zo ga Yahuda, ya basu zuciya daya, su yi abin da sarki da shugabanin suka umarta ta wurin maganar Yahweh.
13Mutane da yawa, taron jama'a mai girma, suka taru a Yerusalem domin su yi Bikin Idin Abinci Marar Gami a wata na biyu.14Suka tashi suka cire bagadan da kecikin Yerusalem, da dukkan bagadan ƙona turare; suka zubar da su a kwarin Kidron.15Sa'an nan suka kashe ragunan Idin ‌Ƙetarewa a rana ta huɗu ga watan biyu, Firistoci da Lebiyawa kuwa suka ji kunya, saboda haka suka tsarkake kansu suka kawo hadayu na ƙonawa a gidan Ubangiji.
16Suka ɗauki gwalgwadon matsayinsu, bisa ga yadda dokar Musa, mutumin tsauni ta faɗa, Firistocin suka yarfa jinin da suka karɓa daga hannun Lebiyawa.17Gama akwai waɗansu da yawa a taron da ba su tsarkake kansu ba. Saboda haka Lebiyawan suka yanka ragunan Idin ‌Ƙ‌etarewa domin duk wanda ba shi da tsarki kuma ba zai iya tsarkake hadayunsa ga Yahweh ba
18Gama babban taron mutane, yawancinsu daga Ifraimu da Manasa da Issaka da Zabulun, ba su tsarkake kansu ba, duk da haka suka ci abincin Idin, găba da rubutaccen umarnan. Gama Hezekiya ya yi masu addu'a cewa,19"Ubangiji Yahweh ya gafarci duk wanda ya sa zuciyarsa ga neman tsauni, Yahweh, tsaunin kakaninsa, ko bai da tsarki ta ka'idar tsarkakewa na wuri mai tsarki."20Saboda haka Yahweh ya saurari Hezekiya ya kuma warkar da mutanen.
21Mutanen Isra'ila waɗanda suke a Yerusalem sun yi Idin Abinci Mara Gami da murna mai yawa har kwana bakwai. Lebiyawa da firistoci suka yabi Yahweh rana bayan rana, suna waƙa da kayayyakin kiɗe-kiɗe masu ƙara ga Yahweh.22Hezekiya ya yi magana ta ƙarfafawa ga dukkan Lebiyawan da suka gane hidimar Yahweh. Sai suka ci abinci a duk lokacin idin na kwana bakwai, suna miƙa hadayu na salama, suna ta furta zunubai ga Yahweh, tsauni na kakaninsu.
23Dukkan taron jama'an kuwa suka shirya su ƙara yi bikin na kwana bakwai kuma, suka kuma yi haka da murna.24Gama Hezekiya sarkin Yahuda ya ba jama'an bijimai dubu ɗaya da tumaki dubu bakwai a matsayin baiko; shugabanin kuma suka baiwa jama'ar bijimai dubu ɗaya da tumakai da awakai dubu ɗaya. Firistoci da yawa kuma suka tsarkake kansu.
25Dukkan jama'ar Yahuda, tare da firistoci da Lebiyawa, da dukkan mutanen da suka zo tare daga Isra'ila, da kuma baƙin da suka zo daga ƙasar Isra'ila da waɗanda ke zaune a Yahuda - Dukkansu sun yi farin ciki.26Saboda haka aka yi babban murna a Yerusalem, gama tun daga lokacin Suleman ɗan Dauda, sarkin Isra'ila, babu wani abu kamar haka a Yerusalem.27Sa'an nan firistoci da Lebiyawa suka tashi suka sa wa mutane albarka. Aka kuwa ji muryarsu, addu'arsu kuma ta kai sama, wuri mai tsarki da tsauni yake.

31

1Yanzu sa'ad da aka gama dukkan waɗannan, sai mutanen Isra'ila da kewurin suka fiita daga biranen Yahuda suka rurrushe ginshiƙan duwatsu suka kakkarye sandunan Ashera, suka kuma karya masujadar bisa da bagadun a dukkan Yahuda da Benyamin da Ifraim da Manasse, har sai da suka rurrusa su dukka. Sai dukkan mutanen Isra'ila suka dawo, kowanne ga nasa mallaka da nasa birnin.

2Hezekiya ya rarraba ɓangarorin firistoci Lebiyawa kumaya shirya su bisa ga ɓangarorinsu, kowanne mutum da aikinsa, da firistoci da Lebiyawa. Yasa su su yi hadayun ƙonawa dana zumunci, su yi hidima, su yi godiya, su yi yabo a ƙofar haikalin Yahweh.3Ya kuma shirya sashin hadayar ƙonawa ta sarki daga mallakarsa, wato domin hadayun ƙonawa na safe dana yamma da hadayun ƙonawa domin ranakun Asabar, saɓobbin watanni, da sanyayyun bukukuwa, kamar yadda yake a rubuce a shari'ar Yahweh.
4Bugu da ƙari, ya umarci mutanen da kezama a Yerusalem su bada ɓangaren da ya shafi firistoci da Lebiyawa, saboda su ci gaba da sa ƙarfi ga biyayya da doka na Yahweh.5Ba tare da ɓata lokaci ba bayan an aiko da umarnin, mutanen Isra'ila suka bayar hannu sake wato nunan fari na hatsi da sabon ruwan inabi da maida zuma da dukkan girbin gona. Suka kawo zakka na dukkan kome; waɗannan abu kuwa masu tarin yawa ne.
6Mutanen Isra'ila da Yahuda waɗanda ke zama a biranen Yahuda suka kawo zakkar shanu da tumaki, da kuma zakkar abubuwa masu tsarkin da aka keɓe ga Yahweh tsauninsu, kuma suka tattaro su dami-dami.7A watan uku ne sa'ad da suka fara harhaɗa gudunmawarsu dami-dami, suka kuma gama a wata na bakwai.8Sa'an da Hezekiya da shugabanin suka zo suka ga dammunan, suka albarkaci sunan Yahweh da mutanensa Isra'ila.
9Sa'annan Hezekiya ya tambayi firistocin da Lebiyawa game da dammunan.10Azariya, babban firist, na gidan Zadok, ya amsa masa ya ce, "Tun da mutanen suka fara kawo baye-baye cikin gidan Yahweh, Mun ci kuma mun sami isasshe, kuma muna da ragowa da yawa, gama Yahweh ya albarkaci mutanensa. Abin da ya rage shi ne wannan da yawa a nan."
11Sa'an nan Hezekiya ya umarta ayi wuraren ajiya a gidan Yahweh, sai suka kuwa shirya wuraren.12Sa'an nan suka yi aminci suka kawo baye-bayen, zakka da abubuwan da kena Yahweh. Kononiya, Balebiye, shi ne shugaba mai lura da su, kuma Shimei, dan'uwansa ne na biye da shi.13Yehiyel, da Azaziya, da Nahat, da Asahel, da Yerimot, da Yozabad, da Eliyel, da Ismakiya, da Mahat, da Benaya na karkashin Konaniya da Shime'i dan'uwamsa, bisa ga zaɓen Hezekiya, sarki, da Azariya, mai lura da gidan Yahweh.
14Kore ɗan Imna Balebiye da shugaba na ƙofar gabas, su ne masu lura da bayarwar yardar rai ga tsauni da shugabanci a kan rarrabawar baye-baye ga Yahweh da abubuwa mafi tsarki cikin baye-bayen.15A ƙarƙashinsa akwai Iden da Mini'amin da Yeshuwa da Shemaya da Amariya da Shekaniya a biranen firistocin. Suka cika ayyukan amanar shugabanci, Domin a bayar da waɗannan baye-baye ga 'yan'uwansu maza ɓangare ɓangare ga kowa da kowa.
16Suka kuma ba wa mazajen da keshekara uku zuwa sama, waɗanda aka lisafta a rohotonin kakaninsu da suka shiga gidan Yahweh, kamar yadda ake bukata a kowacce rana, ayi aiki bisa ga muƙamansu da ɓangarorinsu.
17Suka rarraba wa firistocin bisa ga rahotonin kakaninsu, haka kuma ga Lebiyawan da kesama da shekara ashirin ko fiye, bisa ga muƙamansu da ɓangarorinsu.18Suka haɗa da 'yan ƙananansu da matayensu da 'ya'ya mazansu da 'ya'ya matansu, a dukkan unguwan, gama su masu aminci ne ga kiyaye zaman tsarkinsu.19Gama firistocin wato zuriyar Haruna waɗanda ke filayen ƙauyukan da keta biranensu ne, ko kuwa a kowacce birni dai, akwai mazajen da aka sa da sunayesu, su bada rabo ga duk mazaje cikin firistoci, da kuma ga waɗanda aka lisafta a rahotonin kakaninsu cewa suna cikin Lebiyawa.
20Hezekiya ya yi wannan a dukan Yahuda. Ya aiwatar da abin da kenagari, dai-dai, da kuma aminci a gaban Yahweh, tsauninsa,21A duk aikin da ya fara cikin hidimar gidan tsauni da dokoki da farilai, don kusantuwa da tsauninsa, ya aikata su da dukkan zuciyarsa, kuma ya yi nasara.

32

1Bayan waɗannan abubuwan da amintattun ayyuka, Senakirib sarkin Asuriya, ya zo ya shiga Yahuda. Ya kafa sansani ya kai ma birane masu garu hari, da niyar ya yi kamu domin kansa.

2Sa'ad da Hezekiya ya ga Senakirib ya iso kuma ya yi niyar yaƙi da Yerusalem,3sai ya yi shawara da shugabanninsa da mazajensa masu iko su tsayar da ruwayen da kefitowa daga maɓuɓɓugar da suke bayan birnin; suka taimake shi ya yi hakan.4Saboda haka mutane da yawa suka taru suka tsayar da dukkan maɓuɓɓugai da rafuffuka da kegudu ta cikin ƙasar. Su na cewa, "Me zai sa sarakunan Asuriya su zo su sami ruwa mai yawa?"
5Hezekiya ya yi karfin hali ya sake gina dukkan ganuwar da aka rushe, ya gina hasumiyar da inganci, haka kuma ɗaya garun da kewaje. Ya kuwa ƙara ƙarfin Milo a birnin Dauda, ya kuma yi makamai na yaƙi da yawa da garkuwoyi.
6Sai ya sa manyan sojoji su shugabanci mutane. Ya tattaro su gareshi a dandalin ƙofar birnin ya yi magana ta ƙarfafawa da su. Ya ce,7"Ku ƙarfafa da nagartaccen ƙarfin hali. Kada ku ji tsoro ko ku yi fargaba saboda sarkin Asuriya da dukkan sojojin da ketare da shi, gama wani yana tare da mu wanda ya fi waɗanda ke tare da shi.8Hannun mutum ne kawai ke tare da shi, amma mu Yahweh tsauninmu yake tare da mu domin ya taimake mu ya yi mana yaƙi." Mutane kuwa suka ta'azantu da maganar Hezekiya, sarkin Yahuda.
9Bayan wannan, sai Senakirib sarkin Asuriya ya aika da barorinsa zuwa Yerusalem (Yanzu dai yana a gaban Lakish, kuma dukkan mayaƙansa na tare da shi), ga Hezekiya, sarkin Yahuda da dukkan Yahuda waɗanda ke a Yerusalem. Ya ce,10Ga abin da Senakirib, sarkin Asuriya, ya ce: "Ga me kake dogara a kai don ka dage wa yaƙi kewaye da kai a cikin Yerusalem?
11Ba ruɗin ku Hezekiya yake yi ba, don ya sa ku mutu da yunwa da ƙishi, sa'ad da yake gayă maku, 'Yahweh tsauninmu zai cece mu daga hannun sarkin Asuriya'?12Ba wannan Hezekiyan ba ne yake ɗauke wuraren bisansa da bagadensa ya kuma umarci Yahuda da Yerusalem, 'A kan bagadi guda ne ya wajaba ku yi sujada, a kansa ne kuma zaku ƙona hadayunku?
13Ba kun san abin da ni da kakannina muka yi wa dukkan manyan mutane na waɗansu ƙasashen ba? Allolin manyan mutane na ƙasashe sun iya ceton ƙasashensu daga hannuna?14Daga cikin dukkan manyan waɗancan al'ummai waɗanda kakannina suka hallakar kakaf, da wanda ya iya ceton mutanensa daga hannuna? Donme tsauninku zai iya cetonku daga hannuna?15Yanzu fa kada ku yarda Hezekiya ya ruɗe ku ko ya ɓadda ku haka. Kada kuwa ku gaskata shi, gama ba wani tsauni na wata al'umma ko mulki wanda ya taɓa ceton mutanensa daga hannuna, ko kuma daga hannun kakannina. Wane ne tsaunin ku har da zai iya cetonku daga hannuna?"
16Barorin Senakirib sun yi maganganu fiye da haka găba da Yahweh tsauni da bawansa Hezekiya.17Senakirib ya kuma rubuta wasiƙu don ya yi ba'a ga Yahweh, tsauni na Isra'ila, ya kuma yi maganar găba da shi. Ya ce, "Kamar yadda allolin al'ummai na sauran ƙasashe basu ceci mutanensu daga hannuna ba, hakanan kuma tsaunin Hezekiya ba zai iya ceton mutanensa daga hannuna ba."
18Suka yi kuka da babban murya, da harshen Yahudanci, suka yi ta magana da mutanen Yerusalem waɗanda suke kan garu, don su tsoratar da su, su kuma firgita su, domin su danƙe birnin.19Suka yi magana a kan tsauni na Yerusalem kamar yadda suka yi ta magana a kan allolin waɗansu mutanen duniya, waɗanda aikin hannuwan mutane ne kurum.
20Sarki Hezekiya da annabi Ishaya ɗan Amoz, suka yi addu'a saboda wannan al'amari kuma suka yi kuka zuwa sama21Yahweh kuwa ya aiki mala'ika, wanda ya karkashe mazajen yaƙi da manyan jarumawa da shugabanni na sarkin a sansanin. Saboda haka Senakirib ya koma ƙasarsa cike da kunya. Sa'ad da ya shiga gidan tsauninsa, sai waɗansu daga cikin 'ya'yan cikinsa suka kashe shi da takobi.
22Ta haka Yahweh ya ceci Hezikiya da mazaunan Yerusalem daga hannun Senakirib, sarkin Asuriya, daga kuma hannun dukkan sauran, ya kuma hutar da su ta kowace ɓangare.23Mutane da yawa suka kawo wa Yahweh sadakoki a Yerusalem, da kuma abubuwa masu daraja ga Hezekiya sarkin Yahuda, saboda haka ya sami ɗaukaka a idanun dukkan sauran al'ummai tun daga lokaci nan har zuwa gaba.
24A kwanakin nan kuwa Hezekiya ya yi ciwo gab da mutuwa. Sai ya yi addu'a ga Yahweh, wanda kuwa ya yi magana da shi ya ba shi alamar cewa zai warke.25Amma Hezekiya bai mayar da godiya a kan taimakon da ya ba shi ba, domin a zuciyarsa akwai girman kai. Saboda haka hasala ta auka kansa, da kan Yahuda da Yerusalem.26Duk da haka dai, daga baya Hezekiya ya ƙasƙantar da kansa saboda fahariyar zuciya da ya yi, da shi da mazaunan Yerusalem, don haka hasalar Yahweh ba ta faɗo masu ba a kwanakin Hezekiya.
27Hezekiya yana da dukiya ƙwarai yana kuma da girma. Sai ya gina wa kansa taskoki inda zai ajiye azurfa da zinariya da duwatsu masu daraja da kayan yaji da garkuwoyi da dukkan tasoshi, da kwanoni masu daraja.28Yana kuma da ɗakunan ajiya na hatsi, da na ruwan inabi dana mai, da wuraren turke dabbobi na kowanne iri, yana kuma da garkuna a cikin rufar dabbobinsa.29Bugu da ƙari, ya kuma tanada wa kansa birane da mallakar garkunnan tumaki da na shanu a yalwace. Gama tsauni yaba shi wadata mai yawa.
30Hezekiyan nan ne kuwa ya datse ruwan da yake gangarowa daga kogin Gihon, ya kuma kawo su su gangara zuwa wajen yammacin birnin Dauda. Hezekiya ya yi nasara da dukkan ayyukansa.31Ko da shi ke, game da jakadun hakiman Babila, waɗanda aka aika su tambaye shi game da waɗanda suka san irin abin al'ajibin da aka yi a ƙasar, sai tsauni ya ƙyale shi kurum, don ya jaraba shi ya san dukkan abin da kea zuciyarsa.
32Sauran ayyukan Hezekiya da kyawawan ayyukansa, gashi an rubuta su a wahayin annabi Ishaya ɗan Amoz a littafin Sarakunan Yahuza da na Isra'ila.33Sai Hezekiya ya rasu, suka bizne shi a sashe na bisa na hurumin 'ya'yan Dauda, maza da dukkan Yahuda da mazaunan Yerusalem suka girmama shi sa'ad da ya rasu, sai Manasa ɗansa ya gaji gădon sarautarsa.

33

1Manasse yana da shekara goma sha biyu sa'ad da ya fara mulki; ya yi mulki shekaru hamsin da biyar a Yerusalem.2Ya yi abin da kemugunta a fuskar Yahweh, kamar ƙazantattun abubuwan da al'umman da Yahweh ya kore su a gaban mutanen Isra'ila.3Gama ya gina wuraren kan tudun da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe, kuma ya gina bagadai domin Ba'aloli. Ya ƙera sandunan Ashera, kuma ya russuna wa dukkan taurarin sammai ya yi masu sujada.

4Manasse ya gina bagadin a gidan Yahweh, koda shi ke dai Yahweh bai umarta ba, "A Yerusalem ne sunana zai kafu har abada."5Ya gina bagadai ga dukkan taurarin sama a cikin shirayu biyun da kegidan Yahweh.6A Kwarin Ben Hinnom ya sa 'ya'yansa maza a wuta. Ya aikata tsafe-tsafen tsubbu; ya yi karatun baƙaƙen zabura; kuma ya tuntuɓi masu magana da matattu da ruhohi. Manasse aikata miyagun ayyuka da dama a fuskar Yahweh, ya kuma tsokani Yahweh ga fushi.
7Sarafaffen siffar da ya yi, ya sa shi a gidan tsauni. A kan wannan gidan ne tsauni ya yi magana da Dauda da Suleman ɗansa. Ya ce, "A wannan gidan da Yerusalem ne, waɗanda na zaɓa daga dukan ƙabilun Isra'ila, cewa zan kafa sunana har abada.8Ba zan ƙara fitar da mutanen Isra'ila daga ƙasar dana ba wa kakaninsu ba, idan za su yi biyayya su kiyaye dukkan abin dana umarce su, su bi dukkan dokoki da farillai dana umarta ta hannun Musa."9Manasse ya jagoranci Yahuda da mazaunan Yerusalem ga yin mugunta fiye da al'umman da tsauni ya hallakar a gaban mutanen Isra'ila.
10Yahweh ya yi magana da Manasse da jama'arsa amma babu wanda ya kula.11Saboda haka Yahweh yasa sarakunan yaƙi na sarkin Asiriya su kama Manasase su ɗaure shi da sarƙoƙin tagulla su kai shi Babila.
12Sa'ad da Manasse ke shan wahala, sai ya roƙi Yahweh, tsauninsa, ya ƙasƙantar da kansa sosai a gaban tsauni na kakaninsa.13ya yi addu'a zuwa gare shi; sai ya roƙi tsauni, sai tsauni ya ji rokonsa ya komo da shi Yerusalem, ga mulkinsa. Sa'an nan ne Manasse ya sani Yahweh shi ne tsauni.
14Bayan haka sai Manasse ya gina garu a bayan birnin Dauda a gefen yammacin Gihon, a kwari, zuwa ‌Ƙofar Kifi. Ya kewaye tudun Ofel, bayan wannan kuma ya gina shi da tsayi sosai. Sa'an nan yasa sarakunan yaƙi a garuruwa masu garu na Yahuda.15Ya kwashe baƙin alloli, wato gumaku daga cikin gidan Yahweh, da dukkan bagadin da ya giggina a bisa dutse na gidan Yahweh da Yerusalem. Ya zubar da su a bayan birnin.
16Ya kuma komar da bagadin Ubangiji ya miƙa hadayu na salama dana godiya a kansu; ya kuma umarci Yahuda da ta bauta wa Yahweh, tsauni na Isra'ila.17Duk da haka, jama'a suka ci gaba da miƙa hadayunsu a masujadar bisa, amma ga Yahweh, tsauninsu kaɗai.
18Game da sauran ayyukan Manasse da addu'o'insa ga tsauninsa, da abubuwan da masu gani suka faɗa masa cikin sunan Yahweh, tsauni na Isra'ila, gasu, suna a rubuce cikin ayyukan sarakunan Isra'ila.19A cikin rahoton akwai tarihin addu'arsa, da yadda tsauni ya ƙarɓi rokonsa, akwai kuma rahoton dukkan zunubinsa da rashin amincinsa, da wuraren da ya gina masujada a bisa, ya kafa sandar Ashera da sarafaffun siffofi, kamin ya ƙasƙantar da kansa - suna nan a rubuce a Tarihin Masu Duba.20Haka dai Manasse ya kwanta tare da kakaninsa, suka binne shi a gidansa. Sai Amon, ɗansa, ya zama sarki a madadinsa.
21Amon yana da shekara ashirin da biyu sa'ad da ya fara sarauta, ya yi shekara biyu yana mulki a Yerusalem.22Ya aikata mugunta a gaban Yahweh, kamar yadda Manasse, mahaifisa ya yi. Amon ya miƙa hadayu ga dukkan siffofin da mahaifinsa Manasse ya yi, ya bauta masu.23Bai ƙasƙantar da kansa a gaban Yahweh, kamar yadda mahaifinsa Manasse ya yi ba. Maimakon haka, shi wannan Amon fa ya ƙara yin zunubi gaba-gaba.
24Sai fadawansa suka yi masa maƙarkashiya suka kashe shi a gidansa.25Amma jama'ar ƙasar suka ƙarkashe dukkan waɗanda suka yi wa sarki Amon maƙarƙashiya, sai suka naɗa Yosiya, ɗansa, ya gaji gadon sarautarsa.

34

1Yosiya yana da shekara takwas sa'ad da ya fara sarauta, ya yi mulki shekara talatin da ɗaya a Yerusalem.2Ya yi abin da ke dai-dai a fuskar Yahweh, ya kuma yi tafiya a hanyoyin Dauda mahaifinsa, kuma bai juya dama ko hagu ba.3Gama a shekara ta takwas na mulkinsa, tun yana yaro ya fara biɗan tsauni na Dauda, kakansa, a shekara ta goma sha biyu ne ya fara tsarkake Yahuda da Yerusalem daga tsafin wuraren bisa da sandar Ashera da sarafaffun siffofi da zuben siffofin ƙarfe.

4Mutanen suka rurrusa bagadan Ba'alolin a gabansa; ya rurrusa bagadan turaren da kebisansu. Ya karya sandar Ashera da saraffaffun sifoffi da siffofin ƙarafuna har suka ragargaje zuwa ƙura. Ya yayyafa ƙurar a kan kaburburan waɗanda suka yi masu hadaya.5Ya ƙona kasusuwan firistocinsu a bagadansu. Ta haka ya tsarkake Yahuda da Yerusalem.
6Ya yi haka kuma a biranen Manasa da Ifraimu da Saminu har zuwa Naftali da lalatattun wurare da kekewaye da su.7Ya rusar da bagadan; ya ragargaza sandar Ashira da sarafaffun siffofi zuwa gǎri, ya kuma rurrusa bagadan turare a dukkan ƙasar Isra'ila; sa'an nan ya koma Yerusalem.
8Yanzu a shekara ta goma sha takwas ta mulkinsa, bayan Yosiya ya tsarkake ƙasar da haikalin, ya aiki Shafan ɗan Ma'aseya da gwamnan birnin da Yowa ɗan Yowahaz magatakarda, da su gyaggyara gidan Yahweh tsauninsa.9Suka je wurin Hilkaya, babban firist, suka danƙa masa kuɗin da aka kawo gidan Yahweh wanda Lebiyawa da masu gadin ƙofofi suka tara daga Manasse da Ifraimu, daga dukkan ragowar Isra'ila, daga dukkan Yahuda da Benyamin da kuma daga mazaunan Yerusalem.
10Suka danƙa kuɗin ga mazan da kelura da gidan Yahweh. Waɗannan mazan ne ke biyan ma'aikatan da ke gyaggyarawa da adana haikalin.11Suka biya kafintoci da magina kuɗin da zasu sayi sassaƙaƙƙen duwatsu da katakai domin yin tsaiko kuma da tankaru don gine- ginen da waɗansu sarakuna na Yahuda suka bar su suka lalace.
12Mazajen sun yi aikin da aminci. Masu shugabancinsu su ne Yahat da Obadiya wato Lebiyawa, 'ya'yan Merari; da Zekariya da Meshullam, daga 'ya'ya mazan Kohatawa. Sauran Lebiyawan waɗanda dukkansu ƙwararrun mawaƙa ne, sun yi shugabancin ma'aikatan.13Waɗannan Lebiyawan ne ke shugabancin masu ɗaukan kayan gini da duk sauran ma'aikata daban-daban. Akwai kuma Lebiyawan da kemasu rubuce=rubuce da masu gudanar da shugabanci da masu gadin ƙofofi.
14Sa'ad da suka kawo kuɗin da aka kawo gidan Yahweh, Hikaya firist ya samo littafin shari'a ta Yahweh wanda aka bayar ta wurin Musa.15Hikaya ya cewa Shafan magatakarda, "Na sami littafin shari'a a gidan Yahweh." Hikaya ya kawo littafin ga Shafan.16Shafan ya kai ma sarki littafin, ya kuwa ba shi rahoto, cewa, "Barorinka na yin dukkan abubuwan da aka basu amanan yi.
17Suka tattaro kuɗin da aka samu agidan Yahweh, sai suka bayar da shi ga hannun shugabannin lura da mazan aikin."18Shafan magatakarda ya faɗa wa sarki, "Hilkaya firist ya ba ni littafi." Sa'an nan Shafan ya karanta wa sarkin.19Ya zamana kuwa a sa'an da sarki ya ji kalmomin shari'a, sai ya yayyage tufafinsa.
20Sarkin ya umarce Hilkaya da Ahikam ɗan Shafan da Abdon ɗan Micah da Shafan magatakarada da Ashaya, baransa, cewa,21"Ku je ku bincika nufin Yahweh domina, da kuma domin waɗanda aka bar su a Isra'ila da Yahuda, saboda kalmomin littafi da aka samo. Gama yana da girma, hasalar Yahweh da aka zubo mana. yana da yawa, saboda kakaninmu basu saurari kalmomin wannan littafi ba don su yi biyayya da dukkan abin da aka rubuto cikinta."
22Saboda haka Hilkaya, da waɗanda sarki ya umarta, suka je wurin annabiya Huldah, matar Shallum ɗan Tokhat ɗan Hasra, mai lura da tufafin firistoci (tayi zama a Yerusalem a Gunduma ta Biyu), sai suka yi magana da ita haka.
23Sai ta ce masu, "Ga abin da Yahweh, tsaunin Isra'ila, ya ce: "Gaya wa mutumin da ya aiko ku wuri na,24Ga abin da Yahweh ya faɗi: Duba. 'Ina gab da kawo bala'i a nan wurin da kan mazaunanta, dukkan la'anonin da aka rubuta a littafi da suka karanta a gaban sarkin Yahuda.25Saboda sun ƙi ni kuma sun ƙona turare ga waɗansu alloli, saboda su zuga ni ga fushi da dukkan ayyukan da suka aikata- Don haka fushi na zai zubo a wannan wurin, kuma ba za a datse shi ba.'
26Amma ga sarkin Yahuda, wanda ya aiko ku ku tambayi Yahweh abin da zai yi, ga abin da zaku gaya ma sa, 'Yahweh, tsauni na Isra'ila ya faɗi haka: Game da maganganun da ka ji,27saboda baka taurare zuciyarka ba, kuma ka ƙasƙantar da kanka a gaban tsauni sa'ad da ka saurari maganganu game da wannan wurin da mazaunanta, kuma domin ka ƙasƙantar da kanka a gaba na, ka yayyaga taufafinka ka yi kuka a gabana, Ni kuma na saurare ka - wannan furcin Yahweh ne -28duba, Zan tattara ka da kakaninka. Za a tattara ka zuwa kabarinka cikin salama, kuma idanuwanka ba za su ga bala'in da zan kawo a wurin nan da mazaunanta ba." Mazajen nan suka kai wa sarki wannan saƙon.
29Sa'an nan sarkin ya aiko manzanni su tattaro dukkan dattawan Yahuda da Yerusalem tare.30Sa'an nan sarkin ya haura zuwa gidan Yahweh, da dukkan mazajen Yahuda da mazaunan Yerusalem, da firistoci da Lebiyawa da dukkan mutane, daga manya zuwa ƙanana. Sa'an nan ya karanto ga saurarawarsu dukkan kalamomin littafin Alƙawari da aka samo a gidan Yahweh.
31Sarkin ya tsaya a wurinsa ya yi alƙawari a gaban Yahweh, ya yi tafiya bisa ga jagorancin Yahweh, ya kuma kiyaye dokokinsa da farillansa da umarnansa, da dukkan zuciyarsa da dukkan ransa, ya yi biyayya da maganganun alƙawari da kea rubuce a wannan littafi.32Ya sa dukkan waɗanda aka same su a Yerusalem da Benyamin su tsaya a kan alƙawarin. Mazaunan Yerusalem sun yi aiki cikin biyayya ga alƙawarin tsauni, tsauni na kakanninsu.
33Yosiya ya ɗauke dukkan ƙazamtattun abubuwa daga ƙasashen da suke na mutanen Isra'ila. Ya sa kowa a Isra'ila ya bauta wa Yahweh, tsauninsa. Gama a dukkan kwanakinsa, ba su juya daga bin Yahweh, tsaunin kakaninsu ba.

35

1Yosiya ya kiyaye Idin ‌Ƙetarewa ga Yahweh a Yerusalem, kuma suka kashe 'yan ragunan Idin a rana ta goma sha huɗu ga wata na fari.2Ya sa firistocin a matsayinsu ya ƙarfafa su a cikin hidimar gidan Yahweh.

3Ya cewa Lebiyawan da suka koyar da dukkan Isra'ila waɗanda aka keɓe ga Yahweh, "Ku sa akwati mai tsarki a gidan da Suleman ɗan Dauda, sarkin Isra'ila ya gina. Kada ku dinga ɗaukar sa a bisa kafaɗunku kuma. Yanzu ku bauta wa Yahweh tsauninku, ku yi wa mutanensa Isra'ila hidima.4Ku shirya kanku ta sunayen gidajen kakaninku da ɓangarorinku, bisa ga rubutaccen umarnin Dauda, sarkin Isra'ila, da ta Suleman, ɗansa.
5Ku tsaya a wuri mai tsarki, kuna ɗaukan matsayinku tare da ɓangarorin 'yan'uwanninku maza ta cikin gidajen kakaninku da zuriyoyin mutane, kuna kuma ɗaukan matsayinku tare da ɓangarorinku ta cikin gidajen kakaninku na Lebiyawa.6Ku kashe 'yan ragunan Idin ‌Ƙetarewa, ku tsarkake kanku, ku shirya ragunan domin 'yan'uwanku maza, kuyi bisa ga maganar Yahweh da aka bayar ta hannun Musa."
7Yosiya ya baiwa dukkan mutane 'yan raguna dubu talatin da 'yan awakai daga turkuna domin baikon Idin ‌Ƙ‌etarewa ga dukkan waɗanda suka kasance. Ya kuma bada bijimai dubu talatin; waɗannan daga mallakar sarki ne.8Shugabaninsa sun bayar da baikon yardar rai ga mutane da firistoci da Lebiyawa. Hilkaya da Zekariya da Yehiyel da manyan ma'aikatan da kelura da gidan tsauni, sun ba firistoci baikon ƙananan shanu 2,600 da bijimai ɗari uku domin Idin ‌Ƙetarewa.9Konaniya kuwa da Shemaya da Netanel, 'yan'uwansa maza, da Hashabiya da Ye'iyel, da Yozabad, waɗanda ke shugabancin Lebiyawa, sun ba Lebiyawan baiko domin Idin ‌Ƙ‌etarewa ƙananan shanu dubu da bijimai ɗari biyar.
10Don haka aka shirya hidimar, sai firistocin suka tsaya bisa ga matsayinsu, da Lebiyawan ta ɓangarorinsu, cikin yin biyayya da umarnin sarki.11Suka kashe 'yan ragunan Idin ‌Ƙ‌etarewa, sai firistoci suka zuba jinin da suka karɓo daga hannun Lebiyawan, sai Lebiyawan suka feɗe 'yan ragunan.12Suka cire hadayun ƙonawa, don su rarraba su ga ɓangarorin gidajen kakanin mutanen, suƙa miƙa su ga Yahweh, kamar yadda aka rubuta a cikin littafin Musa. Suka yi haka kuma da bijiman.
13Suka gaggasa 'yan ragunan Idin ‌Ƙetarewan da wuta bisa ga umarni. Game da tsarkakkun baye-bayen, suka dafa su cikin ruwa a tukwane daban-daban, suka kuma ɗauka da sauri suka kai wa dukkan mutane.14Suka shirya baye-baye daga baya domin kansu da firistocin, saboda firistocin, wato zuriyar Haruna, suna fama da miƙa hadaya ta ƙonawa da kitsen har sai dare ya yi, saboda haka Lebiyawan sun shirya baye-bayen domin kansu da firistoci, zuriyar Haruna.
15Mawaƙan, zuriyar Asaf, suna wurin, bisa ga bishewar Dauda da Asaf da Heman da Yedutun mai duba na sarki, kuma masu tsaro suna a kowacce ƙofa. Ba za su taɓa barin wurin tsayawarsu ba, saboda 'yan'uwansu Lebiyawa sun shirya abu dominsu.
16Don haka, a lokacin nan dukkan hidimar Yahweh ana yi domin bikin Idin ‌Ƙ‌etarewa ne da miƙa baye-bayen ƙonawa a bagaden Yahweh, kamar yadda sarki Yosiya ya umarta.17Mutanen Isra'ilan da suka kasance sun kiyaye Idin ‌Ƙ‌etarewa a lokacin, sa'an nan kuma da Shagulgulan Gurasa Marar Gami na kwana bakwai.
18Irin wannan bikin Idin ‌Ƙetarewan ba a taɓa yin sa a Isra'ila ba tun daga kwanakin su annabi Sama'ila, ba kuwa wani daga cikin sauran sarakunan Isra'ila da ya yi hidimar bikin Idin ‌Ƙ‌etarewa kamar yadda Yosiya ya yi, tare da firistoci da Lebiyawa da dukkan mutanen Isra'ilan da suka kasance, kuma da mazaunan Yerusalem.19Wannan Idin ‌Ƙ‌etarewa an kiyaye shi ne a shekara ta goma sha takwas na mulkin Yosiya.
20Bayan dukkan wannan, bayan Yosiya ya shirya haikalin bisa ga tsari, Neko, sarkin Masar, ya hauro ya yi faɗa da Karkemish a Kogin Yuferetis, sai Yosiya ya je ya yi faɗa da shi.21Amma Neko ya aiko wakilai gun sa, cewa, "Mene ne zan yi da kai, sarkin Yahuda? Ba na zuwa găba da kai yau, amma găba da gidan da nake yaƙi da su. tsauni ya umarce ni da in yi sauri, saboda haka ka janye daga shisshigi da Allah, wanda ke tare da ni, don zai iya hallaka ka."
22Koda shi ke, Yosiya ya ƙi ya juyo daga gare shi. Ya ɓoye kamaninsa don ya yi yaƙi da shi. Bai saurari maganar Neko da ta zo daga bakin Allah ba; sai ya je ya yi faɗa a Kwarin Megiddo.
23Jarumawa suka harbi Yosiya, sai sarki ya cewa barorinsa, "Ku tafi dani, gama na sami mumunar rauni,"24Sai barorinsa suka ɗauke shi daga karusar, suka sa shi a karusa ta biyu. Suka kai shi Yerusalem, inda ya mutu. Aka binne shi a wurin binne kakaninsa. Dukkan Yahuda da Yerusalem suka yi makoki domin Yosiya.
25Irimiya ya yi makoki domin Yosiya; dukkan mazaje da mata mawaƙa suna maƙoƙi game da Yosiya har yau. Waɗannan waƙoƙin suka zama al'ada a Isra'ila; Suna a rubuce a waƙoƙin maƙoƙi.
26Game da sauran abubuwan da suka shafi Yosiya, da nagargarun ayyukansa da ya yi cikin biyayya da abin da kea rubuce a shari'ar Yahweh -27kuma dukkan ayyukansa, daga farko zuwa karshe, na a rubuce cikin littafin sarakunan Yahuda da Isra'ila.

36

1Sa'an nan mutanen ƙasar suka ɗauki Yehowahas ɗan Yosiya, suka maida shi sarki a madadin mahaifinsa a Yerusalem.2Yehowahas yana da shekara ashirin da uku sa'ad da ya fara mulki, ya kuma yi mulki watanni uku a Yerusalem.

3Sarkin Masar ya cire shi a Yerusalem, ya sa wa ƙasar tara na talenti ɗari na azurfa da talenti ɗaya na zinariya.4Sarkin Masar ya maida Iliyakim, ɗan'uwansa, sarki a kan Yahuda da Yerusalem, (ya sauya wa Iliyakim suna zuwa Yehoyakim). Sa'an nan Neko ya ɗauki ɗan'uwan Iliyakim Yehowahas ya kawo shi Masar.
5Yehoyakim yana da shekara ashirin da biyar sa'ad da ya fara mulki, kuma ya yi mulki shekara goma sha ɗaya a Yerusalem. Ya yi abin mugunta a fuskar Yahweh Allahnsa.6Sa'an nan Nebukadnezar, sarkin Babila, ya kai masa hari ya ɗaure shi da sarƙoƙi ya kai shi Babila.7Nebukadnezar kuma ya ɗauki waɗansu kayayyakin gidan Yahweh zuwa Babila, ya sa su a fadarsa a Babila.
8Game da sauran zantattukan da suka shafi Yehoyakim, abubuwan ƙazamtar da ya yi, da abin da aka samo găba da shi, gashi, suna a rubuce a littafin sarakunan Yahuda da Isra'ila. Sa'an nan Yehoyakin, ɗansa, ya zama sarki a madadinsa.
9Yehoyakin yana da shekara takwas sa'ad da ya fara mulki; ya yi mulki wata uku da kwana goma a Yerusalem. Ya yi abin da kemugunta a fuskar Yahweh.10Da bazara, Sarki Nebudkanezar ya aiki mazaje aka kawo shi Babila, tare da abubuwa masu daraja daga gidan Yahweh, sai ya maida Zedekiya, danginsa, sarki a kan Yahuda da Yerusalem.
11Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa'ad da ya fara mulki; ya yi mulki shekara goma sha ɗaya a Yerusalem.12Ya yi abin da kemugunta a fuskar Yahweh Allahnsa. Bai ƙasƙantar da kansa a gaban annabi Irimiya ba, wanda ya yi magana daga bakin Yahweh.
13Zedekiya kuwa ya yi tayarwa gãba da Sarki Nebudkanezar, wanda ya sa shi rantsuwar yin biyayya gare shi da sunan Allah. Amma Zedekiya ya taurare zuciyarsa da wuyansa gãba da juyowa ga Yahweh, Allahn Isra'ila.14Bugu da ƙari, dukkan shugabannin firistocin da mutanen sun yi mummunan rashin aminci, kuma suka bi kazamtattun aikin al'ummai. Suka lalatar da gidan Yahweh wanda ya tsarkake a Yerusalem.
15Yahweh, Allahn kakaninsu, ya aiko da kalma garesu ta manzaninsa a kai a kai, saboda yana da tausayi a kan mutanensa da wurin da yake zamne.16Amma sun yi ma manzanin Allah ba'a, suka yi banza da maganarsa, suka kuma wulaƙantar da annabawansa, har sai da fushin Allah ya taso gãba da mutanensa, har babu taimako game da haka.
17Don haka Allah ya kawo masu sarkin Kaldiyawa, wanda ya kashe 'yan mazansu da takobi a masujada, kuma ba su ji tausayin 'yan maza ko budurwai ko tsofoffin maza ko masu farin gashi ba. Allah ya bayar da su dukka ga hannunsa.
18Dukkan kayan ɗaki na gidan Allah, masu manya da ƙanana da dukiyoyin gidan Yahweh da dukiyoyin sarki da ma'aikatansa- dukkan waɗannan ya kwashe zuwa Babila.19Suka ƙona gidan Allah, suka rurrushe garun Yerusalem, suka ƙona dukkan fadodinta, kuma suka hallakar da dukkan abubuwa masu kyau a ciki.
20Sarki ya ɗauke zuwa Babila waɗanda suka kuɓce wa takobi. Suka zama barori dominsa da 'ya'yansa maza har zuwa mulkin Fasha.21Wannan ya faru ne domin a cika maganar Yahweh ta bakin Irimiya, har sai ƙasar ta ji daɗin hutun Asabatunta. Ta jira Asabbatu na tsawon lokacin da take zama a yashe, don a wuce shekaru saba'in ta haka.
22Yanzu kuwa a shekara ta farko ta Sairus, sarkin Fasha, domin maganar Yahweh ta bakin Irimiya ta cika, Yahweh ya zuga ruhun Sairus, sarkin Fasha, don haka ya sanar da umarni ga dukkan mulkinsa, ya kuma sa ta a rubuce. Ya ce,23Ga abin da Sairus, sarkin Fasha, ya ce: "Yahweh, Allahn sammai, ya bani dukkan mulkokin duniya. Ya umarce ni in gina gida dominsa a Yerusalem, wanda yake a Yahuda. Duk wanda ke cikinku daga dukkan mutanesa, Yahweh Allahnku, ya kasance tare da ku. Bari ya haura can zuwa ƙasar."

Littafin ezra

1

1A shekarar farko ta sarautar Sairus, sarkin Fasiya, Yahweh ya cika maganarsa wadda ta zo ta bakin Irmiya, wadda ta motsa ruhun Sairus. Muryar Sairus ta kai dukkan masarautarsa. Wannan shi ne abin da aka faɗa aka kuma rubuta:2"Sairus sarkin Fasiya ya ce; Yahweh, Allah na Sama, ya bani dukkan mulkokin duniya, ya kuma zaɓe ni in gina masa gida a Yerusalem a Yahudiya.

3Duk wanda ya ke daga cikin mutanensa (Ubangijinsa ya kasance tare da shi) zai tafi Yerusalem ya gina gida domin Yahweh, Allah na Isra'ila, Allah da ke a Yerusalem.4Mutanen da ke kowanne sashi na mulkin inda waɗanda suka ragu ke zama sai su basu guzirin azurfa da zinariya, da mallakoki da dabbobi, da kuma kyauta ta yardar rai domin gidan Allah a Yerusalem."
5Sai shugabannin zuriyar Yahuda da ta Benyamin, da firistoci da Lebiyawa, da duk waɗanda Allah ya iza ruhunsu su je su gina gidansa ya kafu.6Waɗanda ke kewaye da su suka taimaki aikinsu da azurfa da zinariya da kayayyaki, da dabbobi, da abubuwa masu daraja, da kyautai na yardar rai.
7Sarki Sairus kuma ya fito da kayayyakin da ke gidan Yahweh waɗanda Nebukadnezza ya kwaso daga Yerusalem ya kuma ajiye a gidajen allolinsa.8Sai Sairus ya danƙa su a hannun Miteredat ma'aji, wanda ya ƙirga su ta hannun Sheshbazza shugaban Yahudiya.
9Wannan shi ne yawansu: daro talatin na azurfa, daro dubu ɗaya na zinariya, da kuma wasu daro ashirin na sauran kayayyaki,10Tasoshi talatin na azurfa, ƙananan tasoshi na zinariya guda 410, da kuma sauran kayayyaki guda dubu.11Akwai a ƙalla kayayyakin zinariya da azurfa guda 5,400 da aka haɗa jimla dukka. Sheshbazza ya kawo dukkan waɗannan a lokacin da masu zaman talala suka fita daga Babila zuwa Yerusalem.

2

1Waɗannan su ne mutanen lardin da suka fita daga bautar talalar sarki Nebukadnezza, wanda ya bautar da su a Babila, mutanen da suka koma biranensu na Yerusalem da kuma Yahudiya.2Sun dawo tare da Zerubbabel, Yoshuwa, Nehemiya, Serayya, da Re'elaya, Modekai, Bilshan, Misfar, Bigbai, Rehum, da Bãna. Wannan shi ne lissafin mutanen Isra'ila.

3Zuriyar Farosh: 2,172.4Zuriyar Shefatiya: 372.5Zuriyar Arak: 775.6Zuriyar Fahat Mowab, ta wurin Yeshuwa da Yowab: 2,812.
7Zuriyar Elam: 1254.8Zuriyar Zattu: 945.9Zuriyar Zakkai: 760.10Zuriyar Bani: 642.
11Zuriyar Bebai: 623.12Zuriyar Azgad: 1,222.13Zuriyar Adonikam: 666.14Zuriyar Bigbai: 2,056.
15Zuriyar Adin: 454.16Mutanen Ater, ta wurin Hezekiya: su tasa'in da takwas.17Zuriyar Bezai: 323.18Zuriyar Yorah: 112.
19Mutanen Hashum: 223.20Mutanen Gibba: tasa'in da biyar.21Mutanen Betlehem: 123.22Mutanen Netofa: hamsin da shida.
23Mutanen Anatot:128.24Mutanen Azmabet: arba'in da biyu.25Mutanen Kiriyat Arim, Kefira, da Birot: 743.26Mutanen Rama da Geba: 621.
27Mutanen Mikmas:122.28Mutanen Betel da Ai: 223.29Mutanen Nebo: hamsin da biyu.30Mutanen Magbish: 156.
31Mutanen ɗayar Elam: 1,254.32Mutanen Harim: 320.33Mutanen Lod, Hadid, da Ono: 725.
34Mutanen Yeriko: 345.35Mutanen Senã: 3,630.
36Sai firistoci zuriyar Yedayya na gidan Yeshuwa: 973.37Zuriyar Immer: 1,052.38Zuriyar Fashur: 1,247.39Zuriyar Harim: 1,017.
40Lebiyawa zuriyar Yeshuwa da Kadmiyel zuriyar Hodabiya: saba'in da huɗu.41Mawaƙan haikali, zuriyar Asaf: 128.42Zuriyar masu kula da ƙofa: na Shallum, Ater, Talmon, Akkub, Hatita, da Shobai: 139.
43Waɗanda aka sa su yi hidima a haikali: zuriyar Ziha, Hasufa, Tabbawot,44Keros, Siyaha, Fadon,45Lebana, Hagaba, Akkub,46Hagab, Shalmai, da Hanan.
47Zuriyar Giddel: Gahar, Re'ayya,48Rezin, Nekoda, Gazzam,49Uzza, Faseya, Besai,50Asnah, Meyunim, da Nefusim.
51Zuriyar Bakbuk: Hakufa, Harhur,52Bazlut, Mehida, Harsha,53Barkos, Sisera, Tema,54Neziya, da Hatifa.
55Zuriyar bayin Suleman: zuriyar Sotai, Hassoferet, Feruda,56Jãla, Dakon, Giddel,57Shefatiya, Hattil, Fokeret Hazzebem, da Ami.58Akwai 392 jimlar zuriyar waɗanda aka sasu yi aiki a haikali da kuma zuriyar bayin Suleman.
59Waɗanda suka fita Tel Melah, Kerub, Addon, da Imma - amma basu iya gane asalinsu a Isra'ila ba -60sun kai 652 in an haɗa da zuriyar Delayya, Tobiya, da Nekoda.
61Hakanan, daga zuriyar firistoci: da zuriyar Habayya, Hakkoz, da Barzillai (wanda ya auro matarsa daga 'ya'yan Barzillai ta Gileyed waɗanda kuma ake kiran su da sunansu).62Sun yi ta bincika asalinsu amma basu samo su ba don haka aka cire su daga aikin firist saboda rashin tsarki.63Don haka gwamnan ya ce da su kada su ci duk wani abu mai tsarki na hadaya har sai firist da Urim da Tummin sun amince.
64Aka haɗa jimlarsu dukka ta kai mutum 42,360,65ba a haɗa da bayinsu ba (waɗannan sun kai 7,337) da mazansu da matansu mawaƙan haikali sun kai (ɗari biyu).
66Dawakansu: 736.67Takarkaransu: 245. Raƙumansu: 435. Jakunansu: 6,720.
68Da suka je gidan Yahweh a Yerusalem, manyan ubanni suka yi bayarwa ta yardar rai don a gina gida.69Sun bayar gwargwadon iyawarsu don asusun raya aikin: suka bada awon zinariya sittin da ɗaya, da azurfa jaka dubu biyar da kuma kayan sha na firistoci guda ɗari.
70To sai firistoci da Lebiyawa, da jama'a, da mawaƙan haikalin da masu tsaron ƙofofi, da waɗanda aka sa suyi hidima a haikali suka mallaki biranensu. Dukkan mutane a Isra'ila suka zauna a biranensu

3

1A wata na bakwai ne bayan da mutanen Isra'ila suka dawo biranensu, inda suka tattaru a matsayin al'umma ɗaya a Yerusalem.2Yeshuwa ɗan Yozadak da 'yan'uwansa firistoci, Zerubbabel ɗan Sheltiyyel da 'yan uwansa suka tashi don su gina bagadin haikalin Allah na Isra'ila don su miƙa hadaya ta ƙonawa kamar yadda aka umarta a shari'ar Musa mutumin Allah.

3Sai suka kafa bagadin a wurin tsayuwarsa, don sun firgita saboda mutanen ƙasar. Suka miƙa hadaya ta ƙonawa ga Yahweh da yammaci.4Hakanan suka yi idin bukkoki kamar yadda ya ke a rubuce suka riƙa miƙa hadaya kowacce rana kamar yadda aka aiyana, ana yin kowanne aiki bisa ga ranarsa.5Bisa ka'ida, akwai baye-baye na ƙonawa ta kowacce rana da kowanne wata da kuma baye-baye na kowanne idi na Yahweh da aka aiyana tare da dukkan kyautai na yardar rai.
6Suka fara miƙa baye-baye na ƙonawa ga Yahweh a rana ta farko a wata na bakwai, koda ya ke ba a kafa haikali ba tukuna.7Don haka suka bada zinariya ga masu aikin dutse da maƙera, suka bada abinci, da abin sha, da mai ga mutanen Sidon da Taya don su kawo itacen sida ta kan teku daga Lebanon zuwa Yoffa kamar yadda sarki Sairus ya bada umarni ga sarkin Fasiya.
8Sa'an nan a wata na biyu na shekara ta biyu bayan sun zo gidan Allah a Yerusalem, sai Zerubbabel ɗan Sheltiyyel, Yeshuwa ɗan Yozadak, da sauran firistoci da Lebiyawa da waɗanda suka dawo daga bauta zuwa Yerusalem suka fara aiki. Suka sa Lebiyawa 'yan shekaru ashirin su kula da aikin gidan Yahweh.9Yeshuwa yasa 'ya'yansa da 'yan'uwansa, Kadmiyel yasa 'ya'yansa, (da zuriyar Hodabiya), kuma 'ya'yan Henadad da 'ya'yansu da 'yan'uwansa - dukkansu Lebiyawa ne - da suka haɗu tare wajen lura da masu yin aikin gidan Allah.
10Masu ginin suka kafa harsashen ginin haikalin Yahweh. Wannan yaba firistoci da masu sa tufafinsu da kayan hurawarsu, su kuma Lebiyawa 'ya'yan Asaf suka yabi Yahweh da garaya, kamar yadda Dauda ya yi umarni.11Suka rera waƙar yabo da godiya ga Yahweh, Cewa "Shi nagari ne! Amintaccen alƙawarinsa mai aminci ga Isra'ila ya tabbata har abada."Dukkan mutane suka tada babbar murya da ƙarfi suna yabon Yahweh saboda kafa harsashin ginin haikalin da aka yi.
12Amma da yawa daga cikin firistoci da Lebiyawa, da manyan ubannin shugabanni, da tsofaffin mutanen da suka ga lokacin da aka kafa harsashen ginin haikali na farko suka yi kuka da ƙarfi. Amma da yawa suka rera waƙar farinciki da murna da muryoyi masu daɗi.13A sakamakon haka mutane ba su iya tantance muryar farinciki da ta baƙinciki ba, Don mutane suna ta kuka da matuƙar farinciki, kuma an jiwo ƙararsu daga nesa.

4

1Yanzu kuwa waɗansu abokan gãba na Yahuda da Benyamin suka ji cewa mutanen da ke ƙasar bauta sun fara gina haikali domin Yahweh, Allahn Isra'ila.2Sai suka tuntuɓi Zarubbabel da sarakunan zuriyoyin kakaninsu. Suka ce da su, "Bari mu yi gini tare da ku, gama kamar ku, muna neman Allahnku kuma mun yi hadaya gare shi tun kwanakin da Esarhadon, sarkin Asiriya, ya kawo mu nan wurin."

3Amma Zarubbabel da Yeshuwa da shugabanin dangogin kakannin suka ce, "Ba ku ba ne, amma mune waɗanda tilas ne mu gina gidan Allahnmu, gama mune waɗanda zasu yi gini domin Yahweh, Allah na Isra'ila, kamar yadda sarki Sairus na Fasiya ya umarta."
4Sai mutanen ƙasar suka sa hannuwan mutanen Yahuda suka raunana;5Suka sa mutanen Yahuda suka tsorata da ci gaba da yin ginin. Suka kuma ba mashawartan cin hanci don su lalatar da shirin. A wannan lokacin sun yi haka a dukkan kwanakin sarki Sairus har zuwa mulkin Dariyos sarkin Fasiya.6To sai a farkon mulkin Ahasuras suka rubuto takardar tuhuma game da mazaunan Yahuda da Yerusalem.
7A kwanakin Atazazas ne Bishilam, da Mitiredat, Tabiyel da aminansu suka rubuto wa Atazazas. An rubuta wasiƙar a harshen Aramaik aka kuma fassara.8Rehum babban rundunan sojoji da Shimshaya marubuci sun rubuta haka ga Atazazas game da Yerusalem.
9Sai Rehum da Shimshaya da aminansu waɗanda ke Alƙalai da waɗansu hafsoshi a gwamnati, da Fasiyawa, daga mazajen Irek da Babila da mazajen Susa (wato Ilemawa) - suka rubuta wasiƙa -10suka haɗa kai da mutane masu daraja da Ashurbanifal ya tilasta su zama a Samariya suka bi su tare da sauran waɗanda ke a Lardin Gaba da Kogin.
11Wannan ne kwafin wasiƙar da suka aika wa Atazazas: "Barorinka, mazajen Lardin Gaba da Kogin, sun rubuta wannan:12Bari sarki ya sani cewa Yahudawan da suka tafi daga gareka sun taso mana a Yerusalem don su gina birnin tayarwa. Sun kammala garun da gyare-gyaren harsasun.
13Yanzu kuwa bari sarki ya sani cewa idan birnin nan ya ginu kuma an kammala garun, ba zasu bayar da kuɗin fito da haraji ba, amma zasu azabtar da sarakunan.
14Tabbas saboda mun ɗanɗana gishirin fãda, bai cancanci mu ga wani raini na faruwa da sarki ba. Saboda haka ne muke sanar da sarki15ka duba daga cikin rubutun kididdiga na mahaifinka don ka tabbatar da cewa wannan birnin tayarwa ne da zai azabtar da sarakuna da lardunan. Ya sha tayar da matsaloli ga sarki da kuma larduna. Ya kuma zama cibiyar tawaye tun da daɗewa. Dalilin haka ne ma aka hallakar da birnin.16Muna sanar da sarki cewa idan aka gina wannan birnin da garun, to babu wani abin da zai rage dominka a Lardin Gaba da Kogin."
17Sai sarkin ya aika da amsa ga Rehum da Shimshaya da aminansu a Samariya da sauran waɗanda ke a Lardin Gaba da Kogin: "Salama gareku.18Wasiƙar da kuka aika mani an karanta an kuma fassara mani.19Don haka nasa aka yi bincike kuma na gano cewa a kwanakin baya sun yi tayarwa da rashin hankali ga sarakuna.
20Sarakuna masu iko sun yi mulki a kan Yerusalem kuma sun kasance da iko a kan kowanne abu a Lardin Gaba da Kogin. Ana kuma biyansu haraji.21Yanzu kuwa a yi umarni ga waɗannan mutanen su tsaya kuma kada su gina wannan birnin sai na umarta.22Ku yi hankali kar ku yi banza da wannan. Me zai sa a bar wannan jayayyar ta yi girma ta sa mu hasara a wannan masarauta?
23Sa'ad da aka karanta umarnin sarki Atazazas a gaban Rehum, da Shimshaya da aminansu, sai suka fita da sauri zuwa Yerusalem suka sa Yahudawan su tsayar da ginin.24Don haka aiki a gidan Allah a Yerusalem ya tsaya har zuwa shekara ta biyu ta mulkin Dariyos sarkin Fasiya.

5

1Sai annabi Haggai da Zakariya ɗan annabi Iddo suka yi annabci da sunan Allah na Isra'ila ga Yahudawa a Yahuda da Yerusalem.2Zarubbabel ɗan Sheltiyyel da Yeshuwa ɗan Yozadak suka tashi tsaye suka fara gina gidan Allah a Yerusalem tare da annabawan da suka ƙarfafa su.

3Daga nan Tattenai gwamnan Lardin Gaba da Kogin, Shetar Bozenai, da abokan aikinsa suka zo suka ce masu, "Wane ne ya baku umarni ku gina wannan gidan ku kuma ƙarasa waɗannan katangun?"4Sai suka kuma ce, Mene ne sunayen mutanen da ke yin wannan ginin?"5Amma idanun Allah na kan dattawan Yahudawa kuma maƙiyansu basu tsayar da su ba. Suna jiran wasiƙar da za a aika wa sarki da kuma umarnin da za a komar masu game da wannan.
6Wannan shi ne kwafin wasiƙar Tattenai wato gwamnan Lardin Gaba da Kogi, da Shetar Bozinai da tawagarsa a cikin Lardin Gaba da Kogi, wanda suka aikawa sarki Dariyos.7Sun aika da rahoto, suka rubuta wa sarki Dariyos haka, "Bari dukkan salama ta zama taka.
8Bari sarki ya sani cewa mun je Yahuda gidan Allah mai Girma. Ana gininta da manyan duwatsu da katakan da aka shirya a ganuwar. Wannan aikin kuwa ana yin sa sosai da sosai, kuma yana tafiya dai-dai a hannuwansu.9Muka tambayi dattawan, 'Wa ya baku umarni ku gina wannan gida da wannan ganuwar?'10Mun kuma tambayi sunayensu domin ka iya sanin sunan kowanne mutum da ya jagorance su.
11Suka amsa suka ce, 'Mu barorin wanda shi ne Allah na sama da ƙasa, kuma muna ginin wannan gida wanda aka gina a shekarun baya masu yawa a sa'ad da sarki mai girma na Isra'ila ya gina, ya kuma ƙarasa shi.
12Koda ya ke, Sa'ad da kakaninmu suka sa Allah na sama ya yi fushi, sai ya bada su ga hannuwan Nebukadnezza, sarkin Babila, wanda ya rushe wannan gidan ya kuma ɗauke mutanen zuwa ɓauta a Babila.13Duk da haka, a shekara ta fari sa'ad da Sairus ya ke sarkin Babila, Sairus ya bada umarni a gina gidan Allah.
14Sarki Sairus ya kuma mayar da kayayyakin zinariya da azurfa na gidan Allah da Nebukadnezza ya kawo daga haikali a Yerusalem zuwa ga haikali na Babila. Ya mayar da su ga Sheshbazza, wanda yasa ya zama gwamna.15Ya ce da shi, "‌Ɗauki waɗannan kayayyakin. Tafi ka aje su a haikali a Yerusalem. Bari a sake gina gidan Allah a wurin."
16Sai Sheshbazza yazo ya ƙafa harsashe domin gidan Allah a Yerusalem; kuma ana kan yi, amma ba a ƙarasa shi ba.'
17Yanzu kuwa, idan sarki ya yarda, sai a bincika a gidan ajiyar rahotonin dã a Babila koda akwai huƙunci daga Sarki Sairus game da gina gidan Allah a Yerusalem. To sai sarki ya aiko da ra'ayinsa gare mu.

6

1Sai sarki Dariyos ya bada umarni a yi bincike a gidan ajiyar rahotanin dã a Babila.2A ƙasaitaccen birnin Ikbatana a Midiya aka sami takarda; wannan ne abin da aka rubuta a cikinta:

3A shekara ta farko ta Sarki Sairus, Sairus ya bada umarni game da gidan Allah a Yerusalem: 'Bari gidan ya sake ginuwa domin ya zama wurin hadaya, bari a kafa harsasunsa, bari tsawonsa ya zama kamu 27, faɗinsa kamu 27,4da layin manyan duwatsu guda uku da layi ɗaya na sababbin katakai, kuma bari gidan sarki ya biya duk kuɗin da aka kashe.5Yanzu a dawo da kayayyakin zinariya da azurfa na gidan Allah wanda Nebukadnezza ya kawo Babila daga haikali a Yerusalem sai a aika da su kuma ga haikali a Yerusalem. Zaku kuwa aje su a gidan Allah.'
6Yanzu Tattenai, gwamnan Lardin Gaba da Kogi da Shetar Bozinai da tawagar da ke Lardin Gaba da Kogi, ku rabu da su!7Ku bar aikin gidan nan na Allah yadda ya ke. Gwamna da dattawan Yahudawa zasu gina wannan gidan Allah a wancan wurin.
8Ina umarta cewa tilas ne kuyi wannan domin waɗannan dattawan Yahudawan da suka gina wannan gida na Allah: Kuɗi daga asusun sarkin gaba da Kogi za a yi amfani da su a biya waɗannan mutanen don kada su tsayar da aikinsu.9Ko mene ne ake bukata - bijimai, ko raguna, ko 'yan raguna domin hadaya ga Allah na Sama, ko hatsi, ko gishiri, ko ruwan inabi, ko mai bisa ga umarnin firistocin Yerusalem - ku ba su waɗannan abubuwa kowacce rana babu fasawa.10Ku yi wannan domin su kawo bayarwarsu ga Allah na Sama kuma ku yi mani addu'a, sarki, da 'ya'yansa.
11Ina umarta cewa duk wanda ya taka wannan doka, za a ciro ginshiƙi daga gidansa a soke shi da shi. Gidansa kuwa tilas ne a mayar da shi juji saboda wannan.12Bari Allah wanda yasa sunansa ya zauna a wurin ya cisge kowanne sarkin ko mutanen da suka ɗaga hannu su canza wannan doka, ko su lalata wannan gidan na Allah a Yerusalem. Ni, Dariyos, nake umarta wannan. Bari a yi tare da kula!"
13To saboda umarnin da sarki Dariyos ya aika, Tattenai, gwamnan Lardin Gaba da Kogi da Shetar-Bozinai da abokan aikinsa, suka yi dukkan abin da Sarki Dariyos ya umarta.14Saboda haka dattawan Isra'ila suka yi ginin kamar yadda Haggai da Zakariya suka umarta ta wurin annabci. Suka gina shi bisa ga dokar Allah na Isra'ila da Sairus da Dariyos da Atazazas, sarakuna Fasiya15An kammala gidan a rana ta uku ga watan Adar, a shekara ta shida ta mulkin sarki Dariyos.
16Mutanen Isra'ila da firistoci da Lebiyawa da sauran masu zaman bauta suka yi bukin keɓe gidan Allah tare da jin daɗi.17Suka ba da bijimai ɗari da raguna ɗari da 'yan raguna ɗari huɗu domin keɓe gidan Allah. Awaki goma sha biyu aka bayar a matsayin bayarwa ta wanke zunubi domin dukkan Isra'ila, ɗaya domin kowacce kabilar Isra'ila.18Suka kuma sa firistoci da Lebiyawa su rarraba wa mutanen aiki domin sujada ga Allah a Yerusalem, kamar yadda aka rubuta a Littafin Musa.
19Saboda haka waɗanda suke cikin bauta suka yi bukin idin Ƙetarewa a watan huɗu.20Firistocin da Lebiyawa dukka suka tsarkake kansu suka kuma yanyanka hadayun idin ‌Ƙetarewa domin dukkan waɗanda suka yi bauta, har da su kansu.
21Mutanen Isra'ila da suka ci kaɗan daga cikin naman idin ‌Ƙetarewa su ne waɗanda suka dawo daga bauta suka kuma raba kansu daga rashin tsarkin mutanen ƙasar suka kuma biɗi Yahweh, Allah na Isra'ila.22Cikin jin daɗi kuwa suka sha shagulgulan bukin gurasa marar gami har kwanaki bakwai, gama Yahweh ya kawo masu jin daɗi ya kuma juya zuciyar sarkin Asiriya ta ƙarfafa hannunsu a cikin aikin gidansa, gidan Allah na Isra'ila.

7

1Yanzu bayan wannan, a zamanin mulkin Atazazas sarkin Fasiya, Ezra ya dawo daga Babila. Kakannin Ezra su ne kamar haka, Seraiya, Azariya, Hilkiya,2Shallum, Zadok, Ahitub,3Amariya, Azariya, Merayot,4Zerahiya, Uzzi, Bukki,5Abishuwa, Fenihas, Eliyeza, wanda shi ne ɗan Haruna babban firist.

6Ezra ya dawo daga ƙasar Babila kuma ƙwararren marubuci ne cikin shari'ar Musa wanda Yahweh, Allah na Isra'ila, ya bayar. Sarki ya ba shi dukkan abin da ya ke buƙata domin hannun Yahweh na tare da shi.7Wasu daga cikin zuriyar Isra'ila da kuma firistoci, da Lebiyawa, da mawaƙan haikali, da masu tsaron ƙofa da kuma waɗanda aka shirya domin hidima a haikali suma suka tafi Yerusalem a cikin wata na bakwai na mulkin Atazazas.
8Ya isa Yerusalem a wata na biyar na wannan shekara.9Ya baro Babila a rana ta ɗaya na watan farko. A rana ta ɗaya ne na watan biyar ya isa Yerusalem, tun da hannun Allah mai kyau na tare da shi.10Ezra ya kafa zuciyarsa domin ya yi bincike, ya aikata, ya kuma koyar da farillai da hukumtai da dokokin Yahweh.
11Wannan shi ne umarnin da sarki Atazazas ya ba Ezra firist da kuma marubucin dokoki da farillun Yahweh domin Isra'ila.12"Sarkin sarakuna Atazazas, zuwa ga firist Ezra, marubuci na dokokin Allah na sama:13Ina bada umarni cewa kowannene daga Isra'ila cikin harabar mulkina tare da firistocinsu da Lebiyawa da ya ke da niyar tafiya zuwa Yerusalem, zaya iya tafiya da kai.
14Ni, sarki, tare da mashawartana guda bakwai, muna aiken ku dukka ku bincika game da Yahuda da kuma Yerusalem bisa ga dokokin Allah, wanda ke cikin hannuwanku.15Ku dawo da azurfa da zinariyar da suka bayar da yardar rai zuwa ga Allah na Isra'ila, wanda mazauninsa ke a Yerusalem.16Ku bayar hannu sake dukkan azurfa da zinariya da dukkan Babila ta bayar kuma da dukkan abin da mutane da firistoci suka bayar hannu sake domin gidan Allah a Yerusalem.
17Saboda haka ku saya da farashi cikakke shanun, da ragunan, da 'yan tumakin, da hatsi da baye-baye na sha. Ku miƙa su a bisa bagadin da ke cikin gidan Allahnku a Yerusalem.18Ku yi haka da sauran azurfar da zinariyar dukkan abin da kuka ga ya dace maku da 'yan'uwanku, domin ku gamshi Allahnku.
19Ku ɗibiya kayayyakin da aka yi maku kyautarsu a gabansa domin hidima cikin gidan Allahnku a Yerusalem.20Duk wani abin da ake buƙata domin gidan Allahnku da za kuyi bukatarsa, sai a biya daga cikin ma'ajina.
21Ni, sarki Atazazas, na yi umarni ga dukkan masu ajiya cikin Lardin Gaba da Kogi, da cewa dukkan abin da Ezra zai yi buƙata daga gareku bari a ba shi a cike,22har sama da talantai na azurfa ɗari, tuli buhu ɗari na hatsi, da ruwan inabi gallan ɗari, da gallan ɗari na mai, da kuma gishiri babu iyaka.23Dukkan abin da suka fito daga umarnin Allah na Sama, ka aikata da kuzari, domin gidansa. Donme ne ne hasalarsa za ta yi ƙuna a bisa masarauta ta da 'ya'yana?
24Muna sanar da su game da ku da kada su ɗora maku wata tãra ko haraji ga kowanne firistoci, ko Lebiyawa, ko mawaƙa, ko masu tsaron ƙofa, ko ga mutanen da aka ba hidimar haikalin da kuma bayin gidan wannan Allah.
25Ezra, ta wurin hikimar da Allah ya baka, dole ka naɗa alƙalai da masanan hikima su yiwa mutane hidima a cikin dukkan Lardin Gaba da Kogi, su kuma yi hidima ga kowannene da ya san shari'ar Allahnka. Dole kuma ka koyar da shari'ar ga dukkan waɗanda basu san dokar ba.26Ku hori duk wanda ba ya yi cikakkiyar biyayya ga shari'ar Allah ba ko shari'ar sarki ba, ko ta mutuwa, ko kora daga ƙasa, ko a ƙwace mallakarsu, ko jefawa cikin kurkuku.
27Yi yabo ga Yahweh, Allahn kakanninmu, wanda ya sanya dukkan wannan cikin zuciyar sarki ya ɗaukaka gidan Yahweh cikin Yerusalem,28kuma wanda ya nuna amincin alƙawarinsa gareni a gaban sarki, da mashawartansa, da kuma dukkan majalisarsa masu iko. Na sami ƙarfafawa daga hannun Yahweh Allahna, sai na tara shugabanni daga Isra'ila su tafi tare da ni.

8

1Waɗannan su ne shugabanni na kakannin iyalansu waɗanda suka baro Babila tare da ni a zamanin mulkin sarki Atazazas.2Na zuriyar Fenihas, Geshom. Na zuriyar Itamar, Daniyel. Na zuriyar Dauda, Hattush,3wanda ya zama na zuriyar Shekaniya, wanda ya zama daga zuriyar Farosh; da kuma Zakariya, kuma tare da shi akwai mazaje 150 da aka lisafta su cikin rubutattun tarihin zuriyarsu.

4Na zuriyar Fahat Mowab, Elihonai ɗan Zerahiya kuma tare da shi akwai mazaje ɗari biyu.5Na zuriyar Zatti, Ben Yahaziyel kuma tare da shi akwai mazaje ɗari uku.6Na zuriyar Adin, Ebed ɗan Yonatan kuma tare da shi an lisafta mazaje hamsin.7Na zuriyar Ilam, Yeshayya ɗan Ataliya kuma tare da shi an lisafta mazaje saba'in.
8Na zuriyar Shefatiya, Zebadiya ɗan Mikayel kuma tare da shi an lisafta mazaje tamanin.9Na zuriyar Yowab, Obadiya ɗan Yehiyel kuma tare da shi aka lisafta mazaje 218.10Na zuriyar Bani, Shelomit ɗan Yesofiya kuma tare da shi aka lisafta mazaje 160.11Na zuriyar Bebai, Zakariya ɗan Bebai kuma tare da shi aka lisafta mazaje ashirin da takwas.
12Na zuriyar Azgad, Yohanan ɗan Hakkatan kuma tare da shi aka lisafta mazaje 110.13Waɗanda suke daga zuriyar Adonikam suka zo daga baya. Waɗannan su ne sunayensu: Elifelet, Yewuyel, tare da Shemayya kuma mazaje sittin ne suka zo tare da su.14Na zuriyar Bigbai, Uttai da Zakku kuma tare da shi aka lisafta mazaje saba'in.
15Na tara matafiyan a mashigin daya tafi har zuwa Ahaba, kuma muka yi sansani a nan kwana uku. Na bincike mutanen da kuma firistoci, amma babu wani daga zuriyar Lebi a nan.16Sai na aika a kirawo mani Eliyeza, da Ariyel, da Shemayya, da Elnatan, da Yarib, da kuma Elnatan da Natan, da Zakariya da kuma Meshullam - waɗanda su ne shugabanni - da kuma Yoyarib tare da Elnatan waɗanda su ne masu koyarwa.
17Daga nan sai na aike su wurin Iddo, shugaban da ke a Kasifiya. Na faɗa masu abin da zasu faɗawa Iddo da kuma danginsa, su bayi na haikali da ke zaune a Kasifiya, wato, su aika mana da bayi domin gidan Allah.
18Sai suka aika mana ta hannun Allahnmu mai nagari mutum mai suna Sherebiya, mutum mai tattali. Shi daga zuriyar Mahali ne ɗan Lebi ɗan Isra'ila. Ya zo da 'ya'ya sha takwas da 'yan'uwa.19Hashabiya ya zo tare da shi. Haka kuma akwai Yeshayya, ɗaya daga cikin 'ya'yan Merari, da ɗan'uwansa tare da 'ya'yansu, dukkan su mazaje ashirin.20Cikin waɗanda aka ɗaurawa hidimar haikali, waɗanda Dauda da bayinsa suka ɗora wa haƙin yiwa Lebiyawa hidima: 220, kowanne ɗayansu aikinsa bisa ga sunansa.
21Sai nayi shelar azumi a mashigin Ahaba domin mu ƙasƙantar da kanmu a gaban Allah, mu biɗi hanya madaidaiciya dominmu, domin ƙanananmu, da dukkan mallakarmu.22Na ji kunyar tambayar sarki sojoji ko dawakai da zasu yi tsaronmu daga maƙiya a hanya, gama mun gaya wa sarki, 'hannun Allah na bisa dukkan waɗanda suka neme shi da gaskiya, amma ƙarfinsa da fushinsa na bisa dukkan waɗanda suka manta da shi.'23Sai muka yi azumi muka nemi Allah game da wannan, muka yi roko gare shi.
24Daga wannan sai na zaɓi mazaje guda sha-biyu daga cikin shugabannin firistoci: Sherebiya, Hashabiya, da kuma yan'uwansu guda goma.25Na auna masu azurfa goma, da zinariya, da kayayyaki da baye-baye na gidan Allah da sarki, da mashawartansa da kuma shugabanninsu, da dukkan Isra'ila suka bayar hannu sake.
26Sai na auna cikin hannunsu azurfa talanti 650, talanti ɗari na kayayyakin azurfa, talanti ɗari na zinariya,27kwanonin zinariya guda ashirin waɗanda aka haɗa su dukka aka ƙimanta farashinsu akan sulallan zinari dubu ɗaya, da kuma a kan gogaggun tagulla biyu masu daraja kamar zinariya.
28Sa'an nan na ce masu, "An keɓe ku ga Yahweh, da waɗannan kayayyakin, kuma azurfar da zinariyar dukka baiko ne na yardar rai ga Yahweh, Allah na kakaninku.29Ku kula da su ku kuma adanasu, har sai kun auna su a gaban shugabannin firistoci, da Lebiyawa, da kuma shugabannin kakannin zuriyar Isra'ila a Yerusalem cikin ɗakunan gidan Allah."30Su firistoci da kuma Lebiyawa suka yi na'am da azurfa, da zinariya da kuma kayayyakin da aka auna domin su tafi da su Yerusalem, zuwa gidan Allahnmu.
31Muka fito daga mashigin Ahaba a rana ta sha biyu na watan farko domin mu tafi Yerusalem. Hannun Allahnmu na a bisanmu; ya kare mu daga hannun maƙiyanmu da kuma waɗanda suka yi niyyar yi mana kwanto a kan hanya.32Sai muka shiga Yerusalem muka kwana uku a cikinta.
33Daga nan a rana ta huɗu aka auna azurfa, da zinariya, da kuma kayayyakin cikin gidan Allahnmu ta hannun Meremot ɗan Yuriya firist, kuma tare da shi akwai su Eliyeza ɗan Fenihas, Yozabad ɗan Yeshuwa, da kuma Nodiya ɗan Binnui Balebi.34Aka tabbatar da jimilla da nauyin komai. Dukkan nauyin komai aka rubuta a wannan lokacin.
35Waɗanda suka komo daga bautar talala, su mutanen 'yan gudun hijira, suka miƙa ƙonannun baye-baye zuwa ga Allah na Isra'ila: raguna goma sha biyu, awakai tasa'in da shida, tumaki guda saba'in da bakwai, da kuma tunkiyoyi goma sha biyu domin hadayar zunubi. Dukkansu hadayu ne na ƙonawa na Yahweh.36Sa'an nan suka ba da umarnai na sarki ta hannun manyan shugabannin sarki da kuma gwamnonin Lardin Gaba da Kogi. Sai kuma suka taimaki jama'ar da kuma gidan Allah.

9

1Bayan waɗannan abubuwa sun faru, shugabanni suka same ni suka ce, "Mutanen Isra'ila, da firistoci da Lebiyawa basu keɓe kansu daga mutanen sauran ƙasashe ba da kuma abin ƙyamarsu: Kan'aniyawa da Hittiyawa da Ferizziyawa da Yebusiyawa da Ammoniyawa da Mowabiyawa da Masarawa da kuma Amoriyawa.2Domin sun ɗauki wasu daga cikin 'yan matansu da samarinsu, kuma sun hada mutane masu tsarki da sauran mutanen ƙasashen, shugabanni da magabata su ne na farko ga wannan rashin bangaskiya."

3Lokacin da na ji wannan, na yayyage rigata da alkyabbata na kuma tsittsige gashin kaina da gemuna, sai na zauna a ruɗe.4Sai dukkan waɗanda suka yi rawar jiki saboda maganar Allah na Isra'ila saboda wannan rashin aminci da suka same ni lokacin da nake zaune ina jin kunya har baikon yamma.
5Amma a lokacin baikon yamma sai na tashi daga matsayin ƙasƙanci a cikin rigata da alkyabbata a yayyage, na russuna da gwiwoyina, na ɗaga hannuwana zuwa ga Yahweh Allahna.6Na ce, "Ya Allahna, ina jin kunya da takaici in ɗaga fuskata gare ka, muguntarmu ta ƙaru a kanmu, kuma zunubanmu sun yi girma har sun kai sammai.
7Tun daga lokacin kakanninmu har yanzu muna da babban laifi. Saboda zunubanmu, mu da sarakunanmu, da firistocinmu sun bada mu a hannun sarakunan wannan duniya, ga takobi, ga bauta, da ganima da kuma kunyatar da mu, kamar yadda muke a yau.
8Amma yanzu a ƙaramin lokaci, alheri daga Yahweh Allahnmu ya zo ya bar mana ringi ya kuma bamu wuri a wurinsa mai tsarki. Wannan yasa Allahnmu ya buɗe mana idanu, ya kuma bamu 'yar wartsakewa daga bautarmu.9Domin mu bayi ne, amma duk da haka Allahnmu bai manta da mu ba amma ya cika alƙawarinsa da amincinsa a gare mu. Ya yi wannan ta wurin sarkin Fasiya domin ya bamu ƙarfi, don mu sake gina gidan Allahnmu mu kuma sake gyaransa. Ya yi wannan saboda ya bamu tsaron gina garu a Yahuda da Yerusalem.
10Amma yanzu, Allahnmu, me zamu ce bayan wannan? Mun manta da umarnanka,11umarnan daka ba bayinka annabawa, daka ce, "Wannan ƙasar da kuke shiga don ku mallake ta ƙazamtaciyar ƙasa ce. Ta ƙazamtu ta wurin mutanen ƙasar da abubuwan ƙyamarsu. Sun cikata daga ƙarshe zuwa ƙarshe da abubuwansu na ban ƙyama.12Saboda haka, kada ku bada 'ya'yanku 'yan mata su auri 'ya'yansu maza; kada ku ɗauki 'ya'yansu mata don 'ya'yanku maza, kuma kada ku nemi salamarsu da jin daɗi, don zaku yi ƙarfi ku ci abu mai kyau a ƙasar, domin zaku sa 'ya'yanku su gaje ta a dukkan lokaci."
13Bayan da dukkan abubuwan nan suka same mu saboda mugayen ayyukanmu da zunubanmu masu yawa - tun da kai, Allanmu, ka ɗauke dukkan laifoffinmu ka kuma bar mana ringi -14ko zamu sake karya umarninka mu kuma yi auratayya tare da waɗannan mutane da ke ƙazamtattu? Ba zaka yi fushi da mu ka shafe mu don kada a sami wani da ya rage, har babu wani da zai tsira ba?
15Yahweh, Allah na Isra'ila, kai mai adalci ne, gama mun zama 'yan ringi da suka tsira a wannan rana. Duba! Ga mu nan gabanka da zunubanmu, don ba wanda zai iya tsayawa a gabanka saboda wannan.

10

1Sa'ad da Ezra ya ke yin addu'a da roƙon gafara, ya yi kuka har yasa kansa ƙasa a gaban gidan Allah. Sai babban taron jama'a maza da mata da yara daga Isra'ila suka taru wurinsa, don mutane na kuka mai zafi sosai.2Shekaniya ɗan Yehiyel na zuriyar Elam ya ce da Ezra, "Mun yiwa Allahnmu rashin aminci har mun auri mata bãƙi daga mutanen ƙasar waje. Amma duk da haka akwai sauran bege ga Isra'ila.

3Saboda haka yanzu bari muyi alƙawari da Allahnmu mu kori dukkan matan da 'ya'yansu bisa ga umarnin shugabanni da waɗanda suke rawar jiki don umarnin Allahnmu, bari a yi haka bisa ga doka.4Tashi, domin wannan hakinka ne ka aiwatar, mu kuma muna tare da kai. Ka yi ƙarfin hali, ka yi wannan."
5Ezra kuwa ya tashi, yasa shugabannin firistoci, Lebiyawa, da dukkan Isra'ila su yi alƙawarin aiki ta wannan hanyar. Saboda haka dukkansu suka ɗauki alƙawarin rantsuwa.6Sai Ezra ya tashi daga gidan Allah, ya tafi ɗakunan Yehohanan ɗan Eliyashib. Bai ci ko da gurasa ba bai kuma sha ruwa ba, tun da ya ke yana baƙinciki a kan rashin amincin waɗanda suka yi a zaman talala.
7Saboda haka suka aika da magana a Yahuda da Yerusalem ga dukkan mutane da suka komo daga zaman talala su kasance a Yerusalem.8Duk wanda bai zo ba a cikin kwana uku bisa ga umarni daga shugabanni da dattawa zai rasa dukkan abin da ya mallaka za a kuma ware shi daga cikin babban taron mutanen da suka dawo daga zaman talala.
9Sai dukkan mutanen Yahuda da na Benyamin suka taru a Yerusalem a cikin kwana uku. A ranar ashirin ga watan tara. Dukkan mutanen suka tsaya a dandalin gidan Allah, suna kuma rawar jiki saboda maganar da kuma ruwan sama.10Ezra firist kuma ya miƙe tsaye ya ce, "Ku kunyi rashin aminci. Kun zauna da mata bãƙi ta haka kuka ƙarawa Isra'ila laifi.
11Amma yanzu sai ku bada yabo ga Yahweh, Allah na kakanninku, ku kuma aikata nufinsa. Ku ware daga mutanen ƙasar da mata bãƙi.
12Dukkan taron suka amsa da babbar murya, '"Za muyi kamar yadda ka ce.13Amma, akwai mutane da yawa, kuma lokacin marka ne. Ba mu da ƙarfin tsayawa a waje, kuma wannan ba aikin da za ayi shi a kwana ɗaya ko biyu bane, tun da mun yi babban laifi a wannan al'amari.
14Saboda haka bari shugabanninmu su wakilci dukkan taron. Bari dukkan waɗanda suka bar baƙin mata su zauna a biranenmu su zo su sa lokaci tare da dattawan birni da kuma alƙalan birnin har sai fushin Allah ya huce daga kanmu.15Yonatan ɗan Asahel da Yazeyya ɗan Tikba ne basu yarda da wannan ba, da Meshullam da Shabbetai Balebi suka goyi bayansu.
16Saboda haka mutane waɗanda suka komo daga zaman talala suka yi wannan. Ezra firist ya zaɓi maza, da dattawa kakanin zuriyarmu da gidaje - dukkansu kuwa ta wurin sunaye, sai suka duba al'amarin a kan rana ta farko ga wata na goma.17Sun gama binciken a rana ta farko a wata na farko ga mazajen da suke zama tare da baƙin mata.
18A cikin zuriyar firistoci ma akwai waɗanda suke zama da bãƙin mata. A cikin zuriyar Yeshuwa ɗan Yehodak da ɗan'uwansa su ne Mãseyya, Eliyeza, Yarib da Gedaliya.19Suka yi niyyar sakin matansu. Tun da su masu laifi ne, suka bada baikon rago daga cikin garkensu don laifinsu.
20A cikin zuriyar Imma akwai Hanani da Zebadiya.21A cikin zuriyar Harim akwai Mãseyya da Iliya da Shemayya da Yehiyel da Uzziya.22A cikin zuriyar Fashu akwai Elihonai da Mãseyya, Isma'il da Netanel da Yozabad da Elasa.
23A cikin Lebiyawa akwai Yozabad da Shimei da Kelayya - wato Kelita, Fetahiya, Yahuda da Eliyeza.24a cikin mawaƙa akwai Eliyashib.25A cikin masu tsaron ƙofa akwai Shallum, Telem da Uri. A cikin sauran Isra'ilawa - a cikin zuriyar Farosh akwai Ramiya, Izziya, Malkiya, Miyamin, Eliyeza, Malkiya da Benayya.
26A cikin zuriyar Elam akwai Mattaniya, Zakariya, Yehiyel, Abdi, Yeremot da Iliya.27A cikin zuriyar Zattu akwai Elihonai, Eliyashib, Mattaniya, Yeremot, Zabad da Aziza.28A cikin zuriyar Bebai akwai Yehohanan, Hananiya, Zabbai da Atlai.29A cikin zuriyar Bani akwai Meshullam, Malluk, Adayya, Yashub da Shil Yeremot.
30A cikin zuriyar Fahat Mowab akwai Adana, Kelal, Benayya, Mãseyya, Mattaniya, Bezalel, Binnuyi da Manasse.31A cikin zuriyar Harim akwai Eliyeza, Ishiya, Malkiya, Shemayya, Shimiyon,32Benyamin, Malluk da Shemariya.
33A cikin zuriyar Hashum akwai Mattenai, Matatta, Zabad, Elifelet, Yeremai, Manasse, Shimei.34A cikin zuriyar Bani akwai Mãdai, Amram, Uwel,35Benayya, Bedeya, Keluhi,36Waniya, Meremot, Eliyashib,
37Mattaniya, Mattenai, da Yãsu.38A cikin zuriyar Binnuyi akwai Shimei,39Shelemiya, Natan, Adayya,40Maknadebai, Shashai, Sharai,
41Azarel, Shelemiya, Shemariya,42Shallum, Amariya da Yosef.43A cikin zuriyar Nebo: Yehiyel, Matitiya, Zabad, Zebina, Yaddai da Yowel da Benayya.44Dukkan waɗannan sun auro mata bãƙi kuma suna da 'ya'ya tare da wasun su.

Littafin nehemiya

1

1Maganar Nehemiya ɗan Hakaliya ke nan: A wata na Kislif, a shekara ta ashirin, a lokacin da nake a fãdar Shusha,2Sai wani daga cikin 'yan'uwana mai suna Hanani ya zo tare da waɗansu mutane daga Yahuda, sai na tambaye su labarin Yahudawan da suka tsira, da kuma sauran Yahudawan da ke a can, waɗanda ke a Yerusalem.

3Suka ce da ni "waɗanda suka kuɓuta daga zaman bauta suna cikin babbar damuwa da wulaƙanci, saboda ganuwar Yerusalem ta karye ta faɗi, an kuma ƙone ƙofofinta da wuta"
4Nan da nan bayan na ji waɗannan maganganu sai na zauna na yi kuka, har tsawon kwanaki ina damuwa da azumi a gaban Yahweh na sama.5Sai na ce Yahweh "kai ne Ubangiji Allah na sama, Allah wanda ya ke da girma da nagarta, mai cika alƙawari, mai kuma madawammiyar ƙauna ga masu ƙaunarsa da kuma kiyaye dokokinsa.
6Ka ji addu'ata ka kuma buɗe idanunka, don ka ji addu'o'in bayinka da nake yi a gare ka dare da rana, don mutaten Isra'ila bayinka. Ina furta zunuban mutanen Isra'ila, waɗanda suka yi maka. Duk da ni da gidan ubana mun yi zunubi.7Mun yi aikin mugunta sosai a gabanka kuma bamu kiyaye dokokinka da farillanka waɗanda ka ba mu ba, da kuma ƙa'idojin da ka umarci bawanka Musa.
8Ka tuna da abin da ka umarci bawanka Musa, cewa "In kun yi rashin biyayya, zan warwatsa ku cikin al'ummai,9amma in kun komo gare ni kuka kuma bi umarnina kuka aikata su, to ko da ya ke an warwatsa mutanenku a faɗin duniya, zan tattaro su daga can zan kuma kawo su wurin nan da na zaɓa domin sunana ya zauna."
10Yanzu su bayinka ne da kuma mutanenka, waɗanda ka kuɓutar da ƙarfin ikonka da kuma ƙarfin dantsenka.11Yahweh ina roƙon ka, ka saurari addu'ar bayinka yanzu, kuma addu'ar bayinka waɗanda ke son yi maka biyayya, yanzu ka ba bawanka nasara, ka kuma ba shi tagomashi a gaban wannan mutum." Ni mai aikin shayar da sarki ne.

2

1A watan Nisan, a shekara ta ashirin ta sarautar Atazazas sarki, ya zaɓi ruwan inabi, sai na ɗauki ruwan inabin na ba sarki. Sai ya zamana fuskata ta ɓaci a gaban sarki kuma ban taba ɓata fuska a gabansa ba.2Amma sarki ya ce mani " me ya sa fuskarka ta ɓaci haka? Kuma gashi ba ciwo kake yi ba. Hakika wannan damuwar zuciya ce "Daga nan sai na tsorata sosai.

3Na ce da sarki "Ran sarki ya daɗe! me zai hana ni baƙinciki? Da ya ke birni da maƙabartar iyayena sun zama kufai, kuma an ƙone ƙofofinta da wuta."
4Sai sarki ya ce mani "Me kake so in yi?" Sai na yi addu'a ga Allah na sama.5Sai na amsa wa sarki" Idan ya gamshi sarki, in kuma na sami tagomashi a idon sarki, sai ka aike ni Yahudiya, garin maƙabartar iyayena, don in sake gina shi."6Sai sarki ya amsa mani (sarauniya kuma tana zaune a gefen sarki), "Har zuwa yaushe za ka ɗauka, kuma yaushe za ka dawo?" Bayan na faɗawa sarki lokacin da zan dawo sai ya yi farincikin aike na.
7Sai na ce da sarki "Idan ya gamshi sarki, ina roƙo a ba ni wasiƙu domin gwamnonin lardin da ke gefen rafi don su bani damar wucewa ta yankunansu a kan hanyata ta zuwa Yahuda.8Kuma ina roƙo a bani wasiƙa domin in ba Asaf mai kula da mashigin dajin sarki don ya ba ni katakan da zan yi madogarai na mashigin kusa da haikalin, da kuma ganuwar birnin, da kuma ɗakin da zan zauna." To da ya ke hannun Allah na tare da ni, sai sarki ya yarda da buƙatuna.
9Sai na zo wurin gwamnoni a cikin Lardi Gaba da Kogin na basu wasiƙun sarki. Sarki kuma ya haɗa ni tare da waɗansu jarumawa na sojojin dawakai.10Lokacin da Samballat Bahorine da kuma Tobiya Ba'amone bayi suka ji wannan, sai suka da mu sosai cewa wani ya zo don ya taimaki mutanen Isra'ila.
11Sai na zo Yerusalem na zauna a can har kwana uku.12Sai na tashi da dare ni da mutane kima da ke tare da ni. Ban faɗa wa kowa abin da Allahna ya sa a zuciyata in yi domin Yerusalem ba. Ba dabba tare da ni, in ban da wacce na ke hawa ba.
13Da duhu sai na bi ta Ƙofar Kwari, kusa da Rijiyar Dila zuwa Ƙofar Kashin Shanu, na dudduba ganuwar Yerusalem, an rushe ta kuma a buɗe take, aka kuma ƙone ƙofofinta na katakai da wuta.14Daga nan sai na je ƙofar ƙorama da kuma Madatsin ruwan Sarki. Wurin yana da matsi sosai ga dabbar da nake a kai har da za ta iya wucewa ta ciki.
15To sai na tafi da duhu ta kwari na dudduba ganuwar, sai na dawo na shiga Ƙofar Kwari, ta haka na dawo.16Shugabanni basu san inda na je da kuma abin da na yi ba, kuma ban sanar da Yahudawa ba tukuna, ban kuma faɗa wa firistoci ba, hakanan ma manyan mutanen garin, da kuma sauran mutanen da suka yi aikin.
17Sai na ce da su, "Kun ga masifar da muke ciki, yadda Yerusalem ta zama kufai kuma an ƙone ƙofofinta da wuta. Ku zo mu sake gina ganuwar Yerusalem, don kada mu ƙara zama abin wulaƙanci."18Na faɗa masu cewa hannun Allah na tare da mu da kuma maganar da sarki ya faɗa mani. Sai suka ce "Mu tashi mu kama ginin." Sai suka ƙarfafa hannuwansu don wannan aiki nagari.
19Amma lakacin da Samballat Bahorine, da Tobiya bawan nan Ba'amone, da Geshem Balarabe suka ji labarin aikin, sai suka yi mani ba'a da reni, suka ce, "Me ku ke yi? Kuna yiwa sarki tayarwa ne?"20Sai na amsa masu na ce, "Allah na sama zai ba mu nasara. Mu bayinsa ne kuma za mu tashi muyi ginin. Amma ku baku da gãdo, ko iko, kuma baku da tarihin da zaku ce naku ne a Yerusalem".

3

1Eliyashib ya tashi tare da 'yan'uwansa firistoci, sai suka gina Ƙofar Tumaki. Suka ke‌ɓe ta suka sa ƙofofinta a inda suke. Suka keɓe ta har zuwa Hasumiyar Ɗari da kuma Hasumiyar Hananel.2A gaba da shi sai mutanen Yeriko suka yi aiki, a gaba da su kuma Zakkur ɗan Imri ne ya yi aiki.

3'Ya'yan Hassina'a ne suka gina Ƙofar Kifi. Suka sa mata madogarai, da ƙyamarenta, da sakatunta, da mãkarenta.4Meremot ne ya gyara sashi na gaba. Shi ɗan Yuriya ne ɗan Hakkoz. Gaba da su sai Meshullam ya gyara. Shi ɗan Berekiya ne ɗan Meshezabel. Gaba da su sai Zadok ya gyara. Shi ɗan Ba'ana ne.5Gaba da su sai Tikoyitawa suka gyara, amma shugabanninsu suka ƙi yin aikin da masu duba aikinsu suka umarce su.
6Yohaida ɗan Fasiya da Meshullam ɗan Besodeiya ne suka gyara Tsohuwar Ƙofa. Suka sa mata madogarai, da ƙyamarenta, da sakatunta, da mãkarenta.7Gaba da su sai Melatiya mutumin Gibiyon da Yadon mutumin Meronot, su mutanen Gibiyon da Mizfa ne, suka yi gyare-gyaren inda gwamnan Lardin Gaba da Kogi ke zama.
8Gaba da shi sai Uziyel ɗan Harhahiya, ɗaya daga cikin maƙeran zinariya, ya yi gyara, Gaba da shi kuma sai Hananiya mai yin turare. Su ne suka sake gina Yerusalem da Babban Garun.9Gaba da su kuma sai Refayiya ɗan Hur ya gyara. Shi ke mulkin rabin gundumar Yerusalem.10Gaba da su sai Yedayiya ɗan Harumaf ya gyara kusa da gidansa. Gaba da shi sai Huttush ɗan Hashabniya ya gyara.
11Malkiya ɗan Harim da Hasshub ɗan Fahat- Mowab suka gyara ɗaya sashin tare da Hasumiyar Matoya.12Gaba da su sai Shallum ɗan Hallohesh, shugaban sashin gundumar Yerusalem, ya yi gyara tare da 'ya'yansa mata.
13Hannun da mazaunan Zanowa suka gyara Ƙofar Kwari. Suka sake gina ta suka sa ƙyamarenta, da sakatunta, da mãkarenta. Suka yi gyara har zuwa kamu dubu tun daga Ƙofar Kashin Shanu.
14Malkiya ɗan Rekab, shugaban gundumar Bet Hakkerem, ya gyara Ƙofar Kashin Shanu. Ya gina ta ya sa ƙyamarenta, da sakatunta, da mãkarenta.15Shallun ɗan Kol-Hozeh, shugaban gundumar Mizfa, ya sake gina Ƙofar Ruwa. Ya gina ta ya sa murfi akan ta da ƙyamarenta, da sakatunta, da mãkarenta. Hakanan ya sake gina Shirayin Siloyam a lambun sarki, tun daga ƙasa har ya zuwa birnin Dauda.
16Nehemiya ɗan Azbuk, shugaban rabin gundumar Bet Zur, ya yi gyara har zuwa wurin kabarin Dauda, zuwa madatsar ruwan da mutum ya yi, har ya kai gidan manyan mutane.17Bayansa sai Lebiyawa suka yi gyara, tare da Rehum ɗan Bani, gaba da shi kuma sai Hashabiya, shugaban rabin gundumar Keilah don gundumarsa.
18Bayansa sai jama'ar ƙasarsu suka yi gyara, suka haɗa da Binuyi ɗan Henadad, shugaban rabin gundumar Keilah.19Gaba da shi sai, Ezar ɗan Yeshuwa, shugaban Mizfa, ya gyara ɗaya sashin da ke fuskantar ƙurya har kwanar garun.
20Bayansa sai Baruk ɗan Zabbai ya ba da kansa domin gyaran ɗaya gefen, tun daga kwanar garun har ya zuwa ƙofar gidan Eliyashib babban firist.21Bayansa sai Meremot ɗan Yuriya ɗan Hakkoz ya gyara ɗaya gefen ƙofar gidan Eliyashib har zuwa ƙarshen gidan Eliyashib.
22Gaba da shi sai firistoci, da sauran mutane daga yankin Yerusalem suka yi gyara.23Gaba da su Benyamin da Hasshub suka gyara gefen gidajensu. Gaba da su Azariya ɗan Ma'asiya ɗan Hananiya ya gyara kusa da gidansa.24Gaba da shi Binuyi ɗan Henadad ya gyara ɗaya gefen daga gidan Azariya zuwa kwanar garun.
25Falal ɗan Uzai ya yi gyaran wajen kwanar bango, da kuma hasumayar da ta kai har dogon gidan sarki a fãdar tsaro. Gaba da shi sai Fedaiya ɗan Farosh ya yi gyara.26Barorin da ke zama a Ofel suka yi gyara har kusa da Ƙofar Ruwa a wajen gabas da kuma bangon da ya haɗe garin.27Daga shi sai Tekoyawa suka yi gyaran ɗaya gefen da ke kusa da babbar hasumaya har zuwa garun Ofel.
28Sai firistoci suka gyara sama da Ƙofar Doki, kowanne kusa da gidansa.29Bayansu sai Zadok ɗan Immar ya gyara wajen sashen gidansa. Daga bayansa sai Shemaiya ɗan Shekaniya mai tsaron ƙofar gabas ya yi gyara.30Bayansa Hananiya ɗan Shelemiya da Hanun ɗan Zalaf na shida, ya gyara ɗaya ɓangaren. Bayansa sai Meshullam ɗan Berekiya ya gyara kusa da ɗakin da ya ke zama.
31Bayansa sai Malkiya, ɗaya daga cikin maƙeran azurfa, ya yi gyara har zuwa gidan masu hidima a haikali da kuma na fataken dake haɗe da ƙofa da kuma ɗakin fira na kan kwana32Maƙeran zinariya da kuma fatake suka gyara sama da ɗakin fira da ke kwanar Ƙofar Tumaki.

4

1Da Sanballat ya ji muna yin ginin ganuwar, sai abin ya dame shi, ya fusata sosai, ya yi wa Yahudawa ba'a.2A gaban 'yan'uwansa da sojojin Samariya, sai ya ce, mene ne waɗannan kumaman Yahudawan ke yi? Ko zasu iya dawo da birni don kansu? Ko zasu miƙa hadayu? Ko zasu iya gama aikin a rana ɗaya? Ko zasu iya samun duwatsu daga tarin matattun duwatsu da aka ƙone?3Tobiya Ba'amone na tare da shi, sai ya ce, "Ai ganuwar da suke ginawa dila ma kawai in ya bi ta kan abin da suke ginawa zai rushe ganuwarsu ta dutse!"

4Ya Allahnmu, ka ji yadda aka rena mu. Ka mayar masu da reninsu a kansu, ka sa a kwashe su suzama ganimar yaƙi zuwa ƙasar da zasu yi zaman jarun.5Kada ka rufe laifofinsu, kada ka shafe zunubansu daga fuskarka, don sun sa maginan sun yi fushi,6To sai muka gina katangar kuma katangar ta haɗu har ta kai rabin tsawonta, don jama'ar na da marmarin aiki.
7Amma bayan Sanballat, da Tobiya, da Larabawa, da Amoniyawa, da kuma Ashdodiyawa suka ji yadda ake yin gyaran katangar Yerusalem da kuma yadda aka gyaggyara wuraren da suka lalace, sai matsanancin fushi ya kama su.8Sai duk suka haɗa baki, suka fito don su yaƙi Yerusalem, da kuma kawo rikici a cikinta.9Amma muka yi addu'a ga Allahnmu kuma muka sa masu tsaronsu dare da rana, saboda wannan maƙarƙashiyar tasu.
10Daga nan sai mutanen Yahuda suka ce, "Ƙarfin ma'aikatan yana kasawa. Akwai kayayyaki da yawa da za a kwashe, kuma ba zamu iya ci gaba da ginin ganuwar ba".11Maƙiyanmu suka ce, "Ba za su gan mu ko su san lokacin da zamu auko masu mu kashe su ba, mu tsayar da aikin."
12A lokacin, Yahudawan da ke zama kusa da su ne suka zo ta ko'ina suka yi magana da mu sau goma, suka gargaɗe mu akan maƙarƙashiyar da suke shirya mana.13Sai na sa mutane a gangaren ganuwar a wuraren da ke da hatsari nasa kowanne iyali da takobinsu, mãshi, da kibiya.14Daga nan sai na miƙe na duba, sai na ce da manyan mutane da shugabanni, da sauran mutanen, "Kada ku ji tsoronsu. Ku tuna da Ubangiji, wanda ya ke da girma da kuma ban razana. Ku yi yaƙi domin iyalinku da 'ya'yanku maza da mata da matayenku da kuma gidajenku."
15Sai ya kasance bayan maƙiyanmu sun ji mun san shirye-shiryensu, Allah kuma ya rikirkita shirye-shiryensu, sai kowa ya koma ya kama aikin garun, kowa ga nasa aikin16Tun daga rabin barorina suka koma aikin katanngar, rabinsu kuma suka riƙe mãsu da kwalkwali da kwari, suka kuma sa sauran kayan yaƙi, shugabanni kuma na bayan mutanen Yahuda.
17Mutanen dai dake aikin ginin katangar da kuma ɗauko kaya, suke kuma tsaron in da suke. Sai kowannen su ya kama aiki da hannu ɗaya, ɗaya hannun kuma yana riƙe da makami.18Kowanne mai gini kuma yana rataye da takobinsa a kwiɓi, yadda suka yi aikin kenan, mai busa ƙaho kuma yana gefena.
19Sai na ce da manyan mutane da shugabannin, "Aikin babba ne kuma yanzu ya yi fãɗi, kuma mun rabu a kan garun, mun kuma yi wa juna nisa20To dole ne ku ruga inda kuka ji ƙarar ƙaho sai ku tattaru a can. Allahnmu zai yi yaƙi a madadinmu."
21Da haka muka yi aiki. Rabinsu na riƙe da mãshi tun daga safe har fitowar taurari.22Hakannan sai na ce da mutanen a wancan lokacin, "Sai kowanne mutum da baransa su kwana a tsakiyar Yerusalem, don su zama masu gadi, da dare da kuma ma'aikata da rana."23To ko ni ko 'yan'uwana, ko bayina, ko masu gadi dake tare da mu ba wanda ya canza tufafin da yasa, kuma kowannen mu ya ɗauki makaminsa, ko dama ya tafi ɗebo ruwa ne.

5

1Daga nan sai mazaje da matansu suka yi babban kuka kan 'yan'uwansu Yahuduwa.2akwai waɗanda suka ce "Mu da 'ya'yanmu maza da mata muna da yawa. To sai mu sami hatsin da za mu ci mu rayu."3Akwai waɗanda suka ce, muna jinginar da filayenmu da kuringar inabinmu, da gidajenmu don mu sami abinci a lokacin yunwa."

4Hakannan waɗansu suka ce. '"Mun ranci kuɗi don mu biya harajin sarki saboda gonakin inabinmu.5Yanzu kuma jikkunanmu da jininmu dai-dai ya ke da na 'yan'uwanmu, 'ya'yanmu kuma dai-dai da nasu 'ya'yan. An tilasta mana mu sayar da 'ya'yanmu su zama bayi. Tuni ma aka bautar da 'ya'yanmu mata. Amma mu ba mu da iko mu yi komai sabada gonakinmu na inabi suna hannun waɗansu mutane"
6Bayan na ji wannan kuka nasu da waɗannan maganganu sai na fusata sosai7Sai na yi tunani na kuma ba manyan mutane da shugabanni laifi. Na ce da su, "Kowa na neman riba a kan ɗan'uwansa." Sai na jagoranci babban taron gãba da su,8sai na faɗa masu cewa, "Mun sha fama kafin mu fito daga ƙangin bauta musamman 'yan'uwanmu Yahudawa da aka sayar a cikin al'ummai, amma sai ga shi kuna sake sayar da 'yan'uwanmu don a sake sayar da su a gare mu kuma!" Sai suka yi shiru ba wanda ya ce uffan.
9Hakanan na ce da su abin da kuke yi ba shi da kyau. A she ba za ku yi tafiya cikin tsoron Allahnmu ba, don kada mu zama abin ba'a ga al'umman da ke gãba da mu ba?10Ni da 'yan'uwana da bayina ne ke basu rancen kuɗi da hatsi. Amma dole ne mu dena sa ruwa a kan wannan bashin.11Sai ku mayar masu da filayensu, da gonakin inabinsu. Da na zaitun ɗinsu, da gidajensu da kuma ƙiyasin kuɗi da na hatsi, da sabon ruwan inabi, da kuma man da kuka karɓa daga gare su."
12Daga nan sai suka ce. "Za mu mayar da abin da muka karɓa daga wurinsu, kuma ba za mu karɓi komai daga wurinsu ba. Za mu yi kamar yadda ka faɗi. 'Daga nan sai na kira firistoci, na sa su rantse cewa zasu yi kamar yadda suka alƙawarta.13Sai na kakkaɓe tufafina na ce, "Ubangiji ya kakkaɓe dukiya da gidan duk wanda bai cika alƙawaransa ba. Da ma a kakkaɓe shi ya zama fanko sai taron suka amsa, "Amin," sai suka yabi Yahweh jama'ar kuma suka aikatata kamar yadda suka yi alƙawari.
14To, tun daga lokacin da aka naɗa ni na zama gwamnan a ƙasar Yahuda, daga shekara ta ashirin har ya zuwa shekara ta talatin da biyu ta sarautar sarki Atazazas, ko kuma in ce shekaru sha biyu ba mu taɓa cin abincin da ake ba gwamna ba.15Amma su tsofaffin gwamnoni da suka gabace ni suka ɗora wa jama'ar ɗawainiya mai nauyi, suka kuma karɓi awo, da zinariya da kuma abincin yau da kullum, da ruwan inabi. Har ma bayinsu suka dinga ƙuntatawa mutane. Amma ni ban yi haka ba, saboda tsoron Allah.
16Na kuma ci gaba da aikin ganuwar, ba mu kuma sayi ƙasa ba, duk barorina suka taru a can don wannan aiki.17A kan teburi kuma inda Yahudawa da shugabaninsu, su 150 suke, in ban da sauran waɗanda suka zo tare da mu daga al'umman dake kewaye da mu.
18Kuma kowacce rana akwai sã da aka shirya, zaɓaɓɓun tumaki guda shida, da tsuntsaye, kuma bayan kwana goma a kan kawo kowanne irin ruwan inabi, kuma duk da haka ban taɓa karɓar kuɗin abincin gwamna ba, don buƙatu sun yi wa mutane yawa.19Ka tuna da ni ya Allahna, saboda duk abin da na yi domin mutanen nan.

6

1To, bayan Sanballat da Tobiya da Geshem Balarabe da sauran maƙiyanmu suka ji labarin na sake gina ganuwar, ba kuma inda ya ragu a buɗe, duk da ya ke ban sa ƙyamare a ƙofofin ba,2sai Sanballat da Geshem suka aiko mani da saƙo cewa, "Ka zo mu haɗu a wani wuri a filin Ono." Amma so suke su cutar da ni.

3Na aika masu da 'yan'saƙo, cewa, "Ina yin babban aiki, kuma ba zan sauko ƙasa ba. Donme aiki zai tsaya a lokacin da na bar shi na gangaro wurinku?"4Sai suka sake aiko mani da dai irin wannan saƙon har sau huɗu kuma na dinga ba su amsa da irin amsar da na saba basu a kullum.
5Sanballat ya aiko bawansa gare ni da dai irin wannan saƙon a karo na biyar, da rubutu a buɗe a hannunsa.6A cikin sa aka rubuta cewa, "An ba da rahoto cikin al'ummai hakannan Geshem shi ma ya faɗa cewa, kai da Yahudawa kuna so kuyi tayarwa, don wannan ya sa kuke sake gina ganuwar. Daga cikin abin da rahoton ya ce har ma ka kusa zama sarkinsu.
7Kuma ka zaɓi annabawa su yi wannan shela game da kai a Yerusalem, cewa, 'Akwai sarki a Yahuda!' Kuma ka tabbata sarki zai ji waɗannan saƙonnin. Don haka ka zo muyi magana da juna."
8Sai na aika da saƙo gare shi cewa, "Ba wani abu kamar irin abin da ka ce ya faru, amma ka ƙago su ne daga cikin zuciyarka."9Don dukkansu sun so su tsoratar da mu, suna tunanin, "Za su sa hannunsu su tsai da aikin, don kada a kammala shi." Amma ya Allah ka ƙarfafa hannuwana.
10Na je gidan Shemaiya ɗan Delaiya ɗan Mehetabel, wanda a gidansa aka ƙulla maƙarƙashiyar. Ya ce, "Sai mu je gidan Allah tare a cikin haikali, sai mu kulle ƙofofin haikalin don suna zuwa don su kashe ka. Da dare suna son su kashe ka."11Na ba su amsa cewa, "Ko namiji kamar ni zai iya guduwa? Ko namiji kamar ni zai iya zuwa haikali don ya tsirar da ransa? Ba za ni ciki ba."
12Na gane cewa ba Allah ne ya aiko shi ba, amma ya yi anabci ne gãba da ni. Tobiya da Sanballat ne suka yi hayar sa.13Sun yi hayar sa don ya tsoratar da ni, don in yi abin da ya ce in yi zunubi, don su bani laifi har su wulaƙanta ni.14Ya Allahna ka tuna da Tobiya da Sanballat, da duk abin da suka yi. Hakannan ka tuna da annabiya Nowadiya da sauran annabawan da suka so su sa in tsorata.
15Da haka aka kammala ginin garun a ranar ashirin da biyar ga watan Elul, bayan kwana hamsin da biyu.16Bayan duk maƙiyanmu sun ji labarinsa, sai dukkan al'umman da ke kewaye da mu suka ji tsoro sosai duk fuskarsu ta yanƙwane. Don sun san an kammala aikin ne ta wurin taimakon Allahnmu.
17A wannan lokaci sai masu daraja na Yahuda suka aika da wasiƙu masu yawa ga Tobiya, wasiƙun Tobiya kuma suka zo masu.18Don akwai waɗanda ke yi masa alƙawari, don shi surukin Shekaniya ne, ɗan Ara. Ɗansa Yehohanan ya auri 'yar Meshullam ɗan Berekiya ta zama matarsa.19Sun faɗa mani labarin ayyukansa masu kyau nima kuma na bashi nawa rahoton. Tobiya ya aika mani da wasiƙu don ya firgita ni.

7

1Bayan an gama ganuwar na kuma sa ƙofofin a wurarensu, na kuma zaɓi masu tsaron ƙofofin da mawaƙa da Lebiyawa,2na ba ɗan'uwana Hanani iko kan Yerusalem, tare da Hananiya muka kula da masarautar, don shi amintacce ne, kuma mai tsoron Allah fiye da masu yawa daga cikinsu.

3Na ce da su, "Ka da ku buɗe ƙofofin Yerusalem har sai rana ta yi zafi. Lokacin da masu tsaron ƙofofin ke tsaro, zaku kulle ƙofofin kusa mãkaransu. Ku zaɓi masu gadi daga cikin mazaunan Yerusalem, waɗansu a bayan gidajensu, waɗansu kuma su tsaya inda aka sa su gadin."4Yanzu birnin yana da faɗi da kuma girma, amma kuma waɗanda ke ciki basu da yawa, kuma ba'a gama sake gina gidaje ba tukuna.
5Ya Allahna ka ba ni iko in tattara mutane masu girma da shugabanni da dukkan jama'a in sa su bisa ga iyalansu. Sai na samo littafin asalin waɗanda suka dawo daga farko sai na samo wannan rubutun a cikinsa.
6Waɗannan sune mutanen lardin da suka fito daga bautar talala waɗanda sarki Nebukadnezza sarkin Babila ya kwasa zuwa bauta. Sun dawo zuwa Yerusalem da Yahuda, zuwa birninsa.7Sun zo tare da Zerubbabel, da Yeshuwa, da Nehemiya, da Azariya, da Ra'amiya, da Nahamani, da Modakai, da Bilshan, da Misferet, da Bigbai, da Nehum, da Ba'ana. Yawan mazajen mutanen Isra'ila ya haɗa da waɗannan.
8Zuriyar Farosh, 2,172.9Zuriyar Shefatiya, 372.10Zuriyar Ara, 652.
11Zuriyar Fahat-Mowab, zuwa zuriyar Yeshuwa da Yowab, 2,818.12Zuriyar Elam, 1,254.13Zuriyar Zattu, 845.14Zuriyar Zakkai, 760.
15Zuriyar Binuyi, 648.16Zuriyar Bebai, 628.17Zuriyar Azgad, 2,322.18Zuriyar Adonikam, 667.
19Zuriyar Bigbai, 2,067.20Zuriyar Adin, 655.21Zuriyar Ater na Hezekiya, 98.22Zuriyar Hashum, 328.
23Zuriyar Bezai, 324.24Zuriyar Harif, 112.25Zuriyar Gibiyon, 95.26Mutane daga Betlehem da Netofa, 188.
27Mazaje daga Anatot, 128.28Mutane daga Bet Azmabet, 42.29Mutanen daga Kiriyat Yeriyim, da Kefira, da Birot, 743.30Mutanen daga Rama da Geba, 621.
31Mutanen Mikmas,122.32Mutanen Betal da Ai, 123.33Mutanen Nebo, 52.34Mutanen wancan Elam, 1,254.
35Mutanen Harim, 320.36Mutanen Yeriko, 345.37Mutanen Lod, Hadid, da Ono, 721.38Mutanen Sena'a, 3,930.
39Sai firistoci: Zuriyar Yedayya (na gidan Yeshuwa), 973.40Zuriyar Immer, 1,052.41Zuriyar Fashur, 1,247.42Zuriyar Harim, 1,017.
43Sai Lebiyawa: Zuriyar Yeshuwa, na Kadmiyel, na Binuyi, da Hodiba, 74.44Mawaƙa: Zuriyar Asaf, 148.45Masu tsaron ƙofa na zuriyar Shallum, da zuriyar Ater, da zuriyar Talmon, da zuriyar Akkub, da zuriyar Hatita, da kuma zuriyar Shobai, 138.
46Masu hidimar haikali: Zuriyar Ziha, da zuriyar Hasufa, da zuriyar Tabbawot,47da zuriyar Keros, da zuriyar Siya, da zuriyar Fadon,48da zuriyar Lebana, da zuriyar Hagaba, da zuriyar Shalmai,49da zuriyar Hanan, da zuriyar Giddel, da zuriyar Gahar.
50Da zuriyar Riyayya, da zuriyar Rezin, da zuriyar Nekoda,51da zuriyar Gazzam, da zuriyar Uzza, da zuriyar Faseya,52da zuriyar Besai, da zuriyar Mewunim, da zuriyar Nefushesim.
53Da zuriyar Bakbuk, da zuriyar Hakufa, da zuriyar Harhur,54da zuriyar Bazlut, da zuriyar Mehida, da zuriyar Harsha,55da zuriyar Barkos, da zuriyar Sisera, da zuriyar Timah,56da zuriyar Neziya, da zuriyar Hatifa.
57Da zuriyar bayin Suleman: da zuriyar Sotai, da zuriyar Soferet, da zuriyar Ferida,58da zuriyar Ya'ala, da zuriyar Darkon, da zuriyar Giddel,59da zuriyar Shefatiya, da zuriyar Hattil, da zuriyar Fokeret Hazzebayim, da zuriyar Amon.60Dukkan masu hidimar haikali, da zuriyar bayin Suleman, 392.
61Waɗannan su ne mutanen da suka tafi daga Tel Mela, Telkasha, Kerub, Addon, da Imma. Amma ba zasu iya ba da shaida cewa iyayensu zuriyar Isra'ila ba ne:62da zuriyar Delaiya, da zuriyar Tobiya, da zuriyar Nekoda, 642.63Waɗanda ke daga firistoci: zuriyar Habaiya, da Hakkoz, da Barzilai (wanda ya auro matarsa daga mutanen Barzillai na Giliyad ake kuma kiran su da sunansu).
64Waɗannan sun binciko rubutaccen tarihinsu a cikin waɗanda aka karɓo tarihinsu bisa ga asalinsu, amma ba'a samu ba, don haka aka cire su daga aikin firist don ba su da tsarki.65Daga nan sai gwamna ya ce da su ba za a barsu su ci rabon firistoci ba na abinci daga cikin abincin hadaya har sai an sami firist tare da Urim da Tummim.
66Dukkan taron baki ɗaya shi ne 42,360,67ban da barorinsu maza da mata, waɗanda daga cikinsu aka sami 7,337. Suna da mawaƙa maza da mata da suka kai 245.
68Dawakansu guda 736, bijimansu 245,69raƙumansu, 435, da jakunansu, 6,720.
70Waɗansu daga cikin shugabannin iyaye suka bada kyautai domin aikin. Gwamna ya bada awo dubu na zinariya, da bangaji 50, da suturar firistoci guda 530.71Waɗansu daga cikin shugabannin iyalai suka bayar da awo dubu ashirin na zinariya da awon azurfa 2,200.72Sauran jama'a suka bayar da awo dubu ashirin na zinariya, da kuma awo dubu biyu na azurfa, da suturar firistoci guda sittin da bakwai,
73To sai firistoci da Lebiyawa, da masu tsaron ƙofa da mawaƙa, da waɗansu mutane da masu hidima a haikali da dukkan Isra'ila dake cikin birane. A wata na bakwai sai mutanen Isra'ila suka zauna a biranensu."

8

1Sai dukkan mutane suka taru a matsayin mutum ɗaya a fili a gaban Ƙofar Ruwa. Sai suka tambayi Ezra marubuci ya kawo Littafin Shari'a na Musa, wanda Yahweh ya umarci Isra'ila.2A rana ta fari a wata na bakwai, Ezra firist ya kawo shari'a a gaban taron mutanen maza da mata, da duk waɗanda zasu iya ji su kuma fahimta.3Sai ya fuskanci filin Ƙofar Ɍuwa, sai ya yi karatu daga cikinsa tun daga asubahi har zuwa tsakar rana, a gaban dukkan maza da mata waɗanda zasu ji su kuma fahimta, kuma dukkan mutanen suka saurari karatun littafin shari'a a hankali.

4Sai Ezra marubuci ya tsaya a kan dogon dakali na katako wanda mutane suka shirya saboda wannan dalilin. Waɗanda ke tsaye a gefansa su ne Mattitiya, Shema, Ananiya, Yuriya, Hilkiya, da Ma'aseiya, a gefen damarsa; da Fedaiya, Mishyel, Malkiya, Hashun, Hashbaddana, Zakariya, da Meshullum suna gefensa na hagu.5Sai Ezra ya buɗe littafin a gaban dukkan mutane, don yana tsaye ne a saman mutanen, sa'ad da ya buɗe littafin sai dukkan mutane suka miƙe tsaye.
6Sai Ezra ya yi godiya ga Yahweh, Allah mai girma, sai dukkan mutane suka ɗaga hannuwansu sama suka amsa, "Amin! Amin!" Sai suka sunkuyar da kansu suka yi sujada ga Yahweh da fuskokinsu a ƙasa.7Hakannan Yeshuwa, Bani, Sherebiya, Yamin, Akkub, Shabbetai, Hodiya, Ma'aseiya, Kelita, Azariya, Yozabad, Hanan, da Felaiya - Lebiyawa - suka taimaki mutane su fahimci shari'ar, a sa'ad da mutane suke a wurarensu.8Sun karanta daga cikin littafin, Shari'ar Allah, suka faiyace ta a fili suka kuma fassarata suka bada ma'anarta ga mutane don mutane su fahimci karatun.
9Nehemiya gwamna, da Ezra firist da marubuci, da kuma Lebiyawa da ke yiwa mutane fassara suka ce da dukkan mutanen, "Wannan rana ce mai tsarki ga Yahweh Allanku. Kada ku yi baƙinciki ko kuka." Don dukkan mutanen sun yi kuka bayan da suka ji manganganun shari'a.10Sai Nehemiya ya ce da su, "Kuje ku ci kitse ku kuma sami abu mai zaƙi ku sha, ku kuma aikawa waɗanda basu da abin yin bikin, don wannan rana mai tsarki ce ga Ubangijinmu. Kada ku yi alhini, don farincikin Yahweh shi ne ƙarfinku."
11Sai Lebiyawa suka sa mutane su yi shiru, suna cewa, "Ku natsu! Don wannan rana mai tsarki ce. Kada ku yi baƙincikin."12Daga nan sai mutane suka tafi don su ci, su sha, su kuma yi zumunci, suyi biki cikin murna sosai saboda sun fahimci maganar da aka koyar da su.
13A rana ta uku sai shugabannin iyalai da iyaye daga dukkan mutane, da firistoci, da Lebiyawa, suka taru a wurin Ezra marubuci don su sami fahimta daga manganganun shari'a.14Sai suka ga wani wuri inda Yahweh ya umarta ta wurin Musa cewa 'ya'yan Israi'la su taru a cikin bukkoki a lokacin bikin watan bakwai.15Sai suyi shela a cikin dukkan biranensu, da Yerusalem, cewa, "Kuje can ƙasa mai duwatsu, ku kawo rassan zaitun da zaitun na daji, da tuwon-biri, da na dabino, da durumi da sauran itatuwa masu rassa don ku yi bukkoki, kamar yadda ya ke a rubuce."
16To sai mutanen suka fita suka samo rassan suka yi wa kansu bukkoki, dukkansu kowa da nasa rufe-rufen, da harabunsu, da kuma harabar gidan Allah, a fili a gaban Ƙofar Ruwa da kuma dandalin dake ƙofar Efiraim.17Dukkan mutanen da suka dawo daga bautar talala suka kakkafa bukkoki suka zauna a cikinsu. Don tun daga kwanakin Yoshuwa ɗan Nun har ya zuwa wannan rana mutanen Isra'ila ba su yi wannan biki ba, don haka suka yi murna sosai.
18Hakanan rana bayan rana, daga rana ta fari zuwa rana ta ƙarshe, Ezra ya karanta littafin shari'ar Allah. Su kan yi bikin a kwanaki bakwai a rana ta takwas sai ayi babban taro, don nuna biyayya ga wannan umarni.

9

1A rana ta ashirin da huɗu a wannan watan dai sai mutanen Israi'la suka taru suna kuma yin azumi, suna sanye da tufafin makoki, suka kuma baɗa toka a kawunansu.2Zuriyar Israi'la suka keɓe kansu daga dukkan bãƙi. Suka tsaya, suka furta zunubansu, da kuma ayyukan mugunta na kakaninsu.

3Suka tsaya a wurarensu, har kusan faɗuwar rana suna karanta littafin shari'ar Yahweh Allahnsu. Har kusan rabin ɗaya ranar suna ta furta zunubansu suna sunkuyawa a gaban Yahweh Allahnsu.4Sai Lebiyawa, Yeshuwa, Bani, Kadmiyel, Shebaniya, Bunni, Sherebiya, Bani, da Kenani, suka tsaya a filin suka yi kuka ga Yahweh Allahnsu.
5Sai Lebiyawa, Yeshuwa, da Kadmiyel, Bani, Hashabneyya, Sherebiya, Hodiya, Shebaniya, da Fetahiya, suka ce, "Ku miƙe tsaye ku yabi Yahweh Allahnku har abada abadin." Dama su yabi sunanka maɗaukaki, kuma ya ɗaukaka fiye da dukkan albarku da yabo.6Kai ne Yahweh. Kai kaɗai. Ka yi samaniya da sammai mafiya nisa, da dukkan rundunoninsu, da duniya da duk abin da ke cikinta, da tekuna da duk abin da ke cikinsu. Ka ba dukkan su rai, kuma dukkan rundunar sama na yi maka sujada.
7Kai ne Yahweh, Allahn da ya zaɓi Abram, ya kawo shi daga Ur ta Kaldiyawa ya bashi suna Ibrahim.8Ka gane cewa yana da aminci a gare ka, ka kuma yi masa alƙawari zaka bada ƙasar Kan'aniyawa, da Hitiyawa, da Amoriyawa, da Feriziyawa, da Yebusiyawa, da Girgashiyawa, ga zuriyarsa. Ka kiyaye alƙawarinka saboda kai adali ne.
9Ka ga ƙuncin kakanninmu a Masar ka kuma ji kukansu a bakin Tekun Iwa.10Ka bada alamu da al'ajibai gãba da Fir'auna da dukkan bayinsa da dukkan mazaunan ƙasarsa don ka san Masarawa sun yi masu mugun hali sosai. Amma ka samarwa kanka suna wanda ya ke nan har ya zuwa yau.
11Kai ne kuma ka raba teku biyu a gabansu, don su bi ta cikin tsakiyar teku a kan sandararriyar ƙasa; ka kuma kora masu runtumarsu cikin zurfafa kamar dutse a cikin ruwaye zurfafa.
12Ka bida su ta wurin ginshiƙin girgije da rana, da kuma ginshiƙin wuta da dare don ta nuna masu hanyar da za su bi.13A kan Dutsen Sinai ka sauko ƙasa ka yi magana da su daga sama ka kuma ba su ka'idojinka na adalci da kuma shari'arka ta gaskiya, da farillanka da dokokinka masu kyau.
14Ka koyar da su game da Asabar ɗinka mai tsarki, ka basu dokoki da farillai da shari'u ta wurin Musa bawanka.15Ka basu gurasa daga sama saboda yunwarsu, da kuma ruwa daga dutse saboda ƙishinsu, ka kuma ce da su ku shiga ku mallaki ƙasar da ka rantse za ka basu.
16Amma su da kakaninmu suka nuna rashin girmamawa, suka yi taurin kai, basu saurari dokokinka ba,17Suka ƙi su saurara, kuma suka ƙi tunani a kan al'ajibanka da kayi a cikinsu, amma suka yi tayarwa, saboda tayarwarsu suka zaɓi shugaba don su koma zaman bautarsu. Amma kai Allah ne wanda ya ke cike da gafara, da alheri da tausayi, mai jinkirin fushi, mai madawwamiyar ƙauna. Baka yashe su ba.
18Ko ma a lokacin da suka kafa ɗan maraƙin daga narkakken ƙarfe suka ce, 'Wannan Allahnku wanda ya fitar da ku daga ƙasar Masar,' suka kuma yi babban saɓo,19kai, cikin tausayinka, baka yashe su ba a cikin jeji. Ginshiƙin girgijen ya bi da su akan hanya bai kuma rabu da su ba da rana, hakama ginshiƙin wutar bai rabu da su ba da dare don ya haskaka masu hanyar da zasu bi.
20Ruhunka manargaci ka basu don ya gargaɗe su, Baka janye mannarka daga bakunansu ba, ka kuma basu ruwa saboda ƙishinsu.21Har shekaru arba'in ka yi masu tanadi a cikin jeji, kuma basu rasa komai ba. Suturunsu basu koɗe ba ƙafafunsu kuma ba su kumbura ba.
22Ka basu mulkoki da al'ummai ka ba kowannesu lungu-lungu na ƙasar. Sa'an nan suka mallaki ƙasar Sihon da sarkin Heshbon da kuma ƙasar Og sarkin Bashan.
23Ka sa 'ya'yansu su yawaita kamar taurarin sama, ka kuma kawo su ƙasar da ka faɗawa ubanninsu su je su mallake ta.24Sai mutanen suka je suka mallaki ƙasar ka kuma kori mazauna ƙasar a idonsu, wato Kan'aniyawa. Ka ba da su a hannuwansu, tare da sarakunansu da mutanensu na ƙasar, don Isra'ila su yi yadda suka so da su.
25Suka kame ƙayatattun birane da kuma ƙasa mai bada abinci, sun kuma mamaye gidaje cike da abubuwa kyawawa da rijiyoyin da tuni aka haƙa, da garkar inabi da ta zaitun, da itatuwa masu bada 'ya'ya sosai. Da suka ci suka ƙoshi suka yi ƙiba suka ji daɗin kansu a cikin babbar nagartarka.
26Daga nan suka yi rashin biyayya a gare ka. Suka yi watsi da dokokinka. Suka karkashe annabawanka da suka gargaɗe su su komo gare ka, sun kuma yi babban aikin saɓo.27Don haka sai ka ba da su a hannun maƙiyansu, waɗanda suka wahalashe su. A cikin wahalarsu, suka yi kuka gare ka, ka kuwa ji su daga sama, Kuma saboda babban jinƙanka ka aika masu da masu kuɓutarwa waɗanda suka kuɓutar da su daga ƙasar maƙiyansu.
28Amma bayan sun huta, sai suka ƙara yin aikin mugunta a gabanka, sai ka yashe su a hannun maƙiyansu suka mulke su. Duk da haka sa'ad da suka juyo suka yi kuka gare ka, ka ji su daga sama, da kuma a lokuta da yawa saboda yawan jinƙanka ka 'yanto su.29Ka gargaɗe su da su juyo ga dokokinka. Duk da haka suka yi husuma kuma ba su saurari umarnanka ba. Suka yi zunubi kan sharuɗan da ke bada rai ga wanda ya kiyaye su. Sun miƙa kafaɗunsu na taurin kai suka ƙi sauraro.
30Ka yi ta watsi da su da kuma yi masu gargaɗi ta wurin Ruhunka ta hannun annabawanka. Duk da haka ba su saurara ba. Don haka sai ka miƙa su ga magabtan ƙasashensu31Amma a cikin jinƙanka mai girma baka hallakar da su dukka ba, ko kuma ka yashe su, Don kai Allah ne mai yawan jinƙai da alheri.
32Yanzu saboda haka ya Allahnmu - kai mai girma ne, maɗaukaki, managarci wanda ka riƙe alƙawarinka da kuma ƙaunarka madauwamiya - kar ka bari duk wannan wahalar da ta same mu ta zama kamar 'yar ƙarama a gare ka, ga sarakunanmu, ga masu mulkinmu, da kuma firistocinmu, da annabawanmu, da iyayenmu, da dukkan mutanenka tun daga kwanakin sarakunan Asiriya har ya zuwa yau.33Kai mai adalci ne a cikin duk abin da ya same mu, don da amincinka ka bi da mu, amma muka yi aikin mugunta.34Sarakunanmu da masu mulkinmu, da firistocinmu da iyayenmu, ba mu kiyaye shari'arka ba, ko mu saurari dokokinka ko sharuɗɗan da ka gindaya mana waɗanda kuma ka gargaɗe su ba.
35Koma da a cikin mulkinsu, sa'ad da suka ji daɗin babban alherinka a gare su, a wannan babbar ƙasa mai yalwa da ka basu, ba su bauta maka ba ko kuma su juyo daga mugayen hanyoyinsu ba.
36Yanzu mu bayi ne a ƙasar da ka ba iyayenmu su ji daɗin yalwarta da dukkan abubauwa masu kyau da ke cikinta, yanzu mun zama bayi a cikinta!37Dukkan wadatar da ka ba mu tana hannun sarakunan da ka ɗora a kanmu saboda zunubanmu. Suna mulkin jikkunanmu da dabbobinmu yadda suka so. Muna cikin babban ƙunci.
38Saboda dukkan wannan, muka yi dauwamammen alƙawari a rubuce. A kan littafin da aka hatimce akwai sunayen shugabanninmu, da Lebiyawa da firistoci."

10

1A bisa takardu masu tambari akwai Nehemiya, wanda ya ke gwamna, ɗan Hakaliya da Zedekiya,2Sera'iya, Azariya, Irmiya,3Fashhur, Amariya, Malkiya,

4Hattush, Shebaniya, Malluk,5Harim, Meremot, Obadiya,6Daniyel, Ginneton, Baruk,7Meshullam, Abiya, Miyamin,8Ma'aziya, Bilgai, da kuma Shemaiya. Waɗannan su ne firistocin.
9Lebiyawan su ne: Yeshuwa ɗan Azaniya, Binuyi na iyalin Henadad, Kadmiyel,10da kuma sauran yan'uwansu Lebiyawa, Shebaniya, Hodiya, Kelita, Felaiya, Hanan,11Mika, Rehob, Hashabiya,12Zakkur, Sherebiya, Shebaniya,13Hodiya, Bani, da kuma Beninu.14Shugabannin mutanen su ne: Farosh, Fahat-Mowab, Ilam, Zattu, da Bani,
15Bunni, Azgad, Bebai,16Adoniya, Bigbai, Adin,17Atar, Hezekiya, Azzur,18Hodiya, Hashum, Bezai,19Harif, Anatot, Nebai,20Magfiyash, Meshullam, Hezir,21Meshezabel, Zadok, da Yadduwa,
22Felatiya, Hanan, Anaya,23Hoshiya, Hananiya, Hasshub,24Hallohesh, Filha, Shobek,25Rehum, Hashabna, Ma'aseiya26Ahiya, Hanan, Anan,27Malluk, Harim, da kuma Ba'ana.
28Game da sauran mutanen kuwa, waɗanda suke firistoci, Lebiyawa, matsaran ƙofofi, mawaƙa, da masu hidimar haikali, da kuma dukkan waɗanda suka keɓe kansu daga mutanen ƙasashen maƙwabta suka kuma miƙa kansu ga shari'ar Allah, har da matayensu, da 'ya'yansu maza da mata, dukkan waɗanda suke da ilimi da kuma fahimta,29suka haɗu tare da 'yan'uwansu, da sarakunansu, kuma suka ɗaure kansu da la'ana da kuma alƙawarin yin tafiya bisa shari'un Allah, wadda Musa bawan Allah ya bayar, su kuma kula su kuma yi biyayya da dukkan dokokin Yahweh Ubangijinmu da kuma umarnai da kuma farillunsa.
30Mun yi alƙawari ba zamu ba da 'ya'yanmu mata aure ga mazaunan ƙasar ba ko mu auro 'yan matansu ga 'ya'yanmu maza.31Mun kuma yi alƙawari idan mazaunan ƙasar suka kawo kayayyaki ko wani hatsi domin sayarwa a ranar Asabarci, ba zamu saya daga gare su ba a ranar Asabaci ko wata rana mai tsarki. Kowacce shekara ta bakwai zamu bar filayenmu su huta, kuma zamu ṣoke dukkan basusuwan da aka yi.
32Mun yi na'am da dokokin bayar da ɗaya cikin uku na awo a shekara domin hidimar gidan Allahnmu,33domin tanadin gurasar wuri-mai tsarki, da kuma hatsin baiko na kullum, baye-baye na ƙonawa a ranakun Asabaci, bukukuwan sabon wata da kuma shiryayyar liyafa, da kuma baye-baye masu tsarki, da kuma baye-baye na zunubi domin yi wa Isra'ila kaffara, haka kuma domin dukkan ayyukan gidan Allahnmu.
34Da firistoci da Lebiyawa da mutane suka jefa ƙuri'u domin itacen yin baiko. Ƙuri'un zasu zaɓi wane ne daga cikin iyalanmu zai kawo itace zuwa gidan Allahnmu a sanyayyun lokatai kowacce shekara, domin ƙonawa a bisa bagadin Yahweh Allahnmu, kamar yadda ya ke a rubuce cikin shari'a.35Mun yi alƙawari mu kawo nunar fari da aka shuka a ƙasarmu cikin gidan Yahweh, da kuma nunar fari na kowanne itace duk shekara.36Kamar yadda aka rubuta a shari'a, mun yi alƙawari mu kawo cikin gidan Allah da kuma ga firistoci masu hidima a can, ɗan fari cikin 'ya'yanmu da kuma na garkunan shanunmu da garkunan tumakinmu.
37Zamu kawo cụrinmu na fari da kuma baye-bayenmu na hatsi, da kuma 'ya'yan kowacce itaciya, da kuma sabon inabi da kuma mai zamu kawo su ga firistoci, ga rumbunan gidan Allahnmu. Zamu kawo wa Lebiyawa zakka daga ƙasarmu domin su Lebiyawa na karɓar ɗaya daga goma daga dukkan garuruwan da muke aiki.38Firist, zuriyar Haruna, dole yana tare da Lebiyawa sa'ad da suke karɓar ɗaya daga goma. Su Lebiyawa dole su kawo ɗaya daga goma ga gidan Allahnmu zuwa cikin runbunan ma'aji.
39Gama mutanen Isra'ila da kuma zuriyar Lebi zasu kawo gudumuwoyin na hatsi, da sabon inabi, da kuma mai zuwa ga runbuna inda ake ajiyar santalolin wuri mai tsarki inda firistoci masu hidima suke, da kuma matsaran ƙofa, da kuma inda mawaƙa ke zama. Ba za mu yi watsi da gidan Allahnmu ba.

11

1Shugabannin mutanen suka zauna cikin Yerusalem, sai kuma sauran mutanen suka jefa ƙuri'u domin kawo ɗaya daga cikin goma ya zauna a Yerusalem, birni mai tsarki, sai kuma sauran kashi taran a bar su a wasu garuruwan.2Sai mutanen suka albarkaci dukkan waɗanda suka yarda su zauna a Yerusalem.

3Waɗannan su ne shuagabannin lardin dake zama Yerusalem. Duk da haka, a cikin garuruwan Yahuda kowanne na zama a ƙasarsa, harma da waɗansu Isra'ilawa, firistoci, Lebiyawa, masu hidimar haikali, da zuriyar bayin Suleman.4A Yerusalem akwai mazauna waɗanda suke na zuriyar Yahuda da kuma zuriyar Benyamin. Mutanen Yahuda su ne: Atayya ɗan Uzziya ɗan Zakariya ɗan Amariya ɗan Shefatiya ɗan Mahalalel, na zuriyar Ferez.
5Akwai Ma'aseiya ɗan Baruk ɗan Kol-Hoze ɗan Hazayya ɗan Adayya ɗan Yoyarib ɗan Zakariya, ɗan Bashiloni.6Dukkan 'ya'yan Ferez da suka zauna cikin Yerusalem 468 ne. Su zama shahararrun mutane.
7Waɗannan su ne zuriyar Benyamin: Sallu ɗan Meshullam ɗan Yoyed ɗan Fedayya ɗan Kolayya ɗan Ma'aseyya ɗan Itiyel ɗan Yeshayya,8da waɗanda suke binsa, da Gabbai da Sallai, mutane 928.9Yowel ɗan Zikri shi ne mai kula da su, da kuma Yahuda ɗan Hassenuwa shi ya zama na biyu a shugabanci bisa birnin.
10Daga firistocin: Yedayya ɗan Yoyarib, Yakin,11Serayya ɗan Hilkiya ɗan Meshullam ɗan Zadok ɗan Merayot ɗan Ahitub, babban mai kula da gidan Allah,12da kuma abokan aikinsu waɗanda suka yi aikin gidan Allah, mutane 822, tare da Adayya ɗan Yeroham ɗan Felaliya ɗan Amzi ɗan Zakariya ɗan Fashhur ɗan Malkiya.
13Yan'uwansa ne shugabannin zuriya, mutane 242; da kuma Amashsai ɗan Azarel ɗan Ahzai ɗan Meshillemot ɗan Immer,14da kuma yan'uwansu, mutane 128 masu ƙarfin halin yaƙi; mai kula da su shi ne Zabdiyel ɗan Hagedolim.
15Daga Lebiyawa: Shemayya ɗan Hashub ɗan Azrikam ɗan Hashabiya ɗan Bunni,16da kuma Shabbetai da Yozabad, su da ke daga wajen shugabannin Lebiyawa kuma su ne ke da haƙin aikin waje da gidan Allah.
17Akwai Mattaniya ɗan Mika ɗan Zabdi, na zuriyar Asaf, shi ne jagora da ya fara bada godiya cikin addu'a, da kuma Bakbukiya, shi ne na biyu cikin yan'uwansa, da kuma Abda ɗan Shammuwa ɗan Galal ɗan Yedutun.18Dukkan Lebiyawa da ke cikin birni mai tsarki lissafinsu 284 ne.
19Masu kula da ƙofa: Akkub, Talmon, kuma sauran abokan hurɗarsu, da suke kula da ƙofofi, mutane 172.20Sauran Isra'ila da kuma sauran firistoci da Lebiyawa suna cikin dukkan garuruwan Yahuda. Kowannen su na zaune a wurinsa na gãdo.21Ma'aikatan haikali suna zaune cikin Ofel, da Ziha da Gishfa su ne masu kula da su.
22Babban shugaba a bisa Lebiyawan da ke a Yerusalem shi ne Uzzi ɗan Bani ɗan Hashabiya ɗan Mattaniya ɗan Mika, daga zuriyar Asaf, mawaƙa a bisa aikin cikin gidan Allah.23Suna a ƙarƙashin umarnai masu girma daga wurin sarki, kuma an bada umarnai masu tsanani ga mawaƙa yadda kowacce rana ke bukata.24Sai Fetaniya ɗan Meshezabel, daga zuriyar Zera ɗan Yahuda, ya zauna a ɓarayin sarki a game da kowanne al'amari da ya shafi mutane.
25A game da ƙauyuka da kuma filayensu, wasu mutanen Yahuda sun zauna a Kiriyat Arba da ƙauyukanta, da kuma cikin Dibon da ƙauyukanta, da kuma cikin Yekabzil da ƙauyukanta,26da cikin Yeshuwa, Molada, Bet Felet,27Hazar Shuwal, da kuma Biyasheba da ƙauyukanta.
28Wasu daga mutanen Yahuda sun zauna cikin Ziklag, Mekona da kuma ƙauyukanta,29Enrimmon, Zora, Yamut,30Zanowa, Adullam, da kuma ƙauyukanta, da cikin Lakish da filayenta, da Azeka da ƙauyukanta. Sai suka zauna daga Biyasheba zuwa Kwarin Hinnom.
31Benyamin suka zauna daga Geba, a Mikmash da Aiya, a kuma Betel da ƙauyukanta,32Anatot, Nob, Ananiya,33Ramah, Gittayim,34Hadid, Zeboyin, Neballat,35da kuma Ono kwarin maƙera.36daga cikin Lebiyawa dake zama cikin Yahuda aka sanya su kan mutanen Benyamin.

12

1Waɗannan su ne firistoci da Lebiyawa da suka fito tare da Zerubbabel ɗan Sheltiyel da kuma tare da Yeshuwa: Serayya, da Irmiya, Ezra,2Amariya, Malluk, Hattush,3Shekaniya, Rehum, da kuma Meremot.

4Akwai su Iddo, Ginneton, Abiya,5Miyamin, Mowadiya, Bilga,6Shemayya, da Yoyarib, Yedayya,7Sallu, Amok, Hilkiya, da Yedayya. Waɗannan ne shugabannin firistoci da mataimakansu a kwanakin Yeshuwa.
8Lebiyawan su ne Yeshuwa, Binuyi, Kadmiyel, Sherebiya, Yahuda, da Mattaniya, wanda shi ne shugaban waƙoƙin godiya, tare da abokan aikinsa.9Bakbukiya da Unni, su ne abokan aikinsu, suka tsaya daura da su lokacin yin sujada.
10Yeshuwa shi ne mahaifin Yowakim, Yowakim shi ne mahaifin Eliyashib, Eliyashib ne Mahaifin Yowada,11Yowada ne mahaifin Yonatan, kuma Yonatan shi ne mahaifin Yadduwa.
12A zamanin Yowakim waɗannan su ne firistoci, su ne shugabannin iyalai: Merayya ne shugaban Serayya, Hananiya ne shugaban Irmiya,13Meshullam shi ne shugaban Ezra, Yehohanan shi ne shugaban Amariya,14Yonatan ne shugaban Malluk, kuma Yosef shi ne shugaban Shebaniya.
15Adna ne shugaban Harim, Helkai shugaban Merayot,16Zakariya shi ne shugaban Iddo, Meshullam shi ne shugaban Ginneton17Zikri shi ne shugaban Abiya. ... na Miniamim. Filtai shi ne shugaban Mowadiya.18Shammuwa shi ne shugaban Bilga, Yehonatan shi ne shugaban Shemayya,19Mattenai shi ne shugaban Yoyarib, Uzzi shi ne shugaban Yedayya,20Kallai shi ne shugaban Sallai, Eba shi ne shugaban Amok,21Hashabiya shi ne shugaban Hilkiya, da Netanel shi ne shugaban Yedayya.
22A kwanakin Eliyashib, Lebiyawa Eliyashib, Yowada, Yohanan, da Yadduwa aka lisafta su a matsayin shugabannin iyalai, kuma aka lisafta firistocin a zamanin mulkin Dariyos na Fasiya.23Su zuriyar Lebi, shugabannin iyalansu aka lisafta su a cikin littafi na tarihi har zuwa kwanakin Yohanan ɗan Eliyashib.
24Su shugabannin Lebiyawan su ne Hashabiya, Sherebiya, da Yeshuwa ɗan Kadmiyel, tare da abokan tarayyarsu, suna zaune daura da su domin raira waƙoƙin yabo da kuma bada godiya, suna aikinsu cikin ka'ida, suna biyayya da umarnin Dauda, mutumin Allah.25Mattaniya, Bakbukiya, Obadiya, Meshullam, Talmon, da Akkub su ne matsaran ƙofofi masu tsaro a tsaye a ɗakunan ajiya dake gefen ƙofofin.26Sun yi hidima a cikin kwanakin Yoyakim ɗan Yeshuwa ɗan Yozadak, da kuma a kwanakin Nehemiya gwamna da kuma Ezra firist da marubuci.
27A lokacin keɓewar ganuwar Yerusalem, mutane suka nemi firistoci dukkan inda suke zama, suka kawo su Yerusalem su yi bikin keɓewar tare da farinciki, da godiya da kuma waƙoki tare da kuge, da molo, da giraya, da tsarkiyoyi.28Zumuntar mawaƙa suka tattaru tare daga garuruwa kewaye da Yerusalem daga kuma ƙauyuka na Netofatiyawa.
29Sun kuma fito daga Bet Gilgal daga kuma filin Geba da Azmabet, domin mawaƙa sun gina wa kansu ƙauyuka kewaye da Yerusalem.30Su firistoci da Lebiyawa suka tsarkake kansu, suka kuma tsarkake mutanen, da ƙofofin, da kuma ganuwar.
31Sai na sa shugabannin Yahuda suka hau kan ganuwar, na kuma shirya manyan ƙungiyoyin mawaƙa guda biyu domin su yi waƙoƙin godiya. Sashi ɗaya suka yi dama bisa ganuwar ta sashen ‌Ƙofar Kashin Shanu.
32Hoshayya da rabin shugabannin Yahuda suka tafi tare da su,33bayan su Azariya, Ezra, Meshullam,34Yahuda, Benyamin, Shemayya, da Irmiya,35da wasu 'ya'yan firistoci ɗauke da algaitu, da kuma Zekariya ɗan Yonatan ɗan Shemayya ɗan Mattaniya ɗan Mikayya ɗan Zakkur ɗan Asaf.
36Da akwai waɗansu cikin 'yan'uwan Zakariya, Shemayya, Azarel, Milalai, Gilalai, Ma'ai, Netanel, Yahuda, Hanani, suna ɗauke da kayayyakin kiɗe-kiɗen Dauda mutumin Allah. Ezra marubuci na tsaye gabansu.37Daga ‌Ƙofar Maɓulɓula suka haura kai tsaye zuwa matakalar birnin Dauda, daga matakala zuwa ganuwa a bisa fãdar Dauda, zuwa wajen Kofar Ruwa daga gabas.
38‌Ɗaya ƙungiyar mawaƙan masu bada godiya suka tafi zuwa wancan sashen. Na bi su a bisa ganuwar tare da rabin mutanen, sama da Hasumiyar Murahu, zuwa kan Ganuwa Mai Faɗi,39da bisa Kofar Ifraim, da kuma daga Tsohuwar ‌Ƙofa, da kuma daga ‌Ƙofar Kifi da kuma Hasumiyar Hananel da kuma Hasumiyar Ɗari, zuwa ga ‌Ƙofar Tumaki, sai suka tsaya a ‌Ƙofar Matsara.
40Da haka dukkan mawaƙa suka bada godiya suka ɗauki wurinsu a cikin gidan Allah, nima na ɗauki wurina tare da rabin ma'aikatan da ke tare da ni.41Sai su firistoci suka ɗauki wurin zamansu: Eliyakim, Ma'aseyya, Miniyamin, Mikayya, Elihonai, Zakariya, da kuma Hananiya, tare da ƙahonni,42da kuma Ma'aseyya, Shemayya, Eliyaza, Uzzi, Yehohanan, Malkiya, Elam, da kuma Eza, sai kuma mawaƙan suka sa aka ji su Jezrahiya kuma shi ne shugabansu.
43Suka bada manyan hadayu a wannan rana, da farinciki kuma, gama Allah ya sa suka yi farinciki da murna mai girma. Haka mataye da kuma yara suka yi murna. Da haka aka ji farincikin Yerusalem daga nesa.
44A wannan rana aka naɗa mutane su shugabanci ɗakunan ajiya domin gudumuwa, nunar fari, da zakka, domin su tara adadin da aka shirya bisa ga shari'a a cikinsu domin firistoci da kuma Lebiyawa. Kowannen su aka ba shi aikin noma filayen da ke kusa da garuruwan. Domin Yahuda sun yi farinciki da firistoci da kuma Lebiyawa waɗanda ke tsaye a gabansu.45Suka yi hidimar Allahnsu, da kuma hidimar tsarkakewa, haka kuma mawaƙa da matsaran ƙofofi suka yi, domin kiyaye umarnan Dauda da na Suleman ɗansa.
46A tun zamanin dã, cikin kwanakin Dauda da Asaf, akwai shugabannin mawaƙa, aka yi waƙokin yabo da godiya ga Allah.47A zamanin Zerubbabel da kuma zamanin Nehemiya, dukkan Isra'ilawa suka kawo rabonsu na kowacce rana ga mawaƙa da kuma matsaran ƙofofi. Suka keɓe wa Lebiyawa rabonsu na kowacce rana, su kuma Lebiyawa suka keɓe wa 'ya'yan Haruna nasu rabon.

13

1A wannan rana suka karanta Littafin Musa mutane na saurare. Aka iske a rubucce a cikinsa cewa kada wani Ba'ammone ko mutumin Mowab ya shigo cikin taron jama'ar Allah, har abada.2Dalili kuwa shi ne domin basu taryi mutanen Isra'ila da gurasa da ruwan sha ba, amma suka yiwo hayar Bala'am domin ya la'anci Isra'ila. Duk da haka, Allahnmu ya juyar da la'anar zuwa albarka.3Da dai suka ji shari'ar, sai suka ware kowanne baƙo daga Isra'ila.

4Yanzu dai kafin wannan aka sa Eliyashib firist ya zama shugaban ɗakunan ajiya na gidan Allahnmu. Yana da dangantaka da Tobiya.5Eliyashib ya shirya wa Tobiya babban ɗaki na ajiya, inda dã aka ajiye hadayar gari, da ta turare, da tasoshi, da kuma zakkar hatsi, da sabon inabi, da mai, wanda aka keɓe domin Lebiyawa, da mawaƙa, da matsaran ƙofofi, da kuma gudumuwa domin firistocin.
6Amma cikin dukkan wannan lokacin ba na cikin Yerusalem. Gama a cikin shekara ta talatin da biyu ta sarautar Atazazas sarkin Babila na tafi wurin sarki. Bayan lokaci kaɗan sai na nemi izinin tafiya daga wurin sarki7sai kuma na komo Yerusalem. Na fahimci muguntar da Eliyashib ya aikata da ya ba Tobiya ɗakin ajiya a cikin haikali na gidan Allah.
8Na fusata ƙwarai sai na watsar da kayan ɗakin Tobiya zuwa waje daga ɗakin ajiya.9Na umarta a tsabtace ɗakunan ajiyar, na sake zuba kayayyakin gidan Allah a cikinsu, wato baye-bayen hatsi, da kuma turare.
10Sai na fahimci cewa ba a ba wa Lebiyawa rabonsu ba, kuma duk sun gudu, kowannen su zuwa ga gonarsa, su Lebiyawa da mawaƙa waɗanda suka yi aikin.11Sai na yiwa shugabannin faɗa na ce, "Me ya sa aka yi watsi da gidan Allah?" Na tara su tare kowannen su a wurin aikinsa.
12Sa'annan dukkan Yahuda suka kawo zakkar hatsi, sabon inabi, da kuma mai cikin ɗakunan ajiya.13Sai naɗa ma'aji bisa gidajen ajiya su Shelemiya firist da Zadok marubuci, kuma daga wurin Lebiyawa, Fedayya. Na kusa da su shi ne Hanan ɗan Zakkur ɗan Mattaniya, gama an iske su amintattu ne. Aikinsu shi ne su rarraba ragowar kayayyakin ga abokan aikinsu.14Ka tuna da ni, Allahna, game da wannan, kuma kada ka shafe sarai ayyukan alherin da na aikata sabili da gidan Allahna da kuma hidimarsa.
15A waɗannan kwanakin na gani a Yahuda mutane na matsar inabi a ranar Asabaci suna kuma kawo tulin hatsi da ɗauro su bisa jakkai, da kuma inabi, da zaitun, da ɓaure, da kuma kowanne kayan nauyi, wanda suka kawo cikin Yerusalem a ranar Asabaci. Na yi tsayayya da su ganin cewar suna sayar da abinci a wannan rana.
16Mutanen Tiya masu zama cikin Yerusalem suka kawo kifi da dukkan kowanne kayayyaki, suka sayar a ranar Asabaci ga mutanen Yahuda da kuma cikin birnin!17Sai na fuskanci shugabannin Yahuda kai tsaye, "Wacce irin mugunta ce haka kuke yi, ku na mai da ranar Asabaci wofi?18Ba abin da iyayenku suka yi ba kenan? Ba Allahnmu ya aiko da dukkan wannan masifar a bisanmu da kuma wannan birni ba? Yanzu kuna ƙara kawo wata hasala kan Isra'ila ta wofintar da Asabaci."
19Daga nan da zarar dare ya yi a bakin ƙofofin Yerusalem kafin Asabaci, na ba da umarni a kulle ƙofofin kada kuma a buɗe su har sai bayan Asabaci. Na sanya wasu bayina a bakin ƙofofin don kada a iya shigo da kaya ciki ranar Asabaci.20'Yan kasuwa da masu sayar da kowanne irin tufafi suka taru a wajen Yerusalem sau ɗaya ko biyu.
21Amma na yi masu kashedi, "Donme ku ke taruwa a wajen ganuwa? Idan kuka ƙara yin haka, zan kore ku da hannuna!" Daga wannan lokaci ba su ƙara zuwa a ranar Asabaci ba.22Sai na dokaci Lebiyawa su tsabtace kansu, su kuma zo su tsare ƙofofin, a tsarkake ranar Asabacin. Ka tuna da ni game da wannan kuma, Allahna, ka kuma yi mani jinƙai sabili da amintaccen alƙawarinka zuwa gare ni.
23A waɗannan kwanaki na kuma ga Yahudawan da suka auro matan Ashdod, da Ammon, da kuma Mowab.24Rabin 'ya'yansu na magana da yaren Ashdod. Babu waninsu da zai iya magana da harshen Yahuda, amma sai ɗaya daga cikin harshen sauran mutanen kawai.
25Na fuskance su kai tsaye, na kuma la'anta su, na kuma bugi wasu daga cikinsu har na tsige sumar kansu. Na sa suka yi rantsuwa ga Allah, cewa, "Ba za ku bada 'ya'yanku mata ga samarinsu ba, ko ku ɗauko wa 'ya'yanku maza 'yanmatansu, ko don kanku.26Ba haka Suleman sarkin Isra'ila ya yi zunubi ta dalilin waɗannan matayen ba? A cikin al'ummai masu yawa babu sarki kamarsa, kuma Allahnsa ya ƙaunace shi, kuma Allah ya maishe shi sarki bisa dukkan Isra'ila. Duk da haka, matayensa bãƙi suka sa yayi zunubi.27‌Ƙaƙa zamu saurare ku mu aikata dukkan wannan babbar mugunta, mu kuma yi rashin aminci ga Allahnmu ta wurin auro mataye bãƙi?"
28‌Ɗaya daga cikin 'ya'yan Yowada ɗan Eliyashib babban firist surukin Sanballat Bahorone ne. Saboda haka na sa shi ya gudu daga fuskata.29Ka tuna da su, Allahna, domin sun ƙazantar da firistanci, da kuma alƙawarin firistanci da kuma Lebiyawa.
30Da haka na tsabtace su daga duk abin da da ke na bãƙunci, na kuma kafa ayyukan firistoci da na Lebiyawa, kowanne ga aikinsa.31Na yi tanadi domin baikon itace a lokatansu da na nunar fari. Ka tuna da ni, Allahna, domin alheri.

Littafin esta

1

1A kwanakin Ahasuros (wannan shi ne Ahasuros wanda yayi mulki daga Indiya har zuwa Kush, bisa larduna 127),2a kwanakin nan Sarki Ahasuros ya zauna bisa kursiyin sarautarsa a fadar Susa.

3A shekara ta uku ta sarautarsa, yayi wa dukkan sarakunansa da barorinsa biki. Mayaƙan Fasiya da Midiya da manyan sarakuna da hakimai da gamnonin larduna duk suna gabansa.4Ya nuna darajar arziƙin mulkinsa da bangirman ɗaukakar ƙasaitarsa kwanaki da yawa, har kwanaki 180.
5Da kwanakin nan suka cika, sarki yayi biki kuma na kwana bakwai. Yayi bikin ne saboda dukkan mutanen da suke a fadar Susa, manya da ƙanana. Anyi wannan a farfajiyar lambu da ke a fãdar sarki.6Anyi wa farfajiyar lambun ado da labulai farare da shunayya, aka ratayesu bisa kirtani na lallausar lilin mai launin shunayya haɗe da zobban azurfa aka ɗaure ajikin ginshiƙan duwatsu masu daraja. Akwai kujeru na zinariya, dana azurfa da suke a shirayin da aka daɓe da duwatsun ado masu daraja kamar su fofari mabil, fiyel da duwatsun dakali masu launi.
7Aka bada abin sha a moɗayen zinariya, kowacce moɗa daban take, kuma ga ruwan inabin sarakai a yalwace saboda tsabar alfarmar sarki.8An shayar ne bisa ga umarni, "Kada a tilasa wa kowa." Sarki ya ba fadawan fadarsa umarni suyi wa kowa yadda yake so.
9Har wayau, Sarauniya Bashti ta yawa mata biki a fadar Sarki Ahasuros.10A rana ta bakwai da sarki ke jin daɗi a zuciyarsa saboda ruwan inabi, ya cewa Mehuman, Bizta, Harbona, Bigta, Abagta, Zetar, da Karkas (shugabanni bakwai da ke masa hidima),11su kawo Sarauniya Bashti a gabansa da kambin sarauta a kanta. Yana so ya nuna wa mutane da fadawansa ƙyanta, gama tana da ƙyaƙƙyawan fasali.
12Amma Sarauniya Bashti taƙi zuwa bisa ga faɗar sarki sa'ad da fadawa suka je suka faɗa mata. Sai sarki ya husata ƙwarai; fushinsa yayi ƙuna a ransa.
13Sai sarki yayi shawara da waɗanda aka san su masu hikima ne, sun fahimci lokatai (domin haka sarki ya saba yi ga waɗanda suka ƙware a shari'a da hukunci).14Na kusa da shi su ne Karshina, Shetar, Admata, Tashish, Meres, Marsina, da Memukan, sarakuna bakwai na Fasiya da Midiya. Suna da 'yancin shiga gun sarki, suke da mafifitan muƙamai a mulkin.15"Bisa ga shari'a me za a yiwa Sarauniya Bashti saboda taƙi yin biyayya da umarnin Sarki Ahasuros wanda ya aika mata ta hannun shugabanni?'
16Sai Memukan yace a gaban sarki da fadawansa, "Ba ga sarki ne kaɗai Sarauniya Basti tayi laifi ba, amma ga dukkan fadawa da dukkan mutanen da ke a lardunan Sarki Ahasuros.17Gama wannan al'amari da sarauniya ta aikata zai zama sananne ga dukkan mata. Zai sasu rena mazajensu. Zasu ce, 'Sarki Ahasuros ya umarta a kawo Sarauniya Bashti a gabansa amma taƙi.18Kafin faɗuwar ranar yau manyan matan Fasiya da Midiya da suka ji al'amarin sarauniya zasu maimaita wa dukkan hakiman sarki haka. Wannan zai kawo reni da fushi mai yawa.
19Idan ya gamshi sarki bari a aika dokar sarauta daga gareshi, a kuma rubuta a shari'ar Fasiyawa da Midiyawa da bata canzawa, cewa Bashti ba zata ƙara zuwa gaban sarki ba. Bari sarki ya bada matsayin ta ga wacce ta fita.20Sa'ad da dokar sarki ta kai ko'ina a faɗin masarautarsa, dukkan mata zasu girmama mazansu, daga manyansu har zuwa ƙananansu."
21Sarki da hakimansa sun gamsu ƙwarai da wannan shawara. Sarki kuwa yayi yadda Memukan ya shawarta.22Ya aika wasiƙu zuwa dukkan lardunansa, kowanne lardi da irin rubutunsa, kowaɗanne mutane da harshensu. Ya umarta kowanne namiji ya zama shugaban gidansa. Wannan doka an bada ita a cikin harshen kowaɗanne mutane da ke cikin masarautarsa.

2

1Bayan waɗannan abubuwa, sa'ad da fushin Sarki Ahasuros ya huce, sai ya tuna da Bashti da abin da tayi. Ya kuma tuna da dokar da ya zartar akanta.2Sai samari waɗanda ke wa sarki hidima suka ce, "Bari a madadin sarki a binciko kyawawan budurwai masu tãshe."

3Bari sarki yasa shugabanni a dukkan lardunan mulkinsa, su tara dukkan kyawawan budurwai ma su tãshe a gidan mata a cikin masarauta a Susa. A sasu a ƙarƙashin shugabancin Hegai, hakimin sarki, wanda shi ne mai lura da mata, ya kuma basu kayan kwalliyarsu.4Bari yarinyar data gamshi sarki ta zama sarauniya a madadin Bashti." Wannan shawarar ta gamshi sarki, sai yayi haka.
5Akwai wani Bayahude a fadar Susa mai suna Modakai ɗan Yair ɗan Shimeya ɗan Kish ɗan Benyamin.6An ɗauko shi ne daga Yerusalem tare da 'yan bautar talala waɗanda aka kwasosu tare da Yehoiachin, sarkin Yahuda, su ne Nebukadnezza sarkin Babila ya kwashe.
7Yayi ta lura da Hadassa, wato Esta ɗiyar kawunsa, domin bata da uba ko uwa. Yarinyar tana da kyan fasali tana kuma da kyan fuska. Modakai ya ɗauketa a matsayin 'yarsa.
8Sa'ad da aka yi shelar umarni da dokar sarki, aka kawo 'yan mata da yawa a masarautar Susa. Sai aka sasu a hannun Hegai ya kula dasu. Esta ma aka kaita fadar sarki aka sata a ƙarƙashin Hegai mai lura da mata.9'Yar yarinyar ta gamshe shi, ta kuma sami tagomashi a wurinsa. Sai nan da nan ya tanada mata kayan kwalliyarta da kuma abincinta. Ya tanada mata kuyangi bakwai daga fadar sarki, ya kuma kaita da ita da kuyanginta wuri mafi kyau a gidan mata.
10Esta bata gayawa kowa su wane ne mutanenta da danginta ba, gama Modakai ya umarce ta kada ta faɗa.11Kowacce rana Modakai yana kai da kawowa a shirayin gidan da aka sa mata, domin ya san lafiyar Esta, da kuma ko me za ayi da ita.
12Da lokaci yayi da kowacce yarinya zata shiga wurin Sarki Ahasuros - bisa ga ƙa'idar da ke na mata, kowacce yarinya sai ta cika watanni goma sha biyu na kwalliyar mata, wata shida tana shafe jikinta da man mur, wata shida tana shafa turare da mai -13sa'ad da yarinya mace ta shiga wurin sarki, duk abin da ranta yaso sai a bata daga cikin gidan matayen domin ta kai fãda.
14Da yamma zata shiga ciki, da safe zata koma gidan matayen na biyu, a hannun Sha'ashigaz, shugaba na sarki wanda shi ke lura da ƙwaraƙwarai. Ba zata ƙara komawa wurin sarki ba sai in ko yaji daɗinta a ransa kamin ya sake kiranta.
15Sa'ad da lokacin Esta ('yar Abihel kawun Modakai wanda ya ɗauke ta a matsayin 'yarsa) yazo da zata shiga wurin sarki, bata roƙi komai ba sai abin Hegai bafaden sarki, wanda shi ke kula da matayen, ya bata. A yanzu Esta ta sami farin jini wurin dukkan waɗanda suka dube ta.16Aka kai Esta wurin Sarki Ahasuros a masarautar fãda a wata na goma, wanda shi ne watan Tebet a shekararsa ta bakwai da mulki.
17Sarki ya ƙaunaci Esta fiye da dukkan sauran matayen ta kuma sami karɓuwa da tagomashi daga gare shi, fiye da dukkan sauran budurwan. Sai ya ɗibiya mata kambin sarauta a kanta ya maisheta sarauniya a madadin Bashti.18Sai sarki ya yi ƙasaitaccen biki domin dukkan hakimansa da kuma barorinsa, wato, "Bikin Esta'," kuma ya tsaida biyan haraji a duk lardunansa. Ya kuma bada kyautai bisa ga falalar yalwar mulkinsa.
19Ananan sa'ad da aka tara budurwai karo na biyu, Modakai ya zauna a ƙofar sarki.20Esta ba ta rigaya ta faɗa wa kowa game da 'yan uwanta ko mutanenta ba, domin Modakai ya umarceta. Ta ci gaba da bin shawarar Modakai, kamar yadda tayi lokacin daya reneta.21A kwanakin da Modakai ke zama a ƙofar sarki, hakiman sarki guda biyu, Bigtan da Teres, masu tsaron ƙofa, suka fusata suka nema su cuci Sarki Ahasuros.
22Da aka bayyana wa Modakai al'amarin sai ya gaya wa Sarauniya Esta, Esta ta faɗa wa sarki a sunan Modakai.23Aka bincika rahoton aka tabbatar haka yake, sai aka rataye dukkansu biyun a bisa gungume. Aka rubuta wannan al'amari a Littafin Tarihi a gaban sarki.

3

1Bayan waɗannan abubuwa, Sarki Ahasuros ya ɗaukaka Haman ɗan Hamedata Ba'agage, ya fifita matsayin ikonsa bisa kan dukkan shugabanni da ke tare da shi.2Dukkan barorin sarki da ke ƙofar sarki kulluyomi sukan durƙusa su rusuna wa Haman, gama sarki ya umarta suyi haka. Amma Modakai bai durƙusa masa ba ko kuma ya rusuna masa ba.

3Sai barorin sarki da ke a kofar sarki suka cewa Modakai, "Me yasa kake rashin biyayya da dokar sarki?"4Suka yita masa magana kowacce rana, amma yaƙi ya cika burinsu. Saboda haka suka gaya wa Haman domin suga ko za a bar al'amarin game da Modakai ya zama haka, gama ya gaya musu shi Bayahude ne.
5Da Haman yaga Modakai baya durƙusa ko ya rusuna masa ba, sai Haman ya cika da hasala.6Sai ya ƙudurta ba Modakai kaɗai zai kashe ba, gama barorin sarki sun gaya masa irin mutanen Modakai. Haman yana so ya hallakar da dukkan Yahudawa, mutanen Modakai, waɗanda suke cikin dukkan masarautar Ahasuros.
7A cikin wata na fari (wanda shi ne watan Nisan), a shekara ta goma sha biyu ta mulkin Sarki Ahasuros, aka jefa Fur - wato ƙuri'a - a gaban Haman, domin a zaɓi rana da wata. Suka yita jefa ƙuri'a akai akai har sai data faɗa akan watan goma sha biyu (wato watan Ada).
8Sa'an nan Haman ya cewa Sarki Ahasuros, "Akwai waɗansu mutane a warwatse an kuma baza su a dukkan lardunan masarautarka. Shari'arsu daban take data sauran mutane, basa kuma kiyaye dokokin sarki, sabili da haka bai kyautu ba sarki ya bar su da rai.9Idan sarki ya amince, ya bada umarni a kashe su, ni kuma zan bada talanti dubu goma na azurfa a hannun waɗanda ke tafiyar da cinikaiyar sarki, domin susa a cikin baitulmalin sarki."
10Sai sarki ya tuɓe zobensa daga yatsansa ya ba Haman ɗan Hamedata Ba'agagite, maƙiyin Yahudawa.11Sarki ya cewa Haman, "Zan tabbatar an mayar maka da kuɗin da kuma mutanenka. Za ka yi abin daka gadama da su."
12Sai aka kira magatakardun sarki a rana ta goma sha uku ga watan fari, aka rubuta doka game da dukkan umarnin da Haman ya bayar zuwa ga masu mulkin lardunan sarki, waɗanda suke bisa dukkan larduna, zuwa ga gwamnonin dukkan al'umma, da shugabannin dukkan mutane, ga kowanne lardi bisa ga irin rubutunsa, da kowacce al'umma kuma bisa ga harshenta. Da sunan Sarki Ahasuros aka rubuta, aka kuma hatimce shi da zobensa.13Aka aika da takardun hannu da hannu ta wurin manzanin zuwa ga dukkan lardunan sarki, domin a shafe su, a kashe, a kuma hallaka dukkan Yahudawa, samari da tsofaffi, yara da mata, rana ɗaya - a rana ta goma sha uku a watan goma sha biyu (wato watan Ada) - a kuma washe mallaƙarsu.
14Sai aka sanar kowanne lardi takardar data zama shari'a. Aka sanar da dukkan mutane a kowanne lardi cewa su shirya domin wannan rana.15Manzanin suka tafi da hanzari domin su baza umarin sarki. Aka baza umarnin kuma a fadar Susa. Da sarki da Haman suka zauna domin su sha, amma birnin Susa ya ruɗe.

4

1Da Modakai ya ji dukkan abin da aka riga aka yi, sai ya kyekketa tufafinsa yasa rigar makoki da toka. Ya fita waje ya je tsakiyar birni, ya yita rusa kuka da bacin rai mai tsanani.2Iyakarsa bakin ƙofar sarki kaɗai, domin ba a yardar wa kowa ya wuce wurin sanye da tsummoki ba.3A kowanne lardi, duk inda umarnin da dokar sarki ya kai, Yahudawa suka yi ta makoki ƙwarai, tare da azumi, kuka da makoki. Da yawa kuma suka zauna cikin tsummoki da toka.

4Da kuyangun Esta da barorinta suka zo suka faɗa mata, sarauniya ta damu ƙwarai. Ta aika wa Modakai tufafin sawa (domin ya tuɓe tsummokaransa), amma ya ƙi karɓarsu.5Sai Esta ta kira Hatak, ɗaya daga cikin wakilan sarki wanda aka sasu yi mata hidima. Ta umarce shi ya je wajen Modakai ya binciko abin daya faru da kuma ma'anar al'amarin.
6Sai Hatak ya tafi wurin Modakai a dandalin birnin da ke gaban ƙofar sarki.7Modakai ya gaya masa dukkan abin daya faru da shi, da kuma jimillar azurfar da Haman ya alƙawarta zai auna ya sa a baitulmalin sarki domin a kashe Yahudawa.8Ya kuma ba shi takardar umarnin bugu na biyu a Susa domin hallaka Yahudawa. Yayi haka ne domin Hatak ya nuna wa Esta, ya kuma ba ta nawaiyar tafiya wurin sarki don ta roƙi tagomashi ta kuma nemi alfarma daga gare shi game da mutanenta.
9Sai Hatak ya tafi ya faɗa wa Esta abin da Modakai yace.10Sai Esta ta yi magana da Hatak cewa ya koma wurin Modakai.11Ta ce, "Dukkan barorin sarki da mutanen lardunan sarki sun sani cewa duk wani namiji ko mace wanda ya shiga cikin farfajiyar sarki ba tare da an kira shi ba, doka ɗaya ce tak: wato dole a kashe shi - sai ko wanda sarki ya miƙa wa sandar zinariya kaɗai domin ya rayu. Ba a kira ni in je wurin sarki ba kwanakin nan talatin."12Sai Hatak ya tafi ya faɗa wa Modakai abin da Esta ta ce.
13Modakai ya mayar da wannan saƙo: "Kada ki yi tsammanin saboda kina gidan sarki zaki kuɓuta fiye da sauran Yahudawa.14Idan kika yi shiru a wannan lokaci, to gudunmawa da tsira zasu zo wa Yahudawa daga wani wuri, amma ke da gidan mahaifinki zaku hallaka. Wa ya sani ko kin sami wannan matsayin mulkin saboda makamancin lokaci irin wannan?"
15Sa'an nan Esta ta aika wa Modakai wannan saƙo,16"Kaje ka tattara dukkan Yahudawan da ke zaune a Susa, kuyi azumi domina. Kada ku ci ko ku sha har kwana uku, rana ko dare. Ni da 'yan matana ma zamu yi haka. Sa'an nan zan je wajen sarki, koda yake yin hakan ya saɓa wa shari'a, idan na hallaka, na hallaka."17Modakai ya tafi yayi duk abin da Esta ta faɗa masa yayi.

5

1Bayan kwana uku, sai Esta ta saka rigunan sarauta ta tafi ta tsaya a shirayin ciki na fadar sarki, a gaban gidan sarki. Sarki yana zaune a kan kursiyinsa a masarautar gidansa, yana fuskantar kofar shiga gidan.2Lokacin da sarki ya ga sarauniya Esta tana tsaye a shirayi, sai ta sami amincewa a idanunsa. Sai ya miƙa mata sandar zinariya da ke hannunsa. Sa'an nan Esta ta matso ta taɓa kan sandar.

3Sa'an nan sarki yace mata, "Mene ne kike so Sarauniya Esta? Mene ne roƙon ki? Har ma rabin masarautata, za a ba ki."4Esta tace, "Idan sarki ya yarda, bari sarki da Haman su zo yau wurin liyafar dana shirya domin sa."
5Sa'an nan sarki yace, "Ku kawo Haman nan da nan, yayi abin da Esta ta ce." Sai sarki da Haman suka tafi liyafar da Sarauniya Esta ta shirya.6Lokacin da ana raba ruwan inabi a liyafar, sai sarki ya cewa Esta, "Me kike so? Za a baki. Mene ne kike roƙo? Har ma rabin masarautar, za a baki ita."
7Esta ta amsa, "Abin da nike so da kuma roƙona shi ne,8idan na sami tagomashi a idanun sarki kuma idan ya gamshi sarki ya amsa roƙona kuma ya girmama roƙona, bari sarki da Haman su zo liyafar da zan shirya maka gobe, sa'an nan zan amsa tambayar sarki."
9A wannan rana Haman ya tafi gida da murna da farinciki, a zuciyarsa. Amma da Haman ya ga Modakai a bakin ƙofar sarki, kuma Modakai bai tashi tsaye ba balle yayi rawar jiki a gabansa da ko wani tsoro, sai ya cika da hasala găba da Modakai.10Duk da haka Haman ya kame kansa ya tafi gidansa. Ya aika aka kira abokansa, ya kuma tattarosu da matarsa Zeresh.11Haman ya rattaba masu darajar wadatarsa, yawan "ya'yansa maza, da dukkan yawan matsayi da sarki ya girmama shi da su, da yadda yake da fifikon daya zarce na dukkan shugabanni da barorin sarki.
12Haman yace, "Sarauniya Esta bata gayyaci kowa ba sai ni zan je da sarki liyafar data shirya. Har ma gobe ta sake gayyata ta in zo tare da sarki.13Amma ban ɗauki duk wannan a bakin komai ba a gareni muddin in na ganin Modakai zaune a bakin ƙofar sarki."
14Sai Zeresh matarsa ta cewa Haman da dukkan abokansa. Bari a kafa wani gungume mai tsawon ƙafa hamsin. Da safe sai ka yi magana da sarki domin su rataye Modakai a kai. Sa'an nan ka tafi da murna tare da sarki wurin liyafar." Wannan ya gamshi Haman sai yasa aka kafa gungumen.

6

1A daren nan sarki ya kasa barci. Sai ya umarci barori su kawo tarihin ayyukan mulkinsa, aka kuma riƙa karanta wa sarki da murya.2Sai aka tarar a rubuce a wurin cewa Modakai ya faɗi game da Bigtana da Teresh, fadawan sarki biyu da ke tsaron ƙofa, da suka yi ƙoƙarin su cuci Sarki Ahasuros.3Sarki ya tambaya, "Me aka yi don a bashi girma ko a maida Modakai sananne saboda yayi wannan abu?" Sai samari matasa na sarki da ke masa hidima suka ce, "Ba a yi masa komai ba."

4Sarki yace, "Wa ke a shirayi?" Yanzu fa Haman ya rigaya ya shigo shirayin gidan sarki na waje domin yayi masa magana game da rataye Modakai a kan gungumen daya kafa masa.5"Barorin sarki suka ce masa, Haman yana tsaye a shirayi." Sarki yace bari ya shigo ciki."6Da Haman ya shigo, sarki yace masa, "Me za a yiwa mutumin da sarki yake jin daɗin ya girmama shi?" Sai Haman yace a zuciyarsa, "Wane ne kuwa sarki zai ji daɗin girmama shi fiye da ni?"
7Haman ya cewa sarki, "Saboda mutumin da sarki ke jin daɗin girmama shi,8bari a kawo rigunan sarauta, waɗanda sarki ya taɓa sawa, da dokin da sarki ya taɓa hawa, kuma a sa masa kambin sarauta.9Sa'an nan da rigunan da dokin a ba da su ga ɗaya daga cikin manyan shugabanni. Bari su sa wa mutumin da sarki ke so ya girmama rigunan, bari kuma su bishe shi a kan dokin, a titunan birni. Bari kuma su yi shela a gabansa, "Wannan shi ne abin da ake yi wa wanda sarki ke jin daɗin girmama shi!'"
10Sai sarki ya cewa Haman, "Yi hanzari ka ɗauki rigunan da dokin, kamar yadda ka faɗi kayi wa Modakai Bayahude wanda ya kan zauna a ƙofar sarki. Kada ka kasa yin ko abu ɗaya daga abin da ka faɗa."11Sai Haman ya ɗauki rigunan da dokin. Ya sanya wa Modakai rigunan ya bishe shi bisa dokin a dukkan titunan birnin. Yayi ta shela a gabansa, '"Haka ake yi wa mutumin da sarki yake jin daɗin girmama shi."
12Modakai ya dawo ƙofar sarki. Amma Haman ya gaggauta zuwa gidansa, yana makoki, da kansa a lulluɓe.13Haman ya gaya wa matarsa Zeresh da dukkan abokanansa duk abubuwan da suka faru da shi. Sai mutanensa sanannu domin hikimarsu, da Zeresh matarsa suka ce masa, "Idan dai Modakai, wanda ka fara faɗuwa a gabansa Bayahude ne, ba zaka ci nasara a kansa ba, amma hakika zaka faɗi a gabansa."14Suna cikin magana da shi haka, sai ga hakiman sarki sun iso. Suka gaggauta suka tafi da Haman wurin liyafar da Esta ta shirya.

7

1Sai sarki da Haman suka tafi su yi liyafa da Sarauniya Esta.2A kan rana ta biyu, da ake bada ruwan inabi, sarki ya cewa Esta, "Mene ne roƙonki, Sarauniya Esta? Za a biya maki. Me kike tambaya? Har ma rabin masarautar ma, za a kuma baki."

3Sai Sarauniya Esta ta amsa, "Idan na sami tagomashi a idanun ka, idan kuma ka yarda, bari a barni da raina - wannan shi ne roƙona, ina kuma roƙon wannan domin mutanena.4Gama an sayar damu - ni da mutanena, domin a hallaka mu, a kashe, a kuma shafe mu gaba ɗaya. Dama a ce an sayar damu ga bauta, maza da mata bayi, dana yi shuru, gama ba wani ƙunci makamancin haka da zai bada dalilin damun sarki."5Sai Sarki Ahasuros ya cewa Sarauniya Esta, "Wa ye shi? Ina za a sami wannan mutum daya ƙudurta a zuciyarsa yayi makamancin abu haka?"
6Esta tace, "Mafaɗacin mutumin, wannan maƙiyi shi ne mugun nan Haman!" Sai Haman ya firgita a gaban sarki da sarauniya.7Sarki ya miƙe tsaye cikin hasala wurin shan ruwan inabin liyafar ya tafi cikin lambun fãda, amma Haman ya jira ya roƙi ransa daga Sarauniya Esta. Ya lura sarki yana niyyar zartar da hallakarwa gãba da shi.
8Sarki ya komo daga lambun fãda zuwa cikin ɗakin da aka shayar da su ruwan inabi. Haman ya faɗi a kan kujerar da Esta take. Sai sarki yace, "Zai ci mutuncin sarauniya a gabana a cikin gidana?" Da zarar fitar wannan magana daga bakin sarki, sai barorin suka lulluɓe fuskar Haman.
9Sai Harbona, ɗaya daga cikin hakimai da ke wa sarki hidima, ya ce, "Akwai wani gugume mai tsawon kamu hamsin kusa da gidan Haman. Ya kafa shi ne saboda Modakai, wanda yayi magana domin a kare sarki." Sarki yace, "A rataye shi a kai."10Sai suka rataye Haman bisa gungumen da ya shirya saboda Modakai. Sai hasalar sarki ya huce.

8

1A wannan ranar Sarki Ahasuros ya bai wa Sarauniya Esta mallakar Haman, maƙiyin Yahudawa, sai kuma Modakai ya fara hidima a gaban sarki, gama Esta ta gaya wa sarki dangartakarta da Modakai.2Sai sarki ya cire zobensa na hatimi, wanda ya karɓe daga wurin Haman, sai ya ba da shi ga Modakai. Esta ta sa Modakai ya zama mai lura da gidagen Haman.

3Sai Esta ta sake yin magana da sarki. Ta kwantar da fuskartar a ƙasa tana kuka yayinda take roƙo gareshi ya kawo ƙarshen mugun shirin Haman Ba'agage, da maƙarkashiyar daya ƙulla wa Yahudawa.4Sai sarki ya miƙo sandar zinariya na sarauta ga Esta, ta tashi ta tsaya a gaban sarki.
5Sai ta ce, "Idan ya gamshi sarki, kuma idan na sami tagomashi a wurinka, idan abin yayi dai-dai a ganin sarki, kuma idan na sami tagomashi a idanunka, bari a bada rubutaccen umarni da zai soke wasi‌ƙ‌un da Haman ɗan Hamedata Ba'agage, ya rubuta domin ya hallakar da Yahudawa waɗanda suke warwatse cikin lardunan sarki.6Gama yaya zan jimre da ganin masifar da za ta faɗo wa mutanena? Ta yaya zan iya daure wa ganin hallakarwar dangina?"
7Sarki Ahasuros ya cewa Sarauniya Esta da kuma Modakai Bayahude, "Duba, na miƙa wa Esta gidan Haman, kuma sun rataye shi a bisa gungume, domin yayi shirin kaiwa Yahudawa farmaki.8Rubuta wani umarni domin Yahudawa a cikin sunan sarki a kuma hatimce shi da zoben sarki. Gama umarnin da aka riga aka rubuta da sunan sarki aka kuma hatimce shi da zoben sarki ba za a iya soke shi ba."
9Sai aka kirawo magatakardan sarki a wannan lokaci, a cikin wata na uku, wanda shi ne watan Siban, a ranar ashirin da uku ga wata. Aka rubuta umarni ɗauke da dukkan abin da Modakai ya umarta game da Yahudawa. Aka rubuta zuwa ga gwamnonin larduna, su gwamnoni da shugabannin lardunar da ke zaune daga Indiya zuwa Kush, larduna 127, ga kowanne lardi aka rubuta da irin rubutunsu, da kuma ga kowaɗanne mutane cikin yarensu, da kuma ga Yahudawa da rubutunsu da yarensu.
10Modakai yayi rubutu da sunan sarki Ahasuros ya kuma hatimce shi da zoben hatimin sarki. Ya aika takardun ta hannun 'yan kada ta kwana mahaya doki masu gudu sosai da ake yin anfani da su a hidimar sarki, wanda aka yi renon su daga masarauta.11Sarki ya baiwa Yahudawa na kowanne birni izinin taruwa tare a kuma yi tsayayya don kariyar rayukarsu: su shafe su gaba ɗaya, su kashe, su kuma hallakar da kowacce taruwar masu makamai daga kowaɗanne mutane, ko lardin da ke niyyar kawo masu farmaki, da yaransu da kuma matayensu, ko su kwashi dukiyoyinsu ganima.12Wannan za a aiwatar cikin dukkan lardunan sarki Ahasuros, a ranar sha uku na watan sha biyu, wanda shi ne watar Ada.
13Takardar dokar za a miƙa ta a matsayin shari'a kuma za a bayyana ta a fili ga dukkan mutane. Yahudawa sai su zauna da shiri a wannan rana don ɗaukar fansa kan maƙiyansu.14Sai 'yan kada ta kwana suka hau dawakan masarauta da ake amfani dasu a hidimar sarki. Suka tafi babu ɓata lokaci. Dokar sarki kuwa aka miƙa ta daga fada a Susa.
15Sai Modakai ya tashi daga gaban sarki sanye da rigunan sarauta na shuɗi da fari, tare da gagarumin kambi na zinariya da kuma alkyabba ta lillin mai ruwan shunayya, sai birnin Susa tayi sowa da kuma farinciki.16Yahudawa suka sami sauƙi da kuma farinciki, da kuma murna da kuma daraja.17A kowanne lardi da cikin kowanne birni, dukkan inda umarnin sarki ya kai, aka yi farinciki da kuma murna a tsakanin Yahudawa, aka yi biki da kuma hutu. Dayawa daga cikin mutane daban-daban a ƙasar suka zama Yahudawa, domin tsoron Yahudawa ya faɗo masu.

9

1Yanzu a cikin watan sha biyu, wanda shi ne watan Ada, a ranar sha uku, lokacin da za a aiwatar da shari'a da kuma dokar sarki, a ranar da makiyan Yahudawa ke sa ran zasu sha karfinsu, aka juyad da yanayin. Yahudawa suka sha karfin waɗanda suka tsane su.2Yahudawa suka tattaru a biranensu cikin dukkan lardunan sarki Ahasuros, su tayar wa waɗanda suka so su kawo masu bala'i. Babu wanda ya iya tsayayya dasu, gama tsoronsu ya abko wa dukkan mutanen.

3Dukkan shugannin lardunar, da gwamnonin lardunar, su gwamnoni, da ma'aikatan sarki, suka taimaka wa Yahudawa domin tsoron Modakai ya abko masu.4Gama Modakai ya zama mutum mai girma a gidan sarki, kuma labarinsa ya bazu a dukkan larduna, domin mutumin Modakai ya zama mai girma.5Yahudawa suka kai hari ga makiyansu da takobi, suna kisansu da hallakar da su, kuma suka yi masu yadda suka ga dama ga waɗanda suka ƙisu.
6A cikin fãdar Susa da kanta Yahudawa suka kashe da kuma hallakar da mutum ɗari biyar.7Suka kashe Farshandata, Dalfon, Asfata,8Forata, Adaliya, Aridata,9Farmashta, Arisai, Aridai, da Baizata,10da kuma 'ya'ya maza na Haman ɗan Hamedata su goma, maƙiyin Yahudawa. Amma basu kwashi ganima ba.
11A wannan rana jimillar waɗanda aka kashe cikin fãdar Susa, aka faɗa wa sarki.12Sai sarki ya cewa Sarauniya Esta, "Yahudawa sun kashe mutum ɗari biyar cikin fãdar Susa, har da 'ya'ya maza na Haman su goma. Mene ne kuma suka aiwatar cikin sauran lardunar sarki? Yanzu mene ne roƙonki? Za a baki. Mene ne bukatarki? Za a biya maki."
13Esta tace, "Idan ya dace a ganin sarki, bari a baiwa Yahudawan da ke cikin Susa izinin aiwatar da dokar yau a gobe kuma, bari kuma a rataye gawawakin 'ya'ya maza na Haman su goma a bisa gumagumai."14Sai sarki ya umarta da a yi haka. Aka zartar da dokar a cikin Susa, aka kuma rataye 'ya'ya maza goma na Haman.
15Yahudawa da ke a Susa suka taru tare a rana ta sha huɗu a watan Ada, suka kashe mutum ɗari uku cikin Susa, amma ba su kwashi ganima ba.16Sauran Yahudawa da ke a lardunan sarki suka taru tare don su kare rayukansu, sun kuma ƙuɓuta daga makiyansu suka kuma kashe mutum dubu saba'in da biyar daga waɗanda suka tsanesu, amma basu ɗibiya hannunsu bisa dukiyan waɗanda suka kashe ba.
17Wannan ya faru ne a ranar sha uku na watan Ada. A rana ta sha huɗu sai suka huta suka maishe ta ranar shagali da kuma murna.18Amma Yahudawan da ke a Susa suka taru tare a ranakun sha uku da sha huɗu. A rana ta sha biyar suka ka huta suka maishe ta ranar shagali da kuma murna.19Shi yasa Yahudawan da ke ƙauyuka, waɗanda suka yi gidajensu a ƙauyukan karkara, suka maida rana ta sha huɗu na watan Ada ranar murna da kuma shagali, da kuma ranar da zasu aika wa juna kyaututtukan abinci.
20Modakai ya rubuta waɗannan abubuwan ya kuma aika wasiƙu zuwa ga dukkan Yahudawan da ke cikin dukkan lardunan sarki Ahasuros, na kusa dana nesa,21yana umurtansu dasu kula su kuma kiyaye ranakun sha huɗu da kuma sha biyar na Ada a kowacce shekara.22A wannan kwanaki ne Yahudawa suka kuɓuta daga maƙiyansu, da kuma watan da baƙin cikinsu ya zama farin ciki, kuma ranar makoki ta zama ranar shagali. Zasu maishe su ranakun shagali da kuma murna, da kuma aikar da kyaututtukan abinci ga juna, da kuma kyaututtuka ga talakawa.
23Sai Yahudawa suka cigaba da shagali kamar yadda suka fara, suna aiwatar da abin da Modakai ya rubuta garesu.24A wannan lokacin da Haman ɗan Hamedata Ba'agage, maƙiyin dukkan Yahudawa, ya shirya wa Yahudawa makirci don ya hallakar dasu, ya kuma jefa Fur (wato, ya jefa ƙuri'u), don ya hargitsa su ya hallakar da su.25Amma da zancen ya kai ga sarki, sai ya bada umarnai ta wasiƙu domin makircin da Haman ya ƙulla gãba da Yahudawa shi koma kansa, da kuma a rataye shi da 'ya'yansa maza a bisa gumagumai.
26Saboda haka aka kira waɗannan ranakun sunan Furim, bisa ga sunan Fur. Saboda dukkan abubuwan da aka rubuta cikin wannan wasiƙa, da dukkan abin da suka gani da idanunsu ta kuma same su,27Yahudawa suka yi na'am da sababbin ranaku da al'ada. Wannan ranaku zasu zama dominsu, da kuma zuriyarsu, da kuma dukkan wanda zai haɗa kai da su. Ya kuma zama cewa za su tuna da waɗannan ranakun biyu sau biyu a kowacce shekara. Zasu kula da waɗannan ranakun a hanyoyi na musamman da kuma a lokaci ɗaya kowacce shekara.28Waɗannan ranaku za a yi bukukuwa a kuma kula dasu a kowacce tsara, da kowanne iyali, da kowanne lardi, da kowanne birni. Waɗannan Yahudawan da kuma zuriyarsu ba zasu dena tunawa da waɗannan ranakun Furim cikin aminci ba, domin kada su manta da su.
29Sarauniya Esta ɗiyar Abihel da Modakai Bayahude suka yi rubutu da cikakken iko suka kuma tabbatar da wannan wasika ta biyu game da Furim.
30Aka aika wasiƙu zuwa ga dukkan Yahudawa cikin larduna 127 na masarautar Ahasuros, ana yi wa Yahudawa barka na salama da gaskiya.31Waɗannan wasiƙu suka tabbatar da ranakun Furim cikin lokacinsu, kamar yadda Modakai Bayahude da Sarauniya Esta suka dokaci Yahudawa. Yahudawa suka yi na'am da wannan doka domin kansu da kuma zuriyarsu, kuma kamar yadda suka yi na'am da lokacin azumi da makoki.32Dokar Esta ta tabbatar da waɗannan sharuɗɗai game da Furim, an kuma rubuta su cikin littafi.

10

1Sa'an nan Sarki Ahasuros yasa dokar haraji a ƙasar da kuma kasashen tuddai na bakin teku.2Dukkan aikin ci gaba na iko dana karfi, tare da cikakken tarihin girman Modakai ta yadda sarki ya darajartar da shi, aka rubuta su cikin littafin tarihin sarakunan Midiya da kuma Fasiya.

3Modakai Bayahude ya zama na biyu bayan sarki Ahasuros ta fannin mulki. Mai girma ne cikin Yahudawa da kuma sananne cikin 'yan'uwansa Yahudawa masu yawa, gama yana kula da lafiyar mutanensa yana yin maganar salama domin dukkan mutanensa.

Littafin ayuba

1

1Akwai wani mutum a ƙasar Uz mai suna Ayuba; Ayuba kuwa marar laifi ne mai gaskiya, wanda ke tsoron Yahweh ya kuma juya wa mugunta baya.2A ka haifa masa 'ya'ya bakwai maza da 'yammata uku.3Ya mallaki tumaki dubu bakwai da raƙuma dubu uku da bijimai ɗari biyar da jakai ɗari biyar da kuma bayi masu yawan gaske. Shi ne ya fi girma a cikin dukkan mutanen Gabas.

4An keɓe rana domin kowanne ɗă, ya yi liyafa a cikin gidansa. Sukan aika a kira 'yan'uwansu mata su uku su ci su sha tare da su.5Sa'ad da kwanakin liyafar suka ƙare, sai Ayuba ya aika su zo ya tsarkake su. Ya kan tashi da sassafe ya miƙa baye--baye na ƙonawa domin kowanne ɗaya a cikin 'ya'yansa, gama ya kan ce, "Ya yiwu yarana sun yi zunubi sun yi saɓon Yahweh a cikin zukatansu." Haka Ayuba yakan yi kullun.
6A ranar da 'ya'yan Allah maza suka zo domin su bayyana kansu a gaban Yahweh. Sai Shaiɗan ma ya biyo su. Sai Yahweh yace da Shaiɗan, "Daga ina ka zo?"7Sai Shaiɗan ya amsawa Yahweh yace, "Daga garari cikin duniya da zirga--zirga a cikinta."8Sai Yahweh yace da Shaiɗan, "Ka kuwa lura da Ayuba bawana? Gama babu kamar sa a duniya, marar laifi ne kuma mutum ne mai gaskiya yana tsoron Yahweh ya juya wa mugunta baya.
9Sa'annan Shaiɗan ya amsawa Yahweh yace, "Haka nan Ayuba ya ke tsoron Allah ba dalili?10Ba ka kare shi ta kowanne gefe ba, shi da gidansa da dukkan abin da ya ke da shi? K a sawa ayyukan hannuwansa albarka da shanunsa sun yaɗu da yawa a cikin ƙasa.11Amma yanzu ka miƙa hannunka ka taɓa abin da ya ke da shi dukka, ka gani idan bai la'ance ka kana gani ba."12Sai Yahweh yace da Shaiɗan, "Duba, dukkan abin da ya ke da shi na hannunka." Sai dai a kansa ne kaɗai ba zaka sa hannunka ba." Sa'annan Shaiɗan ya fita daga wurin Yahweh.
13Sai ya zama a wata rana, 'ya'yansa maza da mata suna ci suna shan ruwan inabi a gidan babban wansu.14Wani ɗan aike ya zo wurin Ayuba yace, "Bijimai suna huɗa jakai kuma suna kiwo a gefensu.15Sai Sabiyawa suka auko ba zato suka kwashe su. Bayin kuma sun kashe su da kaifin takobi. Ni kaɗai ne na tsira don in gaya maka."
16Yana cikin yin magana, sai wani kuma ya zo ya ce, "Wutar Allah ta sauko daga sama ta cinye tumaki duk da bayin. Ni kaɗai ne na tsira don in gaya maka."17Yana cikin yin magana, sai wani kuma ya zo ya ce, "Kaldiyawa sun zo a ƙungiyoyi uku, sun kawo hari a kan raƙuman sun kwashe su. Sun kuma kashe bayin da kaifin takobi. Ni kaɗai ne na tsira don in gaya maka."
18Yana cikin yin magana, wani kuma ya zo ya ce, "Ya'yanka maza da matan suna ci suna sha a gidan babban wansu.19Sai wata iska mai ƙarfi ta taso daga cikin jeji ta buge kusurwoyin gidan guda huɗu. Gidan ya faɗa a kan matasan, kuma sun mutu. Ni kaɗai ne na tsira don in gaya maka."
20Sai Ayuba ya tashi, ya keta tufafinsa, ya aske kansa, ya faɗi da fuskarsa a ƙasa, ya yi wa Yahweh sujada.21Ya ce, "Sa'ad da na fito daga cikin mahaifiyata tsirara nake, kuma tsirara zan koma can. Yahweh ne ya bayar, Yahweh ne kuma ya ɗauke. Bari sunan Yahweh ya zama mai albarka."22A cikin wannan lamari dukka, Ayuba bai yi zunubi ba, bai kuma yi zargi ga Allah kan ya yi kuskure ba.

2

1Wata rana kuma da 'ya'yan Allah maza suka zo su baiyana kansu a gaban Yahweh. Shaiɗan ma ya biyo su don ya baiyana kansa a gaban Yahweh.2Yahweh yace da Shaiɗan, "Daga ina ka zo?" Sai Shaiɗan ya amsawa Yahweh yace, "Daga garari cikin duniya da kai da kawowa a kanta."

3Yahweh yace da Shaiɗan, "Ka lura da bawana Ayuba? Gama babu kamar sa a duniya, marar laifi ne, mutum ne mai gaskiya, yana juya wa mugunta baya. Har yanzu yana nan riƙe da nagartarsa, duk da yake ka sa in yi gãba da shi, don in hallaka shi babu wani dalili."
4Shaiɗan ya amsawa Yahweh yace, "Jiki magayi, tabbas mutum zai iya rabuwa da dukkan abin da yake da shi domin ya ceci ransa.5Amma ka miƙa hannunka yanzu ka taɓa ƙasusuwansa da jikinsa, ka gani idan bai la'ance ka kana gani ba."6Yahweh yace da Shaiɗan, "Ga shi, yana hannunka; ransa ne kaɗai ba zaka taɓa ba."
7Daga nan sai Shaiɗan ya tafi daga gaban Yahweh. Ya bugi Ayuba da marurai tun daga tafin ƙafarsa har zuwa kansa.8Ayuba ya ɗauki ɓallin kasko yana susa da shi, kuma ya zauna a cikin tsakiyar toka.
9Sai matarsa tace da shi, "Har yanzu kana nan riƙe da nagartarka? Ka la'anci Allah ka mutu."10Amma ya ce da ita, "Kina yin magana kamar yadda gaɓuwar mace ke yi. Za mu karɓi abu mai kyau daga wurin Allah mu ƙi karɓar marar kyau"? A cikin wannan lamari dukka, Ayuba bai yi zunubi da leɓunansa ba.
11A na nan, sa'ad da abokan Ayuba uku suka ji dukkan wannan bala'in da ya same shi, kowannen su ya tawo daga garinsa: Elifaz Batemane da Bildad Bashune da Zofar Banamate. Suka sa lokaci domin suzo su makoki tare da shi su kuma ta'azantar da shi.
12Sa'ad da suka hango daga nesa, basu iya gane shi ba. Suka tada muryoyinsu suka yi kuka; kowannen su ya keta tufafinsa ya watsa ƙura a sama dakuma bisa kansa.13Sa'an nan suka zauna a ƙasa tare da shi a ƙasa har yini uku da dare uku. Ba wanda ya yi masa magana, gama sun ga yana da baƙin ciki mai yawa.

3

1Bayan wannan, Ayuba ya buɗe bakinsa ya la'anci ranar da aka haife shi.2Ya ce:3"Bari ranar da a ka haife ni ta lalace, kuma da daren aka ce, 'an ɗauki cikin yaro.'

4Bari ranar ta zama baƙa; Dãma kada Yahweh ya tuna da ita daga sama, kada ma rana ta yi haske a kanta.5Dãma duhu da inuwar kwarin mutuwa su maishe ta tasu. Dãma girgije ya tsaya a kan ta, dãma kowanne abu mai sa rana ta yi baƙi ya ba ta tsoro da gaske.
6Wannan daren kuma, dãma baƙin duhu ya rufe shi. Dãma kada ta yi farinciki a ranakun shekara; dãma kada a lissafa ta cikin kwanakin watanni.7Duba, dãma wannan dare ya zama wofi; kada muryar farinciki ta zo cikinsa.
8Dãma su la'anci wannan rana, waɗanda suka san yadda a ke tashin Lebiyatan.9Dãma taurarin wayewar giri na wannan rana su yi duhu. Dãma wannan rana ta nemi haske, amma ta rasa; dãma kada ta ga ƙyallin wayewar gari,10saboda bata rufe ƙofofin cikin uwata ba, kuma domin bata ɓoye masifa daga idanuna ba.
11Me yasa ban mutu sa'ad da na fito daga ciki ba? Me yasa ban saki ruhuna sa'ad da uwata ta haife ni ba?12Me yasa gwiwoyinta suka marabce ni? Me yasa nonanta suka yarda na shã su?
13Gama da yanzu ina kwance shiru. Da ina barci ina hutawa14tare da sarakuna da mashawartan duniya, waɗanda suka gina wa kansu kaburbura kuma yanzu sun ruɓe.
15Ko kuwa da yanzu ina kwance tare da sarakuna waɗanda dã suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.16Ko kuwa ƙila da an yi ɓari na, kamar jariran da basu taɓa ganin haske ba.
17A can masu mugunta sun huta da masifa; a can masu gajjiya suna cikin hutu.18A can 'yan kurkuku sun sami saki tare; bãsu jin muryar masu kora bayi.19Manya da ƙananan mutane suna can; bawa yana da 'yanci daga wurin ubangijinsa a can.
20Me yasa ake ba wanda ke cikin ƙunci haske? Me yasa a ke ba wanda ke da baƙin ciki rai,21wanda ya ƙagara yaga mutuwa bata zo ba, ga wanda yake neman mutuwa kamar ɓoyayyiyar dukiya?22Me yasa a ke bada haske ga wanda yake farinciki ƙwarai da murna idan ya sami kabari?
23Me yasa a ke ba mutum wanda hanyarsa take a ɓoye haske, mutum wanda Allah ya kulle shi?24Gama ajjiyar zuciya nake yi maimakon cin abinci; an zubar da gurnanina kamar ruwa.
25Gama abin da na ji tsoro ya zo kaina; abin dana tsorata yazo mani.26Ba sauƙi a gare ni, ban yi shuru ba, kuma ban huta ba; maimakon haka masifa ce take zuwa."

4

1Sai Elifaz Batemane ya amsa ya ce,2Idan wani yayi ƙoƙari ya yi magana da kai, baza ka yi haƙuri ba? Amma wa zai iya hana kansa yin magana?3Ka ga, ka koyawa mutane da yawa; ka ƙarfafa raunanan hannuwa.

4Kalmominka sun tallafi wanda yake faɗuwa; ka sa raunanan gwiwoyi sun yi ƙarfi.5Amma yanzu masifa ta zo kanka, kuma ka gaji; ta taɓa ka, kuma ka kaɗu.6Tsoronka bai zama ƙarfi a gare ka ba, ammincinka bai ishe ka bege ba?
7In ka yarda yi tunanin game da wannan: Wanda ba shi da laifi ya taɓa lalacewa? Ko a ina aka taɓa datse masu adalci?8Bisa ga abin da na gani, waɗanda suka huɗa mugunta suka shuka masifa su ke girbin ta.9Sukan lalace ta wurin numfashi Yahweh; zafin fushinsa ya kan cinye su.
10Rurin zaki, muryar zaki mai ban tsoro, haƙoran 'yan zakuna --sukan karye.11Tsohon zaki yakan lalace idan ba abin da zai kama; 'ya'yan zakanya sukan warwatsu ko'ina.
12An kawo mani wata matsala a asirce, kunnena ya karɓi raɗa game da ita.13Sa'annan tunanin ruya ya zo mani cikin dare, sa'adda barci mai nauyi ya zo kan mutane.
14A cikin dare tsoro da fargaba suka zo mani, dukkan ƙasusuwana suka motsa.15Sai wani ruhu ya wuce a gaban fuskata, gashin jikina ya tashi tsaye.
16Ruhun ya tsaya cik, amma ban iya gane baiyanuwarsa ba. Wani abu ya rufe idanuna; an yi shiru, sai na ji wata murya tace,17"Mutum mai mutuwa ya iya fin Allah adalci? Mutum zai iya fin mahallicinsa tsarki?
18Ka gani, idan Yahweh bai amince da bayinsa ba; idan ya zargi mala'ikunsa da wawanci,19yaya ga waɗanda ke zama a cikin gidaje na yumɓu, waɗanda tushensu yana cikin ƙasa, waɗanda a kan mutsuke su nan da nan fiye da ƙwaro.
20Tsakanin safiya zuwa yamma an hallaka su; sun lalace har abada ba abin da zai sa a tuna da su.21Ba a kan tsinke iggiyar ransu a jikinsu ba? Su mutu; su mutu ba tare da hikima ba.

5

1Ka yi kira yanzu; akwai wani mai ansa maka? Ga wanne cikin masu tsarkin zaka juya?2Gama fushi ya kan kashe wawan mutum; kishi yakan kashe dolo.3Na ga wawan mutum yana kahuwa, amma nan take na la'anci gidansa.

4Zaman lafiya yana nesa da 'ya'yansa; an murƙushe su a ƙofar birni. Ba wanda zai kuɓutar da su.5Mayunwaci ya kan cinye anfaninsa dukka; sukan ma ɗauko shi daga cikin ƙayayuwa. Masu jin ƙishi suna hãki domin dukiyarsu.
6Gama wahala bata fitowa daga cikin turɓaya; masifa kuma bata fitowa daga cikin ƙasa.7Maimakon haka an haifi mutum saboda masifa, kamar yadda tartsatsi yakan tashi sama.
8Amma a gare ni, zan juya wajen Allah shi da kansa; a gare shi zan danƙa al'amurana--9shi wanda ke yin manyan al'amuran da ba a iya ganewa, abubuwan mamakin da basu lissaftuwa.10Yakan bada ruwa a kan ƙasa, yakan aika da ruwa bisa filaye.
11Yakan yi haka ne domin ya tada ƙasƙantattu; yasa masu baƙin ciki su zauna lafiya.12Yakan lalata shirye--shiryen masu yaudara, domin kada su kai ga cika manufarsu.13Yakan kama mutane masu wayo cikin aikin yaudararsu; da sauri shirye--shiryen masu murɗiya sukan zo ƙarshe.
14Dare kan same su da rana, sukan yi lalube da rana sai kace dare ne.15Amma ya kan ceci mutum matalauci da takobi cikin bakinsu mabukata kuma daga hannun ƙarfafan mutane.16Domin mutum matalauci ya sami bege, rashin adalci kuma ya rufe bakinsa.
17Duba, mai albarka ne mutumin da Allah yakan hore shi; saboda haka kada ka rena horon Mai Iko Dukka.18Gama yakan sa a ji ciwo yayi magani, ya kan sa a ji rauni hannunsa kuma ya warkar.19Zai kuɓutar da kai daga masifu shida; hakika, a cikin masifu bakwai, babu muguntar da zata taɓa ka.
20A cikin yunwa zai fanshe ka daga mutuwa, a cikin yaƙi kuma daga hannun takobi.21Za a ɓoye ka daga la'anar harshe; ba zaka ji tsoron hallaka ba ko ta zo.22Zaka yi dariya a kan hallakar yunwa, ba zaka ji tsoron namun jeji na duniya ba.
23Gama zaka yi alƙawari da duwatsu a gonarka, namun jeji na gona zasu yi zaman lafiya da kai.24Zaka sani rumfarka tana lafiya; zaka ziyarci garken tumakinka ba kuwa zaka rasa kome ba.25Zaka kuma sani irinka zai yi girma, tsatsonka zasu zama kamar ciyawa a kan ƙasa.
26Zaka je kabari da tsufanka, kamar zangarkun damin hatsi da suke tafiya a lokacinsa.27Ka gani, mun yi binciken wannan lamari; ga kamanninsa, ka saurare shi, ka san shi kai da kanka."

6

1Sa'an nan Ayuba ya amsa ya ce,2"Oh, da dai an auna nauyinbaƙin cikina; da dai an sa wahalata a ma'auni!3Gama yanzu za tafi yashin tekuna nauyi. Shi yasa nake magana barkatai.

4Gama kibawun Mai Iko Dukka suna cikina, ruhuna yana shan dafin; razana daga Yahweh ta shiryo kanta gãba da ni.5Jakin jeji yakan yi hargowa inda yana da ciyawa? Sã yakan yi kuka ga abinci a gabansa?6Za a iya cin abin da ba shi da ɗanɗano ba tare da an sa masa gishiri ba? Ko akwai ɗanɗano ga farin ƙwai?
7Na ƙi taɓa su; suna kama da abinci mai gundura a gare ni.8Oh, dãmã za a amsa mani roƙona; oh, dãma Yahweh zai yarda in sami abin da nake ta nema in samu:9dãma Yahweh zai yarda ya ruƙurƙushe ni kawai, dã zai saki hannunsa ya datse ni daga wannan rayuwa!
10Bari wannan ya zama abin ƙarfafa ni--ko da ciwona ya ƙaru bai ragu ba: ban yi musun maganar mai tsarki ba.11Menene ƙarfina, da zan yi ƙoƙarin jira? mene ne ƙarshena, da zan ci gaba da rayuwa?
12Ƙarfina kamar ƙarfin dutse yake? Ko an yi jikina da tagulla ne?13Ba gaskiya ba ne cewa ba ni da taimako a cikin kaina ba, kuma an kori hikima daga cikina?
14Mutumin da ya kusa suma, ya kamata abokansa su ji tausayinsa; ko da ya watsar da jin tsoron Mai Iko Dukka.15Amma 'yan'uwana sun zama da aminci kamar hamadar da kan ƙafe, kamar magudanar ruwa marar anfani da ke wucewa a magudanai,16waɗanda sukan yi duhu saboda ƙanƙara ta rufe su, kuma saboda dusar ƙanƙara da ta ke a cikin su.17Idan su ka ji ɗumi sai su, sai su ɓace; idan zafi ya zo, sai su narke a inda suke.
18Fataken da ke bi ta wurinsu sukan ruƙa neman ruwa; sukan yi garari a busasshiyar ƙasa su lalace.19Fatake daga Tema sun duba can, fatake daga Sheba sun sa bege a cikin su.20Sun kunyata saboda sun gaskata zasu sami ruwa. Sun je wurin, amma an ruɗe su.
21Gama yanzu ku abokai baku da anfani a gare ni; kun ga takaicin da nake ciki kun ji tsoro.22Nace da ku, 'ku bani wani abu ne?' Ko ku bani wani abu daga dukiyarku?'23Ko ku cece ni daga hannun maƙiyina?' Ko ku fanshe ni daga hannun mai tsananta mani?'
24Ku koya mani, ni kuwa zan yi shiru; ku ganar da ni inda ban yi dai-dai ba.25Gaskiya dai ɗaci gare ta! A ina gardandaminku suka ga laifina?
26Kun yi shirin ku watsar da maganata, ku ɗauki maganar mutumin da yake cikin wahala kamar iska?27Tabbas, kun jefa ƙuri'a a kan ɗan da bashi da uba, kun mai da aboki abin samun riba.
28To, yanzu, idan kun yarda ku dube ni, gama tabbas ba zan yi ƙarya a gaban kuba ba.29Ku dena magana haka, na roƙe ku; kada kuyi rashin gaskiya; hakika ne, ku dena yin haka, hakika ina da gaskiya a al'amarina.30Akwai mugunta a kan harshena ne? Bakina ba zai iya ganewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?

7

1Ba wani mutum da ya taɓa yin aiki mai wuya ne a duniya?2Ashe kwanakinsa ba kamar na ɗan ƙwadago suke ba? Kamar bawan da ya ƙosa yamma ta yi, kamar ɗan ƙwadago mai neman haƙƙoƙinsa -3don haka an sa ni in jure da watannin wahala; An ba ni kwanaki cike da wahala.

4Sa'ad da na kwanta, sai in ce da kaina, 'Yaushe zan tashi kuma yaushe gari zai waye? Ina ta juye-juye har sai gari ya waye.5Jikina yana cike da tsutsotsi da sanyin ƙasa; gyambunan jikina sukan bushe sai kuma su fashe su zama sababbi.
6Kwanakina sun fi kibiya sauri; sukan wuce ba bege.7Allah ya tuna raina numfashi ne kawai; idona ba zai ƙara ganin alheri ba.
8Idon Yahweh, da ke gani na, ba zai ƙara gani na ba; idanun Yahweh za su dube ni, amma ba zan kasance ba.9Kamar yadda girgije yakan ɓace, haka wanda ya je Lahira ba zai ƙara fitowa ba.10Ba zai ƙara dawowa gidansa ba.; wurinsa ba zai ƙara sanin sa ba.
11Saboda haka ba zan kama bakina ba; zan yi magana cikin zafin rai a ruhuna; zan yi gunaguni cikin ɗacin raina.12Ni teku ce ko ni dorina ce da kuke tsaro na?
13Idan nace, 'gadona zai yi mani ta'aziya, shimfiɗata zata sa in ji sauƙi,'14sai ka firgita ni da mafarkai ka sa in ji tsoro da wahayoyi,15har na kan so a maƙare ni in mutu da a raya ƙasusuwana.
16Na rena rayuwata; bana marmarin in rayu koyaushe; ku ƙyale ni gama kwanakina basu da anfani.17Mene ne mutum har da zaka lura da shi, da zaka sa hankalinka a kan sa,18da zaka lura da shi kowacce safiya ka gwada shi kowanne lokaci?
19Sai yaushe zaka dena dube na, kafin ka bar ni ni kaɗai in samu in haɗiyi yawuna?20Ko dana yi zunubi, me zaka yi da ni, kai da kake tsaron mutane? Me yasa ka sã mani ido, har da zan zama matsala a gare ka?
21Me yasa ba zaka yafe laifofina ka ɗauke muguntata ba? Gama yanzu zan kwanta a cikin turɓaya; zaka neme ni a hankali, amma ba zan kasance ba."

8

1Sa'an nan Bildad Bashune ya amsa ya ce,2"Har yaushe zaka yi ta faɗin waɗannan abubuwa? Har yaushe maganar bakinka zata zama iska mai ƙarfi?3Ko Allah yana ɓata shari'a ne? Ko Mai Iko Dukka yana ɓata adalci ne?

4'Ya'yanka sun yi masa zunubi; mun san wannan, gama ya bashe su a hannun zunubansu.5Dama ace ka jure da neman Allah da miƙa roƙonka ga Mai iko dukka.
6Idan da kana da tsarki da aminci, to da babu shakka da ya tashi da kansa a madadin ka ya dawo da kai inda ya kamace ka.7Ko da yake ka farkonka kaɗan ne, har yanzu matsayin ƙarshenka ya fishi girma ƙwarai.
8Idan ka yarda ka tambayi mutanen dã, ka mai da hankali a kan abin da ubanninmu suka koya.9(Jiya a ka haife mu kuma bamu san kome ba saboda kwanankinmu a duniya inuwa ne).10Baza su gaya maka ko su koya maka ba? Baza su yi magana daga zuciyarsu ba?
11Tsire-tsire kan iya yin girma inda ba laima? Iwa ta iya yin girma ba tare da ruwa ba?12Tun suna da korensu ba tare da an sare su ba, zasu riga kowacce shuka bushewa.
13Haka kuma hanyoyin dukkan wanda ya mance da Allah; begen wanda bashi da halin kirki zai lalace.14Gabagaɗinsa zai lalace, bangaskiyarsa bata da ƙarfi kamar yanar gizo take.15Ya dogara ga gidansa, amma ba zai tallafe shi ba; ya riƙe shi, amma bai tsaya ba.
16A ƙarƙashin rana kore ne shi, rassansa sukan rufe lambunsa dukka.17Tarin duwatsu sun rufe sauyoyinsa, sukan nemi wurare masu kyau cikin duwatsu.18Amma idan aka hallaka wannan mutum daga wurinsa, sa'an nan wannan wurin zai yi musun sa yace, 'Ban taɓa ganin ka ba.'
19Duba, wannan ne "farinciki" na mutum mai irin wannan hali; waɗansu shuke--shuken zasu fito a wannan ƙasar a wurinsa.20Duba, Allah ba ya jefar da mutum marar laifi; kuma ba ya kama hannuwan masu aikin mugunta.
21Zaya sake cika bakinka da dariya, leɓunanka kuma da sowa.22Kunya zata rufe maƙiyanka; rumfar masu mugunta zata lalace har abada."

9

1Sa'an nan Ayuba ya amsa yace,2"Gaskiya ne haka yake na sani. Amma yaya mutum zai iya zama dai-dai wurin Allah?3Idan yana so yayi gardama da Allah, a cikin dubu ba zai iya amsawa ko sau ɗaya ba.

4Allah mai hikima ne kuma mai ƙarfi ne; wane ne ya taɓa yin jayayya da shi yaci nasara5shi wanda yake cire duwatsu ba tare da gargaɗi ba yakan birkice kowannen su a cikin fushinsa--6shi wanda yake girgiza duniya daga wurinta yasa ginshiƙanta su raurawa.
7Shi ne Allahn nan wanda yakan ce da rana kada ta fito, kuma ba ta fito ba, shi wanda ya kan lulluɓe taurari,8shi wanda yakan miƙar da sammai da kansa ya tattaka raƙuman ruwan teku,9shi wanda ƙungiyoyin taurari da zara da gamzaki da mafarauci da kare da zomo da kuma kaza da 'yayanta, gungun taurarin kudu.
10Shi wanda ke yin manyan abubuwan da ba za a iya bincika su ba, da abubuwan mamaki da basu lissaftuwa.11Duba, yana tare da ni kuma bana ganin sa, kuma yakan wuce, amma bana ganin sa.12Idan ya ɗauke wani abu, wa zai iya hana shi? Wane ne zai iya cewa da shi, 'Me kake yi?'
13Allah ba zai janye fushinsa ba; masu taimakon Rahab suna sunkuya wa a ƙarƙashinsa.14Yaya zan iya amsa masa, zan iya zaɓar kalmomin da zan iya yin nazari tare da shi?15Ko da ace ni mai adalci ne, ba zan iya amsa masa ba; sai dai in roƙi jinƙai kaɗai daga mai yi mani hukunci.
16Ko dana yi kira ya amsa mani, ba zan gaskata cewa yana sauraren muryata ba.17Gama ya karairaya ni da iska mai ƙarfi ya ruɓanɓanya ciwukana ba dalili.18Ya hana ni in ja numfashi kuma; ya cika ni da baƙinciki.
19Idan maganar ƙarfi ce, duba, shi mai iko ne! Idan maganar shari'a ce, wa zai iya sashi ya zo?20Ko da ina da gaskiya, bakina zai kãshe ni; koda ba ni da abin zargi, maganata zata nuna ni mai laifi ne.
21Bani da abin zargi, amma ban damu da kaina ba ko kaɗan; na rena raina.22Bai bambanta da komai ba da nace yakan hallaka marar abin zargi tare da mai mugunta.23Idan bulala tayi kisa nan da nan, sai ya yi wa al'amuran marar laifi ba'a.24An bayar da duniya a hannun masu mugunta; Yahweh ya rufe fuskokin alƙalanta. Idan bashi ba ne, to, wane ne?
25Kwanakina sun fi ɗan aike mai gudu sauri; kwanakina suna wucewa; basu ganin alheri a ko'ina.26Suna da sauri kamar jiragen ruwan iwa, yana sauri kamar gaggafar da ta kawo bãra a kan nama.
27Idan nace zan mance da koke--kokena, zan dena baƙinciki in yi murna,28sai in ji tsoron dukkan wahalhaluna saboda na sani kai ba zaka dube ni a matsayin marar laifi ba.29Tun da za a kashe ni, me kenan, zan yi ƙoƙari a wofi?
30Idan na yi wanka da ruwan ƙanƙara nasa hannuwana suka yi tsafta sosai,31Allah zai tura ni a kwari mai taɓo, tufafina zasu zama abin ƙyama tare da ni.
32Gama Allah ba mutum ba ne, kamar yadda nake, balle in ba shi amsa, har da zamu zo kotu tare da shi.33Ba wani alƙali a tsakanin mu wanda zai sa mana hannu mu dukka biyu.
34Ba wani alƙalin da zai iya ɗauke sandan Allah daga kaina, wanda ya hana tsoronsa ya firgitar da ni.35Sa'an nan ba zan yi magana in ji tsoronsa ba. Amma ga yadda abubuwa suke yanzu, ba zan iya yin haka ba.

10

1Na gaji da raina; zan yi maganar matsalata a fili; zan yi magana cikin ɗacin raina.2Zan ce da Allah, 'Kada ka kashe ni haka kawai; ka nuna mani abin da kake zargi na a kai.3Ya yi maka kyau ka wahalshe ni, ka rena aikin hannuwanka sa'ad da kake yin murmushi da shirye--shiryen masu mugunta.

4Ko kana da idanu na jiki ne? Kokana gani kamar mutum ne?5Ko kwanakinka kamar na ɗan'adam ne ko shekarunka kamar na mutane ne,6da kake yin bincike a kan muguntata kana neman zunubina,7duk da ka san bani da laifi kuma ba wanda zai iya kuɓutar da ni daga hannunka?
8Hannuwanka ne suka sifanta ni suka tsara kome nawa, amma kana hallaka ni.9Ina roƙon ka, ka tuna kai ne ka siffanta ni kamar yumɓu; zaka maishe ni cikin turɓaya ne kuma?
10Baka zubar da ni kamar madara ka cakuɗe ni kamar abin taunawa ba?11Ka lulluɓe ni da fata da nama ka ɗinke ni da ƙasusuwa da guringuntsi.
12Ka bani rai da jiyejiyenƙai; taimakonka ya tsare ruhuna.13Duk da haka ka ɓoye waɗannan abubuwaa zuciyarka--na san waɗannan abubuwan ne da kake tunaninsu:14idan na yi zunubi zaka kula da shi; ba zaka baratar da ni daga muguntata ba.
15Idan na yi aikin mugunta, kaito na; ko da nayi aikin adalci, ba zan yi fahariya ba, da yake ina cike da kunya ka dubi wahalata!16Idan na ɗaukaka kaina zaka bi ni kamar zaki; kuma zaka nuna kanka da ayyukan na ban mamaki na iko a kaina.
17Ka kawo mani sababbin shaidu ka ƙara fushinka a kaina; ka kawo mani hari da sababbin sojoji.
18To, me yasa ka fito da ni daga cikin ciki? Dama na saki ruhuna ba idon da ya gan ni.19Dãma na zama kamar ban taɓa kasancewa ba; dama an ɗauke ni daga cikin ciki zuwa kabari.
20Kwanakina ba 'yan kaɗan ba ne? Tsaya haka, ka rabu da ni, domin in ɗan sami hutu21kamin in kai inda ba zan iya dawowa ba, zuwa ƙasar duhu da inuwar mutuwa,22ƙasa mai duhu kamar tsakiyar dare, ƙasa ta inuwar mutuwa, babu wata ka'ida, inda haske kamar tsakar dare yake.'"

11

1Sa'an nan Zofar Banamate ya amsa ya ce,2"Ba za a bada amsa a kan waɗanan maganganun masu yawa ba? A gaskata da wannan mutumin, mai yawan magana?3Fankamarka zata sa sauran mutane suyi shuru ne? Sa'ad da kayi ba'a, ba wanda zai sa ka ji kunya ne?

4Gama kace da Allah, 'Bangaskiyata sahihiya ce, bani da laifi a idanunka.'5Amma, da Allah zai yi magana ya buɗe bakinsa gãba da kai;6da zai nuna maka asirin hikima! Gama shi yana da fahimta mai girma. Ka sani ba kamar yadda muguntarka take Allah yake nema ba.
7Zaka iya ganewa da Allah ta wurin binciken sa? Zaka iya fahimtar Yahweh sarai?8Matsalar tayi tsawo kamar samaniya ne; me zaka iya yi? Ta fi Lahira zurfi; me zaka iya sani?9Ta fi duniya tsawo, kuma ta fi teku faɗi.
10Idan ya wuce ya kulle wani, ko idan ya hukunta wani, wane ne zai iya hana shi?11Gama ya san maƙaryata; idan ya ga mugunta, baya lura da ita ne?12Amma wawayen mutane basu ganewa; zasu same ta sa'ad da jakin jeji ya haifi ɗan mutum.
13Amma da ka tsayar da zuciyarka sosai ka miƙa hannuwanka zuwa ga Yahweh;14da akwai mugunta a hannunka, amma daka kasa ta nesa da kai, da baka bari rashin adalci ya zauna a rumfarka ba.
15Da ka tada fuskarka ba tare da kunya ba; lallai da ka tsaya da ƙarfi ba tare da tsoro ba.16Da ka manta da damuwarka; sai dai ka tuna da ita kamar wucewar ruwa.17Da ranka yayi haske fiye da rana; ko da akwai duhu da ya zama kamar safiya.
18Da zaka natsu saboda akwai bege; lallai da ka sami tsaro kewaye da kai da ka huta a tsanake. Kuma da ka kwanta ka huta,19Kuma ba wanda zai tsoratar da kai; lallai da mutane da yawa sun nemi tagomashi a wurin ka.
20Amma idanun masu mugunta zasu kasa; ba zasu sami wurin ɓuya ba; begensu numfashin ƙarshe ne kaɗai"

12

1Sa'an nan Ayuba ya amsa ya ce,2"Ba shakka ku ne mutanen; hikima za ta mutu tare da ku.3Amma ni ma ina da fahimta kamar yadda kuma kuke da shi; ni ban gaza ku ba. Hakika, waye bai san irin abubuwa kamar waɗannan ba?

4Ni wani abu ne da makwabcina zai yiwa dariya - Ni, da nake kira bisa sunan Allah wanda ya kuma amsa mani! Ni, mutum mai adalci marar aibu kuma - yanzu na zama wani abin dariya.5A tunanin wani wanda yake zaune lafiya, akwai reni game da masifa; yakan yi tunani irin na ƙara kawo masifa kan waɗanda ƙafafunsu ke zarmewa.6Rumfunan mafasa na azurta, waɗanda kuma ke cakunar Allah suna nan lafiya; hannunwansu ne allolinsu.
7Amma yanzu ka tambayi dabbobi, kuma zasu koya maka; ka tambayi tsuntsayen sammai, zasu kuma gaya maka.8Ko kuma kayi wa ƙasa magana, zata kuma koya maka; kifayen teku zasu shaida maka.
9Wace dabba ce cikin dukkan waɗannan da bata sani cewa hannun Yahweh ne yayi wannan ba?10A cikin hannunsa ran kowanne rayayyen abu yake da kuma numfashin dukkan 'yan adam.
11Ashe kunne ba yakan gwada dukkan maganganu kamar yadda baki ke ɗanɗana abinci ba?12Hikima tana ga tsoffin mutane; a tsawon kwanaki kuma akwai fahimta.
13Hikima da iko suna ga Allah; shi ke da shawara da fahimta.14Duba, yakan rushe, ba za a kuma iya ginawa ba, idan ya kulle mutum, ba sauran kuɓutarwa.15Duba, idan ya janye ruwaye, sai su bushe ƙurmus; kuma idan ya aika da su, sai su malale ƙasa.
16A gunsa ƙarfi da hikima suke; mutanen da aka ruɗe su da mai ruɗin dukkansu biyu suna cikin ikonsa.17Yakan ɓad da mashawarta zuwa baƙinciki, ya mai da alƙalai wawaye.18Yakan tuɓe rawanin iko daga sarakuna; ya ɗaura ɗan ƙyalle a kwankwasonsu.
19Yakan ɓad da firistoci su tafi ƙafa ba takalmi cikin baƙinciki ya kuma kaɓantar da manyan mutane.20Yakan ɗauke iya maganar mutanen da aka dogara gare su ya kuma ɗauke fahimtar dattawa.21Yakan zuba reni a kan hakimai ya kuma kwaɓe ɗamarar mutane masu ƙarfi.
22Yakan bayyana zurfafan abubuwan duhu ya kuma kawo baƙin duhu cikin haske.23Yakan sa al'ummai suyi ƙarfi, yakan kuma hallakasu; yakan faɗaɗa al'ummai, ya kuma bi da su kamar 'yan kurkuku.
24Yakan ɗauke fahimta daga shugabanin mutanen duniya; yasa su suyi ta yawo a jeji inda ba tafarki.25Suyi lalube cikin duhu babu haske; yakan sa suyi tangaɗi kamar bugaggen mutum.

13

1Duba, idona ya ga duk wannan; kunnena yaji ya kuma fahimce shi.2Abin da kuka sani, ni ma ina sane da shi; ni ban gaza ku ba.

3Duk da haka, na gwammace in yi magana da Mai Iko Dukka; ina so in tattauna da Allah.4Amma ku kuna lulluɓe gaskiya da ƙarereyi; ku dukka likitoci ne marasa amfani.5Kash, dama zaku yi shuru! Wannan zai zama maku hikima.
6Ku saurari nawa hujjojin; ku kasa kunne ga ƙarar tawa leɓunan.7Za ku yi magana marar adalci domin Allah, zaku kuma yi maganar munafunci dominsa?8Zaku nuna masa bambanci? Zaku yi jayayya domin Allah?
9Zai zama da kyau domin ku sa'ad da ya bincike ku? Zaku iya ruɗinsa kamar yadda zaku ruɗi mutane?10Hakika zai kwaɓe ku idan a ɓoye kuka nuna bambanci.
11Darajarsa ba zata firgita ku ba, tsoronsa kuma ya faɗo a kanku?12Batutuwanku masu daɗin ji misalai ne da aka yi su da toka; hanzarinku hanzari ne da aka yi su da yumɓu.
13Ku riƙe salamarku, ku kyale ni kawai, domin in yi magana, bari abin da zai auko kaina ya auko.14Zan sa namana a bakina; in ɗauki raina a hannuwana.15Bari mu gani, ko zai kashe ni, zan zama ba sauran bege; duk da haka, zan kare hanyoyina a gabansa.
16Wannan zai zama dalilin cetona, gama ba wani mugun mutum da zai zo gabansa.17Allah, ka kasa kunne ga furcina; bari furcina ya zo kunnuwanka.
18Duba yanzu, na shirya hanzarina sosai; na sani ba ni da aibu.19Wane ne wannan da zai yi jayayya gãba da ni a gaban sharia? Idan kun zo ne don ku yi, idan kun tabbatar da laifina, sai in yi shuru in saki raina.
20Allah, kayi mani abu biyu kawai, sa'an nan bazan boye kaina daga fuskarka ba:21ka janye hannunka mai azaba daga gare ni, kuma kada ka bari razanarka ta tsorata ni.22Sa'an nan ka kira ni, zan kuma amsa; ko kuma ka bari in yi magana da kai, kai ka amsa mani.
23Laifofina da zunubaina nawa ne? Bari in san kuskurena da zunubina.24Don me kake boye fuskarka daga gare ni ka maishe ni kamar maƙiyinka?25Zaka tsanantawa ganyen da iska ke kora? Zaka far wa tattaka?
26Domin ka rubuta abubuwa masu ɗaci gãba da ni; kasa in gãji laifofin ƙuruciyata.27Ka kuma sa ƙafafuna a turu; kana duba dukkan tafarkuna kurkusa; kana bincike inda sawayen ƙafafuna suka taka,28ko da yake ni kamar ruɓaɓɓen abu ne da yake lalacewa, kamar rigar da asu suka cinye.

14

1Mutum, da mace ta haifa, ya kan rayu 'yan kwanaki kaɗan yana kuma cike da damuwa.2Ya kan tsiro daga ƙasa kamar fure sai kuma a datse shi; ya tsere kamar inuwa baya daɗewa.3Kana duba kowanne su? Kana gabatar da ni a gaban shari'a tare da kai?

4Wane ne zai iya fitar da abu mai tsabta daga cikin marar tsabta? Babu ko ɗaya.5Kwanakin mutum a ƙayyade suke. Yawan watanninsa na tare da kai; ka ƙayyade masa iyaka da ba zai iya wucewa ba.6Ka ɗauke idonka daga gare shi domin ya huta, domin ya ji daɗin kwanansa kamar ɗan ƙwadago in ya iya.
7Mai yiwuwa ne itace na da bege; idan an sare shi, zai iya toho kuma, 'yan sabbin rassansa ba sa ɓata.8Ko da yake saiwoyinsa sun tsufa a ƙasa, kututturensa kuma ya mutu a ƙasa,9amma da zarar ya ji ƙanshin ruwa, sai yayi toho ya kuma fid da rassa kamar tsiro.
10Amma mutum yakan mutu; ya zama da rauni; hakika, mutum yakan bar yin numfashi, sa'an nan fa ina yake?11Kamar yadda ruwa ke ɓacewa a tafki, da yadda rafi ke rasa ruwa ya ƙone,12haka mutane ke kwantawa basa sake tashi. Sai ko in sammai sun ɓace, ba zasu farka ba ko kuma a tashe su daga barcinsu.
13Kash, dama zaka ɓoye ni can Lahira nesa da wahalhalu, ka kuma a ajiye ni a ɓoye har sai fushinka ya wuce, sai kasa mani lokaci da zan kasance a can sa'an nan ka tuna da ni!14Idan mutum ya mutu, zai sake rayyuwa kuma? Idan haka ne, zan so in jira dukkan lokacin gajiyata a can har sai 'yantarwata ta zo.
15Zaka kira, zan kuwa amsa maka. Zaka zama da marmarin aikin hannuwanka.16Zaka ƙididdige ka kuma lura da takawata; baza ka bi diddigin zunubina ba.17Za a ɗaure kurakuraina a jaka; zaka rufe laifofina.
18Amma har tsaunuka ma sukan faɗi su zama ba komai ba, harma duwatsu akan kawar da su daga wurinsu;19ruwaye sukan zaizaye duwatsu; ambaliyarsu na kwashe ƙurar ƙasa. Haka nan ne, kake hallakar da begen mutum.
20Kullum kana cin nasara a kansa, sai ya rasu; ka kan sauya fuskarsa ka aike shi ya mutu.21Idan an girmama 'ya'yansa maza, ba zai sani ba; ko kuma an wulaƙanta su, ba zai gani ba.22Yakan ji ciwon jikinsa ne kawai, yana kuma makokin domin kansa.

15

1Sa'an nan Elifaz Batemane ya amsa ya ce,2"Ya kamata mutum mai hikima ya amsa da ilimin banza kuma cika kansa da iskar gabas?3Koya kamata ya kawo hujja da magana marar amfani ko kuma furce furce waɗanda baza su amfana ba?

4Hakika, kana rushe bangirma ga Allah; kana hana sujada gare shi,5gama ƙuraƙuranka suna koya wa bakinka; ka zaɓa ka zama da harshen mutum mai wayo.6Bakinka da kansa ya kashe ka, ba nawa ba; hakika, leɓunanka suna shaida gãba da kai.
7Kai ne mutum na fari da aka haifa? An kawo ka cikin rayyuwa kafin tuddai ne?8Ko ka taɓa jin asirin ilimin Allah? Ka ɗauka kai kaɗai ke da hikima?9Me ka sani da bamu sani ba? Me ka fahimta da baya cikinmu muma?
10Tare da mu akwai masu furfura da tsoffi maza waɗanda suka girmi mahaifinka ainun.11Ta'aziyun Allah sun yi maka kaɗan ne, maganganu masu taushi zuwa gare ka?
12Don me zuciyarka take yaudarar ka? Me yasa ka ke ruwan idanu,13har ka mai da ruhunka gãba da Allah kana fitar da maganganu irin waɗannan daga bakinka?14Wane ne mutum da zai zama da tsarki? Waye shi wanda mace ce ta haife shi da zai zama da tsarki?
15Duba, Allah ba ya amincewa da tsarkakansa; hakika, sammai basu da tsarki a idanunsa;16ballantana wanda ya gaza a tsarki ƙazantacce lalatacce kuma, mutum wanda yake shan laifi kamar ruwa!
17Zan nuna maka; ka kasa kunne gare ni; zan yi maka shelar abubuwan da na gani,18abubuwan da masu hikima suka gãda daga ubanninsu, abubuwan da kakannisu basu ̀ɓoye ba.
19Waɗannan su ne kakanninsu, waɗanda su kaɗai aka ba ƙasar, wanda ba wani baƙo da ya taɓa ratsawa.20Mugun mutum yana murmurɗewa don zafin ciwo dukkan kwanakinsa, shekarun da aka aza wa a‌zalumi yasha azaba.‌21Ƙarar firgitarwa na cikin kunnuwansa; sa'ad da yake cikin wadata, mai hallakarwa zai auka masa.
22Baya tunani cewa zai komo daga cikin duhu; takobi na jiransa.23Sai ya tafi wurare da bam da ban domin abinci, yana cewa, 'Ina yake?' Ya sani ranar duhu ta gabato.24‌Ƙunci da raɗaɗi sukan tsoratar da shi; su ci nasara a kansa, kamar sarkin da ya shirya domin yaƙi.
25Domin ya miƙa hannunsa gãba da Allah, ya kuma nuna girman kai gãba da Mai Iko Dukka,26wannan mugun mutum yana gudu zuwa ga Allah da taurararriyar zuciya, da garkuwa kakkaura.
27Wannan gaskiya ne, ko da yake ya rufe fuskarsa da kitsensa ya kuma tara kitse a kwiɓinsa,28ya kuma zauna a rusassun birane; a gidajen da ba mazauna yanzu kuma suna shirye su zama tsibi.
29Ba zai yi arzaki ba; arzaƙinsa ba zai daɗe ba kuma mallakarsa baza ta yaɗu a ƙasar ba.30Ba zai fita daga duhu ba; harshen wuta zai ƙona karmaminsa; numfashi daga bakin Allah zai kora shi ya tafi..
31Kada ya dogara ga abubuwa marasa amfani, yana ruɗin kansa; gama abubuwa marasa amfani zasu zama ladansa.32Zai faru kafin lokacin mutuwarsa yazo; reshensa ba zai zama kore ba.33Zai kakkaɓe ɗanyun inabinsa kamar kuringar inabi; zai zubar da furanninta kamar itacen zaitun.
34Gama tawagar marasa tsoron Allah ba zasu zama da zuriya ba; wuta zata cinye rumfar masu cin hanci.35Sukan ɗauki cikin ƙeta su haifi zunubi; mahaifarsu na ɗaukar cikin rikirkicewa.

16

1Sa'an nan Ayuba ya amsa yace,2"Na sha jin abubuwa da yawa kamar haka; ku dukka masu ta'aziyar ma abin ban tausai ne.3Maganganu marasa amfani basu da ƙarshe ne? Me ya dame ku da kuke amsawa haka?

4Nima zan iya magana kamar yadda kuke yi, in da kuna gurbina; zan iya tattara maganganu in haɗa su tare gãba da ku kuma in girgiza kaina a gabanku don reni.5Zan ƙarfafa ku da bakina, ƙaɗawar leɓunana zasu kawo maku sauƙi.
6Idan na yi magana wannan ba zai sauƙaƙe baƙincikina ba; idan na yi shiru, ƙaƙa wannan zai taimake ni?7Amma yanzu, Allah, ka sani na gaji; ka mai da dukkan iyali na wofi.8Ka sa na ƙeƙashe, wannan ma shaida ce gãba da ni; ƙeƙashewar jikina ya tashi gãba da ni, yana kuma shaida gãba da ni a fuskata.
9Allah ya kekketa ni cikin hasalarsa ya kuma tsananta mani; Yana tauna haƙoransa cikin zafin fushi; magabcina ya kafa idanunsa a kaina sa'ad da ya kekketa ni.10Mutane sun buɗe bakinsu suna mani gwalo; sun buge ni ba dalili a kunci; sun taru gaba ɗaya gãba da ni.
11Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefar da ni cikin hannun mugayen mutane.12Ina zaune lau, sai ya kakkarya ni. Hakika, ya kama ni a wuya ya jefar ya jefar da ni gutsu-gutsu; ya kuma tsai da ni daf a gabansa.
13Maharbansa dukka sun kewaye ni; Allah ya sossoke ka'idojina bai yi mani rangwame ba; ya zubar da matsarmamata a ƙasa.14Yana bubbuga bangona akai akai; yana gudu a kaina kamar mayaƙi.
15Na ɗaura tsumma a fatata; na soka ƙaho na cikin ƙasa.16Fuskata tayi jawur da kuka; a kan girata akwai inuwar mutuwa17ko da yake ba ta'addanci a hannuwana, addu'ata mai tsarki ce.
18‌Ƙasa, kada ki rufe jinina; kada kukana ya sami wurin hutawa.19Ko yanzu ma, duba, shaidata tana cikin sama; wanda yake lamuni domina yana sama.
20Abokaina suna yi mani ba'a, amma idona yana zubar da hawaye ga Allah.21Ina roƙo domin wannan mashaidi a cikin sama yayi muhauwara da Allah kamar yadda mutum zai yi da makwabcinsa!22Domin bayan 'yan shekaru sun wuce, zan tafi wurin da bazan komowa daga can ba.

17

1An cinye ruhuna, kwanakina sun ƙare; kabari na shirye domina.2Lallai da akwai masu ba' a tare da ni; idona dole kullum ya ga cakunar su.3Ka bani shaida, kayi mani lamuni da kanka; wane ne kuma ke nan da zai taimake ni?

4Domin kai, Allah, ka hana wa zuciyarsu fahimta; saboda haka, ba zaka ɗaukaka su a bisa na ba.5Wanda yaci amanar abokansa domin ya sami lada, idanun 'ya'yansa zasu dushe.
6Amma ya maishe ni abin karin magana ga mutane; suna tofa mani miyau a fuska.7Idona ya sace saboda baƙin ciki; dukkan gaɓaɓuwan jikina sun ƙanjame kamar inuwa.8Mutane masu adalci zasu yi mamaki da wannan; mutum marar aibu zai husata kansa gãba da mugayen mutane.
9Mutum mai adalci zai kiyaye hanyarsa; wanda ya ke da hannuwa mararsa laifi zai yi ta ƙaruwa da ƙarfi.10Amma game da dukkanku, kuzo yanzu; ba zan sami wani mai hikima a cikinku ba.
11Shekaruna sun wuce; shirye shiryena sun watse, haka kuma marmarin zuciyata.12Waɗannan mutane, waɗannan masu reni, suna sauya dare zuwa rana; haske ya fi kusa da duhu.
13Idan gidan da nake bege Lahira ne kaɗai; idan na baza shimfiɗata cikin duhu;14idan kuma na cewa rami, 'Kai ne mahaifina,' da kuma tsutsa, 'Ke ce mahaifiyata ko kuma 'yar'uwata,'15to ina begena ya ke? A game da begena, wa ya iya ganin ko da ɗan kaɗan?
16Bege zai tafi tare da ni zuwa ƙofar Lahira ne sa'ad da zamu gangara cikin turɓaya?

18

1Sai Bildad Bashune ya amsa ya ce,2"Shin yaushe zaka dena maganarka? Kayi tunani, daga bayan haka zamu yi magana.

3Don me za a ɗauke mu dabbobi, marasa wayo a ganinka?4Kai da ka ke yayyage kanka a cikin fushinka, ya kamata a kawar da duniya domin ka ko kuma ya kamata a tumbuƙe duwatsu daga wurarensu?
5Hakika, za a ɓice hasken mugun mutum; tarwatsun wutarsa ba za ta haskaka ba.6Haske zai zama duhu a rumfarsa; fitilar da ke bisansa za a ɓice ta.
7Takawar ƙarfinsa zata ragu; shirye shiryen kansa zasu kada shi.8Gama za a jefa shi cikin raga da ƙafarsa; zai yi tafiya zuwa cikin tarko.
9Tarko zai kama diddigensa; ashibta zata riƙe shi.10An binne masa igiyar zarmewa a ƙasa a ɓoye; tarko ne dominsa akan hanya.11Banrazana zai sa shi tsoro a kowanne gefe; zasu fafari digadigansa.
12Arzikinsa zai juya ya zama yunwa, kuma masifa na shirye a gefensa.13Gaɓaɓuwan jikinsa zasu mutu; hakika, ɗan farin mutuwa zai ci gaɓaɓuwansa.
14Za a fizge shi daga rumfarsa da yake zaune lafiya a kora shi zuwa ga sarkin razanai.15Mutanen da ba nasa ba zasu zauna a rumfarsa bayan da suka ga wutar ƙibiritu ta bazu cikin gidansa.
16Saiwowinsa zasu bushe daga ƙasa; a sama za a daddatse rassansa.17Ba sauran tunawa da shi a duniya; ba zai sami suna a titi ba.
18Za a kora shi daga haske zuwa cikin duhu kuma za a kore shi daga wannan duniya.19Ba zai zama da ɗa namiji ko jikoki maza a cikin mutanensa ba, ko ragowar dangi inda dã ya zauna.20Waɗanda ke zaune a kudu zasu tsorata da abin da ya faru da shi wata rana; waɗanda ke zaune a gabas zasu firgita da wannan.
21Tabbas haka gidan marasa adalci yake, wuraren waɗanda basu san Allah ba."

19

1Sai Ayuba ya amsa ya ce,2"Har yaushe zaku sa ni cikin wahala kuma ku daddatse ni gutsu gutsu da maganganu?

3Sau goma ɗin nan kun zarge ni; baku ji kunya ba cewa kun wulaƙanta ni ainun.4Idan lallai gaskiya ne nayi kuskure, to kuskurena ya zama abin da ni kaina zan yi tunani sa.
5Idan hakika zaku ɗaukaka kanku fiye da ni ku kuma yi amfani da ƙasƙancina gãba da ni,6sai ku sani Allah bai yi mani dai-dai ba ya kuma kama ni cikin ragarsa.
7Duba, na ƙwala ihu, "Ta'adanci!" amma ban sami amsa ba. Na yi kira domin neman taimako, amma babu adalci.8Yasa katanga a hanyata domin kada in iya wucewa, ya kuma sa duhu a tafarkina.9Ya tuɓe mani darajata, ya kuma ɗauke kambi daga kaina.
10Ya kakkarya ni ta kowanne gefe, na kuma ƙare; ya janye begena kamar itace.11Ya kuma kunna wutar hasalarsa gãba da ni; ya maishe ni ɗaya daga cikin abokan gabarsa.12Rundunarsa sun tashi gaba ɗaya; sun tula tsibin shara gãba da ni kuma sun kewaye rumfata.
13Ya nisantar da 'yan'uwana maza daga gare ni; sanin idona an ware su gaba ɗaya daga gare ni.14Dangina sun yashe ni; aminaina na kurkusa sun manta da ni.
15Waɗanda dã na saukar baƙi a gidana da barorina mata sun maishe ni kamar baƙo; ni bare ne a idanunnunsu.16Na kira barana, amma bai ba ni amsa ba ko da yake na roƙe shi da bakina.
17Numfashina ya dunguri matata; har ta maishe ni abin watsi ga waɗanda mahaifiyarmu ɗaya.18Har ma 'yan yara ƙanana sun rena ni; idan na tashi zan yi magana, sai suyi magana gãba da ni.19Dukkan idon sani abokanaina sun kyamace ni; Waɗanda nake ƙauna suna gãba da ni.
20‌Ƙasusuwana sun manne wa fatata da kuma naman jikina; ina raye da ƙyar.21Ku ji tausayina, ku ji tausayi na, abokaina, gama hannun Allah ya taɓa ni.22Me yasa kuke farautata kamar yadda Allah ke yi? Zaku taɓa ƙoshi da naman jikina?
23Kash, da ma za a rubuta maganganuna! Aiya, dama za a rubuta su a cikin littafi!24Kash, dama da alƙalamin ƙarfe da tamã aka sassaƙa rubutun akan dutse har abada!
25Amma a gare ni, na sani mai fansata yana raye, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya;26bayan fatata, watau, wannan jiki, an hallaka shi, sa'an nan a cikin jiki zan ga Allah.27Zan gan shi da idanuna-ni, ba kuma wani da bam ba. Zuciyata ta karai a cikina.
28Idan kun ce, 'Yaya zamu tsananta masa! Tushen matsalarsa tana cikinsa,'29sai ku ji tsoron takobi, domin hasala na kawo hukuncin takobi, domin ku sani a kwai shari'a."

20

1Sa'an nan Zofar Banamate ya amsa ya ce,2"Tunane tunanena suna sa ni in amsa da garaje saboda damuwar da ke cikina.3Ina jin zargi da ke kunyatar da ni, amma wani ruhu daga fahimtata yana amsa mani.

4Baka san wannan abu tun daga zamanan dã ba, da Allah ya ajiye mutum a duniya:5cin nasarar mugun mutum na gajeren lokaci ne, kuma murnar marar tsoron Allah daɗewarta kamar ƙiftawar ido ne?
6Ko da tsayinsa ya kai sammai, kuma kansa ya taɓa gizagizai,7duk da haka irin mutumin nan zai lalace tuttur kamar najasarsa; waɗanda suka gan shi zasu ce, 'Ina yake?'
8Zai yi firiya ya ɓace kamar mafarki ba za a kuma same shi ba; hakika, za a fafare shi kamar wahayin dare.9Idon da ya ganshi ba zai ƙara ganin sa ba; mazauninsa ba zai ƙara ganinsa ba.
10'Ya'yansa zasu roƙi gafarar matatalauta; hannuwansa zasu mayar da dukiyarsa.11‌Ƙasusuwansa suna cike da ƙarfin ƙuruciya, amma zai kwanta tare da shi cikin turɓaya.
12Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa, ko da yake ya ɓoye shi ƙarƙashin harshensa,13ko da yake ya riƙe shi a can bai bari ya fita ba amma ya riƙe ya gama cikin bakinsa -14abincin da ke cikin hanjinsa zai juya ya zama da ɗaci; ya zama dafin maciji a cikinsa.
15Yakan haɗiye arziki, amma sai ya haras da su kuma; Allah zai tutturo su waje daga cikinsa.16Zai sha dafin maciji; harshen kububuwa zai kashe shi.
17Ba zai ji daɗin rafuffuka ba, yalwar zuma da madara.18Zai mayar da rabon wahalar aikinsa kuma ba zai iya ya cin sa ba; ba zai ji daɗin dukiyar da ya samu ta wurin cinikaiyarsa ba.19Gama ya wulaƙanta matalauta ya kuma yashe su; ya ƙwace gidajen da bai gina ba ƙarfi da yaji.
20Domin bai san ƙoshi ba, ba zai iya tanada wani abin da yake marmari ba.21Ba wani abin da ya rage da bai cinye shi ba; saboda haka arzikinsa ba zai daɗe ba.22A cikin yalwar wadatarsa zai faɗa cikin wahala; hannun kowanne matalauci zai yi tsayayya da shi.
23Sa'ad da yake gaf da cika cikinsa, Allah zai jeho masa fushinsa mai ƙuna a kansa; Allah zai kwararo masa shi sa'ad da yake cin abinci.24Ko da yake mutumin nan ya guje wa makamin ƙarfe, bakan tagulla zai harbe shi.25Idan ya cire shi a bayansa sai bakin mai tsini ya shiga hantarsa. Razana zata faɗo masa.
26Duhu ne baƙi ƙirin ke ajiye domin kayansa masu daraja; wutar da ba a izawa zata cinye shi; zata cinye ragowar abin da ke rumfarsa.27Sammai zasu bayyana zunubansa, ƙasa kuma zata miƙe gãba da shi ta zama shaida.
28Dukiyar gidansa zata ɓace; kayayyakinsa zasu gudu a ranar hasalar Allah.29Wannan shi ne rabon mugu daga Allah, gadon da Allah ya ajiye masa kenan."

21

1Sai Ayuba ya amsa ya ce,2"Ku kasa kunne da kyau ga maganganuna, kuma bari wannan ya zama ta'aziyar da kuke yi mani.3Ku daure da ni, ni kuma zan yi magana; bayan nayi magana, sai ku cigaba da ba'a.

4Ni dai kam, ƙarata ga mutum ne? Don mene ne bazan yi rashin haƙuri ba?5Ku duba ni kuyi mamaki, ku ɗibiya hannuku a kan bakinku.6Sa'ad da nayi tunani akan wahaluna, nakan tsorata, makyarkyata sai ta kama jikina.
7Me yasa mugayen mutane suke a rayuwa, su tsufa, su girma su ƙasaita a iko?8Zuriyarsu ta kafu tare da su a kan idanunsu, kuma jikokinsu su da su a idanunsu.9Gidajensu lafiya ba tsoro; kuma babu hukuncin Allah a kansu.
10Bijiminsu na barbara; baya fasa yi; shanunsu suna haifuwa basa yin ɓarin 'yan maruƙansu'11Sukan aika da 'yan maruƙansu kamar garke, 'ya'yansu suna rawa.12Suna waƙa da kuge da molo kuma suna farinciki da waƙar sarewa.
13Suna zaman kwanakinsu cikin wadata, su gangara shuru zuwa Lahira.14Sai su cewa Allah, 'Ka rabu da mu domin ba ma son wani fahimta game da hanyoyinka.15Wanene Mai Iko Dukka, da zamu yi masa sujada? Wace riba ce zamu samu idan muka yi addu'a gare shi?'
16Duba, arzikinsu ba a hannunsu yake ba? Ba ruwana da shawarar mugayen mutane.17Sau nawa fitilar mugayen mutane ana hure ta, ko kuma masifarsu ta auka masu? Sau nawa yakan faru sai Allah ya rarraba ma su baƙin ciki cikin fushinsa?18Sau nawa su ke zama kamar tattaka cikn iska ko kamar ƙaiƙai da iskar hadari ke kwashewa.
19Kun ce, 'Allah yana tara alhakin mutum domin 'ya'yansa su biya.' Bari shi da kansa ya biya, domin ya san laifinsa.20Bari idanunsa su ga hallakarsa, kuma bari ya sha hasalar Mai Iko Dukka.21Gama me ya dame shi da iyalinsa da ya bari bayan an datse kwanakinsa?
22Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da shima yana shari'anta har waɗanda suke sama?23Wani mutum yakan mutu cikin goshin ƙarfinsa, ya yi shuru a natse.24Jikinsa na cike da madara, kuma ɓargon ƙashinsa da danshi.
25Wani mutum kuma ya mutu cikin ɓacin zuciya, wanda bai taɓa ɗanɗana wani abin kirki ba.26Dukkan su sukan kwanta a cikin turɓaya; tsutsotsi su mamayesu.
27Duba, na san tunaninku, kuma da hanyoyin da ku ke so ku aibata ni.28Domin kun ce, 'Ina yanzu gidan ɗan sarki? Ina rumfar da mugun mutumin nan ya zauna a ciki?'
29Baku taɓa tambayar mutane matafiya ba? Ko ba ku san shaidar da zasu iya faɗi ba,30cewa mugun mutum an keɓe shi daga ranar masifa, an kuma janye shi daga ranar hasala?
31Wane ne zai zargi hanyoyin mugun mutum a fuskarsa? Wane ne zai sãka masa domin abin da ya yi?32Duk da haka za a kai shi kabari; mutane zasu yi ta kiyaye kushewarsa.33‌Ƙurar kabarinsa da aka tula a kansa zata zama masa da daɗi; dukkan mutane za su bi bayansa, kamar yadda mutanen ba su ƙidayuwa sun sha gabansa.
34To ƙaƙa zaku ta'azantar da ni da rashin hankali, tun da cikin amsoshinku babu komai sai ƙarairayi?"

22

1Sai Elifaz Batemane ya amsa, yace,2"Mutum zai zama da amfani ga Allah? Mutum mai wayau zai zama da amfani ga gare shi?3Zai zama da jin daɗi ga Mai Iko idan ka zama mai adalci? Zai zama da wata riba gare shi idan hanyoyinsa marasa laifi ne?

4Ai ba domin kana tsoronsa ba ne ya kwaɓe ka, ko kuma ka ɗauki shari'a?5Ba babbar muguntarka ba ce? Ashe babu ƙarshen muguntarka?
6Domin ka bukaci a ba ka bashin da ke daga wurin ɗan'uwanka ba tare da wani dalili ba, ka kuma ƙwace tufafi daga wurin wanda ba shi da komai.7Ka hana ruwa ga mutane masu ƙishinruwa su sha; ka hana abinci ga mutane masu jin yunwa8ko da ya ke kai mutum ne mai iko, kana da kayan duniya, ko da ya ke kai, mutum ne mai girma, kana rayuw a cikinta.
9Ka kori mata da mazajensu suka mutu ba tare da komai ba; hannuwan marayu sun karye.10Saboda haka, ramummuka a ko'ina kewaye da kai, sun kuma kawo maka tsoron damuwa.11Akwai duhu, saboda har baza ka iya gani ba; ruwaye masu yawa sun sha kanka.
12Ashe Allah ba a saman sammai yake ba? Dubi taurare a sama, yaya nesan su a can!13Kace, 'Me Allah ya sani? Zai iya shari'a a cikin baƙin duhu?14Gizagizai masu duhu sune ke rufe shi, saboda haka ba ya ganin mu; yana tafiya a kan iyakar sararin sama.'
15Kana bin tsohowar hanyar da mugayen mutane suke tafiya a kai--16waɗanda aka ƙwace kafin lokacinsu, waɗanda tuwasunsu suka shafe kamar rafi,17sune waɗanda suka ce da Allah, 'Tafi daga wurin mu,' su ne suka ce, 'Mene ne Mai Iko zai yi da mu?'
18Duk da haka ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, shirye-shiryen mugayen mutane suna nesa daga gare ni.19Adalan mutane su na ganin kaddararsu suna murna; mutane marasa laifi kuma suna dariyarsu.20Sun ce, 'Babu shakka waɗanda suka taso gãba da mu an yanke su, wuta kuwa ta lashe mallakarsu.'
21Yanzu ka yarda da Allah salama ta kasance tare da kai; ta wannan hanya, abu mai kyau zai zo gare ka.22Karɓi, ina rokon ka, ka koya daga bakinsa; ka riƙe kalmominsa a zuciyarka.
23Idan zaka juyo ga Mai Iko, za a sake gina ka, idan za ka ajiye rashin adalci nesa daga gidanka.24Ka ajiye dukiyarka can cikin ƙura, zinariya daga ofir a cikin duwatsun rafuffuka,25Mai Iko zai zama dukiyarka, da azurfa mai daraja ga gare ka.
26Sa'an nan zaka sami farin ciki a wurin Mai Iko, za ka tada fuskarka ga Allah.27Za ka yi addu'a gare shi, shi kuma zai ji ka; zaka kiyaye alkawaran da ka yi masa.28Za ka kuma hurta komai, za a kuma tabbatar maka, haske zai haskaka a hanyoyinka.
29Allah yakan ƙasƙantar da mutum mai girmankai, yakan ceci mai tawali'u.30Zai ceci kowane mutum wanda ke da laifi; wanda za a ceta ta wurin abin da hannuwansa ke yi dai-dai."

23

1Sai Ayuba amsa ya ce,2"Har yau ƙarata nada zafi, hannuna yayi nauyi saboda gunagunina.

3Oh, dama na san inda zan same shi! Oh, da sai in tafi wurinsa!4Da zan kai ƙarata a gabansa, da na cika bakina da muhawara.5Zan koyi kalmomi waɗanda zaya amsa mani, yadda zan san abin da zai ce da ni.
6Zaya yi gardamar gãba da ni duk da ƙarfin ikonsa? A'a, zai saurare ni.7Akwai amintaccen mutum da zai yi gardama da shi. Ta wannan hanyar zan tabbatar da aminci har abada ta wurin shari'a ta.
8Duba, na tafi gabashi, amma baya can, yammaci, amma ban same shi ba.9A arewa, a wurin yake aiki, duk da haka ban gan shi ba, a kudu, a wurin ya ɓoye kansa domin kada in gan shi.
10Gama ya san hanyar da na ɗauka; ya jarraba ni, zan fito kamar zinariya.11Ƙafata tana bin sawun ƙafarsa; ina bin hanyarsa ban kuma kauce wani gefen ba.12Ban kuma koma da baya ba daga umarnin leɓunansa; na ajiye kalmomin baƙinsa sun zama abinci na.
13Gama yana ɗaya daga cikin masu kirki, wa zai iya juyar da shi? Abin da yake so ya aikata.14Gama ya ɗauki ka'ida gãba da ni; akwai da yawa kamar su.
15Saboda haka, ina rawar jiki a gabansa; duk lokacin da nake tunani a kansa.16Domin Allah ya sa zuciyata tayi sanyi; Mai Iko ya tsorata ni.17Amma duhu bai kawo ni ƙarshe ba, ko da yake baƙin duhu ya rufe mani fuskata.

24

1Meyasa Mai Iko bai tsaida lokatan shari'ar mugayen mutane ba? Meyasa bai tsayar wa waɗanda suke adalai ga Allah suga kwanakinsa na shari'a ya zo?

2Akwai mugayen mutane da yawa da suke kawar da iyaka; akwai mugayen mutane waɗanda suke ɗaukan garke da tsiya su zuba cikin makiyayarsu.3Sukan saci jakin marayu; su kama takarkarin gwauruwa a matsayin jingina.4Sukan tilastawa mutane masu bukata su bar masu hanya; mutane matalauta na ƙasa dukka su ɓoye kansu daga gare su.
5Duba, waɗannan mutane matalauta su fita daga wurin ayyukansu kamar jakunan daji a jeji, suna bi hankali su na neman abinci; me yiwuwa Arabah zai ba su abinci domin 'ya'yansu.6Matalautan mutane na girbi da dare a gonakin wasu mutanen, su na tattara 'ya'yan inabi daga gonakin waɗannan mugayen mutanen.7Su na kwance tsirara dukkan dare ba tare da tufa ba, basu da abin da zai hana su jin sanyi.
8Suna jike sharkaf da ruwa da ke kwararowa daga kan duwatsu; suna kwance kusa da manyan duwatsu domin basu da mafaka.9Akwai mugayen mutane waɗanda suke figar marayu daga nonon iyayansu mata, mugayen mutane waɗanda suke ɗaukan yara a matsayin jingina daga matalautan mutane.10Amma matalautan mutane suna tafiya babu kaya a jikinsu; suna tafiya da yunwa, suna ɗauke da damunan hatsi na waɗansu mutane.
11Matalautan mutane na matse mai a katangar mugayen mutane; suna kuma matsar ruwan inabin mugayen mutane, amma su da kansu suna fama da ƙishi.12Daga cikin birni ana jin nishin masu mutuwa, makogwaron masu rauni na kukan neman taimako. Amma Allah bai kula da masu laifin ba.
13Wasu daga cikin waɗannan mugayen mutanen suna ƙin haske; basu san hanyarsa ba, ko su tsaya a hanyarsa.14Kafin hasken rana mai kisankai yakan fita ya kashe matalauci da mutane masu bukata; da dare kuma ya kan zama kamar ɓarawo.
15Har yau, idon mazinaci yakan jira sai da magariba; ya faɗa, 'Babu idon da zai gan ni.' Yana ɓoye fuskarsa.16A cikin duhu mugayen mutane sukan kutsa kai cikin gidaje; amma suna ɓoye kansu da rana; basu damu da haske ba.17Gama dukkan su, mattsanancin duhu ne kamar duhun safiya; domin su abokan "yan ta'addar baƙin duhu ne.
18Suna wucewa da sauri, duk da haka, kamar kumfa a kan fuskar ruwaye; ƙasar da suka mallaka an la'anta ta; babu wanda zai tafi yayi aiki a cikin gonar inabi.19Kamar dusar ƙanƙara take narkewa, iska mai laima cikin ruwaye, haka Lahira ke ɗaukan waɗanda suka yi zunubi.
20Cikin da ya haife shi ba zai tuna da shi ba; macijin ciki zai ji daɗin ƙoshi a kansa; ba za a ƙara tunawa da shi ba; ta wannan hanya, miyagu zasu lalace kamar itace.21Mugun da ya lanƙwame matan da basu haifi yara ba; bai kuma nuna alheri ga matar da ke gwauruwa ba.
22Duk da haka Allah yakan ja mutane masu iko ta wurin ikonsa; yakan ɗaga ya kuma hana su ƙarfi a rayuwarsu.23Allah ya kan bar su da tunanin sun tsira, suna murna a kan haka, amma idanuwansa na kan hanyoyinsu.
24An ɗaukaka waɗannan mutane; a ɗan lokaci kaɗan, zasu ɓace; za a ƙasƙantar da su; za a tattara su wuri ɗaya kamar sauran; za a hallaka su kamar karan dawa da aka yanke.25Idan ba haka ba, wane ne ya tabbatar ni maƙaryaci ne; wa zai ce kalmomina ba gaskiya ba ne?"

25

1Sai Bildad Bashune ya amsa ya ce,2"Mulki da tsoro suna tare da shi, yayi samaniya wurarensa.3Akwai ƙarshen jimilar yawan sojojinsa? A kan wane ne haskensa yaƙi haskakawa?

4Yaya mutum zai zama adali tare da Allah? Yaya shi wanda mace ta haifa zai zama da tsabta, ƙarɓaɓɓe gare shi?5Duba, ko da wata bashi da haske gare shi, taurari ma basu da tsarki a gabansa.6Yaya kuma mutum, wanda aka haifa--ɗan mutum, wanda aka haife shi!"

26

1Sai Ayuba ya amsa ya ce,2"Yaya ka taimakawa wanda bashi da ƙarfi! Ka cece hannun da bashi da ƙarfi!3Yaya kake ba wanda bashi da hikima shawara, kana sanar da amon ilimi!4Ta wurin wa ka sami taimako ka ke yin maganar waɗannan kalmomi? Wanne ruhu ne ya fito daga gare ka?

5Matattu suna rawar jiki, su waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukkan waɗanda su ke zama da su.6Lahira ta na tsirara gaban Allah; hallakarwa da ke kanta ba rufe take ba a gare shi.
7Ya shimfiɗa arewa a sarari a kan abin da ke fili, ya rataya duniya ba bisa kan kome ba.8Ya ɗaure ruwaye a gizagizai, amma gizagizan ba a ƙarƙashinsu suke ba.
9Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa girgije a kanta.10Ya zana kewayanta a kan iyakar fuskar ruwaye kamar layi tsakanin haske da duhu.
11Ginshiƙan samaniya sun girgiza, sun firgice sakamakon tsautawarsa.12Ta wurin ƙarfinsa ya kwantar da teku; ta wurin saninsa ya hallakar da Rahab.
13Ta wurin numfashinsa yasa sararin sama yayi garau; da hannunsa ya sha zarar macijin nan mai gudu.14Duba, amma waɗannan su ne yatsun hanyoyinsa; yaya ƙanƙantar raɗa da muke ji a gare shi! Wane ne ya gane tsawar ikonsa?"

27

1Ayuba ya fara magana, ya ce,2"Yadda Allah na raye, wanda ya ɗauke mani adalci, Mai Iko, wanda yasa rayuwata ɗaci,3har yanzu raina baya tare da ni, numfashi daga Allah ya cika hancina, wannan shi ne abin da zan yi.

4Leɓena ba zai faɗi mugunta ba, ko harshena ya hurta maganganun yaudara;5ba zan taɓa yarda cewa ku ukun kun yi dai-dai ba; har in mutu ba zan daina tsare mutuncina ba.
6Ina rike da adalcina ba kuwa zan sake shi ba ya tafi; tunanina ba zai zarge ni ba idan dai ina raye.7Bari maƙiyina ya zama kamar mugun mutum; bari wanda ya ke gãba da ni ya zama kamar mutum marar adalci.
8Gama wacce sa zuciya ke ga mutum marar tsoron Allah sa'ad da Allah ya datse shi, sa'ad da Allah ya ɗauke ransa?9Allah kuwa zai ji kukansa a lokacin da wahala ta same shi?10Zai yi farinciki da kansa a wurin Mai Iko, zai yi kira ga Allah a dukkan lokatai?
11Zan koya maka game da hannun Allah; ba zan ɓoye tunanin Mai Iko ba.12Duba, dukkan ku kun ga wannan da kanku; me yasa kuke yin wannan magana ta wawanci?
13Wannan shi ne rabon mugun mutum a wurin Allah, gãdo ne kuma wanda azzalumi zai karɓa daga wurin Mai Iko:14Idan 'ya'yansa sun riɓamɓanya, zasu zama rabon takobi; zuriyarsa kuwa ba zata sami isasshen abinci ba.
15Duk wanda ya tsira za a bizne shi da annoba, gwaurayensu ba zasu yi makoki domin su ba.16Ko da yake mugun mutum ya tsibe azurfa kamar turɓaya, tarin tufafi kamar laka,17zai iya tara tufafi, amma adalan mutane zasu zuba a kai, mutanen kirki zasu raba azurfar a tsakaninsu.
18Ya gina gidansa kamar saƙar gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.19Ya kwanta a gadon mai arzaki, amma ba zai ci gaba da yin haka ba, zai buɗe idanunsa, yaga komai ya tafi.
20Razana zata auko masa kamar ruwaye; iska zata tafi da shi da dare.21Iskar gabas zata fyauce shi, zai tashi; zata share shi daga wurinsa.
22Zata jefar da kanta a kansa, babu tsayawa; zai yi ƙoƙari ya tsere daga hannunsa.23Zata tafa hannuwanta a kansa domin ba'a; zata yi masa ƙara daga wurinsa.

28

1Babu shakka akwai ma'adani na azurfa, a wurin da ake tace zinarya.2Ana samun ƙarfe daga cikin ƙasa; a kuma narkar da tagulla daga dutse.

3Mutum ya kan kawar da duhu, ya kuma bincike zuzzurfar iyaka, ya haƙo duwatsun a lunguna masu sulɓi da ke cikin duhu baƙi ƙirin.4Ya kan buɗe ƙyaure daga wurin da mutane ke zama, wuraren da ƙafar wani ba zata manta ba. Yakan kafa abin lilo nesa da mutane; yayi ta lilo zuwa da komawa.
5Daga cikin ƙasa ake samun abinci, takan juyo ƙarƙashinta kamar ta wurin wuta.6Duwatsu ne wurin da ke samun shudin yakutu, zinariya ɗauke da ƙurarta.
7Tsuntsu mai cin nama bai san hanyarta ba, shaho ma da idanuwansa bai ganta ba.8Namomi masu fahariya basu taɓa bin irin hanyar ba, ko zaki mai zafi ma bai taɓa wucewa can ba.
9Mutum yasa hannunsa a kan ƙanƙarar dutse, yana kuma iya tunɓuke tushen duwatsun daga saiwoyinsu.10Yana kuma iya sarar magudanar ruwa cikin duwatsu; idannunsa kan ga kowanne abu mai daraja a can.11Yana iya datse rafuffuka ya hana su gudu; ya binciko abin da ke ɓoye a can ya kawo shi a sarari.
12Daga ina za a samo hikima? Ina ne wurin haziƙanci?13Mutum bai san darajarta ba; ko a samo ta a ƙasar masu rai.14Zurfafan ruwaye a ƙarƙashin ƙasa sun ce, 'Bata cikina,' teku ta faɗa, 'Bata tare da ni.'
15Ba zata iya samuwa daga zinariya ba; ko azurfa bata yi nauyi kamar tamaninta ba.16Ba zata yi kimanin zinariyar Ofir, tare da darajar baƙin dutse mai daraja ba ko saffir.17Zinariya da madubi ba zasu yi dai-dai da tamaninta ba; ko kuma a musanyata da murjanin da aka yi da zinariya mai kyau.
18Kada ma a ambaci darajar murjani ko dutse mai walkiya; lallai tamanin hikima yafi shi.19Duwatsu masu darajar Kush ba za a dai-dai su da tamaninta ba; ko kuma darajar tamaninta yafi na zinariya tsantsa.
20Daga ina hikima take fitowa? A wanne wuri kuma hazaƙa take?21Hikima a ɓoye take daga idon dukkan abubuwa masu rayuwa, haka nan yake a ɓoye ga tsuntsaye da ke tashi a sammai.22Hallaka da mutuwa sun ce, 'Mun ji ƙishin-ƙishin a kanta a kunnuwanmu.'
23Allah ya fahimci hanyar zuwa gare ta; ya san wurinta.24Saboda yana ganin ƙarshen duniya, yana duban ƙarƙashin dukkan sammai.25Yasa iska mai ƙarfi da ƙunshi daga ciki ta wurin auna ruwaye.
26Yayi ka'ida domin ruwan sama da hanya domin tsawa.27Sai ya ga hikima, ya sanar da ita; ya tabbatar da ita; ya gwada ta.28Ga mutane yace, 'Duba, tsoron Ubangiji -- shi ne hikima; rabuwa daga mugunta kuma ita ce hazaƙa.'"

29

1Ayuba yaci gaba da magana yace,2"Oh, dama ina ma yadda nake a watanin da suka wuce ne? lokacin da Allah yake lura da ni,3sa'ad da fitilarsa take haska mani kai, da kuma lokacin da nake tafiya cikin duhu ta wurin haskensa.

4Kash, dãma na tsaya yadda nake cikakke a kwanakina, sa'ad da abokantaka da Allah ke kan gidana,5lokacin da Mai Iko ke tare da ni, 'ya'yana ke kewaye ni,6sa'ad da aka rufe hanyata da madara, duwatsu kuma na fito mani da rafuffukan mai!
7A lokacin da nakan fito ƙofar birni, sa'ad da na zauna a wurin zamana a dandali,8da samari sukan gan ni, sai su kawar da kansu daga gare ni don girmamawa, tsofaffi mutane kuma su miƙe tsaye domi na.
9Sarakuna na yin shiru da magana sa'ad da nazo; sai su ɗora hannuwansu a kan bakinsu.10Muryoyin manyan mutane sun yi tsit, harshensu ya liƙe a dasashin bakunansu.
11Gama bayan da kunnuwansu suka ji ni, sai su albarkace ni; bayan da idanuwansu suka gan ni, sai su ba da shaida a kaina su kuma amince da ni12domin nakan ceci duk matalauci sa'ad da yayi kuka, da kuma wanda bashi da uba kuma bashi da wanda zai taimake shi.13Albarka ga wanda yake bakin mutuwa idan yazo gare ni; nakan sa zuciyar gwauraye ta yi waƙar murna.
14Na sa sutura ta adalci, ta rufe ni; gaskiyata ita ce kamar suturata da rawanina.15Ni ne idon makafin mutane; ni ne ƙafaffun guragun mutane.16Ni mahaifi ne ga mutane masu bukata; nakan yi bincike don in warware al'amari harma wanda ban san shi ba.
17Nakan karya muƙamuƙan mutum marar adalci; in fisge wanda aka zalunta daga cikin tsakanin haƙoransa.18Sa'an nan nace, 'Zan mutu cikin gidana; zan riɓaɓɓanya kwanakina kamar tsabar yashi.19Saiwoyina suna shimfiɗe cikin ruwaye, raɓa na sauka a dukkan dare a rassana.
20Daraja a gare ni kullum garau take, baka shi ne ƙarfina kullum sabo yake a hannuna.21A gare ni mutane ke saurare; suna jira na, sun tsaya shiru su ji shawarata.22Bayan na gama magana ba wanda ya sake wata magana kuma; maganata tana sauka kamar ruwa a kansu.
23Suna jira na kullum kamar yadda ake jiran ruwan sama; sun buɗe bakinsu sosai don su sha daga kalmomina, kamar yadda suke jiranruwan bazara.24Na yi masu murmushi sa'ad da basu sa tsammaninsaba; ba su yi watsi da fara'ar fuskata ba.
25Nakan zaɓar masu hanya, in zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin sojojinsa, kamar wanda yake ta'azantar da masu makoki.

30

1Yanzu waɗanda na girme su, sai ba'a kaɗai suke yi mani -- waɗannan matasa maza waɗanda iyayensu ban ma yarda in bar su suyi aiki tare da karnukan da suke kiwon garke tumakina ba.2Lallai, ƙarfin hannuwan iyayensu maza, ba zasu iya taimako na ba--mutanen waɗanda ƙarfin balagarsu yake lalacewa?3Sun rame daga talauci da yunwa; sai gaigayar ƙasa suke yi da duhu, cikin jeji da kufai.

4Sukan tsinki ganyaye masu ɗaci na jeji su ci, doyar jeji ita ce abincinsu.5Aka kore su daga cikin mutane ana bin su da ihu kamar yadda ake yi wa ɓarawo ihu.6Sai a kwazazzaban rafi suke zama, ramummukan ƙasa da kogwannin duwatsu.
7A cikin jeji suke ta kuka kamar jakai, sukan taru tare a ƙarƙashin sarƙaƙiya.8Su 'ya'yan wawaye ne, lallai, 'ya'ya maza marasa suna a mutane! Aka kore su daga ƙasar tare da tsumagu.
9Amma yanzu na zama abin yiwa zambo, na zama abin magana a gare su.10Suna ƙyamata ta, sun tsaya da nisa daga gare ni; basu daina tofa mani yawu a fuskata ba.11Domin Allah ya katse lakata, ya ƙasƙantar da ni, waɗanda suka yi mani ba'a sun hana ni sakewa in yi wani abu.
12A hannun damana 'yan iska sun taso mani; sun kore ni suna gãba da ni sun tura ni hanyarsu ta hallaka.13Sun lalata hanyata, sun jawo bala'i domi na, ba wanda ya hana su.
14Sun zo suna gãba da ni kamar soja wanda yabi ta babbar kafar bangon birni; a tsakiyar hallaka sun naɗa kansu a kaina.15Babban tsoro ya faɗo mani; an kore darajata kamar iska; wadatata kuma ta shuɗe kamar girgije.
16Yanzu raina yana kwararowa daga gare ni; kwanakin wahala sun same ni.17A cikin dare ƙasusuwana na karkaɗawa; azaba tana gaigaya ta ba hutawa.
18Ƙarfin girman Allah yaci wuyan rigata; ya kuma kewaye ni kamar ƙarfin taguwata.19Ya jefar da ni cikin laka; na zama kamar ƙura da toka.
20Na yi kuka a gare ka, Allah, amma ba ka amsa mani ba; na tashi tsaye, ka dai kalle ni kawai.21Ka canja sai ka zama mara tausayi a gare ni; da ƙarfin hannunka ka tsananta mani.
22Ka jefa ni cikin guguwa, ka sa ta kora ni; ka jefa ni baya da gaba a cikin hadari.23Gama na sani zaka kai ni ga mutuwa, a gidan da aka ƙaddara wa kowanne mai rai.
24Duk da haka, ba wanda ya isa ya miƙa hannunsa ya roƙi taimako idan ya faɗi? Babu wani da zai nemi taimako idan ya shiga cikin wahala?25Ashe ban yi kuka saboda shi wanda yake cikin wahala ba? Ashe ban yi ɓacin rai saboda mutum mai bukata ba?26Sa'ad da nasa bege don abin kirki, sai ga mugunta ta zo; sa'ad da nake jiran haske, sai duhu ya zo.
27Zuciyata tana cikin damuwa, bata huta ba; kwanakin wahala ya zo a kaina.28Na tafi kamar wanda ke rayuwa cikin duhu, amma ba domin rana ba, na tsaya a gaban taron jama'a ina kukan neman taimako.29Na zama ɗan'uwan dila, aminin jiminai.
30Fatata baƙa ce, ta faɗi daga gare ni; ƙasusuwana suna ƙuna da zafi.31Saboda haka garayata ta juya ga waƙar makoki, sarewata kuma ta zama waƙoƙi ga waɗanda ke kuka.

31

1Na yi alƙawari da idanuna; me zai sa in dubi budurwa har in yi sha'awa?2Gama wanne irin rabo zan samu daga wurin Alla a sama, gãdon me kuma zan samu daga wurin Mai Iko a samaniya?

3Na kan yi tunanin masifa daga wurin mutane mara sa adalci, bala'i na masu aikata mugunta ne.4Ko Allah ba ya ganin hanyoyina da dukkan matakallaina?
5Idan ina tafiya da rashin gaskiya, idan kafata tana hanzarin aikata yaudara,6bari a auna ni da ma'aunin yadda Allah zai san halayena na kwarai.
7Idan ƙafata ta kauce daga hanya, idan kuwa zuciyata ta bi sha'awar idanuna, idan akwai wani aibi ya wuce ta hanuwana,8to bari na shuka, bari wani yaci, bari kuma amfanina ya tumɓuke.
9Idan zuciyata tayi sha'awar wata mace, idan har naje na laɓe a ƙofar maƙwabcina,10to bari matata tayi niƙan hatsi domin wani, bari waɗansu su kwanta a kanta.
11Gama wannan mugun laifi ne ƙwarai; lallai, alƙalai ne zasu hukunta.12Domin wuta mai ci zata hallaka, zata cinye har zuwa Abaddon, zata kone dukkan girbina har saiwa.
13Idan naƙi kulawa da roƙo domin adalci daga barorina maza da mata sa'ad da suka kawo koke-kokensu a kaina,14to me zan yi lokacin da Allah ya tashi don ya hukuntar da ni? Sa'ad da yazo yi mani shari'a, ya ya zan amsa masa?15Ai shi wanda yayi ni a mahaifa shi ne ya yi su kuma? Ba shi ne dai ya siffata mu dukka a cikin mahaifa ba?
16Idan na taɓa hana matalautan mutane daga sha'awarsu, ko idan nasa gwauruwar da mijinta ya mutu idanunta su dushe da kuka,17ko kuwa naci ɗan abincina ni kaɗai ban bar waɗanda basu da iyaye maza suma su ci abincina ba--18gama tun daga yarintaka marayu suka yi girma tare da ni kamar mahaifi, na lura da mahaifiyarsa, gwauruwa, daga cikin mahaifiyata.
19Idan na ga wani yana lalacewa saboda rashin sutura; ko idan naga wani mutum da bukata na rashin sutura;20idan zuciyarsa bata albarkace ni ba domin bai ji dumi da ulun tumakina ba,21idan na daga hannuna gãba da marayun mutane, don naga taimakona a ƙofar birni, sai a kawo ƙara a kaina!
22Idan na yi waɗannan abubuwa, bari kafaɗata ta ɓaɓɓalle daga in da su ke, bari hannuna ya karye daga mahadarsa.23Gama firgici da bala'i daga wurin Allah; saboda ɗaukakarsa, ba zan iya yin kome a kan waɗannan abubuwa ba.
24Idan nasa zinariya abin fatana, idan nace ina da zinariya mai kyau, 'Kana nan yadda na ke da aminci;25idan ina murna saboda dukiyata ta na da girma, ko saboda abin da na mallaka ne, sai su kawo s̀̀̀u a kaina!
26Idan na ga rana tana haske, ko wata yana tafiya da haskensa,27idan zuciyata jarabtu a asirce, yadda bakina zai sumbace hannun a sujadarsu--28wannan ma zai zama laifi wanda shari'a zata hukunta, gama na musanta Allah wanda ke sama.
29Idan ina murna saboda hallaka ta sami wanda ya ke maƙiyina, ko zan yiwa kaina barka ne, idan wahala ta same shi, zai kawo ƙarata!30Lallai, ban ma yarda in bar bakina ya yi zunubi ta wurin tambaya don ransa tare da la'ana.
31Idan a rumfata akwai mutanen da suka ce, 'Wane ne zai sami wanda bai ƙoshi da abincin Ayuba ba?"32(ko da baƙon da baya zama a dandalin birni, domin kullum ina buɗe ƙofufina ga mai tafiya), idan ba haka ba ne, sai a kawo ƙarata!
33Idan, kamar 'yan adam, na ɓoye zunubai na ta wurin ɓoye laifi a cikina34(saboda ina jin tsoron babban taron jama'a, domin tsoron rainin iyalai gare ni, na yi shuru, ban ma iya fita waje ba), sai a kawo ƙarata!
35Oh, idan za a sami wani shi kaɗai ya ji ni! Duba a nan ga sa hannuna; bari Mai Iko ya amsa mani! Idan ni kaɗai na yi ƙarar maƙiyana a rubuce!36Babu shakka zan ɗauke ta a buɗe a kan kafaɗata; zan sa ta kamar rawani.37Zan furta a kansa lissafin takawa ta; a matsayin asirin sarki zan tafi wurinsa.
38Idan ƙasata tana kuka da ni, tare da ƙungiyoyinta,39idan na ci amfaninta ba tare da biya ba, ko na yi sanaɗin mutuwar masu ita,40bari ƙayayuwa su tsiro maimakon alkama, tsire tsire marasa amfani kuma maimakon bali." Maganganun Ayuba sun kare.

32

1Sai mutanen uku suka daina ba Ayuba amsa saboda yana ganin kansa shi adali ne.2Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz daga iyalin Arama, ya husata da fushi a kan Ayuba saboda ya baratar da kansa maimakon Allah ya baratar da shi.

3Elihu ya fusata da fushi a kan abokansa uku saboda sun rasa amsawa Ayuba, duk da haka sun gani Ayuba ne ke da laifi.4Yanzu Elihu ya jira ya yi magana da Ayuba, don sauran mutanen uku sun girme shi da shekaru.5Sa'ad da Elihu ya ga babu wata amsa a bakunan waɗannan mutanen uku, har fushinsa ya yi ƙuna.
6Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya yi magana ya ce, "Ni yaro ne, ku manya ne sosai. Wannan ya sa na yi shuru, ban iya faɗa maku ra'ayina ba.7Na ce, "Yawan kwana su yi magana; yawan shekaru kuma su koyar da hikima.
8Amma akwai ruhu a cikin mutum; numfashin Mai Iko ya ke ba da sani da basira.9Ba manyan mutane ne kaɗai waɗanda suke da wayo da hankali ba, ko tsofaffin mutane kaɗai suke da sanin adalci da gaskiya.10Don haka nace da ku, 'Ku saurare ni; zan kuma faɗa maku ta wa fahintar.'
11Duba, na jira domin inji maganarku; na kasa kunne da jin muhawararku, tun kuna tunani a kan abin da za ku faɗa.12Lallai, na saurare ku, amma duba, babu wanda ya kada Ayuba ko wanda ya bashi amsar maganganunsa.
13Ku yi hankali kada wani ya ce, "Mun sami hikima! Allah ne zai ci nasara a kan Ayuba; mutum mai mutuntaka ba zai iya ba.14Gama Ayuba ba da ni ya ke magana ba, saboda haka ba zan amsa da irin amsarku ba.
15Waɗannan mutane uku abin ya cika masu ciki, ba su ƙara amsawa Ayuba ba; ba su da sauran abin da za su ce kuma.16Ni kuma zan tsaya don su basu ce kome ba, don sun tsaya a wurin shiru, basu da wata amsa kuma?
17A'a, ni kuma zan ba da ta wa amsa; zan kuma faɗa masu na wa sanin.18Gama ina cike da magana, ruhu da ke ciki na ya iza ni.19Duba, kirjina ya na kama da ruwan inabin da ba shi da mafitar iska. kamar sabuwar salkar ruwan inabi wadda ya ke shirin ya fashe.
20Zan yi magana saboda in huce, zan buɗe lebuna na in ba da amsa.21Ba zan nuna san zuciya ba, ko kuma in yi wa wani mutum fadanci.22Gama ni ban san yadda zan iya yi fadanci ba; idan nayi haka kuwa Mahaliccina zai ɗauke ni nan da nan.

33

1Amma yanzu, kai Ayuba, ina roƙon ka, ka saurari abin da zan ce, ka saurari dukkan maganganuna.2Duba yanzu, na buɗe bakina; harshena ya yi magana da bakina.3Kalmomina sun zo da gaskiyar zuciyata; leɓuna suna faɗar ilimi tsantsa.

4Ruhun Allah ne yayi ni; numfashin Mai Iko ne ya bani rai.5Idan za ka iya ka amsa mani; ka shirya kalmominka dai-dai a gabana, kayi tsaye a kansu.
6Duba, ni kamar ka mu ke a wajen Allah; ni kuma daga yumɓu aka siffanta ni.7Duba, razanata ba zata sa ka ji tsoro ba, ko matsawata ta zama da nauyi a kanka.
8Babu shakka maganar da ka yi na ji ta; na kuwa ji amon maganganunka,9ni tsabtattace ne, ba wani laifi, bani da laifi, kuma ba wani zunubi a gare ni.
10Duba, Allah ya sami damar zargi na, ya ɗauke ni tankar maƙiyinsa.11Ya sa ƙafaffuna a turu, ya na lura da dukkan hanyoyina.'12Duba, a wannan kayi kuskure--zan baka amsa, gama Allah ya fi kowane mutum girma.
13Me yasa kake yi masa gunaguni? Baya lissafin kowanne abu da yayi.14Gama Allah yakan yi magana sau ɗaya ne--i, har sau biyu, duk da haka mutum baya kula da ita.15Cikin mafarki, ko cikin wahayi da dare, a sa'ad da dogon barci ya faɗo wa mutane, ana barci a kan gado--
16sai Allah ya buɗe kunnuwan mutane, ya tsorata su da faɗakarwarsa,17don ya kawar da mutum daga zunubinsa da yayi nufi, ya kuma kawar da girmankai daga gare shi.18Allah yakan hana ran mutum daga faɗawa rami, rayuwarsa daga haurawa zuwa mutuwa.
19A kan hori mutum kuma da cuta mai zafi a gadonsa, yayi ta fama da azaba a cikin ƙasusuwansa,20saboda da ransa ya kyamaci abinci, kurwarsa ta ƙyamaci daɗinsa.
21Tsokar jikinsa ta rame ƙangayau yadda ba za a iya ganinta ba, ƙasusuwansa baza a iya gani ba, yanzu sun zama waje.22Lallai, ranna yasa gab da shiga rami, ransa yana wurin waɗanda suke so su hallaka shi.
23Amma idan a ce akwai wani mala'ika wanda zai yi sulhu dominsa, mai sulhu, ɗaya daga cikin duban mala'iku, zai nuna masa abin da ke dai-dai da zai yi,24idan mala'ikan da zai yi masa alheri ya faɗa wa Allah, 'Cece wannan mutum daga gangarawa zuwa cikin ramin; dana sami abin da zai fansa domin sa,'
25Naman jikinsa zai koma fiye da na yaro, zai komo irin kwanakin ƙarfin ƙuruciyarsa.26Zai yi addu'a ga Allah, Allah kuma zai yi masa alheri, saboda ya ga fuskar Allah da murna. Allah zai ba mutumin nasararsa.
27Sai wannan mutum ya raira waƙa a gaban sauran mutane yace, 'Na yi zunubi, ban yi dai-dai ba, amma zunubi bai sa a hore ni ba.28Allah ya fanshi raina daga tafiya can cikin rami, raina zai cigaba da ganin haske.
29Duba, Allah yayi dukkan waɗannan abubuwa ga mutum harma sau biyu, i, harma lokatai uku,30ya komo da ransa daga rami, don a haskaka shi da hasken rai.
31Ka yi lura Ayuba, ka saurare ni, kayi shiru, zan yi magana.32Idan kana da wani abu da zaka ce, ka amsa mani, yi magana, don in tabbatar maka kana dai-dai.33Idan ba haka ba, sai kayi shiru ka ji ni, ka zauna shiru, zan kuwa koya maka hikima."

34

1Hakanan, Elihu ya ci gaba da magana:2"Ku saurari kalmomina, ku masu hikima; ku ji ni, ku masu ilimi.3Domin kunnuwa na gwada kalmomi kamar yadda faranti ke ɗanɗana abinci.

4Bari mu zaɓar wa kanmu abin da ke na adalci, mu kuma yiwa kanmu abin da ke mai kyau.5Domin Ayuba yace ni adali ne, amma Allah ya ɗauke abin da ke dai-dai.6Ba a ma la'akari da adalcina, sai aka ɗauke ni maƙaryaci, raunukana kuma basu warkuwa duk da yake bani da zunubi.
7Wanne irin mutum ne Ayuba wanda ke shan ba'a kamar ruwa,8wanda ke tafiya da ma su yin mugunta, wanda kuma ke rayuwa tare da miyagu.9Domin ya ce ba amfani mutum yayi abin da ke mai kyau a gaban Allah
10Ku saurare ni ku mutane masu fahimta Allah ya sauƙaƙe ace Allah yayi aikin mugunta, kuma Allah ya sha ƙarfin ace yayi zunubi,11Domin yana sakawa kowanne mutum gwargwadon aikinsa, kowanne mutum kuma gwargwadon abin da ya aikata.12Hakika Allah ba ya aikata mugunta, kuma mai iko dukka bai taɓa watsi da adalci ba
13Wane ne ya ɗora shi bisa duniya? Wane ne kuma ya ɗora duniya a ƙarƙashinsa?14Shi kaɗai ne yasan abin da yake so ya aikata, in har ya taɓa tattaro ruhunsa da numfashinsa,15daga nan sai dukkan talikai su lalace mutum kuma ya koma ƙura.
16I kuna da fahimta yanzu sai ku saurari wannan ku saurari ƙarar kalmomina.17Ko wanda yaƙi adalci zai iya yin shugabanci? Ko zaku iya shari'anta Allah? Wanda ke da adalci da kuma girma?
18Allah wanda ke cewa da sarki kai ɗan tawaye ne? ko kuma ya ce da masu daraja ku miyagu ne'?19Allah wanda baya nuna tara ga shugabanni kuma baya la'akari da mawadata fiye da matalauta, domin dukkansu aikin hannunsa ne.20A cikin ɗan lokaci sukan mutu; da tsakar dare za a girgiza mutane zasu kuwa shuɗe; za a kwashe ƙarfafan mutane, amma ba ta hannuwan mutum ba.
21Domin idanun Allah suna bisa hanyoyin mutum; yana ganin dukkan sawayensa.22Babu duhu, ko dishi-dishi inda ƙofofin laifofi zasu ɓoye kansu,23Domin Allah baya bukatar ya sake yiwa mutum ƙwanƙwanto; babu bukatar kowanne mutum yaje gabansa domin alƙalanci.
24Ya kakkarya mutane masu girma gunduwa-gunduwa domin tafarkinsu da ke bukatar ƙarin bincike; ya ɗora waɗansu a madadinsu.25Ta wannan fannin yasan abin da suke yi; ya kaɓantar da waɗannan mutane da dare an kuma hallakar da su.
26A idon sauran, ya karkashe su saboda miyagun ayyukansu kamar masu aikata miyagun laifofi,27saboda sun juya masa baya sun kuma ƙi yin la'akari da dukkan tafarkunsa.28Ta wannan hanya, suka sa kukan mutane matalauta yazo gare shi; yaji kukan waɗanda ake zalunta.
29In ya yi shiru wane ne zai bashi laifi? in ya ɓoye fuskarsa, wane ne zai ji shi? Yana mulkin al'uma haka kuma kowa,30domin kada mutum marar tsoron Allah ya yi mulki, domin kada a sami wanda zai jefa mutane cikin tarko.
31A misali in a ce wani zai ce da Allah, ' Hakika nayi laifi, amma bazan ƙara yin laifi ba,32koya mani abin da bazan gani ba; Nayi zunubi, amma bazan ƙara yinsa ba.'33Kana tunanin cewa Allah zai hori zunubin na wancan mutum, tun da yake kun ƙi abin da Allah ke yi? Dole ne kuyi zaɓi, ba ni ba. To sai ku faɗi abin nan da kuka sani.
34Mutane masu fahimta zasu ce da ni-hakika, duk mutum mai fahimta da ya ji ni zai ce,35Ayuba na yin magana ba tare da sani ba; kalmominsa kuma basu da hikima.'
36In da za a sa Ayuba a ma'auni na ɗan lokaci saboda maganarsa kamar ta miyagun mutane.37Domin ya ƙara tawaye a kan zunubinsa; ya tafa hannuwansa cikin zagi a tsakiyarmu; ya jera kalmomi gãba da Allah."

35

1Bugu da ƙari Elihu ya ƙara cewa,2"Kana tunanin hakan dai-dai ne a lokacin da kayi magana, 'Hakina a gaban Allah'?3Domin kayi tambaya, cewa wanne amfani yake da shi a gare ni?' kuma 'Ashe bai fi ba in da a ce nayi zunubi?'

4Zan amsa maka kai da abokanka.5Ka dubi rana a sama, ka gan ta; ka dubi sararin sama wanda ya fi ka tsayi.
6In ka yi zunubi a ina ka sa Allah ya ji zafi? In laifofinka su jeru zuwa sama, me zaka yi masa?7In kana da adalci me zaka iya bashi? Me zai karɓa daga hanunka?8Aikin muguntarka na iya cutar da mutum, kamar yadda kake mutum, aikin adalcinka kuma na iya amfanar wani ɗan mutum.
9Sabo da ayyukana na tsanantawa, mutane suka yi kuka; suka nemi taimako daga damatsan ƙarfafan mutane.10Amma ba wanda yace ina Allah mahallicina, wanda ke bada waƙoƙi da dare,11wanda ke koyar damu fiye da yadda yake koyar da dabbobin duniya, wanda kuma yasa muka fi tsuntsayen sararin sama hikima?'
12Suka yi kuka a can amma Allah bai amsa ba saboda girman kan miyagun mutane.13Hakika Allah ba zai ji kuka na wawanci ba, maɗaukaki ba zai saurare shi ba.14Yaya kuma zai ƙi amsa maka in ka ce baka ganinsa, cewa kuma ƙararka na gabansa, da kuma cewa kana jiransa!
15Yanzu kuma kuka ce fushinsa baya yin hukunci, kuma baya ko ɗan kula da laifofi.16To Ayuba ya buɗe bakinsa domin kawai ya faɗi maganar; ya jera kalmomi ba tare kuma da sani ba."

36

1Elihu yaci gaba ya ce,2Bani dama in yi magana 'yar kaɗan, zan kuma nuna maka wani abu domin ina da ɗan sauran abin faɗi domin in kare Allah.3Zan sami fahimtata daga can nesa; Zan yi la'akari da adalcin da ke na Mahallicina.

4Domin hakika kalmomina baza su zama ƙarya ba; wani wanda yayi girma cikin sanina tare da kai.5Duba Allah mai iko ne, kuma baya rena kowa; yana da ƙarfi cikin ikon fahimta.
6Baya kiyaye rayukan miyagun mutane, amma a memakon haka ya kan yi abin da ke dai-dai ga waɗanda ke shan wahala.7Baya kawar da idanunsa daga adalan mutane amma yakan ɗora su a kursayi kamar sarakuna har abada, kuma sun ɗaukaka sosai.
8In an ɗaure su da sarƙoƙi da karkiya ta wahala,9to sai ya baiyana musu abin da suka yi, da laifofinsu da girman kansu.
10Hakannan ya buɗe kunnuwansu ga umarnansa, da dokokinsa ya kuma gargaɗe su da su juyo daga aikata laifofi.11In sun saurare shi sun kuma yi masa sujada, zasu yi kwanakinsu cikin wadata, shekarunsu kuma cikin wadar zuci.12Duk da haka, in basu saurare shi ba, zasu hallaka ta wurin takobi; zasu mutu saboda basu da sani.
13Marasa tsoron Allah a zuciya na ajiye wa kansu fushi; basu yi kukan neman temako ba koma da a lokacin da Allah ya ɗaure su.14Sun mutu cikin ƙuruciyarsu; rayukansu sun kai ga ƙarshe a cikin ɗabi'ar karuwanci.
15Allah na kuɓutar da waɗanda ake tsananta wa, ya buɗe kunnuwansu ta wurin tsananinsu.16Hakika zai so ya jawo ka daga cikin tsanani zuwa wuri inda ba ƙunci, kuma inda za a shirya teburinka da abinci mai cike da kitse.
17Amma ka cika da hukunci ga miyagun mutane; hukuncisu ne ke riƙe ka.18Kar ka yarda fushinka ya ruɗe ka ga yin zagi, ko kuwa girman fansa yasa ka ka kauce.
19Ko wadatarka zata amfane ka, domin kada ka shiga damuwa, ko kuwa ƙarfinka zai taimake ka?20Kada kayi marmarin da zaka yi zunubi ga waɗansu, lokacin da a ka kama mutane a cikin wurarensu.21Ka lura domin kada ka koma ga yin zunubi saboda an gwada ka da tsanani domin kada kayi zunubi.
22Duba Allah ya sami ɗaukaka cikin ikonsa, wane ne mai koyarwa kamarsa?23Wa ya taɓa bashi umarni game da tafarkinsa? Wane ne zai iya cewa da shi, ka aikata rashin adalci?24Tuna ka yabi ayyukansa, wanda mutane suka rera waƙarsu.
25Dukkan mutane sun duba waɗannan ayyukan, amma daga nesa ne kawai suke ganin su.26Duba Allah nada girma, amma bamu fahimce shi sosai ba; yawan shekarunsa basu ƙidayuwa.
27Domin ya jawo ɗigon ruwa wanda yasa ya zama ruwan sama daga taskarsa,28wanda giza-gizai ke sheƙowa daga sama cikin wadatuwar mutum.29Hakika ko akwai wanda zai iya fahimtar yawan faɗin yadda giza-gizai suke da kuma yadda tsawa take daga gare shi?
30Duba ya shimfiɗa walƙiyarsa a kewaye da shi ya rufe sauyoyin teku.31A wannan hanya ya hukunta mutane kuma yana bada abinci a yalwace.
32Ya cika hannuwansa da walƙiya har sai da ya umarce ta takai iyakarta.33Tsawarta takan gargaɗi hadari, dabbobima kan ji tana zuwa.

37

1Hakika zuciyata ta firgita a kan wanan; an cire shi daga wurinsa.2Ku saurara, i ku saurari ƙarar muryarsa, ƙarar da ke fita daga bakinsa.3Ya fitar da ita waje a ƙarƙashin dukkan sararin sama, ya kuma aika da walƙiyarsa zuwa iyakokin duniya.

4Sai wata murya tayi ruri a bayansa, yayi tsawa da muryar darajarsa; bai hana mariƙin walƙiya ba a lokacin da aka ji muryarsa.5Allah yayi tsawa mai ban mamaki da muryarsa; yayi manyan abubuwa da ba zamu iya bada da bayaninsu ba.6Domin yace da ƙanƙara, 'faɗo a duniya', haka nan ruwan sama shima ya sheƙo, 'Ya zama babbar mafitar ruwa.'
7Ya dakatar da hanun kowa daga aiki, domin dukkan mutanen daya hallitta suga ayyukansa.8Sai dabbobi su gudu zuwa maɓoya su kuma zauna a kogonninsu.9Hadari yakan zo daga mazauninsa a kudu kuma sanyi ya tattaru daga iskar da ta warwatsu a arewa.
10Ta wurin numfashin Allah a ka bayar da ƙanƙara; sai ruwa ya daskare kamar ƙarfe.11Hakika ya kan tarwatsa baƙin girgije da ikonsa; ya warwatsa walƙiyarsa a cikin giza-gizai.
12Yakan sarrafa giza-gizai ta wurin bishewarsa, domin su yi duk abin da ya umarce su a sararin duniya.13Yasa duk wannan ya faru; waɗansu lokutan yana faruwa domin gyara, waɗansu lokutan domin ƙasarsa, waɗansu lokutan su zama ayyukan amintaccen alkawari.
14Ayuba ka saurari wannan; ka dena kayi tunani kan al'amuran Allah masu girma.15Ko ka san yadda Allah ya shimfiɗa giza-gizai ya kuma sa walƙiya ta haskaka a cikin su
16Ko ka fahimci tashin giza-gizai, da ayyukan ban mamaki na Allah, wanda ke da cikakken sani?17Ko ka fahimci yadda tufafinka suka zama da zafi lokacin da ƙasar ta tsaya saboda iska ta taso daga kudu?
18Zaka iya shimfiɗa rana kamar yadda zai yi, wadda keda ƙarfi kamar madubi an kuma zuba shi kamar ƙarfe?19Koya mana abin da za mu ce da shi, domin ba zamu iya shimfiɗa gardamarmu bisa tsari ba saboda duhun tunaninmu.20Ko za a faɗa masa abin da naso yi masa magana? Ko mutum zai so a haɗiye shi?
21Yanzu kuma mutane baza su iya duban rana ba lokacin da tayi zafi a sararin sama ba bayan iska ta wuce ta share giza-gizanta.22Daga cikin arewa ake samun wadatar zinariya-a sama Allah ya isa aji tsoronsa cikin daraja.
23Ga mai iko dukka, ba zamu iya samunsa ba! Yana da girma cikin iko; baya ƙuntatawa adalci da cikakakken adalci.24Saboda haka mutane ke tsoronsa. Baya sauraron waɗanda ke da hikima a cikin tunaninsu."

38

1Sai Yahweh ya kira Ayuba ta cikin gawurtacciyar guguwa yace,2"Wane ne wannan da ke kawo duhu domin shirye shirye ta wurin kalmomin da ba ilimi?3Yanzu sai ka yi ɗammara kamar namiji domin zan tambaye ka, kuma dole ne ka ba ni amsa.

4Ina ka ke sa'ad da na shimfiɗa ginshiƙan duniya? Faɗa mini, in kana da isarshiyar ganewa.5Wane ne ke aiyana inda iyakokinta? Faɗa mini, in ka sani. Wane ne ya miƙa fitaccen layi a kan ta?
6A kan me a ka kafa ginshiƙanta? wane ne ya ɗora dutsen kan kusurwarta?7lokacin da taurarin asubahi suka rera waƙa tare kuma dukkan 'ya'yan Allah suka yi sowa domin farinciki?
8Wane ne ya kulle tekuna da ƙofofi lokacin da suka tumbatsa, inda ta zama kamar tazo daga mahaifa-9lokacin da nayi giza-gizai su zama suturarta, kuma baƙin duhu ya zama babbar iyakokinta?
10Cewa lokacin da nasa alamomi a kan tekuna da kuma iyakokina,11da kuma lokacin dana sa kuryoyin ƙofofinta, lokacin kuma da nace da ita, 'Zaki iya zuwa daga wannan nisan, amma ba ci gaba; nan ne zan sa iyakoki ga wannan fahariyar ta raƙuman ruwanki.'
12Ka taɓa ba da umarni ga safiya, ko ka sa faɗuwar rana ta san wurinta,13domin ta jira iyakokin duniya ta kuma kakkaɓe miyagu daga cikin ta?
14An canja fasalin duniya kamar yadda yunɓu ke canjawa a ƙarƙashin hatimi; dukkan abubuwa sukan tsaya a kanta a sarari kamar gezar sutura.15Daga miyagu sai aka ɗauke haskensu; dantsensu da ya ɗaukaka sai aka kakkarya shi.
16Ka taɓa zuwa maɓɓuɓɓugan ruwan tekuna? ka taɓa yin tafiya a wuri mafi zurfi?17Ko an taɓa nuna maka ƙofofin mutuwa, ka taɓa ganin ƙofofin inuwar mutuwa?18Ko ka fahimci duniya da duk cikarta? faɗa mini in ka san ta dukka.
19Ina hanyar da haske ke bi domin hutawa-game da dare kuma ina nasa wurin?20Zaka iya yi wa haske da dare jagora zuwa wuraren aikinsu? Zaka iya samun hanya domin su bi su koma gidajensu!21Babu shakka ka sani, domin an haife ka a lokacin; shekarunka kuma suna da yawa!
22Ka taɓa zuwa ma'ajiyar sino, ko ka taɓa ganin ma'ajiyar ƙanƙara,23waɗannan abubuwan da na adana na tsawon lokaci saboda masifa, domin ranar hargitsi da yaƙe-yaƙe?24Ina ne sashen da walƙiya ke warwatsuwa ko kuma inda ake warwatsa iska daga gabas akan duniya?
25Wane ne ya yi kwazazzaban da ruwan damina ke bi, ko kuma wane ne ya yi wa aradu hanya,26yasa tayi ruwa a bisa ƙasa inda ba wani mutum da ke wurin, da kuma jeji, inda ba kowa,27don ƙosar da yasassun wurare ya kuma sa ciyayi su firfito?
28Ko ruwan sama yana da uba, ko kuma wane ne ya zama uba ga raɓa?29Daga mahaifar wa ƙanƙara ke zuwa? Wane ne ya kafa daɓen hasken sararin sama?30Ruwaye kan ɓoye kansu su zama kamar dutse; cikin zurfafa kuma ya zama daskararru
31Zaka iya kafa sarƙoƙi kan taurari na musamman ko ka datse sarƙar Oriyon?32Za ka iya yiwa dandazon taurari jagora su baiyana a lokutan da suka dace? Zaka iya yi wa damisa da 'ya'yanta jagora?33Ko ka san sharruɗan sararin sama? Zaka iya saita wurin da sararin sama ke mulki a kan duniya?
34Zaka iya tada murya har zuwa cikin giza-gizai, domin ruwa mai yawa ya rufe ka?35Zaka iya aika cincirindon walƙiya domin su fita, domin suce da kai, ga mu nan'?
36Wane ne ya bayar da hikima a cikin giza-gizai ko kuma ya bada fahimta ga masu tatsuniya?37Wane ne zai iya ƙirga giza-gizai ta wurin fasaharsa? Wane ne zai iya kwararo ruwan sararin sama,38lokacin da ƙura ta murtuke ƙasa kuma ta murtuke tare?
39Zaka iya kamo abin da zakanya zata ci? ko kuma ka iya ƙosar da marmarin 'ya'yan zaki,40lokacin da suke kuyakuyai a cikin kogonninsu suke kuma cikin inuwa a ɓoye suna fako?
41Wake bada kamammu ga hankaki lokacin da ƙananansu suka yi kuka ga Allah suka kuma yi yako saboda ƙarancin abinci?

39

1Ko ka san lokacin da awakin jeji ke renon ƙananansu a cikin duwatsu? Zaka iya jira lokacin da kishimai ke maza?2Zaka iya ƙirga watannin da suke kammala ɗaukan ciki? Ka san lokacin da suke renon 'ya'yansu?

3Sukan durƙusa su haifi 'ya'yansu, daga nan su gama zafin naƙudarsu.4'Ya'yansu kan yi ƙarfi su yi girma a cikin saura, sai su tafi ba su kuma ƙara dawowa.
5Wane ne ke 'yantar da jakin jeji? wane ne ke kwance dabaibayin jaki,6gidan wa na yi a Arabah, gidansa a ƙasa mai gishiri.
7Sai ya yi dariyar reni ga hayaniyar cikin birni; ba ya jin tsawar mai tuƙi.8Ya yi ta gararanba a kan duwatsu a matsayin makiyayarsa; a can ya yi ta neman koren tsiron da zai ci.
9Ko takarkarin jeji zai yi murna ya bauta maka? Ko zai so ya tsaya a wurin kwaminka?10Za ka iya riƙe jakin jeji da igiya lokacin da ya fusata? Za ka iya baje kwarurruka a lokacin da ya rarake ka?
11Ka iya amincewa da shi domin yana da ƙarfi sosai? Zaka iya bar masa aikinka yayi maka?12Zaka iya dogara gare shi domin ya kawo maka hatsinka gida, ya tattara hatsi domin masussukarka?
13Fukafukan jimina na da faɗi sosai, to amma ko dogayen gashin fuka-fukan da kuma ƙananan gasusuwan zasu iya kare ta?14Domin ta kan bar ƙwaiƙwayenta a ƙasa, ta kan barsu su sha ɗumi a cikin ƙura,15takan manta cewa sawaye zasu iya farfasa su ko kuma dabbobin jeji su tattake su.
16Takan azabtar da 'ya'yanta kamar ba ita ta haife su ba; bata jin tsoro kada naƙudarta ta zama a banza,17domin Allah bai bata hikima ba kuma bai bata wani fahimta ba.18Lokacin da take gudu takan yi dariyar wulaƙanci ga doki da kuma mahayin dokin.
19Ka ba doki ƙarfinsa ne? kai ne ka yiwa wuyansa ado da dogon gashi mai sheƙi?20Ka taɓa sa shi ya yi tsalle kamar bãbe? Girman haniniyarsa abin tsoro ne.
21Yana haniniya da ƙarfi, yana kuma murna da ƙarfinsa; yakan fita domin ya tunkari makamai.22Ya kan rena tsoro kuma baya alhini; baya kafcewa takobi.23Kwari da bãka na hararsa, tare da sheƙin mãshi da dogon ƙarfe mai tsini.
24Yana haɗiye ƙasa cikin ƙarfi ya murtuke ta a lokacin da ya ji ƙarar ƙaho, baya tsayuwa wuri ɗaya.25Duk lokacin da ya ji ƙarar ƙaho, yakan ce, Aha! Ya kan sunsini yaƙi daga nesa-ƙara mai ƙarfi da ihun kwamandoji da hayaniyarsu.
26Ta wurin hikimarka ne shaho ke miƙar da fuka-fukansa ya fuskanci kudu da su?
27Ko ta wurin umarninka ne gaggafa ke yin sheƙarta a can ƙonƙoli?28Yakan zauna a can ƙonƙolin itace yakan yi sheƙarsa a reɗimar rassa, ya zama mafakarsa.
29Daga can yake duban abincinsa idanunsa na hangen su daga can nesa, hakanan30'Ya'yanta kan sha jini a inda aka karkashe mutane, a can yake.

40

1Yahweh yaci gaba da yiwa Ayuba magana cewa,2"Ko duk wani da ke ƙoƙarin ganin laifi zai iya ƙoƙarin yi wa Mafi iko dukka gyara? Shi wanda ke gardama da Allah sai ya amsa."

3Sai Ayuba ya amsawa Yahweh cewa,4"'Duba ni da ban can-canta ba; yaya zan amsa maka? Na sa hanunna a kan bakina.5Sau ɗaya na yi magana, kuma ba zan amsa ba; hakika sau biyu ne, amma ba zan ci gaba da yi ba."
6Sai Yahweh ya amsawa Ayuba daga cikin hadari yace,7"Yanzu sai ka yi wa kanka ɗammara kamar jarumi, domin zan tambaye ka tambayoyi, kuma dole ne ka amsa mini.
8Ko hakika za ka ce ba ni da adalci, ko za ka hukunta ni domin ka nuna mini cewa ka yi dai-dai?9Ko kana da damatsa kamar na Allah? Ko za ka iya yin tsawa da murya kamar sa?
10To ka yi wa kanka sutura cikin ɗaukaka da ƙima, ka yi wa kanka kwalliya da daraja.11Ka baje kewaye da fushinka, ka dubi kowanne mai fahariya ka ƙasƙantar da shi.
12Ka duba duk mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake miyagu a inda suke tsayiwa.13Ka bisne su tare a ƙasa, ka kulle su a ɓoyayyen wuri,14Daga nan zan yi la'akari da kai da kuma sanin cewa hannunka na dama zai cece ka.
15Yanzu ka duba dodon ruwa, lokacin da nayi a lokacin da na halice ka, yana cin ciyawa kamar takarkari,16Yanzu duba, ka ga yadda ƙarfinsa ke ƙirjinsa, ikonsa kuma yana cikin tumbinsa.
17Ya mayar da bindinsa kamar sidar, haƙoransa a haɗe suke.18Ƙasusuwansa kamar cikin ƙarfe suke, ƙafafunsa kuma kamar makaran ƙarfe suke.
19Shi ne sarki a cikin hallitar Allah. Allahn da ya yi shi ne kawai ke iya kayar da shi,20Domin tuddai ne ke ba shi abinci, sauran dabbobi kuma na kusa da wurin suna wasa a kusa.21Yana kwance can cikin lollokin ganyaye.
22Ganyaye masu toho sun rufe shi da inuwarsu duhuwar itatuwa ta shinge shi. Duba23Idan rafi yayi ambaliya ba ya fIrgita, yana da ƙarfin hali ko da ruwan Yodan zai kawo masa iya bakinsa.24Ko wani zai iya kama shi da ashifta, ko ya iya huda hancinsa ta wurin yaudara?

41

1Ko za ka iya jawo Lebiyatan da ƙugiyar kamun kifi? za ka iya ɗaure wuyanta da sarƙa?2Za ka iya sa igiya a hancinta? ko ka iya huda cikin bakinta da ƙugiya? lokacin da ta ke yi maka gurnani3Ko za ta ji daɗinka? Ko za ta yi maka magana mai lumana?

4Kuna da yarjejeniya da ita kan cewa ba za ka mai da ita baiwarka ba har abada?5ko za ka iya wasa da ita kamar yadda zaka yi da tsuntsu? Za ka iya ɗaure ta kamar bayinka mata?6Ko masunta zasu iya ƙulla wata yarjejeniya dominta? Ko zasu iya yin fataucinta a cikin fatake?
7Za ka cika maɓoyarsa da ƙayayuwa, Ko kansa da mãsun kamun kifi?8Ka ɗora hanunka bisansa sau ɗaya tak daga nan za ka san yaƙi ba kuma za ka ƙara yinsa ba.9Duba duk mai begen yin hakan ƙarya yake yi; ba wanda za a jefa masa a gabansa da ba zai tattake ba.
10Ba wanda zai iya tarar dorinar ruwa ba tare da ya furgita ba?11Wane ne ya fara ba ni wani abu domin in biya shi? Duk abin da ke ƙarƙashin sararin sama nawa ne.12Ba zan yi shiru ba game da ƙafafun dorinar ruwa, da kuma game da al'amarin ƙarfinta ba, ba kuma game da tagomashin hallitar da take da ita ba.
13Wane ne zai iya yaye masa wannan lulluɓin na samansa? Wane ne zai iya ratsa garkuwoyinsa masu ninki biyu?14Wane ne zai iya buɗe ƙofofin fuskarsa-zagaye da haƙoransa masu banrazana?15bayansa an yi shi ne da garkuwoyi aka harhaɗa su wuri ɗaya, kamar da wata rufarfiyar alama.
16Suna marmatse da juna domin kada iska ta iya ratsa su, suna harhaɗe da juna.17Suna manne da juna, domin kada a ɓamɓare su.18Haske na walƙatawa daga gurnaninsa; haskensa kamar na hasken fitowar rana.
19Daga cikin bakinsa tartsatsin wuta na fita.20Daga cikin hancinsa kuma hayaƙi na fita kamar na matoyar tukunya da ta toyu ta yi zafi sosai.21Numfashinsa ne ke samar da gawayin wutar; wuta na fita daga bakinsa.
22Wuyansa na da ƙarfi, masifa na rawa a gabansa.23Maɗaukan jikinsa a harhaɗe suke tare, suna kafe a jikinsa; baza su iya ciruwa ba.24Zuciyarsa na da ƙarfi kamar dutse, hakika tana da tauri kamar dutsen niƙa.
25Sa'ad da ya miƙar da kansa tsaye alloli ma kan firgita saboda tsoro, sukan ja baya.26In takobi ya sare shi, ba ya yi masa komai- hakama mãsu da sauran makamai duk ba su yi masa komai.27Ya na ganin kibiya kamar rauga ce kawai, namijin ƙarfe kuma kamar abin da tsatsa ta riga ta cinye.
28Kibiya ba ta sa shi gudu; a gare shi duwatsu masu sulɓi kamar ƙaiƙai suke.29Rundunoni kuma kamar tattakar ciyawa; ya kan yiwa walƙiyar kibiya dariya.30Ƙananan sassansa kamar rusarshiyar masana'antar tukwane ce, yakan bar wuri a damalmale kamar wurin da a ka yi kwaɓar fitar da zinariya da azurfa.
31Ya kan haƙa wuri ya yi zurfi ya zama kamar tukunyar dafa ruwa; ya kan mayar da teku ta zama kamar tukunyar mai.32Ya kan sa haske ya haskaka bayansa; wani zai yi tunanin yadda zurfin suma mai furfura take.
33A cikin duniya babu wanda ke dai-dai da shi, wanda aka yi shi ya zama da rashin tsoro.34Yana ganin duk wani abu da ke taƙama; shi sarki ne a kan dukan 'ya'yan masu taƙama.

42

1Daga nan sai Ayuba ya amsawa Yahweh ya ce,2"Na sani zaka iya yin komai, kuma ba wani nufi naka da ba zai cika ba.3Wane ne wannan da ke ɓata shiri ba tare da ilimi ba? Hakika, na faɗi abubuwan da ban fahimta ba, abubuwan da ke da wahalar fahimta a gare ni, waɗanda ban sani ba.

4Ka ce da ni, 'Yanzu ka saurara, zan yi magana; zan tambaye ka abubuwan da za ka faɗa mini'.5Na ji labarinka da jin kunnuwana, amma yanzu na ganka.6Domin haka na rena kaina ina hurwa cikin toka da ƙura.
7Sai ya zamana bayan ya faɗi waɗannan maganganu ga Ayuba, sai Yahweh yace da Elifhas Batishmine, fushina yayi ƙuna a kanka da kai da abokanka guda biyu, domin ba ku yi mani maganar da ta dace ba, kamar yadda bawana Ayuba ya yi ba.8To yanzu sai ku tanada wa kanku shanu bakwai da raguna bakwai, ku je wurin bawana Ayuba ku miƙa baiko na ƙonawa domin kanku. Ayuba zai yi muku addu'a, zan kuma amsa addu'arsa, domin kada in yi fushi da ku saboda wawancinku, domin ba ku faɗi abin da ya dace game da ni kamar yadda Ayuba bawana ya yi ba."9Sai Elifas da Bildad Bashune, da Zofar Bana'ame suka je suka yi kamar yadda Yahweh ya umarce su, Yahweh kuma ya karɓi Ayuba.
10Bayan Ayuba ya yi addu'a domin abokansa, Yahweh ya komo masa da wadatarsa. Yahweh ya ninka wa Ayuba wadatarsa fiye da ta dã.11Daga nan 'yan'uwan Ayuba mata, da duk waɗanda suka san shi a dã suka zo suka ci abinci tare da shi a gidansa. Suka nuna tausayinsu da kuma ta'aziya a gare shi kan duk asarar da Yahweh ya aukar masa, kowanen su kuma ya ba shi zoben zinariya da kuma azurfa.
12Yahweh ya albarkaci ƙarshen rayuwar Ayuba fiye da lokacin farko, yana da tumaki dubu goma sha huɗu, raƙuma dubu shida, bijimai dubu ɗaya, da matan jakuna ɗari.13Haka nan ya sake samun 'ya'ya bakwai maza da 'ya'ya mata uku.14Ya raɗa wa ta fari suna Yemima ta biyun kuma Keziya, ta ukun kuma Keren-Haffuk.
15A cikin dukkan ƙasar babu matan da aka samu kyawawa da suka kai su kyau, mahaifinsu ya ba su gãdo tare da 'yan'uwansu maza.16Bayan wannan Ayuba ya rayu shekaru 140; ya ga 'ya'yansa da kuma jikokinsa. Har zuwa tsara ta huɗu.17Bayan nan Ayuba ya mutu cikin tsufa da kuma cikakkun kwanaki.

Littafin zabura

1

1Albarka ga mutum wanda ba ya tafiya a cikin shawarar miyagu ko ya tsaya a hanyar masu zunubi ko ya zauna tare da masu ba'a.2Amma yana jin daɗin shari'ar Yahweh, yana nazarinta dare da rana.

3Zai zama kamar itacen da aka dasa a gefen ƙorama wanda ya ke bada 'ya'yansa a kan kari, ganyayensa ba sa yin yaushi, ya kan yi nasara a dukkan abin da ya ke yi.
4Mugaye ba haka suke ba, amma suna kamar yayi wanda iska ke kwashewa.5Saboda haka mugaye ba zasu tsaya a shari'a ba, ko masu zunubi su taru a wurin adalai ba.
6Gama Yahweh yana lura da hanyar adalai, Amma hanyar mugaye za ta lalace.

2

1Meyasa al'ummai suke shirin tayarwa, kuma don me mutane ke ƙulla shawarwarin banza?2Sarakunan duniya ke ɗaukar matsayi tare, masu mulki kuma suna shirya maƙarƙshiya tare su yi gãba da Yahweh da kuma zaɓaɓɓensa Almasihu, cewa,3"Bari mu tsaga karkiyar da suka ɗora a kanmu, kuma mu jefar da sarƙoƙinsu."

4Shi wanda ke zaune a sammai zai yi masu dariya; Ubangiji yana yi masu ba'a.5Ya yi masu magana cikin fushinsa da razanar dasu da kuma hasalarsa, cewa,
6"Ni da kaina na naɗa sarkina a Sihiyona, tsattsarkan dutsena."7Zan yi shelar abin da Yahweh ya furta. Ya ce da ni, "Kai ɗana ne! Wannan rana na zama mahaifinka.
8Ka roƙe ni, zan kuma ba ka al'ummai don gãdonka da yankunan duniya domin su zama mallakarka.9Za ka mallake su da sandar ƙarfe; za ka farfashe su kamar tukunyar yumɓu, za ka ragargaza su su farfashe."
10To yanzu, ku sarakuna, ku ji gargaɗi; ku mai da hankali, ku sarakunan duniya.11Ku bauta wa Yahweh da tsoro da kuma murna tare da rawar jiki.
12Sumbaci ɗan ko ya yi fushi da ku, zaku mutu ta hanyar fushinsa na ɗan lokaci. Albarka ta tabbata ga dukkan waɗanda ke zuwa gare shi neman mafaka.

3

Zabura ta Dauda, lokacin da ya guda daga ɗansa Absalom.

1Yahweh, nawa ne maƙiyana! Nawa ne suka tashi suna gãba da ni.2Da yawa suna magana a kaina, "Babu taimako dominsa daga Allah." Selah

3Amma kai, Yahweh, kai ne garkuwa a gare ni, darajata, kuma wanda ke tallafar kaina.4Na yi kira da muryata ga Yahweh, ya kuma amsa mani daga tsattsarkan dutsensa. Selah
5Na kwanta na kuma yi barci; na farka, gama Yahweh ya tsare ni.6Ba zan ji tsoron taron mutane waɗanda suka kewaye ni ta kowanne gefe.
7Tashi, Yahweh! Ka cece ni, Allahna! Gama zaka buga dukkan abokan gãba har ƙasa; zaka kakkarye haƙuran mugaye.8Ceto zai zo daga wurin Yahweh. Bari ya sa wa jama'arsa albarka. Selah

4

Domin shugaban mawaƙa; a kayayyakin kiɗa masu tsarkiya. Zabura ta Dauda.

1Ka amsa mani sa'ad da cikin matsuwa nayi kira, Allahna mai adalci; ba ni hutu a lokacin da nake cikin matsuwa. Ka ji tausayina ka kuma saurari addu'ata.

2Ku mutanen nan, sai yaushe zaku daina juya ɗaukakata zuwa kunya? Har yaushe zaku yi ta ƙaunar abubuwan banza kuna kuma cigaba da neman abin da ya ke na ƙarairayi? Selah3Amma kun sani Yahweh ne ya keɓe mai tsoronsa don kansa. Yahweh zai ji idan na yi kira a gare shi.
4Ku ji tsoro, domin ku daina zunubi! Ku yi nazari a cikin zukatanku a kan gadajenku, kuma ku yi shuru. Selah5Ku miƙa hadayun adalci kuna kuma dogara ga Yahweh.
6Da yawa sun ce, "Wane ne zai nuna mana wani abu mai kyau? Yahweh, ka ɗaga hasken fuskarka a kanmu.7Ka ba zuciyata farinciki fiye da na waɗanda ke da wadatar hatsi da sabon ruwa inabi.8A cikin salama zan kwanta har barci ya kwashe ni, domin kai kaɗai ne, Yahweh, ka kiyaye ni cikin lafiya sosai.

5

Domin shugaban mawaƙa da kayayyakin kiɗa na bushe-bushe. Zabura ta Dauda.

1Ka saurari kira na zuwa gare ka, Yahweh; kayi tunani a kan nishe-nishena.2Ka saurari muryar kirana, sarkina da Allahna, gama a gare ka nake yin wannan addu'ar.3Yahweh, da safe kaji kukana; da safe zan kawo rokona gare ka in kuma jira ka.

4Gaskiya ne kai ba Allahn dake yarda da mugunta ba ne; ko mugayen mutane su zama bãƙinka.5Masu fahariya ba zasu tsaya a gabanka ba; kana ƙin dukkan mugaye.6Ka kan hallakar da maƙaryata; Yahweh yakan rena masu ta da hankali da mayaudaran mutane.
7Amma ni, saboda babban alƙawarin ƙaunarka, zan zo cikin gidanka; in kuma rusuna maka da bangirma a tsattsarkan haikalinka.8Ya Ubangiji, ka bida ni in aikata adalcinka domin abokan gãbana; ka kuma fayyace mani hanyarka a gabana.
9Gama babu gaskiya a cikin bakinsu; abubuwansu mugunta ne; harshensu kamar buɗaɗɗen kabari ya ke; suna yaudara da harshensu.10Ka furta su masu laifi ne, Allah; bari shirye-shiryensu su zama dalilin faɗuwarsu! Ka kore su sabili da yawan zunubansu, da kuma tayarwar da suke yi maka.
11Amma bari dukkan waɗanda suka fake gare ka su yi farinciki; bari kullum su yi ta murna don kana kiyaye waɗanda ke ƙaunar sunanka.12Gama ka sawa masu adalci albarka, Yahweh; zaka kewaye su da alheri kamar garkuwa.

6

Domin shugaban mawaƙa akan kayan kiɗa masu tsarkiya da aka shirya wa Sheminit. Zabura ta Dauda.

1Yahweh, kada ka tsauta mani a lokacin fushinka ko ka hukunta ni da fushinka.2Ka yi mani jinƙai, Yahweh, gama na tafke sarai, ka warkar da ni, Yahweh, domin ƙasusuwana na makyarkyata.

3Raina yana damuwa ƙwarai. Amma kai, Yahweh - har sai yaushe wannan zai ci gaba?4Ka zo, Yahweh! ka kuɓutar da ni. Ka cece ni domin alƙawarin amincinka!5Gama a cikin mutuwa ba a tunawa da kai. Don wane ne zai yi maka godiya a lahira?
6Na gaji tilis saboda baƙinciki. Dukkan dare gadona ya kan jiƙe da hawayena; Na jiƙa matashin kaina da hawayena.7Idanuna sun yi kumburi saboda kuka; sun zama marasa ƙarfi saboda dukkan abokan gãbana.
8Ku tafi daga wuri na, dukkan ku masu aikin mugunta; Gama Yahweh ya ji kukana. Yahweh ya ji rokona don jinƙai;9Yahweh ya amsa mani addu'ata.10Dukkan abokan gãbana zasu sha kunya da babbar damuwa. Zasu juya baya tare da babban ƙasƙanci.

7

Haɗe-haɗen waƙoƙin Dauda wanda ya yi wa Yahweh game da maganganun Kush Benyamine.

1Yahweh Allahna, na sami mafaka a wurinka! Ka cece ni daga dukkan masu nema na, ka ƙwace ni.2Idan ba haka ba kuwa zasu ɗauke ni kamar zaki, su yayyaga ni har babu wani da zai kawo mani ceto.

3Yahweh Allahna, ban aikata abin da maƙiya suka ce nayi ba; babu rashin adalci a cikin hannuwana.4Ban yi wani abu da ba dai-dai ga kowa ba wanda muke zaman salama dani, ko da ga wani mai gãba da ni.
5Idan ba gaskiya nake faɗa ba bari maƙiya su nemi raina har su kama shi; bari ya taka rayayyen jikina a ƙasa ya bar ni da kunyata a ƙura. Selah
6Ka tashi, Yahweh, cikin fushinka; tashi kayi gãba da hasalar abokan gãbana; ka tashi domina ka aiwatar da alƙawarin amincinka da aka sanka da shi.7Dukkan kabilu sun taru a gabanka; ka sake ɗaukar wurinka a bisan su.
8Yahweh, kai ne alƙalin dukkan alummai; ka 'yantar da ni, Yahweh, gama ni adali ne bani da laifi, Maɗaukaki.9Bari mugun abu na masu aikata mugunta ya zo ƙarshe, amma ka tabbatar da adalan mutane, Allah mai adalci, kai kake gwada zukata da tunane-tunane.
10Kariyata tana zuwa daga Allah, wanda ya ke ceton masu yin adalci a zuciya.11Allah ne alƙali mai adalci, Allah wanda ya ke jin haushi a kowacce rana.
12Idan mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa ya kuma shirya bakansa don yaƙi.13Zai shirya kayayyakin faɗa gãba da shi; zai auna kibansa masu wuta.
14Ka yi tunani akan wanda ya ɗauki ciki da mugunta, wanda ya shirya aiwatar da mugunta, wanda ya haifi cutar ƙarairayi.15Yana haƙa rami mai zurfi har kuma ya faɗa ramin da ya gina.16Mugun shirin da yayi ya koma a kansa kenan, don rikicin ya sauka a kansa kenan.
17Zan gode wa Yahweh saboda adalcinsa; zan raira yabo ga Yahweh Maɗaukaki.

8

Domin shugaban mawaƙa; tsari na salon waƙar bagitte. Zabura ta Dauda.

1Yahweh Ubangijinmu, yaya girman sunanka ya ke a dukkan duniya, ka bayyana ɗaukakarka a cikin sammai.2Daga cikin bakin yara da jarirai ka shirya yabo domin maƙiyanka, domin ka tsai da abokan gãbarka da ramako.

3Sa'ad da na duba sararin sammai, wanda yatsunka suka yi, wata da taurari, waɗanda kasa a wuraren zamansu.4Mene ne mahimmancin 'yan adam har da kake tunawa da su, ko mutune har da kake lura da su?5Duk da haka ka maida su ƙasa kaɗan da halittun dake sama ka kuma naɗa su da ɗaukaka da daraja.
6Ka sa shi yayi mulkin dukkan abin da kayi da hannuwanka; ka ɗora dukkan abubuwa a ƙarƙashin ƙafafuwansa:7dukkan tumaki da shanu har ma da namomin jeji,8tsuntsayen sammai da kifayen teku da dukkan halittun dake cikin tekuna.
9Yahweh Ubangijinmu yaya girman sunanka ya ke a cikin dukkan duniya!

9

Domin shugaban mawaƙa; da aka tsara bisa salon Mut Labben. Zabura ta Dauda.

1Zan yi maka goɗiya Yahweh da dukkan zuciyata; zan furta dukkan abubuwa masu ban mamaki da ka yi.2Zan yi murna da farinciki da kai; zan raira waƙar yabo ga sunanka Maɗaukaki!

3Lokacin da magabtana suka ja da baya, sun faɗi sun mutu a gabanka.4Gama kai ka tsare ni; ka zauna a kan kursiyinka, mai shari'ar adalci!
5Ka kwaɓi al'ummai, ka kuma hallakar da mugaye; ka kawar da sunayensu har abada abadin.6An rugurguje abokan gãba kamar kangaye a lokacin da aka lalata biranensu. Dukkan tunawa dasu ya ƙare.
7Amma Yahweh ka kasance har abada; ka kafa kursiyinka domin yin shari'a.8Zan yi mulkin dukkan duniya da adalci, kuma zai yi wa mutane shari'a da gaskiya.
9Yahweh kuma zai zama mafaka ga waɗanda ake zalunta, wurin ɓuya a lokatan wahala.10Waɗanda suka san sunanka zasu dogara gare ka, domin kai ne, Yahweh, ba za ka yi watsi da duk wanda ya neme ka ba.
11Ku yi waƙar yabo ga Yahweh, wanda ke mulki a Sihiyona; ku faɗa wa al'ummai abin da ya yi.12Gama Allah wanda ke ramakon jinin da aka zubar na tunawa; baya mantawa da kukan waɗanda ake cutar su.
13Ka yi mani jinƙai, Yahweh; dubi yadda waɗanda ke gãba da ni suka wulaƙanta ni, kaine wanda zai kuɓutar da ni daga ƙofofin mutuwa.14Dãma inyi shelar dukkan yabonka. A ƙofofin budurwar Sihiyona zan yi farincikin cetonka!
15Al'ummai sun faɗa cikin ramin da suka haƙa; tarkon da suka kafa don su buya ya kama ƙafafuwansu.16Yahweh ya bayyana kansa; ya gudanar da shari'a; mugu ya kama kansa da abubuwan da ya aikata. Selah
17An maida miyagu makomarsu a Lahira, rabon dukkan waɗanda suka manta da Allah.18Gama ba kullum ne ake mantawa da masu buƙata ba ko masu bege waɗanda ake zalunta zasu ɓace har abada.
19Ka tashi, Yahweh; kada ka bar mutum yayi nasara da kai; bari a yiwa al'ummai hukunci a gabanka.20Tsoratar da su, Yahweh; bari al'ummai su sani su mutane ne kawai.

10

1Yahweh don me kake tsaye, a can nesa? Me ya sa ka ɓoye kanka a lokatan wahala?2Domin fahariyarsu, mugayen mutane na tsananta wa matalauta; amma bari tarkon da mugaye suka ɗana ya kama su.3Gama mugun mutum yana fahariya da manufofinsa; yana albarkatar haɗamarsa har yakan zagi Yahweh.

4Mugun mutum yana ɗaga fuska; ba ya neman Allah. Ba ya tunani a kan Allah domin bai damu ya kula da dukkan al'amura a kansa ba.5Ya kan yi nasara a dukkan lokatai, domin adalcin dokokinka sun yi masa tsada; yana furci a kan abokan gãbansa.
6Ya ce a cikin zuciyarsa, "Ba zan taba faɗuwa ba; a cikin dukkan tsararraki ba zan sadu da wahala ba."7Maganganunsa suna cike da zage-zage da yaudara, da mugayen kalmomi; harshensa kuma mai hatsari ne da hallakar wa.
8Yana kwanto kusa da ƙauyuka; a ɓoyayyun wurare har ya kashe marasa laifi; idanuwansa kuma suna duban waɗanda baza su iya yin komai ba.9Yana jira a inda ya ɓuya kamar zaki a cikin kurmi; ya kan kwanta yana fakon wanda zai kama lokacin da yasa tarkonsa.10Kamammunsa kuma an buga su har ƙasa; suka faɗa cikin ƙaƙƙarfan ragarsa.
11Ya ce a cikin zuciyarsa, "Allah ya manta; ya rufe fuskarsa; ba zai damu ya duba ba."12Tashi, Yahweh! Ɗaga hannunka, Allah! Kada ka manta da waɗanda ake tsanantawa.
13Me yasa mugun mutum zai ƙi Allah har ya ce a cikin zuciyarsa, "Ba zai kama ni da wani alhaki ba"?14Kana kula da komai, don kullum kana ganin wanda ake sa masa damuwa da baƙinciki. Kana sa mai bukata yasa dogararsa a gare ka; kana kuɓutar da marasa iyaye.
15Ka karya hannun mugu da mai aikata mugunta. Kasa ya ɗauki laifin mugun aikinsa, kada ya yi tunanin ba za a taba ganewa ba.16Yahweh Sarki na har abada abadin; al'ummai kuma za a kore su daga ƙasarsa.
17Yahweh, ka ji buƙatun wanda ake tsanantawa; ka karfafa zukatansu, ka saurari addu'arsu.18Zaka kãre marasa iyaye da waɗanda ake ƙuntata masu saboda babu wani mutum a wannan duniya da zai sake jawo razana.

11

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta Dauda.

1Na sami mafaka a wurin Yahweh; yaya zaka ce da ni, "Ka tashi kamar tsuntsu akan tsauni"?2Amma duba! miyagu sun shirya ƙibansu a kan tsarkiya don su harba cikin duhu a zuciyar adali.

3Gama idan ginshiƙai suka lalace, mene ne adali zai iya yi?4Yahweh yana cikin tsatsarkan haikalinsa; idanuwansa suna kallo, idanuwansa suna gwada 'ya'yan 'yan adam.
5Yahweh yana gwada masu kirki da miyagu dukka, amma yana ƙin waɗanda ke ƙaunar tashin hankali.6Yana ruwan garwashin wuta da ƙibiritu a kan mugaye; iska zata kone rabonsu daga finjilinsa!7Gama Yahweh mai adalci ne, yana kuma ƙaunar masu gaskiya; adalai kuma zasu ga fuskarsa.

12

Domin shugaban mawaƙa; da aka shirya wa Sheminit. Zabura ta Dauda.

1Ka yi taimako, Yahweh, saboda mutanen kirki sun ɓace; aminitattu ma sun ɓace.

2Kowanne mutum yana maganar banza ga maƙwabcinsa; kowanne yana maganar yaudara da leɓuna da zuciya biyu.3Yahweh, ka datsa dukkan leɓunan yaudara, kowanne harshe ya riƙa faɗin manyan abubuwa.4Waɗannan sune waɗanda suka ce, "Ta wurin harshenmu zamu rinjaya. Sa'ad da leɓunanmu suka yi magana, wane ne zai zama gwani a bisanmu?"
5"Saboda tashin hankali akan matalauta, domin nishin masu buƙata, zan tashi," inji Yahweh. "Zan basu tsaron da suka yi marmari."
6Kalmomin Yahweh kalmomi ne zalla, kamar azurfar da aka narkar a tanderun wuta, aka tace har sau bakwai.7Kai ne Yahweh! Ka kiyaye su. Ka tsare mutanen kirki daga muguwar tsara har abada.8Mugaye suna tafiya ko'ina a lokacin da mugunta ke ɗaukaka a cikin 'yan adam.

13

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta Dauda.

1Yahweh, har sai yaushe, za ka ci gaba da mantawa da ni? Har yaushe ne zaka ɓoye mani fuskarka daga gare ni?2Har yaushe ne zan daina damuwa da baƙinciki a zuciyata dukkan yini? Har yaushe ne maƙiyana zasu rika cin nasara a kaina?

3Ka dube ni ka kuma amsa mani, Yahweh Allahna! Ka bani haske ga idanuwana, ko in yi barcin mutuwa.4Kada ka bar maƙiyina ya ce, "Na ce nasara a kansa," don kada maƙiyina ya sami abin cewa, "Na yi rinjaye akan abokin gãbana;" idan ba haka ba, maƙiyina zai yi murna saboda faɗuwata.
5Amma na dogara ga amintaccen alƙawarinka; zuciyata zata yi murna da cetonka.6Zan yi waƙa ga Yahweh domin ya yi mani abin kirki ƙwarai.

14

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta Dauda.

1Wawa yace a cikin zuciyarsa, "Ba Allah." Sun lalace sun kuma aikata laifin ban ƙyama; babu wani wanda ya aikata nagarta.

2Yahweh ya duba ƙasa daga sama a kan 'yan adam ya gani idan ko akwai wani mai fahimta, wanda ke neman sa.3Dukkansu sun koma baya. Ga baki ɗayansu sun zama marasa kirki. Ba wanda ya ke aikata abin da ya ke dai-dai, babu ko ɗaya.
4Sun san wani abu, waɗanda suka aikata laifi, waɗanda suke cin mutanena kamar yadda suke cin gurasa, amma wane ne ba ya kiran Yahweh?
5Sun razana tare da fargaba, gama Allah yana tare da taruwar adalai!6Kuna so ku ci mutuncin matalaucin mutum koda ya ke Yahweh ne mafakarsa.
7Oh, dama ceton Isra'ila zai zo daga Sihiyona! Sa'ad da Yahweh ya dawo da mutanensa daga bauta, Yakubu zai yi murna, Isra'ila ma zata yi farinciki!

15

Zabura ta Dauda.

1Yahweh, wane ne zai iya tsaya wa a rumfar sujadarka? Wa zai iya zama a tudun ka mai tsarki?2Duk wanda ba shi da laifi, wanda ke aikata abin dake dai-dai wanda kuma ya ke faɗar gaskiya daga zuciyarsa.

3Wanda baya ɓatanci da harshensa, baya cin mutuncin wasu, baya ɓatanci ga maƙwabcinsa.
4Mutumin wofi abin reni ne a idanunsa, amma yana girmama waɗanda ke tsoron Yahweh. Yana rantsuwa ba don kansa ba, kuma yana cika alƙawaran da yayi.5Baya karɓar ruwa a kuɗin da ya bayar bashi. Baya karɓar cin hanci don ya yi shaidar zur a kan marar laifi. Duk wanda ya ke yin waɗannan abubuwa ba zai taɓa girgiza ba.

16

Salon waƙar Dauda.

1Ka tsare ni, Allah, gama na zo neman mafaka a gare ka.2Na ce da Yahweh, "Kai ne Ubangijina; nagarta ta a banza take idan bana tare da kai.3Kamar yadda tsarkakakkun mutane waɗanda ke a duniya, su mutane masu kirki; dukkan murnata a gare su take.

4Wahalolinsu zasu ƙaru, waɗanda ke neman waɗansu gumaka. Ba zan zubo masu da baye-baye na shan jinin allolinsu ba ko in furta sunayensu da leɓuna na ba.
5Yahweh, kaine kaɗai na zaɓa da ƙoƙona. Kai ne kake riƙe da rabona.6An ajiye ma'aunan layi domina a wuraren jin daɗi; babu shakka gãdon dake kawo jin daɗi nawa ne.
7Zan albarkaci Yahweh, wanda ke bani shawara; ko da dare ma ina tunanin umarninsa.8Na sa kaina a wurin Yahweh a dukkan lokuta, saboda kada in girgiza daga hannun damarsa!
9Don haka cike nake da murna; ɗaukakata na farinciki. Babu shakka zan zauna a cikin tsaro.10Saboda baza ka bar raina a Lahira ba. Ba zaka bar amintaccenka ya ga rami ba.
11Ka koya mani hanyar rai; yalwataccen farinciki na kasancewarka; murna zata zauna a hannun damarka har abada!"

17

Addu'ar Dauda.

1Ka kasa kunne ga roƙona don adalci, Yahweh; ka saurari kirana na neman taimako! Ka kasa kunne ga addu'ata daga leɓuna marasa yaudara.2Bari baratarwata ta zo daga wurinka; bari idanuwanka su ga abin dake dai-dai!

3Idan zaka gwada zuciyata, idan zaka zo gare ni da dare, zaka tsarkakeni ba kuma za a sami wata mugunta a shirye-shiryena ba; bakina ba zai yi saɓo ba.
4Game kuma da ayyukan mutane; sune a cikin maganar leɓunanka waɗanda na tsare kaina daga hanyoyi na marasa bin doka.5Na yi tafiya a kan tafarkinka sosai; sawayena basu kauce ba.
6Na yi kira a gare ka, domin ka amsa mani, ya Allah; ka juyo da kunnenka gare ni ka kuma saurara a lokacin da na yi magana.7Ka nuna mani amintaccen alƙawarinka ta hanya mai banmamaki, kai da ke yin ceto ta hannun damarka ga waɗanda ke neman mafaka a gare ka daga maƙiyansu!
8Ka tsare ni kamar ƙwayar idanunka; ka ɓoye ni a ƙarƙashin inuwar fukafukanka9daga fuskar miyagu waɗanda ke zargi na, maƙiyana da suka kewaye ni.10Basa jin tausayin kowa; bakunansu na magana da fahariya.
11Sun kewaye sawayena. Sun sa idanuwansu don su fyaɗa ni ƙasa.12Su kamar zakoki ne sun ƙosa su ga abin da zasu hallaka, kamar 'ya'yan zakoki suna laɓe a ɓoyayyun wurare.
13Ka tashi, Yahweh! Ka hare su! Ka jefar da su a ƙasa a kan fuskokinsu! Ka cece raina daga takobin mugaye!14Yahweh, ka cece ni daga gare su da hannun ka, daga mutanen wannan duniya waɗanda arziƙinsu a cikin wannan rayuwa ne kaɗai! Za ka cike wuraren ajiyar mutanenka da arziki; zasu zama da 'ya'ya dayawa kuma zasu bar wadatarsu ga 'ya'yansu.
15Amma ni, zan ga fuskarka a cikin adalci; zan gamsu, sa'ad da na farka, da ganin ka.

18

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta Dauda, baran Yahweh, sa'ad da ya rera wa Yahweh maganganun wannan waƙa a ranar da Yahweh ya kuɓutar da shi daga hannun dukkan maƙiyansa da kuma hannun Saul. Ya raira waƙa cewa:

1Ina ƙaunarka, Yahweh, ƙarfina.

2Yahweh ne dutsena, hasumiya ta, wanda ke kawo mani tsaro; shi ne Allahna, dutsena; zan ɓoye a cikinsa. Shi ne garkuwata, ƙahon cetona, shi ne kuma ƙarfina.3Zan yi kira ga Yahweh wanda ya cancanci a yabe shi, za a kuma cece ni daga maƙiyana.
4Sarƙoƙin mutuwa sun kewaye ni, hargowar ruwaye marasa daraja sun sha kaina.5Sarƙoƙin Lahira sun kewaye ni; tarkon mutuwa kuwa ya kama ni.
6A cikin ƙuncina na yi kira ga Yahweh; na yi kiran neman taimako ga Allahna. Ya ji muryata daga haikalinsa; kirana na neman taimako ya kai gare shi; ya shiga har cikin kunnuwansa.
7Sai duniya ta raurawa ta girgiza; ginshiƙan duwatsu kuwa suka jijjigu suka kuma yi rawar jiki saboda Allah ya husata.8Hayaƙi kuwa ya yi ta tuƙaƙowa daga kafofin hancinsa, harshen wuta ya fito daga bakinsa. Gawayin garwashi suka fita ta wurinsa.
9Ya buɗe sammai ya sauko ƙasa, duhu kuma baƙiƙƙirin na ƙarƙashin ƙafafunsa.10Ya hau kan kerub ya tashi; ya yi tafiya a kan fikafikan iska.
11Ya maida duhu rumfa a kewaye da shi, gizagizan ruwan sama masu nauyi a sararin sama.12Ƙanƙara da garwashin wuta sun faɗo daga walƙiya dake gabansa.
13Yahweh ya yi tsawa a cikin sammai! Muryar Maɗaukaki ta yi tsawa.14Ya harba kibansa, ya warwatsar da magabtansa; walƙatawar walƙiyoyi ta warwatsar da su.
15Daga nan hanyoyin ruwa suka bayyana; ginshiƙan duniya dukka aka bayyana su a cikin kukan yaƙinka, Yahweh- a cikin hurawa mai ƙarfi ta numfashin kafofin hancinka.
16Ya miƙo hannunsa ƙasa daga samaniya; ya riƙe ni! Ya tsamo ni daga cikin ruwa mai zurfi.17Ya kuɓutar da ni daga ƙaƙƙarfan abokin gãbata, daga waɗanda ke ƙi na, domin sun fi ni ƙarfi sosai.
18Sun tasar mani a ranar shan ƙuncina amma Yahweh ne mai taimako na!19Ya fitar da ni daga hatsari a buɗaɗɗen wuri; ya cece ni domin yana farinciki dani.
20Yahweh ya sãka mani saboda adalcina; ya dawo da ni saboda hannuwana na da tsarki.21Domin na kiyaye tafarkun Yahweh ban kuma juya ga mugunta daga Allahna ba.
22Gama dukkan ka'idodinsa na adalci suna gaba na; game kuma da fariilansa, ban kauce daga gare su ba.23Na kuma zama marar laifi a gabansa, na kiyaye kaina daga zunubi.24Domin haka Yahweh ya dawo dani saboda adalcina, domin hannuwana masu tsafta ne a idanunsa.
25Ga kowanne mai aminci, kana nuna kanka mai aminci; ga mutum marar laifi, ka nuna kanka marar laifi.26Ga duk wani mai tsarki, ka nuna kanka mai tsarki; amma kana da dabara ga duk mai aikin mugunta.
27Gama kana ceton mutane daga wahala, amma ka kan ƙasƙantar da masu girmankai da suka ɗaga idanunsu!28Domin ka bada haske ga fitilata; Yahweh Allahna ka haskaka duhuna.29Gama ta wurinka zan iya tserewa maƙiyana; ta wurin Allahna zan iya tsallake saman katanga.
30Kamar yadda Allah ya ke, hanyarsa dai-dai take. Maganar Yahweh tsartsarka ce! Shi garkuwane ga duk wanda yake neman mafaka a wurinsa.31Gama wane ne Allah sai Yahweh? Wane ne dutse in ba Allahnmu ba?32Shi ne Allahn dake ƙarfafa ni kamar ɗammara, wanda ya ke sa mutanen da basu da aibu a kan hanyarsa.
33Yana tabbatar da lafiyar ƙafafuna kamar barewa ya kuma sa ni a bisa!34Yakan koyar da hannuwana don yaƙi makamaina kuma za su tankware bakan tagulla.
35Kai ka bani garguwar cetona. Hannunka na dama yana ƙarfafa ni, tagomashinka kuma ya maida ni babba.36Kayi mani buɗaɗɗen wuri don ƙafafuwana suna ƙarƙashina saboda kada santsi ya ɗauke ƙafafuwana.
37Na kori maƙiyana har na kama su; ban juya ba har sai da na lalata su dukka.38Na buga su har ba wanda zai iya tashi; sun faɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.39Gama ka sa ƙarfi a kaina kamar ɗamara don yaƙi; ka sa waɗanda ke gãba da ni a ƙarƙashina.
40Ka bani nasara akan maƙiyana; zan hallaka waɗanda ke gãba da ni.41Suna kira don taimako, amma babu wani da ya cece su; sun yi kira ga Yahweh, amma bai amsa masu ba.42Na buge su har sun zama gutsu-gutsu kamar ƙura a fuskar iska; na jefar da su waje kamar laka a tituna.
43Ka cece ni daga mutane masu husuma. Ka maida ni shugaba a kan al'ummai. Mutanen da ban san su ba, ban ma yi masu aiki ba.44Yayin da suka ji ni, zasu yi mani biyayya; bãƙi zasu rusuna mani dole.45Bãƙin zasu zo da rawar jiki daga kagarunsu.
46Yahweh mai rai ne; dutsena abin yabo. Allah mai cetona a gimama shi.47Shi ne Allah wanda ya ke ɗaukar fansa domina, yana sawa a rinjaye al'ummai a ƙarƙashina.
48Ni 'yantacce ne daga maƙiyana! Lalle, ka ɗaukaka ni sama da waɗanda suka taso suna gãba da ni! Ka cece ni daga mutane masu tawaye.49Saboda haka zan yi yabo a gare ka, Yahweh, a cikin al'ummai; zan raira maka waƙar yabon sunanka!
50Allah yana bada babbar nasara ga sarkinsa, ya kan nuna amintaccen alƙawarinsa ga wanda ya zaɓa, ga Dauda da zuriyarsa har abada.

19

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta Dauda.

1Sammai na bayyana ɗaukakar Allah, sararin sama kuma na bayyana ayyukan hannunsa!2A kowacce rana ana fitar da magana; dare bisa dare na bayyana ilimi.3Babu magana ko kalma da aka furta; ba a ji amonsu ba.

4Duk da haka maganarsu ta tafi dukkan duniya, jawabinsu kuma har ƙarshen duniya. Ya kafa rumfa domin rana a cikinsu.5Rana kamar ango na taƙama daga kagararsa, kuma kamar ƙaƙƙarfan mutum wanda ke farinciki idan ya ƙosa ya yi tsere.6Rana tana fitowa daga ɗaya gefen zuwa ɗaya tsallaken; ba abin da zai tsere daga zafinta.
7Dokar Yahweh cikakkiya ce, tana wartsakar da rai; shaidar Yahweh kuwa abar dogara ce, tana ba da hikima ga masu buƙata.8Ka'idodin Yahweh dai-dai suke, tana sa zuciya ta ji daɗi; umarnin Yahweh na da kyau, yana kawo haske ga idanuwa.
9Tsoron Yahweh tsabbatacce ne, tabbatacce ne har abada; dokokin Yahweh gaskiya ne dukkansu dai-dai suke!10Suna da girma da daraja fiye da zinariya, fiye ma da zinariyar da aka tace; sun fi zuma zaƙi, zuman dake ɗigowa daga saƙarsa.
11I, ta wurinsu bawanka ya sami gargaɗi; akwai lada mai girma idan an yi biyayya dasu.12Wane ne zai iya rarrrabe kuskuren kansa? Ka tsabtacce ni daga ɓoyayyun laifuffuka.
13Ka tsare bawanka kuma daga zunubai marasa kangado; kada ka bari su yi mulki a kaina. Sa'an nan ne zan zama kamili, zan kuma zama mara laifi daga laifuffukana masu yawa.14Ka sa maganar baƙina da tunanin zuciyata su zama abin karɓa a wurinka, Yahweh, dutsena da fansata.

20

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta Dauda.

1Bari Yahweh ya taimake ka a ranar wahala; bari sunan Allah na Yakubu ya tsare ka,2ya kuma aika taimako daga wuri mai tsarki ya kawo maka tallafi daga Sihiyona.

3Bari ya tuna da dukkanbaye-bayenka ya kuma karɓi hadayun ƙonawarka. Selah4Ya biya maka buƙatar zuciyarka, ya kuma cika maka dukkan shirye-shiryenka.
5Sai mu yi sowa ta farinciki saboda ka ci nasara, a cikin sunan Allahnmu, zamu ɗaga tutoci. Yahweh zai biya dukkan roƙe-roƙenmu.6Yanzu dai na sani Yahweh zai ceci zaɓaɓɓensa; zai amsa masa daga wurinsa mai tsarki a sama da iko a hannun damarsa wanda ya cece shi.
7Waɗansu sun dogara ga karusansu wasu kuma ga dawakansu, amma mu muna kira ga Yahweh Allahnmu.8Su zasu yi tuntuɓe har su faɗi ƙasa, amma mu zamu tashi mu tsaya daram!
9Yahweh, ka ceci sarki; ka taimake mu sa'ad da muka yi kira.

21

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta Dauda.

1Sarki na yi farinciki cikin ƙarfinka, Yahweh! Babu iyaka ga farincikinsa daga cikin ceton da ka tanada!2Ka biya masa buƙatar zuciyarsa baka kuma hana masa roƙon leɓunansa ba. Selah.

3Gama ka kawo masa albarku masu wadata; ka sanya bisa kansa kambi na tsabar zinariya.4Ya nemi rai daga gare ka; ka bashi; ka bashi tsawon kwanaki har abada abadin.
5Darajarsa na da girma sabili da nasarar ka; ka ɗibiya masa daraja da ɗaukaka.6Gama ka bashi madawwaman albarku; ka sashi jin daɗi da farinciki da ke a gabanka.
7Gama sarki yana dogara ga Yahweh; ta wurin alƙawarin amincin Maɗaukaki ba zaya jijjigu ba.8Hannunka zaya kama dukkan maƙiyanka; Hannunka na dama zaya kama waɗanda suka ƙi ka.
9A lokacin hasalarka; zaka ƙona su sarai kamar daga cikin tanderu mai ƙuna. Yahweh zai haɗiye su cikin hasalarsa, kuma wutar za ta cinye su.10Zaka hallakar da zuriyarsu daga ƙasar kuma zuriyarsu daga cikin 'yan adam.
11Gama sun shirya yi maka mugunta; sun tsiro da shiri wanda ba za su iya yin nasara ba!12Gama za ka sa su koma da baya; zaka jã kwarinka a fuskarsu.
13Ka ɗaukaka, Yahweh, cikin ƙarfin ka; zamu raira waƙa mu kuma yaɓi ikonka.

22

Domin shugaban mawaƙa; an tsara bisa ga tsallen barewa. Zabura ta Dauda.

1Allahna, Allahna, me yasa ka yashe ni? Me yasa ka yi nisa daga ƙubutar da ni kuma kayi nisa daga muryata ta azaba?2Allahna, na yi kuka da tsakar rana, amma baka amsa mani ba, da dare kuma ban yi shuru ba!

3Amma kai mai tsarki ne; kana zaman sarki tare da yabon Isra'ila.4Iyayenmu sun dogara gare ka; sun dogara gare ka, ka kuma ƙubutar da su. Sun yi kira gare ka an kuma ƙuɓutar da su.5Sun dogara gare ka basu kuma kunyata ba.
6Amma ni tsutsa ne ba mutum ba, abin kunya ga "yan adam da kuma abin raini ga mutane.7Dukkan waɗanda suka ganni suka cakune ni; suka yi mani haibaici; suka kaɗa mani kai.8Suka ce, "Ya dogara ga Yahweh; bari Yahweh ya kuɓutar da shi. Bari ya kuɓutar da shi, gama yana fahariya da shi."
9Gama ka fito dani daga mahaifa; ka sa in dogara gare ka a sa'ad da nake shan nono wurin mahaifiyata.10Tun daga mahaifa aka jefo ni gare ka; kai Allahna ne tun daga mahaifar mahaifiyata!
11Kada ka yi nisa dani, gama damuwa na kusa; babu wani mai taimako.12Bajimai masu yawa sun kewaye ni; Bajimai masu ƙarfi na Bashan suna zagaye dani.13Sun buɗe bakinsu da girma gãba dani kamar zaki mai ruri yana yagar abin da ya kama.
14An kwararo ni kamar ruwa, kuma dukkan ƙasusuwana sun goce. Zuciyata kamar kitse; ta narke daga cikin cikina.15Ƙarfina ya bushe kaf kamar fasasshiyar tukunya; harshena ya manne sama a bakina. Ka kwantar da ni a cikin ƙurar mutuwa.
16Gama karnuka suka zagaye ni; taron masu aikata mugunta suka kewaye ni; suka huda hannuwana da ƙafafuna.17Zan iya ƙirga ƙasusuwana. Suka duba suka kuma zura mani ido.
18Suka rarraba tufafina a tsakaninsu, suka jefa ƙuri'a a bisa kayana.19Kada ka yi nisa, Yahweh; ina roƙon ka kayi sauri domin ka taimake ni, ƙarfina!
20Ka kuɓutar da raina daga takobi, raina ɗaya daga hannuwan karnukan daji.21Ka cece ni daga bakin zaki; ka kuɓutar dani daga ƙahonni na shanun daji.
22Zan furta sunanka ga 'yan'uwana; a tsakiyar taruwar jama'a zan yabe ka.23Ku da kuke tsoron Yahweh, yabe shi! Dukkan ku zuriyar Yakubu, girmama shi! Ku tsaya cik cikin tsoronsa, dukkan ku zuriyar Isra'ila!
24Gama baya rena ko yayi banza da wahalar ƙuntattu ba; Yahweh baya ɓoye fuskarsa daga gare shi ba; a lokacin da ƙuntacce yayi kira gare shi, ya ji.25Yabona zai zama sabili da kai a cikin babban taron jama'a; Zan cika wa'adina a gaban waɗanda ke tsoron sa.
26Tsanantattu za su ci su ƙoshi; Waɗanda suka nemi Yahweh zasu yabe shi. Bari zukatanku su rayu har abada.27Dukkan mazamnan duniya zasu tuna su kuma juyo ga Yahweh; dukkan iyalan al'ummai zasu durƙusa a gabanka.
28Gama mulki na Yahweh ne; shi yake mulki bisa al'ummai.29Dukkan mawadatan mutanen duniya za su yi buki su kuma yi sujada; dukkan su masu gangarawa zuwa turɓaya zasu durƙusa a gabansa, su waɗanda baza su iya adana rayyukansu ba.
30Tsara mai zuwa zata yi masa hidima; zasu gaya wa tsara ta gaba game da Ubangiji.31Zasu zo su kuma yi magana game da adalcinsa; zasu faɗi abin da yayi ga mutanen da ba a haife su ba.

23

Zabura ta Dauda.

1Yahweh makiyayina ne; ba zan rasa komai ba.2Yana sa ni in kwanta a cikin korayen makiyayu; yana bi da ni kurkusa da kwantaccen ruwa.

3Ya maido da raina; yana bishe ni ta tafarku madaidaita domin sunansa.
4Ko da ina tafiya ta cikin kwari na inuwa mafi duhu, ba zan ji tsoron cutarwa ba tun da kana tare da ni; sandarka da kerenka na ta'azantar da ni.
5Ka shirya teburi a gabana a fuskar maƙiyana; ka shafe kaina da mai; ƙoƙona ya cika har yana zuba.
6Tabbas nagarta da amintaccen alƙawari zasu bi ni dukkan kwanakin raina; zan kuma zauna a cikin gidan Yahweh na lokaci mai tsawo sosai!

24

Zabura ta Dauda.

1Ƙasa ta Yahweh ce, da dukkan cikarta, duniyar, da dukkan mazauna cikinta.2Gama ya gina ta a bisa tekuna ya kuma ƙafa ta a bisa koguna.

3Wane ne zai haura tudun Yahweh? Wane ne zai tsaya a cikin wurinsa mai tsarki?4Shi wanda ke da hannuwa masu tsarki da kuma zuciya mai tsabta; wanda baya faɗar ƙarya, ba ya kuma yin rantsuwa domin yayi yaudara.
5Zai karɓi albarka daga wurin Yahweh da kuma adalci daga Allah na cetonsa.6Haka ya ke ga tsarar masu neman sa, masu neman fuskar Allah na Yakubu. Selah
7Tãda kanku, ku ƙyamare; ku tashi, madawwaman ƙofofi, domin Sarkin daraja ya shigo ciki!8Wane ne wannan Sarkin daraja? Yahweh, mai ƙarfi da girma; Yahweh, mai girma cikin yaƙi.
9Tãda kanku, ku ƙyamare; ku tashi, madawaman ƙofofi, domin Sarki na daraja ya shigo ciki!10Wane ne wannan Sarkin daraja? Yahweh mai runduna, shi ne Sarkin daraja. Selah

25

Zabura ta Dauda.

1A gare ka, Yahweh, na miƙa raina!2Allahna, Na dogara gare ka. Kar ka bari a wulaƙanta ni; kar ka bari maƙiyana suyi farincikin nasara a kaina.3Duk wanda yasa begensa a kan kada shi kunyata bari waɗanda suke aikata makirci babu dalili su ji kunya!

4Ka bayyana mani hanyarka, Yahweh; koya mani tafarkinka.5Bishe ni cikin gaskiyarka ka kuma koyar dani, gama kai ne Allah na cetona; na sa begena bisan ka a koda yaushe.
6Ka tuna, Yahweh, ayyukanka na tausayi da kuma amintaccen alƙawari; gama sun kasance tun tuni.7Kada kayi tunanin zunubaina na ƙuruciyata ko tayarwata; ka tuna da ni game da amintaccen alƙawarinka sabili da alherinka, Yahweh!
8Yahweh yana da nagarta kuma yana da alheri saboda haka yana koyawa masu zunubi tafarki.9Yana bi da kamili ga abin da ke dai-dai kuma yana koya masu hanyarsa.
10Dukkan tafarkun Yahweh na dawwamammiyar ƙauna ne da kuma aminci ga waɗanda ke kiyaye alƙawarinsa da kuma umarnansa tabbatattu.11Sabili da sunanka, Yahweh, ka gafarta zunubina, gama yana da girma sosai.
12Wane ne mutumin dake tsoron Yahweh? Ubangiji zaya umarce shi a hanyar da zaya zaɓa.13Rayuwarsa zata bi ta hanya mai kyau; kuma zuriyarsa zasu gaji ƙasar.
14Abokantakar Yahweh na ga waɗanda ke girmama shi, kuma yana sanar da alƙawarinsa gare su.15Idanuna suna bisa Yahweh koda yaushe, gama zaya ƙuɓutar da sawayena daga tarko.16Ka juyo gare ni kayi mani jinƙai; gama ni kaɗai ne kuma cikin ƙunci.
17Damuwoyin zuciyata sun yawaita; ka tsamo ni daga nawayata!18Ka dubi wahalata da kuma matsalolina; ka gafarta zunubaina.19Ka dubi maƙiyana, gama suna da yawa; suna ƙina da ƙiyayya mai zafi.
20Ka kare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari a wulaƙanta ni, gama ina samun mafaka a wurinka!21Bari nagarta da aminci su kiyaye ni, gama begena a cikinka ya ke.
22Ka kuɓutar da Isra'ila, Allah, daga dukkan wahalolinsa!

26

Zabura ta Dauda.

1Yi mani shari'a, Yahweh, gama nayi tafiya da aminci; na dogara ga Yahweh babu ja da baya.2Ka gwada ni, Yahweh, ka kuma jaraba ni; jaraba tsabtar cikin raina da zuciyata!3Gama amintaccen alƙawarinka na gaban idanuna, kuma ina tafiya cikin amincinka.

4Ban yi hurɗa da mutane marasa gaskiya ba, ko in yi cuɗanya da mutane macuta ba.5Na ƙi jinin taruwar masu aikata mugunta, ban kuma zauna da mugaye ba.
6Na wanke hannuna cikin rashin laifi, ina kuma zagaya bagadinka, Yahweh,7domin in raira waƙar yabo da ƙarfi in kuma shaida dukkan ayyukanka masu ban girma.8Yahweh, ina ƙaunar gidan da kake zama, inda ɗaukakarka take!
9Kada ka kawar dani tare da masu zunubi, ko raina tare da mutane masu marmarin shan jini,10waɗanda a cikin hannuwansu akwai mugun shiri, kuma hanunsa na dama ke cike da rashawa.
11Amma ni, zan yi tafiya cikin aminci; ka fanshe ni ka kuma yi mani jinƙai.12Sawayena suna tsaye a shimfiɗarɗiyar ƙasa; a cikin taruwa zan albarkaci Yahweh!

27

Zabura ta Dauda.

1Yahweh ne haske na da cetona; wane ne zan ji tsoro? Yahweh ne mafakar raina; wane ne zai razana ni?

2Lokacin da masu aikata mugunta suka taso mani domin su cinye namana, magabtana da maƙiyana suka yi tuntuɓe suka kuma faɗi.3Koda runduna zasu zagaye ni da gãba, zuciyata baza ta ji tsoro ba; koda yaƙi zai taso gãba dani, duk da haka zan kasance da ƙarfin hali.
4Abu guda ɗaya nayi roƙo ga Yahweh, zan kuma biɗi wannan; shi ne in zauna a cikin gidan Yahweh dukkan kwanakin raina, in dubi kyawun Yahweh in kuma yi bimbini a cikin haikalinsa.
5Gama a ranar wahala zaya ɓoye ni a cikin fukafukansa; a ƙarƙashin inuwar rumfarsa zaya suturce ni. Zaya ɗaukaka ni a bisa dutse mai tsawo!6Sa'an nan za a ɗaukaka kaina fiye da maƙiyana dake kewaye dani, zan kuma miƙa hadayu na farinciki a cikin rumfarsa! Zan raira waƙa in kuma yi waƙoƙi ga Yahweh!
7Yahweh ka ji, muryata a lokacin da nayi kuka! Kayi mani jinƙai, ka kuma amsa mani!8Zuciyata na ce da kai, "Nemi fuskarsa!" Na nemi fuskarka, Yahweh!
9Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni; kada ka juyar da bawanka daga gare ka cikin fushi! Tun dama kaine mai taimakona; kada ka yashe ni ko kayi banza dani, Allah na cetona!10Koda mahaifina ko mahaifiyata sun yashe ni, Yahweh zaya karɓeni.
11Ka koya mani tafarkinka, Yahweh! Ka bishe ni a daidaitacciyar hanya saboda maƙiyana.12Kada ka bayar da ni ga nufin maƙiyana, gama shaidun ƙarya sun tashi gãba dani, suna kuma huro da ta'addanci!
13Da mene ne zai faru dani da ba domin na yarda cewa zan ga alherin Yahweh a cikin ƙasar masu rai ba?14Ka jira ga Yahweh; yi ƙarfi, bari zuciyarka ta ƙarfafa! Saurari Yahweh!

28

Zabura ta Dauda.

1A gare ka, Yahweh, nayi kuka; dutsena, kada kayi banza da ni. Idan baka amsa mani ba, zan harɗe da waɗanda ke gangarawa zuwa kabari.2Kaji ƙarar roƙona a lokacin da nayi kira domin taimako daga gare ka, a lokacin da na tãda hannuwa na zuwa wurinka mai tsarki!

3Kada ka kawar dani tare da masu aikata mugunta, su masu aikata laifuffuka, su dake faɗin alheri da maƙwabtansu da baki amma zuciyarsu cike take da mugunta.4Ka basu dai-dai abin da ayyukansu ya dace dasu da kuma abin da muguntarsu ta wajaba, ka biya su bisa ga aikin hannuwansu ka kuma mayar masu bisa ga ladarsu.5Domin basu gane da ayyukan Yahweh ba ko ayyukan hannuwansa, zaya buga su ƙasa baza a ƙara gina su ba.
6Albarka ga Yahweh domin ya ji muryar kukana!7Yahweh ne ƙarfina da garkuwata; zuciyata ta dogara gare shi, na kuma sami taimako. Saboda haka zuciyata tayi farinciki ƙwarai, zan kuma yabe shi da raira waƙoƙi.8Yahweh ne karfin mutanensa, kuma shi ne maɓoyar ceto na shafaffensa.
9Ka ceci mutanenka ka kuma albarkaci gãdonka. Ka zama makiyayinsu ka kuma ɗauke su har abada.

29

Zabura ta Dauda.

1Bada yabo ga Yahweh, ku 'ya'yan Allah! Bada yabo ga Yahweh domin ɗaukakarsa da ƙarfinsa.2Ba Yahweh ɗaukakar da ta cancanci sunansa. Durƙusa ƙasa ga Yahweh cikin jamalin tsarkinsa.

3An ji muryar Yahweh har bisa ruwaye; Allah maɗaukaki ya yi tsawa, Yahweh na tsawa bisa ruwaye masu yawa.4Muryar Yahweh na da cikakken iko; Muryar Yahweh mai daraja ne.5Muryar Yahweh na fasa itatuwan sida; Yahweh na fasa gutsu-gutsu itatuwan sida na Lebanon.
6Yana sa Lebanon tayi tsalle kamar ɗan maraki da kuma Dutsen Hamon kamar ɗan shanu.7Muryar Yahweh na aikar da harshen wuta.8Muryar Yahweh na girgiza hamada; Yahweh na girgiza hamadar Kadesh.
9Muryar Yahweh nasa rimaye su tanƙware tana kuma kware daji a fili. Kowanne a cikin haikali na cewa, "Daukaka!"10Yahweh na zaman sarki a bisa ruwa mai ambaliya; Yahweh na zaman sarki har abada.
11Yahweh yana bada karfi ga mutanensa; Yahweh yana albarkatar mutanensa da salama.

30

Zabura; waƙar da aka yi a keɓewar haikali. Zabura ta Dauda.

1Zan girmama ka, Yahweh, gama ka tã dani sama kuma baka bari maƙiyana sun yi farinciki bisa na ba.2Yahweh Allahna, nayi kuka gare ka domin taimako, ka kuma warkar dani.3Yahweh, ka tsamo raina daga Lahira; ka adana ni da rai kada in gangara ƙasa zuwa kabari.

4Raira yabbai ga Yahweh, ku amintattunsa! Ku bada godiya a lokacin da kuka tuna da tsarkinsa.5Gama fushin sa na lokaci kaɗan ne; amma tagomashinsa na har abada ne. Kuka na zuwa da dare ne, amma farinciki na zuwa da safe.
6Da ƙarfin hali nace. "Ba zan jijjigu ba."7Yahweh, da tagomashinka ka kafa ni kamar ƙaƙƙarfan tsauni; amma daka ɓoye fuskarka, na shiga damuwa.8Nayi kira gare ka, na kuma nemi tagomashi daga wurin Ubangijina!
9Wacce riba ce ke cikin mutuwata, idan na gangara cikin kabari? Ko turɓaya zata yabe ka? Zata furta tabbatattun amincinka?10Ka saurara, Yahweh, kayi mani jinƙai! Yahweh, ka zama mai taimakona.
11Ka juyar da makokina zuwa rawa; ka cire mani tsumma ka kuma sanya mani rigar farinciki.12Yanzu ɗaukakata zata yi maka waƙar yabo kuma ba zata yi shuru ba; Yahweh Allahna, zan yi maka godiya har abada!

31

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta Dauda.

1A cikin ka, Yahweh, na sami mafaka; kada ka barni in wulaƙanta. Ka kuɓutar dani cikin adalcinka.2Ka saurare ni; Ka kuɓutar dani da sauri; ka zama dutsen mafakata, ƙaƙƙarfar maɓoya domin cetona.

3Gama kai ne dutsena da kuma mafakata; Saboda haka sabili da sunanka, ka shugabance ni ka kuma bishe ni.4Ka ƙwato ni daga cikin tãrun da suka ɓoye domi na, gama kai ne maɓuyata.
5A cikin hannuwanka nake bada ruhuna; zaka fanshe ni, Yahweh, Allah madogarata.6Na ƙi jinin waɗandɑ s‌uke bautawa gumakan banza, amma na dogara ga Yahweh.7Zan yi murna da kuma farinciki cikin amintaccen alƙawarinka, gama ka ga ƙuncina; ka san matsalar raina.
8Baka miƙa ni a cikin hannuwan maƙiyana ba. Ka kafa ƙafafuwana a buɗaɗɗen wuri mai faɗi.9Kayi mani jinƙai, Yahweh, gama ina cikin ƙunci; idanuna sun yi nauyi da azaba tare da raina da jikina.
10Gama raina yayi nauyi da makoki kuma shekaruna na cike da nishe-nishe. Ƙarfina ya gaza sabili da zunubina, ƙasusuwana suna lalacewa sarai.11Sabili da maƙiyana, mutane sun yi banza dani; maƙwabtana suka gaji da yanayina, kuma waɗanda suka san ni suka tsorata. Waɗanda suka gamu dani a hanya suka gudu daga gare ni.
12An manta da ni kamar mataccen mutum wanda babu wanda ke tunaninsa. Ina kama da fasasshiyar tukunya.13Gama na ji raɗe-raɗe masu yawa, labarai masu ban tsoro daga kowanne sashe sa'ad da suke shiri gãba da ni. Sun yi shiri domin su ɗauke raina.
14Amma na dogara gare ka, Yahweh; Na ce, "Kai ne Allahna."15Ƙaddarata na cikin hannuwanka. Ka ‌kuɓutar dani daga hannuwan magabtana daga kuma waɗanda suke fafarata.16Bari fuskarka ta haskaka bisa bawanka; ka cece ni cikin amintaccen alƙawarinka.
17Kada ka bar ni in wulaƙantu, Yahweh; gama na yi kira gare ka! Bari mugu ya wulaƙanta! Bari suyi shuru a cikin Lahira.18Bari harsuna masu ƙarya suyi shuru su dake magana gãba da mai adalci da renin girma da kuma tozartarwa.
19girman alherinka da ka shirya wa masu girmama ka, abin da kake aiwatar wa domin waɗanda suka yi mafaka a cikinka a gaban dukkan 'ya'yan talikai!20A cikin mahallin bayyanuwarka, ka ɓoye su daga makircin mutane. Ka ɓoye su a cikin mahalli daga ta'addancin harsuna.
21Mai albarka ne Yahweh, gama ya nuna mani amintaccen alƙawarinsa mai ban mamaki a lokacin da nake a cikin birnin kwanto.22Ko da ya ke na faɗa cikin gaggawata, "An datse ni daga fuskarka," duk da haka ka ji roƙona domin taimako lokacin da nayi kuka gare ka.
23Oh, ƙaunaci Yahweh, dukkan ku amintattun mabiya. Yahweh yana tsare amintattu, amma yana sãka wa masu girman kai.24Ku ƙarfafa kuyi ƙarfi, dukkan ku dake dogara cikin Yahweh domin taimako.

32

Zabura ta Dauda. Waƙar hikima.

1Mai albarka ne taliki wanda an gafarta masa kurakuransa, wanda aka rufe zunubinsa.2Mai albarka ne mutum wanda Yahweh ba ya lisafta laifi bisansa kuma wanda babu algus cikin ruhunsa.

3Da na yi shuru, ƙasusuwana suna lalacewa sa'ad da nake nishe-nishe dukkan yini.4Gama rana da dare hannunka na da nauyi bisana. ƙarfina ya gaza kamar lokacin fãrin kaka.
5Sa'an nan na furta zunubi na gare ka, ban kuma ƙara ɓoye laifi na ba. Na ce, "Zan furta kurakuraina ga Yahweh," ka kuma gafarta mani ladar zunubina.6Saboda wannan, dukkan waɗanda ke na allahntaka suna adu'a a gare ka a lokacin gwagwarmaya mai girma. Sa'an nan lokacin da ruwaye masu hauka suka taso, baza su cimma waɗannan mutane ba.
7Kai ne maɓuyata; zaka tsare ni daga wahala. Zaka zagaye ni da waƙoƙin nasara.8Zan umarce ka in koya maka hanyar da zaka bi. Zan umarce ka da idanuna a bisanka.
9Kada ka zama kamar doki ko kamar alfadari, wanda ba shi da fahimta; sai tare da linzami da ragama domin a bi da su inda ake so su tafi.10Mugu yana da baƙinciki mai yawa, amma amintaccen alƙawarin Yahweh zai zagaye wanda ya dogara gare shi.
11Yi murna cikin Yahweh, da farinciki, ku adalai; yi sowa ta farinciki, dukkan ku masu tsabta cikin zuciya.

33

1Yi farinciki cikin Yahweh, ku adalai; Yin yabo ya dace ga adalai.2Kuyi godiya ga Yahweh da molo; yi waƙoƙin yabo gare shi da molo mai tsarkiya goma.3Raira sabuwar waƙa gare shi; ku yi kiɗa da ƙwarewarku kuna raira waƙa tare da farinciki.

4Gama maganar Yahweh mai adalci ce, kuma dukkan abin da ya aikata dai-dai ne.5Yana ƙaunar adalci da shari'a. Duniya na cike da amintaccen alƙawarinsa.6Da maganar Yahweh aka hallici sammai, kuma dukkan taurari sun kasance ne ta numfashin bakinsa.
7Yana tara ruwayen teku wuri ɗaya kamar tudu; ya ajiye tekuna cikin ɗakunan ajiya.8Bari dukkan ƙasar taji tsoron Yahweh; Bari dukkan mazaunan duniya su tsaya cik a gabansa.9Gama ya yi magana, aka kuma aikata; ya umarta, ya kuma tabbata.
10Yahweh yana lalatar da ƙawancen al'ummai; yana mulki akan shirye-shiryen mutane.11Shirin Yahweh ya tsaya har abada, shirye-shiryen zuciyarsa ga dukkan tsararraki.12Mai albarka ce al'ummar da Yahweh ne Allahnta, mutanen da ya zaɓa abin gãdonsa.
13Yahweh yana gani daga sama; yana ganin dukkan mutane.14Daga wurin da ya ke zama, yana duban dukkan masu zama cikin ƙasar.15Shi wanda ya ke shirya zuciyarsu dukka yana la'akari da ayyukansu.
16Babu sarkin da zai tsira sabili da yawan runduna; jarumi baya tsira ta dalilin ƙarfinsa.17Doki tsaro ne na banza domin nasara; duk da ƙarfinsa, ba zai iya ƙubutarwa ba.
18Duba, idanun Yahweh na bisan waɗanda ke tsoronsa, a bisa waɗanda suka dangana bisa amintaccen alƙawarinsa19domin ya kuɓutar da rayukansu daga mutuwa ya kuma kiyaye su da rai a lokacin yunwa.
20Muna jiran Yahweh; shi ne taimakonmu da kuma garkuwarmu.21Zuciyarmu tayi farinciki cikinsa, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
22Bari amintaccen alƙawarinka, Yahweh, ya kasance da mu a lokacin da muka kafa begenmu cikinka.

34

Zabura ta Dauda; lokacin da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, wanda ya kore shi waje.

1Zan yabi Yahweh a dukkan lokaci, Yabonsa zai kasance a bakina koda yaushe.

2Zan yabi Yahweh! Bari ƙuntattu su ji su kuma yi farinciki.3Ku yabi Yahweh tare da ni, bari mu ɗaukaka sunansa tare.
4Na nemi Yahweh kuma ya amsa mani, ya kuma ba ni nasara bisa dukkan tsorona.5Waɗanda ke duban sa suna haskakawa, kuma fuskarsu ba ta ji kunya ba.6Wannan matsattsen mutum yayi kuka Yahweh kuma ya ji ya kuma cece shi daga dukkan matsalolinsa.
7Mala'ikan Yahweh na zagaye waɗanda ke tsoronsa ya kuma ƙubutar da su.8Ku ɗanɗana ku kuma gani cewa Yahweh na da kyau. Mai albarka ne mutum wanda ke ɓuya cikinsa.9Ku ji tsoron Yahweh, ku mutanensa masu tsarki. Babu rashi ga waɗanda ke tsoronsa.
10'Ya'yan zakuna wasu lokuttan suna rasa abinci su kuma ji yunwa, amma waɗanda suka nemi Yahweh baza su rasa kowanne abu mai kyau ba.11Ku zo, 'ya'ya maza, ku saurare ni. Zan koya maku jin tsoron Yahweh.
12Wanne mutum ne mai biɗar rai ya ke kuma ƙaunar ranaku masu yawa, domin ya ga alheri?13To, sai ka tsare harshenka daga faɗin mugunta leɓunanka kuma daga faɗin ƙarya.14Ka juyo daga barin mugunta ka kuma aikata nagarta. Nemi salama ka kuma bi ta.
15Idanun Yahweh suna bisa masu adalci kuma kunnuwansa suna karkatawa zuwa ga kukansu.16Fuskar Yahweh na gãba da waɗanda ke aikata mugunta, domin a datse tunawa da su daga duniya.17Masu adalci sun yi kira Yahweh kuma yana kuɓutar da su daga dukkan matsalolinsu.
18Yahweh yana kurkusa da masu karyayyar zuciya, kuma yana ceton waɗanda aka ƙuntatawa a cikin ruhu.19Da yawa suke matsalolin masu adalci, amma Yahweh yana ƙubutar da su daga dukkan su.20Ya kare dukkan ƙasusuwansa, babu ko ɗaya daga cikinsu da za a karya.
21Mugunta zata kashe mai mugunta. Waɗanda suka ƙi masu adalci za a hallakar da su.22Yahweh yana ƙubutar da rayukan bayinsa. Babu ɗaya daga cikin waɗanda ke neman mafaka wurinsa da za a kayar.

35

Zabura ta Dauda.

1Yahweh, ka yi gãba da waɗanda ke aiki gãba da ni; ka yaƙi waɗanda ke yaƙi da ni.2Ka ɗauki garkuwarka ƙarama da babba; tashi ka taimake ni.3Yi amfani da mashi da gatarin yaƙin ka gãba da waɗanda ke runtuma ta; ka ce da raina, "Ni ne cetonka."

4Bari su waɗanda ke neman raina su ji kunya su kuma faɗi. Bari waɗanda ke shirin cuta na a juyar da su a kuma hargitsa su.5Bari su zama kamar ƙaiƙayi a fuskar isaka, a sa'ad da mala'ikan Yahweh ke korar su.6Bari hanyar su ta duhunta tana kuma zamewa, a sa'ad da mala'ikan Yahweh ke runtumar su.
7Babu dalili suka shirya mani tarkonsu; Babu dalili suka haƙa rami domin raina.8Bari halakarwa ta auko masu ba zato. Bari tarkon da suka ɗana ya kama su. Bari su faɗa ciki, ga hallakarsu.
9Amma zan yi farinciki cikin Yahweh in kuma yi murna cikin cetonsa.10Dukkan ƙasusuwana za su ce, "Yahweh, wane ne kamar ka, wanda ke ƙuɓutar da ƙuntattu daga waɗanda suka fi ƙarfinsu da kuma matalauta da kuma mabuƙata daga waɗanda ke ƙoƙarin yi masu fashi?"
11Shaidu marasa adalci sun tashi; sun yi mani zargin ƙarya.12Sun sãka mani nagarta da mugunta. Ina cike da ɓacin rai.
13Amma a lokacin da suke ciwo, na sanya tsummokara; na yi azumi a madadinsu da kaina sunkuye ga ƙirjina.14Na yi tafiya cikin ƙunci domin ɗan'uwana; Na durƙusa cikin makoki domin mahaifiyata.
15Amma da nayi tuntuɓe, suka yi murna suka taru wuri ɗaya; suka taru wuri ɗaya gãba da ni, kuma suka bani mamaki. Suka kawo mani farmaƙi babu fasawa.16Da rashin girmamawa samsam suka yi mani ba'a; suka tauna mani haƙoransu.
17Ubangiji, har yaushe zaka duba? Ka ƙuɓutar da raina daga farmaƙinsu mai hallakarwa, raina daga zakuna.18Sa'an nan zan gode maka a babban taro mai girma; Zan yabe ka a cikin mutane masu yawa.
19Kada ka bar maƙiyana masu ƙarya su yi murna a kaina; kada ka barsu su aiwatar da mugun shirinsu.20Gama basu maganar salama, amma suka shirya maganganun ƙarya gãba da waɗanda ke zaman salama cikin ƙasar.
21Sun buɗe bakunansu da girma gãba da ni; suka ce, "Aha, Aha, idanunmu sun gan shi."22Ka gan shi, Yahweh, kada ka yi shuru; Ubangiji, kada kayi nisa dani.23Ka tãda kanka ka kuma farka domin ka kare ni; Allahna da Ubangijina, ka kare bukatata.
24Ka kãre ni, Yahweh Allahna, sabili da adalcinka; kada ka bar su suyi murna a kaina.25Kada ka bari su faɗa a cikin zuciyarsu, Aha, mun sami abin da muke nema." Kada ka bar su su ce, "Mun haɗiye shi."26Ka basu kunya ka kuma ruɗar da waɗanda ke niyyar cutar da ni. Bari waɗanda ke cakuna ta a rufe su da kunya da ƙasƙanci.
27Bari su dake marmarin kuɓutata suyi sowa ta murna su kuma ji daɗi; bari koyaushe su ce, "Bari Yahweh ya ɗaukaka, shi da ya ke jin daɗi cikin wadatar bawansa."28Sa'an nan zan faɗi game da shari'arka in kuma yabe ka dukkan yini.

36

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta Dauda bawan Yahweh.

1Mugun mutum yana zancen kurakuransa daga cikin zuciyarsa, babu tsoron Allah a idanunsa.2Gama yana yiwa kansa ta'aziya, da tunanin cewar zunubansa ba zasu tonu ba ko kuma a ƙi su.

3Maganganunsa na zunubi ne da yaudara; ba ya son ya zama mai hikima ya kuma aikata nagarta.4A lokacin da ya ke kwance a gado, yana shirya yadda zai yi zunubi; ba ya ƙin mugunta.
5Amintaccen alƙawarinka, Yahweh, na kaiwa har zuwa sammai; amincinka na kaiwa zuwa cikin giza-gizai.6Adalcinka na kama da duwatsun Allah; shari'unka na kama da manyan zurfafa. Yahweh, ka kare talikai da dabbobi.
7Yaya darajar amintaccen alƙawarinka ya ke, Allah! Bil'adama na fakewa a ƙarƙashin inuwar fukafukanka.8Zasu ƙoshi daga yalwar abincin gidanka; zaka sa su sha daga cikin koginka mai manyan albarku.9Domin a gare ka akwai maɓulɓular rai; cikin haskenka zamu ga haske.
10Ka kawo gare ni amintaccen alƙawarinka cikakke ga waɗanda suka san ka, kariyarka zuwa ga kamilai a zuci.11Ka da ka bar ƙafafun mai girman kai shi zo kusa dani. Ka da ka bar hannun mugaye su kore ni da nisa.12A can mugaye suka faɗi; aka buga su ƙasa basu kuma iya tashi ba.

37

Zabura ta Dauda.

1Kada ka damu da masu mugunta; kada ka ji ƙyashin waɗanda ke ayyukan rashin adalci.2Gama zasu bushe da wuri kamar ciyawa, su kuma yanƙwane kamar korayen tsire-tsire.

3Ka dogara ga Yahweh kuma ka yi abin da ke nagari; ka zauna a ƙasar ka yi kiwo cikin aminci.4Sa'an nan ka yi murna da al'amuran Yahweh, kuma zai biya maka buƙatun zuciyarka.
5Ka miƙa hanyoyinka ga Yahweh; ka dagara gare shi, kuma zai yi abu a madadinka.6Zai nuna aɗalcinka kamar hasken rana da rashin laifinka kamar rana tsaka.
7Ka natsu a gaban Yahweh kuma kayi jira da haƙuri domin sa. Kada ka ji haushi idan wani ya yi nasara da abin da ya ke yi, ko sa'ad da ya ke ƙulla mugunta.
8Kada ka ji haushi da takaici. Kada ka damu. Wannan na bada damuwa ne kawai.9Za a datse miyagu, amma waɗanda ke jiran Yahweh zasu gãji ƙasar.10A ɗan lokaci ƙaɗan mugun mutum zai ɓace; zaka dubi wurinsa, amma ba zai kasance ba.
11Amma masu tawali'u zasu gãji ƙasar kuma zasu yi murna da gagarumar wadata.12Mugun mutum yana shirya maƙarƙashiya gãba da adali yana kuma cizon haƙora gãba da shi.13Ubangiji yana yi masa dariya, gama yana ganin zuwan ranarsa.
14Mugaye sun zare takubbansu suka kuma tanƙware bakkunansu don su kãda waɗanda ake masu danniya da masu buƙata, su kashe waɗanda ke da nagarta.15Takkubansu zasu soke zukatansu, kuma bakkunansu zasu kakkarye.
16Gara ƙanƙanen abin da mutumin kirki ya ke da shi da yawan abubuwan mugayen mutane.17Gama za a ƙarɓe ƙarfin mugayen mutane, amma Yahweh zai taimaki adalai
18Yahweh yana lura da marasa abin zargi a kowacce rana, kuma gãdonsu zai kasance har abada.19Ba za su ji kunya a lokacin masifa ba. Sa'ad da Yunwa tazo, zasu samu isasshen abinci.
20Amma mugaye zasu lalace. Maƙiyan Yahweh za su zama kamar darajar ciyawa; za a cinye su su ɓace kamar hayaƙi.21Mugu yakan ci bashi amma ba ya biya, amma adali yana bayarwa hannu sake.
22Waɗanda Allah ya sawa albarka zasu gãji ƙasar; waɗanda ya la'anta zasu zama korarru.23Ta wurin Yahweh ne hanyoyin mutum ke kafuwa, mutumin da hanyarsa amintacciya ce a fuskar Allah.24Ko da ya ke yana tuntuɓe, ba zai faɗi ba, gama Yahweh na riƙe shi da hannunsa.
25Dã ni yaro ne kuma yanzu na tsufa; ban taɓa ganin an yashe da adali ba ko kuma 'ya'yansa na roƙon abinci.26Dukkan yini yana yin alheri yana ba da rance, kuma 'ya'yansa sun zama albarka.27Ka bar mugunta kayi abin da ke dai-dai; zaka cetu har abada.
28Gama Yahweh yana ƙaunar adalci kuma baya rabuwa da amintattun masu binsa. Yana kiyaye su har abada, amma zuriyar mugaye zasu zama korarru.29Adalai zasu gãji ƙasar su zauna ciki har abada.30Bakin adali yana maganar hikima da kuma ƙara adalci.
31Shari'ar Allahnsa na zuciyarsa; ƙafafunsa ba za su yi santsi ba.32Mugu yakan yi fakon adali ya nemi hanyar kashe shi.33Yahweh ba zai bar shi a hannun mugun ba ko kuwa ya yanke masa hukunci sa'ad da ya ke masa shari'a.
34Ka jira Yahweh ka kuma kiyaye hanyoyinsa, zaya kuma ɗaga ka sama ka mallaki ƙasar. Za ka gani sa'ad da ake korar mugaye.
35Na ga mugu da azzalumin taliki ya baje kamar koren itace a ƙasarsa ta asali.36Amma sa'ad da na sãke wucewa kuma, bai kasance a wurin ba. Na neme shi, amma ba ya samuwa.
37Dubi mutumin kirki, ka kuma lura da adali; gaba zai zama da kyau ga mutumin salama,38Masu zunubi kuwa za a hallaka su ƙaƙaf; za a kuma share zuriyar mugun mutum.
39Ceton adalai yakan zo daga Yahweh ne; yakan kiyaye su a lokatan damuwa.40Yahwe ya taimake su ya kuɓutar da su, Ya kuɓutar dasu daga mugaye ya cece su saboda sun sami garkuwa a cikinsa.

38

Zabura ta Dauda, domin ya kawo tunawa.

1Yahweh, kada ka tsauta mani a cikin fushinka; kada ka hukunta ni a cikin hasalarka.2Gama kibiyoyinka suna sukana, kuma hannunka na matse ni har ƙasa.

3Dukkan jikina na ciwo saboda hasalarka; babu lafiya a ƙasusuwana saboda laifina.4Gama zunubaina sun fi ƙarfina; sun zamar mani kaya mai nauyi da yawa.
5Raunukana sun harbu suna wari saboda wawancin zunubaina.6Ana dakatar dani ana wulaƙanta ni kowacce rana; Ina ta makoki dukkan tsawon rana.
7Gama daga ciki, ina cike da zafin ciwo; babu lafiya a jikina.8An sandare ni an ragargaza ni; ina gunaguni saboda fushin zuciyata.
9Ubangiji kana sane da buƙatar zuciyata, kuma gunagunina basa ɓoyu ba daga gare ka.10Zuciyata na bugawa, ƙarfina na ƙarewa, bana kuma gani sosai.
11Abokaina da aminai sun ƙaurace mani saboda yanayina; maƙwabtana na tsaye daga nesa.12Waɗanda ke so su kashe ni sun ƙafa mani tarko. Su waɗanda ke neman yi mani rauni suna maganar hallakarwa da faɗin kalmomin ruɗu dukkan tsawon rana.
13Amma ni, ina kamar kurman mutum kuma bana jin komai; ina kamar beben da ba ya iya faɗin komai.14Ina kamar mutumin da ba ya ji kuma ba shi da amsa.
15Tabbas ina jiranka, Yahweh; zaka amsa, Ubangiji, Allahna.16Na faɗi haka saboda maƙiyana ba zasu yi murna a kan damuwata ba. Idan tafin ƙafata ya zame, zasu yi mani mugayen abubuwa.
17Gama ina gab da mutuwa, kuma ina cikin wahala kowacce sa'a.18Na furta laifofina; na kuma damu da zunubina.
19Amma maƙiyana na da yawa; waɗanda suka ƙi ni cikin kuskure na da yawa.20Suna rama mani nagarta da mugunta; suna ta tuhuma ta koda ya ke ina neman abin da ke nagari.
21Kada ka yashe ni, Yahweh; Allahna, kada ka tsaya nesa dani.22Ka zo da sauri ka taimakeni, Ubangiji, cetona.

39

Domin shugaban mawaƙa, domin Yedutan. Zabura ta Dauda.

1Na yi shiri, "Zan lura da furcin da zan yi saboda kada in yi zunubi da harshe na. Zan sa wa bakina takunkumi a lokacin da nake wurin da mugu ya kasance."

2Na yi shiru; Na riƙe maganganuna daga faɗin wani abu koda nagari ne, shanwuta kuma ta ƙaru.3Zuciyata ta yi zafi; sa'ad da nayi tunani a kan abubuwan nan, yana ci kamar wuta. Sa'an nan a ƙarshe nayi magana.
4"Yahweh, kasa in san yaushe ne ƙarshen rayuwata da tsawon kwanakina. Ka nuna mani ina kurkusa da matuwa.5Duba, kã maida kwanakina kamar tsawon hannuna, kuma rayuwata kamar ba komai take ba a wurinka. Hakika kowanne mutum lumfashi ɗaya ne. Selah
6Hakika kowanne mutum yana tafiya kamar inuwa. Hakika dukkan kowa yana hanzari ya tattara arziki ko da yake basu san wanda zai karbe su ba.7Yanzu, Ubangiji, domin me nake jira? Kai ƙaɗai ne begena.
8Ka cece ni daga zunubaina; kada ka bari in zama abin ba'a ga wawaye.9Na yi shiru kuma bazan iya buɗe bakina ba, saboda kai ne kayi haka.
10Ka daina yi mani rauni; na karaya ta wurin bugun hannunka.11Sa'ad da kake horar da mutane don zunubi, kakan cinye abubuwan da suke marmari kamar asu; hakika dukkan mutane ba komai bane banda tururi kawai. Seleh
12Ka ji addu'ata, Yahweh, ka saurare ni; ka saurari kukana! Kada ka zama kurma a gare ni, gama ni kamar baƙo ne tare da kai, ɗan gudun hijira kamar yadda dukkan kakannina suke.13Ka juyar da harararka daga gare ni domin in sake yin murmushi kafin in mutu,"

40

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta Dauda.

1Na jira Yahweh da haƙuri; ya saurare ni ya ji kukana.2Ya fitar dani daga rami mai furgitarwa, daga taɓo, ya sa ƙafafuna a kan dutse ya tsare takawata.

3Ya sa sabuwar waƙa a bakina, yabo ga Allahnmu. Da yawa zasu gani su kuma girmama shi su dogara ga Yahweh.4Mai albarka ne mutumin da ya maida Yahweh madogararsa kuma baya girmama masu fahariya ko waɗanda suka juya daga gare shi zuwa ƙarairayi.
5Da yawa suke, Yahweh Allahna, ayyukan al'ajiban da ka yi, kuma babu wanda zai iya ƙirga abubuwan da kake tunani gme da mu; Idan na yanke shawara in yi magana a kan su, za su fi abin da za a iya ƙirgawa.6Ba ka buƙatar hadaya ko baiko, amma ka buɗe kunnuwana; ba ka buƙatar baye-baye na ƙonawa ko baye-baye na zunubi.
7Sa'an nan na ce, "Duba, Na zo; a rubuce ya ke a game dani cikin littafin Yahweh.8Ina jin daɗin yin nufinka, Allahna, shari'unka na cikin zuciyata."9Na yi shelar nagartattun labaran ayyukanka na adalci a babban taron jama'a; Yahweh, ka san leɓunana basu dena yin wannan ba.
10Ban ɓoye ayyukan adalcinka a zuciyata kaɗai ba; Na furta amincinka da cetonka; Ban ɓoye amintaccen alƙawarinka ko madawwamiyar ƙaunarka daga babban taron jama'a ba.11Kada ka yi jinkirin yi mani ayyukan jinƙai; ka bar amintaccen alƙawarinka da madawwamiyar ƙaunarka su kiyaye ni.
12Damuwoyin da basu ƙidayuwa sun kewaye ni; alhakin zunubaina ya tarar da ni har yasa bana iya ganin wani abu; Sun fi gashin kaina yawa, kuma zuciyata ta karaya.13In ka yarda, Yahweh, ka cece ni; ka yi hanzari ka taimake ni, Yahweh.
14Ka sa waɗanda suke son kashe ni su sha kunya da yawa. Kasa su koma baya a ci nasara a kansu, ka kawo waɗanda ke murna saboda wahalar da nake sha, cikin ƙasƙanci.15Kasa su razana saboda kunya, su waɗanda ke yi mani ba'a, "
16Amma bari dukkan waɗanda ke neman ka su yi farinciki da murna a cikinka; ka sa duk mai ƙaunar cetonka ya ci gaba da cewa, "A yabi Yahweh."17Na talauce na zama mabuƙaci; duk da haka Ubangiji yana tunani a kai na. Kai ne mai taimako na kuma ka zo domin ka cece ni; kada ka yi jinkiri, Allahna.

41

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta Dauda.

1Mai albarka ne wanda ke kulawa da marasa ƙarfi; a ranar masifa, Yahweh zai 'yantar da shi.2Yahweh zai kiyaye shi ya kare shi, kuma zai zama da albarka a duniya; Yahweh ba zai bar shi ga nufin maƙiyansa ba.3Yahweh zai yi masa gudummawa a gadon wahalarsa; zaka maida gadonsa na ciwo zuwa gadonsa na warkarwa.

4Na ce, "Yahweh, ka yi mani jinƙai! Ka warkar dani, gama na yi maka laifi."5Maƙiyana suna muguwar magana gãba da ni, cewa, 'Yaushe ne zai mutu kuma sunansa ya lalace?'6Idan maƙiyina ya zo gani na, ya furta maganganun banza; zuciyarsa na ƙoƙarin sanin dukkan matsalolina; sa'ad da ya tafi daga gare ni, sai ya gaya wa kowa game da su.
7Dukkan waɗanda ke ƙi na na raɗa da juna gãba da ni; gãba da ni suna fatan shan wahalata.8Suna cewa, "Mugun ciwo ya make shi; yanzu da ya ke kwance ƙasa, ba zai ƙara tashi ba."9Lallai, ko abokina na ƙut da ƙut, da na yarda da shi, wanda ya ci gurasata, ya juya mani baya.
10Amma kai, Yahweh, ka yi mani jinƙai ka ɗaga ni sama saboda in mai da martani.11Ta wannan na san kana farinciki dani, gama maƙiyina bai yi murna a kaina ba.12Amma ni, ka tallefe ni cikin aminncina kuma zaka kiyaye ni a fuskarka har abada.
13Bari Yahweh, Allah na Isra'ila a yabe shi daga dawwama zuwa dawwama. Amin da Amin. Littafi Biyu

42

Domin shugaban mawaƙa. 'Salon waƙa ta 'ya'yan Kora.

1Kamar yadda mariri ke marmarin rafukan ruwa, haka nake ƙishinka, Allah.2Ina ƙishin Allah, Allah mai rai, yaushe zan zo in bayyana a gaban Allah?

3Hawayena sun zama abincina dare da rana, lokacin da maƙiyana kullum suna cewa dani, "Ina Allahnka?"4Waɗannan abubuwan nake tunawa da su yayin da nake zubo raina: yadda na tafi tare da taron mutane na jagorance su zuwa gidan Allah tare da muryar jin daɗi da yabo, babban taro na shagalin buki.
5Me yasa ka rusuna ƙasa, raina? Me yasa kake damuwa daga can ciki? Yi bege ga Allah, gama zan ƙara yabonsa wanda shi ne cetona.6Allahna, raina ya rusuna ƙasa a can ciki, don haka na tuna da kai daga ƙasar Yordan, daga ƙololuwar Dutsen Hamon, kuma daga tudun Miza.
7Zurfi na kira ga zurfi da jin ƙarar kwararowar ruwanka; dukkan raƙuman ruwanka da matsirgan ruwanka sun mamaye ni.8Duk da haka Yahweh zai umarci amintaccen alƙawarinsa da rana; da dare waƙarsa zata kasance tare da ni, addu'a ce ga Allah na rayuwata.
9Zan yi magana ga Allah, dutsena, "Me yasa ka mance da ni" Me yasa nake makoki saboda danniyar maƙiyina?"10Kamar da takobi a ƙasusuwana, maƙiyana ke yi mani zargi, yayin da kullum suke cewa dani, "Ina Allahnka?"
11Me yasa kake rusuna a ƙasa, raina? Me yasa kake damuwa can ciki? Yi bege cikin Allah, gama kuma zan yabe shi wanda shi ne cetona da Allahna.

43

1Kawo mani adalci, Allah, kayi mani taimakon kãriya a kan al'umma marasa tsoron ka.2Gama kai ne Allah na ƙarfina. Meyasa ka yashe ni? Me yasa nake tafiya cikin makoki saboda muzgunawar maƙiya?

3Oh, ka aiko da haskenka da gaskiyarka, su jagorance ni. su kawo ni ga tudunka mai tsarki da wurin zamanka.4Sa'an nan zan yi tafya zuwa ga bagadin Allah, ga Allah matuƙar jin daɗina. Zan yabeka da garaya, Allah, Allahna.
5Me yasa ka rusuna ƙasa, raina? Me ya sa kake damuwa can ciki? Yi bege cikin Allah, gama zan ƙara yabonsa wanda shi ne cetona da Allahna.

44

Domin shugaban mawaƙa. Salon waƙa ta 'ya'yan Kora.

1Mun ji da kunnuwanmu, Allah, Kakanninmu suka faɗa mana irin aikin da ka yi a kwanakinsu, a kwanakin dã.2Ka kore al'ummai da hannunka, amma ka dasa mutanenmu; ka azabci mutane, amma ka baza mutanenmu cikin ƙasar.

3Gama basu samu mallakar ƙasar ta takobin kansu ba, ba kuma ƙarfin kansu ba ne ya cece su; amma hannun damanka da ƙarfinka da hasken fuskarka ne, saboda yi tagomashi gare su.4Allah, kai ne sarkina; ka umarta nasara domin Yakubu.
5Da taimakonka zamu tura maƙiyanmu; da sunanka za mu tattakesu, waɗanda suka tashi gãba da mu.6Gama ba zan dogara ga bakana ba, takobina kuma ba zai cece ni ba.
7Amma ka cece mu daga maƙiyanmu, ka ba masu ƙinmu kunya.8A cikin Allah muke fahariya a kullum, kuma za mu yi godiya ga sunanka har abada. Selah
9Amma yanzu ka ƙi mu ka kawo mu ga kunya, kuma baka yi tafiya tare da mayaƙanmu ba.10Ka sa muka juya baya daga maƙiyin; kuma waɗanda suka ƙi mu suna ɗibi ganima domin kansu.11Ka maida mu kamar tumakin da aka ƙaddara don abinci ka warwatsar da mu cikin al'ummai.
12Ba a bakin komai ka sayar da mutanenka ba; ba ka ƙara wadatarka ta yin haka ba.13Ka maida mu abin zargi ga maƙwabtanmu, waɗanda ke kewaye da mu suna yi mana reni da ba'a.14Ka sa mun zama abin zãgi cikin al'ummai, abin girgiza kai cikin tarrukan mutane.
15A dukkan tsawon rana ƙasƙancina na gabana, kuma kunyar fuskata ta rufe ni16saboda muryar wanda ke tsautarwa da zage-zage, saboda maƙiyi da mai ɗaukar fansa.17Dukkan waɗannan sun zo a kanmu; duk da haka ba mu mance da kai ba ko kuwa mu yi aiki cikin rahin gaskiya da alƙawaranka.
18Zuciyarmu bata juya ba; ƙafafunmu ba su yi nisa daga hanyarka ba.19Duk da haka ka kakkarya mu a wurin diloli ka rufe mu da inuwar mutuwa.20Idan mun mance da sunan Allahnmu ko kuwa muka buɗe hannuwanmu ga wani bãƙon allah,21Allah ba zai bincika haka ba? Gama ya san asiran zuciya.22Hakika, ta dalilinka ake karkashe mu dukkan rana; ana yi mana kallon tumaki domin yanka.
23Farka, me yasa kake barci, Ubangiji? Tashi, kada ka jefar da mu da daɗewa.24Me yasa ka ɓoye fuskarka ka mance da matsananciyar azabarmu da wahalarmu?
25Gama mun narke mun zama ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.26Tashi tsaye domin taimakonmu ka 'yantar da mu ta dalilin amintaccen alƙawarinka.

45

Domin shugaban mawaƙa; an shirya domin shoshanayim. Zabura ta 'ya'yan Kora. Salon waƙa. Waƙar ƙauna.

1Zuciyata na jin daɗi da nagartaccen zance; Zan karanta kalmomin da na harhaɗo a kan sarki da ƙarfi; harshena shi ne al'ƙalamin shiryayyen marubuci.2Ka fi 'ya'yan ɗan Adam kyau; an zuba alheri a leɓunanka; saboda haka mun san Allah ya albarkaceka har abada.

3Kasa takobinka a gefenka, mai girma, cikin ɗaukakarka da martabarka.4Cikin darajarka ka hau dokinka cikin murna saboda yarda da tawali'u da ayyukan adalci; hannun damanka zai koya maka abubuwan bantsoro.
5Kibawunka na da ƙaifi; mutane sun faɗa ƙarƙashinka; kibawunka na cikin zukatan maƙiyan sarki.6Kursiyinka, Allah, yana nan har abada, sandar adalci shi ne sandar mulkinka.7Kana ƙaunar ayyukan adalci kuma kana ƙin mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya shafe ka da mai na murna fiye da abokan taraiyarka.
8Dukkan tufafinka na ƙamshin turaren mur da aloyes da ƙahonnin da aka samo; daga kowacce fadar hauren giwa kayyakin busa da kiɗe-kiɗe sun saka murna.9'Ya'ya mata na sarakuna na cikin matayenka masu martaba; sarauniya na tsaye da tufafin zinariya da Ofir a hannun damanka,
10Saurara, ɗiya, ki maida hankali ki buɗe kunne, ki mance da mutanenki da gidan mahaifinki.11Ta haka sarkin zai yi marmarin kyanki; shi shugabanki ne; ki girmama shi.
12Ɗiyar Taya zata kasance a wurin da kyauta; masu arziki cikin mutanen za su nemi alfarmarku.13Ɗiya gimbiya a fãda tana cikin dukkan ɗaukaka; an yi aikin tufafinta da zinariya.
14Za a kaita wurin sarki cikin kyawawan tufafi masu ado kala-kala; budurwai, ƙawayenta dake binta, za a kawo maka.15Za a jagorance su da murna da farinciki; za su shiga cikin fadar sarki.
16A fãdar ubanninka 'ya'yanka zasu kasance, waɗanda zaka maida su yarimai a dukkan duniya.17Zan sa sunanka ya dawwama a dukkan tsararraki; saboda haka mutanen zasu yi maka godiya har abada abadin.

46

Domin shugaban mawaka. Zabura ta 'ya'yan Kora; shirin Alamot. Waƙa.

1Allah shi ne mafakarmu da ƙarfinmu, Mai matuƙar taimako a lokacin wahala.2Domin haka ba za mu ji tsoro ba, ko duniya zata canza, ko an girgiza duwatsu har cikin tekuna,3ko ruwayenta sun yi ruri da tangaɗi, duwatsu kuma suna motsi saboda kumburinsu. Selah

4Akwai kogi, da ƙoramu waɗanda ke sa birnin Allah farinciki, wuri mai tsarki na shirayi na Maɗaukaki.5Allah yana cikin tsakiyarta; ba zata kawu ba; Allah zai taimake ta, kuma zai yi haka da sassafen safiya.
6Al'ummai suka fusata kuma mulkoki suka girgiza; ya tayar da muryarsa, kuma duniya ta narke.7Yahweh mai runduna na tare da mu; Allah na Yakubu shi ne mafakarmu. Selah
8Zo, dubi ayyukan Yahweh, hallakar da ya kawo wa duniya.9Ya sa yaƙe-yaƙe su ƙare har zuwa iyakar duniya; ya kakkarya baka ya daddatsa mãsu gutsu--gutsu; ya ƙone garkuwoyi.
10Ku yi shiru ku sani Ni ne Allah; Zan sami ɗaukaka a cikin al'ummai; Za a ɗaukaka ni a duniya.11Yahweh mai runduna na tare da mu; Allah na Yakubu ne mafakarmu. Saleh

47

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta 'ya'yan Kora.

1Ku tafa hannuwanku, ku dukkan mutane; ku yi sowa ga Allah da muryar nasara.2Gama Yahweh Maɗaukaki abin tsoro ne; shi Sarki ne mai girma bisa dukkan duniya.

3Ya mayar da mutane ƙarƙashinmu, ya sa al'ummai a ƙarƙƙashin ƙafafunmu.4Ya zaɓi gãdonmu dominmu, ɗaukakar Yakubu wanda ya ke ƙauna. Selah5Allah ya tafi sama da sowa, Yahweh da ƙarar kakaki.
6Raira waƙoƙin yabo ga Allah. raira waƙoƙin yabo; raira waƙoƙin yabo ga Sarkinmu, raira waƙoƙin yabo.7Gama Allah Sarki ne a kan dukkan duniya; raira woƙoƙin yabo da ganewa.
8Allah yana mulki a kan al'ummai; Allah na zaune a tsattsarkan kursiyinsa.9'Ya'yan sarakuna sun tattaru wurin mutanen Allah na Ibrahim; gama garkuwoyin duniya na Allah ne; yana da ɗaukaka mai girma.

48

Waƙa; zabura ta 'ya'yan Kora.

1Yahweh mai girma ne kuma a yabe shi da girma, cikin birnin Allahnmu a tsauni mai tsarki.2Mai kyakkyawan tsawo, farincikin duk duniya, shi ne Tsaunin Sihiyona, a kusurwoyin arewa, birnin sarki mai girma.3Allah ya maida kansa sananne a cikin fadodinta a matsayin mafaka.

4Gama, duba, sarakuna sun tattaro kansu; suna wucewa tare.5Suka gan ta, sa'an nan suka yi mamaki; suka damu ƙwarai, sai suka wuce da sauri.6Firgici ya mamaye su a wurin, da azaba kamar ta mace mai naƙuda.
7Da iskar gabas ka karya jiragen ruwan Tarshish.8Kamar yadda muka ji haka muka gani a birnin Yahweh mai runduna, a birnin Allahnmu; Allah zai kafa shi har abada. Selah
9Mun yi tunanin amintaccen alƙawarinka, Allah. a tsakiyar haikalinka.10Kamar yadda sunanka ya ke, Allah, haka yabonka har ga iyakar duniya; hannun damanka na cike da ayyukan adalci.
11Tsaunin Sihiyona yi murna, bari 'ya'ya mata na Yahuda su yi farinciki saboda shari'unka masu adalci.
12Yi tafiya a kewayen Dutsen Sihiyona, je ka kewaya ta, harabarta da hasumiyarta,13lura da bangayenta sosai kuma ka duba fãdodinta da kyau, don ka faɗa wa tsara mai zuwa.
14Gama wannan Allahn shi ne Allahnmu har abada abadin; shi zai bi damu har mutuwa.

49

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta 'ya'yan Kora.

1Ku ji wannan, dukkanku mutane; ku kasa kunne, dukkanku mazaunan duniya, ƙanana da manya,2masu arziki da matalauta dukka.

3Bakina zai yi maganar hikima kuma nazarin zuciyata zai zama na ganewa.4Zan sa kunnena ga misali; zan fara misalina da molo.5Me zai sa in ji tsoron kwanakin mugunta, sa'ad da zunuban maƙiyana suka kewaye ni.
6Me zai sa in ji tsoron waɗanda suka dogara ga wadatarsu suke kuma yin fahariya game da arzikinsu?7Tabbas babu wanda zai iya fansar ɗan'uwansa ko ya ba Allah fansa dominsa,8Gama 'yantar da ran wani na da tsada, kuma ba wanda zai iya biyan bashinmu.
9Babu wanda zai dawwama da har jikinsa ba zai ruɓe ba.10Gama zai ga ruɓa. Masu hikima na mutuwa; wawaye da sakarkaru ma na lalacewa su kuma bar wadatarsu ga waɗansu.
11Tunaninsu na can ciki shi ne iyalansu zasu cigaba har abada, wuraren da suke zama kuma, su cigaba har dukkan tsararraki; suna kiran gonakinsu da sunayensu.
12Amma mutum, mai arziki ba shi rayuwa har abada; yana kamar dabbobi dake mutuwa.13Wannan, hanyarsu, ita ce wautarsu; duk da haka bayansu, mutane suna amincewa da maganganunsu.
14Kamar tumaki an ƙaddara su ga Lahira, kuma mutuwa zata zama mai kiwon su. Adalai zasu yi mulki a kansu da safe, kuma jikunansu zasu hallaka a Lahira, tare da rashin wurin zama dominsu.15Amma Allah zai 'yantar da rai na daga ikon lahira; zai karɓe ni. Selah
16Kada ka ji tsoro sa'ad da wani ya yi arziki, kuma darajar gidansa ta ƙaru.17Gama sa'ad da ya mutu ba zai tafi da komai ba; darajarsa ba zata tafi tare da shi ba sa'ad da ya mutu.
18Ko da mutum yana farinciki da nasararsa saboda arzikinsa yayin da ya ke raye- kuma mutane na yabonka sa'ad da kake rayuwa don kanka-19zai tafi zuwa tsarar ubanninsa kuma ba za su ƙara ganin haske kuma ba.20Mai wadata amma ba shi da ganewa yana kamar dabbobi, dake lalacewa.

50

Zabura ta Asaf.

1Maɗaukaki, Allah, Yahweh, ya yi magana yana kiran duniya daga fitar rana zuwa faɗuwarta.2Daga Sihiyona, wuri mafi kyau, Allah yana haskakawa.

3Allahnmu ya zo kuma ba ya tsaye shiru; wuta na ci a gabansa, kuma babban hadari na kewaye da shi.4Ya kira sammai da duniya domin ya shar'anta mutanensa.5Tattaro mani amintattuna dukka gare ni, waɗanda suka yi alƙawari dani ta miƙa hadaya."
6Sammai zasu yi shelar ayyukan adalcinsa, gama Allah da kansa alƙali ne. Selah
7Ku ji, mutanena, kuma zan yi magana; Ni ne Allah, Allahnku.8Ba zan kwaɓe ku domin hadayunku ba; hadayunku na ƙonawa na gabana kullum.
9Ba zan ƙarɓi bijimi daga gidanku ba, ko kuwa bunsurai daga garkenku ba.10Gama kowanne naman jeji nawa ne da shanun kan tuddai dubu.11Na san dukkan tsuntsayen duwatsu, kuma namomin jeji na fili nawa ne.
12Idan ina jin yunwa, ba zan faɗa maku ba; gama duniya tawa ce, da dukkan abin da ke cikinta.13Ko zan ci naman bijimai ko in sha jinin awakai?
14Ku miƙa wa Allah hadayar godiya, kuma ku bada alƙawaranku ta rantsuwa ga Mai iko dukka.15Ku yi kira gare ni a ranar damuwa; Zan cece ku, kuma zaku girmama ni."
16Amma ga mugaye Allah yace, "Me zaku yi da furtawar farillaina, har da zaku ɗauki alƙawarina a bakinku,17tunda kun ƙi umarnina kuma kun jefar da maganganuna?
18Sa'ad da kuka ga barawo, kuka yarda da shi; kuna ayyuka tare da waɗanda ke yin zina.19Kun bada bakinku ga mugunta, kuma harshenku na fitar da ruɗu.20Ka zauna kana magana gãba da ɗan'uwanka; ka na saran ɗan mahaifiyarka.
21Kun aikata waɗannan abubuwan, amma na yi shiru, sai kuka zata cewa Ni kamarku nake. Amma zan kwaɓe ku in kawo a gaban idanuwanku, dukkan abubuwan da kuka yi.22Ku lura da wannan da kulawa, ku da kuka mance da Allah, ko kuma zan yayyaga ku gutsu-gutsu, kuma babu wanda zai zo ya taimake ku!
23Wanda ya ke miƙa hadayar godiya yana yabona ne, kuma ga duk wanda ya ke rayuwarsa a hanyar da ta dace zan nuna masa ceton Allah."

51

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta Dauda; Sa'ad da annabi Natan ya je gunsa bayan da ya kwanta da Batsheba.

1Ka yi mani jinƙai, Allah, saboda amintaccen alƙawarinka; saboda kana yin ayyukan jinƙai masu yawa, ka tsige kurakuraina.2Ka wanke ni sosai daga zunubina ka share mani laifina.

3Gama na san kurakuraina, kuma laifina yana gabana kullum.4Gãba da kai, kai kaɗai, na yiwa laifi kuma na yi abin mugunta a fuskarka; ka yi dai-dai sa'ad da kayi magana; baka yi kuskure ba sa'ad da ka shar'anta.
5Duba, An haife ni a cikin zunubi; tun daga cikin mahaifiyata, ina cikin zunubi.6Duba, kana so in yi marmarin aminci cikin zuciyata; a cikin zuciyata zaka sa in san hikima.
7Ka tsarkake ni da abin tsarkakewa, zan kuwa tsarkaka; ka wanke ni, zan kuwa fi auduga fari.8Ka sa in ji daɗin rai da murna saboda ƙasusuwan da ka karya suyi farinciki.9Ka ɓoye fuskarka daga laifofina ka hure dukkan zunubaina.
10Ka sa in so yi maka biyayya kullum, Allah, ka sa kullum in so yin abin da ke dai-dai.11Kada ka kore ni daga gare ka, kar kuma ka ɗauke mani Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
12Ka maido mani da farincikin cetonka, ka riƙe ni da ruhun yin biyayya.13Sa'an nan zan koya wa masu zunubi hanyoyinka, masu laifi kuma zasu komo gare ka
14Ka gafarce ni domin zub da jini, Allahn cetona, sai in yi sowa domin farincikin ayyukan adalcinka.15Ubangiji, ka buɗe leɓunana, sai bakina ya furta yabonka.16Gama baka murna da sadaka, da zan bada ita; Baka jin daɗin baye-bayen ƙonawa.
17Hadayu na Allah sune karyayyen ruhu. Kai, Allah, baza ka ƙi zuciya mai tuba da kuma tawali'u ba.18Kayi nagarta cikin managarcin jin daɗinka ga Sihiyona; ka sake gina garun Yerusalem.19Sa'an nan zaka yi murna da sadakokin ayyukan aɗalci da baye-bayen ƙonawa da ainihin baye-yen ƙonawa; sa'an nan mutanenmu zasu miƙa bijimai a bagadinka.

52

Domin shugaban mawaƙa. Salon waƙar Dauda; lokacin da Dowaj Ba'idome yazo ya faɗawa Saul, ya ce da shi, "Dauda ya zo gidan Ahimelek."

1Meyasa kuke taƙama da tada fitina, ku manyan mutane? Alƙawarin Allah mai aminci yana zuwa kullum.2Harshenku yana shirya hallakarwa kamar reza mai kaifi, kuna aikata yaudara.

3Kuna ƙaunar mugunta fiye da nagarta ƙarya kuma fiye da maganar adalci. Selah
4Ka na ƙaunar maganar da zata hallaka waɗansu, kai harshe mai yaudara.5Haka Allah zai hallaka ka har abada, zai ɗauke ka daga rumfarka ya tumɓuke ka daga ƙasar masu rai. Selah.
6Masu adalci zasu gani su ji tsoro; su yi masa dariya su ce,7"Ku dubi mutumin da bai mayar da Allah wurin fakewarsa ba, amma ya dogara ga dukiya da yawa, kuma yana da ƙarfi sa'ad da ya hallaka waɗansu."
8Amma ni, ina kama da itacen inabi mai sheƙi a cikin gidan Allah; zan dogara ga alƙawarin Allah mai aminci har abada.9Zan yi godiya gare ka har abada saboda abin da kayi. Zan jira ga sunanka, saboda yana da kyau a cikin taron jama'arka masu tsoron ka.

53

Domin shugaban mawaƙa; da aka tsarawa Mahalat. Salon waƙar Dauda.

1Wawa a zuciyarsa yace, "Babu wani Allah." Dukkan su sun gurɓace sun yi aikin mugunta; babu ko ɗaya dake aikata abin kirki.2Allah ya dubo 'yan Adam daga sama, ya gani ko akwai wani mai fahimta, wanda ke neman sa.3Dukkan su sun fanɗare. Gabaɗayan su sun gurɓace. Ba wani mai aikata abin kirki, babu ko guda ɗaya.

4Waɗanda ke aikata mugunta basu da fahimta ne--waɗanda ke cin naman mutanena kamar suna cin gurasa kuma ba su kira ga Allah ba?5Suna cikin tsoro mai yawa ko da ya ke ba wani abin tsoratarwa; gama Allah zai tarwatsa duk wanda ya yi maku kwanto; irin waɗannan mutane zasu sha kunya gama Allah ya ƙi su.
6Oh, dama ceton Isra'ila ya zo daga Sihiyona! Sa'ad da Allah ya dawo da mutanensa daga bauta, Yakubu zai yi farinciki, Isra'ila kuma zai yi murna!

54

Domin shugaban mawaƙa; Akan kayan kaɗe-kaɗe. Salon Dauda; lokacin da Zifaniyawa suka zo suka ce da Saul, "Ashe ba Dauda na ɓoye a cikinmu ba?"

1Ka cece ni ya Allah, ta wurin sunanka, ka yi mani shari'a cikin ƙarfin ikonka.2Allah, ka ji addu'ata, ka saurari kalmomin bakina.3Gama bãƙi sun afko mani, lalatattun mutane na neman raina, basu sa Allah a gabansu ba. Selah.

4Duba, Allah shi ne mai taimako na, Ubangiji shi ne mai tallafa ta.5Zai saka wa maƙiyana da mugunta; cikin amincinka, ka hallaka su!
6Zan baka hadaya ta yardar rai, zan yi godiya ga sunanka, Yahweh gama haka na da kyau.7Gama ya kuɓutar dani daga kowacce damuwa; idona na duban nasara a kan maƙiyana.

55

Domin shugaban mawaƙa akan kayan kiɗa na tsarkiya. Salon Dauda.

1Allah, ka ji addu'ata, kada ka ɓoye kanka daga roƙona.2Ka saurare ni ka amsa mani, gama bani da hutu cikin wahaluna,3saboda muryar maƙiyana, saboda matsin masu mugunta, gama suna tsananta mani cikin fushi.

4Zuciyata tana kiɗima a cikina, tsoron mutuwa ya faɗo kaina.5Firgita da razana sun zo kaina, kuma fargaba ya sha kaina.
6Na ce, "Oh, dãma ina da fukafukai kamar kurciya! Da na tashi in je in huta.7Da zan tafi can nesa in zauna a cikin jeji. Selah
8Da zan yi hanzari in sami mafaka daga hadari mai iska da guguwa.9Ka haɗiye su, Ubangiji, kasa ruɗami cikin harsunansu! Gama na ga ta'addanci da hargitsi a cikin birnin.
10Suna ta yawo a kan ganuwarsa dare da rana. Mugunta da lalata suna cikin tsakiyarsa.11Aikin mugunta na cikin tsakiyarsu; Tsanani da zamba ba su bar hanyoyinsu ba.
12Gama da maƙiyi ne ke tsauta mani, da na iya jurewa; ba kuma wanda ya ke gaba dani ne ya tada kansa gaba dani ba, da na ɓoye kaina daga wurin sa.13Amma kai ne mutum kamar ni, abokina, da aminina kuma.14Mun yi zumunci mai kyau tare, mun je gidan Yahweh tare da ƙarfafa.
15Bari mutuwa ta afko masu, bara su gangara lahira, gama mugunta ce kaɗai rayuwarsu, haka suke.
16Ni kuwa zan kira ga Allah, Yahweh zai cece ni.17Ko da yamma ko da rana ko da safe, idan na yi ƙara da nishi zai ji muryata.18Zai kuɓutar da raina daga masu kawo mani hari, gama waɗanda ke faɗa dani suna da yawa.
19Yahweh, wanda ya ke mulki tun daga farko, zai ji su ya ƙasƙantar dasu. Ba zasu taɓa canzawa ba, kuma ba sa tsoron Yahweh.
20Abokina ya tada hannuwansa gaba da waɗanda ke zaman salama dani. Bai cika alƙawarin da ya yi ba.21Bakinsa yana da taushi kamar mai, amma zuciyarsa tana da hasala; kalmominsa suna da taushi kamar mai, amma a gaskiya takubba ne zararru.
22Ka ɗora wa Yahweh matsalolinka, shi zai riƙe ka, ba zai bari adalai su lalace ba.23Amma kai Allah, za ka kawo miyagu cikin ramin hallakarwa. Masu shan jini da mayaudaran mutane ba za su rayu koda kamar na rabin sauran mutane ba, amma zan dogara gare ka.

56

Domin shugaban mawaƙa; da aka tsarawa Yanat elem rehokim. Zabura ta Dauda. Kewa; lokacin da Filistiyawa suka ɗauke shi zuwa Gat.

1Ka ji ƙaina ya Allah, gama mutane na kawo mani hari! Dukkan yini suna tsananta ɓatancin da suke yi mani.2Maƙiyana na musguna mani dukkan yini, gama waɗanda ke yin faɗa dani cikin wauta suna da yawa.

3Sa'anda na ji tsoro, zan dogara gare ka.4Ina jin daɗin maganar Allah, ga Allah zan dogara; ba zan ji tsoro ba; me mutum kawai zai iya yi ma ni?
5Juya maganata suke yi dukkan yini, dukkan tunaninsu a kaina na mugunta ne.6Sun tattara kansu, sun yi kwanto, suna bin sawuna, suna neman raina.
7Kada ka bari su dena yin mugunta. Ya Allah, ka kayar da su a cikin fushinka.8Ka lissafa yawace-yawacena ka kuma sa hawayena cikin kwalba; ko ba a cikin littafinka suke ba?
9Sa'ad da na kira ka, maƙiyana zasu koma da baya, abin da na sani kenan, Allah yana tare da ni.10A cikin Allah --wanda maganarsa nake yabo, a cikin Yahweh--11a cikin Allah na dogara, bazan ji tsoro ba. Me wani zai iya yi mani?
12Aikina shi ne in cika wa'adina gare ka, Yahweh. Zan miƙa baye-baye na godiya a gare ka.13Gama ka kuɓutar da raina daga mutuwa, ka tsare ƙafafuna daga faɗuwa, domin in yi tafiya a gaban Allah a cikin masu rai.

57

Domin shugaban mawaƙa; da aka tsarawa salon murya. Zabura ta Dauda. Salon waƙa; lokacin da ya gudu daga wurin Saul a cikin kogo.

1Ka yi mani jinƙai, Yahweh, ka yi mani jinƙai, gama na fake wurin ka har sai waɗannan wahalu sun wuce. Na tsaya a ƙarƙashin inuwar fukafukanka har sai wannan hallaka ta ƙare.

2Zan yi kuka ga Allah Maɗaukaki, ga Allah, wanda ya ke yi mani komai.3Zai aiko da taimako daga sama ya cece ni, yana jin haushin waɗanda ke ƙuje ni. Allah zai aiko mani da jinƙansa da amincinsa.
4Raina yana cikin zakuna, ina cikin waɗanda suke a shirye su cinye ni. Ina cikin mutanen da haƙoransu mãsu ne da kibau, haƙoransu kuma kamar takubba masu kaifi.5Ya Yahweh, ka ɗaukaka a bisa sammai, bari ɗaukakarka ta zama a bisa duniya.
6Sun baza taru saboda ƙafafuna; Na shiga cikin ƙunci. Sun gina rami a gabana. Amma su da kansu ne suka faɗa a cikin tsakiyarsa! Selah
7Zuciyata ta kafu, Allah, zuciyata a kafe take; Zan raira, I, zan raira yabbai.8Tashi, ke zuciyata mai daraja, tashi, ke sarewa da molo, nima tun da asuba zan tashi.
9A cikin jama'a zan yi maka godiya, ya Ubangiji; zan raira yabo gare ka a cikin al'ummai.10Gama ƙaunarka tana da girma ƙwarai, ta kai har sama, amincika kuma ya kai gizagizai.11Ka ɗaukaka ya Allah, sama da sammai, darajarka ta ɗaukaka bisa dukkan duniya.

58

Domin shugaban mawaƙa; da aka tsara ga salon murya. Zabura ta Dauda. Salon waƙa.

1Ku shugabanni kuna faɗin gaskiya? Ku jama'a kuna yin shari'ar gaskiya?2Babu, kun yi aikin mugunta cikin zuciyarku; kun baza tashin hankali da hannuwanku a cikin ƙasar dukka.

3Tun daga cikin ciki, masu mugunta ke fanɗarewa, tun daga haihuwarsu suke ratsewa, suna faɗin ƙarya.4Dafinsu kamar dafin maciji ya ke, suna kama da kurmar ƙasa wadda take toshe kunnuwanta,5wadda bata jin muryar masu layu, komai gwanintarsu.
6Ka karairaya haƙoransu a cikin bakunansu, ya Allah; ka ciccire manyan haƙoran 'yan zakuna, ya Yahweh.7Bari su narke kamar ruwan dake gangarewa; idan suka harba kibansu, bari su zama kamar basu yi saiti ba.8Bari su zama kamar dodon koɗi wanda ke narkewa ya lalace, kamar jaririn da mace ta haifa kafin lokacinsa yayi wanda bai taɓa ganin hasken rana ba.
9Kafin tukunyarka ta ji zafin wuta, zai kwashe su da guguwa, da ɗanye da wanda a ke ƙonawa dukka.10Mai adalci zai yi farinciki sa'ad da ya ga ramako daga Allah, zai wanke ƙafafunsa da jinin masu mugunta,11domin mutane su ce, "Gaskiya ne akwai lada ga mutum mai adalci, gaskiya ne akwai Allah wanda ke shar'anta duniya.

59

Domin shugaban mawaƙa; wadda aka tsarawa salon murya. Zabura ta Dauda. Salon waƙa lokacin da Saul ya aika, suka kuma yi fakon gidan domin su kashe shi.

1Ka kuɓutar dani daga maƙiyana, ya Allahna; ka ɗora ni can sama nesa daga waɗanda suke taso mani.2Ka tsare ni daga waɗanda suke aikata mugunta, ka cece ni daga mutane waɗanda suke zubar da jini.

3Gama, duba, sun yi kwanto domin su ɗauki raina. Manya manyan masu aika mugunta sun tattara kansu gãba dani, amma ba saboda nayi kuskure ko zunubi ba, Yahweh.4Sun shirya domin su tattake ni ba tare da laifina ba, duba, tashi ka taimake ni.
5Kai Yahweh, Allah Mai Runduna, Allah na Isra'ila, tashi ka hori dukkan al'ummai. Kada ka ji tausan wani mai laifin aika mugunta ko ɗaya.
6Sukan dawo da yamma, su zagaya birnin suna haushi kamar karnuka.7Duba suna yin gyatsa da bakunansu, takubba suna kan leɓunansu, suna cewa, "Wane ne ya ke sauraren mu?"
8Amma kai, Yahweh, kana yi masu dariya, dukkan al'ummai ba a bakin komai suke a gare ka ba.9Allah, ƙarfina, zan kasa kunne gare ka, kaine hasumiyata mai tsawo.
10Allahna zai same ni da alƙawarin amincinsa, Yahweh, zai biya muradina a kan maƙiyana.11Kada ka kashe su domin kada jama'ata su mance. Yahweh, garkuwarmu, ka warwatsa su, ka sa su faɗi.
12Saboda kalmomin bakinsa, da maganar leɓunansu, ka bari a kwashe su cikin girman kansu, kuma saboda la'ana da ƙarairayin da suka bayyana.13Ka hallaka su cikin hasalarka, ka hallaka su domin kada su ƙara kasancewa. Bari su sani, Allah ne ke mulki cikin Yakubu kuma har iyakar duniya. Selah
14Sukan dawo da yamma, su zagaya birnin suna haushi kamar karnuka.15Sukan yi yawo suna neman abinci, sukan yi gurnani idan ba su ƙoshi ba.
16Amma zan yi rairawa game da ƙarfinka, da safe kuma zan yi rairawa saboda ƙaunarka madawwamiya! Gama ka zama hasumiyata mai tsawo, mafaka a lokacin dani ke cikin matsala.17A gare ka ƙarfina zan raira yabo, gama Yahweh ne hasumiyata mai tsawo, Allah mai amincin alƙawari.

60

Domin shugaban mawaƙa; da aka tsarawa Shushan Idut. Salon waƙar Dauda, domin koyarwa. Lokacin da ya yi faɗa da Aram Naharayim da kuma Aram Zoba da Yowab ya dawo daga kisan Idomawa dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri.

1Yahweh, ka yashe mu, ka kutsa cikin matsararmu, ka yi fushi, ka dawo da mu.

2Kasa ƙasar ta girgiza, ka ɓarke ta; tana girgiza, ka warkar da ɓarakarta.3Kasa mutanenka su ga abubuwa masu wuya, kasa mun sha ruwan inabin tangaɗi.
4Saboda waɗanda ke darjantaka, kasa an tada tuta gãba da masu ɗaukar baka.5Saboda waɗanda kake ƙauna su kuɓuta, ka amsa mani ka kuɓutar da mu da hannun damanka.
6Allah ya yi magana cikin tsarkinsa, "Zan yi farinciki, zan raba Shekem, zan karkasa Kwarin Sukot.7Giliyad tawa ce Manasse ma tawa ce, Ifraim kuma hular kwanona ce, Yahuda kuma sandar girmana ce.
8Mowab bangajin wankina ne, zan ajiye takalmina a kan Idom, zan yi sowa ta murna saboda Filistiya."9Wa zai kawo ni birni mai ƙarfi? Wa zai kai ni Idom?
10Amma kai Yahweh, ba ka yashe mu ba? Gama ba ka tafi yaƙi tare da sojojinmu ba.11Ka taimake mu gãba da maƙiyanmu gama taimakon mutum banza ne.12Da taimakon Allah za mu yi nasara; shi zai tattake maƙiyanmu.

61

Domin shugaban mawaƙa; akan kayan kiɗa na tsarkiya. Zabura ta Dauda.

1Ka ji kukana Yahweh, ka amsa addu'ata.2Daga iyakar duniya zan kira gare ka lokacin da zuciyata ta ruɗe, ka kai ni wurin dutsen da ya fi ni tsawo.3Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi daga maƙiyana.

4Ka bar ni in zauna a shirayinka har abada! Ka bar ni in ɓoye cikin inuwar fukafukanka. Selah5Gama kai Allah, ka ji wa'adina, ka bani gãdon waɗanda suke darjanta sunanka.
6Za ka sa ran sarki ya yi tsawo, shekarunsa kuma kamar tsararraki da yawa.7Zai kasance a gaban Yahweh har abada.
8Zan raira yabo ga sunanka har abada, domin in cika wa'dina gare ka kowacce rana.

62

Domin shugaban mawaƙa; bisa ɗabi'ar Yedutun. Zabura ta Dauda.

1Na yi shiru a gaban Yahweh kaɗai, daga wurin sa cetona ya ke zuwa.2Shi kaɗai ne cetona, shi ne hasumiyata mai tsawo, ba zan girgiza ba sosai.

3Har yaushe ku dukka, zaku kai hari ga mutum ɗaya? Domin ku rufe shi kamar bangon da a ke jigina da shi, shinge mai rawa?4Suna shawara da shi ne domin su ture shi daga matsayinsa mai daraja kaɗai; su na ƙaunar faɗin ƙarya, suna sa masa albarka da bakinsu, amma cikin zuciyarsu suna la'antar sa. Selah
5Ga Allah kaɗai nake saurare, gama shi ne begena.6Shi kaɗai ne dutsena da cetona, shi ne hasumiyata mai tsawo ba zan jijjigu ba.
7Allah ne cetona da ɗaukakata, dutsen ƙarfina da mafakata a cikin Allah suke.8Ku dogara gare shi kowanne lokaci, ku mutane, ku kafa zuciyarku a gaban sa, Allah shi ne mafakarmu. Selah
9Ba shakka mutanen da basu da matsayi ba komai bane, waɗanda ke da matsayin kuma ƙarya ne. Idan a ka auna su a ma'auni ba su da nauyi, inda za a haɗa su a auna ba su da nauyin komai.10Kada ku dogara ga aikin zalunci ko ƙwace, kada ku sa begenku ga dukiyar wofi, gama ba su da amfanin komai, kada ku sa zuciya gare su.
11Allah ya yi magana sau ɗaya, sau biyu kuwa na ji wannan: iko na Allah ne.12Kuma Ubangiji, a gare ka alƙawarin gaskiya yake. Gama kana ramawa kowanne mutum bisa ga abin da ya yi.

63

Zabura ta Dauda, lokacin da ya ke a cikin dajin Yahuda.

1Allah, kai ne Allahna, da gaske raina ya ke neman ka, raina yana ƙishin ka, jikina ya ƙagara ya gan ka, a cikin ƙasa da turɓaya in da babu ruwa.2Na dubo zuwa gare ka a cikin mutane masu tsarki domin in ga ikonka da ɗaukakarka.

3Saboda alƙawarin ka mai aminci yafi rai, leɓunana zasu yabe ka.4Zan albarkace ka sa'ad da nake da rai, a cikin sunanka zan tada hannuwana.
5Zai zama kamar na ci abinci mai ɓargo da kitse, zan yabe ka da leɓuna masu farinciki,6sa'ad da ni ke tunaninka a kan gadona, sa'ad da nake nazarin ka a cikin dare.
7Gama kai ne taimakona, a ƙarƙashin inuwar fukafukanka nake yin farinciki.8Na manne maka hannun damanka yana tallafa ta.
9Amma waɗanda ke nema su hallaka raina, zasu faɗa cikin wuri mai zurfi na duniya;10za a bashe su ga hannun masu aiki da takobi, zasu zama abicin diloli.
11Amma sarki zai yi farinciki cikin Allah, dukkan wanda ya rantse da shi, zai yi fahariya da shi kuma, amma bakin masu faɗin ƙarya za a kwaɓe shi.

64

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta Dauda.

1Ka ji muryata, Allah, ka saurari ƙarata; ka tsare raina daga tsoron maƙiyana.2Ka ɓoye ni daga shirin miyagu, daga hargowar masu aika mugunta.

3Sun wasa harsunansu kamar takubba, sun haro kibansu, wato maganganu masu ɗaci,4domin su harbi wanda ba shi da laifi daga wurin da suke ɓoye, nan da nan suka harbe shi ba tare da sun ji tsoro ba.
5Suna ƙarfafa kansu cikin shirya mugunta, suna shawara a asirce domin su ɗana tarkuna, suna cewa, "Wa zai gan mu?"6Suna ƙulla mugunta; "Mun gama" suka ce, "Natsastsen shiri" Tunanin ciki da zuciyar mutum suna da zurfi.
7Amma Yahweh, zai harbe su, nan da nan kibau zasu ji masu ciwo.8Zasu yi tuntuɓe tun da ya ke harshensu yana gãba da su; dukkan waɗanda suka gan su zasu kaɗa kansu.9Dukkan mutane zasu ji tsoro su bayyana ayyukan Allah. Cikin hikima zasu yi tunani a kan abin da ya yi.
10Masu adalci zasu yi murna da Yahweh, zasu sami mafaka a wurinsa. Dukkan waɗanda ke tafiya dai-dai zasu yi fahariya a cikin sa.

65

Domin shugaban mawaƙa. Zabura. Waƙar Dauda.

1Domin kai Allah a Sihiyona ne, yabonmu; da wa'adodinmu, za a kawo maka su a cikin Sihiyona.2Kai da kake jin addu'a, a gare ka dukkan mutane za su zo.3Laifofi sun yi mana tsayayya, amma za ka gafarta zunubanmu, za ka kuma gafarta su.

4Mai albarka ne mutumin daka zaɓa ya zo ya zauna a kusa da kai a cikin harabarka. Za mu gamsu da kyawawan abubuwan dake a gidanka, haikalinka mai tsarki.
5Cikin adalci za ka amsa mana ka yi abubuwan mamaki, kai Allah na cetonmu, Kai wanda dukkan mutane ke dagara gake ka har da waɗanda ke a can hayin teku.
6Gama kai ne ka kafa duwatsu suka yi ƙarfi, kai wanda ka yi ɗamara da iko.7Kai ne ka kwantar da rurin tekuna da balalloƙansu da hargowar mutane
8Su waɗanda ke zama a can ƙarshen duniya suna jin tsoron alamun ayyukanka, kasa gabas da yamma suna farinciki.9Ka zo domin ka taimaki duniya; ka yi mata banruwa, kasa ta yi arziki, kogin Allah na cike da ruwa; tun da ka hallicci duniya ka tanadawa ɗan Adam hatsi.
10Ka jiƙe kwarin kunyai a wadace, ka dai-daita kwarin kunyai sosai, kakan sa su yi taushi, kasa albarka a kan yabanyarsu.11Ka yi wa shekara dajiyar alherai, sawayen karusanka suka zubo da kitse a kan duniya.12Wuraren kiwo a jeji sun jiƙe da raɓa, ka sa tsire--tsire suyi farinciki.
13Wuraren kiwo sun cika da garkuna, kwarurruka sun cika da hatsi, suna shewa ta farinciki, suna rairawa.

66

Domin shugaban mawaƙa. Waƙa ta Zabura.

1Ku yi sowa ta farinciki ga Yahweh, ku duniya dukka.2Ku raira ɗaukakar sunansa, ku sa yabonsa ya zama ɗaukakakke.

3Ku ce da Allah, "Ayyukanka suna da ban tsoro! Da girman ikonka kasa maƙiyanka su yi ladabi a gabanka.4Dukkan duniya zasu bauta maka su raira yabo gare ka, zasu yi rairawa ga sunanka." Selah
5Ku zo ku ga ayyukan Yahweh, ayyukansa na da ban mamaki ga 'yan Adam.6Ya mayar da teku busasshiyar ƙasa; sun bi ta cikin teku da ƙafa; can muka yi farinciki a cikin sa.7Da ikonsa ya ke mulki har abada, idanunsa suna lura da al'ummai; kada masu tawaye su ɗaukaka kansu. Selah
8Ku albarkaci Allah, ku mutane, bari a ji amon yabonsa.9Ya bar mu cikin masu rai, bai bari ƙafafunmu suka yi tuntuɓe ba.
10Gama kai Yahweh ka gwada mu, ka gwada mu kamar yadda a ke gwada azurfa.11Ka kawo mu cikin taru, ka ɗora mana kaya mai nauyi a kanmu.12Ka bari mutane su tattaka mu, mun shiga cikin wuta da ruwa, amma ka kawo mu cikin wuri mai faɗi.
13Zan zo cikin gidanka da baiko na ƙonawa, zan cika wa'adodina gare ka,14waɗanda leɓunana suka yi alƙawarin su, bakina kuma ya furta, sa'ad da nake cikin wahala.15Zan kawo maka baiko na ƙonawa da dabbobi masu ƙiba da ƙamshin raguna; zan miƙa bijjimai da awaki.
16Ku zo ku saurara, dukkan ku dake tsoron Allah, zan bayyana abin da ya yi domin raina.17Na yi kuka gare shi da bakina, harshena kuma ya yabe shi.18Idan dana dubi zunubi a cikin zuciyata, da Ubangiji bai saurare ni ba.
19Amma da gaske Allah ya ji; ya kula da muryar addu'ata.20Albarka ta tabbata ga Allah, wanda bai yi watsi da addu'ata ba ko ya ɗauke alƙawarinsa mai aminci daga gare ni ba.

67

Domin shugaban mawaƙa; a kan kayan kiɗa na tsarkiya. Zabura, waƙa.

1Bari Allah ya yi mana jinƙai, yasa fuskarsa ta haskaka wajenmu. Selah2domin a san hanyoyinka a duniya, cetonka kuma cikin al'ummai dukka.

3Bari mutane su yabi Allah, dukkan mutane su yabe ka.4Oh, bari al'ummai suyi murna su raira domin farinciki, gama za ka hukunta mutane cikin adalci, ka shugabanci mutanen duniya. Selah
5Bari mutane su yabe ka Allah, bari dukkan mutane su yabe ka.6Ƙasa ta ba da amfaninta kuma Allah, Allahnmu ya albarkace mu.
7Allah ya albarkace mu kuma dukkan ƙarshen duniya na darjanta shi.

68

Domin shugaban mawaƙa; Zabura ta Dauda, waƙa.

1Bari Allah ya tashi, bari maƙiyansa su warwatse, bari kuma waɗanda ke ƙin sa su gudu daga gabansa.2Ka kore su kamar yadda hayaƙi ke watsewa, kamar yadda saƙar zuma kan narke a gaban wuta, haka masu mugunta zasu lalace a gaban Allah.3Amma bari masu adalci suyi murna, su ɗaukaka a gaban Allah; bari su yi farinciki su kuma ji daɗi.

4Ku raira ga Allah! Ku raira yabbai ga sunansa! Ku yabe shi wanda ke ratsawa ta filin kwarin Kogin Yodan! Yahweh ne sunansa! Ku yi farinciki a gabansa!5Uban marar uba, alƙali saboda gwauraye, shi ne Allah daga wurin zamansa mai tsarki.6Allah yakan sa masu kaɗaici cikin iyali, ya kan fito da 'yan kurkuku cikin waƙa, amma 'yan tawaye suna zama a faƙo.
7Allah idan da kayi tafiya a gaban mutanenka, idan ka bi ta cikin jeji, Selah8Ƙasa takan girgiza, sama kan zubo da ruwa a gaban Allah, a gaban Allah sa'ad da ya zo Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra'ila.
9Kai, Allah, ka aiko da ruwa isasshe, ka ƙarfafa abin gãdonka sa'ad da suka gaji.10Mutanenka suka zauna a ciki; kai, Allah, daga cikin alherinka ka bayar ga matalauta.
11Ubangiji ya bada umarnai, waɗanda suka sanar da su kuwa manyan sojoji ne.12Sarakunan sojoji sun gudu, suka gudu, matayen dake zama a gida kuwa suka raba ganima.13Kurciyoyi rufe da azurfa, da fukafukan zinariya rawaya. Sa'ad da waɗansu ku mutane kuka tsaya a garkunan tumaki, me ya sa kuka yi haka?
14Mai iko dukka ya tarwatsa sarakuna a wurin, sai ya zama kamar dusar ƙanƙara a Dutsen Zalmon.15Babban dutse shi ne tudun ƙasar Bashan, dutse mai tsawo shi ne tudun ƙasar Bashan.16Me yasa ki ke ƙyashi ke ƙasar kan tudu, a kan dutsen da Allah ya zaɓi ya zauna a wurin? Tabbas, Yahweh zai zauna a cikinta har abada.
17Karusan Allah dubu ashirin ne, dubbai bisa dubbai; Ubangiji na cikinsu a wuri mai tsarki, kamar a Sinai.18Ka haye sama, ka kwashi 'yan bauta, ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga waɗanda suka yi faɗa da kai, domin kai Yahweh Allah, ka zauna a can.
19Albarka ga Ubangiji, wanda kullum ya ke kula da mu, Allah wanda shi ne cetonmu.20Allahnmu, Allah ne wanda ke yin ceto. Yahweh, Ubangiji, shi ne kaɗai wanda zai iya kuɓutar da mu daga mutuwa.21Amma Allah zai rotsa kan maƙiyansa, ta wurin fatar kai mai gashi ta waɗanda ke tafiya cikin yi masa laifi.
22Ubangiji yace, "Zan dawo da maƙiyana daga Bashan, zan dawo da su daga cikin zurfin teku23domin ka ragargaza maƙiyanka, kana tsoma ƙafarka cikin jini, domin harsunan karnukanka su sami rabo daga cikin maƙiyanka."
24Sun ga shigowar ka, Allah, shigowar Allahna, Sarkina cikin wuri mai tsarki.25Mawaƙa suka fara yin gaba, masu busa na bin baya, a tsakiya kuwa 'yammata na kaɗa molo.
26Ku albarkaci Allah a cikin taro, ku yabi Yahweh, ku zuriyar Isra'ila na gaskiya.27Da fari akwai Benyamin, kabila mafi ƙanƙanta, sai kuma shugabannin Yahuda da jama'arsu, shugabannin Zebulun da shugannin Naftali.
28Allahnka, ya Isra'ila ya umarta ƙarfinka, ka nuna ikonka, Allah, kamar yadda ka nuna shi a lokacin dã.29Ka nuna mana ikonka daga Yerusalem inda sarakuna ke kawo maka kyautai.
30Yi ruri cikin yaƙi gãba da namomin jejin dake zama cikin iwa, a kan mutane, da bijimai masu yawa da 'yan maruƙa. Kunyatar dasu kasa su kawo maka kyautai, ka tarwatsa mutanen dake ƙaunar yin yaƙi.31Sarakuna zasu fito daga Masar; Itofiya zata yi sauri ta kawo hannuwanta ga Allah.
32Ku raira yabbai ga Allah ku mulkokin duniya; Selah ku raira yabbai ga Yahweh.33Gare shi wanda ke sukuwa kan saman sammai, shi wanda ya kasance tun zamanin dã; duba, ya tada muryarsa da iko.
34Ku furta ƙarfi ga Allah, darajarsa tana kan Isra'ila, ikonsa na cikin sararin sama.35Allah, kai abin tsoro ne a cikin wurinka mai tsarki, Allah na Isra'la yana ba da ƙarfi da iko ga mutanensa. Albarka ga Allah.

69

Domin shugaban mawaƙa; da aka tsarawa Shoshanayim. Zabura ta Dauda.

1Ka cece ni Allah, gama ruwaye sun sa raina cikin hatsari.2Na nutse cikin laka, mai zurfi inda ba wurin tsayawa; na zo cikin ruwa mai zurfi, rigyawa ta sha kaina.

3Na gaji da kuka, maƙogwarona ya bushe, idanuna sun dishe sa'ad da nake jiran Allahna.4Waɗanda ke ƙi jinina ba dalili sun fi gashin kaina yawa, su waɗanda zasu datse ni saboda dalilan da ba dai-dai ba, suna da ƙarfi, abin da ban sata ba, sai na mayar.
5Allah, ka san wawancina, zunubaina kuma ba ɓoye suke a gare ka ba.6Kada waɗanda ke jiran ka su ji kunya saboda ni, Ubangiji Yahweh Mai Runduna, kada masu neman ka su ƙasƙanta saboda ni, Allah na Isra'ila.
7Saboda kai na jure da tsautawa; kunya ta rufe fuskata.8Na zama bãƙo ga 'ya'uwana, bare kuma ga 'ya'yan mahaifiyata.9Gama niyyar zuwa gidanka ta ɗauke hankalina, tsautawar waɗanda ke tsauta maka ta faɗo kaina.
10Idan na yi kuka na ƙi cin abinci, sai su zage ni.11Idan kayan makoki suka zama kayan sawata, sai in zama abin misali gare su.12Waɗanda ke zama a ƙofar birni magana suke yi a kaina, mashaya waƙa su ke yi a kaina.
13Amma ni addu'ata gare ka take, Yahweh, sa'ad da ka ga yayi dai-dai, ka amsa mani cikin aminci cetonka.14Ka tsamo ni daga cikin laka, kada ka bari ni nutse; bari a ɗauke ni daga waɗanda ke ƙina, a kuma tsamo ni daga cikin ruwaye masu zurfi.15Kada ka bari rigyawa ta sha kai na, kada ka bari zurfi ya haɗiye ni. Kada ka bari rami ya rufe bakinsa a kaina.
16Ka amsa mani Yahweh, gama alƙawarin amincinka yana da kyau; domin jiye-jiyen ƙanka suna da yawa zuwa gare ni, ka juyo wajena.17Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka, gama ina cikin wahala, ka amsa mani da sauri.
18Ka zo wuri na ka cece ni, saboda maƙiyana ka fanshe ni.19Ka san tsautawar da a ke yi mani, ka san kunyata, ka san ƙasƙancin da nake sha; dukkan magabtana a gabana suke.
20Tsautawa ta karya zuciyata; cike nake da nauyi; na duba ko wani zai ji tausayi na, amma ban samu ba.21Sun ba ni dafi shi ne abincina, cikin ƙishina kuma sai suka ba ni ruwan tsami domin in sha.
22Bari teburin gabansu ya zama tarko, sa'ad da suke tsammanin suna lafiya bari ya zama tarko a gare su.23Bari idanunsu su dishe yadda ba zasu iya gani ba; bari kwankwasonsu su riƙa yin rawa.
24Ka zuba masu hasalarka, bari zafin fushinka ya yi ƙuna a kan su.25Bari wurin zamansu ya zama kufai; kada kowa ya zauna a rumfunansu.
26Gama sun tsanantawa wanda ka fyaɗe ƙasa. Sun ƙarawa waɗanda suka ji rauni zafin ciwo.27Ka zarge su a kan aikata mugunta a kan mugunta; kada ka bari su zo cikin nasararka mai adalci.
28Bari a shafe su daga cikin lattafin rai, kada a rubutasu tare da tsarkaka.29Amma ni matalauci ne mai baƙinciki, bari cetonka; Allah, ya sanya ni can sama.
30Zan yabi sunan Allah da waƙa, zan ɗaukaka shi da shaidar godiya.31Wannan zai gamshi Yahweh fiye da sã da bijimi mai ƙahonni da kofatai.
32Masu taushin zuciya za su gani suyi murna, ku da kuke neman Yahweh, zukatanku zasu rayu.33Gama Yahweh na sauraron mabuƙata, ba ya kuma raina 'yan sarƙarsa.
34Bari sama da ƙasa su yabe shi da tekuna da dukkan abubuwan dake iyo a cikinsu.35Gama Allah zai ceci Sihiyona, zai sake gina biranen Yahuda; mutane zasu zauna a can ya zama nasu.36Zuriyar bayinsa zasu gaje shi, waɗanda ke ƙaunar sunansa zasu zauna a can.

70

Domin shugaban mawaƙa Zabura ta Dauda; ta kawo tunawa.

1Ka cece ni ya Allah, Yahweh, ka zo da sauri ka taimake ni.2Bari waɗanda ke so su ɗauki raina su ji kunya su ƙasƙanta; bari su koma baya a wulaƙance, su waɗanda ke murna da raɗaɗina.3Bari su koma baya cikin kunya, su waɗanda ke cewa, "Aha, aha."

4Bari dukkan waɗanda ke neman ka suyi farinciki, suyi murna a cikin ka, bari waɗanda ke ƙaunar cetonka koyaushe su ce, "A yabi Allah."5Amma ni matalauci ne mai bukata, ka yiwo sauri wurina Allah, kai ne taimakona ka kuɓutar dani, Yahweh, kada ka yi jinkiri.

71

1Yahweh, a gare ka nake samun mafaka, kada ka taɓa bari in ji kunya.2Ka kuɓutar da ni ka sa in zauna lafiya cikin adalcinka.3Ka zama dutsen fakewa a gare ni inda zan zo ko yaushe, ka bada umarni a cece ni, gama kai ne dutsena da kagarata.

4Ka cece ni, Allahna daga hannun miyagu, daga masu shirya mugunta.5Gama kai ne begena, Ubangiji Yahweh. Na dogara gare ka tun ina yaro.
6Kai ne kake ta taimako na tun daga cikin ciki; kai ne ka fito dani daga cikin mahaifiyata; yabona a gare ka ya ke koyaushe.7Na zama misali ga mutane da yawa, kai ne mafakata mai ƙarfi.
8Bakina zai cika da yabonka, da ɗaukakarka dukkan yini.9Kada ka yashe ni a lokacin dana tsufa, kada ka manta dani lokacin da ƙarfina ya ƙare.
10Gama maƙiyana maganata, waɗanda ke neman raina suna shiri tare.11Sun ce, "Allah ya yashe shi, ku bi ku ɗauko shi, gama ba wanda zai cece shi."
12Allah, kada ka yi nisa dani, Allahna, ka yi sauri ka taimake ni.13Bari su sha kunya su hallaka su waɗanda suka hasalar da raina; su ji kunya su hallaka. bari zarga da raini su rufe su, su waɗanda ke so su lahanta ni.
14Amma zan sa begena a gare ka, zan yabe ka gaba-gaba.15Bakina zai yi maganar adalcinka da cetonka dukkan yini, koda yake ba zan iya gane shi ba.16Zan zo da manyan ayyukan Ubangiji Yahweh, zan faɗi adalcinka, naka kaɗai.
17Allah, ka koya mani tun ina saurayi, har yanzu ina shelar ayyukanka na ban mamaki.18I, ko lokacin da kaina ya yi furfura, Allah, kada ka yashe ni, ina ta shelar ƙarfinka ga tsara mai zuwa, ikonka kuma ga kowanne mai zuwa.
19Adalcinka kuma, ya Allah yana da tsawo ƙwarai, kai da ka yi manyan abubuwa, Allah, wane ne kamar ka?20Kai da ka nuna mana wahalhalu da yawa masu tsanani, za ka farfaɗo damu, ka fito damu daga ƙarƙashin ƙasa.
21Ka ƙara mani martaba, ka juyo ka ƙarfafa ni.22Zan kuma yi maka godiya da molo saboda amincinka, Allahna; gare ka zan yi yabo da molo, mai tsarki na Isra'ila.
23Leɓunana zasu yi sowa ta farinciki, sa'ad da nake raira yabo a gare ka-har da raina, wanda ka fanso.24Harshena kuma zai yi maganar adalcinka dukkan yini; gama sun ji kunya sun rikice, su waɗanda ke nema su lahanta ni.

72

Zabura ta Suleman.

1Ka ba sarki dokokinka masu adalci, Allah, adalcinka kuma ga ɗan sarkin.2Dãma ya hukunta jama'arka da adalci, matalautanka kuma da adalci.3Dãma duwatsu su fito da salama saboda mutanenka; dãma tuddai kuma su fito da adalci.

4Dãma ya hukunta mutane matalauta; dãma ya ceci 'ya'yan mabuƙata, ya ragargaza azzalumi.5Dãma su ba ka daraja muddin rana tana haskakawa, wata kuma yana nan har zuwa tsararraki dukka.
6Dãma ya sauko kamar ruwan sama a kan ciyawar da a ka tattake, kamar zubowar ruwan sama a kan ƙasa.7Dãma masu adalci su yalwata a kwanakinsa, dãma kuma a sami salama a yalwace har sai wata ya shuɗe.
8Dãma ya yi mulki daga teku zuwa teku, daga kogi har zuwa ƙarshen duniya.9Dãma waɗanda ke zama a jeji su rusuna a gabansa; dãma maƙiyansa kuma su lashi turɓaya.10Dãma sarkunan Tarshish da na tsibirai su kawo gaisuwa a gare shi, dãma sarakunan Sheba da Seba su ba shi kyautai.
11I, dãma dukkan sarakuna su rusuna a gabansa, dãma kuma dukkan al'ummai su bauta masa.12Gama ya kan taimaki mabuƙacin da yayi kuka da matalaucin da ba shi da mai taimako.
13Ya ji tausayin mabuƙata da matalauta, ya kuma ceci ran mabuƙata.14Ya fanshi rayukansu daga wahala da kuma wulaƙanci, jininsu kuma yana da daraja a idanunsa.
15Dãma ya rayu! Dãma a ba da zinariyar Sheba a gare shi. Bari mutane su yi masa addu'a koyaushe; dãma Yahweh ya albarkace shi dukkan yini.16Dãma a sami hatsi a yalwace a cikin ƙasa, na kan tudu kuma amfaninsu ya yi yabanya. Dãma kawunan hatsinsu ya zama kamar Lebanon, dãma jama'a su sami albarka kamar ciyawa ta saura.
17Dãma sunansa ya kasance har abada, dãma sunansa ya ci gaba muddin rana ta nan; dãma jama'a su sami albarka ta wurinsa; dãma dukkan al'ummai su kira shi mai albarka.
18Dãma Allah Yahweh, Allah na Isra'ila, ya zama mai albarka; wanda shi kaɗai ne ke yin abubuwan ban mamaki.19Dãma sunansa mai daraja ya zama mai albarka har abada, dãma kuma dukkan duniya ta cika da ɗaukakarsa. Amin -- Amin.20Dauda ɗan Yesse ya gama yin addu'o'insa. Littafi na Uku.

73

Zabura ta Asaf.

1Hakika Allah mai alheri ne ga Isra'ila, gare su da suke da tsabtar zuciya.2Amma a gare ni kafafuna sun kusa su zame; kafafuna sun kusa su zame waje daga karkashina.3saboda na ji kishin masu girmankai sa'ad da na ga wadatar masu mugunta.

4Gama basu da raɗaɗi har ranar mutuwarsu, amma suna da ƙarfi kuma suna ci da kyau. Basu da nawayar sauran mutane;5Basu da masifu kamar na sauran mutane.
6Girmankai na rataye a wuyansu kamar sarƙa; tashin hankali ya rufe su kamar riga.7Daga irin wannan makantar zunubi ke zuwa; mugayen tunani sun ratsa zukatansu
8Suna ba'a kuma suna magana cikin mugunta; cikin fankamarsu suna yin kurarin zalunci.9Suna magana gãba da sammai, harsunan su kuma na tattaki a ƙasa.
10Domin haka mutanensa sun juya gare su isassun ruwaye sun cika kwararo.11Suka ce, "Ta yaya Allah ya sani? Akwai wani sani a wurin maɗaukaki?"12Kula: waɗannan mutane mugayene; a koyaushe a huce suke, sai ƙara zama mawadata suke yi.
13Lallai a banza na kiyaye zuciyata kuma na wanke hannuwana cikin rashin laifi.14Kowacce rana ina shan azaba da horo kowacce safiya.15Idan nace, "Zan faɗi waɗannan abubuwa," da naci amanar wannan tsarar ta 'ya'yanka.
16Ko da shike na yi ƙoƙarin fahimtar waɗannan abubuwa, ya zama da wahala a gare ni.17Daga nan sai na tafi cikin wuri mai tsarki na Allah daga nan na fahimci makomarsu.
18Hakika ka sanya su a wurare masu santsi; ka kawo su ƙasa ga hallaka.19Yadda suka zama jeji farat ɗaya! ƙarshensu yazo sun ƙarasa cikin babban tsoro.20Sun zama kamar mafarki bayan da mutum ya farka; Ya Ubangiji, sa'ad da ka tashi, ba zaka yi tunanin komai game da waɗannan mafarkan ba.
21Gama zuciyata ta damu, a cikina nayi rauni. Na zama jahili na kuma rasa basira;22Na zama kamar dabba marar tunani a gabanka.
23Duk da haka kullum ina tare da kai; Ka riƙe hannuna na dama.24Zaka bishe ni da shawarar ka bayan wannan ka karɓe ni zuwa ɗaukaka.
25Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba wani a duniya da nake marmari in ba kai ba.26Jikina da zuciyata sun yi sanyi, amma Allah shi ne ƙarfin zuciyata har abada.
27Waɗanda suke nesa da kai zasu lalace; zaka hallaka dukkan marasa aminci gare ka.28Amma ni, abin da nake bukata shi ne in kusanci Allah. Na mai da Ubangiji Yahweh mafakata. Zan bayyana dukkan ayyukanka.

74

Salon waƙar Asaf.

1Ya Allah, don me ka yashe mu har abada? Don me fushin ka yayi ƙuna a kan tumakin makiyayarka?2Ka da tuna mutanenka, waɗanda ka saya a zamanin dã, kabila wadda ka fãnsa su zama abin gãdonka, da Tsaunin Sihiyona, inda kake zama.

3Kazo ka dubi dukkan hallakarwa, dukkan ɓarnar da maƙiyi yayi a cikin wuri mai tsarki.4Abokan gãbar ka sun yi ruri a tsakiyar zaɓaɓɓen wurinka; sun kafa tutocin yaƙinsu.5Sun sassare ruƙuƙin kurmi da gatura.6Sun ragargaza sun kuma sassake su dukka; sun karya su da gatura da gudumai.
7Sun kunna wa wurinka mai tsarki wuta; sun tozarta wurin zaman ka, sun buga shi har ƙasa.8A cikin zuciyarsu suka ce, "Zamu hallakar dasu dukka," Sun ƙone dukkan wuraren taruwarka cikin ƙasar.
9Bamu ga wasu alamu ba; ba sauran wani annabi, ba wani a cikin mu da yasan har yaushe wannan zai ƙare.10Ya Allah, har yaushe maƙiyi zai yi ta cin mutuncin ka? Maƙiyi zai yi ta saɓon sunanka har abada?11Donme ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fito da hannunka na dama daga cikin rigarka ka hallaka su.
12Duk da haka Allah sarkina ne tun zamanun dã, mai kawo ceto a duniya.13Ka raba teku da ƙarfinka; ka farfasa kawunan dodannin teku cikin ruwaye.
14Ka murƙushe kan Lebiyatan; ka ciyar da waɗanda suke zama cikin jeji da shi.15Ka karya buɗaɗɗun maɓuɓɓulai da ƙoramai; kasa koguna masu gudu su ƙafe.
16Yini naka ne, dare kuma naka ne; kaine ka sanya rana da wata.17Kaine ka sanya dukkan iyakokin duniya; kayi damina da rani.
18Yahweh, Ka tuna yadda maƙiyi yayi ta jefa maganganun banza a kanka, wawayen mutanen nan sun yi saɓon sunanka.19Kada ka miƙa ran kurciyarka ga naman jeji. Kada ka manta da ran mutanenka da ake zalunta har abada.
20Katuna da alƙawarinka, gama wurare masu duhu na ƙasa suna cike da tashin hankali.21Kada ka bari waɗanda ake zalunta su dawo cikin kunya; bari talakawa da waɗanda ake zalunta su yabi sunanka.
22Ka tashi, ya Allah; ka kãre mutuncinka; ka tuna yadda wawaye suke zaginka dukkan yini.23Kada ka manta da muryar magabtanka ko hargowar waɗannan da suke ci gaba da adawa da kai.

75

Domin shugaban mawaƙa; ga Salon murya. Zabura ta Asaf, waƙa.

1Muna yi maka godiya, ya Allah; muna godiya, domin ka bayyana kasancewarka; mutane suna faɗin ayyukanka na al'ajabi.2A ƙayyadajjen lokaci zanyi hukunci da dai-daita.3Koda ya ke duniya da mazauna cikinta sun girgiza cikin tsoro, na kafa wa duniya ginshiƙai. Selah

4Nace wa masu girmankai, "Kada kuyi girmankai," ga masu mugunta kuma, "Kada ku ɗaga ƙaho;5kada ku ɗaga ƙahonku ga sammai; kada kuyi magana da ɗaga wuya na rashin mutuntawa."6Ba daga gabas bane ko daga yamma, kuma ba daga jeji bane ɗaukaka take fitowa ba.
7Amma Allah ne mai shari'a; yakan ƙasƙantar yakan kuma ɗaukaka sama.8Gama Yahweh ya riƙe ƙoƙon inabi cikin hannunsa mai sa buguwa, wanda yake gauraye da kayan yaji, yana tsiyayar da shi. Hakika dukkan miyagun duniya zasu shanye shi dukka.
9Amma zan ci gaba da faɗin abin da kayi; Zan raira yabbai ga Allah na Yakubu.10Yace, zan datse dukkan ƙahonnin miyagu, amma‌‌ ƙahonnin masu adalci zasu ɗaukaka."

76

Domin shugaban mawaƙa, a bisa kan girayu. Zabura ta Asaf, waƙa.

1Allah ya sanar da kansa cikin Yahuda; sunansa mai girma ne cikin Isra'ila.2Rumfarsa cikin Salem take; wurin zaman sa cikin Sihiyona ya ke.3A can ya kakkarya kibawu na baka, garkuwa da takobi da sauran kayan yaƙi. Selah

4Ka haskaka da sheƙi kuma ka bayyana ɗaukakarka, daka sauka daga duwatsu, wurin daka kashe masu azabtar da kai.5Masu ƙarfin zuciya an washe su; an kashe su. Dukkan jarumawa sun rasa mai taimako.
6Bisa ga tsautawarka, Allah na Yakubu, doki da mahayinsa sun faɗi sun mutu.7Kai, I kaine za a ji tsoro; wa zai tsaya gabanka lokacin da kayi fushi?
8Daga sama kasa aji hukuncinka; duniya ta ji tsoro tayi shiru9lokacin da kai, Allah, ka tashi don tabbatar da hukunci kuma ka ceci dukkan waɗanda ake zalunta na duniya. Selah
10Hakika fushin hukuncin ka akan ɗan adam zai kawo maka yabo; ka yiwa kanka ɗamara da sauran abin da ya ragu na fushinka.
11Kayi alƙawura ga Yahweh Allahnka ka kumaa cika su. Bari duk waɗanda suke kewaye da shi su kawo kyautai gare shi wanda ya isa a ji tsoronsa.12Ya datse ruhun 'ya'yan sarakai; sarakunan duniya sun ji tsoron sa.

77

Domin shugaban mawaƙa; kamar na Yedutun. Zabura ta Asaf.

1Da muryata zan yi kira ga Allah; Zan yi kira da muryata ga Allah, Allah zai ji ni.

2A cikin ranar masifata na biɗi Ubangiji; da dare na miƙar da hannuwana waje, ba kuwa zasu gaji ba. Raina yaƙi ta'azantuwa.3Na tuna da Allah yayin da nayi nishi; Nayi tunaninsa yayin dana sụma. Selah
4Ka riƙe idanuna a buɗe; na damu ƙwarai na kasa magana.5Na tuna da kwanakin dã, game da lokuttan da suka wuce tun-tuni.
6A cikin dare na tuna da waƙar dana taɓa rairawa. Nayi tunani a hankali kuma nayi ƙoƙarin fahimtar abin da ya faru.7Ko Ubangiji zai ƙini har abada? Ba zai ƙara nuna cewa ya ji ɗaɗi na ba?
8Amintaccen alƙawarinsa ya tafi har abada? Ko alƙawarinsa ya tsinke har abada?9Ko Allah ya manta zama mai alheri? Ko fushinsa ya kulle jinƙansa ne? Selah
10Nace, "Wannan baƙinciki na ne: Canjin hannun dama na Maɗaukaki a kanmu."
11Amma zan tuna da ayyukanka; Zan yi tunani game da ayyukanka na al'ajabi na dã.12Zan yi bin-binin dukkan ayyukanka kuma in yi tunani a kansu.
13Hanyarka, ya Allah, mai tsarki ce, ba wani allah da za a kwatanta shi da Allahnmu babba?14Kaine Allah wanda kake aikata al'ajibai; ka bayyana ƙarfinka tsakanin dangogi.15Ka ba mutanenka nasara ta wurin girman ikonka - zuriyar Yakubu da Yosef. Selah
16Ruwaye sun ganka, ya Allah; ruwaye sun ganka, kuma sunji tsoro; zurfafa sun raurawa.17Giza-gizai sun zubo da ruwa ƙasa; hadarin sammai sun yi tsawa; hasken walƙiyarka sun tashi kamar kibau.
18Muryar tsawarka an ji ta cikin guguwa; hasken ya ɗaga duniya; duniya ta raurawa ta girgiza kuma.19Hanyarka tabi ta teku tafarkin ka kuma ta manyan ruwaye, amma ba a ga sawayenka ba.20Ka bi da mutanenka kamar garken tumaki ta hannun Musa da Haruna.

78

Salon waƙar Asaf.

1Ku ji koyarwata, ya mutanena, ku saurari maganar bakina.2Zan buɗe bakina cikin misalai; Zan raira game da ɓoyayyun abubuwa na dã.

3Waɗannan sune abubuwan da muka ji muka kuma koya, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana. Ba zamu ɓoye su daga zuriyarsu ba.4Zamu sanar da tsara mai zuwa game da yabban ayyukan Yahweh, ƙarfinsa, da al'ajiban da ya aikata.
5Gama ya tabbatadda shaidar alƙawari cikin Yakubu ya sanya shari'a cikin Isra'ila. Ya umarci kakanninmu cewa su koyar dasu ga 'ya'yansu.6Ya umarta wannan domin tsara mai zuwa ta iya sanin umarnansa, 'ya'yan da ba a haifa ba, su kuma su faɗi wa 'ya'yansu.
7Daga nan sai su sa zuciyarsu ga Allah kada su manta da ayyukansa amma su kiyaye dokokinsa.8Daga nan ba zasu zama kamar kakanninsu ba, da suka zama da taurin kai da tsara mai tayarwa, tsarar da zukatansu ba dai-dai suke ba, waɗanda ruhohinsu basu tsaya sun yi aminci ga Allah ba.
9'Ya'yan Ifraim sun riƙe makamai tare da bakukkuna, amma suka juya baya a ranar yaƙi.10Basu kiyaye alƙawari da Allah ba, suka ƙi yin biyayya da dokarsa.11Suka manta da ayyukansa, ayyukan al'ajiban daya nuna masu.
12Sun manta da ayyukan mamaki da yayi a idanun kakanninsu a cikin ƙasar masar, cikin ƙasar Zowan.13Ya raba teku ya ƙetaradda su; ya sa ruwa ya tsaya kamar bangaye.14Da rana ya bishe su da girgije dukkan dare kuma da hasken wuta.
15Ya tsaga duwatsu cikin jeji, ya basu ruwa a yalwace, isasshe dake iya cika zurfafan teku.16Yasa rafuffuka su malala daga cikin dutse ya kuma sa ruwan ya gudana kamar koguna.
17Duk da haka suka ci gaba da yi masa zunubi, suna tayar wa Maɗaukaki cikin ƙasa busasshiya.18Suka ƙalubalanci Allah cikin zukatansu ta wurin tambayar abinci domin ƙosar da marmarinsu.
19Sun yi wa Allah baƙar magana; suka ce, "Zai yiwu Allah ya shirya teburi a cikin jeji?20Duba, lokacin da ya bugi dutsen, ruwaye suka ɓullo rafuffuka suka yi ambaliya. Amma zai yiwu ya bada gurasa kuma? Zai iya tanada nama domin mutanensa?"
21Lokacin da Yahweh ya ji wannan, yayi fushi; wutarsa tayi ƙuna akan Yakubu, fushinsa kuma ya hari Isra'ila,22saboda basu gaskata Allah ba basu kuma dogara ga cetonsa ba.
23Duk da haka ya umarci sammai a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sararin sama.24Ya zuba masu manna su ci, ya kuma basu hatsi daga sama.25Mutane suka ci abincin mala'iku. Ya aika masu da abinci isasshe.
26Yasa iskar gabas ta hura cikin sama, ta wurin ikonsa kuma ya jagoranci iskar kudu.27Ya zuba masu nama kamar ƙura, tsuntsaye da yawa kamar yashin teku.28Suka faɗo a tsakiyar sansaninsu, ko'ina kewaye da rumfunansu.
29Suka ci suka ƙoshi sosai. Ya basu abin da suke marmari.30Amma duk da haka basu cika ba; tun abincinsu na cikin bakinsu.
31Daga nan fushin Allah ya buge su ya kashe mafi ƙarfin su. Majiya ƙarfin Isra'ila ya buga su ƙasa.32Duk da wannan, sun ci gaba da yin zunubi kuma basu gaskata ayyukan al'ajabansa ba.
33Domin haka Allah ya taƙaita kwanakin su; shekarunsu suna cike da razana.34Duk sa'ad da Allah ya buge su, sai su fara neman sa, za su juyo su neme shi da gaske.
35Zasu tuna cewa Allah ne dutsensu Allah maɗaukaki kuma shi ne mai fansarsu.36Amma suka yi masa daɗin baki suka kuma yi masa ƙarya da maganganunsu.37Gama zukatansu basu dogara gare shi ba, basu yi aminci ga alƙawarinsa ba.
38Amma shi, mai tausayi ne, ya gafarta laifofinsu bai hallaka su ba. I, lokuta da yawa yakan janye fushinsa bai tayar da dukkan hasalarsa ba.
39Ya tuna cikin jiki aka yi su, iska mai wucewa da bata dawowa.40Sau nawa suka yi ta tayar masa cikin jeji suka ɓata masa rai cikin hamada!41Akai akai suka tuhunci Allah suka cakuni Mai tsarki na Isra'ila.
42Ba su tuna da ikonsa ba, yadda ya fanso su daga abokin gaba.43Lokacin da ya aikata alamominsa masu tsoratarwa cikin Masar da al'ajabansa cikin yankin Zowan.
44Ya juyarda kogunan Masarawa su zama jini don kada su sha daga rafuffukansu.45Ya aika da cincirindon ƙudaje da suka cinye su da kwaɗi da suka mamaye ƙasar.46Ya bada amfaninsu ga fãra aikin hannun su kuma ga babe.
47Ya lalata inabinsu da ƙanƙara itatuwansu masu bada 'ya'ya ga jaura.48Ya saukar da ƙanƙara ga garkunansu aradu kuma ta fãɗa akan dabbobinsu.49Ya zuba masu zafin fushinsa. Ya aika da fushi, hasala, da wahala kamar wakili mai kawo masifa.
50Ya baje wa fushinsa hanya; bai barsu su rayu ba amma ya ba she su ga annoba.51Ya kashe dukkan 'ya'yan fari cikin Masar, ɗan farin ƙarfinsu cikin rumfunan Ham.
52Ya fitar da mutanensa waje kamar tumaki ya bishe su cikin jeji kamar garke.53Ya kare su kuma ba su ji tsoro ba, amma teku ya dulmiyadda abokan gabarsu.
54Daga nan ya kawo su kan iyakar ƙasarsa mai tsarki, zuwa tsaunin nan da hannun damansa ya saya.55Ya kori al'ummai daga gaban su ya raba masu gadonsu. Ya sa kabilun Isra'ila suka zauna cikin rumfunansu.
56Duk da haka suka ƙalubalanci da tozartar da Allah Maɗaukaki kuma ba su kiyaye umarnansa ba.57Sun yi rashin aminci suka yi yaudara kamar ubanninsu; suka zama marasa abin dogaro kamar tanƙwararren baka.
58Gama sun sa shi fushi da masujadansu kuma suka harzuƙa shi ga yin kishi da gumakansu.59Sa'ad da Allah ya ji wannan, ya hasala ya ƙi Isra'ila gaba ɗaya.
60Ya yashe da wuri mai tsarki na Shilo, rumfar in da ya zauna a tsakiyar mutane.61Ya bari a ƙwace ƙarfinsa ya bada ɗaukakarsa a cikin hannun abokan gãba.
62Ya miƙa mutanensa ga takobi, yayi fushi da abin gãdonsa.63Wuta ta cinye majiya ƙarfinsu, "yanmatansu kuma ba su sami waƙar aure ba.
64Firistocinsu sun faɗi ta kaifin takobi, gwaurayensu kuma suka kasa yin kuka.65Sa'an nan sai Ubangiji ya farka sai ka ce mai tashi daga barci, kamar jarumi wanda ya fasa kuwwa saboda buguwa da ruwan inabi.66Ya kori magabtansa baya; ya sa su cikin kunya ta har abada.
67Ya ƙi rumfar Yosef, bai kuma zaɓi kabilar Ifraim ba.68Ya zaɓi kabilar Yahuda da Tsaunin Sihiyona wanda yake ƙauna.69Ya gina tsatsarkan wurinsa kamar sammai, kamar duniya wadda ya kafa ta har abada.
70Ya zaɓi Dauda, bawansa, ya ɗauke shi daga wurin tsaron tumaki.71Ya ɗauke shi daga bin tumaki da ƙananan su, ya kawo shi ya zama makiyayin Yakubu, mutanensa, da Isra'ila, abin gãdonsa.72Dauda yayi kiwonsu da mutuncin zuciyarsa, ya bishe su da gwanintar hannuwansa.

79

Zabura ta Asaf.

1Ya Allah bãƙin alummai sun zo cikin gãdonka; sun kazantar da haikalinka maitsarki; sun maida Yerusalem ta zama tsibin kangaye.2Sun bada gawawwakin bayinka a matsayin abinci ga tsuntsayen sararin sama, jikkunan amintattun mutanenka ga dabbobin duniya.3Sun zubar da jininsu kamar ruwa kewaye da Yerusalem, ba wanda zai yi jana'izar su.

4Mun zama abin ba'a ga makwabtanmu, ba'a da reni ga waɗanda ke kewaye damu. Har yaushe, Yahweh? Zaka yi ta fushi har abada?5Har yaushe kishin fushinka zai yi ta ci har abada?
6Ka zubo da fushinka kan al'umman da basu san ka ba da bisa mulkokin da basu kira bisa sunanka ba.7Gama sun cinye Yakubu sun hallaka ƙauyukansa.
8Kada kayi ta tunawa da zunubin kakanninmu har su shafe mu; bari ayyukan jinƙanka su zo kanmu, gama mun yi sanyi ƙwarai.9Ka taimake mu, ya Allah na cetonmu, domin ɗaukakar sunanka; ka cece mu ka yafe zunubanmu sabili da sunanka.
10Don me al'ummai zasu ce, "Ina Allahn su?" Bari jinin bayinka da aka zubar yayi ramako akan al'ummai a idanunmu.11Bari nishin ɗaurarru ya zo gabanka; da girman ikonka ka tsare 'ya'yan waɗanda aka yanke wa mutuwa da rai.
12Ya Ubangiji. Ka maida zagin da ƙasashe maƙwabtanmu suka zazzageka ka sau bakwai bisa cinyoyinsu.13Don haka mu mutanenka da tumakin makiyayarka zamu yi maka godiya har abada. Za mu faɗi yabbanka ga dukkan tsararraki.

80

Domin shugaban mawaƙa shiryayyen salo domin Shoshanayim. Zabura ta Asaf.

1Ka kasa kunne, Ya Makiyayi na Isra'ila, kai mai bida Yosef kamar tumaki; kai mai zama bisan Kerubim, ka haskaka a bisanmu!2A idon Ifraim da Benyamin da Manasse, ka motsa ikon ka; zo ka cece mu.3Ya Allah, ka maishe mu; ka sa fuskarka ta haskaka a bisanmu, mu kuwa zamu tsira.

4Ya Yahweh Allah mai runduna, har yaushe zaka yi fushi da addu'ar mutanenka?5Ka ciyar dasu da gurasar hawaye ka basu hawaye mai yawa su sha.6Kasa mana wani abin da zamuyi jayayya da maƙ‌wabtanmu a kansa, maƙiyanmu kuma suna yi mana dariya tsakaninsu.
7Ya Allah mai runduna; ka dawo damu; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu tsira.8Ka fito da kuringa daga Masar; Ka kori al'ummai ka dasa ta.
9Ka gyara kasa domin ta; ta kafa saiwa ta cika ƙasa.10Duwatsu sun rufe ta da inuwarta, Rassanta suna kama da itacen sida na Allah.11Ta miƙa rassanta har bakin teku tohonta kuma har bakin Kogin Yuferitis.
12Don me ka rushe garunta har dukkan masu wucewa ta hanyar zasu tsinki 'ya'yanta.13Aladun kurmi sun batata, namomin jeji kuma suna kiwo cikin ta.
14Ya Allah mai runduna; ka juyo, ka duba daga sama kayi la'akari ka kula da wannan kuringar.15Wannan itace sauyar daka dasa da hannunka na dama, reshen da kasa ya girma.16An ƙone shi da wuta an sare shi ƙasa; sun hallaka saboda tsautawarka.
17Bari hannunka ya kasance bisa mutumin hannunka na dama, bisa ɗan mutum wanda kasa ya zama da karfi domin kanka.18Daga nan ba zamu juya daga gare ka ba; ka farkar da mu, mu kuwa zamu kira bisa sunanka.
19Ya Yahweh, Allah mai runduna, ka dawo damu; kasa fuskarka ta haskaka a kanmu, ta haka zamu tsira.

81

Domin shugaban mawaƙa bisa ga salon Gitit. Zabura ta Asaf.

1Ku raira da ƙarfi ga Allah karfinmu; ku tada muryar farinciki ga Allah na Yakubu.2Ku raira waƙa ku kaɗa ganga, garaya mai daɗi da molo.3Ku busa ƙahon rago a ranar tsayawar sabon wata, a ranar cikar wata, ranar da bukukuwanmu ke farawa.

4Gama farilla ce ga Isra'ila, sharia da Allah na Yakubu ya bayar.5Ya bada ita a matsayin doka cikin Yosef lokacin da ya tafi gãba da kasar Masar, in da naji muryar da ban fahimta ba.
6Na kawar da nauyin daga kafaɗarsa; an raba hannunsa daga ɗaukar kwando.7A cikin masifa ka yi kira, na taimake ka; Na amsa maka daga duhun tsawar girgije. Na gwada ka a bakin ruwayen Meriba. Selah
8Ku saurara, mutanena, gama zan gargaɗe ku, zan so da kun saurare ni!9Kada wani bãƙon allah ya kasance a cikinku; baza kuyi sujada ga wani bãƙon allah ba.10Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya fito da ku daga kasar Masar. Ku wage bakinku, ni ma in cika shi.
11Amma mutanena basu saurara ga maganata ba; Isra'ila bata yi mani biyayya ba.12Domin haka na bar su da taurinkansu domin suyi abin da suka ga dama.
13Ina ma, mutanena zasu saurare ni; ina ma, mutanena zasu yi tafiya cikin tafarkuna.14Dana hanzarta mamaye abokan gabarsu in kuma juya hannuna akan masu zaluntar su.
15Dama waɗanda suka ƙi Yahweh su faɗi cikin tsoro gabansa! Dama su ƙasƙanta har abada. Zan ciyar da Isra'ila da alkama mai kyau;16Zan ƙosarda ku da zuma daga cikin dutse."

82

Zabura ta Asaf.

1Allah yana tsaye cikin taron jama'ar Allah; cikin tsakiyar alloli yana zartar da hukunci.2Har yaushe zaka yi hukuncin rashin gaskiya ka nuna kana goyon bayan masu mugunta? Selah

3Ka kare talakawa da marasa mahaifa; ka kare hakkin masu shan azaba da marasa galihu.4Ka ceci fakirai da mabukata; ka fisshe su daga hannun mugu.
5Basu da sani basu kuwa da fahimta; suna kai da komowa cikin duhu; dukkan harsasun duniya sun rugurguje.
6Na ce, ku alloline, dukkan ku kuma 'ya'yan Maɗaukaki ne.7Duk da haka za ku mutu kamar mutane kuma ku faɗi kamar ɗaya daga cikin sarakuna."
8Ya Allah, ka tashi, ka shar'anta duniya, gama kana da gãdo cikin dukkan al'ummai.

83

Waƙa. Zabura ta Asaf.

1Ya Allah, kada kayi shiru! Kada ka manta damu kada kuma kaƙi taimakon mu, ya Allah.2Duba, abokan gabarka suna tada hankali, su da suka ƙi ka sun tada kansu.

3Sun shirya wa mutanenka makirci suna ƙulli gaba da waɗanda ka kãre.4Suka ce, "Ku zo mu hallaka su a matsayin al'umma. Daga nan ba za'a ƙara tunawa da sunan Yahweh ba.5"Sun ƙulla Makirci tare dabararsu ɗaya ce; don suyi gãba dakai suka yi ƙawance.
6Wannan ya haɗa da rumfunan Idom da na Ishma'ilawa, da mutanen Mowab da Hagarawa, waɗanda suka ƙulla tare da7Gebal, Ammon, Amalek; ya kuma haɗa da Filistiya da mazaunan Taya.
8Assuriya kuma ta hada kai dasu; suna taimakon zuriyar Lot. Selah
9Kayi masu kamar yadda kayi wa Midiyan kamar yadda kayi da Sisera da Yabin a Kogin Kishon.10Suka hallaka a Endo suka zama kamar taki domin ƙasa.
11Ka sa shugabanninsu sun zama kamar Oreb da Zib, da dukkan sarakunansu kamar Ziba da Zalmunna.12Suka ce, "Bari mu ɗaukar wa kanmu makiyayar Allah."
13Ya Allahna, ka maishe su kamar ƙurar guguwa, kamar ƙaiƙai gaban iska,14kamar wuta mai cin kurmi, kamar harshen wuta mai kama duwatsu.15Ka koresu da iskarka mai ƙarfi, ka razanar dasu da guguwar hadari.
16Ka cika fuskokinsu da kunya domin su nemi sunanka, Ya Yahweh,17bari su sha kunya su firgita har abada; dama su lalace cikin kunya.
18Daga nan zasu sani kai kaɗai ne, Yahweh, kai ne Maɗaukaki bisa dukkan duniya.

84

Domin shugaban mawaƙa; Bisa ga salon Gitit. Zabura ta 'ya'yan Kora.

1Ina misalin ƙaunar wurin da kake zaune, Yahweh mai runduna!2Ina marmarin harabun Yahweh, marmarin da nake da shi dominsa yasa na suƙe. Zuciyata da dukkan kome nawa ya kira ga Allah mai rai.

3Har tsaddu ta samar wa kanta gida mashillira ta yi wa kanta sheka inda zata ajiye 'ya'yanta kusa da bagadanka, Yahweh mai runduna, sarkina, Allahna kuma.4Masu albarkane waɗanda suka zauna cikin gidanka, zasu yita ci gaba da yabonka. Selah
5Mai albarkane mutumin da ƙarfinsa yana cikinka, wanda zuciyarsa ke marmarin zuwa Sihiyona.6Cikin ratsawa zuwa kwarin Hawaye, sun iske maɓulɓulan ruwa domin sha. Ruwan farko ya rufe shi da albarku.
7Suna tafiya daga karfi zuwa karfi; kowanne ɗayan su ya bayyana gaban Allah cikin Sihiyona.8Yahweh Allah mai runduna, kaji addu'ata; Allahn Yakubu, ka saurari abin da nake cewa! Selah9Ya Allah, ka duba garkuwarmu; ka nuna damuwarka ga shafaffenka.10Gama yini ɗaya cikin harabunka ya fi dubu a wani wuri. Na gwammace in zama mai tsaron ƙofa cikin gidan Allahna, da in zauna tsakanin rumfuna na masu mugunta.
11Gama Yahweh Allah shi ne ranar mu da garkuwa;12Yahweh zai bada alheri da ɗaukaka; ba ya hana wani abu mai kyau ga waɗanda suke tafiya cikin gaskiya. Yahweh mai runduna, mai albarkane mutumin da ya ke dogara gare ka.

85

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta 'ya'yan Kora.

1Yahweh ka nuna wa ƙasarka tagomashi; ka dawo da lafiya da arzikin Yakubu.2Ka yafe zunubin mutanenka; ka rufe dukkan zunubinsu.

3Ka janye dukkan fushinka; ka juya baya daga zafin fushinka.4Ka dawo damu, Allahn cetonmu, kasa rashin jindaɗinka tare da mu ya wuce.5Zaka yi ta fushi da mu har abada? Zaka yi ta yin fushi har ga tsararraki masu zuwa?
6Ba zaka sake falkar damu ba? Daga nan mutanenka za suyi murna a cikin ka.7Ka nuna ma na amincin alƙawarinka ya Yahweh, ka bamu cetonka.
8Zan saurari abin da Yahweh Allah zai ce, gama zai kawo salama ga mutanensa, amintattun mabiyansa. duk da haka ba zasu koma ga bin hanyoyinsu na wauta ba.9Hakika cetonsa yana kusa da masu tsoronsa; daga nan ɗaukaka zata zauna cikin ƙasarmu.
10Alƙawarin aminci da gaskiya sun haɗu tare; adalci da salama sun yi wa juna sumba.11Gaskiya tana tsirowa daga ƙasa, adalci yana kallo daga sama.
12I, Yahweh zai ba da albarku masu kyau, ƙasarmu zata bada amfaninta.13Adalci zai tafi gabansa kuma zai yi hanya domin sawayensa.

86

Addu'ar Dauda.

1Ka saurara, Yahweh, ka kuma amsa mani, domin ni matalauci ne, wanda aka tsanantawa.2Ka kare ni domin ina biyayya, ya Allahna, ka ceci bawanka wanda ya ke dogara a gare ka.

3Ka yi mani jinƙai, ya Ubangiji, don a gare ka nake kuka dukkan yini.4Kasa bawanka yayi murna domin a gare ka nayi addu'a ya Ubangiji.
5Ubangiji, kai nagari ne, kuma kana shirye kayi gafara. Kana kuma nuna jinƙai ga duk waɗanda suka yi kuka gare ka.6Yahweh, ka ji addu'ata, ka kuma ji muryar roƙona.7A ranar masifata nayi kira gare ka, domin zaka amsa mani.
8Ya Ubangiji ba wanda za a kwatanta shi da kai a cikin alloli, ba ayyukan da za a kwatanta su da naka.9Dukkan al, umman da kayi zasu zo su rusuna maka. Za su girmama sunanka.
10Domin kana da girma kana kuma yin abubuwan al'ajabi, kai kaɗai ne Allah.11Ka koya mani tafarkinka Yahweh. Sa'an nan zan yi tafiya cikin gaskiyarka. Ka haɗa zuciyata ta girmamaka.12Ubangiji Allahna zan yabe ka da dukkan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
13Domin alƙawarinka mai aminci yana da girma a gare ni, domin ka ceto raina daga zurfafan Lahira.14Ya Allah marasa hankali sun tasar mani. Ƙungiyar masu husuma sun tasar mani suna neman raina, ba su kula da kai ba.
15Amma kai, Ubangiji, Allah ne mai jinƙai da alheri, mai jinkirin fushi, mai mayalwacin alƙawari mai aminci da kuma madogara.16Ka juyo wurina kayi mani jinƙai; ka bada ƙarfinka ga bawanka; ka ceci ɗan baiwarka.17Ka nuna mani alamar jinƙanka. Sa'an nan waɗanda ke ƙi na zasu gani su kunyata saboda kai, Yahweh, ka taimake ni ka kuma ta'azantar dani.

87

Zabura ta 'ya'yan Kora; waƙa.

1Akan dutse mai tsarki birninsa da ya samo ya tsaya;2Yahweh yana ƙaunar ƙofofin Sihiyona fiye da rumfuna na Yakubu.3An faɗi maɗaukakan abubuwa game da kai birnin Allah. Selah.

4Na ambaci Rahab da Babila ga masu bi na. Duba, akwai Filistiya, da Taya, tare da Itofiya- kuma zasu ce, 'Wannan an haife shi a can.'"
5Ga Sihiyona za'a ce, "Dukkan wɗannan an haife su a cikinta, kuma Mafi Girma dukka da kansa zai kafa ta."6Yahweh ya rubuta a cikin littafin ƙidaya na al'ummai, "Wannan an haife shi a can." Selah
7Haka kuma mawaƙa da masu rawa suka faɗa tare, "Dukkan maɓulɓulaina suna cikinka."

88

Waƙar zabura ta 'ya'yan Kora; domin shugaban mawaƙa; da aka shirya bisa ga salon Mahalat Leyanot. Salon Heman Ezrahiye.

1Yahweh, Allah na cetona, Na yi kuka a gabanka dare da rana.2Ka ji addu'ata, ka saurari kukana.

3Domin na cika da damuwoyi, raina kuma ya kai Lahira.4Mutane sun ɗauke ni kamar waɗanda suka faɗa rami; Mutumin da ba shi da ƙarfi.
5An yi watsi da ni a cikin matattu; Ina kama da matacce dake kwance a kabari, game da wanda ka daina kula da shi saboda an datse su daga ikonka.6Ka ajiye ni a wuri mafi ƙasƙanci na cikin rami, a wuri mai zurfi da kuma duhu.
7Fushinka yayi nauyi a kaina, kuma dukkan rigyawarka tabi ta kaina. Selah
8Saboda kai, abokan tarayyata suka yashe ni. Ka maishe ni abin rawar jiki a gare su. An shinge ni a ciki ba kuma zan tsira ba.
9Idanuna sun gaji da damuwa; Dukkan yini ina kira gare ka, Yahweh; na buɗe hannuwana gare ka.10Ko zaka yi mu'ujuzai ga matattu? Ko waɗanda suka mutu zasu tashi su yabe ka? Selah
11Ko za'a yi shelar alƙawarin amincinka a kabari, amincinka kuma a wurin matattu?12Ko za'a san ayyukanka na al'ajibai a cikin duhu, ko kuma adalcinka a wurare na mantuwa?
13Amma nayi kuka gare ka, Yahweh; da safe addu'ata tana zuwa gare ka.14Yahweh me yasa ka ƙi ni? Me yasa ka ɓoye fuskarka daga gare ni?
15Har kullum an tsananta mani kamar a hallaka ni tun daga ƙuruciyata. Na sha hukuncin horonka ina cikin fargaba.16Ayyukanka na fushi sun bi ta kaina, kuma ayyukanka masu ban razana sun kawar da ni.
17Sun kewaye ni kamar ruwa a dukkan yini; dukkan su sun kewaye ni.18Ka kawar da abokaina da duk waɗanda suka shaƙu dani daga gare ni. Wanda ya shaƙu dani duhu ne kaɗai.

89

Salon Etan Ezrahiye.

1Zan raira yabon ayyukan alƙawarin amincin Yahweh na har abada, Zan yi shelar gaskiyarka ga tsararraki masu zuwa.2Domin na ce "Anyi amintaccen alƙawari na har abada; ka kuma kafa gaskiyarka a cikin sammai."

3Na yi alƙawari da zaɓaɓɓena, nayi alƙawari ga Dauda bawana.4Zan kafa zuriyarka har abada, kuma zan kafa kursiyinka a dukkan tsararraki." Selah
5Sammai na yabon al'ajibanka, Yahweh; a na yabon gaskiyarka a taron tsarkaka.6Domin da wane ne za a kwatanta shi da Yahweh a sammai? Wane ne za a kwatanta shi da Yahweh?
7Shi Allah ne dake da girmamawa a taron tsarkaka yana kuma da kwarjini ga dukkan waɗanda suka kewaye shi.8Yahweh Allah mai runduna, wa keda ƙarfi kamar ka? amincinka ya kewaye ka.
9Kana mulkin haukan teku; lokacin da ambaliyoyi su ka tashi ka kwantar da su.10Ka buge Rahab kamar wadda aka kashe. Ka warwatsa maƙiyanka da ƙarfin damtsenka.
11Sammai naka ne, haka kuma duniya. Ka hallici duniya da dukkan abin da ke cikin ta.12Ka hallici arewa da kudu. Tabor da Harmon na murna a cikin sunanka.
13Kana da damtse mai iko da kuma hannu mai ƙarfi, hannunka na dama kuma yana da tsayi.14Aikin adalci da adalci su ne ginshiƙan mulkinka. Alƙawari mai aminci da kuma dogara daga gare ka suke zuwa.
15Masu albarka ne waɗanda ke yi maka sujada! Yahweh, suna tafiya a cikin hasken fuskarka,16Suna murna da sunanka dukkan yini. Ayyukan adalcinka kuma sun ɗaukaka ka.
17Kai ne ƙarfin ikonsu, ta wurin jinƙanka kuma mun yi nasara.18Domin garkuwoyinmu na Yahweh ne; sarkinmu kuma na Mai tsarki na Isra'ila ne.
19Tun da daɗewa kayi magana da tsarkakanka ta wurin wahayi; kace "Na sa kambi bisa mai iko; Na tayar da wani da aka zaɓa daga cikin mutane.20Na zaɓi Dauda bawana, da maina na keɓe shi.21Hannuna zai taimake shi. Damtsena kuma zai ƙarfafa shi.22Ba maƙiyin da zai yaudare shi; ba kuma ɗan magabcin da zai ƙuntata masa.23Zan buge maƙiyansa a gabansa, masu ƙin sa kuma zan hallaka su.
24Gaskiyata da alƙawarin amincina zai kasance tare da shi, ta wurin sunana zai yi nasara.25Zan ɗora hannunsa a kan teku, hannunsa na dama kuma bisa koguna.26Zai yi kira gare ni yace kai ne ubana, 'Kai ne Ubana kuma Allahna, da kuma dutsen cetona.'
27Zan ɗora shi a matsayin ɗan farina, mafi ɗaukaka a cikin sarakunan duniya.28Zan tsawaita alƙawarin amincina a gare shi har abada; zan kuma riƙe alƙawarina da shi.29Zan kafa zuriyarsa har abada, mulkinsa kuma zai kai har sammai.
30Idan 'ya'yansa suka yi watsi da shari'una suka kuma yi rashin biyayya ga sharuɗɗana,31idan kuma sun karya dokokina basu kuma kiyaye umarnaina ba,32to sai in hori rashin biyayyarsu da sandar ƙarfe laifofinsu kuma da nushe-nushe.
33Amma ba zan janye madawammiyar ƙaunata ba daga gare shi ko kuma in yi rashin aminci a kan alƙawarina ba,34Ba zan karya alƙawarina ba ko kuma in canza maganganun leɓuna na ba.
35Sau ɗaya tak na rantse da tsarkina-Ba zan yiwa Dauda ƙarya ba:36zuriyarsa zata ɗore har abada mulkinsa kuma zai zama kamar rana a gabana.37Za a kafa shi har abada kamar wata, amintaccen mashaidi a sararin sama." Selah
38Amma ka ƙi ka kuma yi watsi; kana kuma fushi da shafaffen sarki.39Ka kuma musunta alƙawarin bawanka. Ka ƙazamtar da rawaninsa a ƙasa.40Ka kuma rushe katangunsa dukka. Ka kuma mayar da ƙarfafan kagarunsa kufai.
41Duk masu wucewa suka yi masa ƙwace. Ya zama abin ƙyama a cikin maƙwabta.42Ka tayar da hannun damar maƙiyansa; ka kuma sa dukkan maƙiyansa suyi farinciki.43Ka juya takobinsa ka kuma hana shi ya tsaya a lokacin yaƙi.
44Ka kawo ƙarshen martabarsa; ka kuma karya mulkinsa45Ka gajarta kwanakin ƙuruciyarsa. Ka kuma rufe shi da kunya. Selah
46Yahweh har yaushe? Ko zaka ɓoye kanka, har abada? Har yaushe zaka bar fushinka yayi ta ƙuna kamar wuta?47Oh, ka yi tunanin yadda gajartar lokacina ya ke, da kuma rashin amfanin yadda ka hallici dukkan mutane!48Wane ne zai rayu ba zai mutu ba, ko kuma ya iya kuɓutar da ransa daga Lahira? Selah
49Ya Ubangiji, ina ayyukanka na dã a kan alƙawarin amincinka da ka rantsewa Dauda a cikin gaskiyarka?50Ka tuna ya Ubangiji da rainin da aka yi wa bayinka da kuma yadda na ji a zuciyata ire-iren cin mutunci daga al'ummai.51Maƙiyanka suna nuna wulaƙanci, Yahweh; suna wulaƙanta sawayen keɓaɓɓenka.
52Albarka ta tabbata ga Yahweh har abada. Amin da Amin. Littafi na Huɗu

90

Addu'ar Musa mutumin Allah.

1Ubangiji kai ne mafakarmu a dukkan tsararraki.2Kafin a kafa duwatsu, ko kuma ka hallici duniya da abin dake cikinta, har abada abadin, kai Allah ne.

3Ka kan komar da mutum ƙura, ka ce "ku koma ku zuriyar ɗan adam."4Domin shekaru dubu a gare ka kamar jiya ne data wuce, kamar kuma sa'ar tsaro ce ta dare.
5Ka share su kamar da rigyawa sun kuma yi barci; da safe suna kama da ciyayi da suka yi girma.6Da safe sukan yi yabanya suyi girma; da yamma kuma su kan yanƙwane su bushe.
7Hakika, an cinye mu a cikin fushinka, a cikin fushinka kuma mun gigice.8Ka jejjera zunubanmu a gabanka, laifofinmu na ɓoye kuma kasa su a hasken gabanka.
9Ran mu yana shuɗewa a ƙarƙashin fushinka;10shekarunmu kuma sun wuce da sauri kamar ajiyar zuciya. Shekarunmu saba'in ne, ko kuma tamanin in muna da lafiya; amma koma da shekarunmu mafiya kyau suna cike da damuwa da baƙinciki. Hakika, sukan wuce da sauri sai kuma mu ɓace.
11Wa ya san ƙarfin fushinka, da kuma fushinka da ke dai-dai da tsoronka?12ka koya mana yadda zamu yi la'akari da rayuwarmu domin mu yi rayuwa cikin hikima.13Juya, Yahweh! Har yaushe zai zama? Ka ji tausayin bayinka.
14Ka ƙosar da mu da alƙawarin amincinka da safe domin muyi farinciki a cikin dukkan kwanakinmu.15Ka samu muyi murna gwargwadon kwanakin daka azabtar damu da kuma shekarun da muka fuskanci matsala.16Ka bar bayinka suga aikinka, kuma ka bar 'ya'yanmu suga darajarka.
17Da ma jinƙan Ubangiji Allahnmu ya zama namu; ka wadata aikin hannuwanmu; hakika, ka wadata aikin hannuwanmu.

91

1Wanda ya ke rayuwa a bukkar Mafi Ɗaukaka zai zauna a inuwar Mai Iko Dukka.2Zan ce da Yahweh, "Shi ne mafakata da kagarata, Allahna, wanda na dogara a gare shi."

3Domin zai kuɓutar da kai daga wayon tarkon maharbi kuma daga annoba mai hallakarwa.4Zai rufe ka da fukafukansa, kuma a ƙarƙashin fukafukansa zaka sami mafaka. Madogararsa garkuwa ce da kuma kariya.
5Ba za ka ji tsoron masifa ba da dare, ko kuma kibiyoyin dake shawagi da rana.6Ko kuma annobar dake aukowa da dare ba.7Ko cutar dake samuwa da tsakar rana ba. Dubu zasu faɗi a gefenka dubu goma kuma a hannunka na dama, amma ba zasu iso wurinka ba.
8Zaka duba ne kawai kaga hukuncin da za'a yiwa miyagu,9Domin Yahweh ne mafakata! Kuma ka maida Maɗaukaki mafakarka.
10Ba mugun abin da zai same ka; ba wani abu mai cutarwa da zai kusanci gidanka.11Domin zai umarci mala'ikunsa su kare ka, su kuma yi tsaronka a cikin dukkan hanyoyinka.
12Zasu tayar da kai tsaye da hannunsu domin kada kayi tuntuɓe a kan dutse.13Zaka hamɓare zãkuna da damisoshi a ƙarƙashin ƙafafunka; zaka tattake 'yan zãkoki da kuma macizai.
14Saboda ya sadaukar da kansa gare ni, zan cece shi. Zan kare shi saboda yana yi mani biyayya.15Sa'ad da yayi kira gare ni zan amsa masa. Zan kasance tare da shi a cikin masifa; Zan ba shi nasara zan kuma girmama shi.16Zan ƙosar da shi da tsawon rai in kuma nuna masa cetona.

92

Zabura. Waƙar ranar Asabaci.

1Abu mai kyau ne a yi godiya ga Yahweh, a kuma yi waƙar yabo ga sunanka, Maɗaukaki,2a kuma yi shelar alƙawarin amincinka da safe gaskiyarka kuma kowanne dare,3da garaya mai tsarkiya goma da kuma kayan kaɗe-kaɗe masu daɗi.

4Domin kai, Yahweh, kasa ni murna ta wurin ayyukanka. Zanyi waƙar farinciki saboda ayyukan hannuwanka.5Ina misalin girman ayyukanka, Yahweh! Tunane-tunanenka suna da zurfi.
6Daƙiƙin mutun bai sani ba, haka ma wawa bai fahimci wannan ba:7Lokacin da miyagu suka firfito kamar ciyawa, ko ma a lokacin da miyagu suka taru, duk da haka an miƙa su ga hallaka ta har abada.
8Amma kai Yahweh zaka yi mulki har abada.9Hakika ka duba maƙiyanka, Yahweh! Hakika ka duba maƙiyanka. Hakika zasu hallaka! Duk masu aikin mugunta za'a warwatsa su.
10Ka tada ƙahona kamar na bijimin sã; An keɓe ni da sabon mai.11Idanuna sun ga faɗuwar maƙiyana; kunnuwana kuma sun ji hallakar miyagun maƙiyana.
12Masu adalci zasu yi yaɗo kamar gazarin dabino; zasu yi girma kamar itacen sida na Lebonon.13An dasa sune a gidan Yahweh; Suna sheƙi a harabar Allahnmu.
14Suna ba da 'ya'ya har ma a kwanakin tsufansu; suna nan kore shar,15Don ayi shela cewa Yahweh mai adalci ne. Shi ne dutsena, ba kuma rashin adalci a cikinsa.

93

1Yahweh yana mulki; Yana saye da daraja; Yahweh yasa sutura ya kuma yiwa kansa ɗammara da ƙarfi. An kafa duniya daram; kuma ba zata gusa ba.2Kursiyinka ya kafu tun zamanin dã can; kana nan tun fil azal.

3Tekuna suka tashe, Yahweh; sun ta da muryarsu; raƙuman tekuna sunyi tumbotso sunyi ruri.4Sun fi dukkan sauran ambaliyoyi masu ikon karya teku, Yahweh na sama maigirma ne.
5Manyan umarnanka abin dogara ne na hakika; Yahweh, tsarki ya ƙayata gidanka, har abada.

94

1Yahweh, Allah mai sakayya, Allah mai sakayya ka haskaka a bisan mu.2Ka tashi tsaye mai shari'ar duniya ka ba masu girman kai abin da ya kamance su.

3Har yaushe miyagu, Yahweh har yaushe miyagu za suyi farinciki4Dukkan masu aikin mugunta suna ta yin maganganunsu na wauta; Duk masu mugunta suna fahariya.
5Yahweh; sun buge mutanenka, Sun ƙuntata wa al'ummarka.6Sun kashe gwauruwa da bãƙon dake zaune a ƙasarsu, sun kuma kashe marayu.7Suka ce, "Allah ba zai gani ba, Yahweh na Yakubu bai kula da abin ba."
8Ku lura mutane marasa hankali! Ku wawaye, har sai yaushe zaku koyi darasi?9Shi wanda yayi kunne ashe ba zai ji ba? Shi wanda yayi ido ba ya gani ne?
10Shi dake horon al'ummai, ashe ba zai tsautar ba? Shi ne mai ba da ilimi ga mutum.11Yahweh ya san tunanin mutane, cewa turiri ne kawai.
12Mai albarka ne wanda ka yiwa gargaɗi, Yahweh wanda ka koyar daga cikin shari'arka13Ka bashi hutu a lokutan damuwa har sai da aka gina rami domin miyagu.
14Domin Yahweh ba zai yashe da mutanensa ba ko kuma yayi watsi da abin gãdonsa ba.15Domin hukunci zai sake zama da adalci; kuma dukkan masu tsarkin rai zasu bi shi.16Wa zai tashi ya kuɓutar dani daga masu mugunta?
17In da ba domin Yahweh ya taimake ni ba da yanzu ina can kwance a lahira.18Lokacin dana ce ƙafafuna na barci," Yahweh alƙawarin amincinka ya ɗaga ni sama.19Lokacin da fargaba ya cika ni ta'aziyarka ta kan sani in cika da murna.
20Ko akwai hurɗa tsakaninka da mulkin hallakarwa da ya kafa rashin adalci?21Sun shirya maƙarƙashiya tare domin su kashe mai adalci sun kuma hukuntawa marar laifi mutuwa.
22Amma Yahweh ne babbar hasumiyata, Allahna kuma shi ne dutsen fakewa ta.23Zai saukar masu da laifofinsu zai kuma daddatsa su a cikin aikin muguntarsu. Yahweh Allahnmu zai daddatse su.

95

1Ku zo mu raira yabo ga Yahweh, Sai mu raira waƙar farinciki ga dutsen cetonmu.2Sai mu zo gabansa da godiya, sai mu raira masa yabo da waƙoƙin zabura.3Domin Yahweh Allah ne mai girma, sarki ne mai girma da yafi dukkan alloli.

4Zurfafan duniya dukka a hannunsa suke; Duwatsu masu tsawo kuma nasa ne.5Teku tasa ce, shi ne yayi ta. Hannuwansa kuma suka yi busasshiyar ƙasa.
6Ku zo muyi sujada mu durƙusa ƙasa, sai mu durƙusa a gaban Yahweh mahallicinmu;7Domin shi ne Allahnmu, mu mutanen makiyayarsa ne, tumakin hannunsa kuma. Yau ace dai za ku ji muryarsa!
8Kada ku taurare zuciyarku, kamar a Meriba, ko kuma kamar ranar Massa a cikin jeji,9inda ubanninku suka gwada ni suka kuma jaraba ni, koda ya ke sun ga aikina.
10Shekaru arba'in ina fushi da waccan tsarar na ce, "Waɗannan mutane ne da zuciyarsu ta karkace; basu san hanyoyina ba.11'Domin haka cikn fushina na rantse cewa ba zasu taɓa shiga wurin hutu na ba

96

1Ku raira sabuwar waƙa ga Yahweh; ku raira waƙa ga Yahweh, dukkan duniya.2Ku raira waƙa ga Yahweh, ku albarkaci sunansa; kuyi shelar cetonsa a kowacce rana.

3Ku furta ɗaukakarsa a cikin al'ummai, ayyukansa na ban mamaki a cikin al'ummai.4Domin Yahweh yana da girma ya kuma isa yabo sosai. A ji tsoron sa fiye da dukkan sauran alloli.
5Saboda allolin al'ummai gumaka ne, amma Yahweh ne ya hallici sammai, martaba da wadata suna gabansa.6Jamali da ƙarfi suna cikin wurinsa mai tsarki.
7Kuyi yabo ga yahweh ku dukkan kabilu na mutane, ku yabi Yahweh sabili da ɗaukakarsa da ƙarfinsa.8Ku ba yahweh ɗaukakar da ta dace da sunansa. Ku kawo baiko a haikalinsa.
9Ku durƙusa a gaban Yahweh saye da tufafin dake girmama tsarkinsa. Yi rawar jiki a gabansa, dukkan duniya.10Ku faɗa a cikin al'ummai cewa,"Yahweh ne ke mulki." Hakannan kuma aka kafa duniya; ba kuma zata jijjigu ba. Yana yiwa mutane shari'ar dake dai-dai.
11Sai sammai suyi murna, sai duniya kuma ta yi farinciki; sai teku yayi ruri abin da ke cikinsa kuma su cika da murna.12Filaye suyi murna da duk abin da ke cikin su. Sa'an nan kuma dukkan bishiyoyin duniya su ɓarke da yabo13a gaban Yahweh, domin yana tafe. Yana zuwa domin ya shar'anta duniya. Zai shar'anta duniya da adalci da mutane kuma cikin amincinsa.

97

1Yahweh na mulki sai duniya ta yi murna, sai dukkan ƙasashe masu nisa suyi murna.2Gizagizai da duhu na kewaye da shi. Adalci da gaskiya ne harsashen kursiyinsa.

3Wuta na tafe a gabansa tana cinye magafta ko ina4Walƙiyarsa ta haskaka duniya; duniya ta gani ta furgita.5Duwatsu kuma sun narke kamar tufa a gaban Yahweh Ubangijin dukkan duniya.
6Sararin sama na shaida adalcinsa, dukkan al'ummai kuma sun ga ɗaukakarsa.7Duk waɗanda ke bauta wa abin da hannu ya sassaƙa zasu kunyata, masu taƙama da gumaka marasa amfani- ku rusuna masa da dukkan allolinku!8Sihiyona taji sai tayi farinciki, biranen Yahuda kuma suka yi murna saboda dokokinka na adalci, Yahweh.
9Domin kai, Yahweh, kafi kowa ɗaukaka a cikin dukkan duniya. An ɗaukaka ka fiye da dukkan alloli.10Ku dake ƙaunar Yahweh ku ƙi mugunta! Yana kare ran tsarkakansa, ya karɓo su daga hannun mugun.11An shuka haske domin adalai farinciki kuma domin masu zukata masu aminci.
12Kuyi murna cikin Yahweh ku adalai; ku kuma yi masa godiya lokacin da kuka tuna da tsarkinsa.

98

Zabura.

1Oh, ku raira sabuwar waƙa ga Yahweh domin yayi ayyuka masu ban mamaki; hannunsa na dama da damtsensa sun ba shi nasara.2Yahweh ya sa cetonsa ya sanu; ya nuna adalcinsa a fili ga dukkan al'ummai.

3Ya tuna da alƙawarinsa mai aminci da gaskiya ga gidan Isra'ila; dukkan iyakokin duniya zasu ga nasarar Allahnmu.4Ku raira waƙar farinciki ga Yahweh, dukkan duniya ku ɓarke da waƙa, kuyi waƙa domin murna, kuyi waƙoƙin yabo.
5Ku raira yabo ga Yahweh da garaya, tare da garaya haɗe da waƙoƙi masu daɗi.6Tare da kakaki da ƙarar ƙaho, ku tada muryoyi masu daɗi a gaban Sarki, Yahweh.
7Sai teku yayi ihu da dukkan abin dake cikinsa!8Sai rafuffuka su tafa hannuwansu, sai duwatsu kuma su raira waƙar yabo.9Yahweh yana zuwa domin ya yi wa duniya shari'a da adalci da kuma al'ummai tare da gaskiya.

99

1Yahweh na mulki; bari al'ummai suyi rawar jiki, yana zaune kan kursiyi sama da Kerubim, duniya ta girgiza,2Yahweh yana da girma a Sihiyona yana da ɗaukaka fiye da dukkan al'ummai.3Sai a yabi sunanka mai jamali da girma; yana da tsarki.

4Sarki yana da ƙarfi, yana kuma ƙaunar adalci. ka kafa gaskiya; ka aikata adalci akwai adalci kuma a cikin Yakubu.5A yabi Yahweh Allahnmu a kuma yi sujada a digadigansa. Ya na da tsarki.
6Musa da Haruna na cikin firistocinsa, Sama'ila kuma na cikin waɗanda suka yi addu'a gare shi. Sun yi addu'a ga Yahweh, ya kuma amsa masu.7Ya yi masu magana daga ginshinƙin girgije. Sun kiyaye tsattsarkan umarninsa da farillan da ya basu.
8Ka amsa masu, Yahweh Allahnmu. Kai Allah ne mai gafara a gare su, amma kuma kana horon ayyukansu na zunubi.9Ku yabi Yahweh Allahnmu, ku kuma yi sujada akan tudunsa mai tsarki, gama Yahweh Allahnmu yana da tsarki.

100

Zabura ta Dauda.

1Kuyi ihu da farinciki ga Yahweh ku dukkan duniya,2Ku bautawa yahweh da farar zuciya, kuzo gabansa da waƙoƙin farinciki.

3Ku sani Yahweh Allah ne; yayi mu, mu kuma nasa ne. Tumakin makiyayarsa kuma.
4Ku shiga ƙofofinsa da godiya cikin gidansa da yabo. Kuyi masa godiya ku albarkaci sunansa.5Domin Yahweh nagari ne; alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada gaskiyarsa kuma har dukkan tsararraki ne.

101

Zabura ta Dauda.

1Zan raira alƙawarin aminci da gaskiya; a gare ka, Yahweh, zan raira yabbai.

2Zan yi tafiya cikin aminci. Oh, yaushe zaka zo wurina ne? Ni da gidana za muyi tafiya cikin nagarta.3Ba zan ƙyale mugunta a idanuna ba; Na ƙi mugun aiki marar cancanta; ba zai manne mani ba.
4Ɓatattun mutane zasu rabu dani; bana yin biyayya ga mugunta.5Zan hallaka duk wanda ya yiwa maƙwabcinsa yanke a asirce. Ba zan ƙyale duk wani mai fankama da rashin hankali ba.6Zan nemi masu aminci na ƙasar su zauna a gefena. Masu tafiya cikin gaskiya da riƙon amana ne zasu bauta mani.
7Mayaudara ba zasu kasance a gidana ba; maƙaryata bazan marabce su a idona ba.8Duk safiya zan hallakar da miyagu dukka daga ƙasar; Zan kawar da dukkan miyagu daga birnin Yahweh.

102

Addu'ar wanda ya ke cikin ƙunci sa'ad da yake cikin damuwa ya kuma zuba makokinsa gaban Yahweh.

1Yahweh ka ji addu'ata, Yahweh ka ji kukana dana keyi gare ka.2Kada ka ɓoye mani fuskarka a lokacin da nake damuwa. Ka ji ni. A lokacin da nayi kira gare ka, ka amsa mani da sauri.

3Gama kwanakina sun wuce kamar hayaƙi, ƙasusuwana kuma na ƙuna kamar wuta.4An buge zuciyata na zama kamar ciyawar data bushe. Na manta in ci wani abinci.
5Da nishe-nishena na kullum, na rame.6Na zama kamar zalɓe a hamada; na zama kamar mujiya a kufai.
7Na kwanta ba tare da yin barci ba, kamar tsuntsun dake kaɗaici, shi kaɗai a bisa kan gida.8Maƙiyana nayi mani ba'a; masu yi mani habaici na la'anta sunana.
9Toka ce abincina kuma gurasa abin shana ya gauraye da hawaye na.10Saboda fargaban fushinka ka ɗaga ni sama domin ka fyaɗa ni ƙasa.
11Kwanakina sun zama kamar inuwar data gushe, na kuma yanƙwane kamar ciyawa.12Amma kai Yahweh, kana raye har abada, kuma shahararka ta dukkan tsararraki ce.
13Zaka tashi kayi jinƙai ga Sihiyona. Yanzu ne lokacin nuna mata jinƙai; lokacinta da kasa yayi.14Domin bayinka sun riƙe duwatsunta ƙaunatacce ka ji tausayi saboda ƙurar kufanta.15Al'ummai zasu girmama sunanka, Yahweh, kuma dukkan sarakunan duniya zasu girmama ɗaukakarka.16Yahweh zai sake gina Sihiyona ya kuma bayyana a cikin ɗaukakarsa.
17A wancan lokacin, zai amsa addu'ar wulaƙantattu; ba zai ƙi addu'arsu ba.18Za a rubuta wannan saboda tsararraki masu zuwa, da mutanen da ba'a haifa ba tukuna zasu yabi Yahweh.
19Domin ya dubo ƙasa daga can sammai; Daga samaniya Yahweh ya dubi duniya,20domin ya ji nishe-nishen 'yan sarƙa, ya kuɓutar da waɗanda aka hukuntawa mutuwa.
21Mutane zasu yi shelar sunan Yahweh a Sihiyona da kuma yabonsa a Yerusalem22lokacin da mutane da mulkoki suka tattaru tare su bauta wa yahweh.
23Ya ɗauke ƙarfina a tsakiyar rayuwata. Ya gajarta kwanakina.24Na ce Allahna kada ka kawar dani a tsakiyar rayuwa; kana nan a dukkan tsararraki.
25A can lokacin dã ka kafa duniya a wurinta; sammai kuma aikin hannuwanka ne.26Zasu lalace amma kai zaka dawwama; duk zasu tsufa kamar sutura; kamar tufafi, zaka cire su, zasu kuma ɓace.27Amma kai kana nan yadda kake, shekarunka kuma basu da iyaka.
28'Ya'yan bayinka zasu rayu, zuriyarsu kuma zasu rayu a gabanka."

103

Zabura ta Dauda.

1Ina godiya ga Yahweh da dukkan raina, da dukkan abin da ke cikina, Ina yabon sunansa mai tsarki.2Ina godiya ga Yahweh da dukkan raina, na kuma tuna da dukkan ayyukansa nagari.

3Ya gafarta dukkan zunubanka, ya kuma warkar da dukkan cututtukanka.4Ya ceci ranka daga hallaka yayi maka rawani da alƙawarin aminci da ayyukan jinƙai.5Ya ƙosar da ranka da abubuwa masu kyau domin haka ƙuruciyarka ta sabunta kamar gaggafa.
6Yahweh yakan yi abin dake dai-dai da adalci ga duk waɗanda aka tsanantawa.7ya sanar da hanyoyinsa ga Musa, ayyukansa kuma ga zuriyar Isra'ila.8Yahweh mai jinƙai ne da alheri; yana da haƙuri; yana da matuƙar amincin alƙawari.
9Ba kullum ya kanyi horo ba; ba kullum kuma ya kanyi fushi ba.10Baya yi mana bisa ga gwargwadon zunubanmu ko ya saka mana kan hukuncin zunubanmu ba.
11Domin kamar yadda sammai ke nesa da duniya, to haka girman alƙawarinsa ya ke ga masu girmama shi.12Kamar yadda gabas tayi nisa da yamma hakannan ya kawar da laifofin zunubanmu daga gare mu.13Kamar yadda mahaifi ke tausayin 'ya'yansa, haka Yahweh ke tausayin masu girmama shi.
14Domin yasan yadda aka yi mu; ya sani cewa mu ƙura ne.15mutum kwanakinsa kamar ciyawa ce yakan yi yabanya kamar furen saura.16Iska ta kan hura ta kansa, sai kuma ya ɓace kuma ba wanda zai san yadda yayi girma.
17Amma alƙawarin Yahweh mai aminci har abada abadin ne ga masu girmama shi. Adalcinsa ya kai har ga zuriyar su.18Sun kiyaye alƙawarinsa sun kuma tuna su yi biyayya da dokokinsa.19Yahweh ya kafa kursiyinsa a sammai, masarautarsa kuma na mulkin kowa.
20A yi yabo ga Yahweh, ku mala'ikunsa, ku masu iko dukka dake yin biyayya da maganarsa.21Ku yabi Yahweh, dukkan rundunoninsa, ku bayinsa ne dake yin nufinsa.22A yabi Yahweh, dukkan halittunsa, a dukkan wuraren da ya ke mulki. Zan yabi Yahweh da dukkan raina.

104

1Na bada yabo ga Yahweh da dukkan raina, Yahweh Allahna, kai mai girma ne da ƙawa; Kayi sutura da martaba da daraja.2Ka rufe kanka da haske kamar da sutura; ka shimfiɗa sammai kamar yadda ake simfiɗa labulen rumfa.3Ka shimfiɗa katakan fadodinka a kan gajimarai; ka mai da gajimarai karusanka; kana tafiya akan fika-fikan iska.

4Ya mai da iskoki manzanninsa, harsunan wuta kuma bayinsa.5Ya kafa tushen duniya ba kuma zata jijjigu ba.
6Ka rufe duniya da ruwa kamar sutura; ruwa ya rufe duwatsu.7Tsautawarka nasa ruwaye su janye; da jin ƙarar tsawarka sai suka gudu.
8Duwatsu sun tashi, kwarurruka kuma suka bazu zuwa wuraren da ka shirya masu.9Ka yi masu iyakar da ba zasu tsallake ba; ba zasu ƙara rufe duniya ba.
10Yasa maɓuɓɓugan ruwa su gudana zuwa kwarurruka; maɓulɓulan sun kwarara tsakanin duwatsu.11Suna bayar da ruwa ga dukkan dabbobin saura; jakunan jeji a wurin ne suke kashe ƙishinsu.12A bakin kogunan ruwa tsuntsaye suka yi sheƙunansu; suna raira waƙa a cikin rassa.
13Ya shayar da duwatsu daga ruwansa ya kafa kursiyinsa a sammai. Duniya ta cika da 'ya'yan aikinsa.14Yasa ciyawa ta fito domin dabbobi da kuma tsire-tsire domin mutum ya nome ya sami abinci daga ƙasa.15Yayi inabi domin mutum yayi murna, mai kuma domin fuskarsa tayi haske, abinci kuma domin rayuwarsa.
16Itatuwan Yahweh suna samun ruwa; Sidar Lebanon da ya dasa17Acan tsuntsaye ke yin sheƙunansu. Shamuwa ta mai da itacen sifurus gidanta.18Awakin jeji kuma suna zama a kan duwatsu; rimaye kuma sun mayar da ƙonƙolin duwatsu mafakarsu.
19Yasa wata ya nuna lokuta; rana kuma ta san lokacin faɗuwarta.20Ka yi duhun dare lokacin da duk daji ke fitowa waje.
21Sagarun zakuna kan yi gurnani domin neman abincinsu daga wurin Allah.22Lokacin da rana ta fito sai su koma suyi barci a kogunansu.
23Hakanan mutane kan je waje wurin aikinsu suyi ta aiki har yamma.24Yahweh ayyukanka iri-iri guda nawa ne! Da hikima kayi su dukka; duniya ta cika maƙil da ayyukanka.
25A can kuma sai teku, mai zurfi da faɗi cike da manya da ƙananan hallitu marasa ƙidayuwa,26Jiragen ruwa sukan je can, Lebiyatan kuma a can ya ke, wanda ka yi domin yayi wasa a cikin teku.
27Duk waɗannan gare ka suke zuba ido domin samun abinci a kan lokaci28Lokacin da ka basu, su kan tara; lokacin daka buɗe hannunka, sukan ƙoshi.
29Lokacin da ka ɓoye fuskarka, sukan shiga damuwa; in ka ɗauke numfashinsu sukan mutu su koma ƙura.30Lokacin da ka aiko Ruhunka, aka hallice su, ka kuma sabunta gefen ƙasarsu.
31Dãma ɗaukakar Yahweh ta dawwama har abada; dãma Yahweh ya ji daɗin hallitarsa.32Ya dubi duniya, sai ta girgiza; yakan taɓa duwatsu suyi hayaƙi.
33Zan raira yabo ga Yahweh a dukkan kwanakin raina; zan raira waƙar yabo ga Allah muddin ina raye.34Dãma tunane-tunanena su zama da zaƙi a gare shi; Zan yi murna cikin Yahweh.
35Dãma masu zunubi su hallaka daga duniya, dãma miyagu su ɓace daga duniya. Ina yabon Yahweh dukkan kwanakin raina. A yabi Yahweh.

105

1Ku bada godiya ga Yahweh, ku kira bisa sunansa; ku sanar da ayyukansa cikin al'ummai.2Ku raira gare shi, ku raira yabbai gare shi; kuyi maganar dukkan ayyukansa na ban mamaki.3Kuyi taƙama cikin sunan sa mai tsarki; bari zuciyar waɗanda ke biɗar Yahweh ta yi farinciki.

4Ku biɗi Yahweh da ƙarfinsa kuma; ku biɗi bayyanuwarsa ba fasawa.5Ku tuna da abubuwan ban mamaki da yayi, al'ajibansa da kuma dokoki daga bakinsa,6ku zuriyar Ibrahim bawansa, ku mutanen Yakubu, zaɓaɓɓunsa.
7Shi ne Yahweh, Allahnmu. Dokokin sa suna bisan dukkan duniya.8Cikin ransa yana ajiye alƙawarinsa har abada, maganarsa da ya umarta domin dubun tsararraki.
9Yana tunawa a cikin ransa alƙawarin da yayi da Ibrahim da kuma rantsuwarsa ga Ishaku.10Wannan ne abin da ya tabbatar wa Yakubu a matsayin farilla da Isra'ila a matsayin madawwamin alƙawari.11Ya ce, "Zan baku ƙasar kan'ana a matsayin kasonku na gãdonku."
12Ya faɗi wannan sa'ad da suke kaɗan a lissafi, 'yan kima sosai, kuma suna baƙi a ƙasar.13Suka tafi daga al'umma zuwa al'umma kuma daga masarauta zuwa wata.
14Bai bar wani ya tsananta masu ba; ya tsautawa sarakuna sabili da su.15Ya ce, "Kada ku taɓa shafaffuna, kada kuma ku yi lahani ga annabawana."
16Yayi kira domin yunwa bisa ƙasar; ya yanke dukkan biyan buƙatar gurasa.17Ya aika da mutum gaba da su; Yosef a ka sayar da shi a matsayin bawa.
18Aka ɗaure ƙafafunsa da sarƙoƙi; a bisa wuyansa aka sa maɗaurin ƙarfe,19har sai lokacin da maganganun sa suka zama gaskiya, kuma maganar Yahweh ta gwada shi.
20Sarki ya aika da bayi su sake shi; shugaban mutanen ya 'yantar da shi.21Ya sanya shi lura da gidansa a matsayin shugaban dukkan mallakarsa22ya bayar da umarni ga shugabanninsa yadda ya so ya kuma koyar da dattawansa hikima.23Daga nan Isra'ila ya zo cikin Masar, Yakubu kuma ya zauna na wani lokaci a cikin ƙasar Ham.
24Yahweh yasa mutanen sa suka yi 'ya'ya, ya kuma sa suka yi ƙarfi fiye da maƙiyansu.25Ya kuma sa maƙiyansa suka ƙi Jinin mutanensa, suka muzguna wa bayinsa.26Ya aika da Musa, bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.27Suka aikata alamunsa a tsakiyar masarawa, al'ajibansa a ƙasar Ham.
28Ya aika da duhu ya maida ƙasar duhu, amma mutanen ta basu yi biyayya da umarninsa ba.29Ya maida ruwansu ya zama jini ya kuma kashe kifinsu.30‌Ƙasar ta cika da gungun kwaɗi, har ma cikin ɗakunan shugabanninsu.
31Yayi magana, kuma gungun ƙudaje da ƙwari suka zo cikin dukkan ƙasar.32Ya maida ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da wuta mai ci balbal bisa ƙasarsu.33Ya lalata kuringun inabinsu da itatuwan ɓaurensu; ya karya itatuwan ƙasarsu.
34Yayi magana, fãri suka zo, fãri masu yawan gaske.35Fãrin suka cinye dukkan ganyayyaki a ƙasar; suka cinye dukkan amfanin gona.36Ya kashe kowanne ɗan fãri a cikin ƙasar, 'ya'yan fãrin dukkan ƙarfinsu.
37Ya fito da Isra'ilawa tare da azurfa da zinariya; babu wani cikin kabilunsa da yayi tuntuɓe a hanya.38Masar ta yi farinciki da suka tafi, domin masarawa sunji tsoronsu.39Ya shimfiɗa girgije a matsayin abin rufa ya kuma yi wuta ta haskaka dare.
40Isra'ilawa suka yi roƙon abinci, ya kuma kawo makwarwa ya kuma ƙosar da su da gurasa daga sama.41Ya fasa dutse ruwa kuma ya ɓulɓulo daga gare shi; ya malala cikin jeji kamar kogi.42Domin ya tuna a ransa da alƙawarin sa mai tsarki wanda yayi wa Ibrahim bawansa.
43Ya bida mutanen sa suka fita da farinciki, zaɓaɓɓunsa da sowace-sowace fiye da gaban masu nasara.44Ya basu ƙasashen al'ummai; suka ɗauki mallakar dukiyar mutanen45domin su kiyaye farillansa su kuma yi biyayya da shari'unsa. A yabi Yahweh.

106

1A yabi Yahweh. A bada girma ga Yahweh, domin shi nagari ne, domin alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.2Wa zai lissafa manyan ayyukan Yahweh ko yayi cikakken shelar dukkan ayyukansa da suka cancanci yabo?

3Masu albarka ne waɗanda suke yin abin dake dai-dai, waɗanda kuma a koyaushe ayyukansu baratattu ne.4Ka tuna dani a rai, Yahweh, sa'ad da ka nuna tagomashi ga mutanenka; ka taimake ni sa'ad da ka cece su.5Daga nan zan ga wadatar zaɓaɓɓun ka, in yi farinciki cikin murnar ƙasarka, da ɗaukaka tare da gãdonka.
6Mun yi zunubi kamar Kakanninmu; mun yi laifi, mun kuma aikata mugunta.7Ubanninmu basu yaba wa ayyukanka masu ban mamaki ba a Masar; suka yi banza da ayyukanka masu yawa na alƙawarin aminci; suka yi tawaye a bakin teku, Tekun Iwa.
8Duk da haka, ya cece su domin sunansa saboda ya bayyana ikonsa.9Ya tsautawa Tekun Iwa, ya kuwa bushe. Daga nan ya bida su ta cikin zurfafan, kamar ta cikin jeji.
10Ya cece su daga hannun waɗanda suka ƙi su, ya kuma ƙwato su daga hannun maƙiyansu.11Amma ruwayen suka rufe magaftansu; babu wanin su da ya tsira.12Daga nan suka gaskata maganganunsa, kuma suka raira yabonsa.
13Amma nan da nan suka manta da abin da yayi; ba su jira umarninsa ba.14Suka yi kwaɗayi marar ƙosarwa a jeji, kuma suka ƙalubalanci Allah a cikin hamada.15Ya basu abin da suka roƙa, amma ya aika da cuta wadda ta cinye jikkunansu.
16A sansanin suka zama masu kishin Musa da Haruna, firist mai tsarki na Yahweh.17‌Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta kuma rufe mabiyan Abiram.18Wuta ta ɓarke a tsakaninsu; wutar ta cinye mãsu mugunta.
19Suka yi maraƙi a Horeb suka kuma yi sujada ga sarrafaffar siffar ƙarfe.20Suka musanya ɗaukakar Allah domin siffar maraƙi mai cin ciyawa.21Suka manta da Allah Maicetonsu, wanda yayi manyan ayyuka a Masar.
22Yayi abubuwan ban mamaki a ƙasar Ham ya kuma yi ayyuka masu iko a Tekun Iwa.23Da ya zartar da dokar hallakar dasu, inda ba domin Musa, zaɓaɓɓensa, ya shiga tsakaninsu da shi ba ya juya fushinsa daga hallakar dasu.
24Daga nan suka raina ƙasa mai bayar da amfani; ba su gaskata da alƙawarinsa ba,25amma suka yi gunaguni a rumfunansu, ba su kuma yi biyayya da Yahweh ba.
26Saboda haka ya ɗaga hannunsa kuma ya rantse masu cewa zai barsu su mutu a hamada,27ya warwatsa zuriyarsu cikin al'ummai, ya kuma warwatsa su cikin bãƙin ƙasashe.
28Suka yi sujada ga Ba'al na fowa suka kuma ci hadayun da a ke miƙawa ga matattu.29Suka cakune shi ya yi fushi da ayyukansu, annoba kuwa ta faso a tsakaninsu.
30Daga nan Fenihas ya tashi ya kai ɗauki, annobar kuwa ta tsagaita.31Aka lissafa masa shi a matsayin aikin adalci ga dukkan tsara har abada.
32Suka kuma ba Yahweh haushi a ruwayen Meriba, Musa kuma ya sha wahala saboda su.33Suka sa Musa ya ji haushi, ya kuma yi magana da fushi.34Basu hallakar da al'ummai ba kamar yadda Yahweh ya dokace su,35amma suka gauraye da al'ummai suka kuma koyi hanyoyinsu36kuma suka yi sujada ga gumakansu, waɗanda suka zamar masu tarko.
37Suka yi hadayar 'ya'yansu maza da 'ya'yansu mata ga aljanu.38Suka zubar da jini marar laifi, jinin 'ya'yansu maza da 'ya'yansu mata, waɗanda suka yi hadaya dasu ga gumakan Kan'ana, suka ƙazantar da ƙasar da jini.39Suka ɓãci da ayyukansu; cikin ayyukansu suka zama kamar karuwai.
40Saboda haka Yahweh ya yi fushi da mutanensa, ya kuma rena nasa mutanen.41Ya bayar dasu cikin hannun al'ummai, waɗanda kuma suka ƙi su suka yi mulki a kansu.
42Maƙiyan su suka tsananta masu, aka kuma kawo su ƙarƙashin hukuncinsu.43Lokutta da yawa yazo ya taimake su, amma suka ci gaba da yin tawaye aka kuma kawo su ƙasa ta wurin zunubinsu.
44Duk da haka, ya lura da ƙuncin su sa'ad da ya ji kukansu domin taimako.45Ya tuna a ransa da alƙawarin sa tare dasu ya kuma yi jinkiri saboda matuƙar ƙaunarsa.46Ya sa dukkan waɗanda suka yi nasara dasu suka ji tausayin su.
47Ka cece mu, Yahweh, Allahnmu. Ka tattaro mu daga cikin al'ummai domin mu ba da godiya ga sunan ka mai tsarki mu kuma yi ɗaukaka cikin yabban ka.48Bari Yahweh, Allah na Isra'ila, ya sami yabo daga matuƙa zuwa matuƙa. Dukkan mutane sukace, "Amin." A yabi Yahweh. Littafi na Biyar

107

1Ku ba da godiya ga Yahweh, domin shi nagari ne, kuma alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.2Bari fansassun Yahweh suyi magana, waɗanda ya cafko daga hannun maƙiyi.3Ya tattaro su daga bãƙin ƙasashe, daga gabas daga kuma yamma, daga arewa daga kuma kudu.

4Suka yi yawo a jeji bisa hanyar hamada ba su kuma sami birnin da zasu zauna ba.5Saboda sunji yunwa da ƙishi, suka some cikin gajiya.6Daga nan suka yi kira ga Yahweh cikin damuwarsu, ya kuma ceto su daga ƙuncinsu.7Ya bida su ta miƙaƙƙen tafarki saboda su tafi cikin birnin da zasu zauna.
8Da ma mutane su yabi Yahweh domin alƙawarin amincinsa domin kuma abubuwan ban mamaki da yayi domin 'yan adam!9Domin ya biya buƙatun begen masu jin ƙishi, da marmarin masu jin yunwa ya cika da abubuwa masu kyau.10Waɗansu suka zauna cikin duhu da ɓoyewa, 'yan kurkuku cikin ƙunci da sarƙoƙi.
11Wannan kuwa saboda sun yi tawaye gãba da maganar Yahweh suka kuma yi watsi da umarnin Maɗaukaki.12Ya ƙasƙantar da zukatansu ta wurin shan wuya; suka yi tuntuɓe kuma babu wanda zai taimake su ya ɗaga su.13Daga nan suka yi kira ga Yahweh a cikin damuwarsu, ya kuma fito dasu daga cikin ƙuncinsu.
14Ya fito dasu daga cikin duhu da ɓoyewa ya kuma karya karkiyarsu.15Dãma mutane su yabi Yahweh domin alƙawarin amincinsa domin kuma abubuwan ban mamaki da ya yi domin 'yan adam!16Domin ya karya ƙofofin tagulla ya kuma datse ginshiƙan ƙarfe.
17Sun yi wawanci a cikin hanyoyinsu na tawaye suka kuma ƙuntata saboda zunubansu.18Marmarinsu na cin abinci ya ɓace, suka kuma zo kusa da ƙofofin mutuwa.19Daga nan suka yi kira ga Yahweh a cikin damuwarsu, ya kuma fito dasu daga cikin ƙuncin su.
20Ya aika da maganarsa ya warkar da su, ya kuma ceto su daga hallakarsu.21Dãma mutane su yabi Yahweh domin alƙawarin amincinsa domin kuma abubuwan ban mamaki da yayi domin 'yan adam!22Bari su miƙa hadayun godiya su kuma yi shelar ayyukansa cikin waƙa.
23Waɗansu suka yi tafiya bisa teku cikin jiragen ruwa suka kuma yi sana'o'i bisa tekuna.24Waɗannan sun ga ayyukan Yahweh da al'ajibansa bisa tekuna.
25Domin ya bada umarni ya kuma zuga iskar guguwa dake motsa tekuna.26Suna kaiwa ga sararin sama; su tafi ƙasa cikin zurfafa. Rayuwar suna narkewa cikin ƙunci.27Suna gushewa suyi tangaɗi kamar bugaggu waɗanda kuma suka kawo ga ƙarshen iyawarsu.
28Daga nan suka yi kira ga Yahweh cikin damuwarsu, ya kuma fito dasu daga cikin ƙuncinsu.29Ya tausar da guguwar, kuma raƙuman suka yi tsit.30Daga nan suka yi farinciki saboda tekun ya tausu, ya kuma kawo su in da suke so su sauka.
31Dãma mutane su yabi Yahweh domin alƙawarin amincinsa domin kuma abubuwan ban mamaki da ya yi domin 'yan adam!32Bari su ɗaukaka shi a cikin taron mutane su kuma yabe shi a majalisar dattawa.
33Ya maida koguna suka koma jeji, maɓulɓulan ruwa suka koma busasshiyar ƙasa,34da ƙasa mai bada 'ya'ya zuwa bakararen wuri saboda muguntar mutanenta.35Ya maida jeji kuma ya zama tafkin ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulan ruwa.
36Ya wadatar da masu jin yunwa a wurin, suka kuma gina birni su zauna a ciki.37Suka gina birni su dasa gonaki a ciki, su dasa garkunan inabi, su kuma kawo yalwar kaka.38Ya albarkace su suka zama fiye da lissafi sosai. Bai bar garken dabbobinsu ba su ragu a lissafi.
39Suka ragu aka kuma ƙasƙantar dasu ta wurin ƙunci mai zafi da wahala.40Ya zubo raini bisa shugabanninsu yasa kuma suka yi yawo cikin jeji, in da babu hanyoyi.
41Amma ya kiyaye mabuƙata daga ƙunci ya kuma lura da iyalinsa kamar garken tumaki.42Masu adalci zasu dubi wannan suyi farinciki, dukkan mugunta kuma ta rufe bakinta.43Duk mai hikima ya yi la'akari da waɗannan abubuwa ya kuma yi tunani bisa ayyukan Yahweh na alƙawarin aminci.

108

Zabura ta Dauda.

1Zuciyata ta kafu, Allah; zan raira, I, zan raira yabbai kuma tare da zuciyata ta girmamawa.2Ku tashi, sarewa da garaya; zan tashi da asuba.

3Zan bada godiya gare ka, Yahweh, a tsakanin mutane; zan raira yabbai gareka a tsakanin al'ummai.4Domin alƙawarin amincinka mai girma ne sama da sammai; amincin ka kuma ya kai sararin sama.
5Ka ɗaukaka, Allah, sama da sammai, bari kuma darajarka ta ɗaukaka sama da dukkan duniya.6Domin waɗanda kake ƙauna su sami ceto, ka ceto mu da hannunka na dama ka kuma amsa mani.
7Allah yayi magana cikin tsarkinsa; "Zan yi farinciki; zan raba Shekem in kuma yi kason kwarin Sukkot.8Giliyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Ifraim ma ƙwalƙwali nane; Yahuda kuma sandar sarautana ne.
9Mowab kwanon wankina ne; bisa Idom zan jefa takalmina; Zanyi sowa cikin nasara saboda Filitiya.10Wa zai kawo ni ckin birni mai karfi? Wa zai bida ni zuwa Idom?"
11Allah, baka watsar damu ba? Baka tafi cikin yaƙi tare da mayaƙanmu ba.12Ka ba mu taimako gãba da maƙiyinmu, domin taimakon mutum wofi ne.13Zamu yi nasara da taimakon Allah; zaya tattake maƙiyanmu.

109

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta Dauda.

1Allah wanda nake yabo, kada ka yi shiru,2Domin miyagu da macuta sun kawo mani hari; sun faɗi ƙarairayi game dani.3Sun kewaye ni kuma sun faɗi abubuwan ƙiyayya, kuma sun kawo mani hari babu dalili.

4A ramuwar ƙaunata sun kawo mani sãra, amma nayi addu'a domin su.5Sun biya nagarta ta da mugunta, kuma sun ƙi ƙauna ta.
6Ka naɗa mugun mutum bisa irin waɗannan maƙiya kamar waɗannan mutanen; ka naɗa mai sãra ya tsaya a hannun damansa.7Idan aka shar'anta shi, bari a same shi mai laifi; bari addu'arsa a ɗauke ta zunubi.
8Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani ya ɗauki gurbinsa.9Bari 'ya'yansa su zama marasa mahaifi, matar sa kuma gwauruwa.10Bari 'ya'yan sa su tafi gantali da bara. Suna roƙon abin da aka rage yayin da suka bar rusassun gidajensu.
11Bari mai bin bashi ya ɗauke dukkan abin da ya mallaka; bari bãƙi su washe abin da ya ke samu.12Kada wani ya miƙa wani halin kirki gare shi; kada wani ya ji tausayin 'ya'yansa marasa mahaifi.13Bari a datse 'ya'yan sa; bari a share sunansu daga tsara ta gaba.
14Bari a faɗi zunuban kakanninsa ga Yahweh; bari kuma kada a manta da zunubin mahaifiyarsa.15Bari laifinsu a koyaushe ya kasance a gaban Yahweh; Bari Yahweh ya datse tunawa dasu daga duniya.16Bari Yahweh yayi haka saboda mutumin nan bai kula daya nuna wani alƙawarin aminci ba, amma a maimako ya firgitar da masu shan tsanani, masu buƙata, da masu ɓacin zuciya har ga mutuwa.
17Yana ƙaunar la'ana; bari ta dawo kansa. Yaƙi albarka; bari kada albarka ta zo gareshi.18Ya lulluɓe kansa da la'ana kamar tufafi, kuma la'anarsa ta shiga cikin sa kamar ruwa, kamar mai cikin ƙasusuwansa.
19Bari la'anoninsa su zame masa kamar suturar da ya ke sanyawa ya rufe kansa, kamar ɗamarar da ya ke sanyawa koyaushe.20Bari wannan ya zama rabon masu zargina daga Yahweh, ga waɗanda ke faɗin miyagun abubuwa game dani.
21Yahweh Ubangijina, ka yi mani alheri sabili da sunanka. Saboda alƙawarin amincinka nagari ne, ka cece ni.22Domin ni mai shan tsanani ne mai buƙata kuma, zuciya ta kuma taji ciwo a cikina.23Ina ƙarewa kamar inuwar maraice; Ina kakkaɓewa kamar fãra.
24Gwiwowina sun rasa ƙarfi daga azumi; Ina komawa fata da ƙasusuwa.25Na zama wulaƙantacce wurin masu zargina; idan suka ganni, suna girgiza kawunansu.
26Ka taimake ni, Yahweh Allahna; ka cece ni ta wurin alƙawarin amincin ka.27Bari su san cewa wannan yinka ne, cewa kai, Yahweh, ka yi wannan.
28Koda ya ke sun la'ance ni, ina roƙon ka ka albarkace ni; Idan suka kawo hari, bari su sha kunya, amma bari bawanka yayi farinciki.29Bari magafta na suyi sutura da kunya; bari su sanya kunyar su kamar alkyabba.
30Da bakina na bada babbar godiya ga Yahweh; Zan yabe shi a tsakiyar taro.31Domin zai tsaya a hannun daman wanda keda buƙata; ya cece shi daga waɗanda ke shar'ianta shi.

110

Zabura ta Dauda.

1Yahweh ya cewa ubangijina, "Ka zauna hannun damana har sai na maida maƙiyanka abin takawar ka."

2Yahweh zai riƙe sandar mulkin ƙarfin ka daga Sihiyona; kayi mulki a tsakiyar maƙiyanka.3Mutanenka zasu bi ka cikin tsarkakan tufafi da nufin kansu ranar ikonka; daga mahaifar asubahi ƙuruciyar ka zata zame maka a kamar raɓa.
4Yahweh yayi rantsuwa, kuma ba zai canza ba: "Kai firist ne na har abada, bisa ga ɗabi'ar Melkizadek."
5Ubangiji yana hannun damanka. Zai kashe sarakuna a ranar fushinsa.6Zai shar'anta al'ummai; zai cika filin yaƙi da gawarwaki; zai kashe shugabanni a ƙasashe masu yawa.
7Zai sha daga rafin bakin hanya, daga nan kuma zai ɗaga kansa sama bayan nasara.

111

1Ku yabi Yahweh. Zan bada godiya ga Yahweh da dukkan zuciyata a cikin taron masu adalci, a cikin tattaruwarsu.2Ayyukan Yahweh masu girma ne, ana jira da ɗoki ga dukkan waɗanda ke marmarin su.3Aikin sa mai daraja ne cike da ɗaukaka, adalcinsa kuma ya dawwama har abada.

4Yana yin abubuwan ban mamaki daza a tuna; Yahweh cike da alheri ya ke cike kuma da jinƙai.5Yana bayar da abinci ga amintattun mabiyansa. Za ya tuna a ransa koyaushe da alƙawarinsa.6Ya nuna ayyukansa a cike da iko ga mutanensa inda ya basu gãdon al'ummai.
7Ayyukan hannuwansa sun isa amincewa da hukunci; dukkan umarninsa abin dogara ne.8An kafa su har abada, domin a kiyaye su da aminci a dai-dai kuma.9Ya bada nasara ga mutanensa; ya naɗa alƙawarinsa har abada; tsarki da ban mamaki ne sunansa.
10Girmama Yahweh shi ne farkon hikima; waɗanda suke aikata umarninsa suna da fahimta mai kyau. Yabonsa ya dawwama har abada.

112

1A yabi Yahweh. Mai albarka ne mutumin dake biyayya da Yahweh, wanda ya ke jin daɗin dokokinsa sosai.2Zuriyarsa zasu zama cike da iko a duniya; zuriyar mutum mai tsoron Allah masu albarka ne.

3Dukiya da arziki suna cikin gidansa; adalcinsa zai dawwama har abada.4Haske yana haskaka wa cikin duhu domin taliki mai tsoron Allah; yana cike da alheri, cike da jinƙai, da hukunci.5Yana tafiya lafiya ga mutumin dake aikata alheri da bayar da rancen kuɗi, wanda ke tafiyar da al'amuransa tare da gaskiya.
6Domin ba zai taɓa gusawa ba; mai adalci za a tuna da shi har abada.7Baya jin tsoron mugun labari; yana da ƙarfin hali, dogara ga Yahweh.
8Zuciyar sa lif, ba tare da tsoro ba, har sai ya duba cikin nasara bisa magabtansa.9A yalwace ya ke bayar wa ga talakawa; adalcinsa ya dawwama har abada; za a ɗaukaka shi da girmamawa.
10Wanda ke mugu zai duba wannan kuma ya ji haushi; zai ciza haƙoransa ya kuma narke; marmarin miyagun mutane zaya lalace.

113

1Ku yabi Yahweh. Ku yabe shi ku bayin Yahweh; ku yabi sunan Yahweh.2Albarka ta tabbata ga sunan Yahweh, duk da yanzu da har abada abadin.

3Daga tasowar rana har zuwa faɗuwarta, sunan Yahweh ya sami yabo.4Yahweh ya ɗaukaka sama da dukkan al'ummai, darajarsa kuma ta wuce gaban sararin sammai.
5Wane ne kamar Yahweh Allahnmu, wanda keda mazauninsa a sama,6wanda ke duba sararin sama da duniya?
7Yana taso da talaka daga datti kuma ya ɗaga mabuƙaci daga tarin toka,8domin ya zaunar da shi tare da shugabanni, tare da shugabannin mutanensa.
9Yana bayar da gida ga bakarariyar macen gidan, yana mayar da ita uwar 'ya'ya cike da farinciki. A yabi Yahweh!

114

1Da Isra'ila suka bar Masar, gidan Yakubu daga waɗannan bãƙin mutane,2Yahuda ya zama wurinsa mai tsarki, Isar'ila masarautarsa.

3Teku ya duba kuma ya gudu; Yodan ya juya baya.4Duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai suka yi tsalle kamar 'yan raguna.
5Me yasa ka gudu, teku? Yodan, me yasa ka juya baya?6Duwatsu, me yasa kuka yi tsalle kamar raguna? Ku ƙananan tuddai, me yasa kuka yi tsalle kamar 'yan raguna?7Yi rawar jiki, duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allahn Yakubu.
8Ya juya dutse ya zama tafkin ruwa, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓular ruwa.

115

1Ba gare mu ba, Yahweh, ba gare mu ba, amma ga sunanka ka kawo daraja, domin alƙawarin amincinka domin kuma isar amincewarka.2Me yasa al'ummai zasu ce, "Ina Allahnsu?"

3Allahnmu yana sama; yana yin abin daya so.4Gumakan al'ummai azurfa ne da zinariya, aikin hannuwan mutane.
5Waɗannan gumakai suna da baki, amma ba su magana; suna da idanu, amma basu gani;6suna da kunnuwa, amma basu ji; suna da hanci, amma basu sunsuna wa.
7Waɗannan gumakai suna da hannuwa, amma basu taɓa wa; suna da tafin ƙafafu, amma basu tafiya; ko kuwa suyi magana daga bakunansu.8Waɗanda suka yi su kamar su suke, haka ma duk wanda ya dogara gare su.
9Isra'ila, ku dogara ga Yahweh; shi ne taimakonku da garkuwarku.10Gidan Haruna, ku dogara ga Yahweh; shi ne taimakonku da garkuwarku.11Ku waɗanda ke girmama Yahweh, ku dogara gare shi; shi ne taimakonku da garkuwarku.
12Yahweh yana la'akari damu kuma zai albarkace mu; zai albarkaci iyalin Isra'ila; zai albarkaci iyalin Haruna.13Zai albarkaci waɗanda ke girmama shi, yara da tsofaffi.14Bari Yahweh ya ƙara lissafin ku ƙari da ƙari, naku dana zuriyarku.
15Bari ku yi albarka ta wurin Yahweh, wanda yayi sama da duniya.16Sammai na Yahweh ne; amma duniya ya bayar ga 'yan adam.
17Matattu basu yabon Yahweh, ko kuwa wani wanda ya gangara cikin shiru;18Amma zamu albarkaci Yahweh yanzu da har abada abadin. A Yabi Yahweh.

116

1Ina ƙaunar Yahweh saboda yana jin murya ta da kuma roƙe-roƙe na domin jinƙai.2Saboda yana saurare na, zan yi kira a gare shi muddan ina da rai.

3Sarƙoƙin mutuwa sun kewaye ni, tarkon Lahira kuma ya fuskance ni; naji ƙunci da baƙinciki.4Daga nan nayi kira ga sunan Yahweh: "Ina roƙon ka Yahweh, ka ceto rai na."
5Yahweh yana cike da jinƙai da adalci; Allahnmu mai tausayi ne.6Yahweh yana kiyaye marasa sani; an kawo ni ƙasa, kuma ya cece ni.
7Raina zai koma wurin hutawarsa, domin Yahweh yana yi mani da kyau.8Domin ka ceto raina daga mutuwa, idanu na daga hawaye, tafin ƙafafuna kuma daga tuntuɓe.
9Zan bauta wa Yahweh a ƙasar masu rai.10Na bada gaskiya a gare shi, ko sa'ad da nace, "Ina cikin babban ƙunci."11Nayi garejen cewa, "Dukkan mutane maƙaryata ne."
12Yaya zan biya Yahweh domin dukkan jiyejiyenƙansa zuwa gare ni?13Zan ɗaga ƙoƙon ceto, in kuma yi kira ga sunan Yahweh.14Zan cika alƙawaraina ga Yahweh a gaban dukkan mutanensa.15Abu mai daraja a gaban Yahweh shi ne mutuwar tsarkakansa.
16Yahweh, tabbas, ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka ɗauke tsarƙoƙina.17Zan miƙa maka hadayar godiya in kuma yi kira ga sunan Yahweh.
18Zan cika alƙawaraina ga Yahweh a gaban dukkan mutanensa,19cikin harabun gidan Yahweh, a tsakiyarki, Yerusalem. A yabi Yahweh.

117

1Ku yabi Yahweh, dukkan ku al'ummai; ku ɗaukaka shi, dukkan ku mutane.2Domin alƙawarin amincinsa mai girma ne zuwa gare mu, isar amincin Yahweh kuma ya dawwama har abada. A yabi Yahweh.

118

1Ku bada godiya ga Yahweh, domin shi nagari ne, domin alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.2Bari Isra'ila su ce, "Alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada."

3Bari gidan Haruna su ce, "Alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada."4Bari amintattun masu bin Yahweh su ce, "Alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada."
5A cikin ƙuncina nayi kira ga Yahweh; Yahweh ya amsa mani ya kuma 'yantar dani.6Yahweh yana tare dani; ba zan ji tsoro ba; me mutum zai yi mani?7Yahweh yana gefe na a matsayin mai taimako na; zan duba cikin nasara bisa waɗanda suka ƙi ni.
8Ya fi kyau a ɗauki mahalli cikin Yahweh da a sa dogara cikin mutum.9Gwamma a ɗauki mafaka cikin Yahweh da wani yasa dogararsa cikin sarakuna.
10Dukkan al'ummai sun kewaye ni; a cikin sunan Yahweh na datse su.11Sun kewaye ni; I, sun kewaye ni; a cikin sunan Yahweh na datse su.12Sun kewaye ni kamar zuma; sun ɓace da sauri kamar wuta a tsakiyar sarƙaƙiya; a cikin sunan Yahweh na datse su.
13Sun kawo mani hari saboda su mãke ni ƙasa, amma Yahweh ya taimake ni.14Yahweh ne ƙarfina da farincikina, shi ne kuma ya ceto ni.
15Sowar farinciki ta nasara aka ji a cikin rumfunan adalai; hannun dama na Yahweh ya ci nasara.16Hannun dama na Yahweh ya ɗaukaka; hannun dama na Yahweh yaci nasara.
17Ba zan mutu ba, amma zan rayu kuma inyi shelar ayyukan Yahweh.18Yahweh ya horar da ni da zafi; amma bai miƙa ni ga mutuwa ba.
19Ka buɗe mani ƙofofin adalci; zan shige su kuma zan bada godiya ga Yahweh.20Wannan ce ƙofar Yahweh; adali yana bi ta ciki.21Zan bada godiya a gare ka, domin ka amsa mani, kuma ka zama cetona.
22Dutsen da magina suka watsar ya zama dutsen kusurwa.23Wannan yin Yahweh ne; mai ban mamaki ne a idanunmu.
24Wannan ce ranar da Yahweh ya yi aiki; za muyi farinciki da murna a cikin ta.25Ina roƙon ka, Yahweh, ka bamu nasara! Ina roƙon ka, Yahweh, ka bamu ci gaba!
26Mai albarka ne wanda ya zo cikin sunan Yahweh; mun albarkace ka daga gidan Yahweh.27Yahweh Allahn ne, ya kuma bamu haske; ku ɗaure hadaya da igiyoyi a ƙahonnin bagadi.28Kai Allahna ne, kuma zan bada godiya a gare ka; kai Allahna ne; zan ɗaukaka ka.
29Oh, ku bada gadiya ga Yahweh; domin shi nagari ne; domin alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.

119

ALEPH

1Masu albarka ne waɗanda hanyoyinsu basu da laifi, waɗanda ke tafiya cikin shari'ar Yahweh.2Masu albarka ne waɗanda suka kiyaye umarnansa masu tsarki masu neman sa da dukkan zuciyarsu.

3Sun yi abin da ke dai-dai; suna tafiya cikin hanyoyinsa.4Ka umarce mu mu kiyaye dokokinka, domin muyi lura mu kiyaye su,
5Kash, ina ma zan ɗore a cikin lura da farillanka!6To da ba za a kunyata ni ba a lokacin da nayi tunanin dukkan dokokinka.
7Zan yi maka godiya da zuciya mai tsarki a lokacin dana koyi sharuɗɗanka.8Zan kiyaye farillanka; kar ka barni ni kaɗai.

BETH

9Yaya matashi zai tsare tafarkinsa da tsabta? Ta wurin kiyaye maganarka.10Da dukkan zuciyata na neme ka; Kar ka barni in kauce wa umarnanka.

11Na adana maganarka a cikin zuciyata domin kada in yi maka zunubi.12Yahweh kai mai albarka ne, ka koya mani farillanka.
13Da bakina na furta dukkan ayyukanka na jinƙai da ka bayyana mani.14Ina murna da umarnanka fiye da dukkan wadata.
15Zan yi ta nazarin dokokinka in kuma saurari sharuɗɗanka.16Ina jin daɗin farillanka; ba kuma zan manta da maganarka ba.

GIMEL

17Yiwa bawanka kirki domin in rayu in kiyaye maganarka.18Buɗe idanuna domin in ga ayyukan al'ajibi a cikin shari'arka.

19Ni bãƙo ne a cikin ƙasar; kada ka ɓoye umarnanka daga gare ni.20An rushe marmarina ta wurin jimirin sanin umarnanka masu adalci a kowanne lokaci.
21Ka tsauta wa masu fahariya, waɗanda aka la'anta, Waɗanda suka bauɗe wa dokokinka.22Kãre ni daga wulaƙanci da cin mutunci, domin na kiyaye sharuɗɗan alƙawarinka.
23Koda ya ke shugabanni sun ƙudurta suka yi mani maƙarƙashiya, ni bawanka ina binbinin farillanka.24Alƙawaran farillanka sune nake jin daɗi, sune kuma ke yi mini jagora.

DALETH

25Raina yana birgima a ƙura! Ka bani rai ta wurin maganarka.26Na faɗa maka hanyoyina, ka kuma amsa mani; ka koya mani farillanka.

27Ka sani in fahimci tafarkin umarninka, domin in yi ta nazarin koyarwarka mai al'ajibi.28Baƙinciki ya cika ni! Ka ƙarfafa ni ta wurin maganarka.
29Ka jutar daga gare ni hanyar yaudara; ta wurin alheri ka koya mani shari'arka.30Na zaɓi hanyar aminci; Har kullum na kiyaye farillanka masu adalci daka sa a gabana.
31Na manne wa umarnin alƙawarinka; Yahweh kada ka bar ni in ji kunya.32Zan bi hanyoyin dokokinka da gudu, gama ka faɗaɗa zuciyata tayi haka.

HE

33Ka koya mani, Yahweh, hanyar umarnanka, kuma zan kiyaye su har ga ƙarshe.34Ka bani ganewa, kuma zan kiyaye shari'arka; Zan lura da ita da dukkan zuciyata.

35Ka bishe ni ta tafarkin dokokinka, gama ina fahariya in yi tafiya cikinta.36Ka jagoranci zuciyata ga alƙawarin umarnanka da kaucewa daga ƙazamar riba.
37Ka juya idanuwana daga duban wofintattun abubuwa; ka rayar da ni cikin hanyoyinka.38Ka cika wa bawanka alƙawarin da kayi ga waɗanda ke girmama ka.
39Ka ɗauke zage-zagen da nake tsoro, gama hukuncin adalcinka na da kyau.40Duba, na jira umarnanka; ka farkar dani cikin sanin gaskiyarka.

VAV

41Yahweh, ka ba ni madawwamiyar ƙaunarka- cetonka bisa ga alƙawarinka;42sa'an nan zan sami amsa domin duk mai yi mani ba'a, gama na amince da maganarka.

43Kada ka ɗauke maganar gaskiya daga bakina, gama Na yi jira domin umarnan sanin gaskiyarka.44Zan kiyaye dokarka babu fasawa, har abada abadin.
45Zan yi tafiya cikin kwanciyar hankali, gama ina neman ka'idodinka.46Zan yi magana a kan hakikanin umarninka a gaban sarakuna kuma ba zan ji kunya ba.
47Ina murna da dokokinka, waɗanda nake ƙauna sosai.48Zan ɗaga hannuwana ga dokokinka, waɗanda nake ƙauna; Zan yi nazari a kan farillanka.

ZAYIN

49Ka tuna da alƙawarinka zuwa ga bawanka domin ka ba ni bege.50Wannan itace ta'aziyata a cikin ƙuncina: cewa alƙawarinka ya kiyaye ni da rai.

51Mai girman kai ya yi mani gwalo, duk da haka ban juya daga dokarka ba.52Nayi tunanin umarnanka masu adalci dake tun zamanun dã, Yahweh, kuma sai na yi wa kaina ta'aziya.
53Fushi mai ƙuna ya riƙe ni sabili da mugu da ya ƙi dokarka.54Farillannka sun zama waƙoƙina a cikin gidan da nake zama na ɗan lokaci.
55Na yi tunanin sunanka a cikin dare, Yahweh, na kuma riƙe dokarka.56Wannan ya zama abin da na ke yi domin na kula da umarnanka.

HETH

57Yahweh ne rabona; nayi ƙudirin kula da maganganunka.58Nayi matuƙar neman tagomashinka da dukkan zuciyata; ka yi mani jinƙai, kamar yadda maganarka tayi alƙawari.

59Nayi la'akari da tafarkina na kuma juyar da ƙafafuna zuwa ga umarnan alƙawarinka.60Nayi sauri ban kuma ɓata lokaci ba domin in kiyaye dokokin ka.
61Igiyoyin mai mugunta suka nannaɗe ni; Ban manta da shari'arka ba.62Cikin dare na tashi domin inyi maka godiya sabili da dokokinka masu adalci.
63Ni abokin dukkan waɗanda ke girmamaka ne, da dukkan waɗanda ke kula da umarnanka.64ƙasar, Yahweh, tana cike da amintaccen alƙawarinka; ka koya mani farillanka.

TETH

65Kayi abin alheri ga bawanka, Yahweh, ta wurin maganarka.66Ka koya mani sasancewa da fahimta, gama na gaskata da dokokinka.'

67Kamin a wahalshe ni sai da na bijire, amma yanzu ina kula da maganarka.68Kana da kyau, kuma kai ne mai aikata abu mai kyau; ka koya mani farillanka.
69Mai girman kai ya rufe ni da ƙarairayi, amma na adana umarninka da dukkan zuciyata.70Zuciyarsu ta taurare, amma ina fahariya da shari'arka.
71Ya dace dani dana sha wahala domin in koyi farillanka.72Umarni daga bakinka ya fiye mani daraja fiye da dubban zinariya da azurfa.

YOD

73Hannayenka sunyi ni ka ƙera ni; ka ba ni fahimta domin in koyi dokokinka.74Waɗanda suke yi maka biyayya za suyi murna idan suka ganni saboda na sami bege cikin maganarka.

75Yahweh, Na sani, dokokinka masu adalci ne, cikin amincinka kuma ka hukunta ni.76Bari alƙawarin amincinka ya ta'azantar dani, kamar yadda ka alƙawarta wa bawanka.
77Ka nuna mani jinƙai domin in rayu, gama shari'arka ita ce jin daɗina.78Bari masu girmankai su sha kunya, gama sun ɓata sunana; amma zan yi nazarin umarnanka.
79Bari masu darjanta ka su juyo gare ni, su da suka san alƙawaran dokokinka.80Bari zuciyata ta zama da rashin laifi da darjanta farillanka domin kada in sha kunya.

KAPH

81Na suma domin sauraron cetonka! Na sa zuciya cikin maganarka.82Idanuna na jiran ganin alƙawarinka; yaushe za ka ta'azantar dani?

83Gama na zama kamar salka cikin hayaƙi; Ban manta da farillanka ba.84Har yaushe bawanka zai jiure da wannan; yaushe zaka hukunta waɗanda suke tsananta mani?
85Masu girmankai sun haƙa ramuka domina, suna rena shari'arka.86Dukkan dokokinka abin dogaro ne; waɗannan mutanen suna tsananta mani cikin kuskure; ka taimake ni.
87Saura kaɗan su kawo ƙarshena a duniya, amma ban ƙi umarnanka ba.88Ta wurin tsayayyar ƙaunarka, ka kiyaye ni a raye, domin inyi biyayya da umarnanka.

LAMEDH

89Yahweh, maganarka ta tsaya har abada; maganarka ta kahu da ƙarfi a cikin sama.90Amincinka ya dawwama ga dukkan tsararraki; ka kafa duniya, ta kuwa tsaya.

91Dukkan abubuwa sun ci gaba har yau, kamar yadda ka faɗi cikin amintattun umarnanka, gama dukkan abubuwa bayinka ne.92Da shari'arka ba jin daɗina ba ce, da na hallaka a cikin ƙuncina.
93Ba zan taɓa mantawa da umarnanka ba, gama ta wurinsu ka kiyaye ni da rai.94Ni naka ne; ka cece ni, gama na nemi umarnanka.
95Masu mugunta sunyi shirin hallakar dani, amma zan nemi in san alƙawarin umarnanka.96Naga cewa dukkan abu yana da iyakarsa, amma dokokinka suna da fãɗi, basu da iyaka.

MEM

97Oh ina ƙaunar shari'arka! ita ce abin bin-binina dukkan yini.98Dokokinka sun sani na zama da hikima fiye da maƙiyana, gama dokokinka kullum suna tare dani.

99Ina da sani fiye da dukkan malamaina, gama ina tunani akan alƙawaran umarnanka.100Ina da sani fiye da waɗanda suka girmeni; wannan ya faru domin na kiyaye umarnanka.
101Na kiyaye sawayena daga hanyar mugaye saboda in lura da maganarka.102Ban juya daga dokokin adalcinka ba, saboda kai ne ka bani umarni.
103Ya ya zaƙin maganarka ga ɗanɗanona, I, tafi zuma zaƙi a bakina!104Ta wurin umarninka na ƙaru da basira; saboda haka ina ƙin kowacce hanyar ƙarya.

NUN

105Maganarka fitila ce ga sawayena, haske ne kuma ga hanyata.106Na rantse na kuma tabbatar da ita, saboda haka zan kula da adalcin dokokinka.

107Ina shan azaba; ka bar ni a raye, Yahweh, kamar yadda ka alƙawarta a cikin maganarka.108Yahweh, idan ka yarda karɓi shaidar godiyar bakina, ka koya mani adalcin dokokinka.
109Raina kullum yana hannuna, duk da haka ban manta da shari'arka ba.110Mugaye sun ɗana tarko domina, amma ban ratse daga umarninka ba.
111Na nemi alƙawaran dokokinka a matsayin gãdona har abada, gama su ne murnar zuciyata.112Zuciyata a shirye take don biyayya da farillanka har abada, har kuma zuwa ƙarshe.

SAMEKH

113Ina ƙin waɗanda ba sa son yi maka biyayya, amma ina ƙaunar shari'arka.114Kai ne kake tsare ni da garkuwarka; ina jiran maganarka.

115Ku tafi daga gare ni, ku masu aikata mugunta, domin in kiyaye dokokin Allahna.116Ka ƙarfafa ni ta wurin maganarka saboda in rayu ba domin inji kunyar sa begena ba.
117Ka ƙarfafa ni, zan kuma tsira. Zan yi ta nazari a kan umarninka.118Ka ƙi dukkan waɗanda suka ratse daga umarninka, domin waɗancan mutanen masu yaudara ne kuma ba abin dogara ba ne.
119Ka cire dukkan mugayen duniya kamar dattin maƙera; saboda haka ina ƙaunar mahimman umarninka.120Na cika da tsoronka, kuma ina jin tsoron adalcin ka'idodinka.

AYIN

121Na yi abin da ke na gaskiya da adalci, kada ka bashe ni a wurin masu yi mani tsanani.122Ka tsare lafiyar bawanka, kada ka bari masu girman kai su wahallar da shi.

123Idanuna sun gaji sa'ad da nake jiran cetonka da maganarka mai adalci.124Ka nuna wa bawanka amincin alƙawarinka, ka koya mani farillanka.
125Ni bawanka ne, ka bani fahimta domin in sa alƙawarin farillanka.126Lokaci ya yi da Yahweh zai yi aiki, domin mutane sun karya shari'arka.
127Gaskiya ne ina ƙaunar dokokinka fiye da zinariya, fiye da zinariya mai kyau.128Saboda haka na bi umarninka a hankali, na tsani kowacce hanya ta ƙarya.

PE

129Ka'idojinka suna da ban mamaki, shi yasa nake yin biyayya dasu.130Buɗewar maganarka tana bada haske, tana bada ganewa ga wanda ba koyayye ba.

131Na buɗe bakina ina haki, saboda na ƙagara domin maganarka.132Ka juyo wajena ka yi mani jinƙai kamar yadda ka ke yiwa waɗanda ke ƙaunar sunanka.
133Ka bida ƙafafuna da maganarka, kada ka bari wani zunubi yayi mulki a kaina.134Ka fanshe ni daga hannun masu zalunci domin in lura da umarninka.
135Bari fuskarka ta haskaka a kan bawanka, ka koya mani farillanka.136Ƙoramun ruwaye suna gudu daga idanuna saboda mutane ba sa lura da shari'arka ba.

TSADHE

137Mai adalci ne kai, Yahweh, dokokinka kuma dai-dai suke.138Ka bada dokokinka na alƙawari masu adalci kuma amintattu.

139Fushi ya hallaka ni saboda maƙiyana sun manta da maganganunka.140An jaraba maganarka sau da yawa, bawanka kuma yana ƙaunar su.
141Ni ba komai bane an kuma rena ni, duk da haka ban manta da umarninka ba.142Adalcinka dai-dai ya ke har abada, shari'arka madogara ce.
143Koda ya ke wahala da azaba sun afko mani, duk da haka dokokinka suna faranta mani rai.144‌dokokinka na alƙawari masu adalci ne har abada.; ka bani fahimta domin in rayu.

QOPH

145Nayi kuka da dukkan zuciyata, "Ka amsa mani, Yahweh, zan yi biyayya da farillanka.146Na kira ka; ka cece ni, zan kuwa aikata dokokinka na alƙawari.

147Da asussuba nake tashi in yi kukan neman taimako. Na sa begena a cikin maganarka.148Na kan farka kafin masu gadin dare suyi sauyi domin in yi bin-binin maganarka.
149Ka saurari muryata a cikin alƙawarin amincinka; ka barni da rai, Yahweh, kamar yadda ka alƙawarta a cikin dokokinka na adalci.150Su waɗanda suke tsananta mani suna matsowa kusa dani, amma suna nesa da shari'arka.
151Kana kusa, Yahweh, kuma duk umarnanka amintattu ne.152Tun dã can na koya daga dokokin alƙawaranka cewa ka tsaida su har abada.

RESH

153Ka dubi ƙunci na kayi mani taimako, gama ban manta da shari'arka ba.154Ka tsaya mani ka kuma fanshe ni; ka riƙe ni, kamar yadda ka alƙawarta a maganarka.

155Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa ƙaunar farillanka.156Ayyukanka na jinƙai masu girma ne, Yahweh; ka kiyaye ni da rai, kamar yadda ka saba yi.
157Masu zaluntata da maƙiyana suna da yawa, duk da haka ban bar bin dokokinka na alƙawari ba.158Ina duban maciya amana a ƙyamace domin ba sa biyayya da maganarka.
159Dubi yadda nake ƙaunar umarninka; ka kiyaye ni da rai, Yahweh, kamar yadda ka alƙawarta ta wurin alƙawarinka mai aminci.160Cibiyar maganarka ita ce gaskiya; kowanne ɗaya daga cikin dokokinka na adalci ne sun tabbata har abada.

SHIN

161Sarakuna suna tsananta mani ba dalili; zuciya ta ta karai, gama ina jin tsoron karya maganarka.162Ina farinciki da maganarka kamar wanda ya sami ɗumbin ganima.

163Ina ƙin ƙarairayi ina kuma wofintar dasu, amma ina ƙaunar shari'arka.164Ina yabon ka sau bakwai a rana sabili da dokokinka na adalci.
165Masu ƙaunar shari'arka, suna da babbar salama; ba abin da zai sasu suyi tuntuɓe.166Ina jiran cetonka, Yahweh, ina kuma biyayya da dokokinka.
167Ina aikata dokokinka tabbatattu, ina kuma ƙaunarsu ƙwarai.168Ina biyayya da umarninka da kuma dokokinka tabbatattu, gama kana sane da duk abin da nake yi.

TAV

169Ka saurari kukana na neman taimako, Yahweh; ka bani fahimtar maganarka.170Bari roƙona ya zo gaba gare ka; ka taimake ni, kamar yadda ka alƙawarta a maganarka.

171Bari leɓunana su cika da yabo, gama kana koya mani farillanka.172Bari harshena yayi waƙa akan maganarka, gama dukkan dokokinka dai-dai suke.
173Bari hannunka ya taimake ni, gama na zaɓi umarnanka.174Ina marmarin cetonka, Yahweh, shari'arka ce farincikina.
175Ka rayar dani don in yabe ka, bari dokokinka na adalci su taimake ni.176Nayi makuwa kamar ɓatacciyar tunkiya; ka nemi bawanka, gama ban manta da dokokinka ba.

120

Waƙar takawa sama.

1A cikin ƙuncina nayi kira ga Yahweh, ya kuma amsa mani.2Ka ƙwato raina, Yahweh, daga waɗanda ke ƙarya da leɓunansu da ruɗi da harsunansu.

3Ta yaya zai hore ka, mene ne kuma zai ƙara yi maka, kai wanda ke da harshe na ƙarya?4Zai hore ka da kibiyoyin mayaƙi da aka wãsa bisa garwashin wutar ƙiraren itace.
5Kaito na saboda ina zaune jim kaɗan cikin Meshek; Dã na zauna a rumfunan Keda.6Har dogon lokaci na zauna tare da waɗanda suka ƙi salama.7Ni domin salama nake, amma idan na yi magana, domin yaƙi suke.

121

Waƙar takawa sama.

1Zan ɗaga idanu na ga duwatsu. Daga ina taimakona zai zo?2Taimakona na zuwa daga Yahweh, wanda yayi sama da duniya.

3Ba zai bar sawunka ya zãme ba; shi wanda ya ke kiyaye ka ba zai yi gyangyaɗi ba.4Duba, mai lura da Isra'ila ba zai taɓa gyangyaɗi ba ko barci.
5Yahweh shi ne mai lura da kai; Yahweh shi ne inuwa a hannun damanka.6Rana ba zata cutar da kai ba da rana, ko kuma wata da daddare.
7Yahweh zai kiyaye ka daga dukkan cutarwa, kuma zai kiyaye ranka.8Yahweh zai kiyaye ka cikin dukkan abin da kake yi yanzu da har abada abadin.

122

Waƙar takawa sama, ta Dauda.

1Nayi farinciki da suka ce mani, "Bari mu tafi gidan Yahweh."2Yerusalem, sawayenmu na tsaye cikin ƙofofinki!3Yerusalem, an gina ki birnin da aka yiwa shiri a hankali!

4Kabilun suna tafiya Yerusalem - kabilun Yahweh - a matsayin shaida ga Isra'ila, su bada godiya ga sunan Yahweh.5An kafa kursiyoyin hukuncinsu, kursiyoyin gidan Dauda.
6Kuyi addu'a domin salamar Yerusalem! "Bari masu ƙaunar ki su sami salama.7Bari salama ta kasance cikin katangogin dake kãre ki, bari kuma su sami salama cikin ƙarfafan wurin tsaronki."
8Domin albarkacin 'yan'uwana da abokaina zan ce, "Bari salama ta kasance a cikin ki."9Domin albarkacin gidan Yahweh Allahnmu, zan biɗi alheri game dake.

123

Waƙar takawa sama.

1A gare ka na ɗaga idanuna, kai wanda kake bisa kursiyi a sammai.2Duba, kamar yadda idanun bãyi ke duban hannun ubangijinsu, kamar yadda idanun baiwa ke duban hannun uwargijiyarta, haka idanunmu ke duban Yahweh Allahnmu har sai ya nuna mana jinƙai.

3Kayi mana jinƙai, Yahweh, kayi mana jinƙai, domin cike muke da wulaƙanci.4Mun ma fi cike da ba'ar masu ba'a da kuma renin masu fahariya.

124

Waƙar takawa sama, ta Dauda.

1"Idan da ba don Yahweh yana gefenmu ba," bari Isra'ila suce yanzu,2"Idan da ba don Yahweh yana gefenmu ba sa'ad da mutane suka taso gãba da mu,3daga nan da sun haɗiye mu ɗungum da rai sa'ad da fushin su ya wo hauka gãba da mu.

4Da ruwa ya share mu; igiyoyin da sun sha ƙarfinmu.5Daga nan haukan ruwayen da ya shanye mu."
6Albarka ta tabbata ga Yahweh, wanda bai bari haƙoran sa suka yayyage mu ba.7Mun kucce kamar tsuntsu daga tarkon mafarauta; tarkon ya karye, mun kuma kucce.
8Taimakonmu yana cikin Yahweh, wanda ya yi sama da ƙasa.

125

Waƙar takawa sama.

1Waɗanda suka sa dogararsu ga Yahweh suna kama da Tsaunin Sihiyona, marar jijjiguwa, mai dawwama har abada.2Kamar yadda duwatsu suka kewaye Yerusalem, haka Yahweh ya kewaye mutanensa yanzu da har abada.3Sandar mulkin mugunta ba za tayi mulki ba a ƙasar mai adalci. Idan ba haka ba mai adalci zai iya yin abin da ba dai-dai ba.

4Kayi da kyau, Yahweh, ga waɗanda suke yi da kyau waɗanda kuma suke masu adalci a zukatansu.5Amma ga waɗanda suka kauce gefe ga karkatattun hanyoyinsu, Yahweh zai kawar dasu tare da masu aikata mugunta. Bari salama ta kasance a Isra'ila.

126

Waƙar takawa sama.

1Sa'ad da Yahweh ya maido da kadarorin Sihiyona, mun zama kamar masu mafarki.

2Daga nan bakunanmu suka cika da dariya harsunanmu kuma da waƙa. Daga nan suka ce a tsakanin al'ummai, "Yahweh ya yi masu manyan abubuwa."3Yahweh ya yi mana manyan abubuwa; mun kuwa yi murna!
4Ka maido da kadarorinmu, Yahweh, kamar rafuffukan Negeb.5Su waɗanda suka yi shuka cikin hawaye zasu yi girbi tare da sowace-sowacen farinciki.6Shi wanda ya fita da kuka, yana ɗauke da irin shuka, zai sake dawowa da sowace-sowacen farinciki, yana kawo dammunansa tare da shi.

127

Waƙar takawa sama, ta Suleman.

1Sai idan Yahweh ne ya gina gida, sun yi aikin banza, su waɗanda ke ginin. Sai idan Yahweh ne yayi tsaron birni, masu tsaron suna tsayawa tsaro a banza.2Aikin banza ne a gare ka ka tashi da wuri, ka dawo gida da latti, ko ka ci gurasar aiki tuƙuru, domin Yahweh yana biyan buƙatun masu ƙaunarsa yayin da suke barci.

3Duba, 'ya'ya gãdo ne daga Yahweh, kuma ɗiyan mahaifa lada ne daga gare shi.4Kamar kibiyoyi a hannun mayaƙi, haka nan 'ya'yan ƙuruciyar mutum.5Yaya albarkar mutumin da yake da kwarinsa cike da su. Ba zai sha kunya ba sa'ad da ya fuskanci maƙiyansa a ƙofa.

128

Waƙar takawa sama.

1Mai albarka ne duk wanda ya girmama Yahweh, wanda ya ke tafiya cikin hanyoyinsa.2Abin da hannuwanka suka wadatar, zaka ji daɗin sa; zaka yi albarka da wadata.

3Matarka zata zama kamar inabi mai bada 'ya'ya a cikin gidanka; 'ya'yanka zasu zama kamar itatuwan zaitun yayin da suka zauna kewaye da teburinka.4I, tabbas, mutumin zai zama mai albarka wanda ya ke girmama Yahweh.5Bari Yahweh ya albarkace ka daga Sihiyona; bari kaga wadatar Yerusalem dukkan kwanakin rayuwarka.6Bari ka rayu ka ga 'ya'yan 'ya'yanka. Bari salama ta kasance bisa Isra'ila.

129

Waƙar takawa sama.

1"Sau da yawa tun ƙuruciya ta suke kawo mani hari," bari Isra'ila yace.2"Sau da yawa tun ƙuruciya ta suke kawo mani hari, duk da haka ba su kayar dani ba.3Masu huɗa suna huɗa bisa bayana; sunyi kuyyoyinsu da tsawo.

4Yahweh mai adalci ne; ya datse igiyoyin mai mugunta."5Bari dukkan su su sha kunya su kuma koma baya, su waɗanda suka ƙi jinin Sihiyona.
6Bari su zama kamar ciyawar dake bisa rufin gida wadda ke yaushi kafin ta girma,7wadda ba zata cika hannun mai girbi ba ko ƙirjin mai ɗaure dammuna.8Bari waɗanda ke ratsawa su wuce kada su ce, "Bari albarkar Yahweh ta kasance a kan ka; mun albarkace ka a cikin sunan Yahweh."

130

Waƙar takawa sama.

1Daga zurfafa nayi kuka gare ka, Yahweh.2Ubangiji, ka ji murya ta; bari kunnuwanka su saurari roƙe-roƙe na domin jinƙai.

3Idan kai, Yahweh, zaka kula da kurakurai, Ubangiji, wane ne zai iya tsayawa?4Amma akwai gafartawa tare da kai, saboda a girmama ka.
5Nayi jira domin ka Yahweh, raina yana jira, kuma a cikin maganarsa nake da bege.6Raina yana jira domin Ubangiji fiye da yadda masu tsaro ke jira domin safiya.
7Isra'ila, kuyi bege cikin Yahweh. Yahweh yana cike da jinƙai, kuma yana da nufin gafartawa sosai.8Shi ne wanda zai fanshi Isra'ila daga dukkan zunubansa.

131

Waƙar takawa sama; ta Dauda.

1Yahweh, zuciyata ba tayi fahariya ba ko idanuna suyi tsauri. Bani da manyan bege domin kaina ko in dami kaina da abubuwan da suka sha kaina.

2Tabbas na tsaida kuma na tausar da raina; kamar ɗan da aka yaye tare da mahaifiyarsa, raina a ciki na kamar ɗan yaye ya ke.3Isra'ila, kasa bege cikin Yahweh yanzu da har abada.

132

Waƙar takawa sama.

1Yahweh, albarkacin Dauda ka tuna da dukkan ƙuncinsa.2Ka tuna da yadda ya rantse wa Yahweh, yadda yayi wa'adi ga Mai Iko Dukka na Yakubu.

3Yace, "Ba zan shiga gidana ba ko in kwanta a kan gadona ba,4ba zan ba idanuna barci ba ko kuma in rintsa5sai na samawa Yahweh wuri, rumfar sujada domin Maɗaukaki na Yakubu."
6Duba, munji haka a Ifrata; mun same shi a jejin Yayir.7Zamu shiga rumfar sujada ta Allah; zamu yi sujada a ƙafafunsa.8Tashi, Yahweh, zuwa wurin hutawarka, kai da akwatin alƙawarinka mai nuna ƙarfinka!
9Bari firistocinka su suturta da adalci; bari amintattunka suyi ihu don murna.10Saboda bawanka Dauda, kada ka juya wa zaɓaɓɓen sarkinka baya.
11Yahweh ya rantse da tabbatacciyen wa'adi ga Dauda, tabbataccen wa'adi da ba zai janye ba: "Zan naɗa ɗaya daga cikin zuriyarka in sa shi bisa gadon sarautarka.12Idan 'ya'yanka sun yi biyayya da umarnina da kuma dokokin da zan koya masu, 'ya'yansu zasu zauna a gadon sarautarka har abada."
13Hakika Yahweh ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa.14"Nan ne wurin hutawana har abada. Zan zauna a nan, gama ina marmarinta.
15Zan albarkaceta da yalwar abin da take buƙata, zan ƙosar da matalautanta da abinci.16Zan suturta firistocinta da ceto, amintattunta zasu yi sowa da ƙarfi don murna.
17Can zan sa ƙaho ya toho domin Dauda zan kuma kafa fitila domin zaɓaɓɓena.18Zan suturta maƙiyansa da kunya, amma a kansa kambinsa zai yi walƙiya."

133

Waƙar takawa sama, ta Dauda.

1Duba, yadda ya ke da kyau da kuma daɗi idan 'yan'uwa suka zauna tare!

2Wannan yana kama da mai mai kyau a kai dake gangarowa zuwa gemu - gemun Haruna, yana kuma gangarowa har kan wuyar rigarsa.3Kamar raɓar Hermon da take fadowa bisa duwatsun Sihiyona. Gama a nan ne Yahweh ya umarta albarka - rai na har abada.

134

Waƙar takawa sama.

1Ku zo, ku albarkaci Yahweh, dukkanku bayin Yahweh, ku da kuke wa Yahweh hidima da dare a haikalinsa.2Ku ɗaga hannunwanku zuwa wuri mai tsarki ku albarkaci Yahweh.

3Bari Yahweh ya albarkace ku daga Sihiyona, Shi da yayi sama da ƙasa.

135

1Ku yabi Yahweh. Ku yabi sunan Yahweh. Ku yabe shi, ku barorin Yahweh,2ku da kuke tsayawa a cikin haikalinsa, cikin harabun gidan Allahnmu.

3Ku yabi Yahweh, gama shi nagari ne; ku raira waƙoƙin yabo ga sunansa, gama yana da ƙyau a yi haka.4Gama Yahweh ya zaɓi Yakubu domin kansa, Isra'ila abin mallakarsa.
5Na sani Yahweh mai girma ne, kuma Ubangijinmu yafi dukkan alloli.6Ko mene ne Yahweh ya ke marmari, yakan yi shi a cikin sama, da ƙasa, a cikin ruwaye da dukkan zurfafan tekuna.
7Yakan kawo gizagizai daga nesa, yakan sa walƙiya da ruwan sama su taho tare, ya kuma fito da iska daga rumbunsa.
8Ya kashe ɗan farin Masar, na mutum dana dabbobi.9Ya aika da alamu da al'ajibai a tsakiyarsu, Masar, gãba da Fir'auna da dukkan barorinsa.
10Ya hari al'ummai da yawa ya kuma kashe manyan sarkuna,11Sihon sarkin Amoriyawa da Og sakin Bashan da dukkan mulkokin Kan'ana.
12Ya ba mu ƙasarsu abin gãdo, gãdo ga Isra'ila mutanensa.13Sunanka, Yahweh, ya dawwama har abada; ka shahara, Yahweh, dawwamamme har tsararraki dukka.
14Gama Yahweh zai kare mutanensa, yana juyayin barorinsa.15Allolin al'ummai azurfa ne da zinariya, aikin hannuwan mutane.16Waɗannan allolin suna da bakuna, amma ba su yin magana; suna da idanu, amma ba sa gani;17suna da kunnuwa, amma ba sa ji, babu kuma numfashi a bakunansu.18Waɗanda suka siffanta su kamar su suke, haka kuma wanda ya dogara gare su.
19Zuriyar Isra'ila, ku albarkaci Yahweh; ku zuriyar Haruna, ku albarkaci Yahweh.20Ku zuriyar Lebi, ku albarkaci Yahweh; ku da kuke girmama Yahweh, ku albarci Yahweh.21Mai albarka ne Yahweh a cikin Sihiyona, shi wanda da ya ke zaune cikin Yerusalem. Ku yabi Yahweh.

136

1Oh, kuyi godiya ga Yahweh; gama nagari ne, gama alƙawarin amincisa ya dawwama har abada.2Oh, kuyi godiya ga Allahn alloli, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.3Oh, ku yi godiya ga Ubangiji iyayengiji, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.

4Kuyi godiya ga wanda shi ƙaɗai ya ke manyan mu'ujizai, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -5ga shi wanda ta wurin hikima yayi sammai, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.
6Ku yi godiya ga shi wanda ya shinfiɗa ƙasa da sama da ruwaye, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -7ga shi wanda yayi manyan haske, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.
8Kuyi godiya ga wanda ya bada rana yayi mulkin yini, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -9wata da taurari suyi mulki da dare, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.
10Kuyi godiya ga wanda ya karkashe 'ya'yan fari na Masar, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -11ya fitar da Isra'ila daga tsakiyarsu, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -12da ƙarfin hannunsa ba janyewa, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.
13Ku yi godiya ga wanda ya tsaga Tekun Iwa, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -14yasa Isra'ila suka wuce ta tsakiyarsa, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -15amma ya dulmayar da Fir'auna da rundunarsa cikin Tekun Iwa, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.
16Kuyi godiya ga wanda ya bida mutanensa cikin jeji, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -17ga shi wanda ya kashe manyan sarakuna, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.
18Kuyi godiya ga wanda ya kashe shahararrun sarakuna, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -19Sihon sarkin Amoriyawa, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -20da Og sarkin Bashan, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.
21Kuyi godiya ga shi wanda ya bada ƙasarsu abin gado, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -22abin gado ga Isra'ila bawansa, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -23ga wanda ya tuna damu ya kuma taimake mu cikin ƙasƙancinmu, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.
24Kuyi godiya ga shi wanda ya bamu nasara bisa maƙiyanmu, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -25ga wanda ke bada abinci ga dukkan masu rai, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.26Oh, sai ku yi godiya ga Allah na sama, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.

137

1Muka zauna a bakin kogunan Babila muka yi ta kuka da muka tuna da Sihiyona.2Muka rataye garayunmu akan itatuwa.

3A can waɗanda suka bautar damu suka roƙa muyi masu waƙoƙi, kuma waɗanda suka yi mana ba'a suka matsa mana muyi farinciki, suna cewa, "Ku raira mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona."4Ƙaƙa zamu raira waƙa kan Yahweh a baƙuwar ƙasa?
5Idan na ƙyale tunawa dake, Yerusalem, bari hannun damana ya manta da iya kaɗa garaya.6Bari harshena ya manne a rufin bakina, idan na dena tunaninki, idan ban fi son Yerusalem da abin da nafi jin daɗi ba.
7Ka tuna, Yahweh, abin da Idomawa suka yi a ranar da Yerusalem ta faɗi. Suka ce, "A ragargazata, a ragargazata har harsashenta."
8‌Ɗiyar Babila, an kusa hallaka ki - bari mutumin nan ya zama da albarka, ko ma wane ne wanda ya sãka maki domin abin da kika yi mana.9Bari mutumin nan ya sami albarka, duk wanda ya kwashe 'ya'yanki ƙanana ya fyaɗa su kan duwatsu.

138

Zabura ta Dauda.

1Zan yi maka godiya da dukkan zuciyata; a gaban alloli zan raira yabbai gare ka.2Zan rusuna ina fuskantar haikalinka mai tsarki in kuma bada godiya ga sunanka sabili da amincinka na alƙawarinka domin kuma amincewarka. Ka fifita maganarka da sunanka da muhimmanci fiye da komai.

3A ranar dana kira ka, ka amsa mani; ka ƙarfafa ni ka bani karfin zuciya.4Dukkan sarakunan duniya zasu yi maka godiya, Yahweh, gama zasu ji maganganun bakinka.
5Hakika, zasu raira waƙoƙi akan abubuwan da Yahweh yayi, gama ɗaukakar Yahweh mai girma ce.6Gama ko da ya ke Yahweh mafifici ne, duk da haka yana kula da masu kaɗaici, amma ya san masu girman kai tun daga nesa.
7Koda ya ke ina tafiya a tsakiyar hatsari, zaka tsare raina; zaka miƙa hannunka gãba da hushin maƙiyana, hannun damanka zai cece ni.8Yahweh yana tare da ni har ƙarshe; alƙawarin amincinka, Yahweh, dawwamamme ne har abada. Kada ka yasar da waɗanda hannuwanka suka yi.

139

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta Dauda.

1Yahweh, ka jaraba ni, ka kuma sanni.2Ka san lokacin da zan zauna da lokacin da zan tashi; ka san tunanina tun daga nesa.

3Kana lura da tafarkina da kwanciyata; hanyoyina sanannu ne dukka a gareka.4Gama kafin magana ta kasance a kan harshena, ka sani sarai.5Ka kewaye ni gaba da baya kuma ka ɗibiya hannunka a kaina.6Wannan sani ya fi ƙarfina ƙwarai; yayi mani zurfi, ba zan iya fahimtar sa ba.
7Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan guje wa fuskarka?8Idan na hau cikin sammai, kana can; Idan na tafi na zauna cikin Lahira, to duba, kana can.
9Idan nayi asubanci na tashi sama akan fukafukai na tafi na zauna can nesa a ƙurewar teku,10ko can ma hannunka zai bishe ni, hannun damanka zai riƙe ni.
11Idan nace, "Hakika duhu zai rufe ni, haske kuma ya zama dare kewaye dani,"12ko duhunma ba zai zama duhu a gare ka ba. Daren zai haskaka kamar rana, gama da duhu da haske duk ɗaya suke a gare ka.
13Kai ka yi gaɓaɓuwan cikin cikina; kai ka siffanta ni a cikin mahaifiyata.14Zan yabe ka, gama an yini da ƙyan gaske. Raina ya tabbatar da wannan sosai.
15‌Ƙasusuwana ba a ɓoye suke ba gare ka sa'ad da aka siffanta ni a ɓoye, sa'ad da aka hallita ni a can cikin zurfin ƙasa.16Ka ganni a cikin mahaifa; dukkan kwanakin da an ƙaddara mani suna rubuce cikin littafinka tun kafin na farkon ya faru.
17Tunaninka yana da daraja a guna, Allah! Tarinsu da yawa basu lisaftuwa.18Idan na yi ƙoƙarin ƙididdiga su, zasu fi yashi yawa. Sa'ad da na farka, ina tare da kai.
19Dãma zaka kashe mugaye, ya Allah; ku rabu dani, ku 'yan ta'adda.20Suna yi maka tawaye suna aikata munafunci, maƙiyanka suna faɗar ƙarairayi.
21Ba na ƙi waɗanda suka ƙi ka ba, Yahweh? Ba ina rena waɗanda suka tashi gãba da kai ba?22Na ƙi su fau-fau; sun zama maƙiyana.
23Ka jaraba ni, ya Allah, ka san zuciyata; ka gwada ni ka san tunanina.24Ka duba ko akwai muguwar hanya a cikina, ka kuma bishe ni a madawwamiyar hanya.

140

Domin shugaban mawaƙa. Zabura ta Dauda.

1Yahweh, ka cece ni daga mugaye; ka kiyaye ni daga mutane masu zafin rai.2Sukan shirya mugunta a zuciyarsu; sukan sa yaƙi kowacce rana.3Harsunansu suna sara kamar maciji; dafin kububuwa na leɓunansu. Selah

4Ka tsare ni daga hannuwan mugaye, Yahweh; ka tsare ni daga mutane masu zafin rai waɗanda suka shirya su kada ni ƙasa.5Masu fariya sun ɗana mani tarko; sun baza taru; sun shirya mani tarko. Selah
6Na cewa Yahweh, "Kai ne Allahna; ka kasa kunne ga koke-kokena na neman jinƙai.7Yahweh, Ubangijina, kai mai iko ne ka iya ceto na; kana kare kaina a lokacin yaƙi.8Yahweh, kada ka biya buƙatun mugaye; kada ka bari shirye-shiryensu yayi nasara. Selah
9Waɗanda suka ɗaga kansu sun kewaye ni; bari makircin leɓunansu ya rufe su.10Bari garwashin wuta su afko masu; ka jefa su cikin wuta, cikin rami marar matuƙa, kada su ƙara tashi.11Kada mutane masu mugun harshe su sami kwanciyar rai a duniya; bari bala'i ya farauci ɗan ta'adda ya buge shi ya mutu.
12Na sani Yahweh zai kyautata wa mai shan ƙunci a shari'a kuma zai yi adalci ga matalauci.13Hakika mutane masu adalci zasu bada godiya ga sunanka; mutanen dake yin gaskiya zasu kasance a gabanka.

141

Zabura ta Dauda.

1Yahweh, ina kuka gare ka; ka zo wurina da sauri. Ka saurare ni sa'ad da na kira ka.2Bari addu'ata ta zama kamar turare a gaban ka; bari tãda hannuwana sama ya zama kamar hadayar maraice.

3Yahweh, kasa mai tsaro a bakina; ka kiyaye ƙofar leɓunana,4Kada ka bari zuciyata ta yi marmarin wani mugun abu ko in haɗa kai cikin ayyukan zunubi tare da mutanen dake aikata mugunta. Kada ma in ci wani kayan lashe-lashensu.
5Bari adilin mutum ya buge ni; zai zamar mani alheri. Bari ya tsauta mani; zai zama kamar mai a kaina; bari kada in ƙi karɓar wannan. Amma addu'ata kullum gãba take da ayyukan muguntarsu.6Za a jefar da shugabanninsu daga kan duwatsu; zasu ji cewa maganganuna masu daɗi ne.7Tilas zasu ce, "Kamar yadda mutum yakan yi huɗa ya rugurguza ƙasa, haka suka warwatsar da ƙasusuwanmu a ƙofar Lahira."
8Hakika idanuna suna kanka, Yahweh, Ubangiji; a cikinka zan fake; kar ka bar raina ba tsaro.9Ka tsare ni daga tarkunan da suka ɗana mani, daga tarkunan masu mugun aiki.10Bari mugaye su faɗa cikin tarkonsu ni kuwa in kubce.

142

Salon waƙa ta Dauda, lokacin da ya ke cikin kogo; addu'a.

1Da muryata nayi kuka domin neman taimako daga Yahweh; da muryata na roƙi Yahweh tagomashi.2Na zuba masa koke-kokena a gabansa; na gaya masa wahaluna.

3Sa'ad da ruhuna ya raunana a cikina, ka san tafarkina. Sun ɗana ɓoyayyen tarko domina a hanyar da nake bi.4Na duba hannun damana sai na ga babu wanda ya kula dani. Ba mafita domina, ba wanda ya kula da rayuwata.5Na kira gare ka, Yahweh; nace, "Kai ne mafakata, rabona kuma a ƙasar rayayyu.
6Ka kasa kunne ga kirana, gama an ƙasƙantar dani; ka cece ni daga masu tsananta mani, gama sun fi ƙarfi na,7Ka fitar da raina daga kurkuku domin in yi godiya ga sunanka. Masu adalci zasu tattaru kewaye dani domin ka yi mani alheri."

143

Zabura ta Dauda.

1Ka ji addu'ata, Yahweh; ka ji roƙona. Saboda amincinka da adalcinka, ka amsa mani!2Kada ka gabatar da bawanka a gaban shari'a gama a gabanka babu mai adalci ko ɗaya.

3Maƙiyina ya hari raina; ya ture ni ƙasa; ya sãni in zauna cikin duhu kamar waɗanda suka mutu tun-tuni.4Ruhuna ya karaya a cikina; babu sauran bege a raina.
5Idan na tuna kwanakin dã; na kan yi bin-bini akan ayyukanka; ina tunani akan nasararka.6Na tada hannuwana zuwa gare ka cikin addu'a; raina yana da ƙishinka cikin ƙeƙasasshiyar ƙasa. Selah
7Ka amsa mani da wuri, Yahweh, saboda ruhuna ya some. Kada ka ɓoye mani fuskarka, domin kada in zama kamar masu gangarawa cikin rami.8Bari inji alƙawarinka na aminci da safe, gama na dogara gare ka. Ka nuna mani tafarkin da zan bi, gama nasa zuciyata a gare ka.
9Ka cece ni daga maƙiyana, Yahweh; ina gudu gare ka domin in ɓoye.10Ka koya mani in aikata nufinka, gama kai ne Allahna. Bari Ruhunka mai kyau ya bishe ni cikin ƙasar da ake adalci.
11Yahweh, sabili da sunanka, ka barni da rai; cikin adalcinka ka fitar da raina daga wahala.12Cikin alƙawarin amincinka ka datse maƙiyana kuma ka hallaka dukkan maƙiyan rayuwata, gama ni baranka ne.

144

Zabura ta Dauda.

1Mai albarka ne Yahweh, dutsena, wanda ya ke horar da hannuwana domin yaƙi da yatsuna domin faɗa.2Kai nawane mai amintaccen alƙawari da mafakata, kaine hasumiyata mai tsawo wanda ya ke ceto na, garkuwata wanda a cikinsa nake fakewa, shi ya ke sarayar da al'ummai ƙarƙashina.

3Yahweh, wane ne mutum har da kake kula shi ko ɗan mutum da kake tunani a kansa?4Mutum kamar huci ya ke; kwanakinsa kamar inuwa mai wucewa ne.
5Ka sa sararin sama ya tsage ka sabko ƙasa, Yahweh; ka taɓa duwatsu ka sa suyi hayaƙi.6Ka aika walƙiyar tsawa ka warwatsar da maƙiyana; ka harba kibanka ka kore su su sheƙa a ruɗe.
7Ka miƙo hannunka daga sama; ka cece ni daga ɗumbin ruwaye; daga hannun baƙi.8Bakunansu suna faɗar ƙarairayi, komai kuma dake hannunsu sun samu ne daga rashin gaskiya.
9Zan raira maka sabuwar waƙa, ya Allah; akan garaya mai igiya goma zan raira maka yabo,10kai wanda ke bada ceto ga sarakai, wanda ya tsirar da Dauda bawanka daga mugun takobi.11Ka cece ni ka 'yantar dani daga hannun baƙi. Bakunansu suna faɗar ƙarairayi, a hannun damansu kuma akwai rashin gaskiya.
12Bari 'ya'yanmu maza su zama kamar dashe-dashen da suka yi girma suka ƙosa a samartakarsu 'ya'yanmu mata kuma kamar sassaƙaƙƙun ginshiƙan fãda masu kyan fasali.13Bari rumbunanmu su cika da kowanne irin amfani, bari kuma tumakinmu su hayayyafa dubbai kan dubbai har sau goma a saura.
14Sa'an nan shanunmu zasu haifi 'yan maruƙa da yawa. Ba wanda zai hudo ta katangunmu; baza a tafi bautar talala ba ko a ji koke-koke a tituna.15Masu albarka ne mutanen dake da waɗannan albarku; masu farinciki ne mutanen da Allahnsu shi ne Yahweh.

145

Zabura ta yabo. Ta Dauda.

1Zan ɗaukaka ka, ya Allah, Sarki; zan albarkaci sunanka har abada abadin.2Kowace rana zan albarkace ka; zan albarkaci sunanka har abada abadin.3Yahweh Mai Girma ne, ƙasaitarsa ta cancanci yabo; Girmansa ba ya bincikuwa.

4Daga wata tsara zuwa wata tsara za a yabi ayyukanka kuma za a labarta manyan ayyukanka.5Zan yi bin-bini akan martabar ɗaukakarka da kuma ayyukanka masu ban mamaki.
6Zasu yi magana akan ikon manya-manyan ayyukanka, ni kuwa zan yi shelar girmanka.7Zasu yi shelar ayyukanka nagari masu yawa, kuma zasu raira yabo akan adalcinka.
8Yahweh mai alheri ne kuma mai jinƙai ne, mai jinkirin fushi amincinsa kuma cikin alƙawari ba iyaka.9Yahweh yana yi wa kowa kirki; jinƙansa na bisa dukkan aikin hannunsa.
10Dukkan abubuwan da kayi zasu yi maka godiya, Yahweh; amintattunka zasu sa maka albarka.11Amintattunka zasu yi magana akan darajar mulkinka, zasu faɗi ikonka.12Zasu sanar da 'yan adam ayyukan Allah masu girma da kuma ɗaukakar darajar mulkinka.
13Mulkinka, dawwamammen mulki ne, masarautarka ta dawwama har tsararraki dukka.
14Yahweh yakan tallafa wa dukkan waɗanda suke faɗuwa ya kuma tãda dukkan waɗanda ke a wulaƙance.15Idanun kowa na jiranka; ka kan basu abincinsu a madai-daicin lokaci.16Ka kan buɗe hannuwanka ka biya buƙatun kowanne abu mai rai.
17Yahweh mai adalci ne a dukkan tafarkunsa mai alheri ne a dukkan abin da ya ke yi.18Yahweh na kusa da dukkan waɗanda suke kira gareshi, ga dukkan waɗanda suke kiransa da amincewa.19Yana biyan buƙatun waɗanda suke girmama shi; yana jin kukansu sai kuma ya cece su.
20Yahweh yana lura da dukkan waɗanda ke ƙaunarsa, amma zai hallaka duk mugaye.21Bakina zai furta yabon Yahweh; bari duk 'yan adam su albarkaci sunansa mai tsarki har abada abadin.

146

1Ka yabi Yahweh, Yabi Yahweh, ya raina.2Ina ba da yabo ga Yahweh a dukkan rayuwata; Zan raira yabo ga Allahna muddin ina raye.

3Kada ka dogara ga sarakuna ko ga ɗan adam, waɗanda babu ceto gare su.4Sa'ad da ran mutum ya dena numfashi, sai ya koma turɓaya; a ranan nan shawarwarinsa zasu watse.
5Mai albarka ne wanda mataimakinsa Allahn Yakubu ne, wanda begensa na cikin Yahweh Allahnsa.6Yahweh ne yayi sama da ƙasa, da teku, da dukkan abubuwan dake cikinsu; yana kiyaye gaskiya har abada.
7Yana zartar da hukunci domin dukkan waɗanda ake zalumta kuma yana bada abinci ga mayunwata. Yahweh yakan 'yantar da ɗaurarru;8Yahweh yana ba makafi ganin gari; Yahweh yana tãda waɗanda an tanƙwaresu; Yahweh yana ƙaunar mutane masu aikata adalci.
9Yahweh yana kãre bãƙin dake cikin ƙasa; yana agajin marayu da gwauraye, amma yana tsayayya da mugaye.10Yahweh zai yi mulki har abada, Allahnki, Sihiyona, domin dukkan tsararraki. Mu yabi Yahweh.

147

1Ku yabi Yahweh gama yana da kyau a raira yabo ga Allahnmu, yana da daɗi, ya dace a yi yabo.

2Yahweh zai sake gina Yerusalem, zai sake tattaro warwatsatsun mutanen Isra'ila.3Yana warkar da masu karyayyar zuciya ya ɗaure raunukansu.
4Yana ƙididdiga taurari, ya ba dukkansu sunaye.5Mai girma ne Ubangijinmu mai daraja a iko, saninsa ya zarce gaban aunawa.
6Yahweh yana tãda waɗanda aka wulaƙantasu, yakan jawo miyagu ƙasa.7Ku raira waƙa ga Yahweh tare da godiya, mu raira yabbai ga Allahnmu da garaya.
8Yakan rufe sammai da gizagizai ya shirya ruwan sama domin ƙasa, ya sa ciyayi su tsiro bisa duwatsu.9Yana ba dabbobi abincinsu da kuma 'ya'yan hankaki lokacinda suka yi kuka.
10Ba ya jin daɗin ƙarfin doki, ba ya dogara ga ƙarfin mutum.11Yahweh yana jin daɗin waɗanda suke girmama shi, waɗanda suka kafa begensu akan amintaccen alƙawarinsa.
12Ku yabi Yahweh, Yerusalem, ki yabi Allahnki, Sihiyona.13Gama yana ƙarfafa ƙarafun ƙofofinki, yana albarkatar 'ya'yanki a cikinku.14Yana kawo wadata cikin iyakar ƙasarki, yana ƙosar dake da kyakkyawar alkama.
15Yana aika dokokinsa cikin duniya, dokokinsa yakan sheƙa da gudu.16Yakan yin ƙanƙara kamar ulu, ya baza dusarta kamar toka.
17Yakan aiko da ƙanƙara kamar 'yan gutsittsire, wa zai iya jure sanyin da ya ke aikowa?18Ya aika dokokinsa ya narkar dasu, yakan sa iska ta buga su sai ruwan ya kwarara.
19Ya yi shelar maganarsa ga Yakubu, farillansa da dokokinsa masu adalci ga Isra'ila.20Bai taɓa yin haka ba da wata al'umma, game da dokokinsa ma, basu san su ba. Mu yabi Yahweh.

148

1Ku yabi Yahweh. Ku yabi Yahweh, ku dake cikin sammai; ku yabe shi, ku dake can tuddan sama.2Ku yabe shi, dukkanku mala'ikunsa; ku yabe shi, dukkan rundunarsa.

3Ku yabe shi, rana da wata; ku yabe shi, dukkanku taurari masu ƙyalli.4Ku yabe shi, ku sammai mafi tsayi daku ruwayen dake sama da sarari.
5Bari su yabi sunan Yahweh, gama ya bada umarnj, sai aka hallicesu.6Ya kuma kafasu har abada abadin; ya zartar da doka da bazata taɓa canzawa ba.
7Ku yabe shi daga duniya, ku dodannin ruwa, da dukkan zurfafan teku,8wuta da ƙanƙara, dusar ƙanƙara da giza-gizai, iskar hadari masu biyayya da maganarsa.
9Ku yabe shi, duwatsu, da dukkan tuddai, itatuwa masu bada 'ya'ya, da duk itatuwan sida,10namun jeji da na gida, hallitu masu rarrafe da tsuntsaye.
11Ku yabi Yahweh, sarakunan duniya da dukkan al'ummai, hakimai da dukkan masu mulki a duniya,12samari da 'yan mata, dattawa da yara.
13Bari dukkansu su yabi sunan Yahweh, gama sunansa kaɗai aka fiffita, ɗaukakarsa kuma ta mamaye duniya da sammai.14Ya ɗaga ƙahon mutanensa domin yabo daga dukkan amintattunsa Isra'ilawa. Mutanen dake kurkusa da shi. Ku yabi Yahweh.

149

1Ku yabi Yahweh. Ku raira wa Yahweh sabuwar waƙa; ku raira yabonsa cikin taron amintattunsa.

2Bari Isra'ila su yi murna cikin wannan daya yi su; bari mutanen Sihiyona su yi murna da sarkin sarkinsu.3Bari su yabi sunansa suna rawa; bari su raira masa yabo da bandiri da molo.
4Gama Yahweh yana jin daɗin mutanensa; yana ɗaukaka masu tawali'u da cetonsa.5Bari masu tsoronsa su yi murna cikin nasara; bari su yi waƙa don murna bisa gadajensu.
6Bari yabon Allah ya kasance a bakinsu da takkuba masu kaifi biyu a hannunsu7domin su maida martani kan al'ummai da ayyukan hukunci akan mutane.
8Zasu ɗaure sarakunansu da sarƙoƙi shugabanninsu kuma da baƙin ƙarfe.9Zasu aiwata hukunci da aka rubuta. Wannan ne zai zama ɗaukaka domin dukkan amintattunsa. Ku yabi Yahweh.

150

1Ku yabi Yahweh. Ku yabi Allah cikin wurinsa mai tsarki; ku yabi ƙarfinsa cikin sammai.2Ku yabe shi saboda manyan ayyukansa; ku yabe shi saboda fiffikon girmansa.

3Ku yabe shi da ƙarar ƙaho; ku yabe shi da garayu da molaye.4Ku yabe shi da bandiri da rawa; ku yabe shi da garayu da sarewa.5Ku yabe shi da kuge masu ƙara; ku yabe shi da kuge masu amo.
6Bari dukkan abin dake da numfashi su yabi Yahweh. Ku yabi Yahweh.

Littafin misalai

1

1Misalai na Suleman ɗan Dauda, sarkin Isra'ila.2Waɗannan misalai zasu koyar da hikima da koyarwa, zasu koyar da maganganun fasaha,3domin ka sami koyarwa domin ka rayu ta wurin yin abin da ke dai-dai, gaskiya da adalci.

4Waɗannan misalai kuma zasu bada hikima ga marar sani, su kuma bada ilimi da fahimta ga matasa.5Bari mutane masu hikima su saurara su ƙaru a koyonsu, bari mutane masu ganewa su sami bishewa,6su kuma fahimci misalai, karin magana, da maganganun mutane masu hikima da kacici-kacicinsu.
7Tsoron Yahweh shi ne mafarin ilimi - wawaye sukan rena hikima da koyarwa.‌8Ɗana, ka kasa kunne ga koyarwar mahaifinka, kada kuma ka watsar da dokokin mahaifiyarka;9zasu zamar maka rawani cike da alheri a kanka da abubuwan ratayawa masu kyau a wuyanka.
10‌Ɗana, idan masu zunubi suka jarabce ka zuwa cikin zunubinsu, kada ka bi su.11Idan suka ce, "Ka zo tare da mu, bari mu yi fakon jinin, bari mu yi kwanto mu kai farmaƙi ga mutane marasa laifi ba tare da dalili ba.
12Bari mu haɗiye su da rai, kamar yadda Lahira take ɗauke waɗanda ke lafiyayyu, ta maishe su kamar waɗanda suka faɗa cikin rami.13Zamu sami abubuwa iri iri masu daraja; zamu cika gidajenmu da ganimar da muka sato gun waɗansu.14Ka haɗa kai da mu; zamu kasance dukka da ma'aji guda tare."
15‌Ɗana, kada ka bi wannan hanyar tare da su; kada ka yarda ƙafarka ta bi wajen da suke tafiya;16ƙafafunsu suna gudu garin yin mugunta suna hanzari su zubda jini.17Gama ba amfani a kafa wa tsuntsu tarko a idanunsa.
18Waɗannan mutane jininsu ne suke kafa wa tarko - suna kwanto ne su kama rayukansu.19Haka kuma duk hanyoyin wanda ya sami arziƙi ta rashin adalci; ƙazamar riba takan ɗauke rayukan waɗanda suka riƙe ta kam-kam.
20Hikima tana kuka da ƙarfi a tituna, tana ɗaga murya a dandali;21a karafku da ake hayaniya tana kururuwa, a ƙofofin birane tana magana,22"Har yaushe, ku mutane marasa ganewa, zaku ƙaunaci rashin ganewa? Har yaushe, ku masu ba'a, zaku ci gaba da jin daɗin ba'a, kuma har yaushe, ku wawaye zaku ƙi ilimi?
23Ku kasa kunne ga tsautawa ta; zan faɗa maku tunanina; Zan sanar maku da maganganuna.24Na yi kira, amma kuka ƙi ku saurara; na miƙa maku hannuna, amma ba wanda ya kula.25Amma duk kun yi watsi da koyarwata ba ku saurara da gyaran da na yi maku ba.
26Zan yi dariya sa'ad da masifa ta zo maku, zan yi maku ba'a sa'ad da razana ta zo -27lokacin da abin da kuke jin tsoro ya zo kamar hadari kuma bala'i ya auko kanku kamar guguwa, lokacin da azaba da damuwa suka sauko bisa kanku.
28Sa'an nan zasu kira ni, ba zan kuma amsa ba; zasu kira ni da himma, amma ba zasu same ni ba.29Domin sun ƙi ilimi, kuma ba su zaɓi tsoron Yahweh ba,30ba zasu bi koyarwata ba, kuma suka rena dukkan gyaran kuskurensu da na yi masu.
31Zasu ci 'ya'yan hanyoyinsu, da kuma 'ya'yan shirye shiryensu zasu ƙoshi.32Domin a kan kashe dolaye lokacin da suka bar tafarki, wautar wawaye ta rashin kulawa zata hallaka su.33Amma dukkan wanda ya kasa kunne gare ni zai zauna lafiya, zai huta a tsare babu tsoron masifa."

2

1‌Ɗana, idan ka karɓi zantattukana kuma ka ajiye dokokina tare da kai kamar abu mai tamani,2ka sa kunnenka ya maida hankali ga hikima kuma ka bada zuciyarka ga fahimta.

3Idan ka ƙwala kira domin fahimta ka ɗaga murya dominta,4idan ka nemeta kamar yadda zaka nemi azurfa ka kuma biɗi fahimta kamar yadda zaka biɗi ɓoyayyiyar dukiya,5sa'an nan zaka san tsoron Yahweh zaka kuma sami sanin Allah.
6domin Yahweh yana bada hikima, daga bakinsa ilimi da fahimta ke fitowa.7Yana tanada sahihiyar hikima domin waɗanda suka gamshe shi, kuma garkuwa ne ga waɗanda suke da aminci,8yana tsaron tafarkun adalci zai kuma kiyaye hanyoyin waɗanda suke bin sa da aminci.
9Sa'an nan ne zaka fahimci abin da ke da adalci, da, gaskiya, da kowanne tafarki mai kyau.10Gama hikima zata shiga cikin zuciyarka, ilimi kuma zai ji wa ranka daɗi.
11Hankali zai lura da kai, fahimta kuma zata kiyaye ka.12Zasu cece ka daga hanyar mugunta, daga kuma masu faɗar abubuwan saɓo,13waɗanda suka yi watsi da tafarkun gaskiya suna tafiya a hanyoyin duhu.
14Suna farinciki sa'ad da suke yin mugunta, suna jin daɗi cikin aikata mugunta iri-iri.15Suna bin karkatattun tafarku, suna amfani da ruɗu sun ɓoye manufarsu.
16Hikima da sanin dai-dai zasu cece ka daga mace mazinaciya, daga mace mai ƙazantar rayuwa daga maganganunta na zaƙin baki.17Takan yashe da abokinta na ƙuruciya ta manta da alƙawarin Allahnta.
18Gama gidanta na bishewa zuwa mutuwa hanyoyinta zasu bishe ka zuwa gun waɗanda ke cikin kabari.19Duk masu tafiya wurinta ba zasu sake dawowa ba kuma ba zasu sami tafarkun rai ba.
20Saboda haka zaka yi tafiya a hanyar mutanen kirki ka kuma bi tafarkun adalan mutane.21Domin adalai zasu kafa mazauni a ƙasar, amintattu kuma za a barsu a cikinta.22Amma za a datse mugaye daga ƙasar, marasa bangaskiya kuma za a datse su daga ita.

3

1‌Ɗana kada ka manta da umarnaina ka riƙe koyarwata a cikin zuciyarka,2domin za su ƙara maka tsawon kwanaki da shekarun rayuwa za su kuma ƙara maka salama.

3Kada ka bari alƙawarin aminci da dogara su taɓa barinka, ka ɗaura su tare a wuyanka, rubuta su a allon zuciyarka.4Sa'an nan zaka sami tagomashi da suna mai kyau a gaban Allah da mutum.
5Ka dogara ga Yahweh da dukkan zuciyarka kada ka jingina ga taka fahimta;6cikin dukkan hanyoyinka ka san da shi, shi kuwa zai maida tafarkunka miƙaƙƙu.
7Kada ka zama da hikima a naka idanu; ka ji tsoron Yahweh ka guji mugunta.8Za ta zamar maka warkaswa ga naman jikinka da wartsakewa ga jikinka.
9Ka girmama Yahweh da dukiyarka da nunar fari na dukkan aikinka,10sai rumbunanka su cika kuma matatsar ruwan 'ya'yan inabinka zasu yi ambaliya, su cika da ruwan inabi.
11‌Ɗana, kada ka rena koyarwar Yahweh kuma kada ka ƙi kwaɓarsa,12gama Yahweh yana horon wanda ya ke ƙauna, kamar yadda mahaifi ya ke tarbiyantar da ɗansa wanda ya ke gamsarsa.
13Mai albarka ne wanda ya sami hikima; ya kuma sami fahimta.14Ribar da ka samu daga hikima ta fi abin da azurfa zata bayar a bisani kuma ribarta tafi zinariya.
15Hikima tafi duwatsu masu ƙawa daraja kuma dukkan abin da kake marmari ba za a gwada su da ita ba a tamani.16Tana da tsawon kwanaki cikin hannun damarta a cikin hannun hagunta akwai arziki da ɗaukaka.
17Hanyoyinta hanyoyin alheri ne kuma dukkan tafarkunta na salama ne.18Itacen rai ce ga waɗanda suka kamata, waɗanda suka riƙe ta suna da farinciki.
19Ta wurin hikima Yahweh ya kafa duniya, ta wurin fahimta ya shimfiɗa sammai.20Ta wurin iliminsa zurfafa suka buɗe kuma giza-gizai suka zubo da raɓarsu.
21Ɗana, ka riƙe hukuncin gaskiya da sanin dai-dai kada ka ɗauke ido daga gare su.22Za su zama rai a rayuwarka da kayan ado na alheri da zaka rataya zagaye da wuyanka.
23Sa'an nan zaka yi tafiya a hanyarka lafiya ƙafarka ba zata yi tuntuɓe ba;24sa'ad da ka kwanta, ba zaka ji tsoro ba; lokacin da ka kwanta, zaka yi barci mai daɗi.
25Kada ka ji tsoron masifar da zata zo farat ɗaya ko hallakarwar da mugaye suka haddasa, sa'ad da ta zo,26domin Yahweh za ya kasance tare da kai ya tsare kafafunka daga faɗawa cikin tarko.
27Kada ka janye daga yin alheri ga waɗanda suka cancanta, yayin da kake da ikon aikatawa.28Kada ka cewa maƙwabcinka, "Tafi ka sake dawowa, gobe zan baka," alhali kuwa da kuɗin tare da kai.
29Kada ka shirya cutar da maƙwabcinka - wanda ya ke kusa da kai ya kuma amince da kai.30Kada ka yi jayayya da mutum ba dalili, sa'an nan bai yi komai ba don ya cuce ka.
31Kada ka ji ƙyashin ɗan ta'addar mutum ko ka zaɓi hanyoyinsa.32Domin masu aikata mugunta abin ƙyama ne ga Yahweh, amma yana karɓar mutum mai adalci ya amince da shi.
33La'anar Yahweh tana kan gidan mugun mutum, amma yana sa albarka a gidan adalan mutane.34Yakan yi wa masu ba'a ba'a, amma yakan bada jinƙansa ga mutane masu tawali'u.
35Mutane masu hikima sukan gãji girmamawa, amma za a ɗauke wawaye cikin kunyarsu.

4

1Ku kasa kunne, 'ya'ya maza, ga koyarwar mahaifinku, ku maida hankali, domin ku san ko mene ne fahimta.2Ina baku koyarwa mai kyau; kada ku yi banza da koyarwata.

3Sa'ad da nake ɗan yaron mahaifina, ina cikin ƙuruciya kuma ni kaɗai ne a gun mahaifiyata,4ya koyar da ni ya ce mani, "Bari zuciyarka ta riƙe maganganuna da kirki; ka kiyaye dokokina ka rayu.
5Ka sami hikima da fahimta; kada ka manta kuma kada kuma ka ƙi maganganun bakina;6kada ka ƙyale hikima zata tsare ka; ka ƙaunaceta zata kiyaye lafiyarka.
7Hikima ita ce mafificin abu, saboda haka ka sami hikima ka sayar da duk mallaƙarka don ka sami fahimta.8Ka ƙaunaci hikima za ta girmamaka; zata girmama ka sa'ad da ka rungume ta.9Zata ɗaura maka rawanin girmamawa a kanka; zata ba ka kambi mai kyau."
10Ka kasa kunne, ɗana, ka maida hankali ga maganganuna, zaka kuma sami shekaru da yawa a cikin rayuwarka.11Ina nuna maka hanyoyin hikima; ina bishe ka a miƙaƙƙun tafarku.12Sa'ad da kake tafiya, ba wanda zai tsaya a hanyarka in kana gudu, ba zaka yi tuntuɓe ba.
13Ka riƙe koyarwa, kada ka barta ta kubce; ka tsare ta, gama ita ce ranka.14Kada ka bi tafarkin mugaye kuma kada ka bi hanyoyin masu aikata mugunta.15Ka kauce mata, kada ka bi ta kanta; juya daga gare ta ka bi wata hanyar.
16Domin ba sa iya barci sai sun aikata mugunta kuma sukan rasa barci sai sun sa wani ya yi tuntuɓe.17Domin sukan ci abincin mugunta su sha ruwan inabin ta'addanci.
18Amma tafarkin adalan mutane kamar fitowar rana ne da ke ta ƙara haskakawa; hasken yana ta ƙara girma har tsakiyar rana ta zo.19Hanyar mugu kamar duhu take - ba su san yadda take ba suke tuntuɓe a kai.
20‌Ɗana, ka maida hankali ga maganganuna; ka bada kunnuwanka ga faɗata.21Kada ka bari su guje wa idanunka; ka ajiye su a zuciyarka.
22Gama maganata rai ne ga waɗanda suka same ta lafiya ce kuma ga dukkan jikinsu.23Ka kiyaye lafiyar zuciyarka ka tsare ta da himma, domin daga cikinta maɓuɓɓugar rai ke zubowa.
24Ka kawar da alfasha nesa daga gare ka ka kuma kawar da ruɓaɓɓar magana nesa daga gare ka.25Bari idanunka su dubi gaba sosai ka kuma kafa ƙurawarka miƙe a gaban ka.
26Ka yi wa ƙafarka tafarkin da ke dai-dai; sa'an nan ne dukkan hanyoyinka zasu zama lafiyayyu.27Kada ka juya zuwa dama ko hagu; ka juyar da ƙafafunka daga mugunta.

5

1‌Ɗana, ka maida hankali ga hikimata; ka kasa kunne ga fahimtata,2domin ka koyi sanin abin da ke dai-dai leɓunanka zasu tsare ilimi.

3Domin leɓunan mace mazinaciya suna ɗiga da zuma kuma bakinta yafi mai tabshi,4amma a ƙarshe tana da ɗaci kamar shuwaka, tana yanka kamar takobi mai kaifi.
5Kafafunta suna gangarawa zuwa mutuwa sawunta yana tafiya har Lahira.6Ba ta tunani game da hanyar rayuwa. Sawayenta sun ratse daga hanya; ba ta san inda zata ba.
7Yanzu dai, 'ya'yana maza, ku saurare ni; kada ku juya baya ga barin jin maganganun bakina.8Bari tafarkinku ya yi nesa da ita kuma kada ku je kusa da ƙofar gidanta.
9Da haka ba zaka bada girmamawarka ga waɗansu ba ko shekarun rayuwarka ga mugun mutum ba;10bãƙi ba zasu cinye dukiyarka ba; abin da ka yi wahala ka samu ba zai tafi gidan bãƙi ba.
11A ƙarshen rayuwarka zaka yi nishi sa'ad da jikinka zai lalace.12Zaka ce, "Ai kuwa na ƙi jinin umarni kuma zuciyata ta wofintar da kwaɓa!
13Na ƙi yin biyayya da malamaina na kuma ƙi in saurari umarnansu.14Na kusa lalacewa gaba ɗaya a tsakiyar taro, a cikin tattaruwar mutane."
15Ka sha ruwa a cikin randar da ke taka ka kuma sha ruwa mai gudana daga taka rijiyar.16Ko ya kamata maɓuɓɓugarka ta yi ambaliya ko'ina kuma rafuffukan ruwanka su kwarara a bainar jama'a?17Bari su zama naka kaɗai ba kuma domin bãƙin da ke tare da kai ba.
18Bari maɓuɓɓugarka ta zama da albarka kuma bari ka yi farinciki da matar kuruciyarka,19gama ita ƙaunatacciyar barewa ce kuma kurciya cike da alheri. Bari nonnanta su ƙosar da kai koyaushe; bari ka bugu da ƙaunarta kowanne lokaci.
20Don mene ne, ɗana, zaka shaƙu da mazinaciya; donme za ka rungumi nonnan karuwar mace?21Yahweh yana ganin dukkan abin da mutum ke yi yana kuma lura da dukkan tafarkun da ya ɗauka.
22Zunuban mugun mutum zasu cafke shi; igiyoyin zunubinsa zasu riƙe shi kam-kam.23Zai mutu domin ya rasa umarni; an ɓadda shi ta wurin wautarsa mai girma.

6

1‌Ɗana, idan ka ɗauki lamunin bashin da makwabcinka ya ci, idan ka yi alƙawari domin bashin wani da baka san shi ba,2to ka kafa wa kanka tarko ta wurin alƙawarin da ka yi an kuma kama ka da maganganun bakinka.

3Sa'ad da an kama ka ta wurin maganganunka, ka yi wannan ka ceci kanka, tunda ka faɗa hannun makwabcinka; ka tafi ka ƙasƙantar da kanka ka faɗi wa makwabcinka abin da ya faru.
4Kada ka ba idonka barci ko gyangyaɗi.5Ka tsirar da ranka kamar barewa daga hannun mafarauci, kamar tsuntsuwa daga hannun maharbi.
6Dubi tururuwa, kai ragon mutum, ka yi la'akari da hanyoyinta, ka yi hikima.7Ba ta da hafsa, shugaba, ko mai mulki,8duk da haka tana shirya abincinta da kaka kuma a lokacin girbi ta kan tanada abin da za ta ci.
9Har yaushe zaka yi ta barci, kai ragon mutum? Yaushe zaka tashi daga barcinka?‌10"Ɗ‌an barci kaɗan, ɗan gyangyaɗi kaɗan, ɗan naɗe hannuwa don a huta" -11sai talaucinka ya zo maka kamar ɗanfashi buƙatunka kuma kamar jarumi mai makami.
12Wofin taliki - mugun mutum - yana rayuwa ne ta wuri karkata maganarsa,13yana ƙifci da idanunsa, yana nuni da tafin ƙafarsa yana nuni da yatsunsa.
14Yana shirya mugunta da ruɗi a ransa; kullum yana haddasa rashin jituwa,15Saboda haka masifarsa zata auko masa farat ɗaya; ba zato za a karairaye shi ba damar warkewa.
16Akwai abu shida da Yahweh yaƙi, har ma bakwai da ya ke ƙyamar su.
17Idanun taliki mai girman kai, harshe mai faɗar ƙarairayi, hannaye masu zub da jinin mutane marasa laifi,18zuciya mai ƙago mugayen shirye-shirye, ƙafafu masu saurin gudu su je su yi mugunta,19mashaidi mai furta ƙarairayi yana shuka husuma a tsakanin 'yan'uwa.
20‌Ɗ‌ana, ka yi biyayya da umarnin mahaifinka kada kuma ka watsar da koyarwar mahaifiyarka.21Kullum ka ajiye su a zuciyarka; ka ɗaura su zagaye da wuyanka
22Sa'ad da kake tafiya zasu bishe ka; sa'ad da kake barci, zasu tsare ka; sa'ad da ka farka, zasu koyar da kai.23Gama umarnai fitila ce, koyarwa kuma haske ne; tsautawa da ke zuwa daga koyarwa hanyoyin rai ne.
24Zata kiyaye ka daga muguwar mace, daga lallausar maganganun muguwar mace.25Kada ka yi sha'awar kyanta a zuciyarka kuma kada ka bari ta cafke ka da girar idanunta.
26Kwana da karuwa tsadarsa kamar na kuɗin ɗan curin gurasa ne, amma matar wani zaka biya diyya da ranka.27Mutum zai iya ɗaukar wuta a ƙirjinsa har da ba zata ƙona masa kayan jikinsa ba?
28Ashe mutum zai iya tafiya bisa garwashin wuta mai zafi ba tare da ya ƙona ƙafafunsa ba?29To haka ya ke da mutumin da ya kwana da matar maƙwabcinsa; wanda ya kwana da ita ba zai kuɓuta daga hukunci ba.
30Mutane ba zasu rena ɓarawo ba idan ya yi sata domin biyan buƙatar yunwar cikinsa.31Amma idan an kama shi, zai biya riɓi bakwai na abin da ya sata; dole ya sadaukar da dukkan abubuwa masu daraja da ke cikin gidansa.
32Wanda ya yi zina ba shi da hankali; wanda ya yi ta yana hallakar da kansa.33Raunuka da kunya su ne sakaiyarsa kuma ƙasƙancinsa ba za a iya sharesu ba.
34Gama kishi yakan sa mutum ya husata; ba zai nuna jinƙai ba; sa'ad da zai ɗauki fansarsa.35Ba zai karɓi wata fansa ba, kuma ba za iya ba da toshiya ba ko da an bashi kyautai da yawa.

7

1‌Ɗana, ka adana maganganuna ka kuma ajiye dokokina a cikinka.2Ka kiyaye dokokina ka rayu ka kiyaye koyarwata kamar ƙwayar idonka.3Ka ɗaura su a yatsun hannunka; ka rubata su a allon zuciyarka.

4Ka ce da hikima, "Ke 'yar'uwata ce," kuma ka kira fahimi danginka,5domin ka kiyaye kanka daga mace mazinaciya, daga karuwar mace da maganganunta masu zaƙi.
6Ta tagar ɗakina ina leƙe ta labule.7Sai na duba wasu dolayen mutane, sai na lura cikin samari wani matashi wanda bashi da hankali.
8Saurayin ya gangara wani titi kusa da saƙonta, ya nufi wajen gidanta.9Da maraice, wajen yammaci a ranar nan, a lokacin dare da duhu.
10A can wata mata ta gamu da shi, ta yi shigar karuwa, mai zuciyar wayo.11Tana magana da ƙarfi da iskanci; ƙafafunta basu zauna a gida ba.12Yanzu tana titi, an jima tana kasuwa, a kowanne saƙo takan jira ta yi kwanto.
13Sai ta kama shi kuma ta sumbace shi, da fuska mai yaudara ta ce masa,14"Na yi baikona da salama yau, na cika wa'adina,15shi yasa na fito in sadu da kai, da himma in biɗi fuskarka, na kuma same ka.
16Na baza shimfiɗu a kan gadona, lilin masu launuka daga Masar.17Na fesawa gadona miyor da alos da kirfa.18Ka zo, mu sha ƙaunarmu mu ƙoshi har safiya; bari mu ji daɗi sosai cikin ayyukan ƙauna.
19Gama mijina ba ya cikin gidansa; ya yi tafiya mai nisa.20Ya ɗauki jakkar kuɗi tare da shi; zai dawo in wata ya raba."21Da maganganu masu yawa ta sa shi ya ratso; da daɗin bakinta tasa shi ya karkace.
22Nan da nan ya bi ta kamar san da ake kai shi wurin yanka, kamar barewar da aka kama a tarko,23har sai da kibiya ta tsire shi har zuwa hantarsa. Yana kama da tsuntsun da ya ke gaggautawa ya faɗa tarko. Bai san cewa zai sadaukar da ransa ba ne.
24Yanzu dai, ɗana, ka kasa kunne gare ni; ka maida hankali ga maganganun bakina.25Kada zuciyarka ta kauce zuwa tafarkunta; kada ka bari a ɓadda kai zuwa tafarkunta.
26Ta sa mutane da yawa sun faɗi sokakku; kasassunta da suka mutu na da yawan gaske.27Gidanta yana kan tafarkun Lahira; suna gangarawa ne zuwa ɗakunan kwanan mutuwa mai baƙin duhu.

8

1Ba hikima na ƙwala kira ba? Ba fahimta na ɗaga muryarta ba?2A kan tsaunukan dutse a gefen hanya, a mararrabar hanya, Hikima ta ɗauki matsayinta.3A gaban ƙofofi, inda ake shiga cikin birni, a ƙofofin shiga cikin birni, tana ƙwala kira.

4A gare ku, ku mutane, nake kira; muryata domin 'yan adam.5Ku marasa azanci, ku koyi hikima; ku kuma da kuke wauta, dole ku sami zuciya mai fahimta.
6Ku saurara, domin zan yi magana a kan mafifitan al'amura, kuma sa'ad da bakina ya buɗe zan faɗi madaidaitan al'amura.7Gama bakina yana faɗin gaskiya, mugunta kuma abin ƙyama ce ga leɓunana.
8Dukkan maganganun bakina na adalci ne; a cikinsu ba murɗiya ko karkatarwa.9Dukkansu miƙaƙƙu ne ga mutum mai fahimta; maganganuna dai-dai ne ga wanda ya sami ilimi.
10Ka sami koyarwata maimakon azurfa; ka sami ilimi maimakon zinariya tsantsa.11Domin hikima tafi duwatsu masu ƙawa, ba wata dukiya da ta kai ta daraja.
12Ni Hikima ina zaune da Hankali; Na kuma mallaki ilimi da sansancewa.13Tsoron Yahweh shi ne ƙin jinin mugunta. Na ƙi girman kai da alfarma, da muguwar hanya, da gamtsin baki, ina ƙinsu.
14Ina da shawara mai kyau; da sahihiyar hikima; ni mai gani ce; ƙarfi nawa ne.15Ta wuri na sarakai suke sarauta, kuma masu mulki suke tsara dokoki masu adalci.16Ta wurina mahukunta ke mulki, hakimai, da dukkan masu mulki da adalci.
17Ina ƙaunar masu ƙauna ta, kuma dukkan masu biɗata da himma, suna samu na.18A guna akwai wadata da daraja, dawwamammar dukiya da adalci.
19'Ya'yana sun fi zinariya, koma sahihiyar zinariya ce; amfanina ya fi azurfa da aka tãce.20Ina tafiya a hanyar adalci, cikin tsakiyar tafarkun adalci.21Sakamakon wannan, nakan sa masu ƙaunata su gaji wadata; nakan cika rumbunansu taf.
22"Yahweh ya hallice ni tun farko, ayyukansa na farko a lokacin.23Tun zamanun dãdã da suka wuce aka yini - daga farko, tun farkon duniya.
24Kafin tekuna su kasance, aka haife ni - kafin maɓuɓɓugai masu yawan ruwa.25Kafin kafawar duwatsu kuma kafin tuddai, aka haife ni.
26An haife ni kafin Yahweh ya hallici duniya ko jeji, kafin ma ƙura ta farko a duniya.27Ina nan sa'ad da ya kafa sammai, sa'ad da ya zana alamar zobe a sararin zurfi.
28Ina nan sa'ad da ya kafa giza-gizai a sama da sa'ad da maɓuɓɓugai cikin zurfi suka kafu.29Ina nan sa'ad da ya sa wa teku iyaka, domin kada ruwaye su yi ambaliya su ƙetare umarninsa, da sa'ad da aka dasa iyakar harsashin busasshiyar ƙasa.
30Ina gefensa, kamar gwanin masassaƙi, ni abin farincikinsa ne rana bayan rana, ina farinciki a gabansa koyaushe.31Ina ta murna da dukkan duniyarsa, kuma farincikina game da 'yan adam ne.
32Yanzu dai, 'ya'yana, ku kasa kunne gare ni, domin waɗanda suka kiyaye tafarkuna za a albarkace su.33Ku kasa kunne ga koyarwata ku zama da hikima; kada ku ƙi ta.34Wanda ya saurareni za a albarka ce shi. Zai yi ta tsaro a ƙofofina kowacce rana, yana ta jira a dogaran ƙofofina.
35Gama duk wanda ya same ni, ya sami rai, zai kuma sami tagomashin Yahweh.36Amma wanda ya kãsa, yana cutar ransa ne; dukkan masu ƙina mutawa suke ƙauna."

9

1Hikima ta gina gidanta; ta sassaƙa ginshiƙai bakwai daga duwatsu.2Ta yanka dabbobinta; ta gauraya ruwan inabinta; kuma ta shimfiɗa teburinta.

3Ta aiki barorinta; tana kira daga wurare masu tsayi na birni,4"Wane ne dolo? Bari ya ratso nan!" Tana magana da wanda ba shi da hankali.
5Kazo, ka ci abincina, kuma ka sha ruwan inabi da na gauraya.6Ka bar ayyukan dolonci ka rayu; ka bi tafarkin fahimta.
7Duk wanda ya hori mai reni za a zage shi, kuma duk wanda ya kwaɓi mugun mutum zai sami zargi.8Kada ka tsauta wa mai renako, domin zai ƙi jininka; ka tsauta wa mutum mai hikima, zai ƙaunace ka.9Ka bada hikima ga mutum mai hikima, zai ƙara hikima sosai. Ka koya wa adalin mutum, zai ƙaru cikin koyonsa.
10Tsoron Yahweh shi ne mafarin hikima, kuma sanin Mai Tsarkin nan shi ne fahimta.11Ta wurina za a tsawanta kwanakinka, shekarun rayuwa za a ƙara maka su.12Idan kana da hikima, domin kanka kake da hikimar, idan ka yi renako, zaka ɗauka kai kaɗai."
13Wawuyar mace mai jahilci ce; ba a iya koyar da ita kuma bata san komai ba.14Takan zauna a bakin ƙofarta, a wurare mafi tsayi a gari.15Tana kiran masu wucewa a tituna, ga waɗanda ke tafiya a miƙe a hanyarsu.
16"Bari wani dolo ya ratso wurin," takan cewa dolaye.17"Ruwan da aka sata ya fi daɗi, kuma abincin sirri yana da daɗi.18Amma bai sani ba matattu na wajen, cewa gayyatattunta suna cikin zurfin Lahira.

10

1Misalai na Suleman. ‌Ɗ‌a mai hikima yakan sa mahaifinsa ya yi farinciki amma wawan ɗa yana kawo wa mahaifiyarsa baƙinciki.2Dukiyar da aka tara da mugunta bata da amfani, amma aikata abu nagari zai tsare ka daga mutuwa.3Yahweh ba ya barin ran mutum mai adalci ya yunwata, amma yana kaɓar da kwaɗayin mugaye.

4Hannun da ke da ƙiyuwa sa mutum ya talauce, amma hannun ma'aikacin mutum yakan ribato arziƙi.5‌Ɗa mai hikima yakan tattara amfani da kaka, amma abin kunya ne ya yi barci da kaka.
6Alheran Allah suna kan mutum mai adalci, amma bakin mugu yana cike da ta'addanci.7Mutum mai adalci ya kan sa masu tunawa da shi su ji daɗi, amma sunayen mugaye zasu lalace.
8Mutane masu hankali suna karɓar umarni, amma wawa mai surutai zai lalace.9Mai rayuwa cikin adalci zai yi tafiya lafiya, amma wanda ya maida tafarkunsa na maguɗi, za a kama shi.
10Mai ƙibce da ido yana kawo baƙinciki, amma wawa mai surutai za a kã da shi.11Bakin mutum mai adalci maɓuɓɓugar ruwan rai ne, amma bakin mugu yana rufe da ta'addanci.
12‌̀‌Ƙiyayya tana haddasa tashin hankali, amma ƙauna tana rufe dukkan laifofi.13Hikima tana kan leɓen mutum mai basira, amma bulala domin bayan wanda ba shi da hankali ne.
14Mutane masu hikima suna tara ilimi, amma bakin wawa yana kawo hallakarwa kusa.15Wadatar mutum attajiri shi ne tsararren birninsa; talaucin matsiyaci shi ne hallakarsa.
16Ladan mutum mai adalci yana kai ga rai; ribar mugaye takan kai su ga zunubi.17Akwai tafarkin rai domin wanda ya ke bin tarbiya, amma wanda ya ƙi kwaɓa ya bijire ne.
18Kowanne ya ɓoye ƙiyayya yana da leɓunan ƙarya, wanda ya baza tsegumi wawa ne.19Sa'ad da akwai maganganu dayawa, ba a rasa zunubi, amma wanda ya ke lura da abin da ya ke faɗa mai hikima ne.
20Harshen mutum mai adalci azurfa ne tsantsa; babu wani abin amfani a zuciyar mugu.21Leɓunan mutum mai adalci sukan amfani mutane da yawa, amma wawaye sukan mutu saboda da rashin hankalinsu.
22Alheran Yahweh masu kyau sukan kawo wadata kuma ba ya sa cutarwa a ciki.23Mugunta abu ne da wawa ya ke jin daɗi yana kuma wasa da ita, amma hikima abu ne na jin daɗi ga mutum mai fahimi.
24Abin da mugu ke jin tsoro zai auka masa, amma za a biya muraɗin adilai.25Mugaye kamar hadari mai wargajewa ne, sai kawai ka ga basu kuma, amma adalai ginshiƙi ne da ya dawwama har abada.
26Kamar abu mai tsami a hakori koma kamar hayaƙi a idanu, haka ma rago ya ke ga waɗanda suka aike shi.27Tsoron Yahweh ya kan tsawonta rai, amma shekarun mugaye za a gajarta su.
28Begen mutane adilai shi ne murnarsu, amma shekarun mutane mugaye zasu gajarce.29Hanyar Yahweh ta kan tsare aminci, amma hallaka ce domin mugaye.30Ba za a taɓa kawar da mutum mai adalci ba, amma mugu ba zai zauna a ƙasar ba.
31Daga bakin adilin mutum 'ya'yan hikima suke fitowa, amma za a sare harshe mai gatse.32Leɓunan mutum mai adalci sun san karɓaɓɓiyar magana, amma bakin mugu, sun san abin cutarwa kawai.

11

1Yahweh yana ƙin ma'aunai da ba na gaskiya ba, amma yana murna da madaidaicin nauyi.2Sa'ad da girmankai yazo, daga nan ƙasƙanci ke zuwa, amma tare da tawali'u hikima ke zuwa.

3Mutanen kirki mutuncinsu ke bishe su, amma hanyoyin zamba kan hallaka maciya amana.4Dukiya ba komai ba ce a ranar hukunci, amma yin abin da ke dai-dai zai hana ka mutuwa.
5Halin kirkin amintaccen mutum kansa hanyarsa ta zama a sawwaƙe, amma mugu zai faɗi saboda muguntarsu.6Halin kirki na waɗanda suke gamsar Allah kan kiyaye su lafiya, amma marasa aminci haɗamarsu ce takan zamar masu tarko.
7Sa'ad da mugun mutum ya mutu, sa zuciyarsa takan lalace sa zuciyar kuma da ke kan ƙarfinsa takan ɓace.8Akan kiyaye adalin mutum daga wahala kuma takan aukawa mugu a maimako.
9Marar tsoron Allah da bakinsa yakan hallaka maƙwabcinsa, amma ta wurin hikima adalai sukan sami tsaro.10Sa'ad da adalan mutane suka azurta, birni yakan yi farinciki; sa'ad da mugu ya lalace, akwai sowa ta murna.11Ta wurin kyautai masu kyau na waɗanda ke farantawa Allah rai, birni yakan ƙasaita; amma ta wurin maganganun mugaye, birni yakan ɓarke ƙasa.
12Mutumin da ke rena abokinsa bashi da tunani, amma mutum mai fahimta yakan yi shiru.13Duk mai yawon yin tsegumi yakan bayyana asirai, amma amintaccen mutum yakan rufe al'amarin.
14Wurin da babu jagoranci cikin hikima al'umma takan faɗi, amma nasara takan zo ta wurin tuntuɓar mashawarta masu yawa.
15Duk wanda ya ɗaukar wa bãƙo lamuni lallai shi zai cutu, amma wanda ya ƙi bayarwa ta wurin ɗaukar alƙawari ya kuɓuta.16Mace cike da alheri takan sami girmamawa, amma azzalumai na haɗamar dukiya.
17Mutum mai taimako yakan amfanawa kansa, amma macuci kansa ya ke cuta.18Mugun mutum yakan kwanta ya sami ladansa, amma wanda ya shuka abin da ke dai-dai yakan girbi sakamakon gaskiya.
19Mutum mai gaskiya wanda ya yi abin da ke dai-dai zai rayu, amma wanda ke bin mugunta zai mutu.20Yahweh yana ƙin waɗanda tunaninsu mugaye ne, amma yana murna ga waɗanda hanyoyinsu marasa aibu ne.
21Ku tabbatar da wannan - mugun mutum ba zai tafi ba tare da hukunci ba, amma zuriyar mutane masu adalci zasu zauna lafiya.22Kome kyaun mace idan bata da tunani tana kama da zoben zinariya a hancin alade.
23Abin da adalan mutane suke so yakan jawo abu mai kyau, amma mugayen mutane zasu sa begensu ga hukunci kaɗai.24Akwai mai warwatsawa - zai samu ma da yawa; wani kuma yakan riƙe abin da zai bayar - yakan talauce.
25Mutum mai bayarwa zai azurta kuma wanda ya ke bada ruwa ga waɗansu zai sami ruwa domin kansa.26Mutane sukan la'anta mutumin da yaƙi sayar da hatsi, amma kyaututtuka masu kyau sukan zama kambi akan mutumin daya sayar da nasa.
27Mai la'akarin neman abu mai kyau yana neman tagomashi, amma mai neman mugunta zai same ta.28Masu dogara ga dukiyarsu zasu faɗi, amma kamar ganye, haka adalan mutane zasu azurta.
29Wanda ya jawo wa iyalin gidansa wahala zai gãji iska wawa kuma zai zama bawan mai hikima a zuciya.
30Adalin mutum zai zama kamar itacen rai, amma tashin hankali ya kan ɗauke rayuka.31Duba! Adalin mutum yana karɓar abin da ya dace da shi; balle ma mugu da mai zunubi!

12

1Duk mai son horo yana son ilimi, amma wanda ya ke ƙin yarda da gyara wawa ne.2Mutumin kirki yakan sami tagomashi a wurin Yahweh, amma yakan hukunta mutum mai shirya miyagun dabaru.

3Mutum ba zai kafu ta wurin mugunta ba, amma ba za a tuge adalan mutane ba.4Mace mai tsabtar rai kambi ce ga mijinta, amma ita mai kawo kunya tana kama da cuta mai ruɓar da ƙasusuwansa.
5Shirye-shiryen adali adalci ne, amma shawarar mugu yaudara ce.6Maganganun miyagun mutane su ne ayi kwanto a jira domin a sami zarafin yin kisa, amma maganganun adalai sukan cece su.
7Miyagun mutane ana kaɓantar da su kuma sun tafi, amma gidan adalin mutum zai tsaya.8Akan yabi mutum bisa ga yawan hikimar da ya ke da ita, amma za a rena wanda ya ke tunanin mugunta.
9Gara baka da wani muƙami mai muhimmanci - kawai kana matsayin bawa - da kayi fankamar kai wani ne amma baka da abinci.10Adalin mutum yakan kula da buƙatun dabbobinsa, amma ko tausayin mugu zalunci ne.
11Wanda ya yi aiki a gonarsa zai sami isasshen abinci, amma duk mai bin ayyuka marasa ma'ana ba shi da tunani.12Mugun mutum yana marmarin abin da mugayen mutane suka sato daga wurin waɗansu, amma ribar adalai sukan zo daga gare su ne.
13Maganar mugun mutum takan zamar masa tarko, amma adalin mutum yakan kuɓuta daga wahala.14Mutum zai ƙoshi da abubuwa masu kyau ta wurin amfanin maganganunsa, kamar yadda aikin hannuwansa zai sãka masa.
15Hanyar wawa a ganinsa dai-dai ce, amma mutum mai hikima yakan saurari shawara.16Wawa yakan nuna fushinsa nan da nan, amma mai yin watsi da zagi yana da hikima.
17Wanda ke faɗin gaskiya yana faɗin abin da ke dai-dai, amma mai shaidar zur na faɗin ƙarairayi.18Maganganun mai faɗin magana cikin garaje na kama da saran takobi, amma harshen mai hikima kan kawo warkarwa.
19Leɓuna masu faɗin gaskiya sukan tabbata har abada, amma harshe mai yin ƙarya na ɗan lokaci ne.20Akwai yaudara cikin zukatan masu shirin aikata mugunta, amma murna takan zo wa masu shawarar salama.
21Ba cutar da zata sami adalin mutum, amma mugayen mutane suna cike da wahaloli.22Yahweh yana ƙin leɓunan masu faɗar ƙarya, amma masu zama cikin aminci abin murnarsa ne.
23Mutum mai hikima yakan ɓoye abin da ya sani, amma zuciyar wawaye takan yi shelar wauta.24Hannun mai ƙwazo zai yi mulki, amma ragayen mutane za a sa su aikin dole.
25Damuwa cikin zuciyar mutum takan nawaita masa, amma maganganu masu kyau sukan sa shi ya yi murna.26Adalin mutum jagora ne ga abokinsa, amma hanyar miyagu takan bauɗar da su.
27Ragayen mutane ba zasu iya gasa naman farautarsu ba, amma mutum mai ƙwazo zai sami dukiya mai tamani.28Waɗanda suka yi tafiya a hanyar da ke dai-dai sukan sami rai a cikin tafarkinsa babu mutuwa.

13

1‌Ɗ‌a mai hikima yakan saurari koyarwar mahaifinsa, amma shaƙiyi ba zai saurari tsautawa ba.2Mutum zai ci moriyar abubuwa masu kyau ta wurin amfanin bakinsa, amma marmarin mayaudara ta'addanci ne.

3Mai tsaron bakinsa yana kare ransa, amma wanda ya wage bakinsa zai hallaka kansa.4Raggayen mutane na marmarin samu, amma ba sa samun komai, amma begen mutane masu ƙwazo zai sami ƙosarwa.
5Mutum mai adalci ya kan ƙi ƙarairayi, amma mugun mutum yakan maida kansa abin ƙyama, kuma yakan yi abin kunya.6Adalci yakan tsare kamilai a cikin tafarkinsu, amma mugunta ta kan juyar da waɗanda suka aikata zunubi.
7Akwai wani mai azurta kansa, amma ba shi da komai sam, kuma akwai wanda ba ya ba kansa komai, duk da haka yana da wadata da gaske.8Fãnsar ran mai arzaki dukiyarsa ce, amma matalauci baya jin razanarwa.
9Hasken adalan mutane yakan yi murna, amma fitilar miyagun mutane za a ɓice ta.10Girmankai husuma kaɗai ya ke kawowa, amma akwai hikima ga waɗanda ke karɓar shawara.
11Wadata zata ragu idan hanyar samunta ta banza ce, amma wanda ya sami kuɗi ta wurin yin aiki da hannunsa zai sa kuɗinsa su ƙaru.12Sa'ad da aka dakatar da bege, zuciya takan karaya, amma samun abin da aka sa zuciya itacen rai ne.
13Duk wanda ya rena umarni yana jawowa kansa hallaka, amma mai mutunta doka za a sãka masa.14Koyarwar mai hikima maɓulɓular rai ce, da zasu juyar da kai daga tarkunan mutuwa.
15Tunani mai kyau kan jawo tagomashi, amma hanyar mai cin amana bata da iyaka.16Mutane masu hikima sukan yi aikinsu bisa ga ilimi a cikin kowacce shawara, amma wawa yakan bayyana wawancinsa.
17Mugun ɗan saƙo yakan faɗa cikin damuwa, amma amintaccen wakili yakan kawo sasanci.18Wanda ya ƙi koyarwa zai sami talauci da kunya, amma girmamawa zata zo ga wanda ya koya ta wurin gyara.
19Samun abin da aka daɗe ana sauraro da daɗi ya ke ga rai, amma wawaye na ƙin juyawa daga mugunta.20Ka yi tafiya da masu hikima zaka zama mai hikima, amma abokin tafiyar wawaye zai hallaka
21Bala'i na bin masu zunubi, amma adalan mutane za a saka masu da abu mai kyau.22Nagarin mutum yakan bar gãdo domin 'ya'yan 'ya'yansa, amma a kan ajiye dukiyar mai zunubi domin adalin mutum.
23Gonar talaka da ba'a nomawa akwai abinci da yawa, amma rashin adalci yakan kawar da shi.24Wanda baya horon ɗansa yana ƙinsa, amma mai ƙaunar ɗansa yana kula ya hore shi.
25Adalin mutum yakan ci har sai ya ƙosadda marmarinsa, amma cikin mugu koyaushe yunwa ya ke ji.

14

1Mace mai hikima takan gina gidanta, amma wawar mace takan rushe shi da hannuwanta.2Wanda ya ke tafiya cikin gaskiya yana tsoron Yahweh, amma wanda ba shi da gaskiya yana rena shi.

3Daga bakin wawa tsiron girman kansa ke fitowa, amma leɓunan masu hikima zasu tsare su.4Wurin da babu dabbobi kwamin ciyar da dabbobi yakan zama da tsabta, amma isasshen abinci yakan zo ta wurin ƙarfin bajimi.
5Amintaccen mashaidi ba yayin ƙarya, amma mai shaidar zur ƙarairayi ya ke furtawa.6Mai ba'a yakan nemi hikima amma ba zai samu ba, amma ilimi yakan zo a sauƙaƙe ga wanda ya ke da fahimta.
7Ka guje wa wawan mutum, domin ba zaka sami ilimi daga maganganunsa ba.8Hikimar mutum mai fahimta shi ne ya gane hanyarsa, amma wautar wawaye itace yaudara.
9Wawaye sukan yi ba'a sa'ad da aka miƙa hadayar laifi, amma a kan raba tagomashi tsakanin kamilai.10Zuciya tasan ɓacin ranta bata raba murnarta da bãƙo.
11Za a hallaka gidan mugayen mutane, amma rumfar masu adalci zata yi albarka.12Akwai hanya wadda take dai-dai ga ganin mutum, amma ƙarshenta takan kai ga mutuwa kaɗai.
13Zuciya na iya dariya amma ta kuma kasance cikin damuwa murna kuma kan iya zama baƙinciki.14Marar aminci zai sami abin da ya dace da hanyoyinsa, amma nagarin mutum zai sami abin da ke nasa.
15Marar wayo yakan gaskanta kowanne abu, amma mutum mai himma yakan yi tunani game da takawarsa.16Mutum mai hikima yakan ji tsoro kuma ya rabu da mugunta, amma wawa da gangan yakan yi banza da gargaɗi.
17Mai saurin fushi yakan yi abubuwan wauta, kuma mutum mai tsara mugayen dabaru a na ƙinsa.18Marasa wayo sukan gãji wauta, amma mutane masu himma a na masu kambi da ilimi.
19Mugayen mutane zasu russuna a gaban waɗanda ke nagari masu mugunta kuma zasu russuna a ƙofofin masu adalci.20Matalauci har abokan hurɗansa ƙinsa suke, amma masu arziki suna da abokai da yawa.
21Wanda ya rena maƙwabcinsa zunubi ya ke yi, amma wanda ke taimakon matalauci mai albarka ne.22Masu shirin mugunta ba ratse hanya suke yi ba? Amma masu shirin yin alheri zasu karɓi rabon amintacciyen alƙawari da karɓuwa.
23Ta wurin aiki tuƙuru a kan sami riba, amma wurin da taɗi ne kawai, talauci yakan zo.24Rawanin masu hikima dukiyarsu ce, amma wautar wawaye takan ƙara kawo masu wawanci.
25Mashaidi mai gaskiya yakan ceci rayuka, amma mai shaidar zur yakan furta ƙarairayi.
26Sa'ad da wani yaji tsoron Yahweh, shi ma yana da gabagaɗi a cikinsa; waɗannan abubuwa zasu zama kamar wurin fakewa mai ƙarfi domin 'ya'yan wannan mutumin.27Tsoron Yahweh maɓulɓula ne na rai, domin mutum ya iya juyawa daga tarkunan mutuwa.
28‌Ɗaukakar sarki na cikin yawan mutanensa, amma rashin mutane ke hallaka yarima.29Mutum mai jinkirin fushi na da ganewa mai yawa, amma mutum mai garaje na ɗaukaka wauta.
30Natsattsiyar zuciya rai ce ga jiki, amma kishi yakan ruɓar da ƙasusuwa.31Wanda ya zalunci matalauta yana la'anta Mahaliccinsa, amma wanda ya nuna tagomashi ga mabuƙata yana girmama shi.
32Akan kãda mugun mutum ƙasa ta wurin mugayen ayyukansa, amma mai adalci na da mafaka ko a cikin mutuwa.33Hikima takan zauna cikin zuciyar mai fahimta, amma ko cikin wawaye takan bayyana kanta.
34Aikata adalci na ɗaukaka al'umma, amma zunubi abin kunya ne ga kowacce jama'a.35Tagomashin sarki na tare da baran da ke aiki da himma, amma fushinsa na kan wanda ke aikata abin kunya.

15

1Mayar da magana da taushi kan juyar da hasala, amma magana mai zafi na tada fushi.2Harshen mutane masu hikima na yabon ilimi, amma bakin wawaye yana zuba wauta.

3Idanun Yahweh suna ko'ina, suna lura da mugaye da nagari.4Harshe mai warkarwa Itacen rai ne, amma harshe mai yaudara na karya ruhu.
5Wawa yakan ƙi kulawa da umarnin mahaifinsa, amma wanda ke koya ta wurin gyara mai himma ne.6A cikin gidan adalin mutum akwai dukiya mai yawa, amma dukiyar mugun mutum na ba shi damuwa.
7Leɓunan mutane masu hikima sukan baza ilimi, amma ba haka zukatan wawaye suke ba.8Yahweh yana ƙin hadayun mugayen mutane, amma yana murna da addu'ar adalai.
9Yahweh ya ƙi hanyar mugayen mutane, amma yana ƙaunar wanda ke bin abin da ke dai-dai.10Horo mai zafi na jiran duk wanda yabar hanyar da ke dai-dai shi kuma wanda yaƙi tsautawa zai mutu.
11Lahira da hallakarwa a buɗe suke a gaban Yahweh; to balle zukatan "yan adam?12Mai ba'a baya son gyara; ba zai je wurin mai hikima ba.
13Zuciya mai murna takan sa fuska tayi murmushi, amma ciwon zuciya yakan karyar da ruhu.14Zuciya mai basira takan nemi ilimi, amma bakin wawa naci daga wawanci.
15Mutanen da ke shan tsanani suna cikin takaici dukkan kwanakin ransu, amma zuciya mai farinciki zata yi buki marar matuƙa.16Gwamma a samu kaɗan tare da tsoron Yahweh da samun dukiya da yawa cikin ruɗami.
17Cin abinci tare da 'ya'yan itatuwa a wurin da akwai ƙauna ya fi cin ɗan maraƙi mai ƙiba tare da ƙiyayya.18Mutum mai zafin rai yakan tãda husuma, amma mai jinkirin fushi na kwantar da rigima.
19Hanyar rago na kama da wurin da aka shinge ta da ƙayayuwa, amma hanyar adali lafiyayya ce.20‌Ɗa mai hikima na kawo farinciki ga mahaifinsa, amma wawa yana rena mahaifiyarsa.
21Daƙiƙai na murna da mutumin da ba shi da tunani, amma mai fahimta na tafiya a hanyar da ke dai-dai.22Wurin da babu shawara shirye-shirye kan tafi ba dai-dai ba, amma zasu yi nasara inda akwai mashawarta da yawa.
23Mutum yakan sami farinciki sa'ad da ya bada amsar da ta dace; magana a lokacin da ya dace abu mai kyau ne!24Tafarkin rai na kaiwa sama-sama ga mutane masu himma, domin su tsere daga Lahira ta ƙarƙashi.
25Yahweh yana rushe gidan mai girmankai, amma yana kiyaye dukiyar gwauruwa.26Yahweh yana ƙin tunanin mugayen mutane, amma kalmomi masu daɗi tsabtatattu ne.
27‌Ɗ‌an fashi na kawo masifa cikin iyalinsa, amma mai ƙin cin hanci zai rayu.28Zuciyar adalin mutum takan yi tunani kafin ta bada amsa, amma bakin mugayen mutane na zuba dukkan muguntarsa.
29Yahweh na nesa da mugayen mutane, amma yana jin addu'ar adalan mutane.30Fuska mai fara'a takan kawo murna ga zuciya kuma labari mai daɗi lafiya ce ga jiki.
31Idan ka maida hankali sa'ad da wani ke maka gyara yadda zaka yi rayuwa, zaka zauna cikin mutane masu hikima.32Wanda yaƙi horo rena kansa ya ke yi, amma mai sauraron gyara zai sami fahimta.
33Tsoron Yahweh na koyar da hikima kuma tawali'u kuma na zuwa kafin girmamawa.

16

1Shirye-shiryen zuciya na mutum ne, amma daga harshen Yahweh amsa ke fitowa.2Dukkan hanyoyin mutum suna da tsarki a ganinsa, amma Yahweh ke auna ruhohi.

3Ka miƙa ayyukanka ga Yahweh shirye-shiryenka kuma zasu yi nasara.4Yahweh ya yi kowanne abu da dalili, har da mugu domin ranar wahala.
5Yahweh na ƙin kowanne mutum mai zuciya mai fahariya, amma ku tabbatar da wannan, ba zasu kuɓuta daga hukunci ba.6Ɗa amintaccen alƙawari da gaskatawa akan gafarta zunubi ta wurin tsoron Yahweh mutane suke juyawa daga mugunta.
7Lokacin da hanyoyin mutum suka gamshi Yahweh, zai sa maƙiyan mutumin su zauna lafiya da shi.8Gwamma kaɗan da abin da ke na adalci, da dukiya mai yawa da ke ta rashin adalci.
9A cikin zuciya mutum ke shirya hanyarsa, amma Yahweh ke bida sawayensa.10Ƙudurori masu zurfi na a leɓunan sarki, kada bakinsa ya munafunci adalci.
11Ma'aunai na gaskiya na zuwa ne daga Yahweh; dukkan ma'aunai cikin jakka ayyukansa ne.12Sa'ad da sarakuna suka yi mugayen abubuwa, wannan abin ƙi ne, gama kursiyi na kafuwa ne ta wurin yin abin da ke dai-dai.
13Sarki na murna da leɓunan da ke faɗin abin da ke dai-dai kuma yana ƙaunar mai magana kaitsaye.14Fushin sarki saƙon mutuwa ne amma mutum mai hikima zai yi ƙoƙarin kwantar da fushinsa.
15A cikin fara'ar sarki rai ne kuma tagomashinsa na kama da hadari mai kawo ruwan sama a lokacin bazara.16Yafi kyau a sami hikima fiye da zinariya. A sami fahimta yafi neman azurfa.
17Babbar hanyar adalan mutane na kauce wa mugunta; wanda ke kãre ransa na kula da hanyarsa.18Girmankai na zuwa kafin hallaka kuma ruhun fahariya kafin fãɗuwa.
19Ya fi kyau ka zama mai tawali'u cikin matalauta da ka zama mai raba ganima tare da masu girmankai.20Duk wanda ke tunani a kan abin da aka koya masa zai sami abin da ke mai kyau, waɗanda kuma suka dogara ga Yahweh zasu yi albarka.
21Mai hikima cikin zuciya za a ce da shi mai sansancewa kuma zaƙin maganarsa na inganta iya koyarwa.22Fahimta maɓuɓɓugar rai ce ga wanda ya ke da ita, amma umarnin wawaye wawancinsu ne.
23Zuciyar mutum mai hikima na bada basira ga bakinsa ta kuma ƙara ikon rinjaya ga leɓunansa.24Kalmomi masu daɗi saƙar zuma ce - abin daɗi ga rai warkarwar kuma ga ƙasusuwa.
25Akwai hanyar da ke dai-dai ga mutum, amma ƙarshenta hanyar zuwa ga mutuwa ce.26Marmarin ma'aikaci na yi masa aiki; yunwarsa na tura shi gaba.
27Mutum marar amfani na haƙo da damuwa maganarsa kuma na kama da wuta mai ƙuna.28Mugun mutum na tãda tashin hankali magulmaci kuma na raba abokanai na kurkusa.
29Mutum mai ta'addanci na yin ƙarya ga maƙwabcinsa ya kuma gangara dashi ga tafarki da ba dai-dai ba.30Mutum mai kaɗa ido abubuwan mugunta ya ke ƙullawa; waɗanda ke tsayar da leɓuna zasu kawo mugunta.
31Furfura kambin daraja ce; a na samunta ne ta yin rayuwar data dace.32Ya fi kyau ka zama mai jinkirin fushi da ka zama jarumi kuma wanda ke mulkin ruhunsa ya fi wanda ke mamaye birni.
33Akan jefa ƙuri'a a cikin cinya, amma yanke shawara daga wurin Yahweh ne.

17

1Ya fi a ci busasshiyar gurasa rai kwance da gida cike da shagali tare da tashin hankali.2Bawa mai hikima zai yi mulki bisa ɗan da ke aikata abin kunya zai kuma sami rabon gãdo kamar ɗaya daga cikin 'yan'uwa.

3Maƙera da tanderun wuta domin tãce azurfa da zinariya ne; amma Yahweh ke tace zukata.4Mai aikata mugunta na kasa kunne ga mugayen leɓuna; maƙaryaci na sauraren harshe mai hallakarwa.
5Duk wanda ya yi wa matalauci ba'a Mahallicinsa ya ke zagi kuma wanda ke farinciki da hasara ba zai tsira ba tare da hukunci ba.6Jikoki kambin tsofaffi ne iyaye kuma suna kawo daraja ga 'ya'yansu.
7Yin magana da ƙwarewa bata da daɗi ga wawa; balle leɓuna masu faɗin ƙarya ba dai-dai bane da masu mulki.8Cin hanci na kama da dutsen dabo ga wanda ya bada shi; duk inda ya juya, nasara ya ke yi.
9Duk wanda ke yafe laifi yana neman ƙauna, amma wanda ke maimaita batu yana raba abokai na kurkusa.10Tsautawa kan shiga da zurfi cikin mutumin da ke da fahimta fiye da naushe-naushe ɗari ga jikin wawa.
11Mugun mutum tawaye kaɗai ya ke nema, don haka za a aika masa da mugun manzo ya yi gãba da shi.12Ya fi kyau ka gamu da kerkeci wadda aka kwashe mata 'ya'yanta da ka gamu da wawa cikin wawancinsa.
13Idan wani ya maida mugunta maimakon alheri, mugunta ba zata taɓa rabuwa da gidansa ba.14Mafarin jayayya na kama da wanda ya saki ruwa ko'ina, don haka ka kaucewa jayayya kafin ta ɓarke ko'ina.
15Mutumin da ya baratar da mugun mutum da mutumin da ya kãda adalin mutum - dukkansu abin ƙi ne ga Yahweh.16Donme wawa zai biya kuɗi ya koyi hikima, ganin cewa ba shi da iyawar koyon ta?
17A koyaushe aboki yana nuna ƙaunarsa ɗan'uwa kuma an haife shi ne domin kwanakin damuwa.18Sai mutum marar hankali ke ɗaukar zaunannun alƙawarai domin basusuwan maƙwabcinsa.
19Duk wanda ke ƙaunar rikici yana ƙaunar zunubi; wanda ya sa bakin ƙofarsa tayi yawan tsayi zai haifar da karyewar ƙashi.20Mutumin da ke da gurɓatacciyar zuciya ba ya ganin abin da ke dai-dai; wanda ke da mugun harshe na faɗawa cikin bala'i.
21Mahaifin da ɗansa wawa ne yakan jawowa kansa ɓacin rai; mahaifin wawa kuma ba shi da farinciki.22Zuciya mai farinciki magani ne mai kyau, amma karyayyen ruhu kan busar da ƙasusuwa.
23Mugun mutum yakan karɓi cin hanci a ɓoye domin ya karkatar da hanyoyin adalci.24Mai fahimta yakan sa fuskarsa wajen hikima, amma idanun wawa a kafe suke har ga ƙarshen duniya.
25Wawan ɗa abin baƙinciki ne ga mahaifinsa abin haushi ne kuma ga matar da ta haife shi.26Haka kuma, ba dai-dai ba ne a hukunta mutum mai adalci; kuma ba shi da kyau a bulali mutane masu daraja masu mutunci.
27Wanda ke da ilimi yakan yi amfani da kalmomi kaɗan wanda kuma ke da fahimta yana da natsuwa.28Har wawa idan ya yi shiru za a zaci shi mai hikima ne; sa'ad da bai yi magana ba, ana masa kallon mai basira.

18

1Wanda ya ware kansa muradin kansa ya ke nema yana kuma jayayya da dukkan hukunci mai kyau.2Wawa bai da mu da ya fahimta ba, amma ya da mu kaɗai ya bayyana abin da ke cikin zuciyarsa.

3Sa'ad da mugun mutum yazo, reni yakan zo tare da shi - tare da kunya da ƙasƙanci.4Maganganun bakin mutum ruwaye ne masu zurfi; maɓulɓular hikima rafi ne mai gudãna.
5Ba dai-dai ba ne a nuna son kai ga mugun mutum, ko a hana adalci ga mutum mai adalci.6Maganar wawa takan jawo masa tsatsaguwa bakinsa kuma na gayyatar dũka.
7Bakin wawa ke lalatar da shi da leɓunansa kuma ya ke ɗana wa kansa tarko.8Maganganun magulmaci na kãma da loma mai daɗi sukan kuma gangara zuwa can cikin ciki.
9Haka kuma, wanda ya yi sanyi cikin aikinsa ɗan'uwa ne da wanda ke lalatarwa sosai.10Sunan Yahweh ƙaƙƙarfar hasumiya ne; adalan mutum yakan ruga cikinsa ya kuma tsira.
11Attajiri na zaton dukiyarsa ce zata kare shi kamar garu mai tsayi da ke kewaye da birni.12Kafin faɗuwarsa zuciyar mutum takan kumbura, amma tawali'u yakan zo kafin girmamawa.
13Wanda ya amsa kafin ya saurara - wauta ce a gare shi da kunya.14Ruhun mutum zai jure rashin lafiya, amma wa zai daure da karyayyen ruhu?
15Zuciyar mai ƙwazo takan sami ilimi kunnen mai hikima yana biɗarsa.16Kyautar mutum zata bude masa hanya ta kuma kai shi gaban mutum mai muhimmanci.
17Wanda ya fara gabatar da damuwarsa za a ga shi ne da gaskiya har sai abokin ƙara ya zo ya ƙalubalance shi.18Jefa ƙuri'a takan dai-daita jayayya ta raba tsakanin masu iko da ke jayayya.
19Ɗan'uwan da aka ɓata da shi ya fi birni mai ƙarfi wuyar shiryawa, tantankawa kuma na kama da makaran kagara.20Cikin mutum zai ƙoshi da amfanin bakinsa; zai gamsu da amfanin leɓunansa.
21Mutuwa da rai harshe ne ke sarrafasu, waɗanda ke ƙaunar harshe zasu ci amfaninsa.22Wanda ya sami mata abin kirki ya samu yana kuwa samun tagomashi daga wurin Yahweh.
23Fakirin mutum yakan roƙi jinƙai, amma mawadaci na amsa magana da kaushi.24Wanda ke taƙamar yana da abokai da yawa, sukan yashe shi ta wurinsu, amma akwai abokin da ke zuwa kusa fiye da ɗan'uwa.

19

1Gara matalaucin mutum mai tafiya cikin mutuncinsa da mai maganar mugunta gashi kuwa wawa.2Kuma, ba shi da kyau a kasance da marmari ba tare da sani ba kuma wanda ke gudu da sauri yakan ɓata hanya.

3Wautar mutum takan ɓata ransa zuciyarsa kuma tana fushi gãba da Yahweh.4Arziki na ƙara abokai da yawa, amma matalauci a ware ya ke da abokansa.
5Mai shaidar zur ba zai tserewa hukunci ba mai furta ƙarairayi ba zai kuɓuta ba.6Mutane da yawa zasu roƙi tagomashi daga wurin mutum mai kyauta kuma kowanne mutum aboki ne ga mai bada kyautai.
7Dukkan 'yan'uwan matalauci na ƙinsa; balle ma abokansa waɗanda suka yi nisa da shi! Ya kira su, amma sun tafi.8Wanda ya sami hikima yana ƙaunar ransa; wanda ya kiyaye fahimta zai sami abin da ya ke da kyau.
9Mai shaidar zur ba zai tsere wa hukunci ba, amma mai furta ƙarairayi zai hallaka.10Bai dace da wawa ya zauna cikin daula ba - balle bawa ya yi mulki bisa 'ya'yan sarakuna.
11Mutum mai sanin ya kamata yakan yi jinkirin fushi kuma daraja ce a gare shi ya ƙyale laifi.12Hasalar sarki na kama da rurin ɗan zaki, amma alherinsa na kama da raɓa a bisan ciyawa.
13Wawan ɗa masifa ce ga mahaifinsa mace mai tankiya ɗiɗɗigar ruwa ne koyaushe.14Gida da dukiya ana gãdonsu daga iyaye, amma mace mai hankali daga wurin Yahweh take.
15Ragonci kan jefa mutum cikin barci mai zurfi, amma wanda bai son aiki zai sha yunwa.16Wanda ya kiyaye doka ransa ya ke kiyayewa, amma mutumin da baya tunani game da al'amuransa zai mutu.
17Duk mai jin tausayin fakirai yana bada rance ga Yahweh kuma zai sãke biyansa da abin da ya yi.18Ka hori ɗanka tun da sauran bege kuma kada ka ƙallafa ranka ga kashe shi.
19Mutum mai zafin rai za ya ɗauki alhaki; idan ka cece shi, sai ka sake yi karo na biyu.20Ka saurari shawara ka karɓi koyarwa, domin ka iya zama mai hikima a ƙarshen rayuwarka.
21Shirye-shirye masu yawa ke a cikin zuciyar mutum, amma manufar Yahweh ce zata tabbata.22Biyayya ce ya kamata mutum ya yi marmari kuma gara matalauci da maƙaryaci.
23Girmama Yahweh yakan jagoranci mutane ga rai; wanda ke da shi zai gamsu ba abin da zai cutar da shi.24Rago yakan tsoma hannunsa cikin kwano; ba zai ko iya dawo da shi bakinsa ba.
25Ka bugi mai ba'a, mutum marar wayau zai zama mai tattali; ka hori mai fahimta, zai kuma ƙaru da ilimi.
26Wanda ya yi wa mahaifinsa fashi ya kuma kori mahaifiyarsa ɗa ne mai kawo kunya da zargi.27Idan ka daina jin koyarwa, ɗana, zaka ratse daga zantattukan ilimi.
28Gurɓataccen mashaidi ya kan yi wa adalci ba'a bakin mugu yakan haɗiye laifi.29A kan shirya hallakarwa domin masu ba'a bulala kuma domin bayan wawaye.

20

1Ruwan inabi mai ba'a ne barasa kuma mai tankiya ce; duk wanda ya kauce ta wurin sha marar hikima ne.2Tsoron sarki kamar tsoron ɗan zaki ne mai ruri; wanda yasa shi ya yi fushi zai rasa ransa.

3Abin darajantawane ga kowanne mutum da ya kauce wa husuma, amma kowanne wawa yakan yi tsalle cikin jayayya.4Ragon mutum baya huɗa lokacin bazara; yakan nemi hatsi a lokacin girbi amma ba zai sami komai ba.
5Shawara cikin zuciyar mutum tana kama da ruwa mai zurfi, amma mutum mai fahimta zai jawo ta waje.6Mutane da yawa suna shelar nasu alheri, amma mutum mai aminci wa ya iya samunsa?
7Mutum mai aminci wanda ke tafiya cikin mutuncinsa, 'ya'yansa da suka bishi zasu zama masu albarka.8Sarkin da ya zauna a kan dakalin shari'a ya ke aikin alƙali da idanunsa ya ke sheƙar da dukkan muguntar da ke gabansa.
9Wane ne zai ce, "Na tsabtace zuciyata; Ni tsarkakakke ne daga zunubina"?10Ma'auni daban-daban da mudun da ba dai-dai ba - Yahweh yaƙi su dukka.
11Ko matashi a kan sanshi ta wurin ayyukansa, ko aikinsa mai tsabta ne ko dai-dai kuma.12Kunne mai ji da ido mai gani - Yahweh ne ya yi su dukka biyun.
13Kada kaso barci domin kada ka talauce; ka buɗe idanunka da haka zaka sami isasshen abinci ka ci.14"Ba kyau! Ba kyau!" inji mai saye, amma sa'ad da ya tafi sai fahariya ya ke yi.
15Akwai zinariya da duwatsu masu tsada, amma leɓuna masu sani duwatsu ne masu tamani.16Wanda ya tsayawa bãƙo ka karɓi rigarsa, ka karɓi jingina kuma daga hannun wanda ya tsayawa mace marar kintsuwa.
17Gurasar da aka samu ta wurin yaudarar ɗanɗano mai daɗi ce, amma daga baya bakinsa zai cika da tsakuwa.18Shirye-shirye sukan kahu ta wurin shawara da jagorancin mai hikima kaɗai zaka yi yaƙi.
19Mai tsegumi yakan bayyana asirai domin haka kada kayi hurɗa tare da mutane masu yawan magana.20Idan mutum ya la'anta mahaifinsa ko mahaifiyarsa, za a ɓice fitilarsa a cikin tsakiyar duhu.
21Gãdon da aka samu cikin gaggawa da farko amma a ƙarshe ba zai zama da kyau ba.22Kada ka ce, "Zan rama wannan muguntar!" Ka jira Yahweh zai kuɓutar da kai.
23Yahweh yana ƙin ma'aunin algus mizanan rashin gaskiya basu da kyau.24Al'amuran mutum Yahweh ke shugabantarsu; ta yaya zai fahimci tafarkinsa?
25Tarko ne ga mutum ya yi magana cikin sauri, "Wannan abu mai tsarki," daga nan ya fara tunanin ma'anar bayan ya yi wa'adinsa.26Sarki mai hikima yakan sheƙe miyagu ya juyar da turmin chasa a kansu.
27Ruhun mutum fitilar Yahweh ce, tana bincike dukkan sassan ciki.28Alƙawarin aminci da gaskiya suna tsare sarki; kursiyinsa an kintsa shi da ƙauna.
29‌Ɗ‌aukakar samari ƙarfinsu ne darajar tsofaffin mutane kuma furfurarsu ce.30Buge buge waɗanda ke sa rauni sukan tsarkake mugunta dũka kuma yakan sa sassan cikin jiki su tsarkaka.

21

1Zuciyar sarki kamar tafki ce mai gudanowa a cikin hannun Yahweh kuma yana juya shi a duk inda ya ga dama.2Kowanne mutum na ganin hanyarsa dai-dai ne a idanunsa, amma Yahweh ke auna zukata.

3Aikata abin da ke dai-dai da gaskiya abin karɓa ne ga Yahweh fiye da hadaya;4Idanun masu fahariya da zuciya mai girman kai - fitilar mugaye - zunubi ne.
5Shirye-shiryen mai himma na kai wa ne kaɗai ga wadata, amma duk mai yawan sauri zai kai ga talauci.6Tãra dukiya da harshe na ƙarya kamar tururi ne mai wucewa kuma tarko ne mai kashewa.
7Ta'addancin masu mugunta zai kwashe su ya tafi, domin sun ƙi aikata abin da ke dai-dai.8Hanyar marar gaskiya karkatacciya ce, amma mai gaskiya na aikata abin da ke dai-dai.
9Ya fiye a zauna laɓe a lungun ɗaki da a zauna ɗaki ɗaya da mace mai yawan faɗace-faɗace.10Ƙishin mugu na marmarin aikata mugunta; maƙwabtansa baya samun tagomashi a idanunsa.
11Lokacin da aka yiwa mai ba'a horo, marar wayau na samun hikima, kuma idan aka bai wa hikima umarni, yana tara ilimi.12Mutum mai adalci na lura da gidan mutum mai mugunta; yana kawo masu mugunta zuwa ga bala'i.
13Duk wanda ya hana wa kunnensa jin kukan matalauta, haka zai yi kuka, amma ba za a amsa masa ba.14Kyauta a ɓoye na kwantar da fushi kuma asirtacciyar kyauta na kauda hasala mai girma.
15Lokacin da aka shar'anta gaskiya, tana kawo farincikin ga mutum mai adalci, amma tana kawo fargaba ga masu aikata mugunta.16Wanda ya kauce daga hanyar fahimta, za shi zauna a cikin taron matattu.
17Duk wanda ke ƙaunar annashuwa za shi talauce; wanda ke ƙaunar ruwan inabi da mai ba zai wadata ba.18Mugun mutum abin fansa ne domin mai adalci, maci amana kuma abin fansa ne domin nagargarun mutane.
19Ya fiye a zauna cikin hamada da a zauna tare da mata mai yawan faɗace-faɗace da fushi.20Zaɓaɓɓun dukiya da mai an ajiye su a mazaunin masu hikima, amma mutum marar wayo yana haɗiye su dukka.
21Wanda ke aikata adalci yana kuma kyautatawa - wannan mutum ya sami rai, da adalci, da kuma ɗaukaka.22Mutum mai hikima na tsallake birnin masu iko, kuma yana rusar da ƙaƙƙarfan wurin da suka dogara da shi.
23Duk wanda ya kiyaye bakinsa da harshensa yana tsare kansa ne daga wahala.24Mai girman kai da mutum mai fahariya - "Mai ba'a" ne sunansa - yana ayyukansa da girmankai na kumburi.
25Sha'awar rago tana kashe shi, gama hannunsa na ƙin yin aiki.26Dukkan yini yana marmari yana ƙara marmari, amma mutum mai adalci yana bayarwa kuma baya hanawa.
27Hadayar mugaye ƙazanta ce; ƙazantar na yawaita idan ya kawo su da miyagun manufofi.28Mai shaidar ƙarya zai hallaka, amma wanda ya yi sauraro za ya yi magana a dukkan lokaci.
29Mugun mutum na mai da fuskarsa da tauri, amma mai adalci na dai-daita tafarkunsa.
30Babu hikima, babu fahimta, kuma babu shawara da ke iya gãba da Yahweh.31Ana shirya doki domin ranar yaƙi, amma nasara ta Yahweh ce.

22

1Zaɓen suna mai kyau ya fi wadata mai yawa kuma tagomashi ya fi azurfa da zinariya.2Wannan na faruwa da masu arziƙi da matalauta - Yahweh ne mahallicinsu dukka.

3Mutum mai ƙwazo na hangen wahala ya kuma ɓoye kansa, amma marasa cikakkiyar kula na wucewa har ga wahala.4Ladan tawali'u da tsoron Yahweh arziƙi ne, da ɗaukaka, da kuma rai.
5Ƙayayuwa da tarkuna suna kan hanyar bijirarru; duk wanda ya kiyaye ransa zai yi nisa da su.6Ka koya wa yaro hanyar da zai bi kuma idan ya manyanta ba zai kauce daga wannan umarnin ba.
7Masu arziki ne ke mulkin matalauta kuma mai cin bashi bawa ne ga mai bada bashi.8Shi wanda ya shuka rashin adalci za shi girbi masifa kuma sandar hasalarsa zata ƙare.
9Shi wanda ke da ido na hannu sake za shi yi albarka, gama yana raba gurasarsa da talakawa.10Ka kori mai ba'a, husuma zata fita; faɗace-faɗace da zage-zage zasu ƙare.
11Shi wanda ke ƙaunar tsabtacciyar zuciya wanda kuma kalamansa masu alheri ne, za shi zama abokin sarki.12Idanun Yahweh na bisa ilimi, amma yana rusar da maganganun maci amana.
13Ragon mutum ya ce, "Akwai zaki a kan hanya! Za a kashe ni a buɗaɗɗun filaye."14Bakin karuwa rami ne mai zurfi; Fushin Yahweh na gãba da duk wanda ya faɗi cikinta.
15Ana samun wawanci a zuciyar ɗan yaro, amma sandar horo na korarsa da nisa.16Wanda ke zaluntar matalauta don ya tara dukiyarsa, ko ya baiwa mutane masu arziki, zai talauce.
17Ka kusanto da kunnuwanka ga maganganun masu hikima ka kuma miƙa zuciyarka ga ilimina,18gama zata zamar maka abin daɗi, idan ka adana su cikinka, idan dukkansu suna shirye cikin leɓunanka.19Domin dogararka ta kasance cikin Yahweh, na koyar da su gare ka yau - lallai a gare ka.
20Bana rubuta maka talatin maganganun na umarni da ilimi bane,21domin na koyar da kai waɗannan amintattun maganganu, dominn ka bayar da amintattun amsoshi ga waɗanda suka aike ka ba?
22Kada ka cuci matalauci wai don shi matalauci ne, ko ka murƙushe mabuƙaci a bakin ƙofa,23gama Yahweh zai yi magana a madadin su, kuma zai ƙwace ran wadda ya cuce su.
24Kada ka yi abokantaka da wanda fushi ke mulkinsa kuma kada ka yi tafiya da wanda ke hucin fushi,25in ba haka ba zaka koyi halayensa da haka zaka ɗana wa ranka tarko.
26Kada ka zama wanda ke buga hannu don ɗaukar alƙawari, ko mai tsayawa a madadi na basussuka.27Idan ka rasa hanyar biya, me zai hana wani ya ɗauke gadonka daga gare ka?
28Kada ka matsar da dutsen iyaka na dã wanda ubanninka suka sa.29Ko ka ga mutum ƙwararre ga aikinsa? Zai tsaya a gaban sarakuna; ba zai tsaya a gaban mutane marasa daraja ba.

23

1A lokacin da ka zauna cin abinci da mai mulki, ka kula da kyau abin da a ka ajiye a gaban ka,2ka kuma sa wuƙa a maƙogwaronka idan fa kai wani ne mai yawan son cin abinci mai yawa.3Kada ka yi marmarin kayan kwaɗayinsa, gama abincin ƙarya ne.

4Kada ka wahalar da kanka garin neman arziki; ka sami hikimar sanin lokacin da ya kamata ka huta.5Ko zaka bar idanuwanka bisa arziki? Zai watse, gama lallai za shi ɗauki fuka-fukai kamar gaggafa ya tashi sama.
6Kada ka ci abincin wanda ke da mugun ido - kuma kada ka yi marmarin kayan kwaɗayinsa,7gama shi irin mutum ne da ke ƙirgen farashin abincin. "Ka ci ka sha!" yana ce maka, amma zuciyarsa bata tare da kai.8Za ka yi aman abin da ka ci kuma kalaman abokancin ka su tafi a banza.
9Kada ka yi magana a gaban wawa, gama zai rena hikimar maganganunka.10Kada ka matsar da daɗaɗɗen dutsen iyaka ko ka shige gonar marayu,11gama mai Fansarsu na da ƙarfi kuma zai yi magana a madadin su gãba da kai.
12Ka kafa zuciyar ka ga umarni kuma kunnuwanka ga maganganu na ilimi.
13Kada ka ƙi yiwa yaro umarni, gama idan ka yi masa horo, ba zai mutu ba.14Kai ne ya zama dole ka doke shi da sanda ka kuma ceci ransa daga Lahira.
15Ya ɗa na, idan zuciyarka na da hikima, da haka kuma zuciyata za ta yi murna;16can cikin zuciyata za ta yi farinciki lokacin da leɓunan ka suka furta abin da ke dai-dai.
17Kada ka bar zuciyarka ta yi kishin masu zunubi, amma ka ci gaba da tsoron Yahweh dukkan rana.18Tabbas akwai gobe kuma ba za a datse begen ka ba.
19Ka ji - kai! - ɗa na, ka sami hikima ka kuma bida zuciyarka a hanyar.20Kada ka yi abokantaka da mashaya, ko masu cin abinci fiye da kima,21gama da mashayi da marar horo ga ci suna zama matalauta kuma gyangyadi za shi suturce su da tsummokara.
22Ka saurari mahaifin ka wanda ya haife ka kuma kada ka rena mahaifiyar ka sa'ad da ta tsufa.23Ka sayi gaskiya, amma kada ka sayar da ita; sayi hikima, da umarni, da kuma fahimta.
24Mahaifin mutum mai adalci za shi yi farinciki, kuma duk wanda ya haifi yaro mai hikima za shi yi murna dominsa.25Bari mahaifinka da mahaifiyarka su yi murna kuma bari ita da ta haife ka ta yi farinciki.
26‌Ɗana, ka ba ni zuciyarka kuma bari idanuwanka su kula da hanyoyi na.27Gama karuwa rami ne mai zurfi, kuma mace mai gurɓataccen hali rijiya ce ƙuntacciya.28Tana kwanciya kamar ɗan fashi tana kuma barbaza yawan munafunci cikin 'yan adam.
29Wa keda waiyo? Wa ke da kaito? Wa keda faɗace-faɗace? Wa ke ƙorafi? Wa keda raunuka babu dalili? Wa keda jajayen idanuwa?30Waɗanda suka daɗe da ruwan inabi, waɗanda suka gwada gaurayayyen ruwan inabi.
31Kada ka dubi ruwan inabi sa'ad da ya yi ja, lokacin da ya ke kumfa a cikin moda yana kuma kwararowa ƙasa a hankali.32A ƙarshe zai yi sãra kamar maciji ya kuma yi harbi kamar kãsa.33Idanunka zasu ga baƙon abubuwa kuma zuciyarka za ta furta gurɓatattun abubuwa.
34Za ka zama kamar wanda ke kwanciya bisa tekuna ko kwantawa bisa rufin jirgi.35"Sun buge ni," za ka ce. "amma ban ji ciwo ba. Sun buge ni, amma ban ji zafi ba. Har yaushe zan farka? Zan nemi wani abin shan."

24

1Kada ka yi ƙyashin masu aikata mugunta, ko ka yi marmarin yin abokantaka da su,2domin zuciyarsu na ƙirƙiro da ta'addanci kuma leɓunansu na zancen rigima.

3Ta wurin hikima a ke gina gida ta wurin fahimta a ke kafa shi.4Ta wurin ilimi a ke cika ɗakunan da dukkan dukiya masu tamani da daraja.
5Jarumi mai hikima na da ƙarfi, kuma mutum mai ilimi na ƙara ƙarfinsa;6domin ta wurin shawara na hikima zaka yi yaƙi kuma cikin shawarwari masu yawa akwai nasara.
7Hikima na da tsawo ga wawa; a bakin ƙofa ba ya buɗe bakinsa.
8Akwai wani wanda ke shirin aikata mugunta - mutane na kiransa shugaban dabaru.9Wawan shiri zunubi ne kuma mutane na ƙyamar mai ba'a.
10Idan ka yi sanyi sabili da tsoro a ranar wahala, to ƙarfinka ƙalilan ne.
11Ka ƙwaci waɗanda aka ɗauke ga mutuwa ka kuma hana waɗanda ke gangarawa zuwa yanka.12Idan ka ce, "Duba, ba mu san da komai game da wannan ba," shi wanda ke auna zuciya ba ya fahimci abin da kake faɗa ba? Wanda ke tsaron ranka, ba yana sane da haka ba? Allah ba zai saka wa kowanne abin da ya cancance shi ba?
13Ya ɗana, ka ci zuma domin yana da kyau, domin ɗigo-ɗigon sakar zuma na da zaƙi a bakin ka.14Haka hikima take ga ranka - Idan ka same ta, gobe tabbas ne kuma begen ka baza a katse shi ba.
15Kada ka yi kwanto kamar mugun mutum wanda ke kai farmaki ga gidan mutum mai adalci. Kada ka lalatar da gidansa!16Gama mutum mai adalci na faɗuwa ƙasa sau bakwai ya tashi kuma, amma ana kãda mugayen mutane ƙasa da bala'i.
17Kada ka yi farinciki sa'ad da maƙiyin ka ya faɗi kuma kada zuciyarka ta ji daɗi sa'ad da ya yi tuntuɓe,18domin Yahweh zai gani ya kuma bayyana rashin yardarsa ya kuma juyar da hasalarsa daga gare shi.
19Kada ka da mu saboda masu aikata mugunta, kuma kada ka yi ƙyashin mugayen mutane,20gama mugun mutum ba shi da tabbaccin gobe kuma fitilar mugaye za ta ɓice.
21Ka ji tsoron Yahweh, ka kuma ji tsoron sarki, ya ɗana; kada ka yi abokantaka da waɗanda suka tayar masu,22gama ba zato azaba zata auko kuma wa ya sani girman lalatar da zata zo daga dukkan su biyun?
23Haka ma waɗannan maganganu ne na masu hikima. Nuna bambanci cikin shari'a ba abu ne mai kyau ba.
24Duk wanda ya cewa mugun mutum, "Kai mutum mai adalci ne," mutane zasu la'anta shi al'ummai kuma zasu ƙi shi.25Amma waɗanda suka hori mai mugunta zasu sami jin daɗi kuma kyautai na alheri zasu zo gare su.
26Wanda ya ba da amsa mai kyau yana bada sumba ga leɓuna.27Ka shirya aikinka na waje, ka kuma shirya wa kanka komai cikin fili; bayan haka, sai ka gina gidanka.
28Kada ka zama shaida gãba da maƙwabcinka babu dalili kuma kada ka ruɗar da leɓunanka.29Kada ka ce, "Zan yi masa abin da ya yi mani; Zan sãka masa abin da ya yi."
30na ratsa ta cikin filin rãgo, ta gonar inabi na mutumin da ba shi da hankali.31Duk ƙayayuwa sun rufe ko'ina, ƙasar ta cika da sarƙaƙiya, kuma ganuwarta ta dutse ta rushe.
32Sai na gani na kuma yi lura da ita; na duba na kuma karɓi umarni.33Yin barci kaɗan, da ɗan gyangyaɗi, da ɗan naɗe-naɗen hannuwa domin hutu -34da haka talauci za shi saukar maka, kuma buƙatarka kamar soja mai makami.

25

1Waɗannan ƙarin karin magana na Suleman ne, wanda mutanen Hezekiya, sarkin Yahuda suka kwafa.2‌Ɗ‌aukaka ta Allah ce ya ɓoye zance, amma ɗaukakar sarakuna su bincike shi.3Kamar yadda sammai suke da tsayi duniya kuma tana da zurfi, haka zuciyar sarakuna sun wuce gaban ganuwa.

4Ka sheƙe azurfa gwani kuma za shi yi amfani da azurfar ga aikinsa.5Haka ma, ka cire mugayen mutane daga gaban sarki kursiyinsa kuma zai kafu ta wurin aikata adalci.
6Kada ka ɗaukaka kanka a gaban sarki kada kuma ka zauna a mazaunin da aka shirya wa mutane masu daraja.
7Ya fi kyau shi da kansa ya ce maka, "Hauro zuwa nan," da shi ya kunyatar da kai a gaban mutum mai daraja. Abin da ka yi shaidar sa,8kada ka yi saurin kawo shi ga shari'a. Gama me zaka yi a ƙarshe idan maƙwabcinka yasa ka cikin kunya?
9Ka yi jayayya bisa matsala tsakaninka da maƙwabcinka da kansa kada kuma ka fallasa wani asirin,10domin kada wanda ya ji ka yasa ka ji kunya kuma mugun rohota a kanka da ba za a iya tsayarwa ba.
11'Ya'yan itacen aful na zinariya da aka yi masu jerin azurfa kamar magana ce da aka yi ta dai-dai.12Zobe na zinariya ko sarƙar da aka yi ta da zinariya mai kyau horo ne na hikima ga kunnuwan mai sauraro.
13Kamar yadda sanyin ƙanƙara ya ke lokacin girbi haka ɗan aike mai aminci ke ga waɗanda suka aike shi; yana dawo da ran shugabanninsa.14Giza-gizai da iska amma babu ruwan sama ne wanda ke fahariya da kyautar da bai bayar ba.
15Cikin hakuri ake rinjayar mai mulki kuma harshe mai taushi na iya karya ƙashi.
16Idan ka sami zuma, kada kayi masa shan fitar hankali - in ba haka ba, idan ka sha dayawa, za ka amayas.17Kada ka cika zuwa gidan maƙwabcinka, yana iya gajiya da kai ya kuma ƙi ka.
18Mutumin da ya yi shaidar ƙarya bisa maƙwabcinsa na kama da kulkin da aka yi amfani da shi a yaƙi, ko takobi, ko wani mãshi mai tsini.19Mutum marar amincin daka amince da shi a lokacin wahala na kama da ruɓaɓɓen haƙora ko tafiya da gurguwar ƙafa.
20Kamar mutumin da ya kwaɓe rigarsa a yanayi mai tsananin sanyi, ko zuba inabi bisa ainihin gawayi na soda, haka wanda ke yin waƙoƙi ga zuciya mai nauyi.
21Idan makiyinka na jin yunwa, ba shi abinci ya ci, idan kuma yana jin ƙishi, ba shi ruwa ya sha,22gama zaka tula masa tarin garwashin wuta a bisa kansa Yahweh kuma zai baka lada.
23Kamar yadda iskar arewa ke kawo ruwan sama, haka take da harshen da ke faɗin asirai yana hadasar da fuskoki masu fushi.24Gara a zauna a saƙon rufin ɗaki da a zauna gida ɗaya tare da mace mai yawan faɗace-faɗace.
25Kamar yadda ruwan sanyi ke ga wanda ke ƙishi, haka ya ke ga labari mai daɗi da ke zuwa daga ƙasa mai nisa.26Kamar ƙazantacciyar maɓuɓɓuga ko gurɓatacciyar rijiya haka ya ke da mutum adali da ya yi sanyi a gaban mugayen mutane.
27Ba shi da kyau a sha zuma da yawa; wannan kamar neman yabo ne bisa yabo.28Mutumin da bashi da kamun kai na kama da birnin da ke a buɗe kuma bashi da ganuwa.

26

1Kamar garin ƙanƙara a lokacin zafi ko ruwan sama a lokacin girbi, haka ma yabo bai dace ga wawa ba.2Kamar tsuntsayen da ke shawagi a sama basu sauka ba, haka la'annar da ba a cancance ta ba baza ta sauka ba.

3Tsumagiya domin doki ne, linzami domin jaki sanda kuwa domin bayan wawaye.4Kada ka bada amsa ga wawa bisa ga wawancinsa, in ba haka ba za ka zama kamar sa.
5Ka bada amsa ga wawa sai ka ƙara masa wawancinsa, domin kada ya ɗauki kansa wani mai hikima ne.6Duk wanda ya aika da saƙo ta hannun mai wauta na datse ƙafafunsa ne yana kuma shan ta'addanci.
7Kamar ƙafafuwa shanyayyu da ke rataye da ƙasa haka karin magana ya ke a bakin wawaye.8Kamar a gwada harba dutse a majajjawa haka ya ke a bada yabo ga wawa.
9Kamar ƙaya data shiga hannun mashayin giya haka karin magana a bakin wawaye.10Kamar maharbin da yaji wa dukkan waɗanda ke kewaye da shi raunuka haka wanda ya yi hayar wawa ko hayar duk mai wucewa kan hanya.
11Kamar yadda kare ke komawa ga abin da ya amayas, haka wawan da ke maimaita wawancinsa.12Ko ka ga wani wanda ke ganin kansa mai hikima ne? Ko wawa na da bege fiye da shi.
13Ragon mutum ya ce, "Akwai zaki a kan hanya! Akwai zaki a tsakanin buɗaɗɗun wurare!"14Kamar yadda ƙofa ke juyawa a ƙyaurenta, haka ragon mutum bisa gadonsa.
15Ragon mutum na sa hannunsa cikin abinci duk da haka ba shi da ƙarfin ɗaga shi zuwa bakinsa.16Ragon mutum a ganin sa mai hikima ne shi fiye da mazaje bakwai da suka bada dalilai masu kyau.
17Kamar wadda ya riƙe kunnuwan kare, haka mai wucewa kan hanya da ya yi fushi ga shawarwarin da basu shafe shi ba.
18Kamar mahaukacin da ke harba kibiya mai wuta,19haka wanda ya ruɗi maƙwabcinsa yana cewa, "Ba wasa kawai nake yi ba?"
20Don rashin itace, wuta ke mutuwa; kuma duk inda babu magulmaci faɗace-faɗace na ɗaukewa.21Kamar yadda gawayi ke ga wuta maici itace kuma ga wuta, haka ya ke da mutum mai faɗace-faɗace wurin kunna husuma.
22Maganganun magulmaci suna kama da abinci mai daɗi; suna shigewa can cikin jiki.23Kamar kaskon da aka dalaye da azurfa haka baki mai zafi da kuma zuciya mai mugunta.
24Shi da ke ƙin mutane yana ɓoye yadda ya ke ji da leɓunansa kuma yana ajiyar munafunci cikinsa.25Zai yi maganar alheri, amma kada ka yarda da shi, Gama akwai ƙazanta guda bakwai cikin zuciyarsa.26Ko da ya ke rashin gaskiya ya ɓoye ƙiyayyarsa, za a bayyana muguntarsa a cikin taro.
27Duk wanda ya haƙa rami zai faɗa cikinsa kuma dutsen zai gangaro wa wanda ya turo shi.28Maƙaryacin harshe na ƙin mutanen da ya ke murƙushewa kuma baki mai fahariya na kawo hasara.

27

1Kada ka yi alfahari game da gobe, domin baka san me ranar ke iya kawo wa ba.2Bari wani ne ya yabe ka amma ba naka bakin ba; baƙo amma ba naka leɓunan ba.

3Ka yi la'akari da yadda dutse ke da nauyi da kuma nauyin yashi - cakuna ta wawa tafi dukkansu biyu nauyi.4Akwai rashin imanin hasala da kuma ambaliyar fushi, amma wa zai iya tsayawa a gaban kishi?
5Tsautawa a fili ta fi nuna ƙauna a ɓoye.6Har yanzu akwai aminci a cutar da tazo daga aboki, amma maƙiyi na iya sumbatarka babu iyaka.
7Mutumin da ya ci abinci ya ƙoshi zai ƙi ko da ma saƙar zuma ne, amma ga mutum mai yunwa, kowanne abu mai ɗaci na da zaƙi.8Kamar tsuntsun da ke yawo daga sheƙarsa haka mutumin da ya kauce daga inda ya ke zama.
9Kayan ƙamshi da turare suna sa zuciya ta yi farinciki, amma daɗin aboki na zuwa ne daga amintacciyar shawararsa.10Kada ka yi banza da abokinka da kuma abokin mahaifinka, kuma kada ka tafi gidan ɗan'uwanka a ranar wahalar ka. Maƙwabcin da ke kusa da kai ya fiye maka da ɗan'uwanka mai nisa da kai.
11Ka zama mai hikima, ya ɗana, ka sa zuciyata ta yi farinciki; sa'an nan zan bada amsa ga wanda ke yi mani ba'a.12Mutum mai cikakken hankali na ɓoyewa ne idan ya ga wahala, amma mutane masu halin baƙunci na tafiya kai-tsaye har su kuma shiga wahala.
13Ka karɓe mayafin wanda ya tsaya wa baƙo, ka kuma riƙe shi a matsayin alƙawari sa'ad da ya tsayawa karuwar mace.14Duk wanda yasa wa maƙwabcinsa albarka da babbar murya da sassafe, wannan albarkar za a ganta kamar la'ana ce!
15Mace mai yawan faɗace-faɗace na kama da yayyafi a ranar ruwan sama marar tsayawa;16hana ta na kama da hana iska ne, ko kuma yin ƙoƙarin riƙe mai cikin hannun damanka.
17‌Ƙarfe ke wãsa ƙarfe; haka nan kuma, mutum ke wãsa abokinsa.18Wanda ya yi noman zaitun zai ci 'ya'yan itacensa, kuma wanda ya tsare ubangidansa za a yabe shi.
19Kamar yadda ruwa ke nuna fuskar mutum, haka zuciyar mutum ke bayyana mutumin.20Kamar yadda Lahira da Abaddon basu ƙoshi, haka idanun mutum basu taɓa ƙoshi.
21Maƙera domin gwada azurfa ne tanderun wuta kuwa domin zinariya ne; mutum kuma ana gwada shi ne sa'ad da aka yabe shi.22Ko da zaka daka wawa da taɓarya - harɗe da hatsi - duk da haka wawancinsa ba zai bar shi ba.
23Ka tabbatar ka san lafiyar tumakinka ka kuma nuna damuwarka ga garkenka,24gama dukiya ba ta har abada ba ce. Ko masarauta tana dawwama dukkan tsararraki?25Ka san lokacin da busasshiyar ciyawa ta ɗauke sabuwa kuma ta fito, da kuma lokacin da ciyawa daga bisa tuddai ke taruwa ciki.
26Waɗannan tumakai zasu yi maka tanadin tufafin sawa haka kuma ragunan zasu yi tanadin kuɗi domin filin.27Za a sami madarar awaki domin abincinka - abinci domin iyalinka - kuma wartsakarwa domin 'yan matanka bayi.

28

1Mugayen mutane na gudu babu wani mai korar su, amma masu adalci basu da tsoro kamar ɗan zaƙi.2Saboda kurakuran ƙasa, ta sami shugabanni da yawa, amma ga mutum mai fahimta da ilimi, zata dawwama na lokaci mai tsawo.

3Matalaucin da ke zaluntar wasu matalautan mutane na kama da ruwan sama da baya bada abinci.4Waɗanda suka yi banza da shari'a na koma wa ga yabon mugayen mutane, amma waɗanda ke bin shari'a na gãba da su.
5Mugayen mutane basu fahimtar hukunci, amma masu neman Yahweh na fahimtar komai.6Ya fiye wa matalaucin mutum mai tafiya cikin aminci, da mai arziƙi wanda ke tafiya cikin hanyoyinsa na rashin aminci.
7Shi wanda ya kula da shari'a ɗa ne mai fahimta, amma abokin mashaya abin kunya ne ga mahaifinsa.8Duk wanda ya tara dukiyarsa ta hanyar zamba dukiyarsa zata tafi wurin wani wanda zai tausaya wa matalauta.
9Idan wani ya juyar da kunnuwarsa daga sauraren shari'a, ko addu'arsa ma abin ƙyama ce.10Duk wanda ya ɓatas da mai gaskiya domin aikata mugunta zai faɗa cikin ramin da ya haƙa, amma mai gaskiya zai sami gãdo mai kyau.
11Mai arziki na yi wa kansa kallon shi mai hikima ne, amma mai fahimta wanda ke matalauci zai tona masa asiri.12Lokacin da masu adalci ke mulki, akwai babbar ɗaukaka; amma sa'ad da mugaye suka tashi, ana tone asirin mutane.
13Wanda ya ɓoye zunubansa ba za shi yi albarka ba, amma shi wanda ya furtasu ya kuma rabu da su za a yi masa jinƙai.14Shi wanda ke rayuwa cikin girmamawa mai albarka ne, amma wanda ya taurare zuciyarsa zai abka cikin wahala.
15Kamar zaki mai ruri ko kamar dabbar kerkeci mai huci haka mugun shugaba a bisa mutane matalauta.16Shugaban da ba shi da fahimta azzalumi ne, amma wanda ya tsani zalunci zai daɗe da kwanakinsa.
17Idan mutum ya yi laifi domin ya zubda jinin wani, zai zama mai gudun hijira har sai ya mutu kuma ba wanda zai taimake shi.18Duk wanda ya yi rayuwa cikin gaskiya zai zauna lafiya lau, amma wanda tafarkinsa karkataccc ne zai faɗi ba zato.
19Shi wanda ya yi aiki cikin gonarsa zai sami abinci mai yawa, amma wanda ya bi wofi zai sami talauci mai yawa.20Mutum mai aminci zai sami albarka mai girma, amma wanda ya sami wadata cikin hanzari ba zai tsira daga hukunci ba.
21Bai kamata a nuna sonkai ba, amma akan 'yar gurasa mutum kan iya aikata ba dai-dai ba.22Mutum mai rowa na hanzarin neman arziki, amma bai san da cewar talauci na zuwa bisansa ba.
23Duk wanda ya yi ma wani horo, daga baya zai sami tagomashi daga gare shi fiye da wanda daga shi aka yi masa zaƙin baki.24Duk wanda ya zambanci mahaifinsa da mahaifiyarsa ya kuma ce, "Wannan ba zunubi bane," shi abokin wanda ke hallakarwa ne.
25Mutum mai yawan son kansa na haddasar da rigima, amma wanda ya dangana da Yahweh zai yi albarka.26Shi wanda ya dangana ga tasa zuciya wawa ne, amma duk wanda ya yi tafiya cikin hikima zai yi nisa daga hatsari.
27Wanda ya bayar ga matalauta ba za shi rasa komai ba, amma wanda ya rufe idanunsa gare su zai sami la'ana.28Lokacin da miyagu suka tashi, mutane na ɓoye kansu; amma idan suka lalace, masu adalci na ƙaruwa.

29

1Mutumin da ya karɓi horo dayawa amma ya taurare wuyansa za a karya shi cikin ƙanƙanen lokaci da ba za shi warke ba.2Lokacin da masu adalci suka ƙaru, mutane na farinciki, amma lokacin da mugu ke shugabanci, mutane na ajiyar zuciya.

3Duk wanda ya ƙaunaci hikima nasa mahaifinsa ya yi farinciki, amma wanda ya yi abokantaka da karuwai na lalatar da dukiyarsa.4Sarki na kafa ƙasar da adalci, amma wanda ya nemi cin hanci yana yayyaga ta dukka.
5Mutumin da ya yi wa maƙwabcinsa daɗin yana shinfiɗa wa sawayensa tarko ne.6Cikin zunubin mugun mutum nan akwai tarko, amma mutum mai adalci yana waƙoƙi da farinciki.
7Mutum mai adalci na sane da yancin talakawa; mugun mutum ba shi da wannan ilimin.8Masu ba'a sukan cinna wa birni wuta, amma waɗanda ke da hikima suna juyar da hasala.
9Lokacin da mutum mai hikima ya yi jayayya da wawa, yana fusata yana kuma dariya, ba za a kuma sami hutawa ba.10Masu zubda jini suna tsanar masu gaskiya su kuma nemi ran kamilai.
11Wawa yana bayyana dukkan haushinsa, amma mutum mai hikima na danne shi ya kuma kãme kansa.12Idan mai mulki ya saurari ƙarairayi, dukkan shugabanninsa zasu zama mugaye.
13Matalauci da wanda ke azzalumi sun zama ɗaya, gama Yahweh ya bada haske ga idanunsu dukka.14Idan sarki ya shar'anta matalauta da gaskiya, kursiyinsa zai kafu har abada.
15Sanda da tsautawa na bada hikima, amma ɗan da ba ya sami horo ba na kawo wa mahaifiyarsa kunya.16Yayin da mugayen mutane ke riƙe da iko, kurakurai na ƙaruwa, amma adalai zasu ga faduwar mugayen mutane.
17Ka hori ɗanka zai kuma baka hutu; zai kawo wa ranka jin daɗi.18Inda babu furtacciyar ruya mutane kan yi yadda suka ga dama, amma wanda ya kula da shari'a mai albarka ne.
19Bawa ba zai tsautu da magana kawai ba, ko da ya fahimta, ba zai juya ba.20Ko ka ga mutum mai saurin magana? Ya fiye a sa zuciya ga wawa da wannan.
21Duk wanda ya shagwaɓa bawansa tun yana matashi, a ƙarshe akwai wahala.22Mutum mai fushi na garwaya husuma kuma mai hasala na aikata zunubai masu yawa.
23Girman kan mutum ne ke kãda shi, amma wanda ke da ruhun saukin kai za a ba shi ɗaukaka.24Shi wanda ya yi tarayya da ɓarawo maƙiyin ransa ne; yana jin la'ana bai kuma ce komai ba.
25Tsoron mutum tarko ne, amma wanda ya dogara ga Yahweh za a kiyaye shi.26Dayawa ne masu neman ganin fuskar mai mulki, amma daga wurin Yahweh adalci ke zuwa ga mutum.
27Mutum marar gaskiya abin ƙyama ne ga mutane masu adalci, amma wanda ke mai adalci abin ƙi ne ga mugun mutum.

30

1Maganganun Agu ke nan ɗan Yãke - furcin: Wannan mutumin ya gaya wa Itiyel da Ukal:2Tabbas ni kamar wata dabba ce ba mutum ba kuma bani da fahimta irin na mutum.3Ban koyi hikima ba, bani kuma da ilimi game da Mai Tsarkin.

4Wane ne ya haura cikin sama ya kuma sauko? Wane ne ya tattara iska cikin hannuwansa? Wane ne ya tattara ruwaye cikin mayafi? Wane ne ya kafa iyakokin dukkan duniya? Mene ne sunansa, kuma mene ne sunan ɗansa? Tabbas ka sani.
5Kowacce maganar Allah gwadajjiya ce; garkuwa ce ga duk waɗanda ke ɓuya gare shi.6Kada ka ƙara a bisa maganarsa, domin kada ya hore ka, kuma za a iske ka maƙaryaci.
7Abu guda biyu na tambaya gare ka, kada kuma ka hana mani kamin na mutu:8Kada ka bar wofi da ƙarya su kusance ni. Kada ka ba ni ko talauci ko arziki, ka dai ba ni abincin da nake buƙata.9Gama idan na samu dayawa, ina iya ƙaurace maka in ce, "Wane ne Yahweh?" Ko idan na zama matalauci, ina iya sata har in kawo reni ga sunan Allahna.
10Kada ka zargi bawa a gaban ubangidansa, don kada ya la'anta ka kuma har a kama ka da laifi.
11Akwai wata tsara da ke la'anta mahaifinsu kuma ba ta albarkatar mahaifiyarsu.12Akwai tsarar da ke ganin kanta mai tsarki ce a gaban idanun ta, amma duk da haka basu wanku daga ƙazantarsu ba.
13Akwai tsarar da fuskarsu take ɗage sama, dubi yadda girar idanunsu ke ɗage can sama!14Akwai wata tsara wadda haƙoransu na takobi ne, kuma mataunansu kamar wuƙaƙe, domin su hallaka matalauta daga duniya mabuƙata kuma daga cikin 'yan adam.
15Matsattsaku na da 'yan mata biyu: "Bayar kuma bayar" suke kuka. Akwai abu guda uku da basu ƙoshi, guda huɗu da basu cewa, "Ya isa":16Lahira; da mahaifar da bata ɗaukar ciki; da ƙasar da bata ƙoshi da ruwa; da kuma wutar da bata cewa, "Ya isa!"17Idanun da suka yi wa mahaifi ba'a ko suka rena rashin biyayya ga mahaifiya, hankakin kwari zasu ƙwaƙule idanunsa, kuma angulai zasu cinye namansa.
18Akwai abubuwa guda uku masu ban mamaki gare ni, har huɗu da ban fahimce su ba:19hanyar gaggafa a sararin samaniya; hanyar macijiya a bisa kan dutse; hanyar jirgi a bisa kan teku; da hanyar ɗan saurayi tare da 'yar budurwa.
20Ga hanyar mazinaciya: tana cin abinci ta kuma share baki tana cewa, "Ban yi wani abin da ke ba dai-dai ba."
21A ƙarƙashin abubuwa guda uku duniya ke girgiza, kuma a ƙarƙashin guda huɗu bata iya jurewa:22lokacin da bawa ya zama sarki; yayin da wawa ya ƙoshi da abinci;23macen da aka ƙi lokacin data yi aure; baiwar da kuma ta gãji uwargijiyarta.
24Akwai abubuwa huɗu cikin duniya 'yan ƙanƙanana ne amma suna da hikima sosai:25tururuwa hallitu ne marasa ƙarfi, amma suna tanadin abincinsu cikin rani;26remaye hallitu marasa ƙarfi, amma suna gina gidajensu cikin duwatsu.
27Fãra basu da sarki, amma dukkansu suna cincirindo-cincirido.28Haka ma ƙadangare, kana iya riƙe shi cikin hannunka biyu, duk da haka kana samun su a cikin fadodi.
29Akwai abubuwa uku suna da koƙari cikin ayyukansu haka ma huɗu da ke da takama a yadda suke tafiyarsu:30zaki, mai ƙarfi cikin namun jeji - ba shi juya baya daga kowanne abu,31zakara mai cara; bunsuru; da kuma sarkin da sojojinsa ke tsaye kusa da shi.
32Idan ka yi wauta, kana ɗaukaka kanka, ko idan kana shirye-shiryen mugunta - ka ɗibiya hannuwanka a bakinka.33Kamar yadda kaɗaɗɗar madara ke fitar da mai da kuma kamar yadda hanci ke haɓo yayin da aka buge shi, haka ayyukan da aka aiwatar da su a cikin fushi.

31

1Maganganun sarki Lemuwel - umarnin da mahaifiyarsa ta koya masa.2Mene ne, ya ɗana? Mene ne, ɗan mahaifata? Me kake so, ɗan alƙawarina?3Kada ka bada ƙarfinka ga mata, ko hanyarka ga waɗanda ke hallakar da sarakai.

4Ba girman sarakai ba ne, Lemuwel, ba girman sarakuna bane su sha giya, ko masu mulki su yi kwaɗayin abin sha mai bugarwa,5domin lokacin da suka sha sukan manta da abin da aka umartar, su kuma juyar da yancin dukkan ƙuntattu.
6Ka bada abin sha mai bugarwa ga wanda ke hallaka inabi kuma ga waɗanda ke cikin ƙunci.7Zaya sha ya manta da talaucinsa kuma ba za shi tuna da wahalarsa ba.
8Ka yi magana a madadin waɗanda basu iya magana, don dalilin dukkan masu hallaka.9Ka yi magana a fili ka kuma shar'anta dai-dai da ma'aunin adalci ka kuma yi roƙo sabili da nawayar matalauta da mabuƙatan mutane.
10Wa ke iya samun mace cikakkiya? Darajarta ta fi duwatsu masu daraja.11Zuciyar maigidanta ta yarda ya ita, kuma ba zai taɓa talaucewa ba.12Tana yin abubuwan alheri dominsa ba mugunta ba dukkan kwanakinta.
13Takan nemi ulu da lilin, ta kuma yi aiki cikin jin daɗi da hannuwanta.14Tana kama da fataken jirage; tana kawo abincinta daga nesa.15Takan tashi da dare ta bai wa iyalinta abinci, tana kuma raba wa bayinta mata aikinsu.
16Takan lura da gona ta kuma saya, da ribar hannuwanta takan dasa gonar inabi.17Tana yi wa kanta ado da ƙarfi ta kuma maida kafaɗunta ƙarfafa.
18Takan san abin da zai zama riba mai kyau gare ta; dukkan dare fitilarta ba ta mutuwa.19Tana ɗora hannunta bisa mazarin sãƙa, kuma ta riƙe murɗaɗɗen zaren.
20Tana miƙa hannuwanta zuwa ga matalauta; tana kuma miƙa hannuwanta zuwa ga mutane mabuƙata.21Bata tsoron sanyi ta dalilin iyalinta, gama dukkan iyalinta na sanye da kayan sanyi.
22Tana yiwa gadonta shimfiɗa, tana kuma sanye da tufafi masu kyau na lilin masu laushi na shunayya.23Maigidanta sananne ne a ƙofofi, lokacin da ya ke zama da shugabannin ƙasar.
24Takan ɗinka riguna ta sayar, tana kuma sayar da ɗamara ga fatake.25Tana yafe da ƙarfi da daraja, kuma tana yiwa lokaci mai zuwa dariya.
26Tana buɗe bakinta cikin hikima kuma dokar alheri na a bakinta.27Tana lura da tafarkin iyalanta kuma bata cin abincin zaman banza.
28Yaranta na tashi su kira ta mai albarka, kuma mijinta na yabonta, cewa,29"Mata dayawa sun aikata dai-dai, amma ke kin wuce su gaba ɗaya."
30Kayan kwalliya abin yaudara ne, kyau abin banza ne, amma mace mai tsoron Yahweh, za a yabe ta.31Ka ba ta 'ya'yan hannuwanta kuma bari ayyukanta su yabe ta a bakin ƙofofi.

Littafin mai wa'azi

1

1Waɗannan ne maganganun malami, zuriyar Dauda kuma sarki a Yerusalem.2Malami ya faɗi wannan. "Kamar turirin hayakin raɓa, kamar hurawa a cikin iska, komai na ɓacewa, su na barin tambayoyi masu yawa.3Wacce riba ce 'yan'adam suke samu daga dukkan aikin da suke yin aiki tuƙuru akai a ƙarƙashin rana?

4Tsara ɗaya ta tafi, wata tsarar kuma ta zo, amma duniya ta tabbata har abada.5Rana na fitowa, kuma tana faɗuwa, tana kuma sake saurin komawa wurin da ta fito.6Iska na hurawa kudu tana kuma zagayawa kewaye zuwa arewa, koyaushe ta na tafiya kewaye bisa tafarkinta ta kuma sake dawowa.
7Dukkan koguna suna gangarawa zuwa teku, amma teku bai taɓa cika ba. Inda koguna su ke tafiya, a can kuma suke sake tafiya.8Komai ya zama a gajiye, ba bu kuma wanda zai iya yin bayani. Ido bai ƙoshi da abin da ya ke gani ba, ko kuma kunne ya wadatu da abin da ya ke ji ba.
9Duk abin da ya kasance shi ne zai kasance, duk kuma abin da aka taɓa yi shi ne za'a yi. Ba bu wani abu sabo a ƙarƙashin rana.10Akwai wani abu game da abin da za'a ce, 'Duba, wannan sabo ne'? Duk abin da ya wanzu ya riga ya wanzu da daɗewa, a lokacin shekarun da suka zo da daɗewa kafin mu.11Babu wanda ya ke kamar ya tuna da abubuwan da suka faru a zamanin dã, da abubuwan da suka faru daga bisani sosai da abin da zai faru a nan gaba bai yi kama da za'a tuna da shi ba ma."
12Ni ne Malamin, kuma ni ne nake sarki a bisa Isra'ila a Yerusalem.13Na miƙa raina ga bincike da nemowa ta wurin hikima duk abin da ake yi a ƙarƙashin sama. Cewa nema gajiyayyen aiki ne da Allah ya ba 'ya'yan ɗan'adam suyi ta aiki da shi.14Naga dukkan ayyukan da ake yi a ƙarƙashin rana, kuma duba, dukkan su ɗungum turirin hayaƙi ne da bin iska.15Murɗaɗɗe ba za a iya miƙar da shi ba! Abin da ya ɓace ba za a iya ƙidaya wa ba!
16Nayi magana da zuciyata cewa, "Duba, na sami hikima fiye da waɗanda suke kafin ni a Yerusalem. Raina yaga babbar hikima da ilimi."17Sai na miƙa zuciyata in san hikima da kuma hauka da wawanci. Sai na kai ga fahimtar cewa wannan ma wani yunƙuri ne na kiwon iska.18Gama a cikin yalwar hikima akwai ruɗewa sosai, shi kuma wanda ke ƙara ilimi yana ƙara baƙinciki.

2

1Na cewa zuciyata, "Zo yanzu, zan gwada ki da murna. Sai ki more jin daɗinki." Amma duba, wannan ma 'yar taƙaitacciyar iska ce.2Game da dariya na ce, "Taɓin hankali ce," game da jin daɗi kuma, "Ina amfanin shi?"

3Na nemo a zuciyata yadda zan biya buƙatar marmarina da ruwan inabi. Na bar raina ya bishe ni da hikima kodaya ke har wa yau ina riƙe da wawanci. Na so in samo abu mai kyau da mutane za suyi a ƙarƙashin sama a lokacin kwanakin rayuwarsu.
4Na aiwatar da manyan abubuwa. Na gina gidaje domin kaina na kuma dasa garkunan inabi.5Na ginawa kaina lambuna da tashoshin shaƙatawa; na dasa dukkan ire-iren itatuwa masu ba da 'ya'ya a cikin su.6Na ƙirƙiro tafkunan ruwa domin su bada ruwa ga jejin da ake renon itatuwa.
7Na sawo bayi maza da bayi mata; An haifa ma ni bayi a fãdata. Kuma ina da manyan garkunan shanu da garkunan tumaki da awaki, fiye da duk wani sarki da ya yi mulki kafin ni a Yerusalem.8Na kuma tarawa kaina azurfa da zinariya, dukiyar sarakuna da larduna. Na samar wa kai na mawaƙa maza da mata - abin farincikin 'ya'yan 'yan'adam - da ƙwaraƙwarai masu yawa.
9Sai na zama mafi girma da dukiya fiye da dukkan waɗanda suke kafin ni a Yerusalem, kuma hikimata ta kasance tare da ni.10Duk abin da idanuna suka yi marmari, ban hana masu ba. Ban hana wa zuciyata duk wani jin daɗi ba, saboda zuciyata na farinciki cikin dukkan aikin ƙarfina kuma jin daɗi shi ne ladata domin dukkan aikina.
11Daga nan na duba dukkan ayyukan da hannuwa na suka aiwatar, da aikin da nayi, amma kuma, kowanne abu turiri ne da yunƙurin kiwon iska. A ƙarƙashin rana babu wata riba a cikin su.12Daga nan na juya in yi la'akari da hikima, da kuma hauka da wawanci. Gama me sarki na gaba zai yi wanda zai zo bayan sarki, wanda ba a riga anyi ba?
13Daga nan na fãra fahimtar cewa hikima na da daraja bisa wawanci, kamar yadda haske yafi duhu.14Mutum mai hikima ya kan yi amfani da idanunsa cikin kansa ya ga inda ya ke tafiya, amma wawa yana tafiya cikin duhu, ko da ya ke na san al'amura iri ɗaya ne ke faruwa da dukkan su.
15Daga nan na ce a cikin zuciyata, "Abin da ya fãru da wawa, ni ma zai fãru da ni. To ina ban-banci idan ina da wayau sosai?" Sai na kammala a cikin zuciyata, "Wannan ma turirin hayaƙi ne kawai."16Domin mutum mai hikima, kamar wawa, ba a tunawa da shi har dogon lokaci sosai. A cikin kwanaki masu zuwa an riga an manta da komai. Mai wayau na mutuwa kamar yadda wawa ke mutuwa.
17Sai rayuwa ta gundure ni saboda dukkan aikin da ake yi a ƙarƙashin rana mugunta ce a gare ni. Wannan kuwa saboda komai turiri ne kawai da yunƙurin kiwon iska.18Na ƙi jinin dukkan abin da na aiwatar wanda na aikata a ƙarƙashin rana saboda tilas in bar su baya ga mutumin da zai zo bayana.
19Gama wa ya sani ko zai zama mutum mai hikima ko wawa? duk da haka zai zama shugaba bisa komai ƙarƙashin rana wanda aikina da hikimata suka gina. Wannan ma turirin hayaƙi ne.20Saboda haka zuciyata ta fãra razana bisa dukkan aikin da nayi a ƙarƙashin rana.
21Domin za a sami wanda ya ke aiki tare da hikima, tare da ilimi, da ƙwarewa, amma zai bar duk abin da ya ke da shi ga mutumin da bai yi wani abu kamar sa ba. Wannan ma turirin hayaƙi ne da tsautsayi mai girma.22Domin wacce riba taliki ya samu wanda ya yi aiki tuƙuru kuma ya yi ƙoƙari a zuciyarsa ya kammala aikin ƙarfinsa a ƙarƙashin rana?23Kowacce rana aikin shi cike da ciwo da gajiya, sa'an nan da dare ransa ba ya samun hutawa. Wannan ma turirin hayaƙi ne.
24Babu wani abin da ya fiye wa kowa baya ga ya ci ya sha ya ƙoshi da abin da ke mai kyau cikin aikinsa. Naga cewa wannan gaskiyar ta zo daga hannun Allah ne.25Gama wane ne zai iya ci ko ya sami wani irin jin daɗi idan ba daga Allah ba?
26Domin ga dukkan wanda ya ke faranta masa rai, Allah na bayar da hikima da ilimi da farinciki. Duk da haka, ga mai zunubi yana bayar da aikin tattarawa da adanawa domin ya bayar da su ga wanda ya ke farantawa Allah rai. Wannan ma ɗungum turirin hayaƙi ne da yunƙurin kiwon iska.

3

1Game da kowanne abu akwai tsaidajjen lokaci, da zamani domin kowanne dalili ƙarƙashin sama.2Akwai lokacin haihuwa da lokacin mutuwa, lokacin dasawa da lokacin tuge dashe-dashen,3lokacin kashewa da lokacin warkarwa, lokacin yagawa da lokacin ginawa.

4Akwai lokacin kuka da lokacin dariya, lokacin makoki da lokacin rawa,5lokacin zubar da duwatsu da lokacin tattara duwatsu, lokacin rungume wasu mutane da lokacin janyewa daga rungumewa.
6Akwai lokacin dubawa domin abubuwa da lokacin tsayawa daga dubawar, lokacin ajiye abubuwa da lokacin zubar da abubuwa,7lokacin yaga sutura da lokacin gyara sutura, lokacin yin shiru da lokacin magana.
8Akwai lokacin ƙauna da lokacin ƙiyayya, lokacin yaƙi da lokacin salama.9Wacce riba ma'aikaci ke ci cikin aikin ƙarfinsa?10Naga aikin da Allah yaba talikai su kammala.
11Allah ya yi kowanne abu ya dace domin nasa lokaci. Ya sa madawwamin lokaci a zukatansu. Amma 'yan'adam ba zasu fahimci ayyukan da Allah ya yi ba, daga farkonsu har ya zuwa ƙarshensu.
12Nasan babu abin da ya fiye wa kowa baya ga ya yi farinciki ya kuma yi abin da ke mai kyau dukkan tsawon rayuwarsa -13kowa kuma ya ci ya sha, ya kuma fahimci yadda zai ji daɗin abin da ke zuwa daga dukkan aikinsa. Wannan kyauta ce daga Allah.
14Nasan cewa dukkan abin da Allah ya yi yana dawwama har abada. Babu abin da za a ƙãra akai ko a ɗauke, saboda Allah ne ya yi domin mutane su kusance shi tare da girmamawa.15Kowanne abu da ke wanzuwa ya rigaya ya wanzu; kowanne abu da zai wanzu ya rigaya ya wanzu. Allah ya sa talikai su nemi ɓoyayyun abubuwa.
16Na kalli muguntar da ke ƙarƙashin rana, inda ya kamata a yi hukunci, a gurbin adalci, mugunta ce ke wurin.17Na ce a zuciyata, "Allah zai shar'anta mai adalci da mugu a lokacin da ya dace domin kowanne al'amari da kowanne aiki."
18Na ce a zuciyata, "Allah na gwada talikai ya nuna masu cewa kamar dabbobi suke."
19Gama ƙaddarar ɗan'adam da ƙaddarar dabbobi ƙaddara ce iri ɗaya domin su. Mutuwar ɗaya kamar mutuwar ɗayan ce. Lumfashin iri ɗaya ne domin dukkan su. Babu wata daraja game da ɗan'adam fiye da ta dabbobi. Domin kowanne abu ba lumfashi ne kawai ba?20Kowanne abu na tafiya wuri ɗaya. Kowanne abu ya zo daga turɓaya, kuma kowanne abu zai koma ga turɓaya.
21Wa ya sani ko ruhun ɗan'adam na tafiya sama kuma ruhun dabbobi na tafiya ƙasa cikin ƙasa?22Sai kuma na gane cewa babu abin da ya fiye wa kowa banda ya ji daɗin aikinsa, domin wannan ne hidimarsa. Wa zai maido da shi baya yaga abin da ke fãruwa bayansa?

4

1Na sake yin tunani game da cutarwar da ke faruwa a ƙarƙashin rana. Duba kuma, hawayen mutanen da aka cuta, babu kuma wanda zai ta'azantar da su! Iko na hannun masu cutar da su, babu kuma wanda zai ta'azantar da su!

2Sai na yi la'akari da cewa waɗanda suka mutu sun fi waɗanda ke da rai morewa, waɗanda har yau suna raye.3Duk da haka, wanda ya fisu dukka morewa shi ne wanda bai riga ya rayu ba, wanda bai riga ya ga ayyukan muguntar da ake yi ba ƙarƙashin rana.
4Daga nan naga cewa kowanne aikata aiki da aikin ƙwarewa ya zama kishin maƙwabcin wa ni. Wannan shi ma turirin hayaƙi ne da yunƙurin kiwon iska.
5Wawa yana naɗe hannuwansa kuma baya aiki, domin wannan abincinsa jikinsa ne.6Amma gwamma riba kaɗan tare da aikin natsuwa da hannuwa biyu cike da aikin ƙoƙarin kiwon iska.
7Daga nan na sake yin tunani game da ƙarin aikin wofi, ƙarin turirin hayaƙi mai ɓacewa a ƙarƙashin rana.8Akwai wani irin mutum da ya ke shi kaɗai. Bai da kowa, ba ɗa ko ɗan'uwa. Babu ƙarshe ga dukkan aikinsa, idanunsa ba su ƙoshi da neman wadata. Yana mamaki, "Domin wa nake wahala ina hana wa kaina jin daɗi?" Wannan ma turirin hayaƙi ne, al'amari marar kyau.
9Mutum biyu za su yi aiki fiye da ɗaya; tare za su sami biya mai kyau game da aikinsu.10Domin idan ɗaya ya fãɗi, ɗayan zai iya ɗaga abokinsa. Duk da haka, baƙinciki na biye da wanda ke shi kaɗai sa'ad da ya fãɗi idan babu wanda zai iya ɗaga shi.11Idan biyu suka kwanta tare, za su iya jin ɗumi, amma ta yaya ɗaya zai ji ɗumi shi kaɗai?
12Za a iya fin ƙarfin mutum ɗaya shi kaɗai, amma biyu za su iya yin tsayayya da hari, igiya uku a murɗe ba za su yi saurin tsinkewa ba.
13Gwamma wani ya zama matashi talaka amma mai wayau da tsohon sarki wawa wanda ya daina sanin yadda ake sauraron kashedi.14Wannan gaskiya ne koda saurayin ya zama sarki daga kurkuku, ko kuma an haife shi talaka a masarautarsa.
15Na kalli kowa wanda ya ke da rai kuma yana yawonsa a ƙarƙashin rana, tare da matashin da ke tasowa ya maye gurbinsa.16Babu ƙarshen dukkan mutanen da suke so suyi biyayya da sabon sarki, amma daga ba ya yawancin su ba zasu sake yabonsa ba. Tabbas wannan al'amari turirin hayaƙi ne da yunƙurin kiwon iska.

5

1Ka kiyaye takawarka sa'ad da ka je gidan Allah. Ka matsa kusa ka saurara fiye da miƙa hadayar wawaye, waɗanda basu fahimci cewa suna yin abin da ba dai-dai ba.

2Kada ka yi saurin magana da bakinka, kada kuma ka yi saurin barin zuciyarka ta fito da wani al'amari a gaban Allah. Allah na sama, amma kai ka na duniya, sai ka bari maganganunka su zama kaɗan.3Idan kana da abubuwa da yawa da za ka yi kuma ka da mu a kai, zai yiwu ka sami miyagun mafarkai. Kana ƙara yawan maganganun da zaka furta, kana ƙara yawan abubuwan shirme da zaka iya faɗa.
4Sa'ad da ka ɗauki alƙawari ga Allah, kada ka yi jinkirin aikatawa, domin Allah ba ya jin daɗin wawaye. Ka yi abin da ka yi alƙawarin za ka yi.5Gwamma kada ka ɗauki alƙawari da ka ɗauki wanda ba ka aiwatar ba.
6Kada ka bar bakinka yasa jikinka ya yi zunubi. Kada ka cewa manzon firist, "Wannan alƙawari kuskure ne." Meyasa za ka ba Allah haushi ta wurin alƙawarin ƙarya, kana tunzura Allah ya rushe aikin hannuwanka?7Gama a cikin yawan mafarkai, kamar a cikin yawan maganganu, akwai turirin hayaƙi marar ma'ana. Sai ka ji tsoron Allah.
8Sa'ad da kaga ana zaluntar matalauci kuma ana karɓe masa hakkinsa da ke dai-dai a cikin lardinka, kada ka yi mamaki kamar cewa babu wanda ya sani, saboda akwai mutane da ke kan mulki waɗanda ke lura da waɗanda ke ƙarƙashinsu, akwai kuma waɗanda suka fisu iko sama da su.9Bugu da ƙari, amfanin ƙasar domin kowa ne, sarki kuma kansa yana ɗaukar amfani daga gonakin.
10Duk wanda ke ƙaunar azurfa ba zai ƙoshi ba da azurfa, duk kuma wanda ke ƙaunar dukiya a koyaushe yana son ƙãri. Wannan, shi ma, turirin hayaƙi ne.11Yadda wadata ke ƙaruwa, haka ma mutanen da ke cin ta. Ina amfanin dukiya ga mai ita baya ga ya yi ta kallon ta da idanunsa?
12Barcin ma'aikaci mai daɗi ne, ko ya ci kaɗan ko da yawa, amma dukiyar mai arziki bata barin shi ya yi barci sosai.
13Akwai muguntar da na gani a ƙarƙashin rana: dukiyar da mai ita ya ɓoye, ita ce sakamakon azabarsa.14Sa'ad da mai arziki ya rasa dukiyarsa ta wurin rashin sa'a, ɗansa, wanda ya haifa, za a bar shi ba komai a hannuwansa.
15Yadda mutum ya zo daga mahaifar mahaifiyarsa, haka ma zai tafi tsirara. Ba zai tafi da ko ɗaya daga cikin aikin ƙarfinsa ba cikin hannunsa.16Wani mugun abin kuma shi ne yadda mutum ya zo, haka ya ke tafiya. To wacce riba ce ke akwai game da shi wanda ya ke aiki domin iska?17A lokacin kwanakinsa ya ci tare da duhu kuma ya ƙuntata kwarai tare da ciwo da fushi.
18Duba, abin da na ga yafi kyau da dacewa kuma shi ne mu ci mu sha mu kuma ji daɗin riba daga dukkan aikinmu, yayin da muke aiki tuƙuru ƙarƙashin rana a lokacin kwanakin rayuwarmu wadda Allah ya ba mu. Gama wannan ne hidimar mutum.
19Duk wanda Allah ya ba arziki da dukiya da ikon karɓar rabonsa ya kuma yi farinciki cikin aikinsa - wannan kyauta ce daga Allah.20Domin ba ya yawan tunawa da kwanakin rayuwarsa, saboda Allah ya sa yana ta hidima da abubuwan da ya ke jin daɗin aiwatarwa.

6

1Akwai wata mugunta da na gani a ƙarƙashin rana, kuma ta yi babban nauyi bisa mutane.2Allah zai iya ba mutum arziki, dukiya, da daraja yadda bai rasa wani abin da ya ke marmari ba domin kansa, amma daga nan Allah bai bashi ikon jin daɗin su ba. Maimako, wani daban ke amfani da abubuwansa. Wannan turirin hayaƙi ne, muguwar azaba.

3Idan mutum ya zama mahaifin 'ya'ya ɗari kuma ya rayu shekaru masu yawa, yadda kwanakin shekarunsa masu yawa ne, amma idan zuciyarsa bata ƙoshi da abu mai kyau ba kuma ba a bizne shi ba, daga nan na ce gwamma jaririn da aka haifa matacce da shi.4Wannan irin jariri ma an haife shi a wofi kuma ya wuce cikin duhu, sunansa kuma ya rage ɓoyayye.
5Ko da ya ke wannan ɗan bai ga rana ba ko kuma ya san wani abu, ya huta koda ya ke wancan mutum bai huta ba.6Koda mutum zai yi rayuwa shekaru dubu biyu amma bai koyi ya ji daɗin abubuwa masu kyau ba, yana tafiya wuri guda kamar kowa da kowa.
7Dukkan aikin mutum domin bakinsa ne, duk da haka ɗanɗanonsa ba ya ƙoshi.8Tabbas, wacce moriya mai wayau ya ke da ita bisa wawa? Wacce moriya matalauci ya ke da ita koda ya san yadda zai aiwatar a gaban sauran mutane?
9Gwamma a ƙoshi da abin da idanu ke gani da ayi marmarin abin da ɗanɗano ke sha'awa barkatai, wanda shi ma turirin hayaƙi ne da yunƙurin kiwon iska.10Duk abin da ya wanzu an riga an ba shi sunansa, kamannin mutum kuma an riga an san shi. Sai ya zama marar amfani ayi saɓani da babban mai hukunta kowa.11Ana ƙãra maganganun da ake faɗa, ana ƙãra yawan aikin wofi, to ina moriyar wannan ga mutum?12Gama wa yasan abin da ke mai yau domin mutum a cikin rayuwarsa a lokacin, lissafin kwanakinsa na wofi ta inda ya ke wucewa kamar inuwa? Wa zai gayawa mutum abin da zai fãru a ƙarƙashin rana bayan da ya mutu?

7

1Suna mai kyau ya fi turare mai tsada, kuma ranar mutuwa ta fi ranar haihuwa.2Gwamma a je gidan makoki da a je gidan biki, domin makoki yana zuwa ga dukkan mutane a ƙarshen rayuwa, to mutanen da ke raye tilas su ɗauki wannan a zuciya.

3‌Ɓ‌acin rai ya fi dariya, domin bayan baƙinciki a fuska sai farinciki a zuciya ya zo.4Zuciyar mai hikima na gidan makoki, amma zuciyar wawaye na gidan biki.
5Gwamma a saurari tsautawar mai hikima da a saurari waƙar wawaye.6Domin kamar ƙarar ƙayoyin da ke ƙonewa a ƙarƙashin tukunya, haka ma dariyar wawaye. Wannan, ma, turirin hayaƙi ne.
7Babu shakka ƙwace na sa mutum mai hikima ya zama wawa, kuma cin hanci na ɓãta zuciya.
8Gwamma ƙarshen al'amari da farkonsa; kuma mutane masu haƙuri a ruhu sun fi mutane masu girman kai a ruhu.9Kada ka yi saurin fushi a ruhunka, domin fushi na zama cikin zukatan wawaye.
10Kada ka ce, "Me ya sa kwanakin dã suka fi waɗannan?" Domin ba saboda hikima ka yi wannan tambaya ba.
11Hikima, kamar gãdo, mai kyau ce, waɗanda ke ganin rana na moriyar ta.12Domin hikima na bada kariya kamar yadda kuɗi ke bada kariya, amma darajar ilimi shi ne hikima na ba da rai ga duk wanda ke da ita.
13Yi la'akari da ayyukan Allah: Wa zai miƙar da duk abin da ya tanƙwarar?
14Sa'ad da lokutta ke da kyau, ka zauna da murna cikin kyaun nan, amma sa'ad da lokutta suka ɓaci, yi la'akari da wannan: Allah ya bar dukkan su su wanzu gefe da gefe. Domin wannan dalili, babu wanda zai san wani abu da ke zuwa bayansa.
15Naga abubuwa masu yawa a cikin kwanakina marasa ma'ana. Akwai mutane masu adalci da ke hallaka duk da adalcinsu, akwai kuma mutane masu mugunta da ke yin tsawon rai duk da muguntarsu.16Kada ka zama mai adalcin kai, mai hikima a idanunka. Meyasa za ka hallakar da kanka?
17Kada ka zama mai yawan mugunta ko wawanci. Meyasa za ka mutu kafin lokacinka?18Yana da kyau ka riƙe wannan hikimar, kuma kada ka saki adalci. Domin talikin da ke da tsoron Allah zai kiyaye dukkan farillansa.
19Hikima na da ƙarfi sosai a cikin mutum mai wayau, fiye da shugabanni goma a cikin birni.20Babu mutum mai adalci a duniya da ke aikata nagarta kuma bai taɓa yin zunubi ba.
21Kada ka saurari dukkan maganar da aka furta, saboda kana iya jin bawanka na la'antar ka.22Haka nan kuma, ka sani da kanka cewa a cikin zuciyarka kana yawan la'antar wasu.
23Dukkan waɗannan na tabbatar ta wurin hikima, na ce, "Zan yi wayau," amma ya fi abin da zan iya zama.24Hikima na nesa kuma da zurfi sosai. Wa zai same ta?25Na juya zuciyata in koya kuma in jaraba kuma in biɗi hikima da bayanan zahiri, in kuma fahimci cewa mugunta sakarya ce kuma wawanci hauka ne.
26Na gano cewa abin da yafi mutuwa ɗaci shi ne ko wacce mata wadda zuciyarta ke cike da tarkuna da tãrurruka, wadda kuma hannuwanta sarƙoƙi ne. Duk wanda ya gamshi Allah zai kucce daga gare ta, amma zata ɗauke mai zunubi.
27"Yi la'akari da abin da na gãno," cewar Malamin. "Ina ta tãra gãnowa bisa gãnowa domin in samo bayanin zahiri.28Wannan ne har yanzu nake nema, amma ban same shi ba. A cikin dubu na sami namiji ɗaya mai adalci, amma a cikin dukkan waɗannan ban sami mace ɗaya ba.
29Wannan ne kawai na gãno: Cewa Allah ya halicci 'yan'adam dai-dai, amma suka tafi neman wahalhalu da yawa."

8

1Wane ne mutum mai hikima? Wanda ya san abin da al'amuran rayuwa ke nufi? Hikima a cikin mutum nasa fuskarsa ta haskaka, kuma taurin fuskarsa ya canza.

2Ina ba ka shawara da ka yi biyayya da dokar sarki saboda rantsuwar Allah na kiyaye shi.3Kada ka yi garajen barin gabansa, kada kuma ka goyi bayan abin da ba dai-dai ba, domin sarki na yin abin da ya so.4Maganar sarki ke mulki, to wane ne zai ce masa, "Me ka ke yi?"
5Duk wanda ke kiyaye dokar sarki yana kaucewa cutarwa. Zuciyar mutum mai hikima takan gane dai-dai lokacin daya dace a aiwatar da abu.6Domin ga kowanne al'amari akwai yadda ya dace da lokacin da ya dace, saboda matsalolin mutum manya ne.7Babu wanda ya san abin da ke zuwa a gaba. Wane ne zai gaya mashi abin da ke zuwa?
8Babu wanda ke mulki bisa lumfashinsa yadda zai tsaida lumfashin, babu kuma wanda ke da iko bisa ranar mutuwarsa. Babu wanda ake sallama daga bataliyar sojoji a lokacin yaƙi, kuma mugunta ba ta kuɓutar da waɗanda ke bayinta.9Na gãno dukkan wannan; Na sanya zuciyata ga kowanne irin aiki da ake yi a ƙarƙashin rana. Akwai lokacin da wani taliki ke muzgunawa wani talikin domin cutarwar wannan taliki.
10Sai naga ana bizne miyagu a sarari. An ɗauke su daga wuri mai tsarki aka kuma bizne su mutane kuma suka yabe su a cikin birni inda suka aiwatar da ayyukan muguntarsu. Wannan ma wofi ne.11Sa'ad da zartar da hukunci gãba da aikin mugunta ba a aiwatar dashi ba da sauri, yana jarabtar zukatan 'yan'adam da su aikata mugunta.
12Koda ya ke mai zunubi yana aikata mugunta sau ɗari kuma duk da haka ya yi tsawon rai, duk da haka na sani cewa zai fi kyau ga waɗanda ke girmama Allah, ga waɗanda ke tsayawa a gabansa suna kuma nuna masa girma.13Amma ba zai zama da lafiya ba game da mugun mutum; rayuwarsa ba za tayi tsawo ba. Kwanakinsa kamar inuwa ce mai wucewa saboda ba ya darjanta Allah.
14Akwai wani turirin hayaƙi marar amfani - wani abun kuma da ake yi a duniya. Abubuwa na faruwa da mutane masu adalci yadda suke faruwa da mutane masu mugunta, kuma abubuwa na faruwa da mutane masu mugunta yadda suke faruwa da mutane masu adalci. Na ce shi ma wannan turirin hayaƙi ne marar amfani.15Sai na shawarta murna, saboda mutum ba ya da wani abu a ƙarƙashin rana fiye da ya ci ya sha ya kuma yi murna. Murna ce za ta yi masa rakiya cikin aikin ƙarfinsa domin dukkan kwanakin rayuwarsa waɗanda Allah ya bashi a ƙarƙashin rana.
16Sa'ad da na bada zuciyata in san hikima in kuma fahimci aikin da ake yi a duniya, aikin da yawanci ake yi ba bu barci domin idanu koda rana ko da dare,17daga nan na yi la'akari da dukkan ayyukan Allah, kuma da cewar mutum ba zai iya fahimtar aikin da ake yi ba a ƙarƙashin rana. Ko ta yaya mutum ya yi aiki tuƙuru domin ya sami amsoshi, ba zai same su ba. Koda ya ke mutum mai hikima zai bada gaskiyar cewa ya sani, lallai bai sani ba.

9

1Gama na yi tunani game da dukkan wannan a raina in sami fahimta game da mai adalci da mutane masu hikima da ayyukansu. Dukkan su suna cikin hannuwan Allah. Babu wanda ya sani wataƙila ƙauna ko ƙiyayya zata zo ga wani.

2Kowa na fuskantar ƙaddara ɗaya. ‌Ƙaddara ɗaya ce ke jiran mutane masu adalci da miyagu, masu kyau, masu tsarki da marasa tsarki, da mai miƙa hadayu da wanda ba ya hadaya. Kamar yadda masu kyau suke mutuwa, haka kuma mai zunubi. Kamar yadda mai rantsuwa zai mutu, haka kuma mutumin da ke jin tsoro ya ɗauki wa'adi.
3Akwai muguwar ƙaddara ga kowanne abu da ake yi a ƙarƙashin rana, al'amari ɗaya ne ke faruwa da su dukka. Zukatan 'yan'adam na cike da mugunta, kuma hauka na cikin zukatansu yayin da suke raye. Sai bayan wannan su tafi wurin matattu.
4Domin duk wanda ya ke tare da dukkan masu rai, akwai bege, kamar yadda kare mai rai yafi mataccen zaki.5Domin mutane masu rai sun san cewa za su mutu, amma matattu basu san komai ba. Basu da wani sakamako kuma saboda an manta da tunawa da su.
6‌Ƙaunarsu, ƙiyayyarsu, da kishinsu, sun ɓace da daɗewa. Ba za su sake samun wuri ba kuma cikin kowanne abu da ake yi ƙarƙashin rana.7Ka yi tafiyar ka, ka ci gurasarka da farinciki, ka kuma sha ruwan inabinka da zuciya mai murna, domin Allah ya tabbatar da shagalin ayyuka masu kyau.8Bari suturunka koyaushe su zama farare kanka kuma shafaffe da mai.
9Ka zauna da murna tare da matar daka ke ƙauna dukkan kwanakin rayuwarka marasa amfani, kwanakin da Allah ya baka a ƙarƙashin rana a zamanin kwanakinka marasa amfani. Wannan ne sakamakonka a rayuwa domin aikinka a ƙarƙashin rana.10Duk abin da hannunka ya samu ya yi, ka aikata shi da dukkan ƙarfinka, saboda babu aiki ko bayani ko ilimi ko hikima a Lahira, in da kake tafiya.
11Na ga wasu abubuwa na burgewa a ƙarƙashin rana: Tseren ba na mutane masu sauri ba ne. Yaƙin ba na mutane masu ƙarfi ba ne. Gurasa ba ta mutane masu hikima ba ce. Arziki ba na mutane masu fahimta ba ne. Tagomashi ba na mutane masu ilimi ba ne. Maimako, lokaci da sarari ke shafar su dukka.12Tabbas, babu wanda ya san sa'ad da lokacinsa zai zo. Kamar yadda ake kama kifi cikin tãru mai haɗari, ko ake kama tsuntsaye cikin tarko, a na yi wa 'ya'yan 'yan'adam tarko da miyagun lokutta da ke faɗowa bisan su farat ɗaya.
13Na kuma ga hikima a ƙarƙashin rana ta hanyar da na kalle ta babba a gare ni.14Akwai wani ƙaramin birni mai mutane ƙalilan a ciki, wani babban sarki kuma ya zo gãba da shi ya yi masa sansani ya kuma gina manyan ramukan sansani gãba da shi.15To a cikin birnin an sami matalauci, mutum mai wayau, wanda ta wurin hikimarsa ya ceci birnin. Duk da haka daga baya, babu wanda ya tuna da wannan mutum matalauci.
16Sai na kammala, "Gwamma hikima da ƙarfi, amma aka rena hikimar mutumin nan matalauci, maganganunsa kuma ba a ji su ba."
17Maganganun mutane masu hikima da aka furta a hankali an fi jin su fiye da kururuwar duk wani sarki cikin wawaye.18Hikima tafi makaman yaƙi, amma mai zunubi ɗaya zai lalata abubuwan nagarta masu yawa.

10

1Kamar yadda mataccen ƙuda yana sa turare ya yi wãri, haka wawanci ƙarami zai iya shan ƙarfin hikima da daraja.2Zuciyar mai hikima na gusawa dãma, amma zuciyar wawa na gusawa hagu.3Sa'ad da wawa ke tafiya akan hanya, tunaninsa kasasshe ne, yana tabbatar wa da kowa cewa shi wawa ne.

4Idan hankalin mai mulki ya tashi gãba da kai, kada ka bar aikinka. Natsuwa na iya kwantar da fushi mai girma.
5Akwai muguntar da na gani a ƙarƙashin rana, wani irin kuskure da ke zuwa daga shugaba:6A na ba wawaye matsayin shugabanci, yayin da mutane na ƙwarai ake basu ƙasƙantattun matsayi.7Na ga bayi na hawa dawakai, kuma mutane na ƙwarai na tafiya kamar bayi bisa ƙasa.
8Duk wanda ya ke ginin rami zai iya faɗawa a ciki, duk kuma sa'ad da wani ya fasa katanga, maciji na iya sarar sa.9Duk wanda ke yankan duwatsu za su iya ji masa rauni, kuma mutumin da ke sarar katako yana cikin haɗari dashi.
10Idan bãkin ƙarfe ya dushe, kuma mutum bai wãsa shi ba, daga nan tilas ya yi amfani da ƙarfi sosai, amma hikima na bayar da mafita domin nasara.11Idan maciji ya yi sara kafin a yi masa makari, daga nan babu wani amfani domin mai makarin.
12Maganganun bãkin mutum mai hikima na cike da alheri, amma leɓunan wawa na lanƙwame shi.
13Sa'ad da maganganu suka fãra kwararowa daga bãkin wawa, wawanci na fitowa, a ƙarshe kuma bãkinsa na kwararowa da haukan mugunta.14Wawa yana ruɓanɓanya maganganu, amma babu wanda ya san abin da ke zuwa. Wane ne ya san abin da ke zuwa bayansa?
15Aikin wawaye na gajiyar da su, yadda ba zasu san ma hanyar zuwa gari ba.
16Kaiton ki, ƙasa, idan sarkin ki ƙaramin yaro ne, idan kuma shugabanninki suka fara shagali da safe!17Amma mai albarka ce ke, ƙasa, idan sarkin ki ɗa ne na ƙwarai, idan kuma shugabannin ki na cin abinci lokacin da ya dãce, domin ƙarfi, kuma ba domin buguwa ba!
18Saboda ƙyuya rufin gida na ruftawa, kuma saboda hannaye marasa aiki gida na zuba.19Mutane na shirya abinci domin dariya, ruwan inabi yana kawo jin daɗi ga rayuwa, kuɗi kuma na cika buƙata domin komai.
20Kada ka la'anci sarki, ko a tunaninka ma, kada kuma ka la'anci mutane masu arziki a cikin ƙuryar ɗakinka. Domin tsuntsuwar sararin sama na iya ɗaukar maganganunka; duk abin da ke da fukafukai zai iya baza al'amarin.

11

1Ka aika da gurasar ka bisa ruwaye, domin za ka same ta kuma bayan kwanaki masu yawa.2Ka raba da bakwai, har ma da mutane takwas, domin baka san bala'o'in da ke zuwa bisa duniya ba.3Idan giza-gizai suka cika da ruwa, suna juye kansu bisa duniya, idan kuma itace ya fãɗi zuwa kudu ko zuwa arewa, inda itacen ya fãɗi, nan zai tsaya.

4Duk wanda ke kallon iska ba zai yi shuka ba, duk kuma wanda ke kallon giza-gizai ba zai yi girbi ba.5Kamar yadda ba ka san tafarkin iska ba, ko yadda ƙasusuwan jariri ke girma a cikin mahaifar mai ciki, haka nan kuma ba za ka gãne aikin Allah ba, wanda ya halicci komai.
6Da safe ka shuka irinka; har yamma, ka yi aiki da hannuwanka bisa ga buƙata, domin ba ka san wanda zai wadata ba, ko safe ko yamma, ko wannan ko wancan, ko dukkan su biyu zasu yi kyau.7Gaskiya haske yana da daɗi, kuma abu mai gamsarwa ne ga idanu su kalli rana.8Idan wani ya rayu shekaru masu yawa, bari ya yi murna cikin dukkan su, amma bari ya yi tunani game da kwanakin duhu masu zuwa, domin zasu zama da yawa. Kowanne abu da ke zuwa turirin hayaƙi ne mai wucewa.
9Ka yi farinciki, saurayi, a cikin ƙuruciyarka, bari kuma zuciyarka ta yi farinciki cikin kwanakin ƙuruciyarka. Ka runtumi sha'awoyi masu kyau na zuciyarka, da duk abin da ke cikin ganin idanunka. Duk da haka, ka sani cewa Allah zai kawo ka cikin hukunci domin dukkan waɗannan abubuwa.10Ka kori fushi daga zuciyarka, ka kuma yi watsi da duk wani zafi a cikin jikinka, saboda ƙuruciya da ƙarfinta turirin hayaƙi ne.

12

1Ka kuma tuna da mahaliccinka a kwanakin ƙuruciyarka, kafin kwanaki masu wuya su zo, kafin kuma shekarun su iso waɗanda za ka ce, "Ba ni da marmari a cikin su,"2ka yi wannan kafin hasken rana da na wata da na taurari su duhunta, baƙaƙen giza-gizai kuma su dawo bayan ruwan sama.

3Wannan lokacin ne sa'ad da masu tsaron făda zasu yi rawar jiki, kuma a tanƙwarar da mazaje masu ƙarfi, mataye masu niƙa kuma su tsaya saboda basu da yawa, waɗanda kuma su ke dubawa ta taga sun dena gani sosai.
4Wannan lokacin ne sa'ad da aka kulle ƙofofi cikin tituna, ƙarar niƙa kuma ta tsaya, sa'ad da mazaje ke firgicewa ta muryar tsuntsu, kuma muryoyin waƙoƙin 'yanmata suka dushe.
5Wannan lokacin ne sa'ad da mazaje suka zama masu jin tsoron tuddai da haɗarorin da ke bisa hanya, sa'ad da kuma itacen almon ke yaɗo, sa'ad da kuma fãri suke jan kansu tare, sa'ad da kuma marmari na ɗabi'a ya karye. Daga nan mutum ya tafi madawwamin gidansa masu makoki kuma su gangara bisa tituna.
6Ka tuna da mahaliccinka kafin a datse igiyar azurfa, ko a kwankwatse kwanon zinariya, ko tulu ya farfashe a rafi, ko gargaren murɗo ruwa ya fashe a rijiya,7kafin turɓaya ta koma ƙasa in da ta fito, kuma ruhu ya koma ga Allah wanda ya bayar dashi.
8"A tsakiyar turirin hayaƙi," a faɗar Malamin, "komai turirin hayaƙi ne mai bajewa."9Malamin mai hikima ne kuma ya koyar da mutane ilimi. Ya yi bincike kuma ya yi juyayi kuma yasa misalai masu yawa a jere.
10Malamin ya nemi ya rubuta kuma yana amfani da zahirin, cikakkun maganganun gaskiya.11Maganganun mutane masu hikima kamar zugazugai suke. Kamar ƙusoshin da ake bugawa da zurfi haka nan maganganun gwanayen da suka ƙware wajen tattara misalansu, wanda makiyayi ɗaya ya koyar.
12‌Ɗana, ka zama a faɗake game da wani abin kuma: yin litattafai da yawa, wanda bai da ƙarshe da yawan bincike yana kawo gajiyarwa ga jiki.
13‌Ƙarshen al'amari bayan an ji komai, shi ne tilas ka ji tsoron Allah ka kuma kiyaye dokokinsa, domin wannan gabaɗaya shi ne aikin ɗan'adam.14Domin Allah zai kawo kowanne aiki zuwa hukunci, tare da duk wani ɓoyayyen abu, ko mai kyau ne ko mugu.

Wa‌ƙar suleman

1

1Waƙar Waƙoƙi ta Suleman ce. Matar tana magana da kanta ne2Oh, da ma zai sumbace ni da sumbatar bakinsa, matar kuma tana yin magana da mutumin, gama ƙaunarka ta fi ruwan inabi.3Manka na shafawa yana da ƙanshi mai daɗi, sunanka na kama da turare mai kwararowa, zuwa ga 'yammatan da kake ƙauna.4Ka ɗauke ni mu yi gudu tare. Matar tana yin magana da kanta. Sarkin ya kawo ni cikin ɗakunansa. Matar tana yin magana da mutumin. Muna yin murna; muna farinciki game da kai; bari muyi bukin ƙaunarka; ta fi ruwan inabi. Dai-dai ne waɗansu mata su yi sha'awar ka. Matar tana magana da waɗansu matan.

5Ni baƙa ce amma kyakkawa, ku 'yammatan Yerusalem - baƙaƙe kamar rumfunan Kedar, kyawawa kamar labulen Suleman.6Kada ku ƙyale ni saboda ni baƙa ce, saboda rana ta gasa ni. 'Ya'yan mahaifiyata suna fushi da ni; sun maida ni mai tsaron garka, amma ban iya tsare tawa garkar ba. Matar tana magana da mutumin.
7Ka gaya mani, wanda raina ya ke ƙauna, ina kake kiwon garkenka? Ina kake sa garkenka su huta da tsakiyar rana? Me yasa zan zama kamar wadda take kai da kawo wa a kusa da garkunan abokanka?
8Mutumin yana magana da matar. Idan baki sani ba, wadda ta fi sauran mataye kyau, ki bi sawun garkena, ki kiwaci 'yan awakinki kusa da rumfar makiyaya.
9Ƙaunatacciyata, ina kwatanta ki da goɗiya a cikin dawakin karusar Fir'auna.10Kumatunki kyawawa ne masu ban sha'awa, wuyanki da sarƙoƙin lu'uluai.11Zamu yi maki kayan ado na zinariya da azurfa. Matar tana magana da kanta.
12Sa'ad da sarkin ya ke kwance a kan shimfiɗarsa, yana jin daɗin ƙanshin turaren.13Ƙaunataccena yana kama da jakar mur sa'ad da ya kwanta a tsakanin nonnana.14Ƙaunataccena kamar fure ya ke a garkar En Gedi. Mutumin yana magana da matar.
15Ki saurara, kina da kyau, ƙaunatacciyata; ki saurara, kina da kyau; idanunki suna sheki.
16Matar tana magana da mutumin. Ka saurara, kana da kyau, ƙaunataccena. Shuke-shuke masu taushi sune gadonmu.17Kalankuwar gidanmu ta al'ul ce, raftarmu ta fir ce.

2

1Ni furen kallo ce ta Sharon, fure na bakin kwari. Mutumin yana magana da matar.2Kamar fure a cikin ƙayoyi, haka ƙaunatacciyata take a cikin 'yammata.

3Matar tana magana da kanta. Kamar itacen tsada a cikin itatuwan jeji, haka ƙaunataccena ya ke a cikin samari. Na kan zauna a cikin inuwarsa da jin daɗi mai yawa, ina jin daɗin 'ya'yan itatuwansa.4Ya kawo ni gida mai ruwan inabi, tutarsa a kaina ƙauna ce. Matar tana magana da mutumin.
5Ka farfaɗo dani da waina ka wartsakar da ni da 'ya'yan tsada, gama ƙaunata ta kasa. Matar tana magana da kanta.6Na yi matashin kai da hannunsa na hagu, hannunsa na dama kuma ya rungume ni.
7Matar tana magana da sauran mata. Ku 'yammatan Yerusalem, ina so ku yi rantsuwa, da bareyi da batsiyoyi na jeji, ba zaku farka da ƙauna ba sai ta gamsu.
8Matar tana magana da kanta. Akwai motsin ƙaunataccena! Saurara, gashi yana zuwa, yana sassarfa a kan duwatsu, yana tsalle a kan tuddai.9Ƙaunataccena yana kama da barewa ko ɗan kishimi; duba, ga shi a tsaye bayan katangarmu, yana leƙowa ta taga, yana kallo cikin assabari.
10Ƙaunataccena yayi magana da ni yace, "Tashi, ƙaunatacciyata; kyakkyawata, ki zo mu fita.11Duba, hunturu ya wuce, ruwa ya ɗauke kuma ya tafi.
12Furanni sun fito a kan ƙasa; lokacin aske itatuwa da kukan tsuntsaye ya zo, kuma an ji motsin kurciyoyi a ƙasarmu.13'Ya'yan ɓaure sun nuna, inabi kuma yana sheƙi; sun bayar da ƙanshinsu. Tashi, ƙaunatacciyata, kyakkyawata, mu fita.
14Kurciyata a kogon dutse, a cikin wani asirtaccen kogon dutse, bari in ga fuskarki. Bari in ji muryarki, gama muryarki tana da zaƙi, kuma fuskarki abin ƙauna ce." Matar tana magana da mutumin.
15Ka kamo mana diloli, 'yan dilolin da suke ɓata gonaki, gama gonarmu tana sheƙi.
16Ƙaunataccena nawa ne, ni kuma tasa ce; yana kiwo a cikin furanni na annashuwa. Matar tana magana da mutumin.17Ka tafi, ƙaunataccena, kafin iskar asubahi ta buso inuwoyi kuma su ɓace. Ka zama kamar barewa ko kamar 'yar batsiya a kan dutse mara laushi.

3

1Ina jiran sa da dare a bisa gadona wato shi wanda raina ya ke ƙauna, na neme shi, amma ban same shi ba.2Na ce da kaina, "Zan tashi in shiga cikin birni, a kan hanyoyi da wuraren shaƙatawa; zan neme shi wato shi wanda raina ya ke ƙauna." Na neme shi amma ban same shi ba.

3Masu gãdi suka same ni sa'ad da suke aikinsu na zagayawa a cikin birni. Na tambaye su, "Ko kun gan shi wanda raina ya ke ƙauna?4Na wuce su kenan sai na sami shi wanda raina ya ke ƙauna. Sai na riƙe shi na hana shi ya tafi sai da na kawo shi gidan su mahaifiyata, a cikin ɗakin wadda ta ɗauki cikina.
5Matar tana magana da waɗansu matayen. Ina so ku yi rantsuwa, ku 'yammatan Yerusalem, da bareyi da batsiyoyin jeji, ba zaku tashi ku nuna ƙauna ba sai ta yarda.
6Matar tana magana da kanta. Mene ne wancan mai tahowa daga jeji kamar umudin hayaƙi, tare da kayan ƙanshi masu ƙăwa, tare da dukkan hodar da 'yan kasuwa ke sayarwa?7Duba, gadon Suleman ne; kewaye da mayaƙa sittin, sojoji sittin na Isra'ila.
8Dukkan su gwanayen mãshi ne ƙwararru a wajen yaƙi. Kowanne mutum yana da mashinsa a gefe, shiryayye saboda ta'adanci cikin dare.9Sarki Suleman yayi wa kansa kujera ta alfarma da itacen Lebanon.
10An yi ginshiƙanta da azurfa; bayanta kuma an yi shi da zinariya, da wurin zama na ƙyallen shunayya. Daga ciki 'yammatan Yerusalem sun yi mata ado na ƙauna. Matar tana magana da matayen Yerusalem.11Ku je waje, ku 'yammatan Sihiyona, ku hangi Sarki Suleman, yana ɗauke da rawani wanda mahaifiyarsa ta naɗa masa a ranar aurensa, a cikin ranar da ya ke farinciki a zuciyarsa.

4

1Oh, ke kyakkyawa ce, ƙaunatacciyata; kina da kyau. Idanunki suna kama da kurciya a cikin lulluɓinki. Gashinki kamar garken awaki suna gangarowa daga Dutsen Giliyad.

2Haƙoranki kamar kazganyar da a ka yi wa sabon aski, tana fitowa daga wurin yi mata wanka. Kowanne da na kusa dashi, ba wani a cikin su da ya faɗi.
3Leɓunanki kamar jan zare; bakinki abin ƙauna ne. Kumatunki suna sheƙi da santsi a cikin lulluɓinki.
4Wuyanki yana kama da hasumiyar Dauda da a ka gina da jerin duwatsu, wadda a ka rataye garkuwoyi dubu a kanta, dukkan garkuwoyin sojoji ne.5Nonnanki kamar bareyi biyu, tagwayen bareyi, suna kiwo cikin furanni.
6Sai asuba ta yi inuwa ta ɓace, zan je dutsen mur da tudun kayan ƙanshi.7Ke kyakkyawa ce a kowanne sashi, ƙaunatacciyata babu inda kike da cikas.
8Mu tafi tare daga Lebanon, amaryata. Mu tafi tare daga Lebanon; ki tawo daga ƙololuwar Dutsen Amana, daga ƙololuwar Dutsen Senir da Harmon daga kogon zakuna, daga kogon dutsen damisoshi.
9'Yar'uwata, kin sace zuciyata, amaryata, kin sace zuciyata, da kika dube ni sau ɗaya kawai, da abin wuyanki guda ɗaya kaɗai.
10'Yar'uwata, ƙaunarki tana da kyau, amaryata! Ƙaunarki ta fi ruwan inabi, ƙanshin turarenki yafi kowanne kayan ƙanshi.11Amaryata, leɓunanki suna ɗigo da zuma; zuma da madara suna ƙarƙashi harshenki; ƙanshin tufafinki yana kama da ƙanshin Lebanon.
12'Yar'uwata, amaryata tana kama da lambun da a ka kulle, kullallen lambu, maɓulɓula wadda a ka hatimce.13Rassanki suna kama da rukunin itatuwa masu bada 'ya'ya na musamman, da itacen lalle da nardi,14Nardi da saffron da man ƙanshi da kalamus da kirfi da kayan yaji iri-iri da aloyis da dukkan kayan ƙanshi mafi kyau.
15Ke maɓulɓular lambu ce, rijiya mai sabon ruwa, ƙorama mai gangarowa daga Lebanon. Matar tana magana da mutumin.16Ki taso iskar arewa; ki zo iskar kudu; ki busa a kan lambuna domin kayan yaji suba da ƙanshinsu. Dămă ƙaunataccena zai zo cikin lambunsa yaci zaɓaɓɓun 'ya'yan itatuwa.

5

1Na shigo cikin lambuna, 'yar'uwata, amaryata; na tattaro mur da kayan ƙanshina. Ina shan zumana da saƙarsa; na sha ruwan inabina da madarata. Abokai suna yin magana da mutumin da matar, Ku ci, abokai, ku sha ku bugu da ƙauna. Matar tana magana da kanta.

2Ina barci, amma zuciyata ba barci take yi ba. Ƙaunataccena yana ƙwanƙwasa ƙofa yana cewa, "Ki buɗe mani, 'yar'uwata, abin ƙaunata, kurciyata, ke tawa marar cikas, gama kaina ya jiƙa da raɓa, sumata kuma da danshin dare."
3Na tuɓe rigata; in sake maida ita ne? Na wanke ƙafafuna; in sake sawa su yi dauɗa?"4Ƙaunataccena yasa hannunsa a kan marfin ƙofa, kuma zuciyata tana wajensa.
5Na tashi in buɗe ƙofa saboda ƙaunataccena; hannuwana nashe-nashe da mur, yatsuna da danshin mur, a kan mariƙin ƙofa.
6Na buɗe ƙofar saboda ƙaunataccena, amma ƙaunataccena ya juya ya tafi. Zuciyata ta nutsa sa'ad da yayi magana. Na neme shi, amma ban same shi ba; na kira shi amma bai amsa mani ba.
7Masu gadi suka tarar dani sa'ad da suke aikinsu na zagaya birni. Suka buge ni suka ji mani ciwo; masu gadin da ke kan ganuwa suka ɗauke gyalena daga gare ni. Matar tana magana da matan birni.
8Ina so ku yi rantsuwa, ku 'yammatan Yerusalem, idan kuka haɗu da ƙaunataccena - Me zaku sanar da shi? - ina ciwon ƙauna. Matan birni suna magana da matar.
9Da me ƙaunataccenki ya fi wani ƙaunataccen, ke mafi kyau a cikin mata? Me yasa ƙaunataccenki ya fi wani ƙaunataccen, da kika ce mu ɗauki alkawari kamar wannan?
10Matar ta na magana da matan birni. Ƙaunataccena wankan tarwaɗa ne yana sheƙi, fitacce ne shi a cikin dubu.11Kansa zinariya ce mai tsaftar gaske; sumarsa nannaɗe take baƙa wulik kamar hankaka.
12Idanunsa kamar kurciyoyi a bakin ƙoramar ruwa, sun yi wanka da madara, sun tsaya kamar lu'ulu'ai.
13Kumatunsa suna kama da kwamin kayan ƙanshi, yana bada ƙanshi mai gamsarwa. Leɓunansa abin kallo ne, nashe-nashe da ruwan mur.
14Hannayensa kamar zinariyar da a ka yi wa dajiya da lu'ulu'ai; kwankwasonsa kamar hauren giwar da a ka dalaye da duwatsun saffayar.
15Ƙafafunsa kamar ginshiƙan da a ka yi da zinariya tsantsa, fitowarsa kamar Lebanon, zaɓabbe kamar itacen sidar.
16Bakinsa yana da zaƙin gaske; shi cikakkaken abin ƙauna ne. Wannan shi ne Ƙaunataccena, kuma wannan shi ne abokina, 'yammatan Yerusalem.

6

1Ina ƙaunataccenki ya tafi, ke mafi kyau a cikin mata? Wacce hanya ƙaunataccenki ya bi, domin mu neme shi tare da ke? Matar tana magana da kanta.

2Ƙaunataccena ya gangara zuwa lambunsa, wurin kwamin kayan ƙanshi, domin yayi kiwo a lambu kuma ya ɗebo furen kallo.3Ni ta ƙaunataccena ce, ƙaunataccena kuma nawa ne; yana kiwo a cikin furanni da farinciki. Mutumin yana magana da matar.
4Kina da kyau kamar Tirzah, abin ƙaunata, ƙauna kamar Yerusalem, mai ban sha'awa da gamsarwa kamar tutocin nasara na sojoji.
5Ki juyar da idanunki daga wajena, gama suna ɗaukar mani hankali. Gashinki yana kama da garken awakin da ke gangarowa daga magangarin Giliyad.
6Haƙoranki suna kama da tumakin da a ka yi wa aski suna fitowa daga wurin da a ka yi masu wanka. Kowacce da 'ya'uwarta ba wadda take baƙinciki.7Kumatunki sumul-sumul a cikin lulluɓinki. Mutumin yana magana da kansa.
8Akwai sarauniyoyi sittin, ƙwaraƙwarai tamanin, 'yammata kuwa sun fi a ƙirga.9Kurciyata, marar aibi, ita kaɗai ce; ita kaɗai ce ɗiya a wurin mahaifiyarta; tana da tagomashi a wurin matar da ta haife ta. 'Yammata sun gan ta sun kira ta mai albarka; sarauniyoyi da ƙwaraƙwarai ma sun ganta sun yabe ta: Ga abin da sarauniyoyin da ƙwaraƙwaran suka ce,
10"Wace ce wannan da ta fito kamar tauraron asubahi, kyakkyawa kamar wata, mai haske kamar rana, mai ban sha'awa kamar sojoji da tutocinsu?" Mutumin yana magana da kansa.
11Na gangara cikin rukunin itatuwa domin in ga waɗanda suke yin girma a cikin kwari, in gani ko inabi sun yi lingaɓi, in gani ko itatuwan rumman suna yin fure.12Na yi murna sosai na ji kamar ina cikin karusar sarki. Ƙawayen matar suna magana da ita.
13Ki dawo, ki dawo, ke sahihiyar mata; ki dawo, ki dawo domin mu kalle ki. Matar tana magana da ƙawayenta. Me yasa kuke kallon sahihiyar mata, kamar rawa a tsakanin sojoji biyu?

7

1Ƙafafunki sun yi kyau sosai a cikin takalmanki, ɗiyar sarki! Tsarin cinyoyinki sun yi kama da lu'ulu'ai, aikin ƙwararre a sassaƙa.

2Cibiyarki tana kama da bangaji; dãma kada ta rasa gaurayayyen ruwan inabi. Cikinki yana kama da tarin alkama kewaye da furen kallo.
3Nonnanki biyu suna kama da tagwayen bareyi.4Wuyanki yana kama da hasumiyar hauren giwa, idanunki tafki ne cikin Heshbon a ƙofar Bat Rabbim. Hancinki kamar hasumiya ce cikin Lebanon wadda ta ke fuskantar Damaskus.
5Kanki yana bisanki kamar Karmel; gashin kanki shunayya ne mai duhu-duhu. Kitsonki ya ɗauke hankalin sarki.6Ke kyakkyawa ce kuma abin ƙauna, ƙaunatacciyata, tare da jin daɗi!
7Kina da tsawo kamar itacen dabino, nonnanki suna kama da kurshen 'ya'yan itace.8Na ce, "Ina so in hau wannan itacen dabino; zan kama rassansa." D‌ãmã nonnanki su zama kamar kurasan zaitun, damã ƙanshin hancinki ya zama kamar 'ya'yan tsada.
9Dãmã kitsonki ya zama kamar ruwan inabi mafi kyau, ya malala a hankali domin ƙaunataccena, ya gangara leɓunan waɗanda suke yin barci.
10Matar tana magana da mutumin. Ni ta ƙaunataccena ce, yana marmari na.11Kazo, ƙaunataccena, bari mu je ƙauye; bari mu kwana a can cikin ƙauyuka.
12Bari mu tashi da sassafe mu tafi gonaki; bari mu gani ko inabi sun yi lingaɓi, ko furanninsu sun buɗe, mu gani ko itatuwan rumman sun yi fure. A can zan baka ƙaunata.
13Tsiretsire suna ba da ƙanshinsu; akwai dukkan zaɓaɓɓun 'ya'yan itatuwa a ƙofar wurin da mu ke tsaye, da sabo da tsoho, waɗanda na ajiye saboda kai, ƙaunataccena.

8

1Dãmã kai ɗan'uwana ne, wanda a ka yi renon sa da nonnan mahaifiyata. Daga nan duk inda na ganka a waje, sai na sumbace ka, kuma ba wanda zai rena ni.

2Zan yi maka jagora in kawo ka gidan mahaifiyata - ita wadda ta koyar da ni. Dã na baka ruwan inabi mai ƙanshi ka sha da wani abin sha daga itatuwan rumman. Matar tana magana da kanta.3Na tãda kai da hannun hagunsa hannun damansa kuma yana rungume da ni.
4Matar tana magana da waɗansu mata. Ina so ku yi rantsuwa, ku 'yammatan Yerusalem, ba zaku shiga tsakani ku dame mu ba sai mun gama ƙaunarmu.
5Matan Yerusalem suna magana. Wace ce wannan da ke fitowa daga cikin jeji, tana jingina da ƙaunataccenta? Matar tana magana da mutumin. Na tashe ka a ƙarƙashin itacen tsada; a can mahaifiyarka ta ɗauki cikin ka; a can ta haife ka, ita ta haife ka.
6Ki sani kamar hatimi a zuciyarki, kamar hatimi a hannunki, gama ƙauna tana da ƙarfi kamar mutuwa. Ƙarfin kishi kamar Lahira; harshensa yana ƙonewa; harshen wuta ne mai ci, harshen wutar ya fi kowacce wuta zafi.
7Ruwa mai yawa ba zai iya kashe ƙauna ba, ko rigyawa ma ba zata iya share ta ba. Koda mutum zai bayar da dukkan abin da ya mallaka a gidansa saboda ƙauna, za a rena abin da ya bayar.
8'Yan'uwan matar suna magana da junansu. Muna da 'yar'uwa ƙarama, nonnanta ko fitowa basu yi ba. Me zamu yi wa 'yar'uwarmu sa'ad da za a ba da ita aure?
9Inda ita ganuwa ce, da sai mu gina hasumiyar azurfa a kanta. Inda ita ƙofa ce, da sai mu yi mata ado da katakon al'ul.
10Matar tana magana da kanta. Ni ganuwa ce, amma nonnana yanzu suna kama da hasumiya ƙayatacciya; Ina kama da mai kawo salama a idanunsa. Matar tana magana da kanta.
11Suleman yana da gona a Ba'al Hamon. Ya sa waɗansu su kula da ita. Kowannen su zai kawo masa kuɗi azurfa dubu daga 'ya'yan itatuwanta.12Gonata, tawa ce sosai, tana gabana; Suleman, kuɗi azurfa dubu naka ne, azurfa ɗari biyu kuma na masu kula da 'ya'yan itatuwan gonar ne.
13Mutumin yana magana da matar. Ke da kike zaune a cikin lambuna, abokaina suna sauraren muryarki; bari nima in ji muryarki.
14Matar tana magana da mutumin. Ka yi hanzari ƙaunataccena, ka zama kamar barewa ko batsiya a kan duwatsu inda kayan ƙanshi suke.

Littafin ishaya

1

1Wahayin Ishaya ɗan Amoz, wanda ya gani game da Yahuda da Yerusalem, a kwanakin Uziya, da Yotam, da Ahaz, da Hezekiya, sarakunan Yahuda.

2Ku saurara, ku sammai, ke duniya, ki kasa kunne; gama Yahweh ya yi magana: "Na yi renon 'ya'ya na girmar da su, amma sun tayar mani.3Sã ya san mai shi, jaki kuma ya san inda ubangijinsa ke ciyar da shi, amma Isra'ila ba ta sanni ba, Isra'ila ba ta fahimta ba,"
4Kaito! Al'umma, masu zunubi, mutanen da zunubi ya danne su ƙasa, zuriyar masu aikata mugunta, 'ya'ya masu aikin lalata! Sun yi watsi da Yahweh, sun rena Mai Tsarki na Isra'ila, sun ware kansu daga gare shi.
5Donme a ke ta dukan ku har yanzu? Me ya sa kuke ta tayarwa akai akai? Dukkan kai yana ciwo, dukkan zuciya kuma ta yi rauni.6Tun daga tafin sawu har zuwa kai ba inda ba ciwo; sai ciwuka ne da ƙoƙƙojewa, da sababbin raunuka; ba'a rufe su ba, ba'a tsabtace su ba, ba'a naɗe su ba, ko kuma a sa masu mai.
7Ƙasarku ta zama kufai; an ƙone biranenku; filayenku - a idonku, bãƙi na hallaka su - an yi watsi da su, an yi kaca-kaca da su ta hannun bãƙi.8‌Ɗiyar Sihiyona an barta kamar 'yar bukka a garkar inabi, kamar 'yar rumfa a lambun kukumba, kamar birnin da aka yiwa sansani.
9Idan dã Yahweh mai runduna bai bar mana ragowa ƙalilan ba, da mun zama Sodom, mun kuma zama kamar Gomora.
10Ku ji maganar Yahweh, ku shugabannin Sodom; ku saurari shari'ar Allahnmu, ku mutanen Gomora:11"Mene ne yawan hadayunku a gare ni?" in ji Yahweh. Ina da isassun baye-bayen ƙonawa na raguna, da kitsen manyan dabbobi; da jinin bijimai, da raguna, ko awaki waɗanda bana jin daɗi.
12Lokacin da kuka zo gare ni wa ya buƙaci wannan daga gare ku, don ku tattaka harabaina?13Kada ku ƙara kawo baye-bayenku marasa ma'ana, na ƙi ƙonennan turare, ba zan yarda da bukukuwanku na sabon wata ba da na Asabaci - Ba zan yarda da wannan taron ba.
14Na ƙi bukukuwanku na sababbin watanni da keɓaɓɓun ranaku; sun zama nawaya a gare ni; Na gaji da jurewa da su.15Don haka lokacin da kuka buɗe hannuwanku kuna addu'a na ɓoye fuskata daga gare ku; koda ya ke kun yi addu'o'i da yawa, Ba zan ji ba; hannuwanku sun cika da jini.
16Yi wanka ku tsabtace kanku; ku cire mugayen ayyukanku daga fuskata, ku dena mugunta;17Ku koyi yin abin kirki; ku nemi adalci, ku dena danniya, ku yi adalci ga marayu, ku kare gwauraye."
18Sai ku zo mu tattauna tare," in ji Yahweh; koda zunubanku sun yi kamar jangarura za su yi fari kamar ƙanƙara; koda sun yi jawur kamar jini, za su zama kamar ulun auduga.
19In kun yarda kuka yi biyayya za ku ci mafi kyau daga cikin ƙasar,20Amma idan kuka ƙi kuka yi tayarwa, to takobi zata haɗiye ku," domin bakin yahweh ne ya furta haka.
21Yadda birni mai aminci ya zama karuwa! Ita da dã take cike da adalci, amma yanzu ta cika da masu kisan kai.22Zinariyarki ta zama marar tsarki, ruwan inabinki ya gauraye da ruwa.
23Sarakunanki masu tayarwa ne da kuma abokan ɓarayi; kowa na ƙaunar cin hanci, yana gudu domin ya ci haram. Ba su kare marayu ba, ba su kuma yiwa gwauruwa shari'ar adalci ba a lokacin da ta zo gare su.
24Saboda haka sai ku ji abin da Yahweh mai runduna ya faɗi, Mai Iko na Isra'ila: "Kaiton su! Zan ɗauki fansa a kan maƙiyana, in kuma nuna ramuwata a kan magabtana;25Zan juya hannuna gãba daku, zan tace ku kamar yadda ake tace ƙarfe in kawar da ƙazantarku dukka.
26Zan maido da mahukuntanku kamar farko, mashawartanku kuma kamar na can farko; bayan wannan za a kira ku birnin adalci, gari kuma mai aminci."
27Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma ta wurin adalci.28Masu tayarwa da masu zunubi za a murje su tare, waɗanda suka yi watsi da Yahweh kuma za a kawar dasu.
29Don za ku ji kunyar wurare masu tsarki na itatuwan rimi da kuke marmari, za a kuma kunyata ta wurin lambun da kuka zaɓa.30Gama za ku zama kamar itacen rimi wanda ya kaɗe, kamar kuma lambun da ba ruwa.
31Ƙaƙƙarfan mutum zai zama kamar ƙeƙasesshe, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duk za a ƙone su tare, ba kuma mai kashe su."

2

1Abubuwan da Ishaya ɗan Amoz ya ji a wahayi game da Yahuda da Yerusalem.2Zai zamana a kwanaki na ƙarshe za a kafa tsaunin gidan Yahweh a can ƙololuwar tsaunuka, za a tada shi bisa dukkan tuddai, dukkan al'ummai kuma za su kwararo gare shi.

3Mutane da yawa za su zo su ce, "Ku zo mu je kan tsaunin Yahweh, zuwa gidan Allah na Yakubu, don ya koya mana waɗansu hanyoyinsa, mu kuma yi tafiya cikin tafarkunsa." Gama daga Sihiyona shari'a za ta fito maganar Yahweh kuma daga Yerusalem.
4Zai hukunta tsakanin al'ummai ya kuma yanke shawara ga mutane da yawa; za su mayar da takkubansu garemani, mãsunsu kuma su maida su almakashin yanke rassa; al'umma ba za ta sake tayar da takobi gãba da al'umma ba, ko kuma su sake horar da kansu don yaƙi.
5Gidan Yakubu, ku zo, sai muyi tafiya cikin hasken Yahweh.6Gama ka yi watsi da mutanenka, gidan Yakubu, saboda sun cika da al'adu daga gabas suna kuma karatun sihiri kamar Filistiyawa, suna kuma shan hannuwa da 'ya'yan băƙi.
7Ƙasarsu ta cika da zinariya da azurfa, kuma wadatarsu ba ta da iyaka; ƙasarsu kuma ta cika da dawakai, karusarsu ba ta da iyaka.8Hakannan kuma ƙasarsu ta cika da gumaka; suna bautawa aikin hannun mutum na hannuwansu, abubuwan da yatsunsu suka yi.
9Za a sunkuyar da mutane ƙasa, mutum zai faɗi ƙasa; don haka kada ka tada su tsaye.10Ku je wurare masu duwatsu ku ɓuya a ƙarƙashin ƙasa don ku ɓoye wa hukuncin Yahweh daga kuma ɗaukakar ikonsa.11Za a ƙasƙantar da kallon girman kan mutum, fahariyar mutune kuma za a ƙasƙantar da ita, Yahweh kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana.
12Gama akwai ranar Yahweh mai runduna găba da duk masu girman kai da masu kumbura, găba kuma da duk marasa kunya -13kuma da dukkan itatuwan Labanon waɗanda suka yi girma sosai da kuma găba da dukkan itatuwan rimi na Bashan.
14Waccan ranar ta Yahweh mai runduna za ta yi găba da dukkan dogayen tsaunuka, da tuddai da suka yi tsayi,15gãba kuma da doguwar hasumiya, gãba kuma da kowacce katanga marar gwami,16gãba kuma da dukkan jiragen ruwa na Tarshish, gãba kuma da dukkan kyawawan abubuwan tafiya a ruwa.
17Za a saukar da girman kan mutum ƙasa, taƙamar mutum kuma zata fãɗi; Yahweh kaɗai za a ɗaukaka a waccan rana.18Gumakan za su shuɗe ɗungum.19Mutane za su shiga kogonnin duwatsu da kuma ramummuka a ƙasa, domin ɓuya daga razanar Yahweh, da kuma darajar ɗaukakarsa, a lokacin daya tashi domin ya razana duniya.
20A ranar nan mutane za su watsar da gumakansu na azurfa da zinariya da suka yiwa kansu domin su bauta masu - za su watsar da su a gidan mujiya da jemagu.21Mutane za su shiga cikin matsin duwatsu da kuma cikin tsagar fasassun duwatsu domin su ɓuya daga hasalar Yahweh, kuma daga darajar martabarsa, a lokacin da ya tashi domin ya razana duniya.22Ku dena dogara ga mutum, wanda numfashinsa a ƙofofin hancinsa ya ke, domin kuwa wacce daraja ya ke da ita?

3

1Duba, Ubangiji Yahweh mai runduna, yana gab da ya kawar da Yerusalem da kuma goyon bayansa daga Yahuda, da samar da gurasa da kuma ruwa,2mutum mai iko da mayaƙi, da mai hukunci, da annabi da masu dubarsu, da dattijo;3jagoran hamsin, da mazaunan birnin da ake girmamawa, da mashawarci, da shahararen masassaƙi, da gwanayen masu sihirinsu.

4Zan sa matasa kawai su zama shugabanninsu, matashi kuma zai mulke su.5Za a tsanantawa mutane, za su tsananta wa junansu da kuma maƙwabtansu; yaro zai wulaƙanta dattijo, ƙasƙantattu kuma su ƙalubalanci masu martaba.
6Mutum zai sami ɗan'uwansa a gidan mahaifinsa ya ce, 'Kana da riga; ka yi mulkin mu, kuma bari wannan kangon ya kasance a hannuwanka,'7Ranar zai yi ihu ya ce, 'Ba zan iya zama mai warkarwa ba; ba ni da gurasa ko sutura. Ba za ku mai da ni shugaban mutane ba,'"
8Gama Yerusalem ta yi tuntuɓe, Yahuda kuma ta faɗi, saboda maganganunsu da ayyukansu na gãba da Yahweh, suna rena idanunsa na ɗaukaka9Suka duba shaidunsu a fuskarsu suna gãba da su; suna maganar zunubansu kamar Sodom; ba su ɓoye shi ba. Kaiton su! Gama sun kammalawa kansu bala'i.
10Faɗawa mai adalci cewa komai zai yi dai-dai, domin za su ci 'ya'yan ayyukansu.11Kaiton mugu! abin zai yi masa muni sosai, gama za'a sãka masa abin da ya aikata.12Mutanena 'ya'yansu su ne masu wahalshe su, mata ne kuma ke mulkinsu. Mutanena masu yi maku jagora suna ɓatar da ku suna kuma rikitar da hanyar tafarkinku.
13Yahweh na tsaye domin ya faɗi laifin mutanensa; yana tsaye domin ya zarge su.14Yahweh zai zo da hukunci gãba da dattawan mutanensa da kuma shugabanninsu: "Kun lallatar da garkar inabi; ganimar matalauci na gidajenku.15Donme kuke ƙuje mutanena, kuke kuma musgunawa matalauta?" Wannan furcin Ubangiji Yahweh mairunduna ne.
16Yahweh yace saboda 'yan matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya suna ɗaga wuya sama, suna kuma jujjuya idanunsu, suna rangwaɗa a lokacin da suke tafiya kayan adon ƙafafunsu na ƙãra.17Saboda haka Ubangiji zai saukar masu da ciwon ƙuraje a bisa kawunan 'yan matan Sihiyona, Yahweh kuma zai sa su yi saiƙo.
18A wannan ranar Ubangiji zai cire masu kyawawan kayan adonsu na ƙafa, da maɗaurin kansu, da kayan adonsu masu siffofin wata,19da 'yankunne, da abin hannu, da kayan lulluɓi;20'yankwalaye, da sarkar ƙafa, da ɗamara; da akwatunan turare, da layunsu na neman sa'a.
21Zai cire zobba da kayan adon hanci;22da suturun bukukuwa, da alkyabbobi, da mayanai, da jakkunan hannu;23da madubai na hannu, da linin mai kyau, da ƙyallayen kai, da kuma zannuwa.
24A maimakon ƙanshin turare za su yi wari; a maimakon sarƙa kuma igiya; a maimakon gyararriyar suma kuma saiƙo, a maimakon sutura mai ƙawa kuma kayan makoki; tsaga maimakon kyau.25Mazajenku za su fãɗi da takobi, jarumawanku kuma za su fãɗi a wurin yaƙi.26Ƙofofin Yerusalem za su yi makoki da baƙinciki; za ta kuma zauna a ƙasa a kaɗaice.

4

1A wannan rana mata bakwai za su riƙe namiji ɗaya su ce, "Mă ciyar da kanmu, mu yiwa kanmu suturar da za mu sa. Amma ka yarda a kira mu da sunanka domin a kawar mana da kunya."2A wannan ranar rassan Yahweh za suyi kyau da kuma ɗaukaka, 'ya'yan itatuwan ƙasar kuma za su yi zaƙi, da kuma jin daɗi ga waɗanda suka ragu a Isra'ila.

3Zai kasance a wannan ranar da wanda ya ragu a Sihiyona da kuma wanda ya ragu a Yerusalem za a kira shi mai tsarki, da kuma duk wanda aka rubuta sunansa a matsayin mazaunin Yerusalem.4Wannan zai faru a lokacin da Ubangiji zai share tsaurin idon 'yan matan Sihiyona, ya kuma goge jinin da ya manne daga tsakiyar Yerusalem, ta wurin ruhun hukunci da kuma ruhun harshen wuta.
5Sa'an nan dukkan sassan Tsaunin Sihiyona da kuma kan wuraren taruwarta, Yahweh zai yi girgije da hayaƙi da rana, da kuma hasken harshen wuta da dare; zai zama inuwa a kan dukkan ɗaukaka.6Za ta bada inuwa da rana daga zafi, da kuma mafaka da kuma maɓoya daga hadari da ruwan sama.

5

1Sai in raira waƙa ga ƙaunataccena, waƙar ƙaunataccena game da garkar inabinsa. Wadda nake ƙauna sosai yana da garka a tudu mai dausayi.2Ya gyara ta, ya cire duwatsu, ya kuma shuke ta da irin inabi mai matuƙar daraja. Ya gina hasumiya a tsakiyar gonar, ya kuma kafa wurin matse ruwan inabi. ya jira ta bada 'ya'ya amma sai 'ya'yan inabin jeji kawai ta yi.

3To yanzu, mazauna Yerusalem da mutanen Yahuda, ku yi hukunci tsakanina da garkar inabita.4Me kuma zan ƙara yi wa garkar inabita, da ban taba yi mata ba? Lokacin da na dube ta ta bada 'ya'ya me yasa ta bada 'ya'yan inabin jeji?
5Yanzu zan fada maku abin da zan yi da garkata: Zan cire shingen, zan mayar da ita makiyaya, zan rushe garunta, za a kuma tattaketa ƙasa6Zan watsar da ita, ba zan yi mata noma ko kaftu ba. A maimakon haka ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su tsiro a cikin ta. Zan kuma umarci giza-gizai kada su yi ruwa a kanta.
7Domin garkar inabin Yahweh mai runduna ita ce gidan Isra'ila, mutanen Yahuda kuma dashensa ne da ya ke jin daɗi; ya jiraci adalci, a maimakon haka sai kisa; a maimakon adalci kuma, sai ihun neman taimako.
8Kaiton su masu yawo gida gida, waɗanda ke haɗa wurare daga wannan wuri zuwa wancan wuri, har sai ba ɗakunan da suka ragu sai kai kaɗai za a bari a cikin ƙasar!9Yahweh mai runduna ya faɗa mani, gidaje da yawa za su zama kufai, har ma da manyan gidajen nan masu ban sha'awa, ba mazauna.10Domin kadada goma ta garkar inabi za ta bada garwa ɗaya ne kacal, sannan mudun iri zai bada ɗangongoni ne kawai.
11Kaiton masu tashi da asuba domin neman ƙaƙƙarfan ruwan inabi, waɗanda ba su kwantawa da wuri har sai ruwan inabi ya bugar da su.12Suna shagali da sarewa da garaya da tambari da algaita da ruwan inabi, amma ba su fahimci aikin Yahweh ba Ba su kuma yi la'akari da aikin hannuwansa ba.
13Saboda haka mutanena suka tafi bautar talala saboda rashin fahimta; Shugabaninsu masu daraja suka zauna a cikin yunwa, talakawansu kuma ba su da wani abin sha.14Domin haka Lahira ta maida marmarinta babba ta kuma buɗe bakinta sosai; da masanansu da mutanensu da shugabanninsu da masu duba na cikinsu da kuma waɗanda ke murna a cikin su, sun ɗunguma Lahira.
15Za a tilastawa mutum ya sunkuya ƙasa, Za'a ƙasƙantar da mutum; idanun masu taƙama za su wulaƙanta.16Yahweh mai runduna zai ɗaukaka cikin adalcinsa, Allah Mai Tsarki nan zai nuna kansa da tsarki cikin adalcinsa.17Bayan wannan sai tumakai su yi kiwo kamar a makiyayarsu, a kuma cikin kangaye, 'yan raguna za su yi kiwo kamar bãƙi.
18Kaiton masu cire laifofinsu da sarƙoƙi marasa amfani da masu birgima cikin zunubi kamar an ɗaure su da igiya.19Kaiton masu cewa, "Bari Allah ya yi sauri, bari ya hanzarta ya yi aikinsa, domin mu ga ya faru; kuma bari shirye-shiryen Mai Tsarki na Isra'ila su zo, domin mu sansu."
20Kaiton masu kiran mugunta nagarta, nagarta kuma mugunta; waɗanda suka mai da duhu haske, haske kuma duhu; suka kuma mai da ɗaci zaƙi, zaki kuma ɗaci!21Kaiton masu hikima a fuskarsu, masu daraja kuma a cikin fahimtarsu!
22Kaiton shahararrun shan ruwan inabi, da waɗanda s ka shahara a wajen gauraya ruwan inabi mai ƙarfi;23Waɗanda suka ƙyale mugu saboda a biya su, suka kuma zalunci marar laifi a kan hakinsa!
24Saboda haka kamar yadda harshen wuta ke lanƙwame kututture, kamar kuma yadda busasshiyar ciyawa ke shiga harshen wuta haka saiwarsu za ta mutu, kyansu kuma ya gushe kamar ƙura. Wannan zai faru saboda sun ƙi shari'un Yahweh mai runduna, saboda kuma sun rena maganar Mai Tsarki na Isra'ila.
25Saboda haka fushin Yahweh yana kan mutanensa. Ya miƙa hannusa gãba da su ya kuma hore su. tsaunuka sun razana, gawawwakinsu sun zama kamar sharar da a ka zubar a bakin hanyonyi. A cikin duk waɗannan abubuwa fushinsa bai sauka ba; a maimakon haka hannunsa har yanzu yana miƙe.
26Zai ɗaga alama ta tuta don al'ummai masu nisa zai kuma yi fĩto ga waɗanda ke ƙarshen duniya. Ku duba, za su zo a guje a kan lokaci kuma.
27Ba yagewa ko tuntuɓe a cikinsu; babu masu rurrumi ko bacci. Ba su kuma kwance ɗammararsu ba, ko kuma shimfiɗar takalmansu da ta yage.28Kibawunsu na da tsini kuma dukkan bakkunansu a tanƙware; kofatan dawakansu kuma kamar curin dutse, gargaren karusarsu kuma kamar hadari ya ke.
29Gurnaninsu kuma kamar na zãki; za su yi ruri kamar matasan zãki. Za su yi ruri su fizge abin da suka farauto su kuma ja shi su tafi, ba kuma wanda zai kuɓutar da su.30A wannan ranar za su yi ruri kamar yadda tekuna ke ruri. In wani ya dudduba ƙasar zai ga duhu da shan wuya; ko ma da haske za a mai da shi duhu ta wurin giza-gizai.

6

1A cikin shekarar da sarki Uziya ya mutu, na ga Ubangiji zaune a kan kursiyi; yana da tsayi da kuma martaba, gezar tufarsa kuma ta cika haikalin.2A sama da shi kuma da serafim; kowannen su yana da fuka-fukai shida; kowannen su yana rufe fuska da guda biyu, ya kuma rufe ƙafafu da guda biyu, yana kuma shawagi da guda biyu.

3Suna kiran juna suna cewa, "Mai Tsarki, Mai Tsarki, Mai Tsarki," shi ne Yahweh mai runduna! Dukkan duniya ta cika da ɗaukakarsa."
4Harsashen ginin ƙofofinsa sun girgiza a lokacin da suka tada murya, sai kuma hayaƙi ya cika gidan.5Sa'an nan na ce "kaitona! Gama na hallaka domin ni mutum ne dake da leɓuna marasa tsarki, ina kuma rayuwa a cikin mutane marasa tsarkin leɓuna, saboda idanuna sun ga Sarki, Yahweh, Yahweh mai runduna!"
6Daga nan sai ɗaya daga cikin serafim ɗin yawo shawagi wurina; yana da garwashi jawur a hannunsa, wanda ya ɗauko daga bagadi.7Sai ya taɓa bakina da shi ya kuma ce, "Duba wannan ya taɓa leɓunanka; an kawar da laifofinka, an kuma gafarta zunubanka."
8Na ji muryar Ubangiji tana cewa, "Wa zan aika; wa kuma zai tafi dominmu?" Daga nan sai na ce, "Ga ni; ka aike ni."9Ya ce ka je ka faɗawa mutanen nan, za ku ji amma ba za ku gane ba; za ku gani amma ba za ku sani ba.'
10Mai da zuciyarsu ta zama marar tunani, kunnuwansu kuma su kurmance, idanunsu kuma su makance. A maimakon haka za su iya gani da idanunsu, su ji da kunnuwansu, su kuma fahimta da zuciyarsu, kuma daga nan su juyo su kuma warke."
11Sai na ce Ubangiji har tsawon wanne lokaci? '"Ya amsa "Har sai birane sun zama kangaye ba mazauna a ciki, gidaje kuma sun zama ba mutane, ƙasar kuma ta zama yasasshiya,12Har sai Yahweh ya kora mutanen waje, kaɗaicin ƙasar kuma ya haɓaka.
13Koda kashi ɗaya cikin goma na mutanen suka ragu a cikinsa, duk da haka za a ƙara hallaka shi; zai zama kamar ranar da aka datse itacen rimi wanda gungumensa ya ragu, iri mai tsarki na cikin kututture."

7

1A kwanakin Ahaz ɗan Yotam ɗan Uziya, sarkin Yahuda, Rezin na Aram da Feka ɗan Remaliya da sarkin Isra'ila, suka je Yerusalem domin su yaƙe ta, amma ba su iya yin nasara da ita ba.2Sai aka sanar da gidan Dauda cewa Aram ya haɗa kai da Ifraim. Sai ya tsorata, haka ma zuciyar mutanensa, kamar yadda itatuwan jeji ke kaɗawa a cikin iska.

3Sai Yahweh yace da Ishaya, "Ka tafi tare da ɗanka Shiya-Yashub ku sadu da Ahaz a ƙarshen kwararon babban wurin da aka datse ruwa, a kan hanya zuwa Filin masu wanki da guga.4Ka ce da shi, 'Ka lura, ka tsaya a natse, kada ka ji tsoro ko ka razana saboda waɗannan 'yan guma-gumai na wuta, ta wurin zafin fushin Rezin da Aram, da Feka ɗan Remaliya.
5Aram, Ifraim da ɗan Remaliya sun ƙulla mugun abu găba da kai; sun ce,6"Bari mu kai wa Yahuda hari mu firgita ta, mu kuma fasa cikinta mu naɗa sarkinmu a can, wato ɗan Tabil."
7Ubangiji Yahweh yace, "Ba zai faru ba; ba zai faru ba,8saboda shugabar Aram ita ce Damaskus, shugabar Damaskus kuma ita ce Rezin. Cikin shekaru sittin da biyar, za'a watsa Ifraim kuma ba za su zama al'umma ɗaya ba9Shugabar Ifraim ita ce Samariya, shugaban Samariya kuma shi ne ɗan Remaliya. Idan ba ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya ba, tabbas ba za ku zama da kariya ba.""'
10Sai Ubangiji ya sake yin magana da Ahaz,11"Ka roƙi alama daga Yahweh Allahnka; ka yi roƙonta ko a cikin zurfafa ko a can sama."12Amma Ahaz yace "ba zan yi tambaya, ko kuma in gwada Yahweh ba."
13Domin haka Ishaya ya amsa, "Ku saurara, gidan Dauda. Ya ku mutane ashe bai isheku ba ku gwada haƙurin jama'a? Dole ne kuma ku gwada haƙurin Allahna?14Saboda haka Ubangiji da kansa zai ba ku alama, duba budurwa za ta yi juna biyu za ta haifi ɗa, za a kira sunansa Imanuwel.15Zai ci fãra da ruwan zuma a lokacin da ya ƙi mugunta ya kuma zaɓi nagarta.
16Gama kafin yaron ya san ƙin mugunta da zaɓar nagarta, ƙasar sarakunan nan guda biyu da kuka ji tsoronsu za ta zama kufai.17Yahweh zai sauko maku da wata rana a kan mutanenku da gidan mahaifanku ranar da ba a taɓa ganin ta ba tun da Ifraim ya bar Yahuda - zai aiko maku da sarkin Asiriya."
18A wannan lokacin Yahweh zai yi kira na tashi daga ƙoramu masu nisa na Masar, kuma da na zuma daga ƙasar Asiriya.19Duk za su zo su zauna a dukkan kwazazzabai, a cikin kogonnin duwatsu, a kan dukkan ƙayayuwa, da a kan dukkan makiyaya.
20A wannan lokacin Ubangiji zai yi aski da rezar da aka yi haya daga hayin Kogin Yuferitis - sarkin Asiriya - da kai da gashin ƙafafu; za a kuma share gemu.21A wannan rana mutum zai yi kiwon 'yar karsana da tumaki guda biyu,22Kuma saboda yalwar madarar da za su bayar, zai ci cuku, ga duk waɗanda suka ragu a ƙasar za su ci cuku da ruwan zuma.
23A wannan lokacin, a inda a kwai dubu na inabi da ya kai azurfa dubu, a wurin ba za a ga komai ba sai sarƙarƙiya da ƙayayuwa.24Mutane za su fita farauta da bãka, saboda dukkan ƙasar za ta cika da ƙaya da sarƙaƙiya.25Za su tsaya nesa da dukkan tuddan da aka nome da fartanya, domin tsoron sarƙaƙiya da ƙayayuwa; amma zai zama wurin da dabbobi da tumaki za su yi kiwo.

8

1Yahweh yace mani, "Ka ɗauki babban allo ka yi rubutu a kansa, 'Maha-Shalal-Hash-Baz.'2Zan kira amintattun shaidu su tabbatar mani, Yuriya Firist, da Zakariya ɗan Yebirekiya."

3Na je wurin annabiya, ta kuwa yi juna biyu ta haifi ɗa. Sai Yahweh yace mani, "Ka kira sunansa 'Maha-Shalal-Hash-Baz.'4Gama kafin yaron ya san yin kuka har ya furta, 'Babana da Mamata,' sarkin Asiriya zai kwashe dukiyar Damaskus da ganimar Samariya."
5Sai Yahweh ya sake yi mani magana,6"Saboda waɗannan mutanen sunƙi tausassun ruwayen Shilowa, amma suna murna kan Rezin da ɗan Remaliya,7don haka Ubangiji ya kusa kawo ruwayen Kogi a kansu, masu ƙarfi da yawa, sarkin Asiriya da dukkan ɗaukakarsa. Za ya hau kan dukkan magudanansa ya yi ambaliya kan iyakokinsa.
8Rafin zai shafe har zuwa cikin Yahuda, ambaliyar zata ratsa, har sai ta kai wuyanka. Miƙawar fikafikansa zai cika iya faɗin ƙasarka, Imanuwel."
9Ku mutanen za a daddatsa ku gunduwa-gunduwa. Ku saurara, dukkan ku manisantan ƙasashe: ku yi ɗammara domin yaƙi za a kuwa daddatse ku, ku yi shiri za a kuwa gutsuttsuraku.10Ku yi shiri, amma bãza ku iya aiwatarwa ba; ku ba da umarni, ba za a kiyaye ba, gama Allah yana tare da mu.
11Yahweh ya yi magana da ni, da hannunsa mai ƙarfi a kaina, ya dokace ni kada in yi tafiya cikin tafarkin mutanen nan.12Kada ku kira maƙida akan kowanne abin da mutanen nan suke kira maƙida, kada ku ji tsoron abin da suke tsoro, kada ku firgita kuma.13Amma Yahweh mai runduna za ku girmama a matsayin maitsarki; shi ne wanda dole za ku ji tsoro, shi ne dole zai zama abin razanar ku.
14Zai zama wuri maitsarki; amma zai zama dutse abin bugu da pã abin sa tuntuɓe ga dukan gidajen Isra'ila, zai zama tarko da azargiya ga mutanen Yerusalem.15Mutane da yawa za su yi tuntuɓe a kansa su faɗi su karye, su zama azargiya kuma su kamu.
16Ka ɗaure shaida ta, ka hatimce umarni na musamman, ka kuma bada su ga alma'jiraina.17Zan jira Yahweh, wanda ya ɓoye fuskarsa daga gidan Yakubu; Zan jira shi.18Duba, Ni da 'ya'yan da Yahweh ya bani domin alamu ne da al'ajibai cikin Isra'ila daga Yahweh mai runduna, wanda ya ke zaune akan Tsaunin Sihiyona.
19Za su ce maku, "Ku tuntuɓi mãsu duba da bokaye" waɗanda suke kashe murya suna surkulle. Shin ko mutane ba za su tuntuɓi Allahnsu ba? za su tuntuɓi matattu a madadin masu rai?20Ga shari'a da kuma shaida! idan ba su faɗi waɗannan abubuwan ba, saboda ba bu hasken wayewar gari a garesu.
21Za su ratsa ta cikin ƙasa da babbar damuwa da yunwa. Idan suna jin yunwa, za su yi fushi su la'anta sarkinsu da Allahnsu, yayin da suka ɗaga fuskokinsu sama.22Za su du bi duniya kuma za su ga wahala, duhu, da azabtarwa. Za a koresu zuwa cikin ƙasar duhu.

9

1Amma za a kawar da baƙin duhun daga wurin ta wadda take cikin azaba a dã. A kwanakin da ya ƙasƙantar da ƙasar Zebulun da ƙasar Naftali, amma cikin kwanaki na ƙarshe zai ɗaukakata, ta hanyar teku, ƙetaren Yodan, Galili ta al'ummai.2Mutanen da suka yi tafiya cikin duhu sun ga babban haske; waɗanda suka zauna cikin ƙasa ta inuwar mutuwa, haske ya haskaka bisansu.

3Ka riɓanya al'umma; ka ƙara farincikin su. Suna murna gaban ka kamar murna a lokacin girbi, kamar yadda mutane suke murna sa'ad da suke raba ganima.
4Gama karkiyar kayansa, katakon dake gicciye da kafaɗarsa, sandar mai azabta masa, ka rafke su kamar a ranar Midiyan.5Gama dukkan takalman mayaƙa cikin hayaniyar yaƙi da tufafi mirginannu cikin jini za a ƙone su, su zama abin rura wuta.
6Gama a gare mu an haifi yaro, a gare mu an bada ɗa; mulki kuma zai kasance a kafaɗarsa; za a kira sunansa Al'ajibi Maishawara, Allah maigirma, Uba Madawwami, Sarkin Salama.7Ƙaruwar mulkinsa da salama bata da iyaka, ya yin da ya ke mulki kan kursiyin Dauda, da bisa mulkinsa, a kafa shi a kuma tabbatar dashi cikin gaskiya da adalci daga wannan lokaci har abada kuma. Himmar Yahweh Mairunduna zai yi wannan.
8Sai Ubangiji ya aika da magana gãba da Yakubu, sai ta faɗo kan Isra'ila.9Dukkan mutane za su sani, har Ifraim da mazaunan Samariya, waɗanda suke magana cikin girmankai da taurin zuciya,10"Tubala sun faɗi, amma za mu sake gini da sassaƙaƙƙun duwatsu; an sare durumi ƙasa, amma zamu sa itatuwan sidas amadadinsu."
11Domin haka Yahweh zai tayar masa da Rezin, abokin gabarsa, zai harzuƙa maƙiyansa,12Suriyawa daga gabas, da kuma Filistiyawa daga yamma. Da baki buɗe za su cinye Isra'ila. A cikin waɗannan duka, fushinsa bai juya ba; maimakon haka, hannunsa har yanzu a miƙe ya ke.
13Duk da haka mutane ba za su juya wajen shi wanda ya buge su ba, ba kuwa za su nemi Yahweh mai runduna ba.14Domin haka Yahweh zai datse ma Isra'ila kai da wutsiya, reshen dabino da gazarinsa, cikin rana ɗaya.15Shugaba da mutum maidaraja su ne kai; da annabi mai koyar da ƙarya shi ne wutsiya.
16Waɗanda ke shugabantar jama'ar nan sun karkataddasu, waɗanda suke binsu kuma an haɗiye su.17Domin wannan Ubangiji ba za ya yi murna da majiya karfinsu ba ba kuma zai tausayawa marayunsu da gwaurayensu ba, domin kowannensu marasa allahntaka ne da masu aikata mugunta, kowanne baki kuma yana faɗin wauta. Cikin waɗannan duka fushinsa ba zai juya ba; maimakon haka, hannunsa har yanzu a miƙe ya ke.
18Mugunta tana ƙuna kamar wuta; tana cin sarƙaƙƙiya da ƙayayuwa; tana ƙone ƙungurmin daji, wanda ke tashi cikin tuƙuƙin hayaƙi.19Ta wurin hasalar Yahweh mairunduna ƙasa ta ƙone, mutane kuma sun zama kamar abin rura wuta. Ba mutumin daya bar ɗan'uwansa.
20Za su fizge abinci a hannun dama duk da haka za su ji yunwa, za su ci abinci a hannun hagu duk da haka ba za su ƙoshi ba. Kowanne zai ci naman dantsen hannunsa.21Manasse zai lanƙwame Ifraim, Ifraim kuma Manasse, tare kuma za su kaima Yahuda farmaki. Cikin waɗannan duka, fushinsa yana nan, maimakon haka, har yanzu hannunsa a miƙe ya ke.

10

1Kaitonsu waɗanda ke zartar da hukuncin zalunci suke rubuta umarnan rashin gaskiya.2Suna hana wa mabuƙata adalci, mutanena suna yi masu ƙwace su hana masu haƙƙinsu, gwamraye sun zama ganimarsu, sun maida marayu ganimarsu!

3Me za kuyi a ranar hukunci lokacin da hallakarwa ke zuwa daga nesa? wurin wa za ku gudu domin neman taimako, kuma ina za ku bar dukiyarku?4Ba abin daya rage, za ku laɓe ƙarƙashin 'yan sarƙa, ko ku faɗi tsakanin kisassu. Cikin dukkan waɗannan abubuwa, fushinsa ba zai sauka ba; maimakon haka, har yanzu hannunsa a miƙe ya ke.
5Kaiton Asriyen, kulkin fushina, sandar hannunka a bin harzuƙata ne!6Na aike shi gãba da al'umma mai girmankai, gãba da mutane masu ɗauke da ambaliyar fushina. Na umarce shi ya ɗauki ɓãtattu, ya kwashi ganima, ya tattake su kamar laka cikin tituna.
7Amma ba haka ya ke nufi ba, bai kuma yi tunanin haka ba. Amma shi a cikin zuciyarsa ne ya kawar da al'umma masu yawa.8Gama ya ce, "Shugabannina ba sarakuna ba ne dukkansu?9Kalno ba kamar Karkemish ba ce? Hamat ba kamar Arfad ba ce? Samariya ba kamar Damaskus ba ce?
10Kamar yadda hannuna ya yi nasara da mulkokin tsafi, wanda ƙerarrun gumakansu sun fi na Yerusalem da Samariya,11kamar yadda na yi da Samariya da gumakanta marasa amfani, ba zan yi irin wannan kuma ga Yerusalem da gumakanta ba?"
12Sa'ad da Ubangiji ya gama aikin sa akan Tsaunin Sihiyona da bisa Yerusalem, zan hukunta jawabin faɗin ran sarkin Asiriya da homarsa.13Domin yace, "Da karfina da hikimata Na yi aiki. Ina da fahimta, na kuma kawas da iyakoki na mutane. Na sace taskokin su, kamar sã na nakasadda mazauna nan wurin.
14Hannuna ya tsaya, kamar sheƙa, dukiyar dangogi, kuma kamar wanda ya tattara ƙwan da aka ƙyale. Na tattaro dukkan duniya. Ba bu wanda ya motsa fiffike, ko ya buɗe baki balle suyi ƙara."
15Ko gatari zai iya yiwa mai sara da shi alfahari? ko zarto zai iya ɗaukaka kansa bisa wanda ya ke yanka da shi? sai kace sanda zata iya ɗaga mai ɗaukar ta, ko kuma kulkin katako zai ɗaga mutum.16Domin haka Yahweh mai runduna zai aiko da ramewa cikin jarumawansa; ƙarƙashin ɗaukakarsa kuma za a kunna ƙonewa kamar wuta.
17Hasken Isra'ila kuma zai zama wuta, Mai Tsarkin nasa kuma harshen wuta, za ya ƙone ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya ya cinye su rana ɗaya.18Yahweh kuma zai cinye darajar kurminsa da gonarsa mai albarka, rai duk da jiki; zai zama kamar lokacin da ran marar lafiya ya suma.19Sauran itatuwan kurmin za su zama 'yan kaɗan, ƙaramin yaro zai iya ƙirga su.
20A wannan rana, ringin Isra'ila, da iyalin Yakubu waɗanda suka tsira, ba za su dogara ga wanda ya ci nasara da su ba, amma lallai za su dogara ga Yahweh, MaiTsarkin nan na Isra'ila.21Ringi na Yakubu za su juya zuwa ga Allah mai iko.
22Ko da shike mutanenka, Isra'ila, suna kama da yashin teku, sai ringi daga cikin su za su komo. An zartar da dokar Hallakarwa, kamar yadda adalci mai malalowa ya wajabta.23Gama Yahweh mai runduna, daf ya ke da hallakar da dukkan ƙasar kamar yadda ya ayyana.
24Domin wannan Ubangiji Yahweh mai runduna yace, "Mutanena da suke zaune cikin Sihiyona, kada ku ji tsoron Asiriyen. Zai buge ku da sanda ya ɗaga kerensa ga bada ku, kamar yadda Masarawa suka yi.25"Kada ku ji tsoron sa, gama a cikin ɗan lokaci kaɗan fushina a kanku zai ƙare, fushi na zai kai ga hallakarwarsa."
26Daga nan Yahweh mai runduna zai tayar da bulala akansu, kamar yadda ya fatattaki Midiyan a Tsaunin Oreb. Zai ɗaga sandarsa bisa teku ya ɗaga ta sama kamar yadda ya yi a Masar.27A wannan rana, nauyin kayansa an ɗauke shi daga kafaɗarki kuma karkiyarsa an ɗauke daga wuyanki, kuma karkiyarki zata lalace saboda ƙibar.
28Maƙiyi ya zo Ayiyat ya ratsa ta Migron; a Mikmash ya ajiye abubuwan daya tanada.29Sun ƙetare suka sauka a Geba. Rema tana rawar jiki Gibiya ta Saul kuma ta gudu.
30Ki yi kuka da ƙarfi, ɗiyar Galim! ki saurara, Laisha! ke talautattar Anatot!31Madmena tana gudu, mazaunan Gebim sun gudu domin su ɓuya.32A wannan rana zai sauka a Nob zai girgiza damtsensa a tsaunin ɗiyar Sihiyona, tudun Yerusalem.
33Duba, Ubangiji Yahweh mai runduna zai sassare rassa da ban razana; itatuwan da suka fi tsawo za'a sare su, maɗaukaka kuma za'a ƙasƙantar dasu.34Za ya sassare kuramen jeji da gatari, Lebanon kuma cikin ɗaukakarsa zata faɗi.

11

1Zai toho daga cikin kututturen Yesse, reshe kuma daga cikin sa zai bada 'ya'ya.2Ruhun Yahweh kuma zai zauna bisansa, Ruhun hikima da fahimta, da Ruhun umarni da iko, da Ruhun sani dana tsoron Yahweh.

3Marmarin sa zai kasance tsoron Ubangiji; ba zaiyi shari'a bisa ga abin da idanunsa suka gani ba, ba kuwa zai yi hakunci bisa ga abin da kunnensa ya ji ba.4Maimakon haka zai shar'anta talakwa bisa ga adalci bisa ga dai-daita kuma zai yanke shawara ga masu tawali'u na duniya. Zai bugi duniya da sandar bakinsa, da numfashin leɓunansa kuma zai kashe miyagu.5Adalci zai zama ɗammarar ƙugunsa, aminci kuma ɗammara kewaye da kwatangwalonsa.
6Kyarkeci zai zauna tare da rago, damisa kuma zata kwanta tare da ɗan'akuya, ɗan maraki da ɗan zaki tare da kiwataccen ɗan maraƙi, za su zauna tare, ɗan yaro kuwa zai bishe su.7Saniya da kerkeci za su yi kiwo tare, 'ya'yansu za su kwanta wuri ɗaya. Zaki zai ci ciyawa kamar sã.
8Jariri zai yi wasa a bakin ramin maciji, yayayyen yaro kuma zai sa hannunsa a kogon maciji.9Ba za su cutar ko hallakar ba a ko'ina kan tsaunina mai tsarki; gama duniya za ta cika da sanin Yahweh, kamar yadda ruwaye suka rufe teku.
10A wannan rana, tushen Jesse zai tsaya a matsayin tuta ga mutane. Al'ummai za su neme shi, wurin hutun sa kuma zai zama abin ɗaukaka.11A wannan rana, Ubangiji zai sake sa hannunsa domin ya fanshi sauran mutanensa da suka rage a Asiriya, Masar, Fatros, Kush, Ilam, Shina, Hamat, da tsibirai na teku.
12Zaya kafa tuta domin al'ummai ya tattara korarru na Isra'ila warwatsattsu na Yahuda daga kusurwoyi huɗu na duniya.13Zai juyar da kishin Ifraim, masu azabtar da Yahuda kuma zai datse su. Ifraim ba zai yi kishin Yahuda ba, Yahuda kuma ba zai ƙara kishin Ifraim ba.
14Maimakon haka zasu sauko bisa tuddan Filistiyawa a wajen yamma, tare za su washe 'ya'yan gabas. Za su kai hari ga Idom da Mowab Mutanen Ammon kuma za su yi masu biyayya.15Yahweh zai hallakar da dukkan kwarurruka na Tekun Masar. Da iskarsa mai ƙonewa zai karkaɗe hannunsa bisa kan Kogin Yufiretis zai raba su zuwa rafuffuka bakwai, domin a iya ƙetarewa da takalmi a ƙafa.
16Zai kasance akwai karabka domin sauran mutanensa, waɗanda suka ragu za su dawo daga Asiriya, kamar yadda akayi ga Isra'ila cikin ranar da suka taso daga ƙasar Masar

12

1A wannan rana za ka ce, "Zan gode maka, Yahweh. Koda shike ka yi fushi da ni, fushinka ya juya, ka kuwa yi mani ta'aziya.2Duba, Allah shi ne cetona; zan dogara, ba kuwa zan ji tsoro ba, gama Yahweh, hakika, ƙarfina ne da waƙata. Ya zama cetona,"

3Da farinciki za ku ɗebo ruwa daga rijiyoyin ceto.4A wannan rana za ku ce, "Kuyi godiya ga Yahweh ku kuma kira ga sunansa; ku bayyana ayyukan sa a wurin al'ummai, ku yi shelar sunansa maɗaukaki ne.
5Ku raira ga Yahweh, gama ya aikata al'amura mafifita, bari wannan ya zama sananne ko'ina a duniya.6Ku tada murya ku yi sowa ta murna, ku mazaunan Sihiyona, gama Mai Tsarki na Isra'ila dake tsakiyarku mai girma ne."

13

1Kenan game da Babila, wanda Ishaya ɗan Amoz ya karɓa:2A bisa buɗaɗɗen tsauni ku ɗaga tutar alama, ku tada murya gare su, ku kaɗa hannu gare su domin su shigo ƙofofin hakimai.3Na umarci tsarkakana, I, Na kira masu iko na su aiwatar da fushina, su waɗanda nake fahariya da su da waɗanda aka ɗaukaka.

4Hayaniyar mutane cikin duwatsu, sai kace na mutane da yawa! Hayaniya ta mulkokin al'ummai a tattare! Yahweh mai runduna yana tattara runduna domin yaƙi.5Sun zo daga ƙasa mai nisa, tun daga iyakacin sama. Yahweh kenan da kayan yakinsa na hukunci, domin hallaka dukkan ƙasa.
6Ku yi kuka, gama ranar Ubangiji ta kusa; zata zo da hallakrwa daga Mai iko.7Domin haka dukkan hannuwa za su maƙale, kowacce zuciya kuma za ta narke.8Za su firgita; zafi da baƙinciki za su kama su, kamar mace cikin naƙuda. Za su dubi junansu cikin mamaki, fuskokinsu za su zama kamar gaushen wuta.
9Duba, ranar Yahweh tana zuwa da hasala da fushi mai zafi, za'a maida ƙasar kango, za'a hallakar da masu zunubin daga cikin ta.10Taurarin sama ba za su bada haskensu ba. Rana za ta duhunta a lokacin fitowarta, wata kuma ba zai haskaka ba.
11Zan hori duniya domin muguntarta da Miyagu domin zunubansu. Zan kawo ƙarshen alfarmar masu girmankai in ƙasƙantar da alfarmar mutane masu ban tsoro.12Zan sa maza su yi ƙaranci fiye da zinariya mai daraja, samun mutum kuma ya zama da wuya fiye da tsattsarkar zinariya ta Ofir
13Domin wannan zan sa sammai su yi rawar jiki, duniya kuma za ta girgiza ta gusa daga wurinta, ta wurin hasalar Yahweh mai runduna, da cikin ranar fushinsa mai zafi.14Kamar barewar da aka farauto ko tumakin da ba su da makiyayi, kowanne mutum ya juya ga bin mutanensa, zai gudu zuwa ƙasarsa.
15Duk wanda aka samu za a kashe shi, duk wanda aka kama kuma zai mutu da kaifin takobi.16Jariransu kuma za a yayyanka su akan idanunsu. Gidajensu za a washesu, matan su kuma za a yi masu fyaɗe.
17Duba, Ina gab da tayar da Medes domin su kai masu hari, waɗanda ba za su kula da azurfa ba, ba kuma za su yi murna saboda zinariya ba.18Mãsunsu za su soki samari. Ba za su tausayawa jarirai ba kuma ba zasu bar yara ba.
19Daga nan Babila, mafi daraja a mulkoki, jamalin fahariyar Kaldiyawa, Allah zai juyadda su kamar yadda ya yi da Sodom da Gomora.20Ba za a zauna ciki ko rayuwa a ciki ba daga tsara zuwa tsara. Balarabe ba zai kafa rumfarsa a can ba, makiyaya kuma ba za su bar garken su su huta a can ba.
21Amma namomin jeji za su kwanta a wurin. Gidajensu za su cika da mujiyoyi; Jiminai da Gadai za su yi ta tsalle can.22Kuraye za su yi kuka a cikin kagarorinsu, diloli kuma a cikin fadodinsu masu kyau. Lokacinta ya kusa, kwanakinta kuma ba za a jinkirtasu ba.

14

1Yahweh zai ji tausayin Yakubu; zai sake zãɓen Isra'ila ya sake dawo da su cikin ƙasarsu, bãƙi za su haɗa kai da su, za su haɗa kansu da gidan Yakubu.2Al'ummai za su ɗauke su su kai su garinsu. Gidan Isra'ila zai ɗauke su ya kai su ƙasar Yahweh a matsayi bayi maza da mata. Za su bautadda waɗanda suka kwashe a dã, za su yi mulkin waɗanda suka ƙuntata masu.

3A wannan rana Yahweh ya ba ku hutu daga baƙinciki da wahalarku kuma daga aiki mai wahala wanda aka sa ku yi,4za ku raira wannan waƙar ta habaici gãba da sarkin Babila, "Yadda ƙarshen mai azabtarwa ya zo, fushin masu girmankai ya ƙare!
5Yahweh ya karya sandar mugu, ikon masu mulkin nan,6wanda ya bugi mutane cikin fushi da naushi kowanne lokaci, ya mallaki al'ummai da fushi, da harin da ba mai hanawa.
7Dukkan duniya tana zaune cikin hutu kuma shiru; sun fara biki da raira waƙa.8Har itatuwan sayfres suna murna da kai tare da Sidas na Lebanon; suka ce, 'Tunda aka ƙasƙantar da kai, ba bu wani mai saran itace da ya zo ya sare mu ƙasa.'9Lahira daga ƙasa na marmarin saduwa da kai idan ka je can. Ta tayar da mattatu domin ka, dukkan sarakunan duniya an sa sun tashi daga kursiyinsu, dukkan sarakunan al'ummai.
10Dukkansu za su yi magana su ce maka, 'Ka zama marar ƙarfi kamar mu.11Ka zama irin mu. An yi ƙasa da alfarmarka har Lahira duk da ƙarar amon tamburanka. An shimfiɗa tsutsotsi ƙarƙashinka, tsutsotsi sun rufe ka.'
12Yadda ka faɗo daga sama, tauraron rana, ɗan asubahi! Yadda aka sãre ka ƙasa, kai wanda kayi nasara da al'ummai!13Sai ka ce a cikin zuciyarka, 'Zan hau cikin sama, Zan ɗaukaka kursiyina bisan taurarin Allah, zan zauna bisa tsaunin taruwar jama'a, cikin ƙarshen arewa.14Zan hau can bisa maɗaukakan gajimarai; Zan maida kaina kamar Allah Mai Iko.'
15Yanzu angangaradda kai zuwa Lahira, zuwa ƙarshen rami.16Waɗanda suka ganka za su zuba maka ido kuma za su saurare ka. Za su ce, 'Ko shi ne mutumin da ya sa duniya ta yi rawa, wanda ya girgiza mulkoki,17wanda ya mai da duniya kamar jeji, wanda ya juyadda biranenta ya kuma hana 'yan yãrinsa komawa gida?'
18Dukkan sarakunan al'ummai, dukkan su cikin daraja suke kwance, kowannen su cikin kabarinsa.19Amma kai an jefar da kai can waje da kushewarka kamar reshen da a ka jefar. Mattatu sun rufe ka kamar riga, waɗanda a ka sara da takobi, masu gangarowa zuwa ramin duwatsu.20Ba za ka bi su cikin jana'iza ba, saboda ka hallaka ƙasarka kuma ka kashe mutanenka. Ba za a ƙara ambaton zuriyar masu mugunta ba har abada."
21Ka shira yanka domin 'ya'yansa, saboda zunubin kakanninsu, don kada su tashi su mallaki duniya su cika dukkan duniya da birane.22"Zan tashi in yi gãba da su"-wannan furcin Yahweh mai runduna ne. Zan datse wa Babila sũna, zuriya da tsãra" - wannan furcin Yahweh ne.23Zan maishe ta mallakar mujiyoyi, da kuma tabkunan ruwa, kuma zan share ta tsintsiyar hallakarwa" - wannan shi ne furcin Yahweh mai runduna.
24Yahweh mai runduna ya rantse ya ce, "Hakika, kamar yadda na ayyana, haka zai faru; kamar yadda na shirya haka zai faru:25Zan karya mutumin Asiriya cikin ƙasa ta kuma bisa kan duwatsu zan tattake shi ƙarƙashin sawu. Daga nan za a kawar da karkiyarsa daga gare su kayansa kuma daga kafaɗarsu."
26Wannan shi ne shirin da a ka ƙadartawa dukkan duniya, wannan kuma shi ne hannun da a ka miƙar kan dukkan al'ummai.27Gama Yahweh mai runduna ya shirya haka; wa zai hana shi? hannun Sa a miƙe ya ke, wa za ya juyadda shi?
28A cikin shekarar da sarki Ahaz ya mutu wannan furcin yazo:29Kada ku yi murna, dukkan ku Filistiyawa, cewa sandar da ya buge ki ya karye. Gama daga cikin tsatson maciji ƙasa mai dafi za ta fito, zuriyarsa kuma za ta zama wuta mai firiyar maciji.30Ɗ‌an farin talaka zai yi kiwon tumaki a makiyayata, mabuƙaci kuma zai kwanta cikin tsaro. Zan kashe tsatsonka da yunwa dukkan waɗanda suka tsira za su mutu.
31Ki yi kururuwa, ƙofa, ki yi kuka, birni, dukkan ku za ku narke, Filistiya. Gama daga arewa girgije mai hayaƙi ke fitowa, ba kuma mai ratsewa cikin dagarsa.32Ta yaya za a amsa wa 'yan saƙon al'umman nan? Wato Yahweh ne ya kafa Sihiyona, daga cikin ta ne raunanan mutanensa za su sami mafaka.

15

1Furci game da Mowab. Lallai, a dare ɗaya Ar ta Mowab ta zama marar amfani an hallaka ta, Lallai, a dare ɗaya Kir ta Mowab ta zama marar amfani an hallaka ta.2Sun hau saman masujada, mutanen Dibon sunje sammai don su yi kuka; Mowab na makoki kan Nebo da Medeba. Duk kawunansu an aske su kwal duk gemunsu kuma an yanke su.

3A cikin titunansu suna saye da tsummoki; a kan benayen su da dandalinsu kowannensu yana koke-koke, sun narke da hawaye.4Heshbon da Ileyale sun yi kira domin taimako; a na jin muryarsu har Yahaz. Domin haka mayaƙa na Mowab suna kira domin neman taimako; su kadai suna rawar jiki.
5Zuciyata tana kuka domin Mowab; sanannun ta suna gudu zuwa Zowa da Iglat Shelishiya. Sun hau zuwa wajen Luhit suna kuka; hanyar zuwa Horonayim sun tada murya da ƙarfi kan hallakarsu.6Ruwayen Nimrim sun bushe; ciyawa ta yi yaushi, sabuwar ciyawa ta mutu, ba sauran ɗanyen abu.7Yalwar abin da suka samar da wanda suka ajiye, za su ɗauka su haye kwazazzabon foflas.
8Kukan ya zaga wajen iyakar Mowab; kuwwarta har ta fi Iglaim da Biya Ilim.9Domin ruwayen Dimon cike suke da jini; amma zan kawo wanda ya fi zafi akan Dimon. Zaki zai kai hari ga waɗanda suka tsira a Mowab da kuma sauransu da suka rage a cikin ƙasar.

16

1Ku aika da raguna domin mulkin ƙasa daga Selah cikin jeji; zuwa tsaunin ɗiyar Sihiyona.2Kamar tsuntsaye masu yawo, kamar sheƙar da aka warwatsar haka matan Mowab a mishigan Kogin Arnon.

3"Ka bada umarni, ka tabbatar da adalci; ka sa inuwa ta zama dare a cikin tsakiyar rana; ka ɓoye yasassu; kada ka bashe da waɗanda ba kome ba.4Ka barsu su zauna a cikin ku, 'yan gudun hijira daga Mowab; ka zama maɓuya gare su daga mai lalatarwa." Gama zalunci zai tsaya, hallakarwa kuma zata tsaya, waɗannan da suke tattaka mutane za su ɓace a ƙasar.
5A cikin alƙawarin aminci kuma za'a kafa kursiyi, ɗaya kuma daga cikin rumfar Dauda da aminci zai zauna can, zai yi shari'a yana neman adalci, yana aikata gaskiya.
6Mun ji labarin girmankan Mowab, girmankansa da fahariyarsa da fushinsa. Amma taƙamarsa duk bakomai ba ne.7Sai Mowab tayi koke-koke domin Mowab - dukkan su suna makoki, ku da a ka lalatar ɗungum, domin wainar kauɗar inabin Kir Hareset.
8Gonakin Heshbon sun bushe duk da kuringar inabin Sibma. Sarakunan al'ummai sun tattake zaɓaɓɓun inabin da suka kai zuwa Yaza, da suka yaɗu zuwa cikin jeji. Rassanta sun yaɗu waje; sun fita zuwa ƙetaren teku.
9Domin wannan zan yi kuka tare da Yaza domin kuringar Sibma. Zan dausayar da ku da hawaye na, Heshbon da Ileyale. Gama na kawo ƙarshen farincikinku game da amfanin gonakinku damina da na kaka.10Murna da farincikinku an ɗauke su daga 'ya'yan itatuwan kuramenku, ba sauran waƙa, ba sowa cikin gonakinku. Ba mai taka ruwan inabi a wurin matsewa, gama na kawo ƙarshen sowa ga mai takawar.
11Domin haka zuciyata na tsãki kamar girayar Mowab, can cikina kuma domin Kir Hareset.12Sa'ad da Mowab ya gajiyar da kansa a wuri mai bisa kuma ya shiga masujada ya yi addu'a, addu'o'insa ba za su yi komai ba.
13Wannan ita ce maganar da Yahweh ya faɗi game da Mowab da farko.14Yahweh ya sake yin magana, "Cikin shekara uku, ɗaukakar Mowab za ta ɓace; duk da yawan mutanensa, sauran da za su ragu za su zama 'yan kaɗan marasa amfani."

17

1Furci game da Damaskus.2Biranen Arowa za su zama kufai. Za su zama inda garkuna za su riƙa kwanciya, ba kuwa mai tsoratar dasu.3Biranensu masu kagara za su ɓace daga Ifraim, mulki kuma daga Damaskus, da ringin Aram - za su zama kamar ɗaukakar mutanen Isra'ila - wannan furcin Yahweh mai runduna ne.

4Zai zama kuma a ranar nan darajar Yakubu zata zama 'yar siririya, ƙibar jikinsa zata saɓe.5Zai zama kamar kwanakin da maigirbi ya tattara hatsin dake tsaye, hannunsa kuma yana yankan zangarku. zai zama kamar lokacin da mutum ke kalar zangarku cikin kwarin Refayim.
6Za'a bar kala, duk da haka, kamar lokacin da itacen zaitun ke kakkaɓewa: biyu ko uku cikin reshe mafi bisa, huɗu ko biyar a cikin rassa mafi bisa na itace mai 'ya'ya - wannan furcin Yahweh ne, Allah na Isra'ila.7A wannan rana mutane za su dubi mahaliccinsu, idanunsu za su dubi Mai Tsarki na Isra'ila.
8Za su dubu bagadai, aikin hannuwansu, ba kuwa za su dubi abin da yatsunsu suka yi ba, sandunan Ashera ko siffofin rana.9A wannan rana ƙarfafan biranensu za su zama kamar wuraren da aka bar su kufai cikin kurmi a ƙwanƙolin tsaunuka, da aka bar su saboda mutanen Isra'ila wannan zai zama hallaka.
10Domin kun manta da Allah mai cetonku, kun kuma yi watsi da dutsen ƙarfinku. Kuna dasa tsire-tsiren da suka gamshe ku, kuna dasa rassan inabi da kuka karɓa wurin baƙo,11A cikin rana kayi dashe da shinge da noma. Bada daɗewa ba irinka zai yi girma, amma girbinka zai gaza a cikin ranar baƙinciki da matsananciyar azaba.
12Kaito! ga hayaniyar mutane da yawa, wannan ruri na kama da rurin tekuna, da gudun al'ummai, suna gudu kamar gudun ruwaye masu girma!13Al'ummai za su yi ruri kamar gudun ruwaye masu yawa, amma Allah zai tsauta masu. Za su gudu nesa za'a runtume su kamar ƙai-ƙai a kan tsaunuka gaban iska, kamar guguwa kuma gaban hadari.14Da yamma, ga, razana! Kafin safiya kuma za su tafi! wannan shi ne rabon waɗanda suke yi mana sata, rabon waɗanda suke yi mana fashi.

18

1Kaiton ƙasa ta motsin fukafukai wadda, take rafukan Kush.2Wadda take aika jakadu ta hanyar teku, a cikin ruwaye ta jiragen iwa Ku tafi ku, jakadu masu sauri, wurin dogayen al'ummai masu taushin fata, wurin mutanen da a ke tsoron su nesa da kusa, al'umma mai ban razana mai tattakewa, wadda ruwaye sun raba ƙasarta.

3Dukkan ku mazaunan duniya da waɗanda ke zaune a duniya, idan kuka ga alama a kan duwatsu, ku duba; idan aka busa ƙaho, ku saurara.
4Wannan shi ne abin da Yahweh ya faɗi mani, "A hankali zan lura daga gidana, kamar gumi cikin hasken rana, kamar hazon ƙyasashi a lokacin girbi.5Kafin girbi, ya zo sa'ad da fure ya kaɗe, huda tana zama nunannun 'ya'yan inabi, zai datse maɓulɓula da ƙugiya mai tsini, zai sare ya kuma kwashe rassan da suka barbaje.
6Za a bar su tare saboda tsuntsayen duwatsu da dabbobin duniya. Tsuntsaye za su yi damina a kansu, kuma dukkan dabbobin duniya za su yi lokacin sanyi a kansu."7A wancan lokacin dogayen mutane masu taushin jiki za su kawo hadaya ga Yahweh, daga mutanen da a ke tsoro nesa da kusa, ƙarfafan al'ummai masu ban razana, waɗanda rafuka suka raba ƙasarsu, zuwa wurin da ya ke na sunan Yahweh mai runduna, zuwa Tsaunin Sihiyona.

19

1Furci game da Masar. Duba, Yahweh ya hau girgije mai sauri ya taho Masar; gumakan Masar za su razana a gabansa, zuciyar masarawa za ta narke a cikin su.2"Zan haɗa masarawa gãba da masarawa: Mutum zai yi faɗa gãba da ɗan'uwansa, mutum gãba da maƙwabcinsa; birni kuma gãba da birni, mulki kuma gãba da mulki.

3Ruhun Masar zai karaya daga ciki. Zan rushe shawararsa, koda ya ke sun nemi shawarar gumakai, da ruhun matattu, da masu duba, da masu aiki da ruhohi.4Zan bada masarawa a hannun mugun shugaba, sarki mai ƙarfi zai yi mulkin su - wannan shi ne furcin Yahweh Ubangiji mai runduna."
5Ruwayen teku za su bushe, rafi zai bushe ya zama ba komai.6Rafuka za su yi wari; ƙoramun Masar kuma za su shanye su bushe; iwa da jema za su yi yaushi.
7Iwar dake kusa da Nilu, da bakin gãɓar Nilu, da dukkan gonakin da a ka shuka a gefen Nilu za su bushe, za a kore su, kuma ba za su kasance ba.8Masunta za su yi kuka su yi makoki, da dukkan masu jefa ƙugiya cikin Nilu za su yi makoki, kuma masu jefa tãru za su yi baƙinciki.
9Masu aikin tsifar zare da waɗanda ke saƙar farar tufa za su rame.10Za a murƙushe masu aikin tufafi na Masar; masu aikin lada za su yi baƙinciki a cikin su.
11Sarakunan Zowan wawaye ne gaba ɗaya. Shawarar mashawartan Fir'auna mafiya wayo ta zama rashin hankali. Yaya za ka iya cewa da Fir'auna, "Ni ɗan mutane masu hikima ne, ni ɗan sarakunan dã ne?"12Ina mazajenka masu wayau suke? Bari su gaya maka su kuma sanasshe ka abin da Yahweh mai runduna ke shiryawa game da Masar.
13Sarakunan Zowan sun zama wawaye, an ruɗi sarakunan Memfis; sun sa Masar ta bauɗe, su da suke duwatsun kusurwar kabilunta.14Yahweh ya sa ruhun lalacewa cikin tsakiyarta, suka kuma sa Masar ta bauɗe cikin dukkan abin da take yi, kamar mashayi mai tangaɗi cikin amansa.15Ba abin da wani zai iya yi domin Masar, ko kai ko wutsiya, ko rassan dabino ko iwa.
16A wannan rana, Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki da tsoro saboda ɗagaggen hannun Ubangiji mai runduna a kansu.17Ƙasar Yahuda za ta zama sanadin tangaɗin Masar. Dukkan sa'ad da wani ya tuna masu da ita, za su ji tsoro, saboda shirin Yahweh, kan abin da ya ke shiryawa gãba da su.
18A wannan rana za a sami birane biyar cikin ƙasar Masar da za su yi magana da harshen Kan'ana su yi rantsuwa su yi amana da Yahweh mai runduna. Ɗaya daga waɗannan za a kira shi Birnin Rana.
19A wannan rana za a sami bagadin Yahweh a tsakiyar ƙasar Masar, da dutsen daya zama ginshiƙi na kan iyakar Yahweh.20Zai zama kamar alama da shaida ga Yahweh mai runduna a cikin ƙasar Masar. Idan suka yi kuka ga Yahweh saboda mai tsananta masu, zai aiko masu da mai ceto da mai kariya, zai kuma cece su.
21Yahweh zai zama sananne a Masar, a wannan rana Masarawa za su san da kasancewar Yahweh. Za su yi sujada da hadayu da baye-baye, za su yi wa'adodi ga Yahweh, su cika su kuma.22Yahweh zai azabci Masar, yana azabtarwa da warkarwa kuma. Za su juyo ga Yahweh; zai ji addu'arsu ya warkar dasu.
23A wannan rana za a sami karabka tsakanin Masar da Asiriya, Asiriye zai zo Masar, Bamasare kuma zai je Asiriya; Masarawa kuma za su yi sujada tare da Asiriyawa.
24A cikin wannan rana, Isra'ila za ta zama ta uku tare da Masar da Asiriya, za su zama albarka a tsakiyar duniya;25Yahweh mai runduna zai albarkace su ya ce, "Mai albarka ce Masar, jama'ata; Asiriya, aikin hannuwana; da Isra'ila, abin gãdona."

20

1A cikin shekarar da Tartan ya zo Ashdod, sa'ad da Sargon sarkin Asiriya ya aiko shi, ya yi faɗa gãba da Ashdod ya amshe ta.2A wannan lokaci Yahweh ya yi magana ta wurin Ishaya ɗan Amoz yace, "Ka je ka tuɓe tsummokara daga ƙugunka, ka tuɓe takalma daga ƙafafunka." Ya yi haka, ya yi tafiya huntu ba takalma a ƙafafunsa.

3Yahweh yace, "Kamar yadda bawana Ishaya ya yi tafiya huntu ba takalma a ƙafafunsa shekara uku, wannan alama ce da al'ajibi dangane da Masar da Kush -4ta haka sarkin Asiriya zai tafi da kamammu na Masar, da korarru na Kush, tsoho da yaro, huntu ba takalmi, da ɗuwawunsu a waje, domin Masar ta kunyata.
5Za su karaya su ji kunya, saboda Kush begensu da Masar darajarsu.6Mazaunan wannan yanki a cikin wannan rana za su ce, 'Hakika, wannan shi ne tushen begenmu, inda mu kan ruga neman taimako domin a cece mu daga sarkin Asiriya, to yanzu, ta yaya za mu tsira?"'

21

1Furci game da hamada ta wajan teku. Kamar guguwa mai sharewa ta bi ta Negeb, ta zo tana wucewa ta cikin jeji, daga ƙasa mai ban tsoro.2An ba ni ruya mai ban razana: mutum marar imani yana yin rashin imani, mai hallakarwa yana hallakarwa. Jeka ka kai hari, a kan Ilam; yi sansani, Midiya; zan tsaida dukkan rurinta.

3Saboda haka kwankwasona ya cika da ciwo; ciwo kamar irin ciwon mace mai naƙuda ya kama ni; abin da na ji ya durƙusar da ni; abin da na gani ya tada hankalina.4Zuciyata tana bugawa; na kaɗu da tsoro. Hasken asuba lokacin da nike so, amma ya kawo razana a gare ni.
5Sun shirya teburi, sun shimfiɗa dardumai, sun ci sun sha; ku tashi, yarimai, ku shafe garkuwoyinku da mai.
6Gama abin da Yahweh yace da ni ke nan, "Jeka, ka sa mai tsaro; dole ya faɗi abin da ya gani.7Sa'ad da ya ga karusa, da tagwayen mahaya, a kan jakuna, da raƙuma, sai ya natsu ya yi lura sosai."
8Mai tsaron ya yi kuka, "Ubangiji, a kan kagara nike tsaye dukkan yini, kullum, a kan aikina nike dukkan dare."9Ga karusa tana zuwa da mutum da tagwayen mahaya. Ya yi kira, "Babila ta faɗi, ta faɗi, dukkan sassaƙaƙƙun siffofin allolinta kuma sun ragargaje har ƙasa."
10Masussukaina da sheƙaƙƙu, yaran masussukata! Abin da na ji daga Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, shi na furta maku.
11Furci game da Duma. Wani ya kira ni daga Siya, "Mai tsaro, me ya rage na dare?" Mai tsaro, me ya rage na dare?"12Mai tsaro ya ce, "Safiya ta kan zo haka ma dare. Idan kana so ka yi tambaya, sai ka yi tambaya; ka sake dawowa kuma."
13Furci game da Arebiya. A cikin jejin Arebiya za ku kwana, ku fataken Dedaniyawa.14Ku kawo ruwa saboda masu jin ƙishi; mazauna ƙasar Tema, ku kawo gurasa ga masu gudun hijira.15Gama sun gudo daga takobi, daga takobin da a ka zaro, daga bakan da ke a ɗane, kuma daga nawayar yaƙi.
16Gama abin da Yahweh ya faɗa mani ke nan, "A cikin shekara ɗaya, kamar yadda ma'aikacin da a ka ɗauka domin shekara ɗaya zai gani, dukkan darajar Keda za ta ƙare.17Maharba kaɗan kawai, da jarumawan Keda 'yan kaɗan za su rage," gama Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗi.

22

1Furci game da Kwarin Wahayi: Mene ne dalilin da ya kai dukkan ku bisan gidaje?2Shi ne domin ka ji birni cike da hargowa, birni cike da bukukuwa? Matattunka bada takobi a ka kashe su ba, kuma ba a dãgar yaƙi suka mutu ba.

3Dukkan masu mulkinku sun gudu tare, amma an kamo su ba tare da an yi amfani da baka ba; dukkan su an kamo su tare, koda ya ke sun gudu nesa.4Saboda haka sai na ce, "Kada ku dube ni, zan yi kuka mai zafi; Kada ku yi ƙoƙarin ta'azantar da ni game da hallakar ɗiyar mutanena."
5Gama akwai ranar hargitsi, tana tattakowa, da ruɗami domin Ubangiji Yahweh mai runduna, a Kwari na Wahayi, da rushewar ganuwoyi, da mutane suna kuka ga duwatsu.6Ilam ya ɗauki kwãri, da mahayan karusai da mahayan dawakai, Kir kuma ya ajiye garkuwa a fili.7Zai zama zaɓaɓɓun kwarurrukan ku za su cika da karusai, masu hawan dawaki kuma za su ja dãgarsu a ƙofa.
8Ya ɗauke kariyar Yahuda; a cikin wannan rana ka duba kayan yaƙi a Fada wadda ke Jeji.9Kun ga tsagogin birnin Dauda, suna da yawa, ku ka kuma ɗebo ruwa daga tafki na gangare.
10Kun ƙirga gidajen Yerusalem, kun fasa gidaje domin ku ƙara ƙarfin ganuwa.11kun gina wurin tãra ruwa a tsakanin ganuwowin biyu na tsohon tafki. Amma ba ku kula da wanda ya yi birnin ba, wanda ya shirya shi tun da daɗewa.
12Ubangiji Yahweh mai runduna ya yi kira a wannan rana domin kuka, domin makoki, domin aske kawuna, da sanya tsummokara.13Amma duba, maimakon haka, sai buki da annashuwa, da yanka shanu da tumaki, da cin nama da shaye-shayen ruwan inabi; bari mu ci mu sha, gama gobe za mu mutu.14An bayyana mani haka a kunnuwana daga wurin Yahweh mai runduna: "Babu shakka ba za a gafarta maku wannan muguntar ba, ko kun mutu," inji Ubangiji Yahweh mai runduna.
15Ubangiji Yahweh mai runduna, yace, "Jeka wurin shugaban nan, wurin Shebna, mai lura da gidan, ka ce,16"Me ka ke yi a nan, wane ne ya ba ka izini ka gina kabari domin kanka, sassaƙa kabari ya ke yi a wurare masu tsawo, yana sassaƙawa kansa wurin hutawa a cikin dutse?"'
17Duba, Yahweh ya kusa jefar da kai, ƙaƙƙarfan mutum, ya kusa jefar da kai ƙasa; zai cafke ka da ƙarfi.18Ba shakka zai yi majaujawa da kai, kamar ƙwallo zai wurga ka a cikin ƙasa mai girma. Can za ka mutu, can kuma karusanka masu daraja za su kasance; za ka zama abin kunyar gidan shugabanka!19Zan tumɓuke ka daga matsayin ka daga wurin da kake aiki. Zan jawo ka har ƙasa.
20Zai zama a wannan rana zan kira bawana Iliyakim ɗan Hilkiya.21Zan tufasantar da shi da alkyabbarka in ɗaura masa ɗamararka, zan maida muƙaminka a hannunsa. Za ya zama uba ga mazaunan Yerusalem da gidan Yahuda.22Zan ɗora mabuɗin gidan Dauda a kafaɗarsa; zai buɗe, kuma ba mai kullewa; zai kulle, kuma ba mai buɗewa.
23Zan kafa shi, kamar ƙusa a wuri mai tsaro, zai zama mazaunin ɗaukaka domin gidan ubansa.24Za su rataya masa dukkan ɗaukakar gidan ubansa, 'ya'ya da zuriya-zuriya, kowanne ƙaramin wurin ajiya daga ƙoƙuna zuwa dukkan moɗaye.
25A wannan rana - wannan furcin Yahweh mai runduna ne - ƙusar da a ka kafa a wuri mai ƙarfi za ta cire, ta karye, ta kuma faɗi, nauyin dake kanta kuma zai yanke - Gama Yahweh ya furta.

23

1Furci game da Taya: Ku yi ruri, ku jiragen Tarshish; domin babu gida ko wurin tsayawa; daga ƙasar Sifuros an bayyana masu.2Ku yi shiru, ku mazauna bakin teku; 'yan kasuwar Sidon, masu tafiya kan teku, sun cika ku.3A kan manyan ruwaye ga hatsin Shiho, girbin Nilu ne amfaninta; kuma ta zama wurin cinikin al'ummai.

4Ki ji kunya, ke Sidon; gama teku ya yi magana, babba na teku. Ya ce, "Ban yi naƙuda ba ban haihu ba, ban yi renon samari ba, ban tarbiyantar da 'yammata ba."5Sa'ad da rahoton ya zo ga Masar, za su yi baƙinciki saboda Taya.
6Ku haye zuwa Tarshish; ku yi kuka, ku mazauna bakin teku.7Wannan ya faru da ku ne, birni mai farinciki, wanda tushenta tun daga zamanin dã ne, wadda ƙafafunta sun kai ta can nesa zuwa bãƙin wurare ta zauna?
8Wane ne ya shirya wa wannan gãba da Taya haka, mai bada rawwuna ce, wadda 'yan cinikinta yarimai ne, wanda dillalanta masu daraja ne na duniya?9Yahweh mai runduna ne ya shirya haka domin ya ƙasƙantar da girman kanta da dukkan darajarta, ya kunyatar da dukkan masu martabarta a duniya.
10Ki nome gonarki, kamar mai noma a Nilu, ke ɗiyar Tarshish. Ba sauran wurin kasuwanci a Taya.11Yahweh ya kai hannunsa bisa teku, ya girgiza mulkoki; ya bada umarni game da Fonisiya, ta rushe ƙarfafan wurarensu.12Ya ce, "Ba za ki ƙara yin farinciki ba, ke mai shan tsanani ɗiyar budurwa ta Sidon; ki tashi, ki wuce zuwa Sifuros; Amma ko can ma ba za ki sami hutu ba."
13Dubi ƙasar Kaldiyawa. Waɗannan mutane yanzu ba su; Asiriyawa sun maida ita daji domin dabbobin jeji. Sun kafa hasumiyoyin sansaninsu; sun rushe fãdojinta; sun maida ita tsibin kufai.14Ku yi ruri, ku jiragen Tarshish; gama an rushe mafakarku.
15A wannan rana, za a manta da Taya har shekara saba'in, kamar kwanakin sarki. Bayan shekara saba'in ɗin wani abu zai faru da Taya kamar yadda ya ke a cikin waƙar karuwa.16Ɗauki molo, ki zagaya birnin, ke karuwar da a ka manta da ita; ki kaɗa su da kyau, ki yi waƙoƙi masu yawa, domin a tuna dake.
17Zai zama bayan shekara saba'in, Yahweh zai taimaki Taya, za ta fara samun kuɗi ta wurin aikin karuwanci, za ta bada hidimarta ga dukkan mulkokin duniya.18Ribarta da abin da take samu za a keɓe shi ga Yahweh. Ba za a tara su ko a ajiye su a ma'aji ba, gama za a bada ribarta ga waɗanda suke zama a gaban Yahweh domin ayi amfani da su a ba su abinci isashshe saboda su sami tufafi mafi daraja.

24

1Duba, Yahweh ya kusa mayar da duniya kango, ya lalata ta, ya ɓata fuskarta, ya watsar da mazauna cikinta.2Za ya zama cewa, kamar yadda ya ke da mutane, haka kuma firist; kamar yadda iyayengiji suke haka bayi za su zama, kamar yadda uwargijiya take, haka kuyangarta za ta zama, kamar yadda mai sayarwa ya ke, haka mai saye za ya zama; kamar yadda mai bada bashi ya ke, haka mai karɓar bashin za ya zama; kamar yadda mai karɓar bashi da ruwa ya ke, haka mai bada wa da ruwa.

3Duniya za ta zama kango ta zama huntuwa sarai; gama Yahweh ya faɗi wannan magana.4Ƙasa za ta yanƙwane ta bushe, duniya za ta koɗe ta watse, sanannun mutane na duniya za su lalace.5Duniya ta ƙazamtu daga mazaunanta saboda sun karya dokoki, sun wofinta farillai, sun karya alƙawari na har abada.
6Saboda haka, la'ana ta cinye duniya, an sami mazaunan ta da laifi. Mazauna duniya sun ƙone, mutane kuma kaɗan suka rage.7Sabon ruwan inabi ya bushe, kuringar ta yi yaushi, dukkan masu farinciki a zuciya suna nishi.
8Ƙarar murna ta kacau-kacau ta ƙare, bukukuwan waɗanda suke farinciki; murnar masu garaya ta ƙare.9Ba sa shan ruwan inabi su yi waƙa, kuma barasa ta yi ɗaci ga masu shan ta.
10An rushe birni mai ruɗani; an rufe kowanne gida ba kowa a ciki.11Ana kuka a kan hanyoyi saboda ruwan inabi; dukkan farinciki ya duhunta, murnar birnin ta shuɗe.
12A cikin birnin sai kufai, an rushe birnin, an ɓalle ƙofarsa zuwa kango.13Domin haka zai kasance a dukkan duniya cikin al'ummai, kamar yadda a ke bugun itacen zaitun, kamar yadda a ke kãlar inabi bayan an gama girbi.
14Za su tada muryoyi su yi sowa ga darajar Yahweh, kuma za su yi sowa ta murna daga teku.15Saboda haka daga gabas ku ɗaukaka Yahweh, a cikin tsibiran teku ku ɗaukaka sunan Yahweh, Allah na Isra'ila.
16Mun ji waƙoƙi daga wuri mafi nisa na duniya, "Ɗaukaka ga mai tsarki!" Amma na ce, "Kaito na, na lalace, na lalace! Mazambata sun yi zamba; i, mazambata sun yi zamba ƙwarai."
17Razana, da rami da tarko suna kanku, mazaunan duniya.18Shi wanda ya gudu saboda jin ƙarar razana zai faɗa rami, kuma shi wanda ya fito daga tsakiyar rami tarko zai kama shi. Tagogin sama za su buɗe, tussan duniya kuma za su girgiza.
19Za a rushe duniya sarai, duniya zata tsage, duniya zata girgiza ƙwarai.20Duniya zata yi tangaɗi kamar mutum mashayi ta yi tangaɗi gaba da baya kamar bukka. Zunubinta zai yi mata nauyi zata faɗi ba zata ƙara tashi ba.
21Zai zama a wannan rana, Yahweh zai hukunta rundunar sama a can sammai, sarakunan duniya kuma a duniya.22Za a tattara su tare, 'yan sarƙa a cikin rami, za a rufe su a cikin kurkuku; bayan kwanaki da yawa zai yi masu hukunci.23Sa'an nan rana zata ƙasƙanta wata kuma ya ji kunya, gama Yahweh zai yi mulki a Tsaunin Sihiyona da cikin Yerusalem a gaban dattawansa cikin daraja.

25

1Yahweh, kai ne Allahna; zan ɗaukaka ka, zan yabi sunanka; saboda ka yi abubuwan ban mamaki, abubuwan da a ka shirya tun dã, cikin cikakken aminci.2Gama ka mayar da birnin juji, birni mai daraja ya zama kufai, wurin zaman baƙi ya zama ba birni ba kuwa.3Saboda haka ƙarfafan mutane za su ɗaukaka ka; birnin al'ummai 'yan ta'adda zai ji tsoronka.

4Gama ka zama mafaka ga wanda ya ke matalauci, mafaka ga fakirai mabuƙata - wurin fakewa daga hadari, wurin fakewa daga zafin rana. Sa'ad da hucin marasa hankali ya ke kamar haɗari mai buga bango,5kamar zafi a busasshiyar ƙasa, ka sha ƙarfin hayaniyar bãƙi, kamar yadda inuwar giza-gizai sukan sha ƙarfin zafi, haka aka amsa waƙar 'yan ta'adda.
6A kan wannan tsaunin Yahweh mai runduna zai yiwa dukkan mutane liyafa da abubuwa masu ƙiba, zaɓaɓen ruwan inabi, da nama mai taushi, liyafar ruwan 'ya'yan itace.7A kan wannan tsaunin zai rushe abin da ya rufe dukkan mutane, saƙaƙƙen mayafin lulluɓe dukkan al'ummai.8Zai haɗiye mutuwa har abada, Ubangiji Yahweh zai share hawaye daga dukkan fuskoki; zai ɗauke ƙasƙancin mutanensa daga duniya dukka, gama Yahweh ya faɗe shi.
9A wannan rana za a ce, "Duba, wannan shi ne Allahnmu, mun jira shi, shi kuma zai cece mu. Wannan shi ne Yahweh, mun jira shi, za mu yi murna da farinciki cikin cetonsa."10Gama a wannan tsaunin Yahweh zai ɗora hannunsa; za a tattake Mowab daga wurinsa, kamar yadda ake tattake ciyawa cikin ramin dake cike da taki.
11Za su buɗe hannuwansu a tsakiyarsa, kamar yadda mai iyo ya kan buɗe hannunsa ya yi iyo.12Amma Yahweh zai ƙasƙantar da girman kansu, duk da hikimar hannuwansu. Zai rushe hasumiyoyinsu mai tsawo har ƙasa ta zama turɓaya.

26

1A wannan rana za a yi wannan waƙar a ƙasar Yahuda: Mu na da birni mai ƙarfi; Yahweh yasa ceto ya zama ganuwarsa da kagararsa.2A Buɗe ƙofofin, domin al'umma mai adalci da take riƙe gaskiya ta shiga ciki.

3Wanda ya tsayar da hankalinsa a kanka, za ka riƙe shi cikin cikakkiyar salama, domin ya dogara gare ka.4Ku sa dogara cikin Yahweh, har abada; gama cikin Yah, Yahweh, dutse ne na har abada.
5Gama waɗanda suke zama cikin girman kai zai ƙasƙantar da su; zai rushe tsararren birni, zai rushe shi har ƙasa; ya mayar da shi turɓaya.6Fakirai da matalauta za su tattake shi da ƙafafunsu har ƙasa.
7Hanyar mai adalci an shirya ta, Mai Adalcin nan; ka shirya tafarkin mai adalci ka maishe ta miƙaƙƙa.8I, a tafarkin hukuncinka, Yahweh, za mu jira ka; sunanka da ɗabi'arka su ne marmarinmu.9Na ji marmarinka cikin dare; i, ruhuna a cikina ya neme ka da gaske. Gama sa'ad da hukucinka ya zo duniya, mazaunan duniya suna koyo game da adalci.
10Bari a nuna wa mai mugunta tagomashi, amma ba zai koyi adalci ba. A cikin ƙasar masu tafiya dai-dai, shi mugunta ya ke yi kuma darajar Yahweh shi bai san ta ba.
11Yahweh, an tada hannunka sama, amma su ba su lura ba, amma za su ga himmar ka domin mutane za su ji kunya, saboda wutar magabtanka za ta cinye su.12Yahweh, za ka kawo mana salama; gama hakika ka cika dukkan ayyukanmu domin mu.
13Yahweh Allahnmu, waɗansu shugabanni baya ga kai sun yi mulki a kanmu; amma sunan ka kaɗai muke yabo.14Sun mutu, ba za su tsaya ba sun shuɗe, ba za su tashi ba. Hakika, ka zo cikin hukunci, ka hallaka su, ko tunawa da su ba a yi.
15Ka sa al'umma ta ƙaru, Yahweh, al'umma ta ƙaru ta wurin ka; ka ɗaukaka, an darjantaka; ka faɗaɗa dukkan iyakokin ƙasar.
16Yahweh, a cikin matsala suka dube ka, sai da horon ka ya zo kansu sa'an nan suka yi addu'a.17Kamar mace mai juna biyu sa'ad da lokacin haihuwar ta ya yi kusa, tana zafin ciwon naƙuda ta kuma yi kuka gare ka, haka muke a gaban ka, Ubangiji.
18Muna da juna biyu, muna cikin naƙuda, amma ya zama kamar mun haifi iska. Ba mu kawo ceto ga duniya ba, kuma mazaunan duniya ba su faɗi ba.
19Matattun ka za su rayu; jukkunan su da suka mutu za su tashi. Ku farka ku raira waƙar farinciki, ku mazauna cikin ƙura; gama raɓarku raɓar haske ce, ƙasa kuma za ta fito da matattunta.
20Ku tafi ku mutanena, ku shiga ɗakunanku ku rufe ƙofofi; ku ɗan ɓoye kaɗan, har sai hasalar ta wuce.21Gama, duba, Yahweh ya kusa fitowa daga wurinsa ya hori mazaunan duniya saboda muguntarsu; ƙasa za ta buɗe zubar da jinin da ta yi, ba zata ƙara ɓoye waɗanda ta kashe ba.

27

1A wannan rana Yahweh zai hori Lebiyatan macijin nan mai gudu da takobinsa mai girma, mai karfi, mai ban tsoro, Lebiyatan macijin nan mai tafiya a shagide, zai kashe babban dodon ruwa dake cikin teku.2A wannan rana: kuringar inabi, ta yi masa waƙa.3"Ni, Yahweh, ni ne mai kare shi; zan yi masa banruwa kowanne lokaci. zan yi tsaron sa dare da rana yadda ba wanda zai cuce shi.

4Ban ji haushi ba, Oh, dãma akwai sarƙaƙiya da ƙaya! Zan far masu a filin daga in ƙone su tare duka;5sai dai idan sun nemi kariyata, sun nemi salama da ni; bari su nemi salama da ni.
6A rana mai zuwa, Yakubu zai yi sauya; Isra'ila zaya bunƙasa ya yi fure; su cika sararin ƙasa da 'ya'ya."
7Yahweh, ya kaiwa Yakubu da Isra'ila hari kamar yadda ya kaiwa al'umman da suka kai masu hari? An kashe Yakubu da Isra'ila kamar yadda aka kashe al'umman da suka kashe su?8Ka yi fama bisa mizanin da ya yi dai-dai, ka sallami Yakubu da Isra'ila suka tafi; ka kore su da iska mai ƙarfi sun tafi, a wannan rana ta iskar gabas.
9Haka a wannan rana, za a rufe muguntar Yakubu, wannan shi ne cikakken 'ya'yan kawar da zunubi: sa'ad da zai farfasa duwatsun bagadi ya yi masu gutsu-gutsu kamar alli, ba za a sami sifofin Asheran ko bagadin turarenta a tsaye ba.
10Gama birni mai ganuwa ya zama kufai, an watsar da mazauna a ciki an yashe su kamar jeji. A can ɗan maraƙi ya ke kiwo yana cin rassansa.11Sa'ad da ƙiraruwan suka bushe, za a kakkarye su. Mataye za su hura wuta da su, gama mutane ne marasa fahimta. Wanda ya yi su ba za ya ji tausayin su ba, shi wanda ya yi su ba za ya nuna masu jinƙai ba.
12Rana zata zo inda Yahweh zai yi shiƙa tun daga Kogin Yuferitis har zuwa Wadi ta ƙasar Masar, ku kuma mutanen Isra'ila za a tattaro ku ɗai-ɗai da ɗai-ɗai.13A wannan rana za a busa babban ƙaho; lalatattu na ƙasar Asiriya za su zo, da yasassu na ƙasar Masar, cikin Isra'ila za su yi sujada ga Yahweh a kan tsauni mai tsarki cikin Yerusalem.

28

1Kaiton rawanin girman kai na fure da kowanne mashayan Ifraim ke sanye da shi, kyaun darajarsu na dushewa kamar yadda kyaun fure ke dushewa, haka ma rawanin dake kan waɗanda suka bugu da ruwan inabi a Kwari mai tãki, inda ruwan inabi ya rinjayi wasu!2Duba, Ubangiji yana aiko da wani babba, kuma ƙaƙƙarfa; kamar hadari mai ƙanƙara, da iska mai lalatarwa, kamar ruwan sama mai kwararowa da ambaliyar ruwaye; zai jefar da kowanne rawanin fure a ƙasa.

3Masu rawanin girman kai na fure mashaya na Ifraim za a tattake a ƙarƙashin sawu.4Furen ɗaukakarsa mai ƙyau, dake kan kwari mai arziki, zai zama kamar nunannen ɓaure na fãri da damuna, zai zamana, sa'ad da wani ya dube shi, tun yana hannunsa, zai haɗiye su.
5A ranar nan Yahweh mai runduna zai zama rawani mai daraja da kambi mai kyau ga sauran mutanensa da suka rage,6ruhun adalci ga mahukunta, ƙarfi kuma ga waɗanda suka kori abokan gãba daga ƙofofinsu.
7Amma har ma waɗannan suna tangaɗi da ruwan inabi mai ƙarfi. Da firist da annabi suna tangaɗi da ruwa mai ƙarfi, ruwan inabi ya haɗiye su. Suna tangaɗi da ruwan inabi mai ƙarfi, suna tangaɗi a wahayi da rashin sanin abin yi.8Hakika duk teburorin sun ƙazantu da haraswa, har ma babu tsabtaccen wuri.
9Su waye zai koya wa sani, kuma ga suwa zai fasara saƙon? Ga waɗanda aka yaye daga nono, ko kuma waɗanda a ka cire daga mama?10Gama doka ce bisa doka, doka bisa doka; ka'ida bisa ka'ida; nan ɗan-kaɗan can ɗan-kaɗan.
11Hakika, da leɓunan ba'a da kuma bãƙon harshe zai yiwa mutanen nan magana.12A dã ya ce masu, "Wannan shi ne hutu, a bada hutu ga wanda ya gaji; wannan shi ne wartsakewa ɗin," amma ba za su kasa kunne ba.
13Haka maganar Yahweh za ta zama ma su doka bisa doka, doka bisa doka; ka'ida bisa ka'ida, ka'ida bisa ka'ida; nan ɗan kaɗan, can ɗan kaɗan; domin su tafi da baya su faɗi, a karya su, a sa masu tarko, a kama.
14Ku saurari maganar Yahweh, ku masu ba'a, ku da ke mulki bisa waɗannan mutane dake Yerusalem.15Wannan zai faru domin kun ce, "Mun yi alƙawari da mutuwa, da muka ƙulla yarjejeniya. Saboda haka lokacin da babbar bulala mai bin kan kowa zata ratsa, ba zai iso wurin mu ba. Gama mun mai da ƙarya mafaƙarmu, mun sami mafaka a rumfa cikin ƙarya."
16Saboda haka Ubangiji Yahweh yace, "Duba: Zan kafa harsashin dutse a Sihiyona, dutsen da aka jaraba, dutsen kusurwa mai daraja, tabbataccen harsashi, duk wanda ya gaskata ba za ya kunyata ba.
17Zan sa gaskiya ta zama sandar gwaji, adalci kuma igiyar awo. Ƙanƙara za ta share mafaƙar ƙarairayi, kuma rigyawa zai sha kan maɓuya.
18Za a tada alƙawarin ku da mutuwa, yarjejeniyar da ku ka ƙulla da Lahira za a soke. Sa'ad da rigyawa mai ruri ke wucewa, za a sha kanku.19Duk lokacin da za su wuce, za su sha kanku, daga safiya zuwa safiya za su yi ta aukowa, kuma dare da rana za su wuce kuma da rana da dare zai zo. Sa'ad da aka fahimci saƙon, zai sa firgita.
20Gama gadon ya gajarce da mutum ya miƙe a bisansa, bargon kuma bashi da fãɗin da zai isa ya rufe kansa."21Yahweh zai miƙe kamar a kan Dutsen Ferazim, zai tashi kansa kamar a cikin Kwarin Gibiyan domin ya yi aikinsa, bãƙon aikinsa, ya kuma yi bãƙon aikinsa.
22Saboda haka kada ku yi ba'a, domin kada a karfafa sarƙarku. Na ji daga wurin Ubangiji Yahweh mai runduna, dokar hallaka a kan duniya.
23Ku natsu ku saurari muryata; ku natsu ku saurari maganganuna.24Manomin dake huɗa dukkan rana domin shuka, ya kanyi huɗar ƙasar ne kawai? Zai yi ta huɗa ne kawai yana fasa ƙasa?
25Lokacin da ya shirya ƙasar, ba yakan yafa tamba ba, ya warwatsa riɗi, sai ya sa alkama a jere, da bali a inda ya kamata, da kuma wasu irin a gefuffuka?26Allahnsa yana gaya masa abin yi; yana koya masa da hikima.
27Bugu da ƙari 'ya'yan tamba ba a sussukasu da haƙoran ƙarfe, ba a kuma bin kan riɗi da tayar karusa; amma akan buga tamba da 'gora, riɗi kuma da sanda.28Akan niƙa tsaba domin abinci amma bada laushi ba, koda shike ƙafafun kekensa dana dawakansa sukan warwatsar da shi, dawakansa ba sa murƙushesu.
29Wannan ma daga Yahweh mai runduna ya ke fitowa, shi kuwa mai al'ajibi ne a cikin bishewa mafifici cikin hikima.

29

1Kaiton Ariyel, Ariyel birnin da Dauda ya kafa zango! A ƙara shekara kan shekara; bari bukukuwa su kewayo.2Amma zan kafa wa Ariyel dãga, zata yi ta makoki da kururuwa; kuma zata zamar mani kamar Ariyel.

3Zan kafa dãga gãba dake in kewaye ki, zan yi maki kwanto gãba dake da kuma soro, zan kafa wuraren faƙo gãba dake.4Za a jawo ki ƙasa za ki yi magana daga ƙasa; muryarki zata dushe a cikin ƙura. Muryar ki zata zama kamar ta ruhu dake fitowa daga ƙasa, maganar ki kuma zata zama rarrauna daga cikin ƙura.
5Yawan masu kawo maki hari za su zama kamar 'yar ƙura, ɗunbin mugayen nan kamar dusa dake wucewa. Zai faru, ba zato ba tsammani, farat ɗaya.6Yahweh mai runduna zai zo maki, da tsawa, da raurawar ƙasa, da ƙara mai tsanani, da babbar iska, da gawurtaccen hadari, da harshen wuta mai hallakarwa,
7Zai zama kamar mafarki, wahayi da dare: Taron dukkan al'ummai za su yaƙi Ariyel da kagararta. Za su hare ta da ita da garunta domin su matsa mata.8Zai zama kamar lokacin da mayunwacin mutum ya ke mafarki yana cin abinci, amma da ya farka, cikininsa ba komai. Zai zama kamar lokacin da wani mutum yana jin kishin ruwa, sai ya yi mafarki yana shan ruwa, amma lokacin da ya farka, yana suma, kishin ruwansa ba a kashe ba. I, haka zai zama ga dukkan al'umman da za su yaƙi Dutsen Sihiyona.
9Ku jiwa kanku mamaki, ku kuma yi mamaki; ku makantar da kanku, ku zama makafi! Ku bugu, amma bada ruwan inabi ba, amma bada giya ba.10Gama Yahweh ya kwararo maku ruhun barci mai nauwi. Ya rufe maku idanu, ku annabawa, ya lulluɓe kawunanku, masu gani.
11Dukkan wahayi ya zamar maku kamar maganganun littafin da a ka kulle, wanda mutane za su ba masani, su ce, "Karanta wannan." Shi kuma zai ce, "Ba zan iya ba gama an kulle."12Idan an bada littafin ga wanda bai iya karatu ba, cewa,"Karanta wannan," zai ce, "Ban iya karatu."
13Ubangiji yace, "Waɗannnan mutane suna kusatowa gare ni da bakunansu, suna kuma girmamani da leɓunansu, amma zuciyarsu tana nesa da ni. Girman da suke ba ni na dokokin mutane ne da a ka riga a ka koya.14Saboda haka, duba, zan ci gaba in yi abin ban mamaki cikin mutanen nan, al'ajibi kan al'ajibi. Hikimar masanansu zata lalace kuma fahimtar masu tattalinsu zasu ɓace."
15Kaiton waɗanda suke ɓoye wa Yahweh shirye-shiryensu, waɗanda ayyukansu suke cikin duhu. Suna cewa, "Wa ke ganinmu, wa kuma ya san mu?"
16Kuna juya abubuwa na sama zuwa ƙasa! Za a kwatanta mai ginin tukwane kamar yumɓu, har da abin da a ka yi zai ce game da wanda ya yi shi, "Ba shi ya yi ni ba," ko abin da a ka sarrafa ya cewa wanda ya sarrafa shi, "Bai fahimta ba"?
17A ɗan lokaci kaɗan, za a maida Lebanon fili, filin kuma zai zama kurmi.18A ranar nan kurma zai ji maganganun littafi, idanun makafi kuma za su gani daga cikin duhu baƙiƙƙirin,19Waɗanda a ka murƙushe za su sake yin murna a cikin Yahweh, matalauta kuma a cikin mutane za su yi farinciki cikin Mai Tsarkin na Isra'ila.
20Gama miyagu za su ƙare, masu ba'a za su ɓace. Za a datse dukkan masu ƙaunar aikata mugunta,21waɗanda ta wurin magana su kan maida mutum mai laifi. Suna kafa tarko ga mai neman a yi mashi adalci a ƙofa su kuma kãda mai adalci da holoƙan ƙarairayi.
22Saboda haka ga abin da Yahweh ya faɗi game da gidan Yakubu - Yahweh wanda ya fanshi Ibrahim, "Yakubu ba zai ƙara jin kunya ba, ko kuma fuskarsa ta turɓune.23Amma sa'ad da zai dubi 'ya'yansa, aikin hannuwana, za su tsarkake sunana. Za su tsarkake sunan Mai Tsarki na Yakubu za su kafu cikin tsoron Allah na Isra'ila.24Waɗanda suka ɓata cikin ruhaniya za su sami fahimta, masu gunaguni za su koyi ilimi."

30

1"Kaiton 'ya'yan tawaye," wannan ne furcin Yahweh. Suna shirye-shirye, amma ba daga gare ni ba; suna ƙulla yarjejeniya da wasu al'ummai, amma ba Ruhuna ya bishe su ba, saboda haka suna ƙara zunubi kan zunubi.2Sun kama hanya su gangara zuwa Masar, amma ba su nemi bishe wa daga gare ni ba. Suna neman kariya daga Fir'auna, sun nemi mafaƙa a inuwar Masar.

3Saboda haka kariyar Fir'auna zata zama abin kunyarku, fakewa a inuwar Masar, zai zama ƙasƙancinku,4koda shike hakimansu suna Zowan, jakadunsu sun iso Hanes.5Dukkansu za su ji kunya domin mutanen da ba za su iya taimakonsu ba, waɗanda ba taimako ba ne ko tallafawa, amma abin kunya ne, har ma abin ƙasƙanci."
6Furci game da dabbobin Negeb: Cikin ƙasar wahala da hatsari, da zakanya da kuma zaki, da kububuwa da miciji mai dafi yana shawagi, su kan labta arzikinsu bisa jakkai, da kayayyakinsu masu daraja bisa doron raƙuma, su kaiwa mutanen da ba za su iya taimaka masu ba. Gama taimakon7Masar na banza ne; Saboda haka na kirata Rahab, wadda ta zauna shuru.
8Yanzu ka tafi, ka rubuta shi a gabansu a kan allo, ka maka shi a kan allon fata, domin a adana shi da kyau saboda lokaci mai zuwa ya zama shaida.9Gama mutanen nan 'yan tawaye ne, 'ya'ya maƙaryata, waɗanda ba za su ji umarnin Yahweh ba.
10Sukan cewa masu duba, "Kar ku gani," ga kuma annabawa, "Kada ku faɗa mana annabcin gaskiya; ku faɗa mana maganganun wãsawa, annabcin ruɗami,11Kun kauce daga hanya, kun saki tafarki; kun sa Mai Tsarkin na Isra'ila ya daina magana a fuskarmu."
12Saboda haka Mai Tsarki na Isra'ila yace, "Domin kun ƙi wannan magana, kun dogara ga zilama da ruɗi, kun jingina gare shi,13saboda haka wannan zunubi zai zamar maku kamar ɓangaren shashe dake shirin faɗuwa, kamar curi a kan bango mai tsayi wanda faɗuwarsa zata zo nan da nan, farat ɗaya."
14Zai fasa shi kamar yadda tukunyar magini ke farfashewa; ba zai ƙyale ta ba, don kada a sami cikin farfasassun koda ɗan kaskon da za a ɗauko ɗan garwashin wuta daga sauran garwashin, ko a kwarfo ruwa daga cikin randa.
15Gama wannan shi ne Ubangiji Yahweh, Mai Tsarki na Isra'ila yace, "Cikin komowa da hutu za ku tsira; cikin natsuwa da dogara ƙarfin ku zai tabbata. Amma ba ku yarda ba,16Kuka ce, 'A a, za mu gudu a kan dawakai,' haka za ku gudu; kuma, 'Za mu hau kan dawakai masu zafin gudu,' haka masu bin ku za su yi sauri.
17Dubu za su gudu a tsoratawar mutum ɗaya; a tsoratawar biyar za ku gudu har sai sauranku da suka rage sun zama kamar sandar tuta a kan tsauni, ko kamar 'yar tuta a kan tudu."
18Duk da haka Yahweh yana jira ya yi maku alheri, saboda haka a shirye ya ke ya nuna maku jinƙai. Gama Yahweh Allah ne mai adalci; masu albarka ne dukkan waɗanda suke jiransa.19Gama waɗansu mutane za su zauna a cikin Sihiyona, cikinYerusalem, ba za su ƙara yin kuka kuma ba. Hakika zai yi maku alheri da ya ji ƙarar kukan ku. Idan ya ji shi, zai amsa maku.
20Koda shike Yahweh yana ba ku gurasar wahala da ruwan matsaloli, haka kuma, malaminku ba zai ƙara ɓoye kansa ba, amma za ku ga malamin ku da idanunku.21Kunnuwan ku za su ji magana a bayan ku, cewa, "Wannan ita ce hanya, yi tafiya a cikinta," sa'ad da kuka juya zuwa dama ko kuka juya zuwa hagu.
22Za ku tozartar da sassaƙaƙƙun siffofin ku da a ka dalaye da azurfa da kuma sarrafaffun siffofinku na zinariya. Za ku zubar da su kamar ƙazamtattun tsunmokaran al'ada. Za ku ce masu, "Ku fita daga nan."
23Zai bada ruwan sama domin iri lokacin da kuka yi shuka a ƙasa, da gurasa tare da yalwa daga ƙasa, amfani kuma zai zama da yawa. A ranar nan shanunku za su yi kiwo a makiyaya mai fãɗi.24Shanun noma da jakkai, da suke huɗa, za su ci gyararren abinci wanda aka sheƙe da cebur da matankaɗi.
25Bisa kowanne dogon tsauni, da bisa kowanne dogon tudu, za a sami maɓuɓɓugai da rafuka masu gudanar da ruwa, a ranar gawurtaccen kisa sa'ad da hasumiyoyi za su faɗi.26Hasken wata zai zama kamar hasken rana, hasken rana zai ninka sau bakwai, kamar hasken kwana bakwai. Yahweh zai ɗaure karayar mutanensa ya warkar da ƙujewar raunin da ya yi masu.
27Duba, sunan Yahweh ya zo daga wuri mai nisa, yana ƙũna da fushinsa kuma a cikin turmuƙin hayaƙi. Leɓunansa suna cike da zafi, harshensa kuma na kama da wuta mai cinyewa.28Numfashinsa yana kama da ambaliya wanda ruwansa ya kai har tsakiyar wuya, domin ya rairaye al'ummai da matankaɗin hallakarwa. Numfashinsa linzami ne a muƙamuƙan mutane yasa su warwatse.
29Za ku sami waƙa da dare sa'ad da kuke biki mai tsarki, da murna a zuciya, kamar yadda wani zai tafi da sarewa bisa tsaunin Yahweh, zuwa ga Dutsen Isra'ila.
30Yahweh zai sa aji muryarsa mai daraja, ya nuna motsin hannunsa cikin zafin fushinsa da harshen wuta, tare da guguwa, hadari, da ƙanƙara.
31Gama da jin muryar Yahweh, Asiriyawa za su razana; zai fyaɗe su da sanda.32Kowanne dukkan sanda da Yahweh ya ƙaddara masu za a bi bayansa da waƙoƙin tambura da molo sa'ad da ya ke yaƙi da faɗa da su.
33Domin an shirya wurin ƙũna tuntuni. Hakika, an shirya shi domin sarki, Allah ya shirya shi da zurfi da kuma faɗi. Tarin kuwa a shirye ne da wuta da kuma itace da yawa. Numfashin Yahweh, kamar rafin ƙibiritu ne da zai cinna masa wuta.

31

1Kaiton waɗanda suke gangarawa zuwa Masar domin neman gudummuwa suna jingina ga dawakai, suna dogara ga karusai, (domin suna da yawa), da kuma mahayan dawakai (domin sun zarce ƙididdiga). Amma ba su damu da Mai Tsarki na Isra'ila ba, ba su kuma neman Yahweh!2Duk da haka yana da hikima, zai kuwa kawo masifa ba zai janye maganarsa ba. Zai tashi gãba da gidan mugunta, gãba kuma da kai gudummuwa ga masu aikata zunubi.

3Masar mutum ne ba Allah ba, dawakansu kuma jiki ne ba ruhu ba. Lokacin da Yahweh zai miƙar da hannunsa, dukka da wanda ya yi gudummuwar zai yi tuntuɓe, wanda kuma a ka yiwa gudummuwar zai faɗi; su biyun za su hallaka tare.
4Ga abin da Yahweh yace mani, "Kamar yadda zaki, har ma ɗan zaki ya kan yi ruri a kan dabbar da ya kashe, sa'ad da a ka kira ƙungiyar makiyaya a kansa, amma ba ya rawar jiki saboda muryoyinsu, ko ya sulale domin ƙararsu; haka Yahweh mai runduna zai sauko ya yi yaƙi a kan Dutsen Sihiyona, a kan tudun nan.
5Kamar tsuntsaye masu shawagi bisa sheƙarsu, haka Yahweh mai runduna zai tsare Yerusalem; zai tsare ya kuma cece ta sa'ad da ya ke wuce wa bisanta ya kare ta.6Ki komo wurinsa shi wanda kika juya nesa daga gare shi, mutanen Isra'ila.7Domin a cikin wannan rana kowanne zai jefar da gumakansa na azurfa da gumakansa na zinariya wanɗanda hannuwanku ne cikin zunubi suka yi su.
8Asiriya zata faɗi da kaifin takobi, takobin da ba mutum ne ya ke wurgawa ba zata hallaka shi. Zai gujewa takobi, matasanta za su yi aikin tilas.9Za su karai saboda razana, sarakunansu za su tsorata idan sun ga tutar yaƙin Yahweh - wannan furcin Yahweh ne - wanda wutarsa ke cikin Sihiyona, tanderun wutarsa kuma tana cikin Yerusalem.

32

1Duba, wani sarki zai yi sarauta cikin adalci, yarimai kuma za su yi mulki da gaskiya.2Kowanne ɗayansu zai zama kamar wurin faƙewa daga iska da kuma mafaka daga hadari, kamar rafukan ruwa a ƙeƙasasshiyar ƙasa, kamar inuwar babban dutse a ƙasar gajiya.3Sa'an nan idanun waɗanda suke gani ba za su dushe ba, kuma kunnuwan waɗanda suke ji za su ji sarai.

4Mai saurin baki zai yi tunani da kyau tare da ganewa, mai nauyin baki kuma zai yi magana da kyau da sauƙi kuma.5Ba za a ƙara kiran wawa nagari ba, ko a ce da mayaudari mai aminci.6Domin wawa yakan faɗi wauta, zuciyarsa takan shirya mugunta da mugayen ayyuka, yana kuma faɗar ƙarya akan Yahweh. Yakan tsiyatar da mayunwata, masu jin ƙishirwa kuma ya sa su rasa abin sha.
7Dabarun mayaudari mugaye ne. Yakan ƙago mugayen shirye-shirye, domin ya lalatar da matalauta da ƙarairayinsa, koda matalaucin ya faɗi abin dake dai-dai.8Amma nagarin mutum yakan yi shiri nagari; kuma saboda nagargarun ayyukansa zai tsaya.
9Ku tashi, ku matan dake zaman sake, ku saurari murya ta; ku 'ya'ya mata 'yan ba ruwanmu, ku saurare ni.10Gama nan gaba kaɗan da shekara guda ƙarfin halinku za a karya, ku mata masu zaman sake, gama ba za a sami girbin inabi ba, kuma ba amfanin da za a tattara a rumbuna.
11Ku yi rawar jiki don tsoro, ku mata masu zaman sake; ku yi damuwa, ku masu ƙarfin hali; ku tuɓe ƙyawawan tufafinku, ku tsirance kanku; ku ɗaura tsummokin makoki a kwankwasonku.12Za kuyi kururuwa domin gonakinku masu yalwa, da inabinku masu 'ya'ya.13Ƙasar mutanena zata cika da ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya, har ma a cikin dukkan gidaje da aka taɓa yin farinciki a birnin bukukuwa.
14Gama za a yasar da fãda, birnin mai cincirindon mutane zai koma kango; da tudu da benen tsaro za su zama kogonni har abada, abin murna ga jakan jeji, wurin kiwo domin garkuna;15har sai an kwararo Ruhu a kanmu daga bisa, jeji kuma ya zama gonaki masu bada amfani, gonaki masu bada amfani kuma su zama kamar kurmi.
16Sa'an nan hukunci za ya kasance a jeji; adalci kuma ya kasance a gonaki masu amfani.17Aikin adalci zai zama salama; sakamakon adalci, kwanciyar hankali da gabagaɗi har abada.18Mutanena za su zauna a cikin mazauni na salama, a cikin tsararrun gidaje, da natsattsun wuraren hutawa.
19Amma koda an yi ƙanƙara ko kuma jeji duk ya ƙone, aka kuma rushe birnin gaba ɗaya,20ku da kuka yi shuka a bakin rafuffuka za a albarkace ku, da dukkan ku da kuke aika shanunku da jakai su yi kiwo.

33

1Kaiton ka, mai ɓatawa ba a ɓata ka ba! Kaiton ka mai cin amanar waɗanda ba su ci amanarka ba! Lokacin da ka bar ɓatawa, za a ɓata ka. Lokacin da ka daina cin amana, za a ci amanar ka.

2Yahweh, ka yi mana alheri; muna jiranka; ka zama damtsenmu kowacce safiya, cetonmu kuma a lokacin wahala.
3Da jin ƙararka mai amo mutanen suka gudu; lokacin da ka tashi, al'ummai sai su watse.4Akan tara ganimarka kamar yadda fãri ke taruwa, kamar yadda fãri ke tsalle haka mutane ke tsalle a kanta.
5Daukaka ga Yahweh, yana zaune a mafificin wuri. Zai cika Sihiyona da gaskiya da adalci.6Shi zai zama kafuwarmu a lokatanki, ceto a yalwace, hikima, da ilimi; da tsoron Yahweh shi ne dukiya mai tamani.
7Duba, manzannin suna kuka a tituna; 'Jakadun masu begen salama, suna kuka mai zafi.8An yasar da karabku; ba bu sauran matafiya. Ana ta tada alƙawari, an wofintar da shaidu, kuma ba nuna bangirma ga ɗan adam.
9Ƙasar tana makoki, duk ta yi yaushi; Lebanon ta kunyata ta kuma yi yaushi; Sharon kamar ƙasar filin hamada take; Bashan kuma da Kamel sun kakkaɓe ganyayensu.
10"Yanzu ne zan tashi," inji Yahweh; "Yanzu ne za a ɗagani sama; yanzu za a fifita ni.11Kun ɗauki cikin ƙai-ƙai, kun haifi ciyawa; numfashinku wuta ce da zata cinye ku.12Mutanen za a ƙona su su zama danƙo, kamar yadda a ke sassare sarƙaƙƙiya a ƙone ta.
13Ku da kuke nesa, ku ji abin da na yi; kuma ku da ke kusa, ku shaidi ƙarfina."14Masu zunubi a Sihiyona sun tsorata; makyarkyata ta kama marasa tsoron Allah. Wane ne a cikin mu zai iya zama da wuta mai ruruwa? Wane ne a cikin mu zai iya zaunawa da madawwamin ƙone-ƙone?
15Shi wanda ya ke tafiya bisa adalci yana magana da gaskiya; wanda ke ƙin ribar zilama, yana ƙin karɓar toshi, ba ya shirye-shiryen ta'addanci; ba ya duban mugunta -16zai kafa gidansa a kan tuddai; Mafaƙarsa zai zama kagarar duwatsu; zai dinga samun abincinsa da ruwan shansa a kan kari.
17Idanunku za su ga sarki cikin jamalinsa; za su ga babbar ƙasa.18Zuciyarka zata tuna da razanar da ta faru; ina magatakarda, ina mai auna kuɗi? Ina ya ke mai ƙididdiga hasumiyoyi?19Ba za ku ƙara ganin mutanen nan masu tawaye ba, mutane masu baƙon harshe, waɗanda ba ku fahimce su ba.
20Dubi Sihiyona, birnin bukukuwanmu; idanunku za su ga Yerusalem kamar mazauni mai lafiya, rumfar da ba za a kawas ba, ƙusoshin ta ba za a tumbuƙe su ba, kuma igiyoyinta ba za a katse su ba.21Maimakon haka, Yahweh cikin daraja zai kasance tare damu, a wuri mai manyan koguna da rafuffuka. Ba jirgin ruwan yaƙi da zai bi ta cikinsa, ba kuma manyan jiragen da za su bi ta wurin.
22Domin Yahweh ne alƙalinmu, Yahweh ne mai bamu shari'a; Yahweh ne sarkinmu; shi zai cece mu.
23An kwance maɗaurinka, ba za su iya riƙe tirken tutar jirgin ruwa da ƙarfi ba; ba za su iya baza tutar jirgin ruwa ba; sa'ad da za a raba babbar ganima, har gurgu ma zai sami rabo.24Mazaunan wurin ba za su ce, "Ba ni da lafiya ba," mutanen dake zaune a can za a gafarta zunubansu.

34

1Ku matso kusa, ku al'ummai, ku saurara; ku natsu, ku mutane! Duniya da dukkan cikarta dole su saurara, duniya, da dukkan abin da ke fitowa a cikinta.2Gama Yahweh yana fushi da dukkan al'ummai, da hasala ga dukkan rundunar yaƙin su; ya hallakar da su gaba ɗaya, ya bashe su ga yanka.

3Za a jefar da gawawwakin matattunsu waje. Warin gawawwakin su zai bazu ko'ina; duwatsu kuma za su shanye jininsu.4Dukkan taurarin sama za su dushe, za a naɗe sammai kamar naɗaɗɗen littafi; dukkan taurarinsu za su dushe, kamar yadda ganyayen inabi suke karkaɗewa su faɗi daga itacen, kuma kamar yadda nunannun ɓaure ke faɗuwa daga jikin itacensa.
5Sa'ad da takobina ya sha ya ƙoshi a sama; duba, yanzu zai gangara a kan Idom, akan mutanen da na keɓe domin hallakarwa.6Takobin Yahweh na ɗiɗɗigar da jini da kitse, tana ɗiɗɗigar da jinin 'yan raguna da na awaki, rufe da kitsen ƙodojin raguna. Gama Yahweh yana da hadaya a Bozra da kuma babban yanka a ƙasar Idom.
7Za a kashe bijiman jeji tare da su, ƙananan bijimai tare da manyansu. Ƙasarsu za ta bugu da jini, ƙurarsu za ta yi ƙiba da kitse.
8Gama zata zama ranar sãkayya ga Yahweh da shekarar kuma da zai sãka masu sabili da Sihiyona.9Kogunan Idom za a mai da su baƙin danƙo, ƙurarta kuma ta zama ƙibiritu, ƙasarta kuma ta zama baƙin danƙo mai cin wuta.10Zata ci wuta dare da rana; hayaƙinta zai tashi sama har abada; daga tsara zuwa tsara zata zama yasasshiyar ƙasa; ba wanda zai ratsa ta tsakiyarta har abada abadin.
11Tsuntsaye jeji da dabbobi za su zauna a wurin; mujiya da hankaka za su yi sheƙar su a cikin ta. Kamar yadda mai gini ya ke amfani da igiyar gwaji haka zai auna ƙasar domin rusarwa da hallakarwa.12Ba za a bar wa shugabaninta komai da za su kira masarauta ba, kuma dukkan hakimanta ba za su zama komai ba.
13‌Ƙ‌ayayuwa za su cika fãdodinta, tsidau da dundu a wuraren tsaronta. Zai zama mazaunin diloli, farfajiyar jiminai.14Dabbobin jeji da kuraye za su tattaru a can, awakan jeji za su kira junansu da kuka. Dabbobin jeji masu yawon dare za su tare a nan su kuma samar wa kansu wurin hutawa.15Mujiyoyi za su yi sheƙa, za su nasa ƙwayayensu su ƙyanƙyashe, su ƙyanƙyashe su kuma tsare 'yan ƙananansu. I, a can hankaki za su taru, kowanensu da abokin tarayyarsa.
16Ku binciko daga naɗaɗɗen littafin Yahweh; ba ko ɗayansu da za a rasa. Ba wanda zai rasa ɗan'uwan tarayyarsa; gama bakinsa ya umarta shi, ruhunsa kuma ya tattara su.17Ya jefa ƙuri'a domin mazaunansu, hannunsa kuwa ya auna masu shi da igiya. Za su mallaketa har abada; daga tsara zuwa tsara za su zauna a can.

35

1Jeji da Hamada za su yi farin ciki; hamada kuma za ta yi murna ta faso da fure. Kamar tsire-tsire,2zata faso da furanni ainun ta yi murna da farin ciki da waƙa; za a ba shi darajar Lebanon, da kuma ɗaukakar Karmel da Sharon; za su ga ɗaukakar Yahweh, mafificiyar ɗaukakar Allahnmu.

3Ku ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi, ku tsaida gwiwoyin masu kaɗuwa.4Ku ce wa matsorata, "Ku ƙarfafa, kada ku ji tsoro! Duba, Allahnku zai zo da ramako, da kuma sakamakon Allah. Zai zo kuwa ya cece ku."
5Sa'an nan idanun makafi za su gani, kunnuwan kurame kuma za su ji.6Sa'an nan gurgu zai yi tsalle kamar barewa, bebe zai raira waƙa, gama ruwa zai malalo daga cikin Hamada, koguna kuma cikin jeji.7Yashi mai ƙuna zai zama tafki, ƙasa mai ƙishin ruwa kuma zata zama maɓuɓɓugar ruwa; a mazaunin diloli, inda dă suka kwanta, za a tarar da ciyawa da iwa.
8Wata karafka zata kasance a wurin ana kiran ta Hanya Mai Tsarki. Marar tsarki ba zai bi ta kanta ba. Amma zata kasance domin wanda ya yi tafiya a cikinta. Ba wawan da zai bi ta kanta.9Ba zakin da zai kasance a wurin, ba wata muguwar dabba da zata kasance a kanta; ba za a same su ba a can, amma fansassu ne za su yi tafiya a can.
10Baratattun Yahweh za su komo za su taho suna waƙa zuwa Sihiyona, madawwamin farinciki zai kasance a kansu; murna da farinciki za su mamaye su; baƙinciki da ajiyar zuciya za su shuɗe.

36

1A shekara ta goma sha huɗu ta sarki Hezekiya, Senakerib sarkin Asiriya, ya tasar wa dukkan biranen Yahuda da kagararsu ya kuma kame su.2Sai sarkin Asiriya ya aika da babban shugaban soja daga Lakish zuwa Yerusalem ga sarki Hezekiya tare da babban soja. Ya gabaci dai-dai magudanar kwarin da ya ke kawo ruwa, a babbar hanyar filin da masu wankin tufafi suka tsaya a kanta.3Shugabannin Isra'ilawa waɗanda suka fito wajen birnin su yi magana da su su ne Hilkiya ɗan Iliyakim, shugaba mai kula da fãda, Shebna sakataren sarki, da Yowa ɗan Asaf, wanda ke rubuta matakan gwamnati.

4Sai shugaban sojoji yace da su, "Ku faɗawa Hezekiya babban sarki, sarkin Asiriya, yace, 'Me kake dogara da shi?5Ka na maganganun wofi marar amfani, cewa akwai shawara da ƙarfin yaƙi. To yanzu ga wa kake dogara? Wane ne ya baka ƙarfin zuciya da za ka yi mani tawaye?
6Duba, kana dogora da Masar, da tsabgar da kake amfani da ita a matsayin sandar tafiya, amma duk mutumin da ya dogara da ita, zai karye ya soke hannunsa. Wannan shi ne Fir'auna sarkin Masar zai yiwa dukkan wanda ya dogara gare shi.7Amma idan ka ce da ni, "Mu na dogara ga Yahweh Allahnmu," ba shi ne wanda ya ke a manyan wurare da bagadai Hezekiya ya ɗauke, ya kuma ce Yahuda da Yerusalem, '"Dole ku yi sujada a wannan bagadi a Yerusalem ba"?
8Saboda haka yanzu, zan ba ka abu mai kyau daga maigidana sarkin Asiriya. Zan ba ka dawakai dubu biyu, idan har za ka iya samin masu hawansu.
9Ya ya zaka iya kaucewa ko ɗaya daga cikin barorin shugabana? Kana sa dogara ga karusai da mahaya dawakai na Masar!10To yanzu, na tafi can ba tare da Yahweh ba in tasar wa wannan ƙasar, har in lalatar da ita? Yahweh yace da ni, "Ka faɗawa wannan ƙasar har ka lalatar da ita.'""
11Sa'an nan Iliyakim ɗan Hilkiya, da Shebna, da Yowa suka ce da babban shugaba, "Ka yi magana da barorinka a cikin harshen Aremiyanci, Aremaik, domin muna gane shi. Kada ka yi magana da mu da harshen Yahuda a kunnuwan mutane waɗanda suke a kan garu."12Amma babban kwamanda ya ce, "Babban sarki ya aiko ni ga shugabanku kuma ya faɗi waɗannan maganganu? Ba ya aiko ni ga jama'ar da suke a kan garu ba, waɗanda za su ci kashinsu su kuma sha fitsarinsu tare da ku ba?"
13Sai shugaban sojoji ya tsaya ya tada murya da ƙarfi a cikin Yahudanci, cewa, "Ku saurari magana daga babban sarki, sarkin Asiriya.14Sarki yace, 'Kada ku yarda Hezekiya ya ruɗe ku, shi ba zai iya cetonku ba.15Kada kuma ku bari Hezekiya ya saku ku dogara ga Yahweh, cewa, '"Yahweh zai tabbatar da cetonku; wannan birni ba za a bada shi a hannun sarkin Asiriya ba.'"
16Kada ku saurari Hezekiya, domin wannan shi ne abin da sarkin Asiriya yace: 'Ku nemi salama tare da ni kuma ku fito wuri na. Sai kowannenku ya ci daga cikin 'ya'yan inabin gonarsa, daga kuma itacen ɓaurensa, ya kuma sha ruwa daga rijiyon kansa.17Za ku yi wannan har saina zo na ɗauke ku zuwa wata ƙasa mai kama da irin ta ku, ƙasa mai hatsi da sabuwar inabi, ƙasa ta gurasa da kuringar inabi.'
18Kada ku bar Hezekiya ya ruɗe ku, cewa, 'Yahweh zai kuɓutar da ku.' Ko akwai wasu allolin mutanen da suka cece su daga hannun sarkin Asiriya?19Ina allolin Hamat da na Arfad? Ina allolin Sefarwayim? Sun ceci Samariya daga ikona?20A cikin dukkan allolin waɗannan ƙasashe, akwai wani da ya ceci ƙasarsa daga ikona, ya ya kuke ganin kamar Yahweh zai ceci Yerusalem daga ikona?
21Amma mutane suka tsaya tsit ba bu kuma wanda ya maida martani, don umarnin sarki, "Kada ku amsa masa."22Sai Iliyakim ɗan Hilkiya, wanda ya ke bisa iyalin, Shebna marubuci, da Yowa ɗan Asaf mai kula da tarihi, suka zo wurin Hezekiya da tufaffinsu a kekkece, kuma suka faɗa masa maganganun da shugaban mayaƙa ya faɗa.

37

1Ya zamana a lokacin da sarki Hezekiya ya ji abin da suka faɗa, ya kekkece tufafinsa, ya rufe jikinsa da tsummoki, ya kuma shiga gidan Yahweh.2Ya aika Iliyakim, mai kula da fada, da Shebna marubucin shari'a, da dattawa firistoci, dukkansu suka rufe jikinsu da tsummoki, zuwa wurin Ishaya ɗan Amoz, annabi.

3Suka ce da shi, "Hezekiya yace, 'Wannan rana ce ranar wahala da wulaƙanci da kunya, mun zama kamar lokacin da za a haifi yaro, amma uwar ba ta da ƙarfin da zata haifi yaron.4Watakila Yahweh Allahnka zai ji maganganun shugaban mayaƙansa, wanda sarkin Asiriya uban gidansa ya aiko domin ya wulaƙanta Allah mai rai, ya kuma tsawata wa maganganu waɗanda Yahweh Allahnka ya ji. Yanzu sai ka yi addu'a domin ringin da har yanzu suna nan.'"
5Sa'ad da barorin sarki Hezekiya suka zo wurin Ishaya,6sai Ishaya yace da su, "Ku faɗawa ubangidanku: 'Yahweh yace, "Kada ku ji tsoron irin maganganun da kuka ji, waɗanda dasu barorin sarkin Asiriya suka wulaƙanta ni.7Duba, zan sa ruhu a cikinsa, zai kuma ji jita-jitar da zata sa ya koma ƙasarsa. Zan sa shi ya faɗi ƙasa da takobi a cikin ƙasarsa.'"'
8Sai shugaban mayaƙan ya koma ya kuma sami sarkin Asiriya yana yaƙi da Libna, domin ya ji sarki ya tafi daga Lakish.9Sa'ad da Senakerib ya ji Tirhaka sarkin Kush da Masar sun haɗu domin su yi yaƙi da shi, sai kuma ya aika da manzanni zuwa wurin Hezekiya tare da saƙo:10"Ka ce da Hezekiya, sarkin Yahuda, 'Kada ka bari Allahnka wanda kake dogara da shi ya ruɗe ka, cewa, 'Yerusalem ba zata faɗa hannun sarkin Asiriya ba."
11Ku gani, ku kuma ji abubuwan da sarakunan Asiriya suka yiwa dukkan ƙasashe ta wurin lalata su ga baki ɗaya. Kuna tsammani za ku kuɓuta?12Ko allolin al'ummai sun kuɓutar da su, al'umman da ubannina suka lalata akwai Gozan, da Haran, Rezef, da kuma mutanen Iden a Tel-assa?13Ina sarkin Hamat, da sarkin Arfad, da sarkin biranen Sefarwayim, da Hena, da kuma Iwwa?'"
14Hezekiya ya karɓi wannan wasiƙar daga hannun manzannin ya kuma karanta ta. Sai ya shiga gidan Yahweh ya baza ta gabansa.15Hezekiya ya yi addu'a ga Yahweh:16"Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, kai da ka zauna a sama da kerubim, kai kaɗai ne Allah a kan dukkan mulkokin duniya. Kai ka yi sammai da duniya.
17Ka juyo da kunnuwanka, Yahweh, ka ji mu. Buɗe idanuwanka, Yahweh, ka gani, ka kuma ji maganar Senakerib, wanda ya aika don ya yi ba'a ga Allah mai rai.18I' gaskiya ne, Yahweh, sarakunan Asiriya sun lalata dukkan al'ummai da ƙasashensu.
19Suka sa allolinsu a cikin wuta, domin su ba alloli ba ne amma ayyukan hannunwan mutane ne, itace da dutse ne kawai.20Saboda haka Asiriyawa sun lalata su. Yanzu dai, Yahweh Allahnmu, ka cece mu daga ikonsa, saboda dukkan mulkokin duniya su sani kai kaɗai ne Yahweh."
21Sai Ishaya ɗan Amoz ya aika da saƙo wurin Hezekiya, cewa, "Yahweh, Allah na Israila yace, 'Domin ka yi addu'a gare ni a kan Senakerib sarkin Asiriya,22wannan ita ce maganar da Yahweh ya faɗa a kansa: "Akwai budurwar yariya ta Sihiyona ta rena ka kuma tana yi maka dariyar ba'a; budurwar Yerusalem tana girgiza kanta gare ka.23Wa ka rena ka kuma ci mutunci sa? Gãba da wa ka ɗaga muryarka, ka kuma ɗaga idanuwanka na girmankai? Gãba da Mai Tsarki na Isra'ila.
24Ta wurin barorinka ka rena Ubangiji ka kuma ce, 'Da yawan karusaina har na kai ƙololuwar duwatsu, zuwa tsayin Lebanon. Zan sare dogayen itatuwan sida dana sifuros zaɓuɓɓu, na kuma kai wurare mafi nisa, na jeji mafi 'ya'ya.25Na gina rijiyoyi na kuma sha ruwa; Na busar da dukkan kogunan Masar ƙarƙashin sawayena.'
26Baka ji yadda na ƙudura a yi haka tuntuni kuma na aiwatar tun zamanin ḍã? Yanzu ne nake cikawa. Kana nan ne domin ka mai da birane gagara-shiga zuwa tulin kango.27Mazaunan su, masu ƙaramin ƙarfi, sun warwatse da kunya. Sun zama tsire-tsire a gona, ɗanyar ciyawa, ciyawar dake kan rufi ko a fili, kafin iskar gabas.
28Amma na san zaman ka, da fitar ka, da kuma zuwan ka, na san yadda ka harzuƙa gãba da ni.29Domin harzuƙar ka ta gãba da ni, kuma don girmankanka ya iso kunnuwana, zan sa ƙugiya a hancinka, linzami na kuma a bakinka; zan komar da kai hanyar da ka biyo."
30Wannan ita ce zata zama alama domin ka: A wannan shekara zaku ci gyauro, a kuma shekara ta biyu zaku shuka daga abin da ya tsiro daga gauron. Amma a shekara ta uku dole zaku yi shuka ku kuma girɓe shi, ku dasa kuringar inabi ku kuma ci 'ya'yanta.
31Su da suke ringi na gidan Yahuda da waɗanda kuma suka tsira za su sake kafuwa su haifi 'ya'ya.32Domin daga Yerusalem ringin za su fito; daga Dutsen Sihiyona waɗanda suka tsira za su zo. Himmar Yahweh mai runduna zai yi wannan.'"
33Saboda Yahweh ya faɗi wannan a kan sarkin Asiriya: "Ba zai shiga wannan birnin ba kuma ba zai harba kibiya a nan ba. Ba zai zo gare shi ba tare da garkuwa ko ya kafa sansanin tudu gãba da ita.34Ta hanyar da ya zo ta hanyar kuma zai koma; ba zai shiga wannan birni ba - wannan furcin Yahweh ne.
35Zan kare wannan birnin zan kuma ceto shi, domin ni kaina da kuma bawa na Dauda."
36Sai mala'ikan Yahweh ya fito ya fãɗa wa sansanin Asiriyawa, ya kashe sojoji 185,000. Da mutanen suka tashi da sassafe, sai suka ga jukunan matattu a kwakkwance ko'ina.37Senakerib sarkin Asiriya ya ƙyale Isra'ila ya koma gida ya zauna a Nineba.
38Daga bisani, yayin da ya ke sujada a gidan Nisrok allahnsa, 'ya'yansa Adramelek da Shareza suka kashe shi da takobi. Sai suka tsere zuwa ƙasar Ararat. Isahadon ɗansa ya yi sarauta a matsayinsa.

38

1A kwanakin da Hezekiya ya ke ciwo har ya kusa mutuwa. Sai Ishaya ɗan Amoz, annabi, ya zo wurinsa, ya ce masa, "Yahweh yace, 'Ka kintsa komai dai-dai a gidanka; gama mutuwa za ka yi, ba za ka rayu ba,'"2Sai Hezekiya ya juya ya sa fuskarsa a bango ya yi addu'a ga Yahweh.3Ya ce, "Idan ka yarda Yahweh, ka tuna yadda na yi tafiya a gabanka da dukkan zuciyata da aminci, yadda na yi abin da ke dai-dai a idanunka." Sai Hezekiya ya yi kuka da ƙarfi.

4Sai maganar Yahweh ta zo wurin Ishaya, cewa,5"Tafi ka ce da Hezekiya, shugaban mutanena, 'Wannan shi ne abin da Yahweh, Allah na Dauda kakanka, ya ce: Na ji addu'arka, na kuma ga hawayenka. Duba, ina shirin ƙara maka shekaru goma sha biyar nan gaba.6Daga nan zan cece ka da wannan birnin daga hannun sarkin Asiriya, kuma zan kãre wannan birni.
7Wannan zai zama alama a gare ka daga Yahweh, zan yi abin da na alƙawarta.8Duba, zan komar da inuwa baya da taki goma na hawan benen Ahaz. Saboda haka inuwa ta koma baya da taki goma a kan hawan benen inda ta yi gaba.
9Wannan ita ce rubutacciyar addu'ar Hezekiya sarkin Yahuda, lokacin da ya ke rashin lafiya daga nan kuma ya warke:10"Na ce tsakanin ƙarshen rayuwata zan koma daga ƙofofin Lahira; zan ƙarashe sauran shekaru a can.11Na ce ba zan ƙara ganin Yahweh, Yahweh a cikin ƙasar rayayyu ba; ba kuma zan ƙara duban wani mutum ko mazaunan duniya ba.
12An datse raina an kuma tafi da shi daga gare ni kamar rumfar makiyayin tumaki; na naɗe raina kamar gado; kana sare ni daga masaƙa; tsakanin rana da dare zaka ƙarar da raina.13Na yi ta kuka har gari ya waye; kamar zaki yana kakkarya dukkan ƙasussuwana. Tsakanin rana da dare kana ƙarashe raina.
14Kamar muryar ƙaramin tsuntsu; na yi kuka kamar kurciya; idanuna sun gaji don dubar sama. Ubangiji, an matsa mani; ka taimake ni.15Me zan iya faɗa? Ya yi magana da ni, ya yi haka, zan yi tafiya a hankali dukkan shekaruna sabili da baƙinciki ya rinjaye ni.
16Ubangiji, wahalolin daka aiko suna da kyau a gare ni; ka dawo mani da raina; ka maido mani da raina da kuma lafiyata.17Domin amfani na ne na ji irin wannan baƙincikin. Ka cece ni daga kududufin hallaka; domin ka jefar da dukkan zunubaina bayanka.
18Gama Lahira ba ta yi maka godiya; mutuwa ba ta yabonka; waɗanda suka tafi can cikin rami ba za su bege cikin amincinka ba.19Mutum mai rai, mutum mai rai, shi ne zai iya yi maka godiya, kamar yadda na ke yi a wannan rana, uba yana bayyanawa 'ya'ya irin amincinka.
20Yahweh yana kusa da ceto na, za mu kuma yi buki tare da kaɗe-kaɗe da waƙoƙi dukkan ƙwanakin ranmu cikin gidan Yahweh."
21Yanzu Ishaya yace, "Bari su ɗauki 'ya'yan ɓaure su cura a kuma sa shi akan marurun, zai kuma warke."22Hezekiya kuma ya ce, "Me zai zama alama da yasa zan iya zuwa gidan Yahweh?"

39

1A wannan lokacin sai Maduk-Baladan ɗan Baladan, sarkin Babila, ya aika da wasiƙu tare da kyauta ga Hezekiya; domin ya ji cewa Hezekiya ya yi ciwo ya kuma sami lafiya.2Hezekiya kuwa ya ji daɗin waɗannan abubuwa; har ya kuma nuna wa manzannin ɗakin dukiyarsa - wato su azurfa, da zinariya, da kayan yaji, da mai mai daraja, da daƙin kayayyakinsa na yaƙi, da dukkan abin da ke cikin gidansa. Babu sauran wani abu da ya ke da shi a gidansa, ko cikin dukkan mulkinsa, wanda Hezekiya bai nuna masu ba.

3Sai Ishaya annabi ya zo wurin sarki Hezekiya ya kuma tambaye shi, "Me waɗannan mutane suka ce da kai? Daga ina suka zo?" Hezekiya yace, "Sun zo wuri na daga ƙasa mai nisa ta Babila."4Ishaya ya yi tambaya, "Me suka gani a gidanka?" Hezekiya ya amsa, "Sun ga dukkan abin da ya ke a gidana. Babu wani abu mai daraja da ban nuna masu ba."
5Sai Ishaya yace da Hezekiya, "Saurari maganar da Yahweh mai runduna:6'Duba, ranaku sun kusa zuwa da za a kwashe komai a fadarka, abubuwan da kakaninka suka tara har ya zuwa yau, za a ɗauke su zuwa Babila. Ba abin da za a rage, in ji Yahweh.
7'Ya'ya da aka haifa maka, waɗanda kai ka haife su - za a ɗauke su, kuma za su zama bãbãnni a fadar sarkin Babila.'"8Sai Hezekiya ya cewa Ishaya, "Maganar Yahweh wadda ka faɗa tana da kyau." Domin ya yi tunani, "Za a sami salama da kwanciyar rai a zamanina."

40

1"Ta'aziya, ta'azanta mutanena," in ji Allahnka.2"Yi magana mai taushi ga Yerusalem; ka yi mata shela cewa yaƙinta ya zo ƙarshe, laifofinta kuma an gafarta mata, za ta sami ruɓi biyu daga hannun Yahweh domin dukkan zunubanta."

3Wata murya ta koka, "A cikin jeji shirya hanyar Yahweh; a shirya ta miƙaƙƙiya a cikin Hamada doguwar hanya domin Allahnmu."4Kowanne kwari zai cika, za a baje kowanne tsauni da tudu; ƙasa mai kwazazzabai kuwa za ta zama sumul, wurare kuma masu gargada za su zama sarari;5kuma ɗaukakar Yahweh zata bayyana, dukkan mutane kuwa za su gan shi tare; gama bakin Yahweh ne ya faɗi haka.
6Wata murya na cewa, "Yi kuka." Wata ta amsa, "Kukan me zan yi?" "Dukkan yan adam ciyawa ne, dukkan alƙawarinsu da amincinsu kamar furannin jeji.7Ciyawa ta kan bushe, furanni kuma su yanƙwane sa'ad da numfashin Yahweh ya hura a kansu; ba bu shakka mutane ciyawa ne.8Hakika ciyawa ta kan bushe, furanni kuwa kan yi yaushi, amma maganar Allahnmu zata tsaya har abada."
9bisa tsauni mai tsayi, Sihiyona, mai ɗauke da labari mai daɗi. Ki yi kuwwa da ƙarfi, yaYerusalem. Ke da kika kawo labari mai daɗi, daga muryarki, kada kuwa ki ji tsoro. Ki faɗa wa biranen Yahuda, "Ga Allahnku!"10Duba, Ubangiji Yahweh yana zuwa kamar mayaƙi mai nasara, damtsensa mai ƙarfi zai yi masa mulki. Ga shi, da sakamako tare da shi, kuma waɗanda ya ceto sun sha gabansa.
11Zai ciyar da garkensa kamar makiyayi, zai tattara 'yan tumakin a damtsensa, ya kuma ɗauke su kusa da zuciyarsa, kuma a hankali zai bida tumaki masu shayar da nono.
12Wa ya taɓa auna ruwaye da tafin hannunsa, ko ya auna sararin sama da tafin hannunsa, ko ya iya riƙe ƙurar duniya a kwando, ko ya iya auna nauyi tsaunika a sikeli, ko tuddai a ma'auni?
13Akwai wanda zai iya fahimtar tunanin Yahweh, ko ya ba shi umarni a matsayin mashawarcinsa?14Daga wurin wa ya taɓa karɓar umarni? Wane ne ya koya masa yadda zai yi abubuwa, ya kuma koya masa sani, ko ya nuna masa hanyar fahimta?
15Duba, al'ummai na kamar digon ruwa a bokiti, kuma suna kama da ƙura a sikeli; duba, yana auna tsibirai kamar ɗan ɗigo.16Lebanon bata da isasshen fetur, ko dabbobin dajinta ba su isa baikon konawa ba.17Dukkan al'ummai ba isassu ba ne a gare shi; an ɗauke su ba a bakin komai bane a gare shi.
18Da wa za ka iya ƙwatanta Allah? To da wanne gunki za ka kamanta da shi?19Gunki! Masassaƙi ne ya yi shi: makera suka dalaye da zinariya kuma suka sa shi cikin abin da suka yi da azurfa.20Domin miƙa baiko wani ya zaɓi itacen da ba zai ruɓe ba; ya nemi ƙwararren maƙeri da zaya yi masa siffar gunkin da ba zaya fãɗi ba.
21Ashe ba ka sani ba? Ashe ba ka ji ba? Ba a faɗa maka ba tun daga farko? Ba ka fahimta ba tun daga fara kafa harsashin duniya?22Shi wanda ya ke zaune a bisa bangon duniya; mazaunanta suna kama da fãri a gabansa. Ya miƙar da sammai kamar labule kuma ya baza su kamar rumfa domin a zauna ciki.
23Yana maida masu mulki ba komai ba kuma yana maida masu mulkin duniya yadda ba a san da zamansu ba.24Suna kama da dashe kasafai, dashen da a ka shuka kasafai, dashen da bai yi ko saiwar da ta shiga ƙasa ba, sa'ad da ya hura a kansu sai su yi yaushi, kuma iskar ta hure su kamar ƙaiƙayi.
25"To, da wane ne za a kwatanta ni, ko akwai wani mai kama da ni?" in ji shi Mai Tsarki.26Dubi sararin sama a bisa! Wane ne ya halicce dukkan waɗannan taurarin? Shi ne wanda ya ke masu jagora kuma ya kira su bisa ga sunan kowa. Ta wurin ikonsa da girmansa da kuma ta wurin karfi da iko, ba ko ɗayansu da ya ɓace.
27Me ya sa kuka ce, Yakubu, kuma kuka ce, Isra'ila, "Hanya ta a ɓoye take daga Yahweh, kuma Allahna bai damu da baratarwata ba"?28Ba ku sani ba? Ba ku kuma ji ba? Madawwamin Allah, Yahweh, shi ne mahaliccin ƙarshen duniya, ba ya taɓa jin gajiya ko kasala ba; ba shi da iyakar fahimta.
29Yana ƙarfafa masu jin gajiya; masu kasala kuma ya kan sabunta ƙarfinsu.30Duk da matasa ma sukan ji kasala da gajiya, samari kuma sukan yi tuntuɓe su faɗi:31Amma waɗanda suke dogara ga Yahweh zai sabunta ƙarfinsu; za su tashi da fikafikai kamar gaggafa; za su yi gudu kuma ba za su gaji ba; za su yi tafiya amma ba za su suma ba.

41

1"Ku yi shiru ku kasa kunne gare ni, ku manisantan ƙasashe; bari ƙasashe su sabunta ƙarfinsu; bari su matso kusa su yi magana; bari mu taru ga yin jayayya a kan saɓanin.2Wane ne wannan da ya motso wani daga gabas, ana kiransa cikin adalci ga aikinsa? Ya bada ƙasashe a gare shi ya kuma taimaka masa har ya yi nasara a kan sarakuna. Ya maida su ƙura da takobinsa, kamar ciyawar da iska ta hure da bakansa.

3Yana biye da su har ma ya wuce lafiya, da sauri ƙwarai da ƙyar ƙafarsa take taɓa ƙasa.4Wane ne yasa wannan ya faru kuma su wane ne suka yi waɗannan ayyuka? Wane ne ya kirawo tsararraki tun daga farko? Ni, Yahweh, na farko, da na ƙarshe, Ni ne shi.
5Tsibirai sun gani kuma sun ji tsoro; ƙarshen duniya ta girgiza; sun nufo har sun zo.6Kowanne ya taimaki makwabcinsa, kowanne kuma ya cewa ɗayan, 'Yi ƙarfin hali.'7Masassaki yana ƙarfafa maƙerin zinariya, kuma wanda ya ke aiki da guduma yana ƙarfafa shi wanda ya ke aiki da tubalin ƙarfe, haka nan ya ke cewa mai walda, yana da kyau.' Suna buga ƙusoshi masu ƙarfi domin kada su tuntsure,
8Amma kai, Isra'ila, bawana, Yakubu wanda na zaba, zuriyar Ibrahim abokina,9kai wanda na kawo ka daga maƙurar duniya, kuma wanda na kira daga wurare masu nisa, wanda na ce, 'kai ne bawana,' Na zaɓe ka ban kuma ƙi ka ba.
10Kada ka ji tsoro, ina tare da kai. Kada ka damu da komai, ni ne Allahnka. Zan ƙarfafa ka, zan kuma taimake ka, zan tallafe ka da hannunna na dama mai adalci.
11Duba, za su ji kunya da ƙasƙanci, dukkan su da suke fushi da kai; za su zama ba komai ba za su kuma lalace, waɗannan da suke gãba da kai.
12Za ka neme su amma ba za ku same su ba; wato waɗanda suke gãba da kai; za su zama kamar ba komai ba, ba bu shakka za su zama ba komai ba.13Gama Ni, Yahweh Allahnku, zan riƙe ka da hannun dama, ina faɗi maka, 'Ka da ka ji tsoro; ina taimakonka.'
14Kada ka ji tsoro, kai tsutsa Yakubu, da ku mutanen Isra'ila; zan taimake ku - wannan furcin Yahweh ne, mai fansarku, Mai Tsarki na Isra'ila.15Duba, zan sa ku zama kamar ceburin sussuka mai kaifi, sabo mai baki biyu; za ku sussuke tsaunuka ku lalatar da su; za ku niƙe tuddai kamar ƙaiƙayi.
16Za ku sheƙesu, iska kuma zata hure su; iska kuma zata warwatsa su. Za ku yi murna cikin Yahweh, za ku yi murna a cikin Mai Tsarki na Israi'la.
17Waɗanda ake takurawa da mabuƙata za su nemi ruwa, amma ba bu, harsunansu za su bushe da ƙishi; Ni Yahweh, zan amsa addu'arsu; Ni Allah na Isra'ila, ba zan yashe su ba.18Zan sa kogunan ruwa su yi gudu daga gangare, maɓuɓɓugan ruwa su yi gudu a tsakiyar kwarurruka; zan sa hamada ta zama kududdufan ruwa, busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓuɓɓugan ruwa.
19Zan sa itatuwan sida, da gawo su tsiro a jeji, da itacen ci-zaƙi, da itacen zaitun. Zan dasa siferas a hamada, tare da marke da wuraren renon itacen siferas.20Zan yi wannan domin mutane su gani, su sani, su kuma fahimta tare, hannun Yahweh ya yi wannan, Mai Tsarki na Isra'ila ya halitta shi.
21"Faɗi maganarka," Inji Yahweh, "Faɗi jayayyarka mai kyau don gumakunka," inji Sarkin Yakubu.22Bari ku kawo ma na jayayyarku; ku zo ga ba ku furta ma na abin da da zai faru, saboda mu san waɗannan abubuwa sosai. Ku sa su faɗa mana yadda furcin za su zama, domin mu yi tunani a kansu mu kuma san yadda su ka cika.
23Ku faɗa game da abubuwan da za su faru nan ga ba, domin mu san ko ku alloli ne; ku yi wani abu mai kyau ko bala'i, ko ma cika da jin tsoro ya kuma burgemu.24Ku duba, ku allolin wofi ne kuma ayyukan kuma na wofi ne; wanda ya zaɓe ku ma abin ƙyama ne.
25Na ta da wani daga arewa, kuma ya zo; daga fitowar rana na kira shi wanda ya yi kira bisa sunana, wanda zai tattake masu mulki kamar laka, kamar yadda maginin tukwane ya ke tattake yumɓu.26Wa ne ne ya faɗa ma na wannan tun daga farko, ko ma sani? Kafin wannan lokaci, ko mu ce, "Ya yi dai-dai"? Babu ɗayansu da ya yi dokar haka, i, ba kuwa wanda ya ji kuna faɗar wani abu.
27Ni ne na farko da na ce da Sihiyona, "Duba ga su a nan;" Na aika manzo zuwa Urshalima.28Sa'ad da na duba, ba bu wani, ko ma a cikinsu wanda zai ba da shawara mai kyau, wanda idan Na yi tambaya, zai iya amsawa da magana.29Duba, dukkansu a wofi su ke, ayyukansu na wofi ne; zubin siffofinsu na ƙarfe adadin iska su ke, wofi ne kuma.

42

1Duba, bawana, wanda na riƙe; zaɓaɓɓena, wanda na ke jindaɗin sa. Na sa Ruhuna a bisansa; za ya kawo hukunci ga al'ummai.2Ba za ya yi kuka ko sowa ba, ko ya sa a ji muryarsa a tituna ba.

3Murzajjen kara ba za ya karya shi ba, lagwanin da ba ya ci sosai ba za ya ɓice shi ba: a cikin aminci za ya zartar da hukunci.4Ba za ya suma ba ko ya karaya har sai ya kafa hukunci a duniya; Ƙasashen tsibirai kuma suna jiran shari'arsa.
5Ga abin da Allah Yahweh ya faɗa - shi wanda ya halicci sammai kuma ya shimfiɗasu, shi wanda ya yi duniya da dukkan abin da take fitarwa, shi wanda ya ke bayar da numfashi ga mutanen dake cikin ta da kuma rai ga waɗanda ke zaune a cikin ta:6"Ni, Yahweh, na kira ka cikin adalci kuma zan ri ƙe hannunka. Zan kiyayeka in sanya ka alƙawari domin mutane, haske kuma ga al'ummai,
7Domin a buɗe idanun makafi, za a sako da 'yan kurkuku daga can cikin kogo da kuma waɗanda aka tsare a gidan tsaro waɗanda ke zaune a cikn duhu.
8Ni ne Yahweh, sunana kenan; bazan raba ɗaukakata da wani ba ko yabona da sassaƙaƙƙun gumaka.9Duba, abubuwan da suka wuce sun faru, yanzu ina gaf da furta sabobbin al'amura. Kafin su fara afkuwa zan gaya maku game da su."
10Ku raira sabuwar waƙa ga Yahweh, da kuma yabonsa daga ƙarshen duniya; ku waɗanda ke gangarawa zuwa teku, da dukkan abin da ke ciki, ƙasashen tsibirai da dukkan mazaunan cikin su.11Bari hamada da biranenta su koka, ƙauyuka kuma inda keda ke zaune, ku yi sowa ta farinciki! bari mazauna Sela su raira; bari su yi sowa daga ƙololuwar tsaunuka.
12Bari su bada ɗaukaka ga Yahweh su kuma furta yabonsa a ƙasashen tsibirai.13Yahweh za ya fita a matsayin mayaƙi; a matsayin mutumin yaƙi za ya motsa himmarsa. Za ya yi sowa, I, za ya yi kururuwar koke-koken yaƙinsa; za ya nuna wa maƙiyansa ikonsa.
14Na yi shiru na dogon lokaci; na tsaya cik na hana kaina; yanzu zan yi kuka kamar macen dake cikin naƙuda; zan yi nishi da huci.15Zan rusar da tsaunuka da tuddai in kuma sa ganyayensu su bushe; zan maida koguna tsibirai in kuma sa lakarsu su bushe.
16Zan kawo makafi bisa hanyar da ba su sani ba; bisa tafarkun da ba su san zan bi da su ba. Zan mayarda duhu ya zama haske a gabansu, zan sa karkatattun wurare su miƙe. Zan yi waɗannan abubuwa, ba kuma zan yashe su ba.
17Za a komar da su baya, za a san ya su cikin kunya gabaɗaya, wato su waɗanda suka sa dogararsu ga sassaƙaƙƙun siffofi, su waɗanda suke cewa sarrafaffun siffofin ƙarfe, "Ku ne allolinmu."
18Ka saurara, kai kurma; ka duba, kai makaho, domin ka sami gani.19Wane ne makaho idan ba bawana ba? ko kurma kamar manzona wanda na aika? Wane ne ya yi makantar abokin alƙawarina, ko makaho kamar bawan Yahweh?
20Kana ganin abubuwa da yawa, amma baka fahimta; kunnuwa a buɗe, amma ba bu mai ji.21Ya gamshi Yahweh ya yabawa hukuncinsa kuma yasa shari'arsa a bar ɗaukaka.
22Amma waɗannan mutane ne waɗanda a ka yiwa fashi a ka kuma washe su; an datse su dukka a ramuka, sun zama abin washe wa ba bu kuma mai fansarsu, ba bu wanda kuma ya ce, "A maido da su!"
23Wane ne a cikin ku za ya saurari wannan? Wane ne za ya saurara kuma ya ji a nan gaba?24Wane ne ya miƙa Yakubu ga ɗan fashi, Isra'ila kuma ga masu kwasar ganima? Ba Yahweh bane, wanda muka yiwa zunubi, wanda suka ƙi tafiya cikin hanyoyinsa, wanda kuma suka ƙi yin biyayya da shari'arsa?
25Domin wannan ya zubo da fushinsa mai zafi a bisansu, da masifar yaƙi. Ya haska kewaye da su, amma ba su lura ba; ya ƙona su, amma ba su yi hattara ba a zukatansu.

43

1Amma yanzu ga abin da Yahweh ya faɗa, shi wanda ya halicceka, Yakubu, shi wanda ya yi ka, Isra'ila: "Kada ka ji tsoro, gama na fansheka; na kiraka da sunanka, kai nawa ne.

2Sa'ad da ka bi ta cikin ruwaye, zan kasance tare da kai; ta cikin koguna kuma, ba za su sha kanka ba. Sa'ad da ka yi tafiya ta cikin wuta ba za ka ƙone ba, harsashen wutar kuwa ba za ya lalatar da kai ba.3Gama ni ne Yahweh Allahnka, mai tsarki na Isra'ila, mai cetonka. Na ba da Masar diyya a kanka, Itiyofiya da Seba misanya dominka.
4Tunda kana da tamani da muhimmanci a idanuna, ina ƙaunarka; saboda haka zan bayar da mutane misanya dominka, wasu mutanen kuma misanya domin rayuwarka.5Kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai; zan kawo zuriyarka daga gabas, in tattaro ka daga yamma.
6Zan cewa arewa, 'Miƙosu,' kudu kuma, 'Kada ka riƙesu,' A kawo 'ya'yana maza daga ne sa, 'ya'yana mata kuma daga lungun sassan duniya,7dukkan wanda ake kira da sunana, wanda na halitta domin ɗaukakata, wanda na yi, I, wanda na halitta.
8Fito da mutane makafi, koda ya ke suna da idanu, da kuma kurame, koda ya ke suna da kunnuwa.9Dukkan al'ummai ku tattaru wuri ɗaya, dukkan mutane kuma ku taru. Wane ne a cikinsu za ya furta wannan, ya kuma yi mana shelar al'amuran farko? Bari su kawo shaidunsu su tabbatar da gaskiyarsu, bari su saurara su kuma tabbatar, 'Gaskiya ne.'
10Ku ne shaiduna," Yahweh ya furta, "Bawana kuma wanda na zaɓa, domin ku sani ku kuma gaskata da ni, ku kuma fahimci cewa ni ne shi. Kafin ni babu wani allah da a ka yi, kuma ba za ayi wani ba bayana.11Ni, ni ne Yahweh, kuma babu wani mai ceto sai ni.
12Na furta, na ceto, kuma na yi shela, kuma babu wani allah a tsakaninku. Kune shaiduna," Yahweh ya furta, '"Ni ne Allah.13Daga wannan rana har zuwa nan gaba ni ne shi, kuma babu wanda za ya ceci wani daga hannuna. Na aikata, wane ne za ya canza?"
14Wannan ne abin da Yahweh yace, Mai fansarku, Mai tsarki na Isra'ila: "Sabili da ku na yi aike a Babila na turasu dukka zuwa gudun hijira, na maida farincikin Babiloniyawa zuwa waƙoƙin makoki.15Ni ne Yahweh, Mai tsarkinku, Mahaliccin Isra'ila, Sarkinku."
16Wannan shi ne abin da Yahweh yace (Wanda ya buɗe hanya ta cikin teku da kuma tafarki ta cikin manyan ruwaye,17wanda ya bida karusa da doki, sojoji da babbar runduna. Suka faɗi tare; ba za su sake tashi ba; an kawar da su, aka ɓice su kamar lagwanin da ke ci.)
18Kada ku yi tunani akan waɗannan abubuwa da suka wuce, ko ku kula da abubuwan dã can.19Duba, ina gaf da yin sabon abu; yanzu ya fara faruwa; ba ku yi la'akari ba? zan yi hanya a hamada da magudanan ruwa a cikin jeji.
20Dabbobin jeji za su girmamani, diloli da jiminai, saboda na bayarda ruwa a jeji, da koguna a hamada, domin zaɓaɓɓun mutanena su sha,21waɗannan mutane waɗanda na yi su domin kaina, domin su maimaita yabbaina.
22Amma ba ku yi kira gare ni ba, Yakubu; kun gaji da ni, Isra'ila.23Ba ku kawo mani ko ɗaya daga cikin tumakinku ba a matsayin baye-bayen ƙonawa, ko kuka girmamani da hadayunku ba. Ban ɗora maku nauyin baye-bayen hatsi ba, ko na gajiyar daku da kawo turare.
24Ba ku sawo mani ƙiraren ƙanshi da kuɗi ba, ko kuwa ku zubo mani kitsen hadayunku ba; amma kuna ɗoramani nauyin zunubanku, kun gajiyar da ni da miyagun ayyukanku.
25Ni, I, Ni, Ni ne wanda na ke share kurakuranku sabili da ni; kuma bazan sake tunawa da zunubanku ba.26Ku tuna mani da abin da ya faru, bari mu yi mahawara tare; ku kawo ƙararku, domin a tabbatar da ku marasa laifi.
27Ubanku na farko ya yi zunubi, kuma shugabanninku sun yi mani laifi.28Saboda haka zan gurɓata tsarkakan shugabanni; zan miƙa Yakubu ga lalacewa ɗungum, Isra'ila kuma ga wulaƙantaccen ƙasƙanci."

44

1Ka saurara yanzu, bawana Yakubu, da Isra'ila, wanda na zaɓa:2Ga abin da Yahweh yace, shi wanda ya yi ka ya kuma nasa ka cikin mahaifa wanda kuma za ya taimake ka: "Kada ka ji tsoro, bawana Yakubu; da kai kuma, Yeshurun, wanda na zaɓa.

3Gama zan zubo da ruwa a bisa ƙasa mai ƙishi, da magudanan ruwa a bisa busasshiyar ƙasa; zan zubo da Ruhuna a bisa zuriyarku, da albarkata a bisa 'ya'yanku.4Za su tsiro daga cikin ciyawa, kamar itatuwan kurmi dake gefen magudanan ruwa.
5Wani za ya ce, 'Ni na Yahweh ne,' wani kuma za ya yi kira ga sunan Yakubu, wani kuma zaya rubuta a kan hannunsa, 'Na Yahweh ne,' ya kuma raɗawa kansa suna da sunan Isra'ila."
6Wannan ne abin da Yahweh yace - Sarkin Isra'ila da mai fansarsa, Yahweh mai runduna: "Ni ne farko, ni ne kuma ƙarshe; babu kuma wani Allah sai ni.
7Wane ne kamar ni? bari ya yi shela kuma ya yi mani bayanin al'amuran da suka afku tunda na kafa mutanen dã, bari kuma su yi bayanin al'amuran da za su zo.
8Kada ku ji tsoro ko ku firgita. Ba na furta maku ba tuntuni, na kuma shelarda shi? Ku ne shaiduna: Akwai wani Allah baya gare ni? Babu wani Dutse; bansan da wani ba."
9Dukkan masu sarrafa gumakai ba komai bane; abubuwan da suke jiwa daɗi wofi ne; shaidunsu basu gani ko sanin wani abu, kuma za a sa su sha kunya.10Wane ne za ya yi allah ko ya sarrafa gumaka da ke wofi?
11Duba, dukkan abokan tarayyar shi za su sha kunya; masu sassaƙa shi mutane ne kawai. Bari su ɗauki matsayinsu tare; za su noƙe kuma za a sa su sha kunya.
12Maƙeri na aiki da kayan aikinsa, ya yi su, ya zuga su a garwashi. Ya siffantashi da guduma ya aikatashi da ƙarfin damtsensa. Ya ji yunwa, ƙarfinsa ya ƙare; bai sha ruwa ba sai ya sume.
13Kafinta yana gwada katako da abin gwaji, za ya yi mashi zane-zane da abin salo. Da kayan aikinsa zai yi masa siffofi, ya zãne shi da abin zãne. zai yi shi siffa-siffa bisa ga siffar mutum, kamar mutum mai ban sha'awa, domin ya zauna a cikin gida.
14Yana saro itatuwan sida, ko ya zaɓo itatuwan sifares ko itacen rimi. Yana ɗaukowa kansa itatuwa daga jeji. Za ya dasa itacen fir ruwan sama kuma za ya sa ya yi girma.
15Sai mutum ya yi amfani da shi ya kunna wuta kuma ya ji ɗumi. I, yana kunna wuta ya gargasa gurasa. Daga ciki kuma yana ɗauka ya yi wa kansa allah sai ya rusuna masa; ya yi wa kansa gumaka kuma ya rusuna masa.16Daga cikin katakan yana yin amfani da wasu ya kunna wuta, ya kuma gasa nama a kai. Ya ci ya ƙoshi. yana ɗunɗuma kansa sai ya ce, "Ah, na ji ɗumi, na ga wutar."
17Sauran itatuwan da suka rage kuma sai ya yi allah da su, siffar da ya sassaƙa kuma; sai ya rusuna masa yana ba shi girma, sai ya yi addu'a gare shi yana cewa, "Cece ni, gama kai ne allahna."
18Ba su sani ba, balle kuma su fahimta, domin idanunsu makafine ba su kuma gani, kuma zukatansu ba su ganewa.
19Babu mai yin tunani, ko su yi nazari su ce, "Daga cikin katakon na yi abin wuta da wasu; I, kuma na gasa gurasa bisa garwashin. Na gasa nama bisa garwashin na ci. To ya ya zan ɗauki sauran katakon da ya rage in yi abin ƙazanta da shi domin sujada? Ya ya zan rusuna ga wani kututturen katako?"
20Ya yi kamar toka ya ke ci; ruɗaɗɗiyar zuciyarsa ta sa ya kauce. Baya iya ceton kansa, ko kuwa ya ce, "Wannan abin da ke hannun damana ba allahn gaskiya ba ne."
21Yi tunani a kan waɗannan abubuwa, Yakubu, da Isra'ila, domin kai bawana ne: na yi ka, kai bawana ne; Isra'ila bazan manta da kai ba.22Na share, ayyukan tawayenka sarai, kamar girgije mai kauri, kamar girgije kuma, zunubanka sun dawo mani, gama na fanshe ka.
23Ku raira, ku sammai, gama Yahweh ya yi wannan; ku yi sowa, ku zurfafan duniya. Ku fashe da waƙa, ku tsunuka, kai daji da duk itatuwan da ke cikinka; gama Yahweh ya fanshi Yakubu, kuma za ya nuna ɗaukakarsa a Isra'ila.
24Wannan ne abin da Yahweh yace, mai fansarka, wanda ya yi ka daga cikin mahaifa: "Ni ne Yahweh, wanda ya yi dukkan abubuwa, wanda shi kaɗai ya shimfiɗa sammai, shi kaɗai ya sarrafa duniya.25Ni wanda na lalata kayan tsafin masu maganar wofi na kuma wulaƙanta masu karanta kayan tsafin; Ni wanda na juyarda hikimar masu hikima na kuma maida shawararsu wawanci.
26Ni, Yahweh, wanda ke tabbatarda maganganun bawansa wanda kuma ke sa hasashen manzanninsa su afku, wanda ya cewa Yerusalem, 'Za a sake zaunawa a cikinki,' da kuma garuruwan Yahuda, 'Za a sake ginaku, kuma zan ɗaga rusassun wurarensu';27wanda ya ke cewa teku mai zurfi, 'Ki bushe, kuma zan busar da igiyoyinki.'
28Yahweh ne ya faɗa game da Sairus, 'Makiyayina ne shi, za ya aiwatar da dukkan nufina; za ya zartar da doka game da Yerusalem, 'Za a sake ginata,' game da haikalin, 'Bari a sake kafa harsashensa.'"

45

1Ga abin da Yahweh ya faɗi wa shafaffensa, ga Sairus, wanda nake riƙe da hannun damansa, domin inci ƙarfin al'ummai a gabansa, in tuɓe makaman sarakuna, in kuma buɗe ƙofofi a gabansa, domin ƙofofin su zauna a buɗe:

2Zan shiga gabanka in rusar da duwatsu; zan farfasa ƙofofin tagullar in kuma dardatse sandunan ƙarfensu,3zan baka taskokan duhu da kuma dukiyoyin da a ka ɓoye, domin ka sani cewa Ni ne, Yahweh, wanda ya kira ka da sunanka, Ni, Allah na Isra'ila.
4Saboda Yakubu bawana, da Isra'ila zaɓaɓɓena, na kira ka da sunanka: Ina baka daraja kaɗan, koda ya ke ba ka sanni ba.5Ni ne Yahweh, babu wani kuma; babu wani Allah sai ni. zan shirya ka domin yaƙi, koda ya ke ba ka sanni ba;6domin mutane susan cewa daga tasowar rana, daga kuma yamma, cewa babu wani allah sai ni: Ni ne Yahweh, babu kuma wani.
7Ni na yi haske kuma na halicci duhu; Ina kawo salama in kuma ƙirƙiro bala'i; Ni ne Yahweh, wanda ke yin dukkan waɗannan abubuwa.8Ku sammai, ku kwararo ruwa daga sama! bari sararin sammai su kwararo da adalci. Bari duniya ta shanyesu, domin ceto ya tsiro, da adalci kuma su yi girma tare. Ni, Yahweh, na halicce su dukka.
9Kaiton duk wani wanda ke gardama da wanda ya halicce shi, ga wanda ya ke kamar kowacce tukunyar yunɓu a cikin tukwanen yunɓu a ƙasa! yunɓun za ya iya cewa mai yin tukwanen, 'Me kake yi?' ko 'Aikin naka baya da abin riƙewa a jikinsa'?
10Kaiton wanda za ya cewa Mahaifi, 'Mahaifin wa kake yi?' ko kuwa ga mace, 'Me kike haihuwa?'
11Ga abin da Yahweh yace, Mai Tsarki na Isra'ila, Mahaliccinka: 'Me yasa kake tambayoyi game da abin da zan yi domin 'ya'yana? zaka gaya mani abin da zan yi game da aikin hannuwana?'
12Ni na yi duniya kuma na halitta mutum a kanta. Hannuwana ne suka shimfiɗa sammai, kuma na umarci dukkan taurari su bayyana.
13Na motsa Sairus cikin adalci, kuma zan miƙar da tafarkunsa dukka. Zai gina birnina; za ya bar mutanena 'yan gudun hijira su koma gida, ba kuma da farashi ba ko cin hanci,'" Yahweh mai runduna ya faɗa.
14Ga abin da Yahweh ya faɗa, "Za a kawo maku cinikayyar Masar da fataucin Itiyofiya tare da Sabiyawa, mutane masu doguwar siffa. Za su zama naku. Za su biyo ku, tafe cikin sarƙoƙi. Za su rusuna a gabanku suna roƙonku suna cewa, 'Tabbas Allah na tare daku, babu kuma wani sai dai shi.'"15Hakika kai ne Allah wanda ka ɓoye kanka, Allah na Isra'ila, Mai ceto.
16Dukkansu za su kunyata su wulaƙanta tare; masu sassaƙa gumakai za su yi tafiya cikin ƙasƙanci.17Amma Yahweh za ya ceci Isra'ila da madawwamin ceto; ba za ku sake shan kunya ba ko ƙasƙanci.
18Ga abin da Yahweh ya faɗa, shi wanda ya halicci sammai, Allahn gaskiya wanda ya ƙirƙiro duniya, ya halittata, ya kafa ta. Ya halittata, ba a matsayin jujiba, Ya zãna ta domin a zauna a cikinta: "Ni ne Yahweh, babu wani kuma.
19Ban yi magana a asirce ba, a wani ɓoyayyen wuri; Ban cewa zuriyar Yakubu, 'Ku neme ni a wofi ba!' Ni ne Yahweh, Mai yin magana a gaskiya; Ina furta abubuwan da ke dai-dai.
20Ku tattaro kanku ku zo! ku taru wuri ɗaya, ku 'yan gudun hijira daga cikin al'ummai! basu da Ilimi, su waɗanda ke ɗaukar sassaƙaƙƙun siffofi su kuma yi addu'a ga allolin da ba su iya ceto.
21Ku zo kusa ku furta mani, ku kawo shaida! bari su yi mugun shirinsu tare. Wane ne ya nuna wannan tundã can? Wane ne ya yi shelar shi? Ba Ni ne ba, Yahweh? Babu wani Allah sai dai ni, Allah baratacce Mai ceto kuma; babu wani baya gare ni.
22Ku juyo gare ni ku sami ceto, ku dukkan ƙarshen duniya; gama Ni ne Allah, babu wani kuma.23Na yi rantsuwa da kaina, maganar dokar adalci tawa, kuma ba za ta koma baya ba: 'A gare ni kowacce gwiwa zata durƙusa kuma kowanne harshe za ya rantse.
24Za su ce mani, "A cikin Yahweh ne kawai akwai ceto da ƙarfi kuma.""' Ma su jin haushina kuma za su sha kunya.25A cikin Yahweh dukkan zuriyar Isra'ila za su barata; za su yi taƙama a cikinsa.

46

1Bel ta rusuna, Nebo ta sunkuya; an ɗauke gumakansu a bisa dabbobi da bisashen ɗaukar kaya. Waɗannan gumakai da kuka ɗauko kaya ne masu nauyi a bisa dabbobin da suka gaji.2Gaba ɗaya sun sunkuya ƙasa, durƙushe a ƙasa; basu iya fanso siffofin, su kansu kuma sun tafi cikin bauta.

3Ku saurareni, gidan Yakubu, dukkanku ragowar gidan Isra'ila, waɗanda nake ɗauke daku tun kafin a haifeku, a ɗauke tun daga mahaifa.4Har zuwa tsufanku Ni ne shi, kuma zan ɗaukeku har sai gashinku ya zama furfura. Na halicceku kuma zan riƙeku; zan ɗaukeku kuma zan fansheku.
5Da wa za ku kwatantani? da wa kuke tunanin na yi kama, domin ku kwatantamu?6Mutane sukan zubo da zinari waje daga Jaka sukan kuma gwada azurfa a bisa ma'auni. Sai su yi hayar maƙeri, sai ya narka ya yi masu allah; sai su rusuna su kuma yi mashi sujada.
7Za su ɗagashi su ɗora a kafaɗa su ɗaukeshi; sai su ajiye a wurin zamansa, zai tsaya a wurin zamansa ba kuma zai matsa daga wurin ba. Za su yi kuka zuwa gare shi, amma ba za ya iya amsawa ba ko kuwa ya ceci wani daga matsalarsa.
8Ku yi tunani game da waɗannan abubuwa; kada ku yi watsi dasu, ku fitsararru!9Ku yi tunani game da abubuwan farko, na lokutan da suka wuce, gama Ni ne Allah, babu wani kuma, Ni ne Allah, babu wani kama da ni.
10Ina sanar da ƙarshen tun daga farko, tukunna kuma abin da bai riga ya faru ba; Na faɗa, "Shirina za ya faru, kuma zan yi yadda nake so."11Na kira tsuntsun ganima daga gabas, mutumin dana zaɓa kuma daga ƙasa mai nisa; I, na faɗa; Zan kuma aiwatar da shi; ina da manufa, zan kuma aikata.
12Ku saurareni, ku mutane marasa ji, waɗanda ke nesa da yin abin dake dai-dai.13Ina kawo adalcina kusa; baiyi nisaba, kuma cetona baya jira; zan bada ceto kuma ga Sihiyona kyauna kuma ga Isra'ila.

47

1Sauko ki zauna cikin turɓaya, ke budurwa ɗiyar Babila; zauna ƙasa babu kursiyi, ɗiyar Kaldiyawa. Baza a sake kiranki mai kwarjini da taushi ba.2‌Ɗauki dutsen niƙa ki niƙa gari; kware lulluɓinki, ki tuɓe doguwar rigarki, buɗe ƙafafunki, ki tsallake rafuffuka.

3Za a buɗe tsiraccinki, I, za a ga kunyarki: I zan ɗauki fansa kuma bazan bar kowa ba.4Mai fansarmu, Yahweh mai runduna sunansa, Mai tsarki na Isra'ila.5Ki zauna shiru ki tafi cikin duhu, ke ɗiyar Kaldiyawa; domin ba za a sake kiranki sarauniyar masarautai ba.
6Na yi fushi da mutanena; na lalata gãdona na miƙasu cikin hannunki, amma ba ki nuna masu jinƙai ba; ki ka ɗora kaya mai nauyi bisa tsofaffin mutanen.7Ki ka ce, "Zan yi mulki har abada a matsayin sarauniya ni kaɗai." ba ki yi la'akari da abubuwannan ba a zuciyarki, ba ki kuwa duba yadda za su kasance ba.
8To yanzu saurari wannan, ke da kika ƙaunaci annashuwa kika zauna a tsare; ke da kika ce a zuciyarki, "Zan wanzu, babu kuma wani kamar ni; Bazan taɓa zaunawa kamar gwauruwa ba, ko in taɓa fuskantar rashin 'ya'ya ba."9Amma abubuwan nan biyu za su zo maki a lokaci guda a rana ɗaya: rashin 'ya'ya da gwauranci; da cikakken ƙarfi za su afko maki, duk da sihirinki da surkullen ki masu yawa da layunki.
10Kin dogara ga muguntarki; ki ka ce, "Babu mai gani na"; hikimarki da iliminki sun kai ki ga hallaka, amma kika ce a zuciyarki, "Na wanzu, babu kuma wani kama da ni."11Bala'i za ya afko maki; ba za ki iya korar shiba da surkullenki. Lalacewa zata faɗo maki; ba za ki iya kawar da ita ba. Babbar hasara zata afko maki nan da nan, kafin ki farga.
12Ki yi naciya wurin zuba magungunanki da sihirorinki mãsu yawa waɗanda kika yi aminci wurin nanatawa tun cikin kuruciyarki; watakila za ki yi nasara, watakila za ki kori bala'in.13Kin gaji da yawan zuwa wurin bokayenki; bari su waɗannan mutanen su tashi su ceceki - su waɗanda ke shawagi a sammai suna duba taurari, waɗanda ke furta sabobbin watanni - bari su ceceki daga abin da zaya faru dake.
14Duba, za su zama kamar haki, wuta za ta cinye su. Ba za su ceci kan su ba daga cikin harsashen. Babu garwashin da za su ji ɗumi dashi babu kuma wutar da za su zauna a gefe!15Ga abin da za su zama a gare ki, su waɗanda kika yi aiki tare da su, kika yi saye da sayarwa tare da su da ki na yarinya, dukkansu kuma su ka ci gaba da aikata abubuwansu na wawanci; da kika yi kukan neman taimako kuma, ba bu wanda zai iya ƙwato ki."

48

1Ku saurara, ya gidan Yakubu, waɗanda a ke kira da suna Isra'ila, waɗanda kuma kuka fito daga tsatson Yahuda; ku da kuka yi rantsuwa da sunan Yahweh kuka kuma tono Allahn Isra'ila, amma bada gaske ba ko kuma ta hanyar adalci.2Domin suna kiran kansu mutanen birni mai tsaki masu dogara kuma ga Allahn Isra'ila. Yahweh mai runduna ne sunansa.

3Na furta abubuwa tunda daɗewa; sun fito daga bakina, na sa a sansu, sai nan da nan kuma na yi su, su ka kuma kasance.4Saboda na sani ku masu taurinkai ne, tsokar wuyanku ta cije kamar karfe, goshinku kuma kamar tagulla,5domin wannan na furta waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na sanardaku, domin kada ku ce, 'Gunkina ya yi wannan,' ko kuwa 'Sassaƙaƙƙen siffana ko sarrafaffen siffar ƙarfena ya ƙaddara waɗannan abubuwa.'
6Kun ji game da waɗannan abubuwa; ku duba dukkan alamunnan; kuma ku, ba za ku yarda da cewa abin da na faɗi gaskiyane ba? Daga yanzu zuwa nan gaba, zan nunamaku sabobbin abubuwa, ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.7Yanzu, ba daga baya ba, za su kasance, kuma kafin yau ba ku taɓa ji game da su ba, saboda haka ba za ku iya cewa, 'I, na san da su ba.
8Ba ku taɓa ji ba; ba ku sani ba; ba a bayyana abubuwan nan a kunnuwanku ba kafin yanzu. Domin na san ku macutane sosai, kuma ku masu taurinkai ne tunda a ka haife ku.
9Sabili da sunana zan yi jinkirin fushina, domin darajata kuma zan dakata daga lalatar daku.10Duba, na tãce ku, amma ba kamar azurfa ba; Na tsarkakeku cikin garwashin azaba.11Sabili da kaina, sabili da kaina zan aiwatar; domin tayaya zanbar sunana ya wulaƙanta? ba zan bayar da ɗaukakata ga wani dabam ba.
12Ku saurareni, Yakubu, da Isra'ila, wanda na kira: Ni ne shi; Ni ne farko, Ni ne kuma ƙarshe.13I, hannuna ya kafa harsashen duniya, hannun damana kuma ya shimfiɗa sammai; Idan na yi kira gare su, suna tashi tsaye tare.
14Ku tattara kanku, dukkanku, ku saurara! wane ne a cikinku ya yi shelar waɗannan abubuwa? Wanda Yahweh ya zaɓa za ya cika nufinsa a kan Babila. Za ya aiwatar da nufin Yahweh a kan Kaldiyawa.15Ni, na faɗa, I, na kiraye shi, na kawo shi, kuma za ya yi nasara.
16Ku zo kusa da ni, ku saurari wannan: Tun daga farko ban yi magana a asirce ba; sa'ad da ya faru, ina nan." Yanzu Ubangiji Yahweh ya aike ni, da Ruhunsa kuma.
17Ga abin da Yahweh, Mai fansarku, Mai tsarki na Isra'ila ya faɗa, "Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ke koya maku yadda za ku yi nasara, wanda ke bida ku a hanyar da za ku bi.18Inda ace kawai kunyi biyayya da dokokina! da salamarku da wadatarku sun malala kamar kogi, cetonku kuma kamar raƙuman teku.
19Da yawan zuriyarku yakai kamar rairayi, 'ya'ya kuwa daga mahaifarku kamar ƙwayoyin rairayi; da baza a datse sunansu ba ko kuwa a gogesu daga gabana.
20Ku fito daga Babila! ku tsere daga Kaldiyawa! da ƙarar kuka mai ƙaraurawa ku yi shelar shi! ku sanar da wannan, ku sa ya bazu zuwa iyakar duniya! Ku ce, 'Yahweh ya fanshi bawansa Yakubu.'
21Ba su ji ƙishi ba da ya bida su ta cikin jeji; Ya sa ruwa ya kwararo daga dutse dominsu; Ya fasa dutse, ruwayen kuwa suka ɓulɓulo.22Babu salama ga mugu - inji Yahweh."

49

1Ku saurare ni, ku dake gaɓar tekuna! ku kasa kunne gare ni, ku manisantan mutane. Yahweh ya kira ni tun da a ka haife ni da suna na, sa'ad da mahaifiyata ta kawo ni cikin duniya.2Ya maida bakina kamar takobi mai kaifi; ya ɓoye ni a inuwar hannunsa; ya maida ni gogaggiyar kibiya; a cikin kwarinsa ya ɓoye ni.

3Ya ce mani, "Kai bawana ne, Isra'ila, wanda ta wurinka ne na nuna ɗaukakata."4Amma sai na ce, "Koda ya ke nayi zaton nayi aiki a banza, na ɓata karfina a banza, duk da haka adalcina yana ga Yahweh, kuma sakamakona na gun Allahna."
5Yanzu Yahweh ya yi magana - wanda ya sifanta ni daga haihuwata in zama bawansa, za ya maida Yakubu kuma gare shi, domin a tattaro Isra'ila zuwa gare shi, gama an ɗaukaka ni a gaban Yahweh, kuma Allahna ya zama ƙarfina -6sai ya ce, "Abu mafi ƙanƙanta kai ka zama bawana da zan sa ya sake kafa kabilun Yakubu, ya kuma farfaɗo da tsirarrun Isra'ila. Zansa ka zama haske ga Al'ummai, domin ka zama cetona ga duk karshen duniya."
7Wannan ne abin da Yahweh yace, mai 'Fansar Isra'ila, Mai Tsarkin Nan nasu, gare shi wanda a ka rena ransa, al'ummai suka ƙi shi, da kuma barorin masu mulki, "Sarakuna za su ganka su miƙe, kuma "hakimai za su ganka su rusuna, saboda Yahweh mai aminci ne, wato Mai Tsarkin nan na Isra'ila, wanda ya zaɓe ka."
8Ga abin da Yahweh ya faɗi, "A lokacin dana shirya nuna tagomashina zan ba ka amsa, kuma a ranar ceto zan taimake ka; zan yi maka kariya, in kuma bada kai a matsayin alƙawari domin mutanen, domin a sake gina ƙasar, a kuma sake raba gãdon da ya lalace.
9Za ka cewa 'yan kurkuku, 'Ku fito waje;' ga waɗanda ke ramuka masu duhu, 'Ku nuna kanku.' Za su yi kiwo a hanyoyi, kuma dukkan sararin gangare zai zama makiyayarsu.
10Ba za su ji yunwa ko ƙishi ba, ko kuwa zafi ko rana ta buge su, domin shi mai yi masu jinƙai zai jagorance su; zai bishe su har ga maɓulɓulan ruwa.11Daga nan zan sa dukkan tsaunuka su zama hanya, in kuma sa karafku su zama miƙaƙƙu."
12Duba, waɗannan za su zo daga nesa, waɗansu daga arewa da yamma; waɗansu kuma daga ƙasar Sinim.13Ku yi waƙa, sammai, da murna, duniya; fashe da waƙoƙi ku duwatsu! Gama Yahweh zai ta'azantar da mutanensa, ya kuma ji tausayin nãsa masu tsanancin wahala.
14Amma Sihiyona ta ce, "Yahweh ya yashe ni, kuma Ubangiji ya manta da ni."15Mace za ta iya mantawa da jaririnta, da ke shan nononta, har ta rasa jin tausayin ɗan da ta haifa? I, za su iya mantawa, amma Ni ba zan manta daku ba.
16Duba, na zana sunanki a tafin hannuwa na; katangunki na gabana a kowanne lokaci.17'Ya'yanki suna dawowa da sauri, yayin da waɗanda suka lalatar dake suna watsewa.18Duba kewaye ki gani, suna tattarowa suna zuwa gare ki. Lallai hakika idan ina raye - wannan Yahweh ne ya faɗa -za ki sa su kamar kayan ado, ki kuma sanya su kamar amarya.
19Koda shi ke ke lalatacciya ce kuma kufai, ƙasa ce da dã a ka hallakar, yanzu za ki yiwa mazaunan ƙasar ƙanƙanta, kuma masu takura maki za su yi nisa dake.20'Ya'yan da a ka haifa a lokacin da a ka yi maki rashi za su faɗa a kunnuwanki, 'Wurin ya yi mana ƙanƙanta, a yi mana ƙãri, saboda mu zauna a nan.'
21Sa'an nan za ki tambayi kanki, 'Wane ne ya haifi waɗannan 'ya'yan domina? An yi mani rashi kuma ni bakarariya ce, mai gudun hijira da sakakkiya ni ke. Wane ne ya yi renon waɗannan yaran? Duba, ni kaɗai a ka bari; daga ina waɗannan suke?"'
22Wannan ne abin da Ubangiji Yahweh yace, "Duba, Zan tayar da hannuna ga al'ummai; Zan tayar da tutar alamata ga mutane. Za su zo da 'ya'yanki maza a hannuwansu su kuma taho da 'ya'yanki mata a kafaɗunsu.
23Sarakuna za su zama kamar ubanninki, kuma sarauniyoyinsu kamar masu renonki; za su rusuna maki da fuskokinsu ƙasa suna lasar ƙurar ƙafafunki; kuma za ki san cewa ni ne Yahweh; waɗanda suke jira na ba za su kunyata ba."
24Za a iya karɓe ganima daga jarumi, ko a ƙubutar da kamammu daga 'yan ta'adda?25Amma ga abin da Yahweh yace, "I, za a karɓe kamammun daga jarumi, kuma a washe ganimar; Gama zan yi tsayayya da magabcinki in kuma ceci 'ya'yanki.
26Zan ciyar da masu tsananta maku da naman jikinsu; kuma za su bugu da jininsu, kamar a ce ruwan inabin ne. Sai dukkan 'yan adam su sani cewa Ni, Yaweh, ne mai cetonku da mai fansarku, Maɗaukaki na Yakubu."

50

1Wannan ne abin da Yahweh ya faɗi, "Ina takardar saki da na saki mahaifiyarku? ga waɗanne masu bina bashi na sayar daku? Duba, an sayar daku domin laifofinku ne, domin kuma tayarwarku, a ka kori mahaifiyarku.

2Me yasa na zo amma babu kowa a wurin? Me yasa na yi kira amma babu wanda ya amsa? Hannu na ya gajarce ga fansar ku ne? Ko babu iko a gare ni da zan ƙuɓutar da ku? Duba, ga tsautawata na busar da teku; na maida koguna hamada; kifayensu suka mutu domin rashin ruwa suka ruɓe.3Na suturtar da sararin sama da duhu; Na rufe shi da tsummoki."
4Ubangiji Yahweh ya bani harshe kamar na ɗaya daga cikin waɗanda a ka koyar dasu, saboda in yi maganar ƙarfafawa ga gajiyayyu; yana farkar da ni daga safiya zuwa safiya; ya kan tasar da kunnena ga saurarawa kamar waɗanda a ka koyar dasu.
5Ubangiji Yahweh ya buɗe kunne na, kuma ban zama mai tayarwa ba, ban kuma koma baya ba.6Na bada bayana ga masu bugu na, kuncina kuma ga masu tuge mani gemu; ban ɓoye fuskata ba daga ayyukan ban kunya da tofa miyau ba.
7Gama Ubangiji Yahweh zai taimake ni; saboda haka ba zan wulaƙanta ba; don haka na maida fuskata kamar dutsen ƙyastawa, domi na san ba zan kunyata ba.
8Shi wanda zai yi mani adalci yana kusa, Wane ne zai yi jayayya da ni? Bari mu tsaya mu fuskanci juna. Wane ne mai tuhuma ta? Bari ya zo kusa da ni.9Duba, Ubangiji Yahweh zai taimake ni. Wane ne zai furta ni mai laifi ne? Duba za su koɗe kamar tufafi; ƙwaro mai cin kaya zai cinye su ɗungum.
10Wane ne a cikinku ke tsoron Yahweh? Wane ne ke biyayya da muryar bawansa? Wa ke tafiya a cikin zurfafan duhu ba tare da haske ba? Sai ya dogara da sunan Yahweh ya kuma jingina ga Allahnsa.
11Ku duba, dukkan ku masu kunna wuta, masu tanadawa kansu cociloli: ku yi tafiya cikin hasken wuta da harsunan wutar da kuka kunna. Wannan ne abin da ku ka karɓa daga gare ni: za ku kwanta a wurin azaba.

51

1Ku saurare ni, ku da ke biɗar ayyukkan adalci, ku dake neman Yahweh: Ku dubi dutsen da aka sassaƙo ku da kuma mahaƙar duwatsu inda aka yanko ku.

2Ku duba Ibrahim, mahaifinku, da Saratu wadda ta haife ku; gama tun yana mutum guda, na kirawo shi, na albarkace shi na maida shi mai yawa.
3I, Yahweh zai ta'azantar da Sihiyona; zai ta'azantar da dukkan kufanta; jejinta ya maida kamar gonar Iden, kuma sararin hamadarta a gefen kogin Yodan ya maida kamar lambun Yahweh; za a sami farinciki da murna a cikinta, godiya, da ƙarar waƙa.
4Ku kasa kunne gare ni, mutane na; ku kuma saurare ni mutane na. Gama zan zartar da doka, kuma zan sa hukuncina ya zama haske domin al'ummai.5Adalci na ya kusato; ceto na zai fito, kuma hannu na zai hukunta al'ummai; ƙasashen kurmi za su jira ni; domin damtsena za su jira ni da ɗoki.
6Ku ɗaga idanuwanku ga sararin sama, sai ku kalli duniya a ƙasa, gama sammai za su ɓace kamar hayaƙi, duniya za ta shuɗe kamar tufa, kuma mazaunanta za su mutu kamar ƙudaje. Amma cetona zai ci gaba har abada, gama adalcina ba zai taɓa daina aiki ba.
7Ku saurare ni, ku da kuka san abin da ya ke dai-dai, ku dake da dokokina a zukatanku: kada ku ji tsoron zage-zagen mutane, ko ku karaya saboda wulaƙancinsu.8Gama ƙwaro mai cin kaya zai cinye su kamar tufafi, tsutsa kuma ta cinye su kamar ulu; amma adalci na zai dawamma har abada, cetona kuma ga dukkan tsararraki."
9Farka, farka, ka suturtar da kanka da ƙarfi, damtsen Yahweh. Tashi kamar kwanakin dã, tsararraki na zamanan dã. Ba kai ba ne ka ragargaza Rahab, kai da ka soke dodon ruwa?10Ba kai ka busar da teku ba, ruwayen manyan zurfafa, ka kuma maida tsakiyar teku hanya domin wucewar tsararraki?
11Waɗanda Yahweh ya fansa za su dawo su zo Sihiyona tare da kukan farinciki tare kuma da murna har abada a kawunansu; kuma murna da farinciki za su mallake su, baƙinciki da makoki za su tsere daga gare su.
12Ni, Ni, ne shi wanda ke ta'azantar da ku. Me ya sa kuke tsoron mutane, waɗanda za su mutu, da 'ya'yan ɗan Adam, wanɗanda aka yi su kamar ciyawa?
13Donme ku ka mance da Yahweh wanda ya yi ku, wanda ya miƙar da sammai ya kuma kafa harsasan duniya? Kun kasance a cikin fargaba kowacce rana saboda zafin fushin mai zalunci sa'ad da ya shirya ya yi hallaka. Ina hasalar mai zaluncin?
14Wanda ya rusuna ƙasa, Yahweh zai hanzarta 'yantar da shi; ba zai mutu kuma ya je rami ba, ko ya rasa gurasa ba.15Gama Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ke motsa teku saboda raƙuman ruwa su yi ruri - Yahweh mai runduna ne sunan sa.
16Na sa maganata a bakinka, kuma na rufe ka da inuwar hannuna, domin in dasa sammai, in kafa harsasan duniya, in kuma cewa Sihiyona, 'ku mutanena ne.'"
17Farka, farka, tashi tsaye Yerusalem, ke da kika bugu a hannun Yahweh daga kwanon fushinsa; ke da kika bugu daga kwanon, har zuwa dago-dago daga ƙoƙon tangadi.18Babu kowa a cikin dukkan 'ya'yanta maza da ta haifa da zai yi mata jagora; babu kowa kuma daga cikin 'ya'yanta maza waɗanda ta rayar da su da zai riƙe hannunta.
19Waɗannan matsalolin biyu sun faru dake - wa zai yi makoki tare dake? - kaɗaici da hallaka, da yunwa da takobi. Wane ne zai ta'azantar dake?20'Ya'yanki maza sun some; suna kwance a kowacce kwanar tituna, kamar barewa a tarko; suna cike da fushin Yahweh, da tsautawar Allahnki.
21Amma yanzu ki ji wannan, ke da a ke muzguna wa ke bugaggiyar nan amma bada ruwan inabi ba22Ubangijinki Yahweh, Allahnki wanda ke kãriyar ki ya ce, "Duba, na ɗauki ƙoƙon tangaɗi daga hannun ki -kwanon, wadda shi ne ƙoƙon fushi na. domin kada ki sake shan sa kuma.
23Zan sa shi a hannun masu ba ki wuya, waɗanda suka ce maki, 'Ki kwanta a ƙasa don mu yi tafiya bisan ki; kin maida bayanki kamar ƙasar da a ke takawa, kamar kuma tituna domin su yi tafiya akai."

52

1Farka, farka, ki sa ƙarfinki, Sihiyona; ki sa sababbin tufafinki, Yerusalem, Birni mai tsarki, gama marasa kaciya da kazamtattu ba za su sake shigar ki ba.

2Girgiza kanki daga ƙura; tashi ki zauna, Yerusalem; cire sarƙa daga wuyanki, ɗaurarriya, ɗiyar Sihiyona.3Gama ga abin da Yahweh ya faɗi, "An sayar dake a banza, kuma za a fanshe ki ba tare da ƙuɗi ba."
4Gama ga abin da Ubangiji Yahweh ya faɗi, "Da farko mutane na zun je can Masar domin zama na 'yan kwanaki; Asiriya bada dadewa ba ta muzguna masu.
5Yanzu me nake da shi a nan - wannan furcin Yahweh ne - ganin an ɗauke mutane na babu dalili,? Waɗanda suke mulkinsu suka yi ba'a - Wannan furcin Yahweh ne - kuma aka ci gaba da saɓon suna na dukkan rana.6Saboda haka mutane na za su san sunana; za su sani a ranan nan cewa ni ne wanda ya ce, "I, Ni ne!"
7Yaya kyaun sawayen manzo mai kawo labarai ma su daɗi ya ke akan duwatsu, wanda ke shelar salama. wanda ke riƙe da saƙonni masu daɗi, wanda ya shelar ceto, wanda ya cewa Sihiyona, "Allahnki na mulki!"8Ki saurara! masu tsaronki sun ɗaga muryoyinsu, tare suna sowa don murna, gama za su gani, kowanne idonsu, dawowar Yahweh zuwa Sihiyona.
9Ku fashe da waƙoƙin farinciki tare, ku duk kufan Yerusalem; Gama Yahweh ya ta'azantar da mutanensa; ya fanso Yerusalem,10Yahweh ya buɗe damtsensa mai tsarki a gaban dukkan al'ummai; dukkan duniya za su ga ceton Allahnmu.
11Tafi, tafi, fita daga nan; kar ki taɓa wani kazamtaccen abu; tafi daga cikinta; ku tsarkake kanku, ku da ke ɗauke da taskokin Yahweh.12Gama ba za ku tafi a cikin hanzari ba, ko ku tafi a cikin fargaba ba; gama Yahweh zai tafi gabanku; kuma Allah na Isra'ila zai kasance a bayanku.
13Duba, bawana zai yi aiki da hikima; za ya zama da ɗaukaka sosai, kuma za a ɗaukaka shi,14Kamar yadda da yawa suka yi fargaba da kai - kamanninsa ya lalace fiye da kowanne mutum, kuma fasalinsa bai sake yin kama da wani abu na mutum ba.
15Duk da haka, bawa na zai yayyafa al'ummai masu yawa sarakuna kuma za su rufe bakunansu saboda shi. Gama abin da ba a taɓa faɗa masu ba, za su gani, kuma abin da ba su taɓa ji ba, za su gane.

53

1Wane ne ya gaskata da abin da ya ji daga gare mu, kuma ga wane ne aka bayyana hannun Yahweh?2Gama ya yi girma a gaban Yahweh kamar 'yar itaciya, kuma kamar tsiro daga cikin busasshiyar ƙasa; ba shi da wani kyakkyawan jamali ko daraja; sa'ad da muka ganshi, babu wani kyau da zai rinjaye mu.

3Mutane suka rena shi suka kuma ƙi shi; mutumin baƙinciki, kuma wanda ya saba da raɗaɗi. Kamar wanda mutane ke ɓoye fuskarsu daga gare shi; aka rena shi; muka kuma ɗauke shi ba a bakin komai ba.
4Amma tabbas ya sungumi cututtukanmu ya kuma ɗauke baƙincikinmu; duk da haka mun yi zaton cewa Allah ne ke hukunta shi, Allah ya mazge shi, ya kuma azabta.
5Amma an soke shi saboda ayyukan tayarwarmu; aka ragargaje shi saboda zunubanmu. Hukunci domin salamarmu ya kasance a kansa, kuma ta wurin raunukansa muka warke.
6Dukkanmu kamar tumaki muka bijire; kowannenmu ya juya zuwa hanyarsa, kuma Yahweh ya ɗora masa laifuffukanmu dukka.
7An muzguna masa; duk da haka sa'ad da ya ƙasƙantar da kansa, bai buɗe bakinsa ba; kamar ɗan ragon da za'a kai yanka, kuma kamar tumakin dake tsaye shiru a gaban masu sausaya, haka shi ma bai buɗe bakinsa ba.
8Ta wurin wulaƙantarwa da hukuntawa aka kayar da shi; wane ne daga wancan tsara ya sake yin tunani a kansa? Amma an datse shi daga ƙasar masu rai; saboda laifuffukan mutanena aka yanke masa hukunci.9Suka sa kabarinsa tare da ma 'yan ta'adda, tare da mai arziki a mutuwarsa, koda ya ke bai yi tawaye ba, ko kuwa wata ruɗarwa a bakinsa.
10Duk da haka, nufin Yahweh ne a murkushe shi a sa shi ciwo. Sa'ad da ya mai da kansa baiko domin zunubi, zai ga 'ya'yansa, zai daɗa tsawon kwanakinsa, kuma dalilin Yahweh zai cika ta wurinsa.11Bayan wahalar rayuwarsa, zai ga haske kuma ya gamsu da saninsa. Bawana mai adalci zai baratar da mutane da yawa; zai ɗauki laifuffukansu.
12Saboda haka zan ba shi nasa kason a cikin yawan mutane, kuma zai raba ganimar da mutane da yawa, domin ya sa kansa ga mutuwa, aka kuma ƙidaya shi tare da masu kurakurai. Ya ɗauki zunuban mutane da yawa ya kuma yi roƙo domin masu kurakurai.

54

1"Yi waƙa, ke bakarariya, ke da ba ki haihu ba; ki fashe da waƙar farinciki ki yi kuka da karfi, ke da ba ki taɓa yin naƙudar haihuwa ba. Gama 'ya'yan yasassa sun fi na matar da aka aura," inji Yahweh.

2Ki faɗaɗa girman rumfarki, ki baza labulen rumfarki da faɗi; bada ƙwauro ba; ki daɗa tsawon igiyoyinki; ki miƙar da dirkokinki,3Gama za ki bazu ta hannun dama da ta hagu, har sai zuriyarki sun mamaye al'ummai sun kuma sake kafa yasassun birane.
4Kada ki ji tsoro domin ba za ki ji kunya ba, ko ki karaya ba gama ba za a wulaƙanta ki ba; za ki mance da abin kunyar kuruciyarki da wulaƙancin yashewarki.
5Gama wanda ya Yiki shi ne mijinki; Yahweh mai runduna shi ne sunansa. Mai Tsarkin nan na Isra'ila shi ne mai Fansarki; Shi a ke kira Allahn dukkan duniya.6Gama Yahweh ya sake kirawo ki a matsayin matar da aka yasar da take kuma cikin ƙunci a ruhu. Kamar matar da a kuruciyarta aka aurota sa'an nan aka ƙi ta," inji Allahnki.
7Gama na yashe ki na ɗan lokaci kaɗan, amma da tausayi mai girma zan tattara ki.8A sa'ad da na yi fushi mai zafi, na ɓoye fuskata daga gare ki na wani lokaci; amma da madawwamin alƙawari aminci zan yi maki jinƙai - inji Yahweh, wanda ya ƙubutar dake.
9Gama wannan kamar ruwayen Nuhu ne a gare ni: kamar yadda na rantse cewa ruwayen Nuhu ba za su sake shan kan duniya ba, saboda haka na rantse cewa ba zan yi fushi dake ko in kwaɓe ki ba.10Koda shi ke tsaunuka za su iya faɗuwa kuma tuddai su girgizu, duk da haka madawwamiyar ƙauna ta ba zata rabu da ke ba, ko alƙawarin salamata ya girgiza ba - inji Yahweh, wanda ke yi maki jinƙai.
11Mai ƙunci, wanda guguwa ke kora kuma marar ta'aziyya, ku duba, zan sa shiryayyar hanya da dutsen tukoyis, in kuma kafa harsashenki da saffiyes.12Zan sa sorayenki da duwatsu masu ƙawa ƙofofinki kuma da duwatsu masu walƙiya, da kuma katangarki ta waje da kyawawan duwatsu.
13Sa'an nan Yahweh zai koyar da dukkan 'ya'yanku; kuma salamar 'ya'yanku zata yi yawa.14A cikin adalci zan sake kafa ku. Ba za ku ƙara fuskantar tsanantawa ba, gama ba za ku ji tsoro ba; kuma ba abin ban tsoro da zai yi kusa da ku ba.
15Duba, idan wani ya tada rikici, ba zai zama daga gare ni ba, duk wanda ya tada rikici da ku, za ku yi nasara a kansa.16Duba na halici maƙeri, mai hura garwashin wuta ya ƙera makamai na aikinsa, Ni kuma na hallici mai hallakarwa domin ya hallakar.
17Babu makamin da aka ƙera gãba da kai da zai yi nasara; kuma zan kayar da duk wanda ya tuhume ka. Wannan shi ne gădon bayin Yahweh, kuma kariyarsu daga gare ni take. wannan furcin Yahweh ne."

55

1Ku zo, kowannen ku dake jin kishin ruwa, ku zo wurin ruwan, ku da baku da kuɗi, ku zo, ku saya, ku ci, ku zo ku sayi ruwan inabi da madara kyauta da arha kuma.

2Me ya sa kuke auna azurfa domin abin da ba abinci ba, kuma me yasa kuke aiki domin abin da ba ya ƙosarwa? Ku saurare ni sosai ku ci abin dake da kyau, ku kuma yi farinciki cikin ƙoshi.
3Ku juyo da kunnuwanku ku zo gare ni! Ku saurara, domin ku rayu! Zan yi madawwamin alƙawari da ku - ingantacce, amintacciyar ƙauna dana alƙawarta wa Dauda,4Duba, na sashi a matsayin shaida ga al'ummai, a matsayin shugaba da mai ba da umarni ga mutane.
5Duba, za ku kira ga al'umman da baku san su ba; kuma al'umman da basu san ku ba za su rugo gunku saboda Yahweh Allahnku, Mai Tsarki na Isra'ila wanda ya ɗaukaka ku."
6Ku nemi Yahweh tun yana samuwa; ku yi kira gare shi tun yana kusa.7Bari mai mugunta ya bar tafarkinsa, haka nan mai zunubi ya bar tunane-tunanensa. Bari ya komo wurin Yahweh, sai ya yi masa jinƙai, da kuma Allahnmu wanda zai gafarta masa a yalwace.
8Gama tunane-tunanena ba dai-dai ne da tunane-tunanenku ba, kuma hanyoyinku ba dai-dai da nawa ba - wannan furcin Yahweh ne -9gama kamar yadda sammai ke nesa da duniya, haka hanyoyina ke nesa da taku, haka kuma tunane-tunanena ke nesa da tunane-tunanenku.
10Gama kamar yadda ruwa da ƙanƙara ke saukowa daga sama, kuma basu komawa sai sun jiƙa ƙasa, susa amfaninta su tsiro su bada 'ya'ya ga manomin da ya yi shuka ya kuma bada abinci ga mai ci,11haka nan ne maganata wadda ta fito daga bakina zata kasance - ba za ta komo gare ni a banza ba, amma zata yi nasara a kan abin da na aike ta ta aiwatar.
12Gama za ku fita da farinciki, a kuma jagorance ku a cikin salama; Tsaunuka da tuddai za su farfashe da murnar ihu a gabanku, kuma dukkan itatuwan filaye za su tafa hannuwansu.13A maimakon ƙayoyin saura, itatuwa masu ganyaye za su fito; kuma a maimakon itacen ƙaya, itacen ganye mai kyau zai fito, kuma zai zama domin Yahweh, domin sunansa, kamar madawwamiyar alama da ba za a tsige ba."

56

1Wannan shi ne abin da Yahweh ya faɗi, "Ku yi abin dake dai-dai; ku yi abin da ya kamata; gama cetona ya yi kusa, kuma adalcina na gaf da bayyana.2Mai albarka ne mutumin dake yin wannan, wanda kuma ya riƙe shi kam-kam. Ya kiyaye ranar Asabaci, ba ya ƙazamtata, yana kuma kiyaye hannunsa daga aikin mugunta."

3Kada bãƙon da ya zama mai bin Yahweh yace, "Yahweh zai tuge ni daga cikin mutanensa." Kada bãbã yace, "Duba, ni busasshen itace ne."
4Gama wannan ne abin da Yahweh yace, "Ga bãbãnni da ke kiyaye Asabataina kuma suna zaɓen abin dake faranta mani rai, su kuma riƙe alƙawaraina kam-kam,5dominsu ne zan kafa alama a cikin gidana da ganuwata abin tunawa da yafi samun 'ya'ya maza da mata. Zan ba su madawwamin abin tunawa da ba za a taɓa datsewa ba.
6Haka ma bãƙin da suka haɗa kansu da Yahweh - su ɓauta masa, waɗanda kuma suke son sunan Yahweh, su ɓauta masa, duk wanda ke lura da Asabaci, da wanda ke kãre kansa daga ƙazamta, da wanda ya riƙe alƙawari na kam-kam7- zan kawo su ga tsarkakken tsaunina in sa su yi farinciki a gidan addu'a ta; baye-bayensu na ƙonawa da hadayunsu za su samu karɓuwa a bagadina. Gama za'a kira gidana gidan addu'a domin dukkan al'ummai,
8Wannan ne furcin Ubangiji Yahweh, wanda ya tattara korarrun Isra'ila - Zan sake tattaro waɗansu in haɗa tare da su."
9Dukkanku namomin jeji na saura, ku zo ku lanƙwame, dukkan ku dabbobin cikin kurmi!10Dukkan matsaransu maƙafi ne, ba su fahimta ba. Su dukka karnuka dake shiru ne waɗanda ba su iya yin haushi. Suna mafarki, kuma a kwance suna ƙaunar yin barci.
11Karnukan na da babban marmarin ci; Ba za su taba samun abin da ya ishe su ba; su makiyaya ne da ba su da ganewa; dukkansu sun juya ga ta su hanya, kowannensu na ƙyashin mugun ribar kansa.12"Zo," suka ce "bari mu sha ruwan inabi da barasa mai karfi," Gobe zai zama kamar yau, rana mai girma fiye da yadda a ke tsammani."

57

1Adali ya hallaka, babu wanda ya kula, kuma mutanen amintaccen alƙawari sun taru a can, amma ba wanda ya gane cewa an ɗauke mai adalici ne daga mugunta.2Ya shiga cikin salama; suna hutawa a cikin gadajensu, waɗanda ke tafiya a cikin kamilcinsu

3Amma ku zo nan, ku 'ya'yan masu sihiri, 'ya'yan mazinaciya da matar da ta karuwantar da kanta. Wane ne kuke yi masa ba'a da murna?4Gãba da wa kuke buɗe bakunanku kuke gwalo? Ku ba 'ya'yan tayarwa ba ne, 'ya'yan zamba?
5Kuna ɗuma kanku ku da kuke kwance tare ƙarƙashin itacen rimi, ƙarƙashin kowanne koren itace, ku dake kashe 'ya'yanku a cikin rafuffukan da suka ƙone da ƙarƙashin duwatsu masu maratayi
6A cikin abubuwa masu laushi na rafin gangare su ne aka ba ku. Wato kayan ibadarku. Kun zuba ruwan baikon abin sha gare su kuka kuma ɗaga baikon hatsi. A waɗannan abubuwan ne ya kamata in ji daɗi?
7Kun shirya gadonku a ƙwanƙwolin tsauni; kun kuma tafi sama can domin ku miƙa hadayu.8A bayan ƙofa da ƙyaurayen kuka shirya alamunku; kun yashe ni, kun yi wa kanku tsiraici, sai kuka haura sama; kuka yi gadonku da faɗi. Kuka yi yerjejeniya da su; kuka ƙaunaci gadajensu; kuka ga tsiraicinsu.
9Kun tafi wurin Molek da mai; kun ruɓanɓanya turare. Kun aika jakadunku nesa; kun gangara zuwa Lahira.10Kun gaji saboda doguwar tafiyarku, amma ba ku taɓa cewa, "babu bege ba." Kun sami rai a hannuwanku; saboda haka ba ku karaya ba.
11Wane ne kuke damuwa dominsa? Wane ne kuke jin tsoronsa da yawa har ya sa kuka aikata abin ruɗi, harma kun manta da ni ko ku yi tunani akai na? Saboda na yi shiru na dogon lokaci, harma yanzu kun dena jin tsoro na.12Zan sanar da dukkan ayyukan adalcinku in kuma faɗi dukkan abin da kuka yi, amma ba za su taimake ku ba.
13Sa'ad'da kuka yi kũka, bari tarin gumakanku su 'yantar daku. Maimakon haka iska za ta ɗauke su dukka, wani numfashi zai ɗauke su dukka. Duk da haka wanda ya yi mafaka a cikina zai gaje ƙasar ya kuma mallaki tsarkakken tsaunina.
14Zai ce, 'Gina, gina! A shãre hanya! Cire dukkan abin sa tuntuɓe a hanyar mutanena!'"15Gama ga abin da mai girma maɗaukaki Kaɗai yace, wanda ke zaune har abada, wanda sunansa tsarki ne, "Ina zaune a maɗaukakin wuri mai tsarki, tare da shi kuma mai karyayye da ƙasƙantaccen ruhu, in falkar da ruhun masu ƙasƙantar da kai, in farkar da zuciyar masu tawali'u.
16Gama ba zan yi zargi har abada ba, ko in yi fushi har abada ba, domin ruhun mutum zai some a gabana, rayyukan dana halitta,17Saboda da zunubinsa na ribar ƙwãce, Na yi fushi, Na kuma hukunta shi; Na ɓoye fuskata na kuma yi fushi, amma ya koma da baya cikin hanyar zuciyarsa.
18Na ga hanyoyinsa, amma zan warkar da shi. Zan jagorance shi in kuma ta'azantar da shi in kuma ƙarfafa waɗanda ke makoki dominsa,19kuma ni na hallici diyan lebuna. Salama, salama, ga waɗanda ke nesa da na kusa - inji Yahweh - Zan warkar da su.
20Amma miyagu suna kama da haukan teku, wanda ba zai huta ba, kuma ruwayen suna amayar da taɓo da laka.21Babu salama domin mugu - inji Allah."

58

1Yi kuka da ƙarfi; kada ku dena. Ku ɗaga muryarku kamar kakaki. Ku ta'azantar da mutanena a kan tayarwarsu, da kuma gidan Yakubu a kan zunubansu.2Duk da haka suna nema na kullum suna kuma fahariya a sanin hanyoyina, kamar al'umma dake yin aɗalci da ba su yashe da dokokin Allahnsu ba. Suna tambayata hukuncin aɗalci; Suna jin daɗin tunani a kan Allah ya kusance su.

3Me yasa muka yi azumi,' suka ce, 'amma ba ka gani ba? Me yasa muka ƙasƙantar da kanmu, amma ba ka kula ba?' Duba, a ranar azuminku, kuna neman jin daɗinku kuna kuma danne dukkan ma'aikatanku,
4Duba, kuna azumi ku yi faɗace-faɗace, kuma ku bugu da hannun mugunta; ba za ku yi azumi yau wanda za ku sa a ji muryarku a sama ba.5Wannan shi ne lallai irin azumin da zan so: Ranar da wani zai ƙasƙantar da kansa, ya sunkuyar da kansa kamar ciyawa, kuma ya yafa tsummokara da toka a ƙarƙashinsa? Kun tabbata za ku kira wannan azumi, rana wadda ta gamshi Yahweh?
6Wannan ba shi ne azumin dana zaɓa ba: A saki miyagun sarƙoƙi, a kwance igiyoyin karkiya, a sa waɗanda aka ragargaza su sami 'yanci, a kuma karya kowacce karkiya?7Ko kuma ku raba gurasarku da mayunwata ku kuma shigo da marasa mazauni cikin gidanku ba?" Idan ku ka ga wani tsirara, sai ku suturtar da shi; kuma kada ku ɓoye kanku daga 'yan'uwa.
8Sa'an nan hasken ku zai faso a buɗe kamar fitowar rana, kuma warkewarku zata tsiro nan da nan; adalcinku zai sha gabanku, kuma ɗaukakar Yaweh zata biyo bayanku.
9Sa'an nan ne za ku yi kira, kuma Yahweh zai amsa; za ku yi kukan neman taimako, kuma zai ce, "Ga ni nan." Idan har kuka ɗauke daga tsakiyarku karkiya, da zargi, da maganganun mugunta,10idan ku da kanku kuka tanada wa mayunwata kuma kuka biya buƙatun gajiyayyu; sa'an nan ne haskenku zai keto daga cikin duhu, kuma duhunku zai zama kamar rana tsaka.
11Sa'an nan Yahweh zai jagoranceku a kullum kuma ya ƙosar da ku a wuraren da babu ruwa, ya kuma ƙarfafa ƙasusuwanku. Za ku zama kamar lambu mai laima, kuma kamar maɓulɓular ruwa, wanda ruwansa ba ya ƙarewa.
12Waɗansunku za su sake gina lalatattun kufaye; za ku tada kufayen tsararraki da yawa; za a kira ku "Masu gyaran Garu," "Masu maido da titunan da za a zauna."
13Dãma a ce kun juyo da ƙafafunku daga tafiya a ran Asabaci, kuma daga yin abin son ranku a ranata mai tsarki. Dãma a ce kun kira ranar Asabaci abin farinciki, kuma harma ku kira sha'anin Yahweh tsarki da martaba. Dãma a ce kun girmama ranar Asabacina wurin barin sha'anin kanku, ku kuma bar neman jin daɗin kanku da kuma kun ƙi faɗar maganganun kanku.
14Sa'an nan za ku yi farinciki cikin Yahweh; kuma zan sa ku yi yawo a ƙwalƙwolin duniya; zan ciyar daku daga gãdon Yakubu mahaifinku - gama bakin Yahweh ya faɗa."

59

1Duba, hannun Yahweh bai gajarce bada ba zai iya ceto ba; kunnensa bai kurmance ba, da ba zai iya ji ba.2Ayyukanku na zunubi, duk da haka, su suka raba ku daga Allahnku, kuma zunubanku sun sashi ya ɓoye fuskarsa daga gare ku daga kuma sauraronku.

3Gama hannayenku sun haramtu da jini kuma yatsunku da zunubi. Leɓunanku na faɗin ƙarya kuma harsunanku na faɗin tsokana.4Babu mai kira cikin aɗalci, kuma babu mai gudanar da ƙararsa cikin gaskiya. Suna dogara da maganganun wofi, suna faɗin ƙarairayi; Suna ɗaukar cikin masifa su kuma haifi zunubi.
5Suna ƙyanƙyashe ƙwayayen maciji mai dafi su kuma sãƙa yanar gizo-gizo. Duk wanda ya ci daga ƙwansu zai mutu, kuma idan aka fasa ƙwan, zai ƙyanƙyashe maciji mai dafi.6sãƙarsu ba za a iya yin tufafi da su ba, kuma ba za su iya rufe kansu da ayyukansu ba. Ayyukansu ayyukan zunubi ne, kuma ayyukan ta'addanci na cikin hannayensu.
7Kafafunsu na gudu gun mugunta, kuma suna gudu domin su zubar da jini. Tunaninsu tunanin zunubi ne; ta'addanci da hallakarwa ne hanyoyisu.8Ba su san tafarkin salama ba, kuma babu adalci a tafarkinsu. Sun ƙago karkatattun tafarkuna; Duk wanda ya yi tafiya kan waɗannan tafarku ba zai san salama ba.
9Saboda haka adalci ya yi nesa daga gare mu, kuma ayyukan adalci ba su kai wurinmu ba. Mun jira haske, amma muna ganin duhu; muna neman haske amma muna tafiya a duhu.10muna laluɓar bango kamar maƙafi, kamar waɗanda basu gani. Mu na yin tuntuɓe da rana kamar da asussuba; a cikin jarumai muna kama da matattun mutane.
11Muna ihu kamar damusai da makoki kamar kurciyoyi; muna jiran adalci amma babu ko ɗaya, domin kuɓutarwa, amma tana nesa da mu.
12Gama yawan zunubanmu suna gabanmu, kuma zunubanmu na shaida gãba damu; gama laifofinmu na tare damu, kuma mun san zunubanmu.13Mun yi tayarwa, muna musanta Yahweh kuma mun juya daga bin Allahnmu. Mun faɗi yaudara da juyin baya, mun ɗauki cikin gunaguni daga zuciya da maganganun ƙarya.
14An kori adalci baya, kuma ayyukan adalci sun tsaya nesa; gama gaskiya ta yi tuntuɓe a dandali, na gaske ba zai iya zuwa ba.15Aminci ya tafi, kuma wanda ya juya ga barin mugunta ya maida kansa abin zargi. Yahweh ya gani kuma bai ji daɗi ba cewa babu adalci.
16Ya ga babu wani mutum, ya kuma yi mamakin cewa babu wanda zai shiga tsakani. Saboda haka damtsensa ya kawo ceto dominsa, kuma ayyukan adalcinsa suka tallafe shi.
17Yasa ayyukan adalci su zamar masa sulke da ƙwalƙwalin ceto a kansa. Ya suturta kansa da rigunan ɗaukar fansa ya yafa himma ya zama alkyabbarsa.18Ya biya su gwargwadon abin da suka yi, hunkuncin fushi ga maƙiyansa, da ramako ga magabtansa, da kuma horo ga tsibirai wannan ne ladarsu.
19Saboda haka za su ji tsoron sunan Yahweh daga yamma, da ɗaukakarsa daga fitowar rana; gama zai zo kamar rafi mai kwararowa, wand numfashin Yahweh ke tunkuɗawa.20Mai fansa zai zo Sihiyona, da kuma ga waɗanda suka juyo daga ayyukan tayarwarsu cikin Yakubu - wannan furcin Yahweh ne.
21Ni dai, wannan shi ne alƙawari na da su - inji Yahweh - ruhuna wanda ya ke bisanku, da maganganuna waɗanda na sa a bakinku, ba za su bar bakinku ba, ko su fita daga bakin 'ya'yanku, ko su fita daga bakin 'ya'yan 'ya'yanku ba - inji Yahweh - daga wannan lokaci zuwa har abada."

60

1Tashi, haskaka; gama haskenki ya iso, kuma ɗaukakar Yahweh ta taso a bisanki.

2Koda shi ke duhu zai rufe duniya, kuma duhu mai kauri ga al'ummai; duk da haka Yahweh zai tashi bisanki, kuma za a ga ɗaukakarsa a bisanki.3Al'ummai za su zo ga haskenki, sarakuna kuma ga sheƙin haskenki dake tashi.
4Duba ko'ina ki gani. Suna tattarowa domin su zo gare ki. 'Ya'yanki maza za su zo daga nesa, kuma 'ya'yanki mata za su ɗaukosu a hannuwansu.5Sa'an nan za ki duba ki cika da farinciki, kuma zuciyarki zata yi ambaliya, domin za a zuba maki yalwar teku, kuma arzikin al'ummai za su zo gare ki.
6Ayarin raƙuma za su rufe ki, takarkaran Midiyan da Ifa; dukkansu za su zo daga Sheba; za su kawo zinari da kayan ƙanshi, kuma za su raira waƙar yabon Yahweh.7Dukkan garkunan Kedar za a tara maki, ragunan Nebayot za su biya buƙatunki; za su zama karɓaɓun baiko a kan bagadina; kuma zan darjanta gidana mai daraja.
8Su wane ne waɗannan dake shawagi kamar girgije, kuma kamar kurciyoyi da za su mafaƙarsu?9Ƙasashen gãɓar tekuna suna nema na, kuma jiragen ruwa na Tarshish suna jagoranci, domin su kawo 'ya'yanki maza daga nesa, zinariyarsu da azurfarsu na tare da su, domin sunan Yahweh Allahnki, da kuma domin Mai Tsarkin Nan na Isra'ila, saboda ya daukaka ki.
10'Ya'ya maza na bãƙi za su gina garunki, kuma sarakunanki za su yi maki bauta; koda ya ke a cikin fushina na hore ki, duk da haka a cikin alheri na zan yi maki jinƙai.11‌Ƙofofinki ma zasu kasance a buɗe kullum; ba za a rufe su da rana koda dare ba, saboda a kawo arzikin al'ummai da sarakunansu dake masu jagora.
12Hakika, al'ummai da masarautu da ba za su ɓauta maki ba za su lalace; waɗannan al'umman za su hallaka kakaf.13‌Ɗaukakar Lebanon za ta zo gare ki, itatuwan fir da makamantansu za su ƙawata masujadata; kuma zan darjanta wurin sa ƙafafuna.
14Za su zo gare ki su yi rusuna, 'ya'yan ki maza waɗanda suka ƙasƙantar dake; za su rusuna a ƙafafunki; za su kira ki Birnin Yahweh, Sihiyona ta Mai Tsarkin Nan na Isra'ila.
15A maimakon ki ci gaba da zaman wadda aka yashe ta aka ƙita, ba kuma wanda ya wuce ta wurinki, zan maishe ki abin fahariya na har abada, abin murna daga tsara zuwa tsara.16Za ki kuma sha madarar al'ummai, kuma za a rene ki a kirjin sarakuna; za ki sani cewa Ni, Yahweh, ni ne Mai cetonki da mai Fansarki. Mai Girman nan na Yakubu.
17A maimakon tagulla zan kawo maki zinariya, a maimakon ƙarfe zan kawo azurfa; a maimakon katako, tagulla, kuma a maimakon duwatsu, karfe. Zan sa salama ta zama gwamnoninki, adalci kuma masu mulkinki.18Ba za a ƙara jin tashin hankali a ƙasarki ba, ko hallakarwa ko aukawar ɓarna a yankin; amma za ki kira garunki Ceto, ƙofofinki kuma Yabo.
19Rana ba za ta ƙara zama haskenki da rana ba, ko hasken wata ya haskaka a kanki; amma Yahweh zai zama haskenki na har abada, Allahnki kuma shi ne darajarki.20Ranarki ba za ta ƙara faɗuwa ba, ko watanki ya dushe ya ɓace ba; Gama Yahweh zai zama haskenki har abada, kuma ranakun makokinki za su ƙare.
21Dukkan mutanenki za su zama adalai; za su karɓi mallakar ƙasar na dukkan lokaci, reshen shuka ta da aikin hanuwana, domin a ɗaukaka Ni22‌Ƙ‌arami ɗaya zai zama dubu, mafi ƙanƙanta guda kuma al'umma mai ƙarfi; Ni, Yahweh, zan aiwatar da waɗannan abubuwa da sauri idan lokacin ya yi.

61

1Ruhun Ubangiji Yahweh na bisana, domin Yahweh ya shãfe ni in yi shelar labari mai da‌ɗi ga ƙuntattu. Ya aike ni in warkar da waɗanda suka karye a zuci, in yi shelar 'yanci ga kamammu, da kuma buɗewar kurkuku domin waɗanda suke a ɗaure.

2Ya aike ni in yi shelar shekarar tagomashi ta Yahweh, ranar ramuwar gayya ta Allahnmu, in kuma ta'azantar da dukkan masu makoki.
3Ya aike ni - in ba masu makoki cikin Sihiyona - in ba su rawani a maimakon toka, mai na farinciki a maimakon makoki, alƙyabba ta yabo a maimakon ruhun baƙinciki, domin a kira su rimayen adalci, dashen Yahweh, domin ya sami ɗaukaka.
4Za su sạke gina rusassun birane nadã; za su gyara lalatattun wurare. Za su gyara rusassun birane, lalatattu tun daga tsararrakin da suka rigaya suka wuce.5Bãƙi za su tsaya su ciyar da garkunanki, 'ya'yan baƙi kuma za su yi maki aiki a gonakinki dana garkunan inabinki.
6Za a kira ku firistocin Yahweh; za su kira ku bayi na Allahnmu. Za ku ci wadatar al'ummai, kuma za ku yi fahariya cikin arzikinsu.7A maimakon kunyar ki zaki sami riɓi biyu; kuma a maimakon ƙasƙanci za su yi farinciki da rabonsu. Haka za su sami riɓi biyu na rabon ƙasarsu; murna zata zama tasu har abada.
8Gama Ni, Yahweh, ina kaunar shari'ar gaskiya, kuma na ƙi fạshi da shari'ar zalunci. Na tabbata zan sạka masu, kuma zan yi madawwamin alƙawari dasu.9Zuriyarsu za su zama sanannu a cikin dukkan al'ummai, kuma 'ya'yan tsatsonsu cikin mutane. Dukkan wanda ya gan su zai tabbatar da su, cewa su ne mutanen da Yahweh ya sawa albarka.
10Zan yi farinciki sosai cikin Yahweh; cikin Allahna zan yi murna sosai. Gama ya suturce ni da mayafan ceto; ya suturceni da rigar adalci, kamar yadda ango ke ƙawata kansa da rawani, kuma kamar yadda amarya takan ƙawata kanta da kayan ado.11Gama kamar yadda ƙasa take fito da dashe-dashenta, kuma kamar yadda gona takan sa shuke-shukenta su tsiro, haka Ubangiji Yahweh zai sa adalci da yabo su tsiro a gaban dukkan al'ummai.

62

1Saboda Sihiyona ba zan yi shuru ba, saboda da kuma Yerusalem ba zan yi tsit ba, har sai adalcinta ya bayyana da haske sosai, kuma cetonta kamar fitila mai ci bal-bal.2Al'ummai za su ga adalcinki, dukkan sarakuna kuma za su ga ɗaukakarki. Za a kira ki da sabon suna wanda Yahweh zai zaɓa.

3Za ki zama kambi mai daraja cikin hannun Yahweh, kuma rawanin sarauta a cikin hannun Allahnki.4Ba za a ƙara ce dake, "Yasasshiya" ba; ko ƙasarki ba za a ce da ita, "Watsattsiya ba." Hakika, za a ce dake "Farincikina na cikin ta," ƙasarki kuma "Aurarra," gama Yahweh na farinciki dake, kuma ƙasarki za ta yi aure.
5Hakika, kamar yadda saurayi matashi yakan auri 'yar budurwa, haka 'ya'yanki za su aure ki, kuma kamar yadda ango ke farinciki da amaryarsa, Allahnki zai yi farinciki dake.
6Na sa masu tsaro a bisa ganuwarki, Yerusalem; ba za su yi shuru ba dare da rana. Ku da kuke tunasshe da Yahweh, kada ku tsagaita.7Kada ku ba shi hutu har sai ya sake kafa Yerusalem ya kuma maishe ta abin yabo a duniya.
8Yahweh ya yi rantsuwa da hannunsa na dama da kuma hannunsa mai iko, "Hakika ba zan ƙara bada hatsinki ya zama abinci ga maƙiyanki ba. Bãƙi ba za su sha sabon ruwan inabinki ba, wanda ke kika aikinta ba.9Gama waɗanda suka yi girbin hatsinsu za su ci su kuma yabi Yahweh, kuma waɗanda suka tsinke 'ya'yan inabisu za su sha ruwan inabin a cikin wurarena masu tsarki."
10Ku shigo, ku shigo ta cikin ƙofofi! Ku shirya hanya domin mutane! Ku gina, ku gina babbar hanya! Ku tattara duwatsu! Ku tada tutar alama sama domin al'ummai!
11Duba, Yahweh yana sanarwa zuwa ga iyakar duniya, "Ku cewa ɗiyar Sihiyona: Duba, Mai cetonki yana zuwa! Ki gani, ladarsa na tare da shi, kuma sakamakonsa ya sha gabansa."12Za su kira ki, "tsarkakakkiyar jama'a; fansassu na Yahweh," kuma za a kira ki "Biɗaɗɗiya; birnin da ba a yashe shi ba."

63

1Wane ne wannan da ya ke zuwa daga Idom, yafe da jar tuffa daga Bozara? Wane ne shi cikin kayan sarauta, yana takawa da ƙarfin hali sabili da girman ƙarfinsa? Ni ne, ina maganar adalci da kuma ikon yin ceto.2Me yasa kayayyakinka suka yi jạ, kuma me yasa suka yi kamar ka daɗe kana tattaka 'ya'yan inabi a wurin matatsar inabi?

3Na tattaka 'ya'yan inabi a matatsar inabi ni kaɗai, kuma babu wani daga cikin al'ummai da ya yi tare da ni. Na tattakesu a cikin fushina na kuma rugurgujesu cikin hasalata. Jininsu ya ɗiɗɗiga a kan kayana kuma ya ɓaɓɓata tufafina.4Gama ina hangen ranar ramuwa, kuma shekara domin fansata ta rigaya ta zo.
5Na duba, kuma babu wani da zai yi taimako. Na yi mamaki cewa babu mai taimako, amma hannuna ya kawo mani nasara, kuma fushina mai tsanani ya iza ni.6Na tattake mutanen a cikin fushina na kuma sa sun bugu cikin hasalata, na kuma zubar da jininsu a fuskar ƙasa.
7Zan faɗi amincin ayyukan alƙawarin Yahweh, ayyukan yabo na Yahweh. Zan faɗi dukkan abin da Yahweh ya yi mana, da kuma manyan alherinsa zuwa gidan Isra'ila. Wannan tausayi da ya nuna mana sabili da jinƙansa, da kuma ayyuka masu yawa na amintaccen alƙawarinsa.8Gama ya ce, "Hakika sụ mutanena ne, 'ya'ya masu biyayya." Ya zama Mai cetonsu.
9Cikin dukkan wahalarsu, shima ya wahala, sai mala'ika daga gare shi ya cecesu. Cikin ƙaunarsa da jinƙansa ya cecesu, ya kuma ɗagasu sama ya kuma bishesu a cikin dukkan zamanan dã.
10Amma suka yi tayarwa suka ɓata wa Ruhunsa Mai Tsarki rai. Saboda haka yạ zama abokin gạbarsu ya kuma yaƙesu.
11Mutanensa suka yi tunani game da kwanakin dã na Musa. Suka ce, "Ina Allah, wanda ya fito da su daga teku da makiyayin garkensa? Ina Allah, wanda ya sanya Ruhunsa Mai Tsarki a cikinsu?
12Ina Allah, wanda yasa darajar ikonsa ya tafiya tare da hannun daman Musa, ya kuma raba ruwa a gabansu, domin ya yiwa kansa suna na har abada?13Ina Allah, wanda ya bi da su ta cikin ruwa mai zurfi? Kamar doki mai gudu a hanya mai kyau, ba su yi tuntuɓe ba.
14Kamar shanu da suke gangarawa zuwa cikin kwari, Ruhun Yahweh ya ba su hutuwa. Sai ka bida da mutanenka, domin ka yiwa kanka suna mai yabo.
15Ka duba daga sama ka kuma kula daga wurinka mai tsarki da kuma maɗaukakin mazauni. Ina himmarka da kuma manyan ayyukanka? Tausayinka da ayyukan juyayinka an hana mana su.16Gama kai ne ubanmu, ko da shi ke Ibrahim bai sanmu ba, kuma Isra'ila bai fahimcemu ba, kai, Yahweh, kai ne ubanmu. 'Mai fansarmu' sunanka kenan tun zamanan dã.
17Yahweh, me yasa ka sạmu muka bijire daga hanyoyinka ka kuma taurare zukatanmu, har ba mu yi maka biyayya ba? Ka dawo ta dalilin bayinka, kabilun gãdonka.
18Mutanenka sun mallaki wurinka mai tsarki na ƙaramin lokaci, amma maƙiyanmu suka tattake ta.19Muka zama kamar waɗanda ba ka taɓa mulkinsu ba, kamar waɗanda ba a taɓa kiransu da sunanka ba."

64

1Ai ya, dãma ace ka tsaga sammai ka sauko ƙasa! Da tsaunuka sun girgiza a gabanka,2kamar yadda wuta ke chinye ƙananan kurmi, ko wuta tasa ruwa ya tafasa. Ai ya, dãma dai sunanka ya zama sananne a wurin magabtanka, domin al'ummai su yi rawar jiki a gabanka!

3A dã, da kayi abubuwan ban mamaki waɗanda ba mu zata ba, kạ sauko ƙasa, kuma tsaunuka suka girgiza a gabanka.4Tun a zamanin dã ba wanda ya taɓa ji ko ya fahimta ko ya gani da ido wani Allah in banda kai, wanda ya ke yin abubuwa ga wanda ya jira gare shi.
5Ka kan zo ka taimaki waɗanda suke farinciki da aikata abin dake na adalci, su dake tunawa da hanyoyinka suna kuma yin biyayya dasu. Kạ yi fushi a lokacin da muka yi zunubi. Ta hanyoyinka kullum za a cecemu.
6Gama dukkan mu mun zama kamar wanda ya ƙazamtu, kuma dukkan aikin adalcinmu kamar tsumman jinin haila. Dukkanmu mun yi yaushi kamar ganyaye; kurakuranmu, kamar iska, sun kwashe mu nesa.7Babu ko ɗaya mai kira bisa sunanka, wanda ya ke ƙoƙarin ya kama ka. Gama ka ɓoye fuskarka daga gare mu ka kuma sa muka lalace a cikin hannun kurakuranmu.
8Duk da haka, Yahweh, kai ne ubanmu; mu ne yimɓu. Kai ne maginin tukunya; kuma dukkanmu aikin hannunka ne.9Kada ka yi fushi sosai, Yahweh, kada koyaushe ka tuna da zunubanmu gãba damu. In ka yarda ka dube mu dukka, jama'arka.
10Biranenka masu tsarki sun zama jeji; Sihiyona ta zama jeji, Yerusalem kuma kango.11Haikalinmu mai tsarki mai kyau, inda dã ubanninmu suka yabe ka, an rusar da su da wuta, kuma dukkan abin dake da muhimmanci yạna a lalace.12Ta ƙaƙa za ka jure wannan, Yahweh? Ta ƙaƙa za kayi shuru ka kuma ci gaba da ƙasƙantar damu?

65

1"Na shirya da su same ni su waɗanda ba su tambaya ba; Na shirya domin su same ni su waɗanda ba su neme ni ba. Na ce, 'Ga ni nan! Ga ni nan!' ga al'ummar da ba su kira bisa sunana ba.2Na miƙa hannayena dukkan yini zuwa ga mutane masu taurin zuciya, masu tafiya a cikin tafarkin da ba dai-dai ba, waɗanda suka yi tafiya bisa ga tunaninsu da shirye-shiryensu!

3Sụ jama'ane dake tozartani a koyaushe, suna miƙa hadayu a cikin gonaki, suna kuma ƙona turare bi sa ginin tuballa.4Sukan zauna cikin maƙabarta suna tsaro dukkan dare, suna kuma cin naman alade tare da romon ruɓaɓɓen nama a cikin kwanoninsu.
5Suna cewa, "Tsaya nesa, kada ka zo kusa da ni, gama nafi ka tsarki.' Waɗannan abubuwa hayaƙi ne cikin hancina, wutar da take ƙonewa duk yini.
6Duba, a rubuce ya ke a gabana: Ni ba zan yi shuru ba, gama zan yi masu sãkayya; zan sãka masu a cikin cinyarsu,7domin zunubansu da zunuban ubanninsu tare," Yahweh ya faɗa. "Zan sãka masu domin ƙona turare a bisa tsaunuka da kuma ba'ar da suke yi mani a bisa tuddai. Saboda haka zan auna masu ayyukansu na dã a cikin cinyarsu."
8Ga abin da Yahweh ke cewa, "Kamar yadda a ke samun ruwan inabi daga nonon 'ya'yan inabi, lokacin da wani na cewa, 'Kada ka lalata shi, gama akwai abu mai kyau a cikinsa; Ga abin da zan yi domin barorina: Ba zan lallatar da su dukka ba.
9Zan fito da zuriya daga Yakubu, kuma daga Yahuda waɗanda za su mallaki tsaunukana. Zaɓaɓɓuna za su mallaki ƙasar, kuma bayina za su zauna a wurin.10Sharon zata zama makiyaya domin garkena, kuma Kwarin Ako wurin hutawar garkuna, domin mutanena masu nema na.
11Amma ku da kuka yashe da Yahweh, waɗanda suke mantawa da tsaunina mai tsarki, masu shirya teburi domin allahn Sa'a, su kuma cika moɗar ruwan inabi mai gauraye domin ‌Ƙaddara.
12Zan ƙaddara ku ga takobi, kuma dukkanku za ku rusuna ga kisa, domin a lokacin da nayi kira, ba ku amsa ba; da nayi magana, ba ku saurara ba. Amma ku ka aikata abin dake mugu a gabana kuka kuma zaɓi ku aikata abin da ba zan ji daɗinsa ba."
13Wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh ke faɗi, "Duba, bayina za su ci, amma ku za ku ji yunwa; duba, bayina za su sha, amma ku za ku ji ƙishi; duba, bayina za su yi murna, amma ku za ku kunyata.14Duba, bayina za su yi sowa da farinciki domin murnar zuciya, amma ku za ku yi kuka saboda da zafin zuciya, kuma za ku yi makoki saboda karayar ruhu.
15Za ku bar sunanku abin la'antawa domin zaɓaɓɓuna su yi managa; Ni, Ubangiji Yahweh, zan kasheku; Zan kira bayina da wani suna.16Duk wanda ya furta albarka ga ƙasar zaiyi albarka ta wurina, Allah na gaskiya. Duk wanda ya yi rantsuwa a duniya zai rantse da ni, Allah na gaskiya, gama matsalolin dã za a manta da su, gama za su ɓoye daga idanuna.
17Gama duba, ina dab da halitta sabobbin sammai da kuma sabuwar duniya; kuma al'amuran dã ba za a tuna dasu ba ko su zo ga rai.18Amma ku za kuyi murna da farinciki har abada a cikin abin da zan hallita. Ga shi, ina dab da halitta Yerusalem abin farinciki, mutanenta kuma abin fahariya.19Zan yi murna bisa Yerusalem in kuma ji daɗi bisa mutanena; kuka da ihu saboda matsala ba za a ƙara ji a cikinta ba.
20Ba zai ƙara faruwa ba ɗan jinjiri ya rayu kwanaki kaɗan; ko tsohon mutum ya mutu kafin lokacinsa. Wanda ya mutu yana shekara ɗari za a ce da shi matashi. Duk wanda ya kãsa kaiwa shekara ɗari za a ɗauke shi la'ananne ne.21Za su gina gidaje su kuma zauna ciki, kuma za su shuka garkunan inabi su ci amfaninsu.
22Ba za su ƙara gina gida wani daban ya zauna ciki ba; ba za su shuka, wani ya ci ba; gama kamar kwanakin itatuwa haka zai zama kwanakin jama'ata. Zaɓaɓɓuna za su kere ayyukan hannuwansu a shekaru.23Ba za su yi aiki a banza ba, ko su haifi kaito. Gama sụ 'ya'yan waɗanda Yahweh yasa masu albarkata ne, kuma da zuriyarsu tare da su.
24Kafin su kira, Zan amsa; kuma a lokacin da suke magana, Zan ji.25Damisa da ɗan rago za su yi kiwo tare, kuma zaki zai ci ciyawa kamar sã; amma ƙura ce za ta zama abincin maciji. Ba za su ƙara cutarwa ko su hallakar a kan dukkan tsaunina mai tsarki," inji Yahweh.

66

1Wannan shi ne abin da Yahweh ya ke cewa, "Sama kursiyina ne, ƙasa kuma matashin sawuna. To ina gidan da za ku gina mani? Ina wurin da zan iya hutawa?

2Hannuwana suka yi dukkan waɗannan abubuwa; haka waɗannan abubuwa suka zo suka kasance - wannan shi ne abin da Yahweh ya furta. Wannan shi ne mutumin dana zaɓa, karyayye da tawali'u a ruhu, kuma wanda ya ke rawar jiki ga maganata.
3Shi wanda ya yanka rago ya kuma kashe mutum; shi wanda ya yi hadayar ɗan rago ya kuma karya wuyan kare; shi wanda ya miƙa baikon hatsi ya miƙa jinin alade; shi wanda ya miƙa turare na tunawa shima yasa wa mugunta albarka. Sun zaɓi hanyoyin kansu, kuma suna fahariya da aikin ƙazamtarsu.
4Ni ma haka zan zaɓi masu horonsu; zan kawo a bisansu abin nan da suke tsoro, domin a lokacin dana yi kira, ba bu wanda ya amsa; dana yi magana, ba bu wanda ya saurara. Suka aikata abin da ke mugu a gabana, suka zaɓi su yi abin dake ɓata mani rai."
5Ku saurara ga maganar Yahweh, ku da kuke rawar jiki da maganarsa, "Yan'uwanku da suka ƙi ku suka ware ku sabili da sunana suka ce, 'Bari Yahweh ya ɗaukaka, sa'an nan za mu ga murnar ku'; amma za a kunyatar dasu.
6Hayaniyar yaƙi na fitowa daga birnin, hayaniya daga haikali, hayaniyar Yahweh yana sãka wa maƙiyansa.
7Kafin ta shiga naƙuda, ta haihu; kafin zafi ya abko mata, ta haifi ɗa namiji.8Wane ne ya taɓa jin abu kamar haka? Wane ne ya taɓa ganin abubuwa kamar haka? Ana iya haihuwar al'umma a rana ɗaya? Al'umma tana iya haihuwa a ɗan ƙanƙanin lokaci? Duk da haka da Sihiyona ta shiga naƙuda, nan da nan ta haifi 'ya'yanta.
9Zan kawo jinjiri a cikin ƙofar fita in kuma hana a haifi jaririn?- Yahweh yana tambaya. Ko ina kawo jariri lokacin haihuwa amma sai in hana shi fitowa?- Allahnka na tambaya."
10Ku yi farinciki da Yerusalem ku yi murna dominta, dukkanku masu ƙaunarta; ku yi farinciki da ita, dukkanku da kuke makoki a kanta!11Gama za kuyi reno ku kuma ƙoshi; da nonnanta za ku ta'azantu; Gama za ku sha ku ƙoshi ku kuma ji daɗin yalwar ɗaukakarta.
12Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Ina gab da zubo wadata bisanta kamar kogi, kuma arzikin al'ummai kamar ambaliyar kogi. Za kuyi reno kusa da ita, a ɗauke ku cikin hannuwanta, a karkaɗa ku da murna a gwuiwarta.13Kamar yadda mahaifiya ke ta'azantar da ɗanta, haka ni ma zan ta'azantar daku, kuma za ku ta'azantu a cikin Yerusalem."
14Za ku ga wannan, kuma zuciyarku za tayi farinciki, kuma ƙasusuwanku za su tsiro kamar 'yan ciyayi. Za a bayyana hannun Yahweh ga bayinsa, amma zai nuna fushinsa gãba da maƙiyansa.
15Gama duba, Yahweh yana zuwa da wuta, kuma karusansa suna zuwa kamar guguwar iska domin ta kawo zafin fushinsa da kwaɓarsa tare da harshen wuta.16Gama Yahweh yana shar'anta 'yan adam da wuta da kuma takobinsa. Waɗanda Yahweh ya kashe za su yi yawa.
17Sun keɓe kansu suna tsabtace kansu, domin su shiga gonaki, suna bi ta tsakiyar waɗanda suke cin naman alade da abubuwan ban ƙyama kamar kũsu. "Za su kawo ga ƙarshe - wannan shi ne furcin Yahweh.
18Gama na san ayyukansu da tunaninsu. Lokaci na zuwa da zan tara dukkan al'ummai da yarurruka. Za su zo su ga ɗaukakata.19Zan sa gaggarumar alama a tsakaninsu. Sa'an nan zan aiko da masu tsira daga gare su zuwa ga al'ummai: Zuwa ga Tarshish, Fut, da Lud, masu harbi da suke jan bakansu, zuwa ga Tubal, da Yaban, da kuma zuwa iyakar ƙasashen bakin ruwa da ke nesa inda ba su taɓa ji game da ni ko suka ga ɗaukakata ba. Za su furta ɗaukakata a tsakiyar al'ummai.
20Za su dawo da dukkan 'yan'uwanku daga cikin al'ummai, abin baiko ga Yahweh. Za su zo bisa dawakai, da karusai, da cikin kekunan shanu, da bisa jakuna, da kuma bisa raƙuma, zuwa ga tuduna mai tsarki Yerusalem - inji Yahweh. Gama jama'ar Isra'ila za su kawo baiko na hatsi a cikin kwanuka masu tsabta cikin gidan Yahweh.21Zan zaɓi wasu daga cikinsu su a matsayin firistoci da kuma Lebiyawa - inji Yahweh
22Gama kamar yadda sabuwar sammai da sabuwar duniya da zan halitta za su dawwama a gabana - wannan shi ne furcin Yahweh - haka zuriyarku za su dawwama.23Daga wata ɗaya zuwa na gaba, kuma daga wannan Asabaci zuwa na gaba, dukkan mutane za su zo su rusuna mani - inji Yahweh.
24Za su fito waje su dubi gawawakin jama'ar da su ka yi mani tayarwa, gama tsutsotsin da za su ci su ba za su mutu ba, kuma wutar da za ta haɗiyesu ba za ta ɓice ba; kuma za su zama abin ƙi ga dukkan masu rai."

Littafin irmiya

1

1Waɗannan su ne kalmomin Irmiya ɗan Hilkiya, ɗaya daga cikin firistocin Anatot cikin ƙasar Benyamin.2Maganar Yahweh ta zo gare shi a kwanakin Yosiya ɗan Amon, sarkin Yahuda, cikin shekara ta goma sha uku ta mulkinsa.3Ta kuma zo cikin kwanakin Yehoyakim ɗan Yosiya, sarkin Yahuda, har sai watan biyar na shekara goma sha ɗaya ta Zedekiya ɗan Yosiya, sarkin Yahuda, lokacin da aka kwashe mutanen Yerusalem a matsayin 'yan fursuna.

4Maganar Yahweh tazo gare ni, cewa,5"Kafin In sifanta ka a cikin ciki, Na zaɓe ka; kafin ka fito daga cikin ciki Na keɓe ka; Na sa ka zama annabi ga al'ummai."6Sai na ce, "Ah, Ubangiji Yahweh!" Na ce, "Ni ban san yadda zan yi magana ba, gama ni yaro ne."
7Amma Yahweh yace mani, "Kada ka ce 'Ni ƙaramin yaro ne.' Dole ka tafi duk inda Na aike ka, kuma ɗole ka faɗi duk abin da Na umarce ka!8Kada ka ji tsoron su, gama Ina tare da kai domin in cece ka - wannan furcin Yahweh ne."
9Daga nan sai Yahweh ya miƙa hanunsa ya taɓa bakina, yace mani, "Yanzu, Nasa maganata a cikin bakinka.10Yau na sanya ka bisa kan al'ummai da kan mulkoki, ka tunɓuke ka kuma rushe, ka hallakar, ka kuma juyar, ka gina ka dasa."
11Sai maganar Yahweh ta zo wurina, cewa, "Me ka gani, Irmiya?" Na ce, "Na ga reshen almond."12Yahweh yace mani, "Ka gani da kyau, gama ina kiyaye maganata domin in cika ta."
13Maganar Yahweh ta sake zuwa wuri na karo na biyu, cewa, "Me ka gani? Na ce, "Na ga tukunya mai zafi, wadda fuskarta na ɓullowa, tana kaucewa daga arewa.14"Yahweh ya ce mani, "Bala'i zai fito daga arewa akan dukkan mazaunan ƙasar nan.
15Gama ina kiran dukkan kabilun mulkokin arewa, inji Yahweh. Zasu zo, kowanne ɗayan su zai kafa kursiyin sa a ƙofofin shiga Yerusalem, gãba da dukkan ganuwar da ta kewaye ta, kuma gãba da dukkan biranen Yahuda.16Zan furta hukunci gãba da su domin dukkan muguntarsu cikin yãshe ni, ta wurin ƙona turare ga waɗansu alloli, cikin kuma yin sujada ga abubuwan da suka ƙera da hannuwansu.
17Ka shirya kanka! Ka tashi ka faɗa masu duk abin da na umarce ka. Kada ka firgita a gaban su, ko in firgitar da kai a gabansu!18Duba! Yau, na maishe ka tsararren birni, ginshiƙin ƙarfe, da bangaye na tagulla gãba da dukkan ƙasar - gãba da sarakunan Yahuda, da hakimansu, firistocinsu, da mutanen ƙasar.19Zasu yi yaƙi gãba da kai, amma ba zasu yi nasara da kai ba, gama zan kasance tare da kai in cece ka - wannan furcin Yahweh ne."

2

1Maganar Yahweh tazo gare ni, cewa,2"Kaje ka yi shela ga kunnuwan Yerusalem. Ka ce, 'Yahweh ya faɗi wannan: Na tuna a madadin ki da alƙawarin aminci cikin ƙuruciyarki, ƙaunarki a lokacin da muna tashe, lokacin da kika bi ni cikin jeji, ƙasar da ba'a taɓa shuka ba.3An keɓe Isra'ila ga Yahweh, nunan farin girbinsa! Dukkan waɗanda suka ci daga nunan farin sun ɗauki laifinsu; bala'i ya afko masu - wannan furcin Yahweh ne."'

4Kuji maganar Yahweh, ya gidan Yakubu, dukkanku iyalin gidan Isra'ila.5Yahweh ya faɗi haka, "Wanne laifi ubanninku suka iske tare da ni, da suka yi nisa daga bi na? Da suka bi alloli marasa amfani su kansu kuma suka zama marasa amfani?6Basu ce, "Ina Yahweh, wanda ya fito da mu daga ƙasar Masar ba? Ina Yahweh, wanda ya bishe mu cikin jeji, zuwa cikin ƙasar Araba da ramummuka, a cikin ƙasar fari da duhu mai zurfi, ƙasa wadda ba wanda ke ratsawa ba kuma wanda yake zama ciki?'
7Amma na kawo ku cikin ƙasar Kamel, domin ku ci 'ya'yan itatuwanta, da sauran abubuwa masu kyau! amma da kuka zo, kuka ƙazantar da ƙasata, kun maida abin gãdona ya zama abin ƙyama!8Firist bai ce, 'Ina Yahweh ba?' masanan shari'a kuma basu da mu da ni ba! Makiyaya sun yi mani laifi. Annabawa suka yi annabci domin Ba'al suka kuma bi al'amura marasa amfani.
9Saboda haka har yanzu zan zarge ku - wannan furcin Yahweh ne - kuma zan zargi 'ya'yan 'yayanku.10Domin ƙetarewa zuwa gaɓar Kittim ku kuma duba. Ku aika da manzanni zuwa Kedar ku bincika ku gani ko an taɓa yin wani abu irin wannan.11Ko al'umma ta musanya allolinta, ko da shike su ba alloli ba ne? Amma mutane na sun musanya darajarsu da abin da ba zai taimakesu ba.
12Ku girgiza, sammai, saboda wannan! ku yi rawar jiki ku kuma firgita - wannan furcin Yahweh ne.13Gama mutanena sun aikata mugayen abubuwa biyu gãba da ni: Sun yi watsi da maɓuɓɓugan ruwayen rai, sun gina wa kansu randuna, hudaddun randuna waɗanda ba zasu iya riƙe ruwa ba.
14Ko Isra'ila bawa ne? An haife shi a gidan ubangidansa? To don me ya zama abin washewa?15'Yan zakuna sun yi masa ruri. Suna surutai da yawa sun kuma mai da ƙasarsu wurin tsoratarwa. An lalatar da biranensu ba sauran mazauna a ciki.16Kuma, mutanen Memfis da Tafanhes zasu aske ƙoƙon kanku.17Ba ku ne kuka yi wa kanku wannan ba lokacin da kuka yashe da Yahweh Allahnku, yayin da yake bishe ku a hanya?
18Yanzu fa, me ya kai ku hanyar Masar kuka kuma sha ruwayen Shihor? Don me kuka bi hanyar zuwa Asiriya kuma kuka sha ruwayen kogin Yufiratis?19Muguntarku ta tsauta maku, rashin bangaskiyarku kuma ya hore ku. Don haka ku yi tunani akai, kuma ku fahimci cewa mugunta ce kuma da ɗaci idan kuka yashe da Yahweh Allahnku, kuma baku da tsoro na - wannan furcin Ubangiji Yahweh mai runduna ne.
20Gama na karye karkiyar da kake da ita tun zamanin dã; na yanke sarƙƙoƙinka. Duk da haka ka ce, 'Ba zan yi bauta ba!' da shike ka russuna wa kowanne tudu mai tsawo da gindin kowanne itace mai ganye, kai mazinaci.21Na dasa ka a matsayin zaɓaɓɓen inabi, cikakke daga iri marar aibi. Amma ta yaya ka canza kan ka zuwa gurɓatacce, inabi marar amfani.22Gama ko da ka wanke kanka cikin kogi ko ka wanke da sabulu mai ƙarfi, zunubinka ya ɓata ka a gaba na - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.
23Ta yaya zaka ce, 'Ban ƙazantu ba! Ban bi Ba'aloli ba?' Dubi abin da ka yi a cikin kwarurruka! Yi la'akari da abin da kayi, kai raƙumi ne mai gaggawar tafiya mai gudu nan da can,24jakar jeji wadda ta saba da zaman jeji, a cikin zuffarta tana numfasa iska! Wa zai tsai da sha'awarta? Babu daga cikin mazajen da ke buƙatar ya gajiyar da kansa wajen binta; a lokacin barbararsu zasu same ta.25Dole ka tsaida ƙafafunka daga zama marar takalmi kuma maƙogwaronka daga jin ƙishi! Amma ka ce, 'Ba bege! A'a, Ina ƙaunar bãƙi kuma zan bi su!'
26Kamar yadda ɓarawo yake jin kunya idan an kama shi, haka gidan Isra'ila zai ji kunya - su, da sarakunansu, hakimansu, da firistocinsu da annabawa!27Waɗannan su suke cewa itace, 'Kai ubana ne,' ga dutse kuma, 'Kai ka haife ni.' Gama bayansu ke fuskanta ta ba fuskokinsu ba. Duk da haka a kwanakin matsaloli zasu ce 'Ka tashi ka cece mu!'28Duk da haka ina allolin da kuka yi wa kanku? Bari su tashi in sun ga dama su cece ku a lokacin damuwarku, gama yawan allolinku yawan biranenku, ya Yahuda!
29To don me kuke zargi na a kan yi ba dai-dai ba? Dukkan ku kun yi mani zunubi - wannan furcin Yahweh ne.30A banza na hukunta mutanenku. Ba zasu karɓi horo ba. Takobinku ya cinye annabawanku kamar zaki mai hallakarwa!31Ku 'yan wannan tsara! Ku saurari maganata, maganar Yahweh! Na zama jeji ga Isra'ila? Ko ƙasa mai baƙin duhu? Don me mutanena zasu ce, 'Bari mu yi yawo mu zagaya, ba zamu ƙara zuwa wurin ka ba?'
32Zai yiwu budurwa ta manta da kayan adonta na zinariya ko amarya da kayan lulluɓin ta? Duk da haka mutanena sun manta da ni kwanaki ba iyaka!33kin shirya hanyarki da kyau don ki nemi ƙauna. Kin koyar da halayenki ga mugayen mata.34A cikin tufafinki an iske jinin ran marasa laifi, mutane talakawa. Waɗannan mutane ba a same su cikin ayyukan sata ba.
35Amma kin ce, 'Ni mara laifi ce; lallai fushinsa ya juya daga gare ni.' Amma duba! zan kawo hukunci a kan ki domin kin ce, 'Ban yi zunubi ba.'36Don me kike ɗauka da sauƙi haka batun canza hanyoyinki? Masar zata kunyatar da ke kamar yadda Asiriya ta yi maki.37Kema za ki fita daga can a wulaƙance, da hannayen ki a kanki, gama Yahweh ya ƙi waɗanda kika dogara gare su, don haka ba za ki sami taimako daga gare su ba."

3

1"Idan mutum ya saki matarsa, ta fita daga wurinsa ta kuma zama matar wani, zai sake komawa wurinta kuma? ‌Ƙ‌asar ba zata ƙazantu ba gaba ɗaya? Kin zama kamar karuwa mai masoya da yawa; yanzu kuma kina so ki sake dawowa wurina? - wannan furcin Yahweh ne.2Ki ɗaga idanun ki sama ki duba tsaunuka! ko akwai wurin da ba kiyi lalata ba? A bakin hanya kin zauna kina jiran masoyanki, kamar Balarabe cikin jeji. Kin ƙazantar da ƙasar da karuwancinki da kuma mugunta.

3Don haka an hana ruwan bazara ruwan kaka kuma bai zo ba. Amma fuskar ki akwai girmankai, kamar fuskar karuwa. Ba ki jin kunya.4Ba yanzu kika kira gare ni ba: 'Ubana! Abokina na kurkusa tun daga ƙuruciyata!5Koyaushe zai yi ta fushi? Kullum zai riƙe fushinsa har ƙarshe?' Duba! Wannan shi ne abin da kika ce, amma kin yi dukkan muguntar da kika iya yi!"
6A kwanakin sarki Yosiya sai Yahweh ya ce mani, "Ka ga abin da Isra'ila marar amana ta aikata? Ta hau bisa kan kowanne tudu mai tsawo ƙarƙashin kowanne itace mai ganyaye, a can ta zama kamar karuwa.7Na ce, 'Bayan ta yi dukkan waɗannan al'amura, zata koma wurina,' amma bata komo ba. Daga nan sai 'yar uwarta mai cin amana Yahuda ta ga waɗannan abubuwa.
8Sai na ga haka, Isra'ila maci amana ta aikata zina na kore ta na bata takardar kisan aure, 'yar uawrta maci amana Yahuda bata ji tsoro ba; ita ma ta fita ta aikata kamar karuwa.9Karuwancinta ba wani abu ba ne a gare ta; ta ƙazantar da ƙasa, ta kuma aikata zina da duwatsu da itatuwa.10Daga nan bayan dukkan waɗannan, 'yaruwarta maci amana Yahuda ta komo wurina, amma ba da dukkan zuciyarta ba, amma da ƙarya - wannan furcin Yahweh ne."
11Daga nan sai Yahweh ya ce mani, "Adalcin Isra'ila ya fi na Yahuda maci amana!12Ka je kayi shelar waɗannan maganganu zuwa ga arewa. 'Ki dawo, ya Isra'ila mai cin amana! - wannan furcin Yahweh ne - ba kulluyaumin zan yi fushi da ke ba. Tun da ni mai aminci ne-wannan furcin Yahweh ne - ba zan zauna cikin fushi ba har abada.
13Ki yarda da zunubinki, gama kin aikata laifuffuka gãba da Yahweh Allahnku; kin raba hanyoyin ki da bãƙi ƙarƙashin kowane itace mai duhuwa! Gama baki saurari muryata ba! - wannan furcin Yahweh ne.14Ku juyo, mutane maciya amana! - wannan furcin Yahweh ne - mijinki ne! zan ɗauke ki, ɗaya daga cikin birni, biyu daga cikin iyali, zan kawo ki Sihiyona!15Zan baku makiyaya gwargwadon zuciyata, kuma zasu yi kiwon ku da sani da fahimta.
16Sa'annan zai kasance a sa'ad da zaku riɓanɓanya ku bada 'ya'ya a waɗannan kwanaki - wannan furcin Yahweh ne - daga nan ba zasu ƙara cewa, "Sanduƙin akwatin alƙawari na Yahweh ba!" Wannan al'amarin ba zai ƙara zuwa cikin zuciyarsu ba, gama ba zasu ƙara tunawa ko su yi kewarsa ba. Kuma ba za a ƙara yin wani ba.'
17A lokacin nan za su yi shela game da Yerusalem, 'Wannan shi ne kursiyin Yahweh,' daga nan sauran al'ummai za su taru a Yerusalem a cikin sunan Yahweh. Ba za su ƙara yin tafiya cikin taurin kai da muguntar zuciyar su ba.18Cikin kwanakin nan, gidan Yahuda zai yi tafiya da gidan Isra'ila. Tare za su zo daga kasar arewa zuwa ƙasa wadda na ba kakannin ku a matsayin gãdo.
19Amma ni, Nace, Yadda nake so in girmamaku a matsayin ɗa in baku ƙasa mai daɗi abin gãdo wanda ya fi kyau fiye da wanda ke cikin sauran al'ummai!' Da sai in ce, 'Zaku kira ni "baba na". 'Ba zaku juya daga bina ba.20Amma kamar mace mai cin amanar mijinta, kun yashe ni, ku gidan Isra'ila - wannan furcin Yahweh ne."
21An ji murya bisan filaye, kuka da godon mutanen Isra'ila! Gama sun canza hanyoyinsu; sun manta da Yahweh Allahnsu,22"Ku juyo, ku mutane maciya amana! Zan warkar da yaudarar ku!" Duba!! Zamu zo wurin ka, gama kai ne Yahweh Allahnmu!
23Hakika ƙarairayi sun zo daga tuddai, muryoyi masu ruɗar wa daga duwatsu; hakika Yahweh Allahnmu shi ne ceton Isra'ila.24Duk da haka gumaka abin kunya sun cinye abin da kakanninmu suka yi wahalarsa - garkunansu na shanu da na awaki, 'ya'yansu maza da mata!25Bari mu kwanta cikin kunya. Bari kunyar mu ta rufe mu, gama mun yi zunubi ga Yahweh Allahnmu! Mu da kakanninmu, tun daga lokacin ƙuruciyar mu har zuwa yau, bamu saurara ga muryar Yahweh Allahnmu ba!"

4

1Idan kuka juyo, Isra'ila - wannan furcin Yahweh ne - zai zama gare ni zaku juyo. Idan kuka kawar da ƙazantattun abubuwa daga gabana kuma baku ƙara bari na ba,2Dole ku zama da gaskiya, marasa aibi, da masu adalci lokacin da kuke rantsuwa, 'Da ran Yahweh.' Sa'annan ne al'ummai za su albarkaci kansu a cikinsa, kuma a cikinsa zasu yi ɗaukaka."3Gama Yahweh ya faɗi haka ga kowanne mutum da ke cikin Yahuda da Yerusalem: 'Ku yi huɗar ƙasarku, kada kuma ku yi shuka cikin ƙayayuwa.

4Kuyi wa kanku kaciya ga Yahweh, ku cire loɓar zuciyarku, mazajen Yahuda da mazaunan Yerusalem, in ba haka ba fushina zai fita kamar wuta, ya ƙone har ba wanda zai kashe shi, saboda muguntar ayyukanku.5Ka sanar cikin Yahuda, bari a ji a Yerusalem. Ka ce, "A busa ƙaho cikin ƙasar." Ayi shela a ce, "Mu taru. Bari mu shiga zuwa birane masu kagara."6A ɗaga alamar tuta kuma ta fuskanci wajen Sihiyona, ku gudu don ku tsira! kada ku tsaya, gama zan kawo bala'i daga arewa da babbar faɗuwa.
7Zaki yana zuwa daga cikin kurminsa wani kuma wanda zai hallakar da al'ummai yana shirin fita. Zai bar wurinsa ya kawo tsoratarwa a ƙasarku, zai mai da biranenku su zama kangaye, inda ba mai zama ciki.8Saboda haka, ku yi ɗammara da tsummoki, ku yi makoki kuna kururuwa. Gama ƙarfin fushin Yahweh bai juya daga gare mu ba.
9Zai zama kuma a ranar nan - wannan furcin Yahweh ne. a ranar nan, zuciyar sarki da hakimansa zata mutu. Firistoci zasu tsorata annabawa kuma zasu razana."10Sai nace, "Ah! Ubangiji Yahweh. Lallai ka ruɗi waɗannan mutane da Yerusalem ta wurin cewa, 'Zaku sami salama.' Duk da haka takobi tana sara gãba da ransu."
11A wannan lokaci za'a ce da waɗannan mutane da Yerusalem, "Iska mai ƙuna daga wajen filayen hamada, zata yi wajen ɗiyar mutanena. Ba zata sheƙe ba ko kuwa ta tsarkake su.12Iska da ta fi wannan ƙarfi zata zo bisa ga umarni na, yanzu kuma zan furta shari'a a kansu.
13Duba, yana kai hari kamar giza-gizai, karusansa kuma suna kamar hadari. Dawakansa sunfi gaggafa sauri. Kaiton mu, gama zamu zama hallakakku!14Ki wanke zuciyar ki daga mugunta ya Yerusalem, domin ki tsira. Har yaushe zuzzurfan tunaninki zai kasance yadda za a yi zunubi?15Gama murya na kawo labari daga Dan, an ji zuwan masifa daga tuddan Ifraim.
16Kasa al'ummai su yi tunani akan wannan: Duba, ka sanar da Yerusalem cewa magewaya suna zuwa daga ƙasa mai nisa su tada muryar yaƙi akan biranen Yahuda.17Zasu zama kamar masu tsaron nomammiyar gona gãba da ita kewaye, domin tayi mani tayaswa wannan shi nefurcin Yahweh -18halinki da ayyukanki ne suka yi maki waɗannan abubuwa. Wannan zai zama hukuncinki. Zai zama da muni! Zai buga har zuciyarki.
19Ya zuciyata! Zuciyata! Ina cikin baƙin ciki a zuciyata, zuciyata tana binbini a cikina. Ba zan iya yin shiru ba, gama na ji ƙarar ƙaho, gangamin yaƙi.20Bala'i na bin bala'i; gama dukkan ƙasar ta zama kango. Farat ɗaya rumfunana an hallaka su, labulena kuwa nan da nan.
21Har yaushe zan ga tutar? Zan ji ƙarar ƙaho?22Saboda wautar mutanena - basu sanni ba. Mutane ne masu halin wauta basu da fahimta. Masu azanci ne wajen mugunta, amma basu da sanin yin abu mai kyau.
23Na duba ƙasar. Duba! ta zama wofi da fanko. Gama babu haske domin sammai.24Na duba duwatsu. Duba, suna rawar jiki dukkan tsaunuka suna girgiza.25Na duba. Duba, babu ko ɗaya, kuma dukkan tsuntsayen sammai sun gudu.26Na duba. Duba, fadamun sun zama jeji dukkan biranenta sun rurrushe a gaban Yahweh, da zafin fushinsa."
27Ga abin da Yahweh yace, "Dukkan ƙasar zata zama kango, amma ba zan hallakar da ita dungum ba.28Saboda wannan dalili, ƙasar zata yi makoki, sammai daga bisa kuma zasu duhunta. Gama na sanar da manufofi na; ba zan sake nufi na ba; ba kuwa zan juya ga barinsa ba.29Kowanne birni zai gudu daga ƙarar mahayan dawakai da maharba; zasu ruga cikin kurmi. Kowanne birni zai hau sama cikin wurare masu duwatsu. Za a bar biranen, ba za a sami wanda zai zauna cikinsu ba.
30Yanzu da kika zama kango, me za ki yi? Ko da kike sa tufafi na mulufi, kike ado da kayan zinariya, kina sa idanunki su zama manya saboda shafe shafe, mazan da suka yi sha'awar ki yanzu sun yashe ki. Maimakon haka, suna ƙoƙarin ɗaukar ranki.31Na ji sautin baƙin ciki, wahala kamar a lokacin haihuwar ɗan fari, sautin muryar ɗiyar Sihiyona. Tana haki. Ta baza hannayenta, ta ce, 'Kaitona! Ina suma saboda waɗannan masu kisan kai."

5

1"Yi gudu ta titunan Yerusalem; yi bincike cikin dandalin birninta, kuma. Daga nan ka duba kayi tunani akan wannan: Ko za a sami mutum ɗaya ko akwai wanda ya ke aikata adalci yana ƙoƙarin aikata aminci, daga nan zan yafewa Yerusalem.2Kodashike suna cewa, 'Mun rantse da ran Yahweh,' duk da haka suna rantsuwa kan ƙarya."3Yahweh, idanunka ba aminci suke kallo ba? Ka bugi mutanen, duk da haka basu ji zafi ba, ka hallaka su gaba ɗaya, amma duk da haka sunƙi kaɓar horo. Sun sa fuskokinsu sun taurare fiye da dutse, gama sun ƙi tuba.

4Sa'annan nace, "Hakika waɗannan mutane talakawa ne. Su wawaye ne, gama basu san tafarkun Yahweh ba, ko umarnan Allahnsu ba.5Zan tafi wurin muhimman mutane domin in sanar da saƙonnin Allah gare su. Gama sun san hanyoyin Yahweh, da umarnan Allahnsu." Amma dukkan su sun karya karkiyarsu tare, sun tsintsinke sarƙoƙin da suka ɗaure su ga Allah.6Domin wannan zaki daga cikin kurmi zai kai masu hari. Kyarkeci daga Araba zai lalata su. Damisa za ta zo gãba da biranensu. Duk wanda ya fita daga cikin birninsa za a yayyage shi. Gama laifofinsu sun ƙaru. Ayyukan rashin amincinsu kuwa basu da iyaka.
7Don me zan gafarta wa waɗannan mutane? 'Ya'yansu sun yashe ni kuma sunyi rantsuwa ga waɗanda ba alloli ba ne. Na ciyar dasu sun ƙoshi, amma sun aikata zina, sun riƙa tafiya suna cincirindo zuwa gidajen karuwai.8Dawakai ne su cikin zafi. Suna yawo suna jira a haɗu, kowanne mutum yana neman matar maƙwabcinsa.9Don haka ba zan hukunta su ba? - wannan furcin Yahweh ne - kuma ba zan ɗaukar wa kai na fansa a kan irin wannan al'ummar ba?
10Ku hau sama gun garkunan inabinta ku gano ku hallaka. Amma kada ku hallakar da ita duka. Ku gyara inabinsu, gama waɗannan inabin ba daga Yahweh suke ba.11Gama gidajen Isra'ila dana Yahuda sun bashe ni gaba ɗaya - wannan furcin Yahweh ne.12Sun faɗi ƙarya game da Yahweh kuma suka ce, "Ba zai yi kome ba; ba wata cuta da zata zo kanmu, ba kuwa zamu ga takobi ko yunwa ba.13Annabawa zasu zama iska, maganar bata cikin su, bari duk abin da suka faɗi ayi masu."
14Yahweh, Allah mai runduna ya faɗi wannan, "Saboda ka faɗi haka, duba, duba zansa maganata cikin bakinka. Zata zama kamar wuta, mutanen nan kuma zasu zama kamar itace! Gama zata cinyesu.15Duba!! zan kawo wata al'umma daga nesa, ya gidan Isra'ila - wannan furcin Yahweh ne - al'ummace wadda ta wanzu, kuma daɗaɗɗiyar al'umma! Al'umma ce wadda baka san yaren su ba, ba kuwa zaka fahimci abin da suke faɗi ba.
16Kwarinsu kamar buɗaɗɗen kabari ne. Dukkansu sojoji ne.17Zasu cinye amfanin da ka girbe, haka 'ya'yanka maza da mata, da abincinka. Zasu cinye garken tumakinku da na awaki da kuma garken shanunku; zasu cinye kuringar anab naka dana ɓaure. Zasu rurrushe biranenka masu ganuwa da takobi waɗanda ka dogara gare su.
18Amma ko a cikin waɗancan kwanaki - wannan furcin Yahweh ne - bani da nufin in hallakar da ku baki ɗaya.19Zai faru idan ku, Isra'ila da Yahuda, kun ce, 'Don me Yahweh Allahnmu ya yi mana dukkan waɗannan abubuwa?' Sai kai, Irmiya, kace masu, 'Kamar yadda kuka yashe da Yahweh kuka yi sujada ga baƙin alloli a cikin ƙasarku, haka kuma dole ku bauta wa baƙi a cikin ƙasar da ba taku bace.
20Ka sanar da wannan a gidan Yakubu bari a ji a gidan Yahuda. Kace,21'Ku ji wannan ku wawayen mutane waɗanda basu da fahimta; kuna da idanu amma baku gani, kuna da kunnuwa amma ba ku ji.22Baku ji tsoro na ba - wannan furcin Yahweh ne - ko kuyi rawar jiki a fuskata ba? Na sa yashi ya zama iyakar teku, bisa madauwamin umarni wanda ba zai ƙetare ba - koda shike teku yana tashi ya na faɗuwa, duk da haka bai karya shi ba, ko da sun yi ruri ba zasu ƙetare ba.
23Amma waɗannan mutane suna da kangararriyar zuciya. Sun yi tayarwa sun tafi abinsu.24Gama a cikin zuciyarsu ba su ce, "Bari mu ji tsoron Yahweh Allahnmu, wanda yake bada ruwa na farko da na ƙarshe a lokacinsu ba, ya ke tabbatar mana da makonnin girbl." Laifofinku sun hana waɗannan faruwa.25Zunubanku sun hana abubuwa masu kyau su zo gare ku.
26Gama an sami miyagun mutane tare da mutanena. Suna fako kamar yadda wani ke laɓewa ya kama tsuntsaye; suna ɗana tarko su kama mutane.27Kamar yadda keji yake cike da tsuntsaye, haka gidajensu suke cike da ha'inci da ruɗi. Don haka sun yaɗu sun zama masu arzaki.28Sun yi ƙiba; suna ƙyalli da lafiyarsu. Suna keta haddin kowacce mugunta. Basu sauraron roƙon mutane ko dalilin marayu. Sun azurta duk da ba sa nuna adalci ga masu bukata.29Bazan hukunta su saboda waɗannan abubuwa ba - wannan furcin Yahweh ne - kuma ba zan ɗaukar wa kaina fansa a kan al'umma irin wannan ba?
30Abubuwan banƙyama da tsoratarwa sun faru a cikin ƙasar.31Annabawa suna anabci da ha'inci, firistoci suna mulki da ikonsu. Mutanena kuma suna son haka, amma me zai faru a ƙarshe?"'

6

1Ku nemi mafaka, mutanen Benyamin, ta wurin fita daga Yerusalem. Ku busa ƙaho cikin Tekowa. Ku tada tuta kan Bet Hakkerem, tun da mugunta tana bayyana daga arewa; babbar hallakarwa na zuwa.2Za a hallaka ɗiyar Sihiyona, kyakkyawar mace 'yar lele.3Makiyaya da garkunansu zasu tafi wurinsu; zasu kafa rumfunansu kewaye dasu; ko wannen su zai yi kiwo tare da hannunsa.

4Ka miƙa kanka ga allolin domin yaƙin. Mu tashi, bari mu kai hari da rana. Bashi da kyau gama hasken rana yana dushewa, inuwoyin yamma suna faɗuwa.5Amma bari mu tashi da dare mu kai hari mu hallaka matsaranki."
6Gama Yahweh mai runduna ke faɗar haka: Ku sare itatuwanta, ayi tudu da aikin kewaye gãba da Yerusalem. Wannan shi nebirnin daya cancanci a kai wa hari, domin cike yake da zalunci.7Kamar yadda rijiya take bada ruwa, haka birnin yake sarrafa mugunta. Ana jin tashin hankali da rashin lafiya a cikinta, cuta da rauni kullum suna gabana.8Ki karɓi horo ya Yerusalem ko in juya daga gareki in sa ki cikin hallaka, ƙasar da babu mai zama ciki.
9Yahweh mai runduna ya faɗi wannan, "Hakika zasu yi kalar waɗanda suka ragu a Isra'ila kamar kuringar inabi. Ka sake sa hanunka ka tsinki inabi daga kuringa.10Ga wa zan sanar in kuma yi gargaɗi domin su ji? Duba! Kunnuwansu marasa kaciya ne; ba su iya saurarawa! Duba! Maganar Yahweh tazo gare su domin ta kwaɓesu, amma basu so ba."
11Amma na cika da hasalar Yahweh. Na gaji da daurewa a cikinta, Yace mani, "Ka zuba ta kan yara cikin tituna, da kan taron majiya ƙarfi. Gama kowanne miji za a ɗauke shi da matarsa; da kowanne tsoho mai yawan shekaru.12Za a ɗauki gidajensu aba waɗansu, gonakinsu da matansu gaba ɗaya. Gama zan kai hari ga mazaunan ƙasar da hannuna - wannan furcin Yahweh ne.
13Yahweh ya furta cewa daga ƙaraminsu zuwa babbansu, dukkansu suna haɗama wajen cin ƙazamar riba.14Daga annabi zuwa Firist, kowannensu yana aikata yaudara. Sun warkar da raunukan mutane na sama sama, suna cewa, 'Salama, Salama,' alhali kuwa ba salamar.15Suna jin kunya lokacin da suka aikata abin ƙyama? Basu jin kunya; basu san yadda zasu juye ba, Don haka zasu faɗi cikin masu faɗowa; za a kawo su ƙasa lokacin hukuncinsu, inji Yahweh.
16Yahweh yace, "Ka tsaya a mararrabar hanya ka duba, ka tambayi daɗaɗɗun tafarkun hanyoyi. 'Ina wannan hanya mai kyau take?' kayi tafiya kanta ka samarwa kanka wurin hutu. Amma mutane suka ce, 'Ba zamu je ba'17Na sa maku matsara ku saurari muryar ƙaho. Amma suka ce, 'Ba zamu saurara ba.'18Don haka ku saurara, al'ummai! ku duba, ku zama shaidar abin da zai same su.19Ki ji, ke duniya! Zan kawo masifa kan mutanen nan - 'ya'yan tunaninsu. Ba su saurari maganata ko dokata ba, amma sun ƙi ta."
20"Mene ne ma'anar wannan turare mai ƙanshi na lubban da ake kawowa daga sheba a gare ni? ko wannan ƙanshi mai daɗi daga ƙasa mai nisa? ƙonannun hadayunku ba abin karɓa ba ne a gareni ko sadakokinku.21Domin wannan Yahweh yace, 'Duba, zan sa sanadin tuntuɓe akan waɗannan mutane. Za suyi tuntuɓe a kan sa - Ubanni da 'ya'ya maza tare. Mazaunan tare da maƙwabtansu kuma zasu hallaka.'22Yahweh yace, 'Duba, al'umma tana zuwa daga ƙasar arewa. Za a zuga babbar al'umma su taso daga ƙasa mai nisa.
23Zasu ɗauki kibau da mãsu. Masu mugunta ne basu da tausayi. ‌Ƙ‌ararsu na ruri kamar teku, suna kuma hawan dawakai, sun fita a jere kamar mayaƙan mutane, gãba da ke, ɗiyar Sihiyona.'"24Mun ji rahotanni game dasu hannuwanmu kuma sun yi sanyi cikin azaba. Azaba ta kama mu kamar mace mai naƙuda.
25Kada ku fita zuwa filaye, kada ku yi tafiya kan hanyoyi, gama takubban abokan gaba da tsoratarwa suna koina.26Ɗiyar mutanena, ki sanya tsummoki ki kuma yi birgima cikin toka; ki yi makoki da kuka mai zafi kamar na tilon ɗa, gama mai hallakarwar zai zo kanmu ba zato.
27"Irmiya, Na maishe ka mai gwada mutanena, kamar mai gwada ƙarfe, zaka duba suka auna hanyoyinsu.28Mutane ne da suka fi kowa rashin ji, suna yawon ɓata waɗansu. Dukkansu jan karfe da baƙin ƙarfe suke, masu aikata cin hanci.29Mazuga suna zuga da wutar dake ƙonesu; dalma tana cinyewa cikin harshen wuta. Tacewar ta ci gaba tsakaninsu, amma bashi da amfani, saboda ba a kawar da muguntar ba.30Za a kira su azurfar da aka ƙi, gama Yahweh ya ƙi su."

7

1Maganar da ta zo ga Irmiya daga Yahweh, cewa,2Ka tsaya a ƙofar gidan Yahweh ka shaida wannan maganar! Kace, 'Ji maganar Yahweh, dukkan kuna Yahuda, ku da kuke shiga waɗannan ƙofofin kuyi ma Yahweh sujada.

3Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗa haka: Ku gyara hanyoyinku da ayyukanku da kyau, haka kuwa zan ƙyale ku ku ci gaba da zama a nan wurin.4Kar ku miƙa kanku ga maganganun ƙarya ku kuma ce, "Haikalin Yahweh! Haikalin Yahweh! Haikalin Yahweh!"
5Gama idan kun tabbatar da ayyukanku da hanyoyinku da kyau; idan kun aiwatar da adalci da gaskiya tsakanin mutum da makwabcinsa -6idan baku zalunci wanda ke zaune a ƙasar ba, da maraya da gwauruwa kuma baku zubar da jini a banza a nan wurin ba, kuma baku bi waɗansu allolin da zasu yi maku illa ba -7sa'annan zan ƙyale ku ku zauna a nan wurin, a ƙasar dana bayar ga kakanin ku daga zamanin zamanai da zuwa har abada.
8Duba!! kun amince da maganganu na ruɗami da ba zasu taimake ku ba.9Kuna sata da kisan kai da zina? kuna rantsuwar ƙarya da kuma miƙa turare ga Baal kuma kuna bin waɗansu allolin da baku sani ba?10Sa'annan sai kuzo ku tsaya a gabana a wannan gidan da ake kira da sunana kuma a ce, "An cece mu," saboda kawai kuyi dukkan waɗannan abubuwan banƙyama?11Wannan gidan dake ɗauke da sunana, ya zama ƙogon mafasa a idanunku? Amma duba, Na gani - wannan furcin Yahweh ne.'
12Saboda haka ku je wuri na dake shiloh, inda na bar sunana ya zauna nan da farko, kuma duba abin da nayi da ita saboda muguntar mutanena Isra'ila.13Don haka yanzu, ta dalilin yin waɗannan ayyuka - wannan furcin Yahweh ne - Nayi magana da ku lokuta zuwa lokuta, amma baku ji ba. Na kira ku amma baku amsa ba.14Saboda haka, abin da nayi a Shilo, Zan kuma yi ma gidan nan da ake kira da sunana, gidan da kuka amince, wannan wuri da na baku da kakaninku.15Gama zan aikar da ku waje daga gare ni kamar yadda na aikar da dukkan 'yan uwanku, dukkan zuriyar Ifraim.'
16Kai kuwa, Irmiya, kar ka yi wa mutanen nan addu'a, kuma kar ka ɗaga muryar makoki ko ka faɗi addu'a a madadinsu, kuma kada ka roƙe ni, gama ba zan ji ka ba.17Baka ga abin da suke yi a biranen Yahuda da titunan Yerusalem ba?18Yaran na tattara katako kuma Ubanin na kunna wuta! Matayen na ƙwaba ƙullu don yin gurasa domin sarauniyar sammai kuma suna zubo da hadayun ruwan inabi ga waɗansu alloli domin su tsokane ni.
19Da gaske tsokana ta suke yi? - wannan furcin Yahweh ne - ba kansu suke tsokana ba, har kunya ta kasance a kansu?20Hakika Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan, 'duba, fushina da hasalata zasu kwararo a wannan wurin, a kan mutum da dabba, a itatuwa na fili da 'ya'yan itace na ƙasa. Zata ƙone kuma ba za a ɓice ta ba.'
21Yahweh mai runduna, Allahn Isra'ila ya faɗi haka, 'Ku ƙara baye -bayen ƙonawa akan hadayarku da naman daga garesu.22Gama sa'adda na fito da kakaninku daga ƙasar Masar, ban nemi komai daga gare su ba. Ban basu ko umurni a kan zancen baye - baye na ƙonawa da hadayu ba.23Na basu wannan umurnin ne, "Ku saurare muryata, sai in zama Allahnku ku kuma ku zama mutanena. Saboda haka kuyi tafiya a hanyoyin da nake umurtar ku, don ya tafi maku dai-dai."
24Amma basu saurara ko su kula ba. Sun rayuwa ta bishewar shirye-shiryen taurin zuciyarsu, saboda haka suka koma baya, maimakon gaba.25Tun daga ranar da kakaninku suka fito daga ƙasar Masar har zuwa wannan ranar, Na aike kowanne ɗaya daga cikin barorina da annabawa na a gare ku. Nayi naciya yayin da nake aikar da su.26Amma basu saurare ni ba. Basu kula ba. Maimako, suka taurare wuyansu. Sun ma fi kakanninsu mugunta.'
27Saboda haka ka sanar da waɗannan maganganun gare su, amma ba zasu saurare ka ba. Faɗi waɗannan abubuwan a gare su, amma ba zasu ba ka amsa ba.28Kace masu Wannan ce al'ummar da ba zata saurari muryar Yahweh Allahnta ba kuma bata karɓi horaswa ba. An hallaka an datse gaskiya daga bakunansu.
29Ku yanke gashinku ku kuma yi wa kanku aski, ku kuma zubar da gashin kanku. Ku raira waƙar jana'iza a kan buɗaɗɗun wurare. Gama Yahweh ya ƙi kuma ya watsar da wannan tsara a cikin hasalarsa.30Gama 'ya'ya maza na Yahuda sun yi mugunta a idona - wannan furcin Yahweh ne - Sun sa abubuwan ƙyamarsu a cikin gidan da ake kira da sunana, domin su ƙazamtar dashi.
31Sa'annan suka gina babban wurin Tofet wanda ke cikin kwarin Ben Hinom. Sun yi haka don su ƙone 'ya'yansu maza da mata a wuta - abin da ban umurta ba, ko ya shiga zuciyata ba,32Saboda haka duba, rana na zuwa - Wannan furcin Yahweh ne - yayin da ba za'a ƙara kiran wurin Tofet ko kwarin Ben Hinnom ba. Zai zama kwarin yanka; za a binne jikkuna a Tofet har sai babu wurin da ya rage.
33Gawawwakin waɗannan mutanen zasu zama abincin tsuntsayen sararin sama da dabbobin duniya, kuma babu wanda zai tsoratar da su.34Zansa ƙarshen titunan Yahuda da na Yerusalem, ƙarar murna da ƙarar farin ciki, ƙarar ango da amarya, gama ƙasar zata zama lalatacciya."

8

1Wannan ne furcin Yahweh - a lokacin nan zasu fitar da kasusuwan sarakunan Yahuda da ofisoshinsu, kasusuwan firistoci da annabawa, da kasusuwan mazaunan Yerusalem daga kaburbura.2Sa'annan zasu shimfiɗa su a waje a hasken rana da wata da dukkan tauraron sararin sammai; waɗannan abubuwan na sararin sama da suka bi suka kuma bauta masu, da suka kuma bisu suka nemesu, kuma suka yi masu sujada. Baza a binne ko a tattara kasusuwan kuma ba, zasu zama kamar kashin dabba a fili.3A dukkan ragowar wuraren da na kore su zuwa, zasu zaɓi mutuwa a maimakon rai domin kansu, dukkan waɗanda aka bar su daga wannan muguwar al'umma - Wannan ne furcin Yahweh mai runduna.

4Saboda haka ka faɗa masu, 'Yahweh yace haka: Akwai wanda ya faɗi kuma bai tashi ba? Akwai wanda ya ɓace da bai yi ƙoƙarin dawowa ba?5Meyasa waɗannan mutanen, Yerusalem, suka juya baya da daɗewa cikin rashin bangaskiya? Sun rungume yaudara kuma sun ƙi su tuba.
6Na kula na kuma saurara, amma basu yi maganan dai - dai ba; ba wanda ke nadama da muguntarsa, ba wanda yace, "Mene ne na yi?" Dukkansu sun tafi wurin da suke so, kamar dokin da ke sauri zuwa fagen fama.7Ko shamuwar sama ma ta san lokutan da suka dace; kurciyoyi kuma, da dila da zalɓe. Suna kiyaye lokacin ƙaurarsu, amma mutanena ba su san dokokin Yahweh ba.
8Yaya zaku ce, "Mu masu hikima ne, don umurnin Allah na tare da mu"? Hakika ku duba! alƙalamin ƙarya na magatakarda ya ƙirƙiro ƙarya.9Mutane masu hikima zasu ji kunya. Zasu tsorata su kuma cafku. Duba! Sun ƙi maganar Yahweh, to mene ne amfanin hikimarsu?10Saboda haka zan bada matayensu ga waɗansu, filayensu kuma ga waɗansu su mallaka, don daga mafi ƙanƙantarsu zuwa babbansu, kowannensu ya na haɗamar cin ƙazamar riba! Daga annabi zuwa firist, dukkansu suna aikata ha'inci.
11Sun warkar da raunin mutanena sama - sama, suna cewa, "Salama, Salama," sa'adda babu salama.12basu ji kunya ba ne a sa'adda suke ayyukan banƙyama? Basu ji kunya ba; basu san yadda zasu kunyata ba! Saboda haka zasu faɗi cikin faɗaɗɗu; za a kawo su ƙasa sa'adda ake horar da su, inji Yahweh.13Zan tuge su kakaf - wannan furcin Yahweh ne - baza a sami inabi a itacen inabi ba, ko 'ya'ya a itacen ɓaure ba, gama ganyen zai bushe, kuma abin da na basu zai ƙuɓuce masu.
14Me yasa muke zama a nan? kuzo mu taru; bari mu je garuruwa masu garu, kuma mu yi shiru a can cikin mutuwa. Gama Yahweh Allahnmu zai sa muyi tsit. Zai sa mu sha guba, tunda mun yi masa laifi.15Muna fatan salama, amma babu wani abu mai kyau. Muna fatan lokacin warkarwa, amma duba, za a sami razana.
16Firjin dawakansa aka ji daga Dan. Dukkan duniya ta girgiza saboda haniniyar ingarmun ƙarfafan dawakansa. Gama zasu zo su cinye ƙasar da wadatarta, birni da masu zama cikinsa.17Gama ku duba! Ina aikar da macizai a cikinku, kãsayen da ba zaku samu makarinsu ba. Zasu cije ku -Wannan furcin Yahweh ne."'
18Baƙincikina ba shi da ƙarshe, kuma zuciyata na ciwo.19Duba!! Muryar ihun ɗiyar mutanena daga ƙasa mai nisa! Babu Yahweh a Sihiyona ne? Ko ba sarkin a cikinta? Me ya sa suke cakuna ta zuwa fushi da sassaƙaƙƙun sifofinsu da banzayen bãƙin gumakansu?
20Girbi ya ƙare, damuna kuma ta wuce. Amma ba a cece mu ba.21Na raunana saboda raunin ɗiyar mutanena. Nayi makokin a kan abubuwan tsoron da suka same ta; Na tsorata.22Babu wani magani a Giliyad ne? Babu mai warkarwa a can ne? Me zai hana warkarwar ɗiyar mutanena ta faru?

9

1Da ma kaina zai ɓullo da ruwa, kuma idanuna su zama maɓuɓɓular hawaye! Gama ina tunanin yin kuka rana da dare domin waɗanda ke cikin ɗiyar mutanena da aka kashe.2Da ma wani zai bani wuri domin matafiya a hamada su zauna, inda zan je in rabu da mutanena. Da ma zan iya barin su, tunda dukkansu mazinata ne, ƙungiyar maciya amana!3Yahweh ya furta, "Sun tanƙwasa bakkunan ƙarerayinsu da na harsunansu, amma ba don wani amincinsu ne ya sa suka yi ƙarfi a duniya ba. Suna ta ci gaba daga aikin mugunta ɗaya bayan ɗaya. Basu san ni ba."

4Kowannen ku, yayi hankali da maƙwabcinsa kuma kada ya amince da kowanne irin ɗan'uwa. Gama kowanne ɗan'uwa hakika mayaudari ne, kuma kowanne maƙwabci mai kushe ne.5Kowanne mutum yana yiwa maƙwabcisa ba a kuma ba ya faɗin gaskiya. Harsunansu na koyar da abubuwan ƙarya. Sun rafke daga aikata laifi.6Zamanku na cikin ruɗu; a cikin yaudararsu sun ƙi su shaida ni - Wannan furcin Yahweh ne."
7Yahweh mai runduna ya faɗi haka, "Duba, Ina gab da tsabtace su in kuma gwada su, gama me zan iya yi, saboda abin da mutanena suka yi?8Harsunansu kibiyoyi masu kaifi ne; suna faɗin abubuwan rashin aminci. Da bakunansu suna shaida salama ga maƙwabtansu, amma da zukatansu suna shirya masu maƙarƙashiya.9Ba zan hukuntasu saboda waɗannan abubuwan ba - wannan shi ne furcin Yahweh - kuma ba zan rama wa al'umma irin wannan ba?
10Zan raira waƙar makoki da kururuwa saboda duwatsu, kuma za a raira wakar jana'iza domin wuraren kiwo. Gama an ƙone su don kar kowa ya wuce ta wurinsu. Ba zasu ji kukan wata dabba ba. Tsuntsaye da namomin daji sun gudu sun tafi.11Saboda haka Zan maida Yerusalem tsibin kufai, maɓoyar diloli. Zan maida biranen Yahuda kufai inda ba mazauna."12Wanne mutum ne ke da isasshiyar hikima ya gane wannan? Ga wane ne bakin Yahweh yayi magana, kuma zai faɗe shi? Me yasa ƙasar ta lalace an kuma hallakar da ita kamar hamadar da ba wanda zai iya wucewa ta cikinta?
13Sai Yahweh yace, "Saboda sun ƙi dokokin da na shirya a gare su, saboda basu saurari muryata ko su yi aiki da ita ba.14Saboda sun yi tafiya da taurarrar zuciyarsu suka kuma bi Ba'aloli kamar yadda ubanninsu suka koya masu suyi.
15Saboda haka Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi haka, 'Duba, Ina gab da sa mutanen nan suci abinci mai ɗaci da ruwan dafi.16Sa'annan zan watsar dasu cikin al'ummar da basu sani ba da su da kakaninsu. Zan aikar da takobi ya bi su har sai na hallaka su kakaf."'
17Yahweh mai runduna ya faɗi haka, "Kuyi tunani a kan wannan: Ku kira masu waƙar jana'iza; bari su zo. Ku aiko a kira matayen da suka ƙware a makoki; bari suzo.18Bari su yi sauri su raira waƙar makoki a kanmu, saboda idanuwanmu su iya zubar da hawaye kuma girar idanuwanmu ta malalo da ruwa.
19Gama an jin muryar kuka a Sihiyona, 'Yaya muke lalacewa. Mun ji kunya sosai, gama mun yi watsi da ƙasar tun da suka rurrushe gidajenmu.'20Saboda haka ku mataye, ku ji maganar Yahweh; ku kula da saƙonni dake zuwa daga bakinsa. Sa'annan ku koyar da 'ya'yanku mata waƙar makoki, kuma kowacce mace maƙwabciya waƙar jana'iza.
21Gama mutuwa ta iso ta tagoginmu; ta shigo cikin fãdodinmu. Ta hallaka yara daga waje, da 'yan maza a dandalin biranen.22Ka faɗi haka, 'Wannan furcin Yahweh ne - gawawwakin mutane zasu faɗo kamar kashin dabbobi a gonaki, kuma kamar dammunan masu girbi, kuma babu wanda zai tara su."'
23Yahweh ya faɗi haka, "Kada ka bar mutum mai hikima yayi taƙama da hikimarsa, ko jarumi a cikin ƙarfinsa. Kada ka bar mai arziki yayi taƙama da arzikinsa.24Gama idan mutum yayi taƙama da wani abu, bari ya zama a wannan, cewa yana da fahimta kuma ya san ni. Gama ni ne Yahweh, wanda yake aiki da alƙawarin aminci da adalci da ayyukan adalci a duniya. Gama a cikin waɗannan ne nake murna - wannan furcin Yahweh ne."
25Duba, kwanaki na zuwa - wannan furcin Yahweh ne - sa'adda zan horar da dukkan masu kaciya a jiki kawai.26Zan horar da Masar da Yahuda da Idom da mutanen Ammon da Mowab da dukkan mutanen da ke yanke gashin kansu suna sanƙo. Domin dukkan waɗannan al'umman marasa kaciya ne, kuma dukkan gidan Isra'ila suna da zuciya marar kaciya."

10

1"Ku ji maganar da Yahweh yake sanar daku, ya gidan Isra'ila.2Yahweh ya faɗi haka, 'Kar ku koyi hanyoyin al'ummai, kuma kada ku da mu da alamun cikin sammai, domin al'ummai na damuwa da waɗannan ne.

3Gama al'adun addinin mutanen nan na banza ne. Suna sare itace a cikin jeji, kuma gwanayen sassaƙa na sassaƙa katako.4Sa'annan suka ƙayata shi da azurfa da zinari. Sun inganta ƙarfin shi da guduma da ƙusa don kada ya faɗo.5abin da suka yi da hanuwansu yana kama da mutummutumi a gonar kukumba, saboda su, ma, ba zasu iya cewa komai ba, kuma ɗaukarsu ake yi domin ba zasu iya tafiya ba. Kada ku ji tsoronsu, gama ba zasu iya jawo mugunta, ko kuma su iya yin wani abu maiƙyau ba."'
6Babu wani kamarka, Yahweh. Kai mai girma ne, kuma sunanka na da girma cikin iko.7Wane ne ba ya jin tsoron ka, sarkin al'ummai? Don ka cancanci haka, gama babu wani kamar ka a cikin dukkan mazaje masu hikima na al'ummai ko dukkan mulkokinsu masu martaba.
8Dukkansu iri ɗaya ne, su daƙiƙai da wawaye ne, almajiran gumaka da ba kome ba ne sai itace.9Suna kawo sarafaffiyar azurfa daga Tarshish da zinariya daga Ufaz waɗanda ƙwararru suka yi, da hannuwan maƙera. Tufafinsu na mulifi da shunayya ne. Gwanayensu ne suka yi dukkan waɗannan abubuwan.10Amma Yahweh shi ne Allah na gaskiye. Shi ne Allah mai rai da madawamin sarki. Fushinsa yakan girgiza duniya, kuma al'ummai ba zasu jure fushinsa ba.
11Zaka yi magana da su kamar haka, "Allolin da basu yi sammai da duniya ba zasu lalace daga duniya kuma daga ƙarƙashin waɗannan sammai."12Amma shi ne wanda yayi duniya ta ikonsa, ya kuma kafa ta ta wurin hikimarsa, kuma ta fahimtarsa ya miƙar da sammai.13Muryarsa ta yi ƙugin ruwa a sammai, ya kuma kawo hayaƙi daga kurewar duniya. Yakan yi walƙiyoyi domin ruwan sama ya kuma aikar da iska daga taskokinsa.
14Kowanne mutum ya zama jahili da marar ilimi. Kowanne maƙerin zinariya zai sha kunya ta dalilin gumakansa. Gama ƙerarrun siffofinsu ƙarya ne; Babu rai a cikinsu.15Basu da amfani, aikin masu ba'a; zasu lalace a lokacin horonsu.16Amma Allah, madogarar Yakubu, ba haka yake ba, gama shi ne yayi dukkan abubuwa. Isra'ila kabilar gãdonsa ne; Yahweh mai runduna ne sunansa.
17Ku tattara kayayyakinku ku bar ƙasar, ku mutanen dake zaune a wuraren dake kewaye da yaƙi.18Gama Yahweh ya faɗi haka, "Duba, Ina gab da jefar da mazaunan ƙasar waje a wannan lokacin. Zan kawo masu ƙunci, kuma zasu kuwa same shi a hakan."
19Kaito na! Saboda karyayyun ƙasusuwana, raunina ya sami lahani. Saboda haka na ce, "Tabbas wannan azaba ce, amma zan jure."20An lalatar da rumfata, kuma dukkan igiyoyin rumfata an yanke su biyu. An ɗauke 'ya'yana daga gare ni, saboda haka basu nan. Babu wanda zai yi shimfiɗa a rumfata ko mai ɗaga labulolin rumfata.
21Gama makiyayan wawaye ne kuma ba sa biɗar Yahweh; saboda haka basu wadata ba, kuma dukkan garkensu an warwatsar.22Rohotonin labarai sun iso, "Duba! Tana zuwa, babbar girgizar ƙasa tana zuwa daga ƙasar arewaci ta sa biranen Yahuda su zama kufai, maɓuya domin diloli."
23Na sani, Yahweh, cewa hanyar mutun ba daga kansa take fitowa ba. Babu mutumin dake jagorar tafiyarsa da takawar kansa.24Ka tsauta mani, Yahweh, da adalci, ba a cikin fushinka ba domin kada ka hallaka ni.25Ka kwarara hasalarka ga al'umman da basu san ka ba, da iyalan da basu kira bisa sunanka. Gama sun cinye Yakubu sun kuma haɗiye shi saboda su hallakar da shi kakaf su kuma rushe mazauninsa.

11

1Maganar da tazo ga Irmiya daga Yahweh, cewa,2"Ka saurari maganganun wannan alƙawari, kuma ka furta su ga kowanne mutum a Yahuda da kuma ga mazaunan Yerusalem

3Ka ce masu, 'Yahweh, Allah na Isra'ila ya faɗi haka: La'ananne ne duk wanda ba ya sauraron maganganun wannan alƙawari.4Wannan shi nealƙawarin da na umurci kakaninku su cika a ranar dana fito da su daga ƙasar Masar, Daga tanderun sarrafa ƙarfe. Nace, "Ku saurari muryata ku kuma yi dukkan waɗannan abubuwan kamar yadda na umurce ku, gama zaku zama mutane na ni kuma In zama Allahnku."5Kuyi mani biyayya saboda in cika rantsuwar da na yi ma kakaninku, rantsuwar cewa zan ba su ƙasar dake kwararo da madara da zuma, inda kuke zama a yau." Sa'annan Ni Irmiya, na amsa nace, "I, Yahweh!"
6Yahweh yace mani, "Kayi shelar waɗannan abubuwan a cikin biranen Yahuda da titunan Yerusalem. Kace, Ku saurari maganganun wannan alƙawari ku kuma aikata su.7Gama na yi ta bayar da tsarkakan umarnai na ga kakaninku daga ranar da na fitar dasu daga ƙasar Masar har zuwa wannan lokacin, nayi ta faɗakar da su cewa, "Ku saurari muryata."8Amma basu saurara ko su kula ba. Kowanne mutum yana tafiya a cikin taurarriyar muguntar zuciyarsa. Saboda haka na kawo dukkan la'anonin cikin wannan alƙawarin da na umurta su zo gare su. Amma mutanen basu yi biyayya ba duk da haka."
9Biye da haka Yahweh yace mani, "An gano tawaye a cikin mutanen Yahuda da mazunan Yerusalem.10Sun juya zuwa zunuban kakaninsu na farko, waɗanda sun ƙi su saurari maganata, maimakon haka suka bi waɗansu alloli suka bauta masu. Gidan Yahuda da na Isra'ila sun karya alƙawarina da na kafa da kakaninsu.
11Saboda haka Yahweh ya faɗi haka, 'Duba, Ina gab da kawo bala'i a kansu, bala'in da ba zasu iya kuɓutar da kansu ba. Sa'annan zasu yi kira gare ni, amma ba zan saurare su ba.12Biranen Yahuda da mazaunan Yerusalem zasu je su yi kira ga allolin da suka bada baye-baye gare su, amm hakika ba zasu sami ceto ta wurinsu a lokacin bala'insu ba.13Gama ke Yahuda, allolinki sun ƙaru dai - dai da yawan biranenki. Kin yi yawan bagadanki masu ban kunya a Yerusalem, da turaren bagadai domin Ba'al, dai - dai da yawan titunanta.
14Saboda haka kai kanka, Irmiya, kada kayi wa mutanen nan addu'a. Kada kayi kuka ko addu'a a madadin su. Gama ba zan saurara ba sa'adda suka kira ni a lokacin bala'insu.15Me ya sa ƙaunatacciyata, wadda take da mugayen ƙudurori da yawa, take ta aikata su a gidana? Naman hadayunki ba zasu iya taimakonki ba. Kina farinciki saboda mugayen ayyukanki.16A baya Yahweh ya kira ki itacen zaitun mai duhuwa, kyakyawa mai 'ya'yan da ake so. Amma zai cinna wuta a kanta wadda zata yi ƙara kamar iskar guguwa; rassanta zasu kakkarye.
17Gama Yahweh mai runduna, shi wanda ya dasa ku, ya furta bala'i gãba da ku saboda mugayen ayyukan da gidan Isra'ila da na Yahuda suka yi - sun sa na husata ta wurin yiwa Ba'al baye-baye."'
18Yahweh ya sa na san waɗannan abubuwan, saboda haka na sansu. Kai, ya Yahweh, ka sa na ga ayyukansu.19Ina kama da ɗan rago mai sauƙin kai wanda ake ja zuwa mayanka. Ba ni da sanin cewa sun yi maƙarƙashiya gãba da ni, "Bari mu lalatar da itacen da 'ya'yansa! Bari mu datse shi daga ƙasar masu rai saboda kada a sake tunawa da sunansa."20Duk da haka Yahweh mai runduna Mai yin shari'ar adalci ne wanda yake bincike zuciya da tunani. Zan shaidi sakayyarka game da su, gama na danƙa maganata a gare ka.
21Saboda haka Yahweh ya faɗi haka game da mutanen Anatot dake biɗar ranka, "Suka ce, 'Kada ka kuskura kayi annabci da sunan Yahweh, ko ka mutu ta hannun mu.'22Domin haka Yahweh mai runduna ya faɗi haka, 'Duba, Ina gab da hukunta su. Samarinsu masu ƙarfi zasu mutu ta takobi. 'Ya'yansu maza da mata zasu mutu saboda yunwa.23Babu waninsu wanda za a bari, domin Ina tahowa da masifa gãba da mutanen Anatot, a shekarar hukuncinsu."'

12

1Kai adali ne, Yahweh, duk lokacin dana kawo rashin jituwata a gare ka. Hakika zan faɗa maka dalilin ƙarata: Me yasa hanyoyin mugaye suke yin nasara? Dukkan marasa bangaskiya suna cin nasara?2Ka dasa su kuma suka yi saiwa. Sun ci gaba da bada 'ya'ya. Kana kusa da su a cikin bakunansu, amma nesa daga zuciyarsu.

3Duk da haka kai, Yahweh, ka san ni. Kana gani na kuma kana gwada zuciyata gare ka. Ka ɗauke su kamar tunkiyar da ake kaiwa mayanka, ka ware su domin ranar yanka!4Yaushe ƙasar zata ci gaba da bushewa, kuma tsire-tsiren kwace gona ke yaushi saboda muguntar mazaunanta? Dabbobi da tsuntsaye an ɗauke. Hakika, mutanen sun ce, "Allah ba zai ga abin da zai faru da mu ba."
5Yahweh yace, "hakika, idan kai, Irmiya, kayi tsere da sojojin ƙafa suka kuma gajiyar da kai, to yaya zaka yi gasa gãba da dawakai? Idan ka faɗi a lafiyayyar karkara, ƙaƙa zaka yi a kurmin Yodan.6Gama ko 'yan'uwanka da gidan mahaifinka sun basheka sun kuma ƙi ka ƙiri-ƙiri. kada ka amince da su, ko sun faɗi maka abubuwa masu daɗi.
7Na yashe da gidana; Na rabu da gãdona. Na bada ƙaunatacciyata cikin hannuwan maƙiyanta.8Abar gãdona ta zamar mani kamar zaki a kurmi; ta kafa kanta gãba da ni da muryarta, saboda na ƙi jininta.9Ashe mallakar da nake ji da ita ta zama dabbare-dabbaren tsuntsu, wacce manyan tsuntsaye ke farauta gãba da ita a kewaye? Tafi ka tattaro dukkan namomin jeji ka kuma kawo su su lanƙwameta.
10Makiyaya da yawa sun lalatar mani da garkar inabi. Sun tattake kan dukkan nawa rabon ƙasar; sun maida kyakkyawan rabona hamada da kufai.11Sun maida ita ba komai. Ina makoki domin ta; ba ta da komai. Dukkan ƙasar an maida ita kango, gama ba wanda ya ɗauke abin a zuciya.
12Masu hallakarwa sun zo gãba da dukkan tsaunukan cikin hamada, gama takobin Yahweh tana hallakarwa daga wannan iyakar ƙasa zuwa waccan. Babu kwanciyar hankali a ƙasar domin kowacce hallita mai rai.13Sun shuka alkama sun girbi ƙayayuwa. Sun gaji da aiki amma basu samu ribar komai ba. Saboda haka ku ji kunyar ribarku saboda fushin Yahweh."
14Yahweh ya faɗi haka a kan dukkan maƙwabtana, mugayen da suka taɓa mallakar dana sa mutanena Isra'ila suka gada, "Duba, Nine wanda ke gab da tumɓuke su daga ƙasarsu, kuma zan jawo gidan Yahuda daga cikinsu.15Sa'annan bayan na tumɓuke waɗancan al'ummai, zai zamana zan sake jin tausayinsu in kuma komo da su; Zan komar da su - kowanne mutum ga gãdonsa da ƙasarsa.
16Zai kuwa zamana idan waɗancan al'umman zasu himmantu su koyi hanyoyin mutanena, su yi rantsuwa da sunana 'In dai Yahweh na raye' kamar dai yadda suka koya ma mutanena suyi rantsuwa da Ba'al, to su ma zasu ginu a cikin mutanena.17Amma idan ba wanda ya saurara, sai in tumɓuke wannan al'ummar. Hakika za a tumɓuke ta a kuma hallakata - wannan furcin Yahweh ne."

13

1Yahweh yace da ni haka, "Jeka ka sayi lilin na yin ɗamara kuma ka sa shi kewaye da kwankwasonka, amma kar ka sa shi a ruwa da farko"2Saboda haka na sayi ɗamarar kamar yadda Yahweh ya jagorance ni, sai na rataya kewaye da kwankwasona.3Daga nan maganar Yahweh ta zo a gare ni karo na biyu, cewa,4"Ka ɗauki ɗamarar da ka saya wadda ke kewaye da kwankwasonka, ka tashi ka tafi yanzu zuwa Ferat. Ka ɓoye ta nan a ƙogon tsaguwar dutse."5Sai na tafi na ɓoye ta a Ferat, kamar yadda Yahweh ya umarce ni.

6Bayan kwanaki da yawa, Yahweh yace mani, "Tashi ka koma Ferat. Ka ɗauki ɗamarar da na ce ka ɗauka daga wurin da ka ɓoye."7Sai na koma Ferat na kuma haƙo ɗamarar a inda na ɓoye ta, kuma duba, ta lalace dukka kuma babu amfani.
8Sai maganar Yahweh tazo gare ni, cewa,9Yahweh ya faɗi haka: Ta dai wannan hanyar zan hallakar da gagarumin kumbura kan Yahuda a Yerusalem.10Waɗannan miyagun mutanen da suka ƙi su raurari maganata, waɗanda ke tafiya a cikin taurin zuciyarsu, waɗanda ke bin bayan waɗansu alloli suyi masu sujada suka kuma russuna masu - zasu zama kamar wannan ɗamarar da ba ta da amfani.11gama kamar yadda ɗamarar nan ta ke manne wa ƙwanƙwason wani, haka na maida gidan Isra'ila da dukkan gidan Yahuda su manne mani - wannan furcin Yahweh ne - su zama mutanena, su kawo mani shahara, a ko'ina da yabo, da girmamawa. Amma ba su saurare ni ba.
12Saboda haka, dole ka faɗa masu wannan magana, 'Yahweh, Allah na Isra'ila, yace: Za a cika kowanne gora da ruwan inabi.' Zasu ce da kai, "Ashe bamu sani hakika cewa kowanne gora za a cika shi da ruwa ba?'13Sai kace da su, Yahweh ya faɗi haka: Duba, Ina gab da cika dukkan mazaunan wannan ƙasa da buguwa, sarakunan dake zaune a kursiyin Dauda da firistoci da annabawa da mazaunan Yerusalem.14Sa'annan zan sa su kara da junansu, iyaye maza da 'ya'yansu tare - wannan shi ne furcin Yahweh - Ba zan ji tausayinsu ko juyayinsu ba, kuma ba zan kiyaye su daga hallaka ba."'
15Ku saurara ku kuma natsu. Kada ku kumbura kai, gama Yahweh yayi magana.16Ku girmama Yahweh Allahnku kafin ya kawo duhu, kafin kuma yasa ƙafafunku su yi tuntuɓe akan duwatsu da hasken asuba. Gama kuna begen haske, amma zai maishe da wurin duhu baƙƙi ƙirin, zuwa baƙin girgije.17Saboda haka idan ba zaku saurara ba, zan yi kuka ni kaɗai saboda kumbura kanku. idanuwa na zasu yi kuka ƙwarai kuma su zub da hawaye, domin an ɗauke garken Yahweh zuwa bauta.
18Kace da sarki da kuma mahaifiyar sarki, 'Ku sauko daga bisa kursiyoyinku, gama rawwunanku masu daraja sun faɗi daga kawunanku.'19Biranen cikin Negeb za a rufe su, kuma babu wanda zai buɗe su. Za a ɗauke Yahuda zuwa bauta, dukkan ƙasar zuwa bauta.
20Ku ta da idanuwanku ku ga waɗanda ke tahowa daga arewa. Ina garken da ya baku, garken dake kyakkyawa a gare ku?21Me zaku ce sa'adda Allah ya naɗa a kanku shugabanin da kuka koyar su zama muhimman aminanku? Ashe ba waɗannan ba ne mafarin zafin azabai da zasu mamaye ku kamar mace mai naƙuda?
22Sa'annan zaku iya cewa a zuciyarku, 'Me yasa waɗannan abubuwan suke faruwa da ni?' Zai zama domin yawan zunubanku ne shi yasa an ɗaga ɗantofinku kuma an wulaƙanta ku.23Mutanen Kush zasu iya sake launin fatarsu, ko kuwa damisa zata iya sake dabbare-dabbarenta? Idan haka ne, to ku kanku, duk da dai kun saba da yin mugunta, zaku iya yin nagarta.24Saboda haka zan watsar da su kamar ƙaiƙayi da kan lalace a iskar hamada.
25Wannan shi ne abin da na baku, rabon da nayi doka dominku - wannan Furcin Yahweh ne - saboda kun mance da ni kun dogara ga ruɗu.26Saboda haka kuma Ni kaina zan kware ɗantofinku, kuma za a ga tsiraicinku.27Na ga zinarki da haniniyarki, da muguntar karuwancinku akan tuddai da cikin gonaki, na kuma ga waɗannan abubuwa masu ban ƙyama! kaiton ki, Yerusalem! Har tsawon wanne lokaci ne zaki sake wankuwa kuma?"

14

1Wannan ita ce maganar Yahweh da tazo wurin Irmiya game da fari,2"Bari Yahuda ta yi makoki; bari ƙofofinta su lalace. Suna kuka domin ƙasar; kukansu domin Yerusalem ta hau sama.3Manyansu sun aiki barorinsu su ɗebo ruwa. Da suka je maɓuɓɓuga, sun tarar ba ruwa. Sai dukkansu suka koma ba tare da samun kome ba, sun lulluɓe kawunansu don kunya da ƙasƙanci.

4Domin wannan ƙasar ta tsage, domin babu ruwan sama a ƙasar. Manoma sun sha kunya har sun lulluɓe kawunansu.5Ko dama barewa ma a saura ta kan gudu ta bar 'ya'yanta sabuwar haihuwa, don ba ciyawa.6Jakunan jeji sukan tsaya akan huntun sararinsu na haki kamar diloli. Idanuwansu ba sa gani, domin ba abinci."
7Ko da yake zunubanmu suna shaida gãba da mu, Yahweh, kayi taimako saboda sunanka. Gama rashin amincinmu yayi yawa; mun yi maka zunubi.8Kai ne begen Isra'ila, mai cetonta a lokacin wahala, ƙaƙa zaka zama kamar baƙo a ƙasar, kamar mai tafiyar yawon buɗe ido wanda ya kwanta a gefen hanya don ya kwana ɗaya?9Ƙaƙa zaka zama kamar jarumin da ya kãsa iya ceton kowa? Duk da haka kana nan a tsakiyarmu, Yahweh, da sunanka ake kiranmu. Kada ka barmu!
10Yahweh yace wannan akan waɗannan mutanen: "Tun da suna ƙaunar yawace-yawace, basu iya daina wa ba."11Yahweh ba ya jin daɗinsu. Yanzu zai tuna da laifofinsu ya kuma hukunta zunubansu. Yahweh yace mani, "Kada kayi addu'a domin lafiyar waɗannan mutane.12Ko da sun yi azumi, ba zan saurare kukansu ba, kuma ko da sun mika hadaya ta ƙonawa da hadayar abinci, ba zan karɓe su ba. Amma zan kawo ƙarshensu da takobi, yunwa, da annoba."
13Sai na ce, "Ah, Ubangiji Yahweh! Duba!! Annabawa suna gayawa mutane, 'Ba zaku ga takobi ba; babu yunwa domin ku, amma zan baku dawwamammen tsaro a wannan wuri.'"14Yahweh yace mani, "Annabawa suna annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba, ko kuwa in basu wani umarni ko kuma in yi magana da su. Amma ƙarairayi da wahayin ƙarya ne, ƙaryar duba da suke yi marar amfani suna fitowa daga tunaninsu waɗanda suke annabcin ƙarya ne."
15Saboda haka ga abin da Yahweh yace, "Akan annabawan da suke yin annabci da sunana amma ba ni ne na aikesu ba - waɗanda suka ce baza a yi takobi ko yunwa ba a ƙasar. Waɗannan annabawa zasu hallaka da takobi da yunwa.16Kuma mutanen da suka yi wa annabci za a jefar dasu waje cikin titunan Yerusalem domin yunwa da takobi, har ma babu wanda zai binne su - su, da matayensu da 'ya'yansu maza da mata - don zan sa muguntarsu a kansu.
17Faɗa masu wannan magana: 'Bari idanuna suyi ta zub da hawaye, dare da rana. Kada su daina, saboda akwai babbar aukawar budurwa 'yar mutane na -babban rauni marar warkewa.18Idan na tafi cikin saura, akwai su da yawa da aka kashe da takobi! Idan kuma na shiga cikin birni, akwai cututtukan da yunwa ta kawo. Gama annabi da firist yawace-yawace suke ta yi a ƙasar, kuma basu sani ba.'"
19Ka ƙi Yahuda kenan dungum? Kana ƙin Sihiyona ne? Me yasa zaka azabtar da mu sa'adda babu warkarwa domin mu? Muna begen salama, amma ba wani abin kirki - don lokacin warkewa, amma ku gani, sai dai tsoro kaɗai.20Mun yarda, Yahweh, laifofinmu da muguntarmu da ta kakanninmu, gama mun yi maka zunubi.
21Kada ka ƙi mu! Saboda darajar sunanka, kada kuma ka ƙasƙantar da darajar kursiyinka. Ka tuna kada kuma ka karya alƙawarinka da mu.22A cikin gumakan al'ummai marasa amfani akwai mai iya sa sammai su bada ruwa? Ba kai kaɗai ba ne, Yahweh Allahnmu, wanda yayi wannan? Mun sa bege a gare ka, gama kai ne mai yin waɗannan abubuwa dukka.

15

1Sai Yahweh yace da ni, "Ko da Musa ko Sama'ila zasu tsaya a gabana, duk da haka ba zan nuna wa waɗannan mutanen tagomashi ba. Ka kore su daga gabana, don su yi tafiyarsu.2Zaya zama sa'ad da suka ce da kai, 'Ina zamu tafi?' Sai ka faɗa masu, Yahweh ya faɗi wannan: Waɗanda an ƙaddara su mutu su tafi ga mutuwa; waɗanda suke na takobi su tafi ga takobi. Waɗanda suke na yunwa su tafi ga yunwa; kuma waɗanda suke na bauta su tafi ga bauta.'

3Zansa su kasance kashi huɗu - wannan furcin Yahweh ne - takobi na kisan wasu ne, karnuka su yayyaga wasu, tsutsaye sararin sama da dabbobin duniya don su cinye su kuma hallakar da wasu.4Zan kuma sa su zama abin banƙyama ga dukkan mulkokin duniya, saboda abin da Manassa ɗan Hezekiya, sarkin Yahuda, ya aikata a Yerusalem.
5Amma wa zai ji tausayinki, Yerusalem? Wa zai yi baƙinciki domin ki?6Kun yashe ni - wannan furcin Yahweh ne - kun koma baya daga gare ni. Saboda haka zan buge ku da hannuna in kuma hallaka ku. Ni na gaji da nuna maku jinƙai.7Saboda haka zan sheƙe su da abin shiƙa a ƙofofin garuruwan ƙasar. Zansa su makoki. Zan hallaka mutanena tun da ba zasu juyo daga mugayen hanyoyinsu ba.
8Zan yawaita gwaurayensu fiye da yashi a bakin teku. Game da uwayen samari zan aika da hallakarwa da tsakar rana. Zan sa azaba da razana su auko masu farat ɗaya.9Uwar da ta haifi 'ya'ya baƙwai zata yi yaushi ta suma. Faɗuwar ranarta zata zo tun da rana. Zata ji kunya da wulaƙanci, don zan bada waɗanda suka ragu ga takobi a gaban abokan gãbarsu -wannan furcin Yahweh ne."
10Kaito na, mahaifiyata! Domin ke kika haife ni, ni ne mutum mai jayayya da gardama cikin dukkan ƙasar. Ban bada rance ba, ko wani ya bani rance, duk da haka dukkansu suna zagina.11Yahweh yace: "Ba zan ceto ka domin alheri ba? Babu shakka zansa abokan gãbarka su roƙi taimako a lokacin bala'i da masifa.12Wani zai iya karya ƙarfe? Musamman ƙarfe daga arewa wanda aka haɗa da tagulla?
13Zan bada wadatarku da dukiyarku ganima kyauta ga abokan gãbarku. Zan yi wannan saboda dukkan zunubanku da kuka aikata a dukkan iyakarku.14Zansa ku bautawa abokan gãbarku a cikin ƙasar da ba ku sani ba, gama wuta zata kama, zata kunnu a cikin fushina gãba da ku."
15Yahweh, ka sani! Ka tuna da ni ka kuma taimake ni. Ka kawo mani fansa ka kuma sãka wa waɗanda suke tsananta mani. Kai mai haƙuri ne, amma kada ka bar su su tafi da ni; ka sani na sha wahala saboda kai.16An sami magangaanunka, na kuwa cinyesu. Maganganunka sun zamar mani abin murna da farincikin zuciyata, gama ana kira na da sunanka, Yahweh, Allah mai runduna.
17Ban zauna cikin ƙungiyar waɗanda suke annashuwa ko murna ba. Na zauna ni kaɗai saboda hannunka mai iko, gama ka sa na cika da haushi.18Me yasa azabata ta ƙi ƙarewa kuma raunukana ba sa warkewa? Zaka yaudare ni kamar ruwaye, ruwaye masu ƙafewa?
19Domin wannan ga abin da Yahweh yace, "Idan ka tuba, Irmiya, sai in komo da kai, sa'annan zaka tsaya a gabana ka kuma bauta mani. Gama idan ka ware abubuwan dake banza daga abubuwa masu daraja, zaka zama kamar bakina. Sai mutanen su dawo wurinka, amma kai ba zaka koma wurinsu ba.20Zan maishe ka kamar garun tagulla da ba za a iya hudawa ba ga waɗannan mutane, zasu yi yaƙi da kai. Amma ba zasu yi nasara a kanka ba, gama ina tare da kai don in cece ka kuma in kuɓutar da kai -wannan furcin Yahweh ne -21gama zan kuɓutar da kai daga hannun mugaye kuma zan fanshe ka daga hannun marasa tausayi."

16

1Sai maganar Yahweh tazo gare ni, cewa,2"Kada ka auri mata domin kanka, kuma kada ka sami 'ya'ya maza da 'ya'ya mata domin kanka a wannan wuri.3Gama Yahweh yace waɗannan 'ya'ya maza da mata waɗanda za a haifa a wannan wuri, da kuma iyayensu mata waɗanda zasu haife su, da iyayensu maza da zasu sa a haife su a wannan ƙasa,4'Zasu mutu da muguwar cuta. Baza a yi makoki ko a bisne su ba. Zasu zama kamar juji a ƙasa. Gama ƙarshe zai kasance ta wurin takobi da yunwa, kuma gawarwakinsu zasu zama abincin tsuntsayen sararin sama da nanamomin ƙasar.'

5Gama maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa, 'Kada ka shiga gidan da ake makoki. Kada kayi makoki ko ka nuna damuwa dominsu, gama na ɗauke salamata daga waɗannan mutanen, da ƙaunata da jinƙaina - wannan furcin Yahweh ne.6Babba da yaro zasu mutu a wannan ƙasa. Baza a bizne su ba kuma ba wanda zai yi makoki domin su ko su tsattsage jikinsu ko su aske kansu ƙwal domin su.
7Tilas kada wani ya raba abinci a cikin makoki don ya ta'azantar da su saboda matattu, tilas kuma kada wani ya bada ƙoƙon ta'aziya ga mahaifinsa ko mahaifiyarsa don ya ta'azantar da su.8Tilas kada kuma ka shiga gidan da ake biki ka zauna don ka ci ka sha tare da su.'9Gama Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan, 'Duba, a gaban idanunka, da zamaninka a kuma wannan wuri, na kusa kawo ƙarshen muryar murna da muryar farinciki, data ango data amarya.'
10Zai kasance idan ka bayyana dukkan waɗannan maganganu ga waɗannan mutane, zasu kuwa ce maka, 'Me yasa Yahweh ya furta dukkan wannan babbar masifa a kanmu? Mene ne laifinmu da zunubin da muka yi wa Yahweh Allahnmu?'11Sai kace da su, 'Domin kakanninku sun rabu da ni - wannan furcin Yahweh ne - sun bi wasu alloli har sun bauta masu sun kuma sunkuya sun yi masu sujada. Sun rabu da ni, kuma basu kiyayye dokokina ba.
12Gama ku kuma kun kawo mugunta fiye da ta kakanninku, ku gani, kowannenku yana tafiyar taurinkai da mugun nufi a zuciyarsa; ba wanda yake saurare na.13Saboda haka zan jefar da ku daga wannan ƙasa zuwa wata ƙasa wadda ku ko kakanninku baku sani ba, a can zaku bauta wa wasu alloli dare da rana, gama ba zan nuna maku wani tagomashi ba.'
14Saboda haka, duba, kwanaki suna zuwa - wannan furcin Yahweh ne - da baza a ƙara cewa, 'Na rantse da ran Yahweh, wanda ya fito da mutanen Isra'ila daga ƙasar Masar ba.'15amma, 'Na rantse da ran Yahweh, wanda ya fito da mutanen Isra'ila daga ƙasar arewa kuma daga ƙasashen da ya warwatsa su.' Gama zan komo da su zuwa ƙasar da na ba kakanninsu.
16Duba!! Zan aika domin masunta da yawa - wannan furcin Yahweh ne - zasu kuwa kama mutane su fitar waje. Bayan wannan zan aika domin mafarauta da yawa don su farauto su daga dukkan tsaunuka da tuddai, da cikin kogunan dutse.17Gama idona yana dukkan hanyoyinsu; ba a ɓoye suke ba a gare ni. Muguntarsu kuma ba a ɓoye take ba daga idanuwana.18Zan fara saka masu ruɓi biyu domin laifinsu da zunubi domin sun ƙazantar da ƙasata da ƙazantattun siffofin gunkinsu, kuma domin sun cika gãdona da gumakansu na banƙyama."
19Yahweh, kai ne kagarata da mafakata, wurin tsarona a ranar wahala. Al'ummai zasu zo gunka daga ƙurewar duniya za a kuma ce, "Babu shakka kakanninmu sun gãji yaudara. Su fanko ne; babu riba a cikinsu.20Mutane zasu iya yiwa kansu alloli?' amma su ba alloli ba ne."21Saboda haka duba!! Zansa su sani a wannan lokacin, zansa su san hannuna da ikona, don haka zasu sani cewa sunana Yahweh ne.

17

1"Zunubin Yahuda a rubuce yake da alƙalamin ƙarfe mai bakin lu'u-lu'u. An zana shi a allon zuciyarsu da ƙahon bagadinku.2Har 'ya'yansu masu na tunawa da bagadansu da sandunan Ashtarot ɗinsu a gindin itatuwa shimfiɗe akan kuma tuddai masu tsayi.

3Dutsena a buɗaɗɗiyar ƙasar, dukiyarku da dukkan wadatarku zan bada su ganima, tare da wuraren tsaunukanku, saboda zunubin da kuka aikata a dukkan ƙasashen.4Zaku rasa gãdon da na baku. Zansa ku bautawa abokan gãbarku a ƙasar da baku sani ba, gama kun kunna wuta cikin fushina, wadda zata yi ta ci har abada."
5Yahweh yace, "Mutumin dake dogara ga ɗan adam la'ananne ne; wanda ya maida jiki ƙarfinsa wanda ya juya zuciyarsa daga Yahweh.6Gama zai zama kamar ƙaramin jeji a Hamada ba kuma zai ga wani abu mai kyau yana zuwa ba. Zai zauna a wurare masu duwatsu a cikin daji, ƙeƙasarshiyar ƙasar da ba mazauna.
7Amma mai albarka ne mutumin da yake dogara ga Yahweh, gama Yahweh ne dalilin madogararsa.8Domin yana kamar itacen da aka dasa gefen rafi, wanda saiwoyinsa suka bazu zuwa cikin rafin. Ba zai ji tsoron zafi ba a duk lokacin da yazo, domin kullum ganyensa kore ne. Ba zai da mu da shekarar fari ba, ba kuma zai fasa yin 'ya'ya ba.
9Zuciya ta fi kome rikici. Cuta gare ta matuka; wa zai iya gane ta?10Ni ne Yahweh, wanda yake binciken tunani, wanda yake gwada zukata. Ina ba kowane mutum gwargwadon al'amuransa, da kuma gwargwadon ayyukansa.11Makwarwar da ta ƙwanta kan ƙwan da ba ita ta saka ba. Mutum zai iya zama mai arzaƙi ta rashin gaskiya, amma lokacin da yayi rabin shekarunsa sun yi, wannan arzaƙin zai bar shi, a ƙarshe zai zama wawa."
12"Wurin haikalinmu kursiyi ne mai daraja, an ɗaukaka shi tun daga farko.13Yahweh shi ne begen Isra'ila. Dukkan waɗanda suka rabu da kai zasu ji kunya. Waɗanda suke cikin ƙasar waɗanda suka juya daga gare ka za a rubuta su akan ƙura. Domin sun rabu da Yahweh, maɓuɓɓugar ruwan rai.14Warkar da ni, Yahweh, zan kuwa warke! Ka cece ni, zan kuwa cetu. Gama kai ne waƙar yabona.
15Duba!, suna ce mani, 'Ina maganar Yahweh take? Tazo mana!'16Amma ni, ban gudu daga zama makiyayi da yake binka ba. Ban kuma so zuwan ranar bala'i ba. Ka kuwa san abin da ya fito daga leɓunana. An yi su a gabanka.
17Kada ka zamar mani abin ban razana. Kai ne mafakata a ranar masifa.18Bari waɗanda suke runtumata su kunyata, amma kada ka barni in kunyata. Bari su karaya, amma kada ka bar ni in karaya. Ka aika masu da ranar masifa gãba da suka kuma rugurkujesu da hallaka riɓi biyu."
19Yahweh ya faɗa mani wannan: "Ka tafi ka tsaya a ƙofar jama'a wadda sarakunan Yahuda suke shiga da fita ta cikinta, ka kuma tafi dukkan ƙofofin Yerusalem.20Ka ce da su, 'Ku ji maganar Yahweh, ku sarakunan Yahuda da dukkan ku mutanen Yahuda, da kowanne mazaunin Yerusalem waɗanda ke shiga ta waɗannan ƙofofi.
21Yahweh ya faɗi wannan: "Kuyi hankali saboda rayukanku kada ku kuma ɗauki kaya a ranar Asabar ku kawo su ta ƙofofin Yerusalem.22Kada ku kawo kaya daga gidajen ku a ranar Asabar. Kada ku yi kowanne irin aiki, sai dai ku kiyaye ranar Asabar da tsarki, kamar yadda na umarce kakanninku su yi.'"23Basu saurara ba ko su mai da hankali, amma suka taurare wuyansu don kada su ji ni ko su karɓi horaswa.
24Zai kasance idan dai kun saurare ni - wannan furcin Yahweh ne - kada ku kawo kaya ta ƙofofin wannan birni a ranar Asabar amma maimako ku tsarkake ranar Asabar ta Yahweh kada kuma ku yi kowanne irin aiki a cikinta,25sa'an nan ne sarakuna, da 'ya'yan sarakuna, da waɗanda ke zaune akan kursiyin Dauda za su shiga ta ƙofofin wannan birni su na hawan karusai da dawakai, su da shugabaninsu, da mutanen Yahuda da mazauna Yerusalem, wannan birni kuma za a zauna cikinsa har abada.
26Zasu zo daga biranen Yahuda daga kuma dukkan kewayen Yerusalem, daga ƙasar Benyamin da ta kwarurruka, daga duwatsu, da ta Negeb, suna kawo baye-bayen na ƙonawa da hadayu, baye-bayen hatsi da na turare, baye-bayen godiya ga gidan Yahweh.27Amma idan baku saurare ni ba - ku kiyaye ranar Asabar ba kuma ku ka ɗauki kaya masu nauyi kuka shiga ta ƙofofin Yerusalem a ranar Asabar ba - sai in cinna wa ƙofofin wuta, zata kuwa cinye tsararrun wurare na Yerusalem, ba kuwa zata kasu ba."

18

1Maganar da ta zo ga Irmiya daga Yahweh, cewa,2"Tashi ka tafi gidan maginin tukwane, domin a can zaka ji maganata.3Sai na gangara zuwa gidan maginin tukwanen, duba yana aikin tukwane akan na'urar ginin tukwanen.4Amma abin da yake mulmulawa da yunɓu ya lalace a hannunsa, sai ya canja tunaninsa ya sake wani abu dabam wanda yake gani yana da kyau a idanunsa.

5Sa'annan maganar Yahweh tazo gare ni, cewa,6"Ba zan iya yin haka da ku ba kamar wannan maginin tukwanen, gidan Isra'ila? -wannan furcin Yahweh ne. Duba! Kamar yadda yumɓu yake a hannun maginin tukwane - haka nan kuke a hannuna, gidan Israi'la.7A lokaci ɗaya, zan iya yin shela wani abu akan al'umma ko mulki, cewa zan kora ta, in kakkaryata, ko hallaka ta.8Amma idan al'umma wadda na yi magana a kanta ta juyo daga muguntarta, sai in janye masifar da nayi niyyar kawo mata.
9A wani lokaci, zan iya yin shelar wani abu akan wata al'umma ko mulki, cewa zan gina ko in kafa ta.10Amma idan ta aikata mugunta a idanuna ta wurin rashin sauraron muryata, daga nan zan janye abu mai kyau da na ce zan yi domin su.
11To yanzu, yi magana da jama'ar Yahuda da mazaunan Yerusalem ka ce, 'Yahweh ya faɗi wannan: Duba, ina gab da shirya masifa gãba da ku. Ina gab da tsara wata dabara gãba da ku. Ku tuba, kowanne mutum daga muguwar hanyarsa, da haka hanyoyinku da ayyukanku zasu kawo maku alheri.12Amma zasu ce, 'Wannan bashi da amfani. Zamu yi kamar yadda muka tsara. Kowanne ɗayan mu zai yi bisa ga muguntarsa, da tattaurar zuciyarsa take marmari.'
13Saboda haka Yahweh ya faɗi wannan, 'Tambayi al'ummai, wane ne ya taɓa jin irin wannan? Budurwa Isra'ila ta yi mugun abu ƙwarai.14Dusar ƙanƙara Lebanon ta taɓa rabuwa da tsaunuka a gefenta? Ko rafuffukan duwatsu masu gangarowa daga nesa sun taɓa lalacewa, waɗannan rafuffuka masu sanyi?
15Duk da haka mutanena sun manta da ni. Suna baye-baye ga gumaka marasa amfani waɗanda aka sasu tuntuɓe a cikin tafarkunsu; sun bar tsofaffin tafarku don suyi tafiya a tafarku masu sauƙi.16‌Ƙasarsu zata zama abar banƙyama, ta zama abin tsaki har abada. Duk wanda ya wuce ta wurin zai razana ya kuma kaɗa kansa.17Zan warwatsa su gaban maƙiyansu kamar iskar gabas. Zan nuna masu bayana, amma ba fuskata ba, a ranar masifarsu.'"
18Sai mutanen suka ce, "Kuzo, mu shirya maƙarƙashiya akan Irmiya, tun da yake shari'a bata lalace daga wurin firist ba, ko shawara daga mutane masu hikima ba, ko maganganu daga annabawa ba. Kuzo, mu kai ƙararsa ta wurin maganarmu kada mu yarda ko mu kula da duk wani abin da zai faɗa."19Ka saurare ni, Yahweh, ka saurari murya abokan gãbata.20Lallai ne masifa daga gare su ta zama ladana don yin abin kirki gare su? Duk da haka sun gina rami domina. Ka tuna yadda na tsaya a gabanka na yi magana akan lafiyarsu, da zai sa a janye fushinka daga gare su.
21Saboda haka ka miƙa 'ya'yansu ga yunwa, ka kuma bashe su a hannun masu amfani da takobi. Bari matansu su zama masu makoki da gwauraye, mazajensu a kashe su, samarinsu a kashe su da takobi a yaƙi.22Bari a ji kururuwa daga gidajensu, don maharan da ka aika masu farat ɗaya. Gama sun haƙa rami don su kama ni sun kuma kafa wa ƙafafuna tarkuna.23Amma kai, Yahweh, ka san dukkan maƙarshiyarsu a kaina don su kashe ni. Kada ka gafarta masu muguntarsu da zunubansu. Kada kuma ka shafe zunubansu daga gabanka. A maimakon haka, bari a jefar da su a gabanka. Ka yi gãba dasu a lokacin fushinka.

19

1Yahweh ya faɗi wannan, "Tafi ka sayo tulun yumɓu a wurin maginin tukwane sa'ad da kana tare da dattawan mutane da kuma firistoci.2Sai ku tafi Kwarin Ben Hinnom na ƙofar Kasko, a wurin zaka yi shelar maganar da zan faɗa maka.3Ka ce, 'Ku ji maganar Yahweh, sarakunan Yahuda da mazaunan Yerusalem! Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan, "Ku gani, na kusa kawo masifa akan wannan wuri, duk kuma kunuwan kowanne da zai ji zai karkaɗa.

4Zan yi wannan domin mutanen sun rabu da ni sun ƙazantar da wannan wuri. A wannan wuri sun miƙa hadayu ga wasu alloli da basu san su ba. Kakaninsu, da sarakunan Yahuda sun cika wannan wuri da jinin marasa laifi.5Sun ginawa Ba'al bagadi don su ƙona 'ya'yansu maza a matsayin baye-bayen ƙonawa gare shi - abin da ban umarta ba, ko in furta, ban ma yi tunanin haka ba.
6Saboda haka, ku gani, rana tana zuwa - wannan furcin Yahweh ne - wadda wannan wuri baza a ƙara kiransa Tofet, Kwarin Ben Hinnom ba, domin zai zama Kwarin Yanka.7A wannan wuri zan wofinta shirin Yahuda da na Yerusalem. Zansa a kashe su da takobi a gaban abokan gãbarsu ta hannun waɗanda suke neman ransu. Sa'annan zan ba da gawawwakinsu su zama abincin tsutsayen sammai da na namomin jeji.8Zan mai da wannan birni kango da kuma abin tsaki, domin duk wanda ya wuce wurin zai yi mamaki da tsaki, akan dukkan annobar.9Zansa su ci naman 'ya'yansu maza da mata; kowanne mutum zai ci naman maƙwbcinsa cikin damuwa da azaba akan abin da ya faru da su daga wurin abokan gãbarsu da waɗanda suke neman ransu.'"
10Sa'annan sai ka fasa tulun yumɓun a gaban mutanen da suka tafi tare da kai.11Ka kuwa ce masu, 'Yahweh mai runduna yace wannan: Haka zan yi wannan abu ga waɗannan mutane na wannan birni - wannan furcin Yahweh ne - kamar yadda Irmiya ya fashe tulun yumɓun yadda ba wanda zai iya gyara shi kuma. Mutane zasu bizne matattu a Tofet har sai an rasa wurin da ya rage da za a sake bizne matattu kuma.
12Wannan shi ne abin da zan yi da wannan wuri da mazaunansa idan na maida wannan birni kamar Tofe -wannan furcin Yahweh ne -13saboda haka gidajen Yerusalem da na sarakunan Yahuda zasu zama kamar Tofet - dukkan gidajen waɗanda akan rufinsu ne ƙazaman mutane suke sujada ga dukkan taurarin sararin sama da suke zuba abin sha na baye baye ga wasu alloli.'"
14Sai Irmiya ya komo daga Tofet, inda Yahweh ya aike shi don yayi annabci. Ya tsaya a filin gidan Yahweh, yace da dukkan mutane.15"Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, y faɗi wannan, 'Ku gani, na kusa auka wa wannan birni da dukkan garuruwansa da dukkan masifu da na ambata gãba da shi, tun da sun taurare wuyansu sun kuma ƙi jin maganganuna.'"

20

1Fashur ɗan Immer firist - shi babban jami'i ne - ya ji Irmiya yana annabcin waɗannan maganganu a gaban gidan Yahweh.2Saboda haka Fashur ya bugi annabi Irmiya sa'annan ya sa shi cikin turu wanda ke ƙofar bisa ta Benyamin a gidan Yahweh.

3Ya zamana kashegari sa'adda Fashhur ya fitar da Irmiya daga turun. Sai Irmiya yace da shi, "Yahweh bai kira sunanka Fashhur ba, amma ya baka suna Magor Missabib.4Domin Yahweh ya faɗi wannan, 'Duba, zan maishe ka abin tsoro, kai da dukkan waɗanda kake ƙauna, amma zasu mutu da takobi ta wurin abokan gãbarsu idanunka kuma zasu gani. Zan kuma bada dukkan jama'ar Yahuda a hannun sarkin Babila. Shi kuwa zai maida dasu bayi a Babila ko kuwa ya kai masu hari da takobi.
5Zan ba shi dukkan dukiyar wannan birni da kuma dukkan arzikinta da dukkan abubuwa masu tamani da dukkan dukiyar sarakunan Yahuda. Zan miƙa waɗannan abubuwa a hannun abokan gãbarsu zasu kuma washe su. Zasu ɗauke su su kuma kai su Babila.6Amma kai, Fashhur, da dukkan mazauna gidanka zasu tafi bauta. Kai zaka tafi Babila a can zaka mutu. Kai da dukkan waɗanda kake ƙauna kuma kayi masu annabcin ƙaryar waɗannan abubuwa a wurin za a bizne ka.'"
7Yahweh, ka ruɗe ni, na kuwa ruɗu. Ka fi ni ƙarfi, ka kuma rinjaye ni. Na zama abin dariya dukkan yini, kowa yana ta yi mani ba'a.8Amma duk lokacin da zan yi magana, na kan kira da murya in yi magana da ƙarfi, 'Hargitsi da hallakarwa.' Sai maganar Yahweh ta zama abin zargi da abin ba'a a dukkan yini.9Idan na ce, 'Ba zan ƙara yin tunani akan Yahweh ba. Ba kuwa zan ƙara yin magana da sunansa ba.' Sai in ji kamar wuta a cikin zuciyata, an sa ta a cikin ƙasusuwana. Sai in yi ƙoƙarin danne ta amma ba zan iya jurewa ba.
10Na kan ji jita-jita ta banrazana daga wurin mutane da yawa a dukkan kewaye. 'Dole mu bada rahoto!' Waɗanda ke kusa da ni su dubawa su gani ko zan faɗi. 'Watakila za a ruɗe shi. Idan haka ne, sa'annan ma iya rinjayarsa har mu ɗauki fansarmu a kansa.'11Amma Yahweh yana tare da ni kamar jarumi mai iko, don haka masu runtumata zasu yi tangaɗi. Baza su ci nasara da ni ba. Zasu ji kunya ƙwarai domin ba zasu yi nasara ba. Ba zasu daina jin kunya ba, kuma ba za a manta ba.
12Amma kai, Yahweh mai runduna, mai gwada adali wanda yake ganin zuciya da tunani. Bari in ga sakayyar da zaka yi masu tun da na kawo ƙarata a gare ka.13Raira waƙa ga Yahweh! A yabi Yahweh! Gama ya kuɓutar da rayukan waɗanda ake zalunta daga hannun mugaye.
14Bari ranar da aka haife ni ta zama la'ananniya. Kada ka bar ranar da uwata ta haife ni ta yi albarka.15Bari mutumin da ya kai wa mahaifina labari ya zama la'annane, wanda yace, An haifa maka ɗa namiji,' don yasa ka farin ciki.
16Bari wannan mutum ya zama kamar biranen da Yahweh ya kaɓantar ba tare da ya ji tausayinsu ba. Bari ya ji kuka don neman taimako da wayewar gari, da rana kuma ya ji gangamin yaƙi,17domin bai kashe ni tun ina ciki ba, ya sa uwata ta zama kabarina, cikin mahaifar da zata dawwama har abada.18Me yasa na fito daga cikin mahaifa in ga damuwa da azaba, don kwanakina su cika da kunya?"

21

1Wannan ita ce maganar da ta zo wa Irmiya daga Yahweh lokacin da sarki Zadakiya ya aiki Fashhur ɗan Malkiya da Zafaniya ɗan Ma'aseya firist gare shi. Suka ce da shi,2"Nemi shawara daga Yahweh a madaddin mu, don Nebukadnezza sarkin Babila yana kawo ma na yaƙi. Me yiwuwa Yahweh zai yi abin ban al'ajabi domin mu, kamar yadda ya saba a lokatan baya, wanda ya sa shi ya janye daga wurin mu."

3Sai Irmiya ya ce da su, "Wannan shi ne abin da dole za ku ce da Zadakiya,4Yahweh, Allah na Israila, ya faɗi wannan: Duba, zan juya baya ga kayan yaƙin da su ke hannunka, waɗanda ka ke yaƙi da su gãba da sarkin Babila da Kaldiyawa waɗanda suke kusa da ku daga wajen garun! Gama zan tara su a cikin tsakiyar wannan birnin.5Ni kaina zan yi faɗa da kai da duk ƙarfina, da kuma hasalata da zafin fushina.
6Gama zan faɗawa mazaunan wannan birnin, mutum da dabba. Za su mutu da babbar annoba.7Bayan wannan - wannan shi ne furcin Yahweh - Zadakiya sarkin Yahuda, da bayinsa da mutanen, da duk wanda ya rage a cikin wannan birni bayan annoba, da takobi da kuma yunwa, zan bashe su dukka a hannun Nebukadnezza sakin Babila, da kuma hannun abokan gãbarsu, da hannun waɗanda suke neman rayukansu. Daga nan shi kuma zai kashe su da kaifin takobi. Ba zai ji tausayinsu ba, ko ya rage su, ko kuma ya yi juyayinsu ba.'
8Game da waɗannan mutane dole ka ce, 'Yahweh ya faɗi wannan: Duba ina kusa da sa hanyar rai da hanyar mutuwa a gabanku.9Shi wanda ya zauna a wannan birnin zai mutu da takobi, da yunwa da kuma annoba; amma shi wanda ya fita zai ba da kansa ga Kaldiyawa waɗanda suka kewaye ku gãba da ku zai rayu. Zai tserar da ransa.10Gama na ƙudura zan yi gãba da wannan birni in kuma kawo masa masifa ba alheri ba - wannan furcin Yahweh ne. An ba da shi a hannun sarkin Babila, shi kuwa zai ƙone shi da wuta.'
11A game da gidan sarkin Yahuda kuwa, ku ji maganar Yahweh.12Ya gidan Dauda, Yahweh ya ce, 'Ku aikata adalci kowace safiya. Ku ceci wanda aka yi masa ƙwace daga hannun mai tsananta masa, ko kuma hasalata ta fita kamar wuta ta yi ƙuna, harma ba mai iya kashe ta, saboda mugayen ayyukanku.
13Duba, mazaunan kwari! Ina gãba da ku, dutsen da ya ke a fili - wannan furcin Yahweh ne - ina gãba da wanda yake cewa, "Wane ne zai iya saukowa ƙasa don ya yi gãba da mu?" Ko kuwa "Wane ne zai iya shiga gidajenmu?"14Na sa sakamakon ayyukanku su yi gãba da ku - wannan furcin Yahweh ne - kuma zan kunna wuta a cikin kurmin, za ta cinye duk abin da ya ke kewaye da ita.'"

22

1Wannan shi ne abin da Yahweh ya ce, "Ka gangara zuwa gidan sarkin Yahuda ka faɗa ma sa wannan magana a can.2Ka ce, 'Sarkin Yahuda, ka saurari maganar Yahweh - kai da ke zaune akan gadon sarautar Dauda - da kai, da barorinka, da mutanenka da ke shigowa ta waɗannan ƙofofi.3Yahweh ya faɗi wannan, "Ku aikata gaskiya da adalci, kuma duk wanda aka yi masa ƙwace - ku cece shi daga hannun masu zalumtarsa. Kada ku wulaƙanta wani baƙon da ke ƙasarku, ko maraya ko kuwa gwauruwa. Kada a yi ta'addanci ko a zubar da jinin marar laifi a wannan wurin.

4Domin idan hakika ku ka yi waɗannan abubuwa, sarakunan da ke zaune kan kursiyin Dauda za su shiga cikin ƙofofin gidan nan haye cikin karusa da dawakai, shi, da barorinsa, da jama'arsa!5Amma idan ba ku kasa kunne ga waɗannan zantattuka waɗanda na yi shelar su ba - wannan furcin Yahweh ne - to wannan masarauta za ta zama kufai.'"
6Gama Yahweh ya faɗi wannan game da gidan sarkin Yahuda, 'Kai kamar Giliyad ka ke, kamar ƙolƙolin Lebanon ka ke a gare ni. Duk da haka zan maisheka jeji, da kuma birane da ba mazauna.7Gama zan ƙaddara masu lalatarwa su tashi gãba da ku! Mutane da makamansu za su daddatse itatuwan sidarku mafi kyau su kuma zuba su a wuta.
8Sa'annan al'ummai da yawa za su shige ta wannan birni. Kowanne mutum zai ce wa na kusa da shi, "Me ya sa Yahweh ya yi haka game da wannan babban birni?"9Sa'annan ɗayan zai amsa, "Saboda sun yi watsi da alƙawarin Yahweh Allahnsu suka russuna wa waɗansu alloli suka yi masu sujada."
10Kada ku yi kuka domin wanda ya mutu ko ku yi makoki dominsa; amma ku yi kuka mai zafi sabili da wanda ya kusa tafiya, domin ba zai ƙara dawowa ya ga ƙasar asalinsa ba.'
11Domin Yahweh ya faɗi haka game da Yehoahaz ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wanda ya gaji sarauta a madadin ubansa Yosiya, 'Ya tafi daga nan wurin ba zai sake komowa ba.12Zai mutu a can inda suka kai shi zaman talala, kuma ba zai ƙara ganin wannan ƙasa ba.'
13Kaiton wanda ya gina gidansa ta hanyar rashin adalci, benayensa kuma ta hanyar rashin gaskiya, ya sa makwabcinsa ya yi masa aiki a banza, bai kuma bashi al'bashinsa ba;14yana cewa, 'Zan gina wa kaina babban gida mai manyan ɗakuna a sama.' Sai ya sa masu manyan tagogi, ya kuma rufe su da itacen sida, ya kuma yi masu jan shafe.
15Wannan ne zai maishe ka sarki mai adalci, da ka ke son ka sami katakan sida? Ko mahaifinka bai ci ya sha ba, duk da haka ya yi gaskiya da adalci? Sai komai ya tafi dai - dai da shi.16Ya shari'anta da alheri ga matalauta da fakirai. Ya yi kyau a lokacin nan. Wannan ba shi ne ma'anar sanina ba? - wannan ne furcin Yahweh.
17Amma ba kome a zuciyarka da idanunka sai dai damuwa domin muguwar ribarka da kuma domin zubar da jinin marasa laifi, da aikata danniya da murƙushe waɗansu.18Sabili da wannan Yahweh ya faɗi haka game da Yehoiyakim ɗan Yosiya, sarkin Yahuda: Ba za su yi makoki domin sa ba, suna cewa, 'Kaito, ɗan'uwana!' ko, 'Kaito, 'yar'uwata!' Ba za su yi makoki dominsa ba, suna cewa, 'Kaito, ubangida!' ko, 'Kaito, mai martaba!'19Za a binne shi kamar yadda ake binne jaki, a janye shi a jefar nesa da ƙofofin Yerusalem.
20Ku haura kan duwatsun Lebanon ku yi ihu. Ku tada muryarku a Bashan. Ku yi ihu daga duwatsun Abarim, gama duk abokanku za a hallaka su.21Na yi maku magana sa'ad da ku ke zaune lafiya, amma kun ce, 'Ba za mu kasa kunne ba.' Al'adarku ce wannan tun kuna samari, gama ba ku saurari muryata ba.
22Iska za ta kora dukkan makiyayanku, abokanku kuma za su tafi bautar talala. Sa'annan lallai za ku kunyata ku ƙasƙantu ta wurin miyagun ayyukanku. Ku da kuke zaune cikin 'Lebanon,'23ku da ku ke shaƙatawa cikin ginin itatuwan sida, za ku zama abin tausayi sa'ad da azabar naƙuda ta afko maku, azaba kamar ta mace mai naƙudar haifuwa!"
24"Na rantse da zatina - wannan furcin Yahweh ne - ko da kai, Yehoiyacin ɗan Yehoiyakim, sarkin Yahuda, zoben hannun damana ne, zan cire ka.25Gama na bashe ka a hannun masu neman ranka da kuma hannun waɗanda ka ke jin tsoro a gabansu, wato hannun Nebukaneza sarkin Babila da Kaldiyawa.26Zan jefar da kai da mahaifiyarka wadda ta haife ka cikin wata ƙasa, ƙasar da ba nan aka haife ka ba, kuma can za ka mutu.
27Game da ƙasar nan da suke so su koma, ba za su dawo nan ba.28Wannan ita ce tukunyar da aka rena aka kuma farfasa? Wannan shi ne mutumin nan Yehoiyacin tukunyar da ba ta gamshi kowa ba? Me ya sa suka jefar da shi waje da shi da zuriyarsa, kuma suka zubar da su cikin ƙasar da ba su santa ba?
29Ƙasa, Ƙasa, ƙasa! Ki ji maganar Yahweh!30Yahweh ya faɗi wannan, "Rubuta akan mutumin nan Yehoiyacin: Ba zai haifu ba. Ba zai yi albarka ba a kwanakinsa, ba kuma wani a zuriyarsa da zai ci nasara ko kuma ya ƙara zama a kursiyin Dauda ya yi mulki bisa Yahuda ba."

23

1"Kaiton makiyayan da ke lalatarwa suke kuma warwatsar da tumakin makiyayata - wannan furcin Yahweh ne."2Saboda haka Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan game da makiyayan da ke kiwon mutanensa, "Kun warwatsar da garkena kun kore su nesa. Ba ku lura da su ba. Sabili da haka na kusa in hukunta ku saboda muguntar da ku ka aikata - wannan ne furcin Yahweh.

3Ni da kaina zan tattara ragowar garkena daga dukkan ƙasashen da na kora su, zan kuma dawo da su wurin kiwo, inda za su hayayyafa su kuma ƙaru.4Sa'anna zan tanada makiyaya bisansu waɗanda za su yi kiwon su domin kada su ƙara tsorata ko su zama karyayyu. Ba za a rasa ko ɗayansu ba - wannan furcin Yahweh ne.
5Duba, kwanaki suna zuwa - wannan ne furcin Yahweh - da zan tada wa Dauda reshe mai adalci. Shi zai yi mulki kamar sarki; zai yi aiki da hikima ya sa gaskiya da adalci su kasance a ƙasar.6A kwanakinsa Yahuda zai tsira, Isra'ila zai zauna lafiya. Ga sunan da za a kira shi da shi: Yahweh shi ne adalcinmu.
7Saboda haka duba, kwanaki suna zuwa - wannan ne furcin Yahweh - da ba za su ƙara cewa, "Na rantse da ran Yahweh wanda ya fito da mutanen Isra'ila daga ƙasar Masar ba.'8Maimakon haka za su ce, 'Na rantse da ran Yahweh, wanda ya fitar ya kuma dawo da zuriyar gidan Isra'ila daga ƙasar arewa da dukkan ƙasar da aka kora su.' Sa'annan za su zauna a ƙasar da ke tasu."
9A game da annabawan, zuciyata ta karai, dukkan ƙasusuwana su na kaɗuwa, na zama kamar bugaggen mutum, kamar mutumin da ruwan inabi ya rinjaye shi, saboda Yahweh da kuma zantattukansa masu tsarki.10Domin ƙasar ta cika da mazinata. Sabili da waɗannan ne ƙasar ta bushe. Wuraren kiwo a jeji sun ƙeƙashe. Tafarkun annabawan nan mugaye ne; ba su mori ikonsu yadda ya kamata ba.
11Gama da annabawan da firstocin dukka biyu sun ƙazamtu. Har ma na ga muguntarsu a cikin gidana! - wannan ne furcin Yahweh -12Sabili da haka tafarkinsu zai zama kamar wuri mai santsi cikin duhu. Za a ture su ƙasa. Za su faɗa a cikinta. Gama zan aiko da masifa găba da su a shekarar da zan hukunta su - wannan ne furcin Yahweh.
13Gama na ga annabawan da ke cikin Samariya su na yin abin kyama: sun yi annabci da Ba'al sun karkatar da jama'ata Isra'ila.14A cikin annabawan da ke Yeruselem na ga mugayen abubuwa: Su na yin zina su na aikata ƙarya. Su na ƙarfafa hannun miyagu; ba wanda yake juyowa daga muguntarsa. Dukkan su sun zama kamar Soduma a gareni, mazamnan su kuma kamar Gwamarata!"15Saboda haka Ubangiji mai runduna ya faɗi wannan game da annabawan, "Duba, na kusa in sa su su ci abu mai ɗaci su sha ruwa mai dafi, gama ƙazamta ta bazu daga annabawa da ke cikin Yeruselem har zuwa dukkan ƙasar."
16Ubangiji mai runduna ya ce, "Kada ku saurari maganganun annabawan da ke yi maku annabci. Sun zurma ku! Suna sanar da wahayi daga nasu tunani, ba daga bakin Yahweh ba.17Kullum su na faɗa wa waɗanda su ka rena ni, 'Yahweh ya ce akwai salama dominku,' Gama kowanne mai tafiya a cikin tattaurar zuciyarsa ya kan ce, 'Masifa ba za ta auko kanmu ba.'18Duk da haka wa ya tsaya a majalisar Yahweh? Wa ya gani ya kuma ji maganarsa? Wa ya natsu ya kasa kunne ya saurari maganarsa?
19Duba, akwai hadarin da ke dannowa daga Yahweh! Hasalar sa na fita, guguwa kuma na juyawa ko'ina. Tana zagayawa kewaye da kan mugaye.20Fushin Yahweh ba zai huce ba sai ya gama aiwatawa da cika nufin zuciyarsa. A ƙarshen kwanaki, za ku gane shi.
21Ban aiki waɗannan annabawan ba. Haka kawai su ka bayyana. Ban shaida masu kome ba, amma duk da haka su ka yi annabci.22Inda sun kasance a majalisar shawarata, da sun sa jama'ata su ji maganata; da sun sa su su juyo daga mugayen maganganunsu da kuma mugayen ayyukansu.
23Ni Allah ne na kusa kaɗai - wannan ne furcin Yahweh - ba kuma Allah na nesa ba?24Akwai wani da zai iya ɓoye wa a wurin da ba zan ganshi ba? - wannan ne furcin Yahweh - ko ni ban cika sammai da ƙasa ba? - wannan ne furcin Yahweh.
25Na ji abin da annabawan su ka faɗi, waɗanda suke annabcin ƙarya cikin sunana. Sukan ce, 'Na yi mafarki! 'Na yi mafarki!26Har yaushe za a ci gaba da haka, annabawa masu annabcin ƙarya daga tunaninsu, da kuma annabci daga ruɗun da ke cikin zuciyarsu?27Su na shirin sa mutanena su manta da sunana ta wurin mafarkan da su ka sanar, kowanne ga maƙwabcinsa, kamar dai yadda kakaninsu su ka manta da sunana su ka so sunan Ba'al.
28Annabin da ya ke da mafarki, bari ya sanar da mafarkin. Amma ga wanda na sanar da shi wani abu, bari ya sanar da maganata da gaskiya. Me ya haɗa ciyawa da al'kama? - wannan ne furcin Yahweh - Maganata ba kamar wuta ta ke ba? - wannan ne furcin Yahweh -29kuma kamar guduma mai farfasa duwatsu gutsu - gutsu?30To ku duba, ina găba da annabawan - wannan ne furcin Yahweh - da kowanne ɗayan da ya saci magana daga wani mutum ya kuma ce maganar ta zo daga gareni.
31Duba, ina găba da annabawan - wannan ne furcin Yahweh - masu amfani da harshensu su yi shelar annabci.32Duba, ina găba da annabawa da ke mafarkan ƙarya - wannan ne furcin Yahweh - sa'annan su yi shela da haka su ke ɓad da mutanena da ƙarairayinsu da kuma fariya. Ina găba da su, gama ban aike su ba ko in ba su umarni. Saboda haka lallai, ba za su taimaki mutanen nan ba - wannan ne furcin Yahweh.
33Lokacin da waɗannan mutane, ko annabi, ko firist ya tambayeku, 'mene ne nawaiyar Yahweh?' za ka ce masu, 'Ku ne nawaiyar, kuma zan jefar da ku - wannan ne furcin Yahweh.34Game da annabawan, da firistoci, da kuma mutanen da ke cewa, 'Wannan shi ne nawaiyar Yahweh' zan hukunta wannan mutum da gidansa.
35Kuna ci gaba da cewa, kowanne mutum ga makwabcinsa da kuma kowanne mutum ga ɗan'uwansa, 'Me Yahweh ya amsa?' kuma 'Me Yahweh ya furta?36Amma ka da ku ƙara yin magana akan 'nawayar Yahweh,' gama nawaiyar ita ce maganar kowanne mutum, kuma kun karkatar da maganganun Allah mai rai, Ubangiji mai runduna, Allahnmu.
37Ga abin da za ku ce wa annabi, 'Wace amsa ce Yahweh ya ba ku? ko kuma, 'Me Yahweh ya ce?'38Amma idan kun ce, 'Nawaiyar Yahweh,' wannan shi ne abin da Yahweh ya ce: 'Sabili da kun faɗi wanɗannan maganganu, 'Nawaiyar Yahweh,' lokacin da na aika maku, cewa, 'Ba za ku ce, "Nawaiyar Yahweh,"' ba.39saboda haka, duba, na kusa ɗaukar ku in jefar da ku nesa da ni, tare da birnin dana ba ku da kakanninku.40Sa'annan zan sa maku madawwamiyar kunya da zargi a kanku wanda ba za a taɓa mantawa ba.'"

24

1Yahweh ya nuna mani wani abu. Duba, ga kwanduna biyu na 'ya'yan baure a gaban haikalin Yahweh. (Wannan wahayi ya faru bayan da Nebukadnezza, sarkin Babila, ya kai waɗannan mutane bautar talala: Yehoyacin ɗan Yehoyakim, sarkin Yahuda, da shugabannin Yahuda, da masassaƙa, da masu ƙira da kwasao daga Yerusalem ya kawo su Babila.)2Ɗaya kwandon ɓauren na da ƙyau sosai, kamar nunar fari na ɓaure, amma ɗaya kwandon ɓauren ba shi da kyau ko kaɗan har ma ba za a iya cin su ba.3Yahweh ya ce mani, "Me ka gani, Irmiya?" Na ce, '"Ya'yan ɓaure. 'Ya'yan ɓaure masu kyau sosai da marasa kyau har ma ba za a iya cinsu ba."

4Sai maganar Yahweh ta zo gareni, cewa,5"Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: Zan dubi 'yan bautar talala na Yahuda da tagomashi, kamar kyawawan 'ya'yan ɓauren nan, 'yan bautar talala waɗanda na kore su daga nan zuwa ƙasar Kaldiya.6Zan kafa idanuna a kansu domin in yi masu alheri, in kuma dawo da su wannan ƙasar. Zan gina su, ba zan rushe su ba. Zan dasa su, ba zan tumbuƙe su ba.7Sa'annan zan ba su zuciyar da za su sanni, gama ni ne Yahweh. Za su zama mutanena, zan kuma zama Allahnsu, haka za su juyo gareni da dukkan zuciyarsu.
8Amma kamar 'ya'yan ɓauren nan marasa kyau har da ba za a iya cinsu ba-ga abin da Yahweh ya ce - Zan yi haka da Zedekiya, sarkin Yahuda, da shugabanninsa, da kuma sauran da ke a Yerusalem waɗanda suka rage a cikin ƙasar nan ko kuwa su ka tafi su zauna cikin ƙasar Masar.9Zan maishe su abin tsoro, abin masifa, a idanun dukkan mulkokin duniya, abin kunya abin zargi da karin magana, da dariya, da la'ana a duk wuraren da na warwatsa su.10Zan aika da takobi, yunwa, da annoba găba da su, har sai an hallakasu daga ƙasar da na basu da kakanninsu."

25

1Wannan ita ce maganar da ta zo wurin Irmiya game da dukkan mutanen Yahuda. Ya zo ne a shekara ta huɗu ta Yehoyakim ɗan Yosiya, sarkin Yahuda. Wannan ita ce shekara ta fari ta Nebukadnezza, sarkin Babila.2Annabi Irmiya ya yi shelar wannan ga dukkan mutanen Yahuda da dukkan mazaunan Yerusalem.

3Ya ce, "Shekaru ashirin da uku, tun daga shekara ta sha uku ta Yosiya ɗan Amon, sarkin Yahuda, har zuwa yau, maganar Yahweh ta na ta zuwa gare ni, ni kuma na yi maku magana akai-akai, amma ba ku kasa kunne ba.4Yahweh ya aika maku dukkan bayinsa annabawa akai-akai, amma ba ku saurare su ba ko ku kasa kunne.
5Waɗannan annabawa sun ce, 'Bari kowanne mutum ya juyo daga hanyar muguntarsa da lalatattun ayyukansa ya dawo ƙasar da Yahweh ya bayar a zamanin dã ga kakanninku da ku kuma, a matsayin madawwamiyar kyauta.6Saboda haka kada ku bi waɗansu alloli ku yi masu sujada ko ku russuna masu, kuma kada ku cakune shi da ayyukan hannuwanku domin kada ya azabtar da ku.'
7Amma ba ku saurare ni ba - wannan ne furcin Yahweh - haka ku ka cakune ni da aikin hannuwanku in cutar da ku.8Domin haka Ubangiji mai ruduna ya faɗi wannan, 'Saboda ba ku saurari maganganuna ba,9duba, ina gaf da aiko da umarni domin a tara dukkan mutanen arewa - wannan ne furcin Yahweh - da Nebukadnezza bawana, sarkin Babila, zan kawo su gãba da ƙasar nan da mazaunanta, gãba kuma da dukkan al'umman da ke kewaye da ku. Gama zan keɓe su domin halakarwa. Zan mai da su abin tsoro, abin yi wa tsaki, da kuma kufai har abada.
10Zan kawo ƙarshen ƙarar murna da ƙarar farinciki, ƙarar ango da ƙarar amarya, ƙarar dutsen niƙa da hasken fitila.11Sa'annan dukkan wannan ƙasa za ta zama kufai da abin tsoro, kuma waɗannan al'ummai za su bauta wa sarkin Babila shekaru saba'in.
12Za ya zama kuwa bayan shekaru saba'in sun cika, zan hukunta sarkin Babila da al'umman nan, ƙasar Kaldiyawa - wannan ne furcin Yahweh - saboda kurakuransu in maishe ta kango marar matuƙa.13Sa'anan kuma zan yi wa ƙasar nan abin gãba bisa ga dukkan maganar da na faɗi, da kuma dukkan abin da aka rubuta a cikin wannan littafi wanda Irmiya ya yi annabci gãba da dukkan al'ummai.14Kuma wasu al'umman da yawa da manyan sarakuna za su bautar da waɗannan al'ummai. Zan sãka masu bisa ga abin da su ka aikata da kuma ayyukan hannuwansu."'
15Gama Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗa mani wannan, "Ka ƙarɓi wannan ƙoƙon ruwan inabi na hasalata daga hannuna ka sa dukkan al'umman da na aike ka gun su su sha shi.16Gama za su sha sa'anan su yi tuntuɓe ko ina su sheƙa da gudu daga takobin da nake aikowa cikinsu."
17Sai na ƙarɓi ƙoƙon daga hannun Yahweh, na kuma să dukkan al'umman da Yahweh ya aike ni su sha shi:18Yerusalem, biranen Yahuda da sarakunanta da shugabanninta-a maida su kufai da abin tsoro, da kuma abin tsaki da la'antarwa, kamar yadda suke a yau.
19Sauran al'ummai dole su sha shi: Fir'auna Sarkin Masar da barorinsa; shugabanninsa da dukkan mutanensa;20dukkan baƙin mutane ruwa biyu da dukkan sarakunan da ke ƙasar Uz; dukkan sarakunan da ke ƙasar Filistiya - Ashkelon, Gaza, Ekron, da ragowar Ashdod;21Idom da Mowab da mutanen Ammon.
22Sarakunan Taya da Sidon, sarakunan gãɓar tsallaken teku,23Dedan, Tema, da Buz da dukkan waɗanda suke aske gashin gefen kawunansu suma sai da suka sha shi.
24Waɗannan mutanen suma dole suka sha shi: dukkan sarakunan Arebiya da dukkan sarakunan mutane masu ruwa biyu da ke zaune a jeji;25dukkan sarakunan Zimri, da dukkan sarakunan Elam, da dukkan sarakunan Madayana;26dukkan sarakunan arewa, waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa - kowanne da ɗan'uwansa da dukkan masarautar da ke duniya da ke a fuskar ƙasa. A ƙarshe, sarkin Babila zai sha a bayansu.
27Yahweh ya ce mani, "Yanzu dole ka faɗa masu, 'Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: Ku sha ku bugu, sa'anan ku haras, ku faɗi ƙasa, kada ku tashi kafin in aiko da takobi a tsakanin ku.'28Idan kuwa sun ƙi su ƙarɓi ƙoƙon daga hannunka su sha, za ka ce masu, 'Yahweh mai runduna ya faɗi wannan, Dole ne lallai ku sha shi.29Ku duba, na kusa kawo masifa akan birnin da ake kira da sunana, to ku da kanku ya kamata a tsirar da ku daga horo ne? Ba za ku tsira ba, gama ina kawo takobi gãba da dukkan mazaunan ƙasar! - wannan ne furcin Yahweh mai runduna.'
30Dole ka yi annabcin dukkan waɗannan maganganu gãba da su, kuma ka ce masu, 'Yahweh zai yi ruri daga sammai zai yi ihu da muryarsa daga wurin zamansa mai tsarki, zai yi ruri da ƙarfi gãba da nasa; kuma zai yi ihu, kamar waɗanda suke matse 'ya'yan inabi gãba da dukkan mazaunan duniya.31Zizar yaƙi zata buga ta kai dukkan bangon duniya, gama Yahweh yana kawo ƙara gãba da dukkan al'ummai, zai kuma kawo hukunci kan dukkan talikai. Zai ba da mugaye ga takobi - wannan ne furcin Yahweh.'
32Ubangiji mai runduna ya faɗi wannan, 'Duba, masifa tana tasowa daga al'umma zuwa al'umma, kuma babban hadari ya danno daga manisantan wurare na duniya.33Sa'anan waɗanda Yahweh ya kashe za su zama daga wannan bangon duniyan zuwa wan can; ba kuma za a yi makokinsu ba, ko a tattarasu, ko kuma a binne su. Za su zama kamar taki a ƙasa.
34Ku yi makoki, makiyaya, ku yi ihu domin taimako! Ku yi birgima a cikin ƙura, ku iyayengijin garke, gama ranar da za a yanka ku ta zo; za a warwatsa ku sa'ad da ku ka faɗi kamar kyawawan tukwane.35Babu mafaka domin makiyaya, ba sauran mafita domin iyayengijin garke.36Ku ji koke-koken makiyaya da makokin iyayengijin garke, gama Yahweh yana lalatar da makiyayarsu.
37Haka makiyayarsu mai salama za a lalatar da ita sabili da zafin fushin Yahweh.38Kamar ɗan zaki, da ya baro maɓuyarsa, gama ƙasarsu zata zama abin ban tsoro saboda fushin mai tsanantawa, saboda kuma zafin fushinsa.'"

26

1A farkon mulkin Yehoyakim ɗan Yosiya, wannan maganar ta zo daga Yahweh cewa,2"Yahweh ya faɗi wannan: Ka tsaya a filin haikalina ka yi magana akan dukkan biranen Yahuda waɗanda suke zuwa su yi sujada a gidana. Yi shelar dukkan maganganun da na umarce ka ka faɗa masu. Kada ka rage ko wata kalma!3Mai yiwuwa su kasa kunne, har kowanne mutum ya juyo ya bar mugayen hanyoyinsa, nima in janye masifar da nake niyyar saukar masu saboda mugayen ayyukansu.

4Saboda haka dole ka ce masu, 'Yahweh ya faɗi wannan: Idan baku kasa kunne gare ni kun yi biyayya da dokokina da na sa agabanku ba -5Idan baku kasa kunne da maganar bayina annabawa waɗanda na ke aiko maku-amma ba ku ji ba! -6to zan maida gidan nan kamar Shiloh; zan maida birnin nan la'ana a idanun dukkan al'umman da ke a duniya.'"
7Da firistoci, da annabawa da dukkan jama'a sun ji annabi Irmiya yana shelar waɗannan maganganu a haikalin Yahweh.8Ananan da Irmiya ya gama shelar dukkan maganar da Yahweh ya umarce shi ya faɗa wa dukkan mutane, sai firistoci, da annabawa da dukkan mutane suka kama shi suka ce, "Zaka mutu lallai!9Me yasa ka yi annabci a cikin sunan Yahweh ka ce wannan gida zai zama kamar Shiloh kuma wannan birni zai zama kufai, har ba mazauna?" Gama dukkan mutanen sun tada tarzoma gãba da Irmiya a cikin haikalin Yahweh.
10Daganan sai shugabannin Yahuda suka ji waɗannan maganganu suka tashi daga gidan sarki su ka tafi gidan Yahweh. Su ka zauna a ƙofa a Sabuwar Ƙofa ta haikalin Yahweh.11Sai firistoci da annabawa suka yi wa shugabanni da dukkan mutane magana. Suka ce, "Dai-dai ne mutumin nan ya mutu, domin ya yi annabci gãba da birnin nan, kamar yadda kuka ji da kunnuwanku!"12Sai Irmiya ya yi magana da dukkan shugabanni da dukkan mutane yace, "Yahweh ya aiko ni in yi annabci gãba da haikalin nan da kuma birnin nan, in faɗi dukkan maganganun nan da kuka ji.
13Saboda haka yanzu fa, sai ku gyara al'amuranku da kuma ayyukanku, ku saurari muryar Yahweh Allahnku domin ya janye masifar da ya yi shela gãba da ku.14Ni da kaina-ku dube ni! - ina hannunku. Ku yi mani abin da kuka ga yayi dai-dai a idanunku.15Amma lallai ya kamata ku sani idan ku ka kashe ni, kuna jawo wa kanku al'hakin jinin marar laifi da kuma wannan birni da mazaunan da ke a cikinsa, gama lallai Yahweh ya aiko ni wurinku in yi shelar waɗannan maganganu a kunnuwanku."
16Daga nan shugabannin da dukkan mutane suka cewa firistoci da annabawa, "Ba dai-dai ba ne mutumin nan ya mutu, gama ya yi mana shelar abubuwa a cikin sunan Yahweh Allahnmu."17Sai wasu maza suka tashi daga cikin dattawan ƙasar suka yi wa dukkan taron mutanen magana.
18Suka ce, "Mika Ba-morashe ya yi annabci a zamanin Hezekiya sarkin Yahuda. Ya yi wa dukkan mutanen Yahuda magana yace, 'Yahweh mai runduna yace: Za a huɗa Sihiyona kamar gona, Yerusalem za ta zama tsibin juji, dutsen haikali zai zama dutsen da ciyayi suka sha kansa.'19To, Hezekiya sarkin Yahuda da dukkan Yahuda sun kashe shi ne? Ashe bai ji tsoron Yahweh ya nemi alheri a fuskar Yahweh domin Yahweh ya janye masifar da ya faɗa masa ba? Ko dai-dai ne muyi mugunta mafi girma gãba da rayyukanmu?"
20Ananan wani mutum kuma ya yi annabci cikin sunan Yahweh - Yuriya ɗan Shemaya daga Kiriyat Yarim-shi ma ya yi annabci gãba da birnin nan da kuma ƙasannan, ya amince da dukkan maganganun Irmiya.21Amma da sarki Yehoyakim da dukkan sojojinsa da shugabanninsa suka ji maganarsa sai sarki ya yi ƙoƙari ya kashe shi, amma da Yuriya ya ji sai ya tsorata, ya gudu ya tafi Masar.
22Sai sarki Yehoyakim ya aiki mutane su tafi Masar - Elnatan ɗan Akbor da waɗansu mutanen aka aike su su bi Yuriya zuwa Masar.23Suka ɗauko Yuriya daga Masar suka kawo shi wurin sarki Yehoiyakim. Sai Yehoiyakim ya kashe shi da takobi ya aika gawarsa makabartar da ke waje inda ake rufe mutane marasa galihu.24Amma hannun Ahikam ɗan Shafan yana tare da Irmiya, saboda haka ba a bada shi ga hannun mutane su kashe ba.

27

1A farkon sarautar Zedekiya ɗan Yosiya, sarkin Yahuda, wannan magana ta zo ga Irmiya daga Yahweh.2Wannan shi ne abin da Yahweh ya faɗa mani, "Ka yiwa kanka karkiyar itace. Ka sa su a wuyanka.3Sa'annan ka aika su wurin sarkin Idom, sarkin Mowab, sarkin mutanen Ammon, sarkin Taya, da kuma sarkin Sidon. Ka aika da su ta hannun jakadun sarki da suka zo Yerusalem gun Zedekiya sarkin Yahuda.4Ka ba su umarni domin iyayengijinsu ka ce, 'Ubangiji mai runduna, Allah na Isra'ila ya ce: Wannan shi ne abin da zaku ce da iyayengijinku,

5Ni da kaina na yi duniya ta wurin ƙarfina mai girma da miƙaƙƙen hannuna. Ni ne nayi mutane da dabbobi a kan fuskar duniya, nakan kuma ba da ita ga wanda na ga ya dace a idanuna.6Saboda haka yanzu, ina bada dukkan ƙasar nan a cikin hannun bawana, Nebukadnezza, sarkin Babila. Kuma ina bada abubuwa masu rai na jeji su bauta masa.7Gama dukkan al'ummai za su bauta masa, da ɗansa da kuma jikokinsa, har sai lokaci domin ƙasarsa ya zo. Sa'annan al'ummai da yawa da manyan sarakuna za su ci ƙarfinsa.
8Saboda haka duk al'umma da mulkin da bai bauta wa Nebukadnezza, sarkin Babila ba, bai kuma ba da wuyansa ya yi karkiya da sarkin Babila ba-zan hukunta wannan al'umma da takobi, yunwa, da annoba - wannan furcin Yahweh ne-har sai na hallaka ta ta hannunsa.
9Saboda haka kada ku saurari annabawanku, da masu mafarkanku, masu dubanku, masu sihiri, da matsubbata, waɗanda suke ta yi maku magana suna cewa, 'Kada ku bauta wa sarkin Babila,'10Gama suna yi maku annabcin ƙarya domin su kora ku nesa da ƙasarku, gama zan kore ku, zaku kuma mutu.11Amma al'ummar da ta bada wuyanta ta yi karkiya da sarkin Babila, ta kuma bauta masa, zan bar su su huta a ƙasarsu - wannan furcin Yahweh ne-zasu kuma noma ta su gina mazauninsu a ciki.""'
12Sai na yi magana da Zedekiya sarkin Yahuda na ba shi wannan saƙon, 'Ku ba da wuyanku ku yi karkiya da sarkin Babila ku bauta masa da shi da mutanensa, zaku kuwa rayu.13Donmi zaku mutu-da kai da mutanenka-da takobi, yunwa da annoba, kamar yadda na faɗa game da al'ummar da ta ƙi ta bauta wa sarkin Babila?
14Kada ku saurari maganganun annabawan da suka ce maku, 'Kada ku bauta wa sarkin Babila,' gama suna yi maku annabcin ƙarya ne.15Gama ni ban aikesu ba-wannan furcin Yahweh ne - gama annabcin ƙarya suke yi cikin sunana domin in kore ku ku tafi ku hallaka, da ku da annabawan da suke maku annabci."
16Na yi shelar wannan ma firistoci da dukkan mutane na ce, "Yahweh ya faɗi wannan yace: Kada ku kasa kunne ga maganganun annabawaku da su kayi maku annabci suka ce, 'Duba! ana dawo da kayayyakin gidan Yahweh daga Babila yanzu!' Annabcin ƙarya suke yi maku,17Kada ku saurare su. Ku bauta wa sarkin Babila ku rayu. Don me wannan birni zai zama kufai?18Idan su annabawa ne, kuma idan lallai maganar Yahweh ta zo gare su, to su roƙi Yahweh mai runduna kada ya aika kayan haikalinsa da suka rage, na gidan sarkin Yahuda, da na Yerusalem zuwa Babila.
19Yahweh mai runduna ya faɗi haka game da ginshiƙai da babban daro da aka sani a matsayin "Tekun" da mazauninta, da sauran kayayyakin da suka rage a wannan birni -20kayayyakin da Nebukadnezza sarkin Babila bai ɗauka ba lokacin da ya tafi da Yehoyacin ɗan Yehoiyakim, sarkin Yahuda bautar talala daga Yerusalem zuwa Babila tare da dukkan hakiman Yahuda da na Yerusalem.
21Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan game da kayayyakin da suka rage a gidan Yahweh, da gidan sarkin Yahuda da Yerusalem,22'Za a kawo su Babila, kuma za su kasance a can har sai ranar da na aza a zo domin su - wannan ne furcin Yahweh - sa'annan zan komo da su in maido su a wannan wuri."'

28

1Sai ya kasance a cikin shekarar nan, a farkon mulkin Zedekaya sarkin Yahuda, a shekara ta huɗu kuma a wata na biyar, Annabi Hananiya ɗan Azzur, wanda ya fito daga Gibiyon, yayi magana da ni a gidan Yahweh a gaban firistoci da dukkan mutane. Yace,2"Yahweh Mai runduna, Allah na Isra'ila, Ya faɗi wannan: Na karya karkiyar da sarkin Babila ya ɗora maku.

3A cikin shekara biyu a wannan wuri zan maido da dukkan kayayyakin gidan Yahweh wanda Nebukadnezza sarkin Babila ya ɗauke daga wannan wuri ya tafi dasu Babila.4Daga nan kuma a wannan wurin zan maido da Yehoiyacin ɗan Yehoiyakim, sarkin Yahuda, da dukkan kamammun Yahuda waɗanda aka aika Babila - wannan furcin Yahweh ne - Gama zan karya karkiyar sarkin Babila."
5Sai Annabi Irmiya yayi magana da Annabi Hananiya a gaban firistoci da dukkan mutanen dake tsaye a gidan Yahweh.6Irmiya Annabi yace, "Bari Yahweh yayi haka! bari Yahweh ya tabbatar da maganganun daka anabta a wannan wuri ya maido da kayayyakin gidan Yahweh, da dukkan kamammu daga Babila.7Duk da haka, ka saurari maganar da nake shelarwa a kunnuwanka da kunnuwan dukkan mutane.
8Annabawan da suka wanzu da daɗewa kafin ni da kai sunyi anabci game da al'ummai masu yawa gãba da manyan masarautu, game da yaƙi, da yunwa, da annoba.9Hakanan Annabin da yayi anabcin za a yi salama - Idan maganarsa ta tabbata, to za a sani cewa lallai annabi ne wanda Yahweh ya aiko."
10Amma annabi Hananiya ya tashi ya ɗauki karkiyar dake wuyan annabi Irmiya ya karya ta.11Daga nan sai Hananiya yayi magana a gaban dukkan mutanen yace, "Yahweh ya faɗi haka: kamar dai haka, cikin shekara biyu zan karya kowace karkiya daga wuyan dukkan al'ummai wanda Nebukadnezza sarkin Babila ya ɗora masu." Daga nan annabi Irmiya yayi tafiyarsa.
12Bayan da annabi Hananiya ya karya karkiyar dake wuyan annabi Irmiya, sai maganar Yahweh tazo ga Irmiya, cewa,13"Kaje kayi magana da Hananiya kace, 'Yahweh ya faɗi haka: ka karya karkiyar itace, a maimako zan yi karkiyar ƙarfe.'14Gama Yahweh Mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi haka: na ɗora karkiyar ƙarfe a bisa wuyan dukkan waɗannan al'ummai domin su bauta wa Nebukadnezza sarkin Babila, kuma zasu bauta mashi. Na kuma bashi bisashen jeji dake cikin gonaki domin yayi mulki a kansu."
15Kuma annabi Irmiya ya cewa annabi Hananiya, "Ka saurara Hananiya! Yahweh bai aiko ka ba, amma kai da kanka kasa mutanen nan su gaskata ƙarya.16Saboda haka Yahweh ya faɗi wannan: duba, ina gab da aika ka daga wannan duniya. A wannan shekarar zaka mutu, tunda kayi shelar tawaye ga Yahweh."17A cikin watan bakwai na wannan shekara, annabi Hananiya ya mutu.

29

1Waɗannan ne maganganun dake cikin littafin da annabi Irmiya ya aika daga Yerusalem zuwa ga ragowar dattawan daga cikin kamammun da kuma firistoci, da annabawa, da dukkan mutanen da Nebukadnezza ya tura bauta daga Yerusalem zuwa Babila.2Wannan ya faru ne bayan da aka aika da sarki Yehoyacin, da mahaifiyar sarki, da manyan dagatai, da shugabannin Yahuda da Yerusalem, da masu sana'o'in hannu daga Yerusalem.3Ya aika da wannan littafi ne ta hannun Elasa ɗan shafan da Gemariya ɗan Hilkiya waɗanda Hezekaya, sarkin Yahuda, ya aika ga Nebukadnezza sarkin Babila.

4Littafin yace, "Yahweh Mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan ga dukkan kamammu waɗanda nasa suka tafi bauta daga Yerusalem zuwa Babila,5'Ku gina gidaje ku zauna a cikinsu. Ku shuka gonaki kuci amfaninsu.
6Ku auri mataye ku haifi 'ya'ya maza da mata. Ku aurowa 'ya'yanku maza mataye, ku aurar da 'ya'yanku mata ga mazaje. Bari su haifi 'ya'ya maza da mata kuma ku ƙaru ta haka ba zaku zama 'yan kaɗan ba.7Ku biɗi salamar birnin da na aika daku bauta, ku yi roƙo gare ni a madadinsa tunda zaku kasance da salama idan yana cikin salama.'
8Gama Yahweh Mai runduna, Allah na Isra'ila, Ya faɗi wannan, 'Kada ku bar annabawanku dake zaune a tsakaninku da masu sihirinku su ruɗe ku, kada kuma ku saurari mafarke-mafarken da ku da kanku kuke yi.9Gama suna ruɗin ku cikin anabcin da suke yi a cikin sunana. Ban aike su ba - wannan furcin Yahweh ne.'
10Gama Yahweh ya faɗi wannan 'Idan Babila ta yi mulkinku har shekaru saba'in, zan taimake ku in aiwatar da maganata mai nagarta game da ku in sake maido da ku a wannan wuri.11Gama ni da kaina na san irin shirye-shiryen da nake da su dominku - wannan furcin Yahweh ne- shirye-shirye na salama ba na bala'i ba, domin in baku gaba mai kyau da bege.
12Daga nan zaku yi kira a gare ni, zaku je ku yi addu'a a gare ni, zan kuma saurare ku.13Gama zaku neme ni ku kuma same ni, tunda zaku neme ni da dukkan zuciyarku.14Daga nan zan samu gare ku - wannan furcin Yahweh ne - zan kuma maido da kadarorinku; zan tattaro ku daga cikin dukkan al'ummai da wuraren da na warwatsar da ku - wannan furcin Yahweh ne - gama zan maido da ku wannan wuri daga inda nasa kuka tafi bauta.'
15Tunda kunce Yahweh ya tado maku da annabawa a Babila,16Yahweh ya faɗi wannan game da wanda ke zaune bisa kursiyin Dauda da dukkan mutanen da ke zaune a cikin birnin, 'yan'uwanku waɗanda basu tafi tare da ku cikin bauta ba -17Yahweh Mai runduna ya faɗi haka, 'Duba, ina gab da aiko da takobi, da yunwa da cuta a kansu. Gama zan maishe su kamar ruɓaɓɓen ɓauren da ba a iya ci.
18Daga nan zan runtume su da takobi, da yunwa, da annoba in maida su abin tsoratarwa ga dukkan mulkokin duniya.-abin ƙyama, abin la'ana da tsãki, abin kunya cikin dukkan al'ummai inda na warwatsa ta.19Wannan saboda basu saurari maganata ba ne - wannan furcin Yahweh ne-wanda na aika masu ta wurin bayina annabawa. Na aike su sau da yawa, amma baku saurara ba-wannan furcin Yahweh ne.'
20Domin wannan ku da kanku ku saurari maganar Yahweh, dukkanku 'yan bautar da ya kora daga Yerusalem zuwa Babila,21Yahweh Mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan game da Ahab ɗan Kolaiya da Zedekaya ɗan Ma'ãseya, waɗanda suke yi maku anabcin ƙarya a cikin sunana: Duba, ina gab da sanya su cikin hannun Nebukadnezza sarkin Babila. Zaya kashe su a kan idanun ku.
22Daga nan za a furta la'ana game da waɗannan mutane daga bakin ɗaurarrun Yahuda da ke Babila. La'anar zata ce: Dãma Yahweh ya maida kai kamar Zedekaya da Ahab, waɗanda sarkin Babila ya gashe cikin wuta.23Wannan zaya faru ne saboda abubuwan kunya da suka aikata a Isra'ila da suka yi zina da matayen maƙwabtansu suka kuma furta maganganun ƙarya a cikin sunana, abubuwan da ban taɓa umurtar su ba su faɗa. Gama Ni ne na sani; Ni ne shaida-wannan furcin Yahweh ne."'
24Game da Shemaiya Nehelamiye, ka faɗi wannan:25Yahweh Mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: Domin ka aika da wasiƙu a cikin sunanka zuwa ga dukkan mutanen Yerusalem, zuwa ga Zefaniya ɗan Ma'ãseiya firist, da dukkan firistoci, kãce,26Yahweh ya maida kai firist a maimakon Yehoaida firist, domin kayi shugabancin gidan Yahweh. Kai ne ke mulkin dukkan mutanen dake girgije-girgije suna maida kansu annabawa. Sai ka sanya su a turu da sarƙoƙi.
27To yanzu, me yasa baka tsautawa Irmiya na Anatot ba, wanda ya maida kansa annabi mai tsayayya da kai?28Gama ya aika mana a Babila yana cewa, 'Lokaci ne mai tsawo za ayi. Ku gina gidaje ku zauna a ciki, ku shuka gonaki ku ci amfaninsu.""'29Zefanaya firist ya karanta wannan wasiƙa a kunnen annabi Irmiya.
30Sai maganar Yahweh tazo ga Irmiya, cewa,31"Ka aika magana ga dukkan 'yan bauta kace, 'Yahweh ya faɗi wannan game da Shemaiya Nehelamiye: Saboda Shemaiya yayi maku anabci wanda Ni da kaina ban aike shi ba, kuma yasa kun gaskata ƙarya,32Domin wannan Yahweh ya faɗi haka: Duba, Ina gab da horon Shemaiya Nehelamiye da zuriyarsa. Ba za a sami wani mutum da zaya tsaya masa ba a cikin mutanen nan. Ba zai ga alherin da zan yiwa mutanena ba - wannan furcin Yahweh ne - Gama yayi shelar tawaye gãba da Yahweh."'

30

1Maganar da ta zo wa Irmiya daga Yahweh, cewa,2"Ga abin da Yahweh, Allah na Isra'ila, yace, 'Ka rubutawa kanka a littafi dukkan maganganun dana furta maka a littafi.3Gama duba, kwanaki suna zuwa - wannan ne furcin Yahweh - da zan maido da kaddarorin mutanena, Isra'ila da Yahuda. Ni, Yahweh, Na faɗi wannan. Gama zan maido da su ƙasar da na ba kakanninsu, zasu kuma mallake ta."'

4Waɗannan ne maganganun da Yahweh ya furta game da Isra'ila da Yahuda,5"Gama Yahweh ya faɗi wannan, 'Munji muryar rawar jiki da fargaba bata salama ba.
6Ku yi tambaya ku ji ko Namiji na haihuwar ɗa. To yaya naga kowanne mutum mai ƙuruciya da hannu a kwankwaso kamar macen da zata haihu? Yaya fuskokinsu suka koɗe?7Kaito! Gama wannan rana babba ce, babu wata kamar ta. Zata zama lokacin fargaba domin Yakubu, amma za a cece shi daga ita.
8Gama zaya kasance a wannan rana - wannan furcin Yahweh ne Mai runduna - zan karya karkiyar daga wuyan ku, zan ɓalle sarƙoƙinku, domin bãƙi ba zasu sake bautar da ku ba.9Amma zasu yi sujada ga Yahweh Allahnsu su kuma bautawa Dauda sarkinsu, wanda zan naɗa sarki a kansu.
10To kai, Yakubu bawana, kada kaji tsoro - wannan furcin Yahweh ne - kada kuma ka firgita, Isra'ila. Gama duba, Ina gaf da maido da kai daga nesa, Zuriyarka kuma daga ƙasar bauta. Yakubu zai dawo ya zauna cikin salama; za a kãre shi, kuma babu sauran tsoratar wa.11Gama ina tare da ku - wannan furcin Yahweh ne - domin in cece ku. Daga nan zan kawo cikakken ƙarshen dukkan al'ummai inda na warwatsar da ku. Amma tabbas bazan kawo ƙarshenku ba, koda yake na horar da ku bisa adalci kuma tabbas bazan barku babu horo ba.'
12Gama Yahweh ya faɗi wannan, 'Rauninku ba ya warkuwa; rauninku ya sami lahani.13Babu wanda za yayi roƙo domin ku; babu wani magani da zai warkar da rauninku.
14Masoyanku dukka sun manta da ku. Ba zasu neme ku ba, gama na yi maku rauni da raunin maƙiyi da kuma horon ubangida mai mugunta saboda kurakuranku masu yawa da zunubanku marasa ƙirguwa.15Me yasa kuke neman taimako domin rauninku? zafinku baya warkuwa. Saboda kurakuranku masu yawa da zunubanku marasa ƙirguwa, na yi maku waɗannan abubuwa.
16Domin wannan duk waɗanda ke cinye ku za a cinye su, kuma dukkan magabtanku zasu tafi cikin bauta. Domin dukkan waɗanda suka washe ku za su zama abin washewa, kuma dukkan waɗanda suka maida ku ganima zan maida su ganima.17Gama zan kawo warkarwa gare ku; zan warkar da ku daga raunukanku - wannan furcin Yahweh ne - zan yi wannan saboda sun kira ku: Yasassu. Babu wanda ya kula da wannan Sihiyonar."'
18Yahweh ya faɗi wannan, "Duba, Ina gab da maido da kaddarorin rumfunan Yakubu in kuma ji tausayin gidajensu. Daga nan za a gina birni a bisa rusassun wurarensu, mafaka mai ƙarfi kuma zata kasance inda take a dã.19Daganan waƙar yabo da ƙarar shagulgula zasu fito daga gare su, gama zan ƙãra su ba kuma zan rage su ba; zan darjanta su domin kada su wulaƙanta.
20Daga nan mutanensu zasu zama kamar dã, taronsu kuma zaya tabbata a gabana yayin da zan horar da masu tsananta masu a yanzu.21Shugabansu zaya fito daga cikin su. Zaya ɓullo daga cikin su yayin da zan jawo shi kusa yayin da kuma ya matso gare ni. Idan ban yi haka ba wane ne zai iya zuwa kusa da ni? - wannan furcin Yahweh ne.22Daganan zaku zama mutanena, ni kuma in zama Allahnku.
23Duba, iskar fushin Yahweh, da hasalarsa, tana fita waje. Iska ce marar tsaitsayawa. Zata yi guguwa bisa kawunan mutane masu mugunta.24Fushin Yahweh ba zai dawo ba har sai ya aiwatar kuma ya haifar da nufe-nufen zuciyarsa. A ranakun ƙarshe, zaku fahimci wannan."

31

1"A wannan lokaci - wannan furcin Yahweh ne- Zan zama Allahn dukkan iyalan Isra'ila, su kuma zasu zama mutanena."2Yahweh ya faɗi wannan, "Mutanen da zuka tsira daga takobi sun sami tagomashi a jeji; zan fita in bayar da hutawa ga Isra'ila."3Yahweh ya bayyana gare ni a baya kuma yace, "Na ƙaunace ka, Isra'ila, da madawwamiyar ƙauna. Saboda haka na jawoka zuwa gare ni da amintaccen alƙawari.

4Zan sake gina ki domin ki ginu, budurwa Isra'ila. Zaki sake ɗaukar tamburanki ki fita da raye-rayen murna.5Zaki sake dasa gonakin inabi a tsaunukan samariya; manoman zasu dasa kuma suyi amfani da 'ya'yan.6Gama rana tana zuwa wadda masu tsaron tsaunukan Ifraim zasu yi shela, 'Ku tashi, mu tafi Sihiyona ga Yahweh Allahnmu.'
7Gama Yahweh ya faɗi wannan, "Ku yi sowa ta farinciki game da Yakubu! Ku yi sowa cikin jindaɗi game da manyan mutanen al'ummai! Bari aji yabo. Ku ce, 'Yahweh ya ceci mutanensa, ragowar Isra'ila.'
8Duba, ina gab da kawo su daga ƙasashen arewa. Zan tattaro su daga sassan duniya mafi nisa. Makaho da gurgu zasu kasance a cikin su; Mataye masu ciki da waɗanda ke kusa da haihuwa zasu kasance tare da su. Babban taro ne zaya dawo a nan.9Za su zo da kuka; zan bishe su yayin da sukeyin roƙo. Zansa suyi tafiya zuwa maɓulɓulan ruwa a bisa miƙaƙƙiyar hanya. Ba zasu yi tuntuɓe akai ba, gama zan zama Uba ga Isra'ila, Ifraim kuma zaya zama ɗan farina."
10Ku saurari maganar Yahweh, al'ummai. Ku yi rahoto har ga ƙasashen kurmi dake nesa. Ku al'ummai dole ku ce, 'Wanda ya warwatsa Isra'ila yana tattara ta kuma yana tsaronta kamar yadda makiyayi ke tsaron tumakinsa.'11Gama Yahweh ya ceto Yakubu ya kuma fanso shi daga hannun wanda yafi ƙarfinsa sosai.
12Daga nan zasu zo su yi farinciki bisa tuddan Sihiyona. Fuskokinsu zasu haskaka saboda alherin Yahweh, bisa hatsi da ruwan inabi, bisa mai da 'ya'yan garken awakinsu da na tumaki da kuma na shanu. Gama rayuwarsu zata zama kamar fadamar da ake yiwa banruwa, ba kuma zasu ƙara jin baƙinciki ba daɗai.
13Daga nan budurwai zasu yi farinciki da rawa, samari kuma da tsofaffi zasu kasance tare. Domin zan canza makokinsu zuwa bukukuwa. Zan ji tausayin su insa su yi farinciki a maimakon baƙinciki.14Daga nan zan mamaye rayuwar firistoci da yalwa. Mutanena zasu cika kansu da nagartata-wannan ne furcin Yahweh."
15Yahweh ya faɗi wannan: "An ji murya a Ramah, kururuwa da kuka mai ɗaci. Rahila ce ke kukan 'ya'yanta. Taƙi ta ta'azantu game da su, gama basu a raye."
16Yahweh ya faɗi wannan, "Ki tsai da muryarki daga kuka idanunki kuma daga hawaye; gama akwai sakamako game da aikinki - wannan ne furcin Yahweh - 'ya'yanki zasu dawo daga ƙasar maƙiya.17Akwai bege domin gabanki - wannan furcin Yahweh ne- zuriyarki zasu dawo cikin kan iyakokinsu."
18Babu shakka naji bakincikin Ifraim, 'Ka horar da ni, kuma na horu kamar maraƙin da ba horarre ba. Ka maido da ni kuma zan sami maiduwa, gama kai ne Yahweh Allahna.19Gama bayan na juyo zuwa gare ka, nayi nadama; bayan na horu, na mari cinyata. Na ji kunya kuma na ƙasƙantu, gama na ɗauki tsarguwar ƙuruciyata.'20Ifraimu ba ɗa na ne mai daraja ba? Ba ƙaunataccena ba ne, ɗan da nake jin daɗinsa? Gama duk sa'ad da na yi maganar tsayayya da shi, babu shakka ina tunawa da shi a raina da ƙauna. Ta haka zuciyata ke marmarin sa. Babu shakka zanji tausayin sa - wannan furcin Yahweh ne."
21Ku kafawa kanku alamun hanya. Ku sanyawa kanku alamun jagora. Ku shirya tunaninku a tafarki mai kyau, hanyar da zaku bi. Ku dawo, budurwan Isra'ila! Ku dawo cikin waɗannan biranen naku.22Har yaushe zaki ci gaba da shakka, ɗiya marar aminci? Gama Yahweh ya halicci wani sabon abu a duniya - mace ta kewaye namiji maji ƙarfi.
23Yahweh Mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan, "Idan na maido da mutanen zuwa cikin ƙasarsu, zasu faɗi wannan cikin ƙasar Yahuda da kuma biranenta, 'Bari Yahweh ya albarkace ka, kai wuri mai adalci inda ya ke zaune, kai dutse mai tsarki.'24Gama Yahuda da biranenta zasu zauna tare a wurin, kamar yadda manoma da waɗanda suka fita da garkunansu.25Gama zan bada ruwa ga gajiyayyu domin su sha, kuma zan cika dukkan sumammu."26Bayan wannan sai na farka, sai na lura da cewa barcina ya wartsakar da ni.
27Duba, ranaku suna zuwa - wannan ne furcin Yahweh - Inda zan shuke gidajen Isra'ila dana Yahuda da zuriyoyin mutane dana bisashe.28A baya, Na keɓe su ciki tsaro domin in tunɓuke su in yage su, in tuntsurar, in lalatar, in kuma kawo masu bala'i. Amma a kwanaki masu zuwa, zan lura da su, domin in gina su in kuma dasa su - wannan furcin Yahweh ne.
29A cikin waɗannan kwanaki babu wanda zaya sake cewa, 'Ubanni sun ci inabi masu tsami, amma haƙoran 'ya'ya ne suka dãsashe.'30Gama kowane mutum zaya mutu cikin kurakuransa; Duk wanda ya ci inabi masu tsami, haƙoransa ne zasu dãsashe.
31Duba, kwanaki suna zuwa - wanna furcin Yahweh ne - inda zan kafa sabon alƙawari tare da gidan Isra'ila da kuma gidan Yahuda.32Ba zaya zama kamar alƙawarin dana kafa da Ubanninsu ba a kwanakin da na ɗauko su na kamo hannusu na fito da su daga ƙasar masar. Waɗannan kwanakin ne inda suka karya alƙawarina, duk da cewa ni miji ne a gare su - wannan furcin Yahweh ne.
33Amma wannan ne alƙawarin da zan kafa da gidan Isra'ila bayan waɗannan kwanaki - wannan furcin Yahweh ne: Zan sanya shari'ata a cikinsu in rubuta ta a zukatansu, gama zan zama Allahnsu, zasu kuma zama mutanena.34Daganan babu sauran wani mutum ya koyawa maƙwabcinsa, ko wani mutum ya koyawa ɗan'uwansa ya ce, 'Ka san Yahweh!' gama dukkan su, daga mafi ƙanƙantarsu har ya zuwa mafi girmansu, zasu san ni - wannan furcin Yahweh ne - Gama zan gafarta kurakuransu ba kuma zan sake tunawa da zunubansu ba."
35Yahweh ya faɗi wannan - shi ne wanda yake sanya rana ta haskaka da rana ya kuma jejjera wata da taurari su haskaka da dare. Shi wanda ke sanya teku na motsi raƙuman ruwanta kuma na ruri. Sunansa Yahweh Mai runduna.36Sai idan waɗannan dawwamammun abubuwan sun ɓace daga gare ni - wannan furcin Yahweh ne- ko zuriyar Isra'ila zasu daina zama al'umma a gabana."
37Yahweh ya faɗi wannan, "Sai idan za a iya ɗaukar gwajin sammai dake nesa, sai kuma idan za a iya gano harsashin duniya dake can ƙasa, shi ne zan iya yashe da dukkan zuriyar Isra'ila saboda dukkan abin da suka yi - wannan furcin Yahweh ne."
38Duba, kwanaki suna zuwa - wannan furcin Yahweh ne - sa'ad da za a sake gina birnin domina, daga hasumiyar Hananel zuwa ‌Ƙ‌ofar kwana.39Daga nan layin gwajin zai fita ya ƙara nisa, zuwa tuddun Gerab da kewayen Goya.40Dukkan kwarin gawawwaki da tokarsu, da dukkan filayen kurmi har ya zuwa Kwarin Kidron har zuwa kwanar ‌Ƙofar Doki da ke gabas, za a keɓe domin Yahweh. Ba za a sake rusarwa ko tuntsurar da birnin ba, har abada."

32

1Wannan ce maganar da ta zo wa Irmiya daga Yahweh a shekara ta goma ta sarautar sarki Zedekiya na Yahuda, a shekara ta sha takwas ta Nebukadnezza.2A wannan lokaci, sojojin sarkin Babila sun yi wa Yerusalem sansani, Annabi Irmiya kuma yana cikin kurkukun harabar 'yan tsaro dake cikin gidan sarkin Yahuda.

3Zedekiya sarkin Yahuda ya sanya shi cikin kurkuku ya kuma ce, "Me yasa kake anabci kana cewa, 'Yahweh ya faɗi wannan: Duba, ina gab da miƙa wannan birni cikin hannun sarkin Babila, kuma zaya ci shi da yaƙi.4Zedekiya sarkin Yahuda ba zai kubce ba daga hannun Kaldiyawa, gama babu shakka za a miƙa shi cikin hannun sarkin Babila. Bakinsa kuma za ya yi magana da bakin sarkin, idanunsa kuma zasu ga idanun sarkin.5Za ya ɗauki Zedekiya zuwa Babila, zaya zauna a can har sai na gama horar da shi - wannan furcin Yahweh ne. Koda yake za ka yi yaƙi da Kaldiyawa, ba zaka yi nasara ba."'
6Irmiya ya ce, "Maganar Yahweh tazo gare ni, tana cewa,7'Duba, Hanamel ɗan Shallum kawunka na zuwa wurin ka kuma zai ce, "Ka saiwa kanka gonata da ke Anatot, domin kai ne ka ke da 'yancin sayen ta.""'
8Daga nan, kamar yadda Yahweh ya furta, Hanamel, ɗan-ɗan kawuna, Yazo wuri na a harabar 'yan tsaro, sai ya ce da ni, "Ka sayi gonata dake a Anatot cikin ƙasar Benyamin, domin kai ne ke da 'yancin gãdo, kuma 'yancin saye na gare ka. Ka sai wa kanka." Daga nan na sani cewa wannan maganar Yahweh ce.9Sai na sayi gonar da ke Anatot daga wurin Hanamel, ɗan-ɗan kawuna, sai na gwada mashi azurfar, shekel sha bakwai a nauyi.
10Sai na rubuta a takarda na hatimce ta, na kuma kawo shaidu su shaida. Sai na gwada mashi azurfar a ma gwaji.11Sai na ɗauki takardar kammala saye da aka hatimce, bisa ga shari'a da ka'idoji, da kuma takardar kammala saye da ba a hatimce ba.12Sai na bada hatimtacciyar takardar ga Baruk ɗan Neriya ɗan Masiyya a gaban Hanamel, ɗan kawuna, da kuma shaidun da suka sa hannu a hatimtacciyar takardar, a kuma gaban Yahudawan da ke zaune a harabar 'yan tsaron.
13Sai na bada umarni ga Baruk a gaban su. Nace,14Yahweh Mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: Karɓi takardunnan, dukkan takardun kammala sayen da wannan da aka hatimce da waɗannan da ba a hatimce ba, sai ka sanya su a cikin tukunyar ƙasa domin suyi ƙarko na dogon lokaci.15Gama Yahweh Mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: Za a sake sayen gidaje, da gonaki, da garkunan inabi a cikin wannan ƙasar."
16Bayan da na bada rasiɗin saye ga Baruk ɗan Neriya, sai nayi addu'a ga Yahweh nace,17Kaito, Ubangiji Yahweh! Duba! Kai ka ɗai ka halitta Sammai da duniya ta wurin babban ƙarfinka da ɗagaggen hannunka. Babu abin da ka faɗa wanda zai gagare ka ka yi.18Kana nuna amintaccen alƙawarinka ga dubbai kana kuma zubo da tsarguwar mutane bisa cinyoyin 'ya'yansu bayansu. Kai ne mai girma Allah mai iko kuma; Yahweh Mai runduna ne sunanka.
19Kai babba ne a hikima mai girma kuma cikin ayyuka, idanunka a buɗe suke ga dukkan hanyoyin mutane, domin kaba kowanne mutum abin da ya cancanci halinsa da ayyukansa.20Ka yi alamu da al'ajibai a ƙasar Masar. Har yazuwa yau a nan ƙasar Isra'ila da kuma cikin dukkan 'yan adam, kasa sunanka ya zama sananne.21Gama ka fito da mutanenka Isra'ila daga ƙasar Masar da alamu da al'ajibai, da hannu mai ƙarfi, da ɗagaggen hannu, da kuma babbar razana.
22Daga nan ka basu wannan ƙasar - wanda ka rantsewa Ubanninsu zaka basu - ƙasar dake zubo da madara da zuma.23Sai suka shiga suka mallake ta. Amma ba su yi biyayya da muryarka ba ko suka zauna cikin biyayya da shari'arka ba. Ba su yi komai ba game da abin da ka umarce su su yi, sai ka kawo dukkan wannan bala'i a kansu.
24Duba! Tarin sansanin ya kai har birnin domin ya ci shi da yaƙi. Gama saboda Takobi, da yunwa, da annoba, an bayar da birnin cikin hannun Kaldiyawa da suke yaƙi da shi. Gama abin da kace zaya faru yana faruwa, kuma duba, kana kallo.25Daga nan kai da kanka kace mani, "Ka sai wa kanka gona da azurfa kuma ka kawo shaidu su shaida, duk da cewar ana bayar da wannan birni a hannun Kaldiyawa."
26Maganar Yahweh ta zo ga Irmiya, tana cewa,27Duba! Ni ne Yahweh, Allahn dukkan 'yan adam. Akwai abin da ya gagare ni in yi?28Saboda haka Yahweh ya faɗi wannan, "Duba, ina gab da bayar da wannan birni cikin hannun Kaldiyawa da Nebukadnezza, sarkin Babila. Za ya ci shi da yaƙi.
29Kaldiyawan da ke yaƙi da birnin nan za su zo su cinna mashi wuta su ƙone shi, tare da gidajen da ke kan rufin wuraren da mutane ke yiwa Ba'al sujada suke kuma zuba baye-bayen shayarwa ga wasu alloli domin su cakune ni.30Gama mutanen Isra'ila da Yahuda babu shakka mutane ne da ke ta aikata mugunta a gaban idanuna tun daga ƙuruciyarsu. Babu shakka mutanen Isra'ila sun ɓata mani rai ta wurin ayyukan hannuwansu - wannan furcin Yahweh ne.
31Yahweh ya furta cewa wannan birni na tunzura fushina da hasalata tun daga ranar da aka gina shi. Haka yake har zuwa wannan rana. To zan kawar da shi daga fuskata32saboda dukkan muguntar mutanen Isra'ila da ta Yahuda, abubuwan da suka yi domin su cakune ni - su, da sarakunansu, da dagatansu, da firistocinsu, da annabawansu, da kuma kowane mutum a Yahuda da dukkan mazaunan Yerusalem.
33Sun juya mani bayansu a maimakon fuskokinsu, koda yake da ɗoki na koyar da su. Nayi ƙoƙari in koyar da su, amma babu wani cikinsu da ya saurara domin ya ɗauki gyara.34Suka jera haramtattun gumakansu a cikin gidan da ake kira da sunana, suka gurɓata shi.35Suka gina dogayen wurare domin Ba'al a kwarin Ben Hinnom domin su sanya 'ya'yansu maza da mata cikin wuta domin Molek. Ban umarcesu ba. Bai taɓa shiga tunanina ba cewa zasu aikata wannan abin ƙyama su sa Yahuda ya yi zunubi.'
36To saboda haka yanzu, Ni, Yahweh, Allah na Isra'ila, Na faɗi wannan game da birnin, birnin da kuke cewa, 'An bayar da shi cikin hannun sarkin Babila ta wurin takobi, da yunwa, da annoba.37Duba, ina gab da tattaro su daga kowace ƙasa inda na kora su cikin fushina, da hasalata, da babban jin haushina, Ina gab da maido su cikin wannan wuri in kuma sa su iya zama cikin tsaro.
38Daga nan zasu zama mutanena, Ni kuma in zama Allahnsu.39Zan basu zuciya ɗaya da hanya ɗaya na girmama ni kullum domin ya zama alheri a gare su da kuma zuriyarsu bayansu.40Daga nan tare da su zan kafa madawwamin alƙawari, cewa bazan juya daga yi masu alheri ba. Zan sa girmamawa domi na a zukatansu, ta haka ba zasu sake juyawa daga gare ni ba.
41Daga nan zan yi farinciki wurin yi masu alheri. Da aminci zan dasa su cikin ƙasar nan da dukkan zuciyata da dukkan raina.42Gama Yahweh ya faɗi wannan, 'Kamar yadda na kawo dukkan wannan babban bala'i a bisa mutanen nan, haka zan kawo masu dukkan abubuwan alherin da nace zan yi domin su.
43Daga nan za a sayi gonaki a cikin wannan ƙasar, wadda kuke cewa, "Wannan busasshiyar ƙasa ce, wadda babu mutum balle dabba. An bayar da ita cikin hannun Kaldiyawa."44Za su sayi gonaki da azurfa su kuma rubuta cikin hatimtattun takardu. Zasu tattara shaidu a cikin ƙasar Benyamin, a dukkan kewayen Yerusalem da biranen Yahuda, a cikin birane a cikin garuruwan tudu da kuma ƙasashen kwari, da kuma biranen Negeb. Gama zan maido da kaddarorinsu - wannan furcin Yahweh ne."'

33

1Daga nan maganar Yahweh ta zo ga Irmiya karo na biyu, yayin da yake kulle a harabar 'yan tsaro, cewa,2"Yahweh mahalicci, ya faɗi wannan - Yahweh, wanda yake halittawa domin ya tabbatar-Yahweh ne sunansa,3Ku kira gare ni, Ni kuma zan amsa maku. Zan nuna manyan abubuwa a gare ku, asirai da baku fahimta ba.'

4Gama Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan game da gidajen da ke cikin wannan birni da gidajen sarakunan Yahuda waɗanda suka rushe saboda mamayewar sansani da takobi,5Kaldiyawa suna zuwa su yi yaƙi su kuma cika waɗannan gidaje da gawawwakin mutane waɗanda zan kashe cikin fushina da hasalata, yayin da na ɓoye fuskata daga wannan birni saboda dukkan muguntarsu.
6Amma duba, Ina gab da kawo warkarwa da lafiya, zan warkar da su in kawo masu yalwa, salama da aminci.7Gama zan maido da kaddarorin Yahuda da Isra'ila; Zan kuma gina su kamar da farko.8Daga nan zan tsarkake su daga dukkan kurakuran da suka yi a gare ni. Zan gafarta dukkan kurakuran da suka yi a gare ni, da kuma dukkan hanyoyin da suka yi tsayayya a gare ni.9Gama wannan birni zai zame mani abin farinciki, waƙar yabo da girmamawa daga dukkan al'umman duniya waɗanda zasu ji dukkan abubuwan alheri da zan yi domin shi. Daga nan zasu ji tsoro su girgiza saboda dukkan abubuwan alheri da salama da zan bayar a gare su.
10Yahweh ya faɗi wannan, 'A wannan wurin wanda yanzu kuke cewa, "Kufai ne, wurin da babu mutum balle dabba," a biranen Yahuda da kuma titunan Yerusalem waɗanda suke kufai babu mutum balle dabba, da za a sake ji a ciki11‌Ƙarar farinciki da ƙarar murna, ƙarar ango, da ƙarar amarya, ƙarar waɗanda suka ce, yayin da suke kawo baye-bayen godiya ga gidan Yahweh, "Ku bada godiya ga Yahweh Mai runduna, gama Yahweh nagari ne, kuma ƙaunarsa marar kasawa ta dawwama har abada!" Gama zan maida kaddarorin ƙasar nan kamar yadda suke a dã,' inji Yahweh.
12Yahweh Mai runduna ya faɗi wannan: 'A wannan kufan wuri, inda yanzu babu mutum balle dabba-a dukkan biranen za a sami saura inda makiyaya zasu hutar da garkunansu.13A cikin biranen da ke ƙasar tudu, da kwari, da kuma Negeb, a cikin ƙasar Benyamin da dukkan kewayen Yerusalem, da kuma cikin biranen Yahuda, garkuna kuma zasu sake bi ta ƙarƙashin hannuwan masu ƙirga su,' inji Yahweh.
14Duba! kwanaki na zuwa - wannan furcin Yahweh ne-inda zan aikata abin da na yi alƙawari game da gidan Isra'ila da kuma gidan Yahuda.15A cikin waɗannan kwanaki da kuma cikin wannan lokaci zan sa reshen adalci ya tsiro domin gidan Dauda, zaya aiwatar da hukunci da kuma adalci a cikin ƙasar.16A waɗannan kwanaki za a ceci Yahuda, Yerusalem kuma zata zauna cikin tsaro, gama ga yadda za a kira ta, "Yahweh ne adalcinmu."'
17Gama Yahweh ya faɗi wannan: 'Daga zuriyar gidan Dauda ba za a taɓa rasa mutum da zaya zauna a kursiyin gidan Isra'ila ba,18ko kuwa a rasa mutum daga Lebiyawa firistoci da zaya tsaya a gabana ya ɗaga baye-baye na ƙonawa ba, ya ƙona baye-bayen abinci ba, ya kuma aiwatar da baye-baye na hatsi a dukkan lokaci."'
19Maganar Yahweh ta zo ga Irmiya, cewa,20Yahweh ya faɗi wannan: 'Idan zaku iya karya alƙawarina da rana da dare yadda ba za a sake yin rana ko dare ba a lokuttansu,21to zaku iya karya alƙawarina da Dauda bawana, yadda ba za a sake samun ɗan da zai zauna a kursiyinsa ba, da kuma alƙawarina da Lebiyawa Firistoci bayina.22Kamar yadda baza a iya ƙirga rundunar sama ba, ko kuma a iya gwada yashin da ke bakin teku, hakanan zan kawo ƙaruwa ga zuriyar Dauda bawana da kuma Lebiyawa da ke bauta a gabana."'
23Maganar Yahweh ta zo ga Irmiya, cewa,24"Ba ku yi la'akari da abin da mutanen nan suka furta ba da suka ce, 'Iyalai biyu da Yahweh ya zaɓa, yanzu ya watsar da su'? Ta wannan hanya sun wulaƙanta mutanena, suna cewa ba al'umma ba ce kuma a gaban mu.
25Ni, Yahweh, Na faɗi wannan, 'Idan da ban kafa alƙawarin rana da dare ba, ban kuma kafa dokokin sama da duniya ba,26to shi ne zan watsar da zuriyar Yakubu da Dauda bawana, har da ba zan kawo wani daga gare su ba da za ya yi mulki bisa zuriyar Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu ba. Gama zan maido da kaddarorinsu in nuna masu jinƙai."'

34

1Maganar da ta zo wurin Irmiya daga Yahweh, lokacin da NebuKadnezza sarkin Babila da dukkan rundunarsa, tare da dukkan sarakunan duniya, su harabobin da ke a ƙarkashin ikonsa, kuma dukkan mutanensu suna zuwa yaƙi gãba da Yerusalem da dukkan biranenta, cewa:2'Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: Jeka ka yi magana da Zedekiya sarkin Yahuda ka kuma ce masa, 'Yahweh ya faɗi wannan: Duba, ina gab da miƙa wannan birni cikin hannun sarkin Babila. Zai ƙone shi.3Ba zaka tsira daga hannunsa ba, gama lallai za a kama ka a miƙa ka a cikin hannunsa. Idanunka za su dubi idanun sarkin Babila; zai yi magana da kai fuska da fuska yayin da kake tafiya zuwa Babila.'

4Saurari maganar Yahweh, Zedekiya sarkin Yahuda! Yahweh ya faɗi wannan game da kai, 'ba za ka mutu ta hanyar takobi ba.5Za ka mutu cikin salama. Kamar yadda aka yi wa kakanninka jana'izar ƙonawa, sarakuna magabatan ka, haka za su ƙone jikinka. Za su ce, "kaito, shugaba!" Za su yi maka makoki. Yanzu dai na faɗi_ wannan furcin Yahweh ne."
6Sai Irmiya annabi ya furta wa Zedekiya sarkin Yahuda dukkan waɗannan maganganu a Yerusalem.7Rundunar sarkin Babila suka yi yaƙi da Yerusalem da dukkan sauran biranen Yahuda: Lakish da Azeka. Waɗannan biranen Yahuda sun kasance kamar birane masu tsaro mai ƙarfi.
8Maganar da ta zo ga Irmiya daga wurin Yahweh bayan da Zedekiya sarki ya yi alƙawari da dukkan mutanen Yerusalem, domin ya furta 'yanci gare su da9cewa bari kowane ya 'yantar da bawansa Bayahude, namiji da ta mace, wato mutum na iya ɗaukan bawa Ba-yahude, wanda ya ke ɗan uwansa.
10Sai dukkan shugabanni da mutanen suka ɗauki alƙawari kowannensu da cewa su 'yantar bayinsu maza da mata domin kada su sake zama bayi. Suka yi biyayya su ka 'yantar su.11Amma bayan haka sai suka canza zuciyarsu. Suka dawo da bayin da suka 'yantar. Suka tilasta masu su sake zama bayi.
12Sai maganar Yahweh ta zo ga Irmiya, cewa,13"Yahweh, Allah na Isra'ila, yana cewa, 'Ni da kaina na yi alƙawari da ubanninku a ranar da na fito da su daga ƙasar Masar, daga gidan bauta. A wannan lokaci ne na ce,14A duk ƙarshen kowacce shekara bakwai, kowanne mutum dole ya 'yantar da ɗan'uwansa, BaIbrane wanda ya sayar da kansa gare ka ya kuma yi maka bauta na shekaru shida. Ka sake shi ya tafi cikin 'yanci." Amma ubanninku ba su saurare ni ba ko su ba da kunnuwansu gare ni.
15Yanzu ku da kanku kuka tuba ku ka fara ayyukan da ke dai-dai a gabana. Ku ka furta yanci, kowanne mutum ga maƙwabcinsa, kuma ku ka yi alƙawari a gabana a wannan gida da ake kiransa da sunana.16Amma kuka juya ku ka ƙazamtar da sunana; kuka sa kowanne mutum ya dawo da bayinsa maza da mata, waɗanda kuka 'yantar domin su tafi inda ransu ke so. Ku ka tilasta masu su sake zama bayinku.'
17Saboda haka Yahweh ya faɗi wannan, 'Ku da kanku ba ku saurare ni ba. Dama kun furta 'yanci, kowannen ku, zuwa ga 'yan'uwanku da dangi Isra'ilawa. Don haka duba! Ina dab da furta 'yanci gare ku--- wannan furcin Yahweh ne- 'yanci ga takobi, ga annoba, da yunwa, gama zan maishe ku abin tsoro a fuskar kowacce masarauta a duniya.18Sa'an nan zan hori mutanen da suka karya alƙawarina, waɗanda suka ƙi su kiyaye maganganun wannan alƙawari wanda suka ɗauka a gabana a lokacin da suka yanka bajimi kashi biyu suka kuma ratsa tsakanin kason,19daga nan sai shugabannin Yahuda da na Yerusalem, da bãbãnni da kuma firistoci, da kuma dukkan mutanen ƙasar suka ratsa tsakanin bajimin.
20Zan ba da su cikin hannun maƙiyansu da kuma cikin hannun waɗanda suke neman rayukansu. Jikkunansu zasu zama abinci ga tsuntsayen sama da kuma namomin jeji a duniya.21Haka zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda da shugabanninsa cikin hannun makiyansu da kuma cikin hannun waɗanda suke neman ransu, da kuma cikin hannun rundunar sarkin Babila da ya tashi tsaye gãba da ku.22Duba, ina dab da bãda ummarni--- wannan furcin Yahweh ne-- kuma zan dawo da su zuwa ga wannan birni su kuma yaƙe shi su kuma karɓe shi, su kuma ƙona shi. Gama zan juyar da birnin Yahuda zuwa yasassun kufai inda ba za a sami mazauna cikinsa ba."

35

1Maganar da ta zo wurin Irmiya daga wurin Yahweh a kwanakin Yehoiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, cewa,2"Jeka wurin iyalin Rekabawa ka yi magana da su. Sai ka kawo su zuwa gidana, cikin ɗaya daga cikin ɗakunan da ke can, sai ka ba su inabi su sha."

3Sai na ɗauki Ya'azaniya ɗan Irmiya ɗan Habazziniya tare da 'yan'uwansa, dukkan 'ya'yansa, da dukkan iyalin Rekabawa.4Sai na kawo su zuwa gidan Yahweh, zuwa cikin ɗakunan 'ya'yan Hanan ɗan Igdaliya, mutumin Allah. Waɗannan ɗakunansu na kurkusa da ɗakunan shugabanni, wanda ke sama da ɗakin Ma'aseiya ɗan Shallum, mai tsaron ƙofa.
5Sai na ajiye kwanuka da kofuna cike da inabi a gaban Rekabawa na ce masu, "Ku sha inabi."6Amma suka ce, "ba za mu sha inabi ba, gama kakanmu, Yonadab ɗan Rekab, ya umurcemu, 'Kada ku sha kowanne inabi, ko ku ko zuriyarku, har abada.7Kuma, kada ku gina gidaje, ko ku shuka iri, ko ku shuka gonakin inabi; wannan ba na ku ba ne. Gama dole ku zauna cikin bukkoki dukkan kwanakinku, domin ku rayu da kwanaki masu yawa a cikin ƙasar da kuke zaman baƙunci.'
8Mun yi biyayya da muryar Yonadab ɗan Rekab, kakanmu, cikin dukkan abin da ya umurce mu, da kada mu sha inabi a duk kwanakinmu, mu, da matayenmu, da 'ya'yanmu, da kuma 'ya'ya matanmu.9Ba zamu taɓa gina gidaje mu zauna ciki ba, ko mu yi gonar inabi, ko fili, ko mu ajiye iri wurinmu.10Mun daɗe da zama a cikin bukkoki kuma mun yi biyayya mun kuma aiwatar da dukkan abin da Yonadab kakanmu ya umurce mu.11Amma da Nebukadnezza sarkin Babila ya kawo farmaki ga ƙasar, muka ce, 'Zo, dole ne mu je Yerusalem domin mu tsira daga rundunar Kaldiyawa da Aremiyawa.' Shi ya sa mu ke zama a Yerusalem."
12Sai maganar Yahweh ta zo ga Irmiya, cewa,13"Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi haka, 'Ka je ka ce da jama'ar Yahuda da mazauna Yerusalem, "Ba za ku karɓi gyara ku kuma saurari maganata ba?--- wannan shi ne furcin Yahweh.14Maganganun Yonadab ɗan Rekab da ya yi wa 'ya'yansa a matsayin umurni, kada su sha kowanne inabi, an yi la'akari da haka har zuwa yau. Sun yi biyayya da umurnin kakansu. Amma a nawa, Ni da kai na ina ta naciya wurin shaida maku, amma ba ku saurare ni ba.
15Na aika zuwa gare ku dukkan bayina, su annabawa. Na yi naciya da aiken su su ce, 'Bari kowanne mutum ya juyo ga barin muguwar hanyarsa ya kuma aikata ayyuka na gari; kada wani ya sake yin tafiya bisa ga tafarkin wasu alloli ko ya kuma yi masu sujada. A maimakon haka, ku dawo zuwa ga ƙasar da na ba ku da kuma kakanninku.' Duk da haka ku ka ƙi ku saurare ni ko ku bada hankalinku gare ni.16Domin zuriyar Yonadab ɗan Rekab sun kula da umurnin kakansu da ya ba su, amma waɗannan jama'a suka ƙi su saurare ni."
17Sai Yahweh, Allah mai runduna da kuma Allah na Isra'ila, ya faɗi haka, 'Duba, Ina kawo masifa bisa Yahuda da kuma bisa kowanne mai zama cikin Yerusalem, dukkan masifar da na furta game da su domin na yi magana da su, amma ba su saurara ba; Na yi kira gare su, amma ba su amsa ba."'
18Irmiya ya cewa iyalin Rekabawa, "Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, na faɗin haka: Kun saurari umurnan Yonadab kakanku kuka kuma yi biyayya da su dukka- kun yi biyayya da dukkan abin da ya dokace ku ku yi-19sai Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan, 'A kullum za a sami wani daga zuriyar Yonadab ɗan Rekab da zai bauta mani."'

36

1Sai ya kasance a cikin shekara ta huɗu ta Yehoyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, da wannan maganar ta zo ga Irmiya daga Yahweh, ya kuma ce,2"Ka ɗaukar wa kanka naɗaɗɗen littafi ka rubuta dukkan maganar da na faɗa maka game da Is'raila da Yahuda, da kowacce al'umma. Ka yi haka da duk abin da na faɗa tun daga zamanin Yosiya har zuwa yau.3Watakila jama'ar Yahuda za su saurara da dukkan masifar da na yi niyyar kawo wa bisan su. Watakila kowanne zai juyo daga barin muguwar hanyarsa, da haka zan gafarta kurakuransu da zunubansu."

4Sai Irmiya ya kira Baruk ɗan Neriya, sai kuma Baruk ya yi rubutu cikin naɗadɗen littafi, sa'ada da Irmiya ya ke magana, dukkan maganganun Yahweh da aka faɗa masa.5Bayan wannan Irmiya ya bada umurni ga Baruk. Ya ce, "Ina cikin kurkuku kuma ba zan iya zuwa gidan Yahweh ba.6Saboda haka sai ka tafi ka karanta daga cikin naɗaɗɗen littafin da ka rubuta daga maganar da na faɗa. A ranar azumi, dole ne ka karanta maganganun Yahweh jama'a suna sauraro cikin gidansa, haka kuma a cikin kunnuwan dukkan Yahuda waɗanda suka fito daga birane. Furta waɗannan maganganu a gare su.
7Wataƙila roƙonsu na jinkai kai zuwa ga Yahweh. Wataƙila kowannen su zai juyo daga muguwar hanyarsa, da yake fushi da hasalar da Yahweh ya furta game waɗannan mutane masu zafi ne."8Sai Baruk ɗan Neriya ya aiwatar da dukkan abin da Irmiya annabi ya doka ce shi ya yi. Ya karanta maganganun Yahweh da babbar murya a cikin gidan Yahweh.
9Sai ya zama kuma a cikin shekara ta biyar ga watan tara na Yehoiyakim ɗan Yosiya, sarkin Yahuda, sai dukkan jama'ar Yerusalem da kuma mutanen da suka zo Yerusalem daga biranen Yahuda suka yi shelar azumi don girmama Yahweh.10Sai Baruk ya karanta maganganun Irmiya da ƙarfi a cikin gidan Yahweh, daga cikin ɗakin Gemariya ɗan Shafan marubuci, a cikin harabar da ke bisa, dab da mashigin ƙofa ta gidan Yahweh. Ya yi wannan a kunnuwan dukkan jama'a.
11Yanzu Mikaiya ɗan Gemaraya ɗan Shafan ya ji dukkan maganganun Yahweh daga cikin naɗaɗɗen littafi.12Ya gangara zuwa gidan sarki, zuwa ga ɗakin sakatare. Duba, dukkan shugabanni na nan zaune: Elishama sakatare, da Delaya ɗan Shemaya, da Elnatan ɗan Akbor, da Gemaraya ɗan Shafan, da kuma Zedekiya ɗan Hananiya, da dukkan shugabanni.
13Sai Mikaiya ya kawo masu rahoton dukkan maganganun da ya ji Baruk ya karanta da ƙarfi jama'a suna saurare.14Sai dukkan shugabanni suka aiki Yehudi ɗan Netanaya ɗan Shelemaya ɗan Kushi, zuwa ga Baruk. Yehudi ya ce wa Baruk, "Ɗauki naɗaɗɗen littafin cikin hannunka, naɗaɗɗen littafin da ka karanta ga sauraron jama'a, ka kuma zo." Sai Baruk ɗan Neraya ya ɗauki naɗaɗɗen littafin cikin hannunsa ya tafi wurin shugabannin.15Sai suka ce masa, "Zauna ka kuma karanta muna jinka." Sai Baruk ya karanta naɗaɗɗen littafin.
16Sai ya zama sa'ad da suka ji dukkan waɗannan maganganu, kowanne mutum ya juya yana kallon na kusa da shi cikin tsoro suka ce wa Baruk, "Dole ne mu kai rohoton dukkan waɗannan maganganu ga sarki."17Sai su ka tambayi Baruk, "Gaya mana, ta yaya ka rubuta dukkan waɗannan maganganu daga bakin Irmiya?18Baruk ya ce masu, "Ya furta dukkan maganganun gare ni, ni kuma na rubuta su da tawada cikin wannan naɗaɗɗen littafi."19Sai shugabannin su ka cewa Baruk, "Ka tafi, ka ɓoye kanka, da Irmiya, kuma. Kada ka bar wani ya san inda ku ke."
20Sai su ka ajiye naɗaɗɗen littafin a cikin ɗakin Elishama sakatare, kuma suka tafi wurin sarki cikin haraba suka kuma faɗawa sarki komai.21Sa'annan sarki ya aiki Yehudi ya kawo naɗaɗɗen littafin. Yehudi ya ɗauko shi daga ɗakin Elishama sakatare. Sa'annan ya karanta wa sarki da dukkan shugabanni da suke tsayawa kusa da shi.22Yanzu sarki na zama a gida lokacin hunturu a cikin wata na tara, kuma wutar kasko na ci a gaban shi.
23Ya zama kuwa da Yehudi ya karanta shafi uku ko huɗu, sarkin za ya datse su da wuƙa ya jefa cikin wuta cikin kaskon wuta har dukkan naɗaɗɗen littafin ya ƙare.24Amma babu wani ko sarki ko wani daga cikin bayinsa da ya ji dukkan waɗannan maganganun ya kuma tsorata, basu kuma yayyage tufafinsu ba.
25Elnatan, da Delaya, da kuma Gemariya sun riga sun roƙi sarki da kada ya ƙona naɗaɗɗen littafin, amma ya ƙi ya sauraren su.26Sai sarkin ya umarci Yeramil, na dangi, da Seraya ɗan Aziriyel, da kuma Shelemiya ɗan Abdil domin su damƙe Baruk sakatare da kuma Irmiya annabi, amma Yahweh ya riga ya ɓoye su.
27Sai maganar Yahweh ta zo wa Irmiya bayan sarki ya ƙona naɗaɗɗen littafin da kuma maganganun da Baruk ya rubuta daga furcin bakin Irmiya, cewa,28"Ka koma, ka ɗaukar wa kanka wani naɗaɗɗen littafi, ka kuma rubuta cikin sa dukkan maganganun da suke a cikin naɗaɗɗen littafin na farko, wanda Yehoyakim sarkin Yahuda ya ƙona.29Sa'annan dole ka faɗi wannan ga Yehoyakim sarkin Yahuda: 'Ka ƙona wannan naɗaɗɗen littafi, kana cewa, 'Don me ka yi rubutu a cikinsa, 'Sarkin Babila lallai zai zo ya hallakar da wannan ƙasar, gama za ya hallakar da mutum da kuma dabba a cikinta'?""'
30Saboda haka Yahweh ya faɗi wannan game da kai, Yehoiyakim sarkin Yahuda: "Babu zuriyarka da za ta taɓa zama a kan kursiyin Dauda. Game da kai, gawarka za a jefa ta a waje cikin zafin rana da kuma cikin sanyin dare.31Gama zan yi maka horo, da zuriyarka, da kuma bayinka domin kurakuranku duka. Zan kawo a bisanka, da bisan dukkan mazamnan Yerusalem, da kuma a bisa kowanne mutum cikin Yahuda dukkan masifun da na tsoratar daku da su, amma baku ba da hankali ga wannan ba."
32Sai Irmiya ya ɗauko wani naɗaɗɗen littafi ya kuma miƙa shi ga Baruk ɗan Neriya marubuci. Baruk ya rubuta ciki daga bakin Irmiya dukkan maganganun da suka kasance a cikin naɗaɗɗen littafin da Yehoyakim sarkin Yahuda ya ƙona. Bugu da ƙari kuma, aka ƙara maganganu da yawa makamantan waɗannan cikin wannan naɗaɗɗen littafin.

37

1Yanzu Zedekiya ɗan Yosiya ya yi sarauta a madadin Yehoiyacin ɗan Yehoyakim. Nebukadnezza sarkin Babila ya naɗa Zedekiya sarki bisa ƙasar Yahuda.2Amma Zedekiya, da bayinsa, da mutanen ƙasa ba su saurari maganganun Yahweh da ya furta ta hannun Irmiya annabi ba.

3Sai sarki Zedekiya, da Yehukal ɗan Shelemiya, da kuma Zefanaya ɗan Maseya firist ya aika saƙo zuwa ga Irmiya annabi. Su ka ce, "Yi addu'a a madadinmu ga Yahweh Allahnmu."4Yanzu Irmiya na shigowa da fitowa a cikin mutanen, gama ba a rigaya an saka shi cikin kurkuku ba.5Rundunar Fir'auna suka fito daga Masar, sai kuma Kaldiyawa waɗanda suke kafa wa Yerusalem sansani suka ji labari game da su sai kuma su ka bar Yerusalem.
6Sai maganar Yahweh ta zo ga Irmiya annabi, cewa,7"Yahweh, Allahn Isra'ila, ya faɗi wannan: Ga abin da za ka faɗi wa sarkin Yahuda, domin ya aike ka neman shawara wurina, 'Duba, rundunar Fir'auna, wacce ta kawo maku taimako, tana dab da komawa Masar, ƙasarta.8Su Kaldiyawa za su dawo. Za su yaƙi wannan birni, su karɓe shi, su kuma ƙona shi.'
9Yahweh ya faɗi wannan: Kada ku ruɗi kanku kuna cewa, 'Hakika Kaldiyawan na tafiya suna barin mu,' domin ba za su tafi ba.10Ko da ace kun ci dukkan rundunar Kaldiyawan da yaƙi da ke yaƙi da ku da har ace raunannun mutane ne aka bari cikin runfunansu, za su tashi sama su kuma ƙone wannan birnin."
11Haka ya zama lokacin da rundunan Kaldiyawa su ka bar Yerusalem lokacin da rundunar Fir'auna ke gabatowa,12sai Irmiya ya fito Yerusalem domin ya tafi kasar Beyamin. Ya bukaci ya mallaki wani ɗan fili a nan a tsakanin mutanensa.13Sa'ad da ya ke a bakin ‌Ƙ‌ofar Benyamin, wani shugaban matsara na wurin. Sunansa Iriya ɗan Hananiya. Ya riƙe annanbi Irmiya gama kuma ya ce, "Kana zanzarewa zuwa ga Kaldiyawa."
14Amma Irmiya ya ce, "Wannan ba gaskiya ba ne. Ba zanzarewa na ke yi ba zuwa ga Kaldiyawa." Amma Iriya ya ƙi ya saurare shi. Ya ɗauki Irmiya ya kawo shi wurin shugabanni.15Shugabannin suka ji haushin Irmiya. Suka yi ma sa duka suka sa shi cikin kurkuku, wanda ya ke cikin gidan Yonatan marubuci, gama sun maishe shi kurkuku.
16Sai aka sa ka Irmiya cikin kurkuku na ƙarƙashin ƙasa, inda ya zauna ranaku da yawa.17Sai sarki Zedekiya ya aika da wani wanda ya kawo shi zuwa ga fada. A gidansa, sarkin ya tambaye shi a asirce, "Akwai wata magana daga Yahweh?" Irmiya ya amsa, "Akwai magana: Za a miƙa ka cikin hannun sarkin Babila."
18Sai Irmiya ya ce wa sarki Zedekiya, "Ta yaya na yi maka zunubi, ko bayinka, ko waɗannan mutane da har ka saka ni cikin kurkuku?19Ina annabawanka, waɗanda suka yi maka anabci kuma suka ce sarkin Babila ba zai zo gãba da kai ko gãba da wannan birnin ba?20Amma ka saurara yanzu, shugabana sarki! Bari roƙona shi zo gare ka. Kada ka maida ni zuwa ga gidan Yonatan marubuci, don kada in mutu a can."
21Sai sarki Zedekiya ya ba da umarni. Bayinsa suka tsare Irmiya cikin harabar matsara. Aka ba shi curin gurasa kowace rana daga layin matoya, har sai da dukkan gurasar ta ƙare cikin birnin. Haka Irmiya ya zauna cikin harabar matsaran.

38

1Shefatiya ɗan Matan, da Gedaliya ɗan Fashhur, da Yehukal ɗan Shelemiya, da kuma Fashhur ɗan Malkiyah su ka ji maganganun da Irmiya ya ke furtawa ga dukkan mutanen. Yana cewa,2"Yahweh ya faɗi haka: Duk mai zama cikin wannan birni za a kashe shi da takobi, da yunwa, da kuma annoba. Amma kowanne da ya fita zuwa ga Kaldiyawa za shi rayu. Zai tsira da ransa, shi rayu.3Yahweh ya faɗi wannan: Wannan birni za a ba da shi ga hannun rundunar sarkin Babila, kuma za ya karɓe shi."

4Sai shugabannin suka ce wa sarkin, "Bari wannan mutum shi mutu, gama ta wannan hanya yana raunanar da hannuwan mazaje mayaƙa waɗanda suka rage a wannan birni, da kuma hannun dukkan mutane. Ya na furta waɗannan maganganu, gama wannan mutum bai kula da lafiyar waɗannan mutane ba, sai dai bala'i."5Sai sarki Zedekiya ya ce, "Duba, yana cikin hannunku da shi ke babu sarkin da ya isa shi yi tsayayya da ku."
6Sai su ka ɗauki Irmiya su ka jefa shi cikin ramin Malkiyah, ɗan sarki. Ramin na cikin harabar masu tsaro. Suka zurara Irmiya ƙasa da igiyoyi. Babu ruwa cikin ramin, amma taɓo ne, sai kuma ya nutse ƙasa cikin taɓon.
7Yanzu Ebed Melek Ba-Kushi yana cikin ubanni na gidan sarki. Ya ji cewa an jefa Irmiya cikin rami. Yanzu sarkin yana zama a Kofar Benyamin.8Sai Ebed Melek ya tafi daga gidan sarki ya yi magana da sarki. Ya ce,9"Shugabana sarki, waɗannan mutane sun aikata mugunta ta yadda suka yi da Irmiya annabi. Sun jefar da shi cikin rami domin ya mutu cikinsa da yunwa, tun da babu wani abincin da ya rage cikin birnin."
10Sai sarkin ya bada umurni ga Ebed Melek Ba-Kushe. Ya ce, "Ka ɗauki shugabancin mutane talatin daga nan ka kuma ciro annabi Irmiya daga ramin kamin ya mutu."11Sai Ebed Melek ya ɗauki shugaban waɗannan mutanen ya tafi gidan sarki, zuwa ga ɗakin ajiyar kaya na ƙarƙashin gidan. Daga nan ne ya ɗauko tsummokara da kuma koɗaɗɗun kaya sai kuma ya zurara su da igiyoyi ga Irmiya cikin ramin.
12Ebed Melek mutumin Kush ya cewa Irmiya, "Sanya tsummokaran da koɗaɗɗun kayan a ƙarƙashin hannunka da kuma bisa igiyoyin." Irmiya kuwa ya yi haka.13Sai suka jawo Irmiya da igiyoyin. Da haka suka fito da shi daga cikin ramin. Irmiya kuma ya zauna cikin harabar masu tsaro.
14Sai sarki Zedekiya ya aika magana ya kuma kawo Irmiya annabi wurin sa, zuwa cikin mashigi na uku cikin gidan Yahweh. Sarkin ya cewa Irmiya, "Ina so in tambaye ka wani abu. kada ka hana mani amsar."15Irmiya ya ce da Zedekiya, "Idan na amsa maka, lallai ba za ka kashe ni ba? Amma idan na ba ka shawara, ba za ka saurare ni ba."16Amma sarki Zedekiya ya rantse wa Irmiya a asirce ya kuma ce, "Na rantse ga Yahweh mai rai, wanda ya yi mu, ba zan kashe ka ba ko in miƙa ka cikin hannuwan waɗannan mutanen nan da suke neman ranka ba."
17Sai Irmiya annabi ya cewa sarki Zedekiya, "Yahweh, Allah mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi haka: Idan ka fita zuwa ga shugabannin Babila za ka rayu kuma ba za a kone wannan birni ba. Kai da iyalin ka za ku rayu.18Amma idan ka ƙi fita zuwa ga shugabannin sarkin Babila, to za a miƙa wannan birnin cikin hannun Kaldiyawa. Za su kona shi, kai kuma ba za ka tsira daga hannun su ba."
19Sarki Zedekiya ya cewa Irmiya, "Amma ina jin tsoron mutanen Yahuda waɗanda suka ƙaurace zuwa ga sansanin Kaldiyawa domin ana iya miƙa ni cikin hannuwansu, domin su wulaƙanta ni sosai."
20Irmiya ya ce, "Ba zasu miƙa ka cikin hannuwansu ba. Kai dai ka yi biyayya da saƙon Yahweh da nake faɗa maka, domin komai ya zamar maka lafiya lau, domin kuma ka rayu.21Amma idan ka ƙi ka fita, wannan shi ne abin da Yahweh ya nuna mani.
22Duba! Dukkan matayen da aka rage a gidanka, sarkin Yahuda, za a fito da su zuwa ga shugabannin sarkin Babila. Waɗannan matayen za su ce maka, 'Abokananka sun ruɗe ka; sun rusar da kai. ‌Ƙafafunka yanzu sun nutse cikin taɓo, kuma abokanka za su gudu.'23Gama dukkan matayen ko da 'ya'yanka ma za a fito da su zuwa ga Kaldiyawa, kai kuma da kanka ba za ka tsira daga hannunsu ba. Za a kama ka ta hannun sarkin Babila, kuma za a ƙona wannan birnin."
24Sai Zedekiya ya cewa Irmiya, "Kada ka sanar da kowa game da wannan maganganu, don kada ka mutu.25Idan shugabannin suka ji labari na yi magana da kai, idan kuma suka zo su ka ce maka, "Ka faɗi mana abin da ka faɗi wa sarki kuma kada ka ɓoye mana, ko mu kashe ka,26sa'annan dole za ka amsa masu da cewa, na yi roƙo ne da zuciya ɗaya ga sarki da kada ya komar da ni gidan Yonatan don kada in mutu a can."
27Sai dukkan shugabannin suka zo wurin Irmiya suka tambaye shi abin da ya gaya wa sarki, shi kuma sai ya amsa masu yadda sarki ya umarce shi da ya faɗi. Sai suka daina magana da shi, domin ba su ji tattaunawar da aka yi tsakanin Irmiya da sarkin ba.28Sai Irmiya ya zauna a cikin harabar masu tsaro har zuwa ranar da aka karɓe Yerusalem.

39

1A shekara ta tara na watan goma na Zedekiya sarkin Yahuda, Nebukadnezza sarkin Babila ya zo da dukkan rundunarsa gãba da Yerusalem ya kuma kafa mata sansani.2A shekara ta sha ɗaya da kuma wata na huɗu na Zedekiya, a rana ta tara ga wata, aka rusar da birnin.3Sai dukkan shugabannin sarkin Babila suka zo suka zauna a ƙofa ta tsakiya: Nagal Shareza, da Samgar Samgal Nebo, da kuma Sarsekim, shugaba mai muhimmanci. Nagal Shareza shugaba ne babba kuma dukkan sauran sun zama shugabannin sarkin Babila.

4Sai ya zamana da Zedekiya sarkin Yahuda, da dukkan mayaƙan sa suka gan su, suka gudu. Suka fita da dare daga birnin ta hanyar gonar gidan sarki, ta cikin ƙofa ta tsakanin ganuwa biyun. Sarkin ya fita ta bangon hanyar Araba.5Amma rundunar Kaldiyawa suka runtume su suka kuma cimma Zedekiya a cikin filin Kogin Yodan kwari kusa da Yeriko. Sai suka cafko shi suka kawo shi wurin Nebukadnezza, sarkin Babila, a Ribla cikin ƙasar Hamat, inda Nebukadnezza ya yanke masa hukunci.
6Sarkin Babila ya kashe 'ya'yan Zedekiya a fuskarsa a Ribla. Ya kuma kashe dukkan muhimman mutanen Yahuda.7Sai ya cire idanuwan Zedekiya ya kuma ɗaure shi da sarƙoƙin jan karfe domin ya tafi da shi Babila.
8Sai Kaldiyawan suka ƙone gidan sarki da gidajen mutane. Suka kuma rushe ganuwar Yerusalem.9Nebuzaradan, hafsan masu tsaron sarki, ya kwashe sauran mutanen waɗanda aka rage cikin birnin zuwa bauta. Wannan ya haɗa har da waɗanda suka yi ƙaura zuwa ga Kaldiyawa da kuma sauran mutanen waɗanda aka rage cikin birnin.10Amma Nebuzaradan babban hafsan masu tsaron sarki ya bar sauran mutanen waɗanda suke fakirai waɗanda basu da wani abu na kansu su zauna a cikin Yahuda. Ya kuma ba su gonakin inabi da filaye a wannan rana.
11Nebukadnezza sarkin Babila ya ba da umarni game da Irmiya ga Nebuzaradan hafsan masu tsaron sarki. Ya riga ya ce,12"Ka ɗauke shi ka kula da shi. Kada ka ji ma sa rauni. Yi ma sa duk abin da ya ce ma ka.13Sai Nebuzaradan hafsan masu tsaron sarki, Nebushazban babban bãbãn, Nagal Shareza babban shugaba, da dukkan muhimman shugabannin sarkin Babila su ka aiki mutane waje.14Mutanensu su ka ɗauki Irmiya daga harabar masu tsaro su ka miƙa shi cikin hannun Gedaliya ɗan Ahikam ɗan Shafan, ya kai shi gida, sai Irmiya ya zauna a tsakanin mutanen.
15Yanzu dai maganar Yahweh ta zo ga Irmiya tun ya na a tsare a cikin harabar masu tsaro, cewa,16"Yi magana da Ebed Melek mutumin Kush ka ce, "Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: Duba, ina dab da cika maganganuna da na furta game da wannan birni bala'i kuma ba alheri ba. Gama za su faru dukka a idanunka a wannan rana.
17Amma zan cece ka a wannan rana- wannan ne furcin Yahweh- kuma ba za a bashe ka cikin hannun mutanen da ka ke jin tsoronsu ba.18Gama babu shakka zan tsirar da kai. Ba za ka faɗi ga takobi ba. Za ka tsira da ranka, tun da ka yarda da ni- wannan shi ne furcin Yahweh."

40

1Maganar ta zo wurin Irmiya daga wurin Yahweh bayan da Nebuzaradan babban hafsan masu tsaron sarki ya sa ke shi a Rama. Ya sami Irmiya a ɗaure da sarƙoƙi a tsakiyar dukkan 'yan sarƙar Yerusalem da Yahuda waɗanda aka kwashe zuwa ga ƙasar bauta a Babila.2Shugaban matsara ya ɗauki Irmiya ya kuma ce ma sa, "Yahweh Allahnka ya umarta wannan masifar domin wannan wurin.

3Don haka Yahweh ya kawo hakan. Ya aikata kamar yadda ya umarta, tun da ku mutanen nan kun yi ma sa zunubi kuma ba ku yi biyayya da muryar sa ba. Shi ya sa wannan abu ya faru da ku mutanen nan.4Amma yanzu duba! Na sa ke ka yau daga sarƙokin da ke hannuwanka. Idan ka ga ya dace a idanunka ka bi ni zuwa Babila, sai ka bi ni, ni kuwa zan kula da kai. Amma idan ba ya dace a idanunka ba da ka biyo ni zuwa Babila, to kada ka yi haka. Duba dukkan ƙasar da ke a gabanka. Ka tafi duk inda ya ke da kyau da kuma dai - dai a idanunka ka tafi."
5Da Irmiya ba ya amsa ba, Nebuzaradan ya ce, "Tafi wurin Gedaliya ɗan Ahikam ɗan Shafan, wanda sarkin Babila ya ɗora wa haƙin kula da biranen Yahuda. Ka zauna da shi a tare da sauran mutanen ko ka tafi ko inda da ya yi ma ka kyau a idanunka ka tafi." Sai hafsan masu tsaron sarki ya bashi abinci da 'yar kyauta, daga nan ya sallame shi.6Sai Irmiya ya tafi wurin Gedaliya ɗan Ahikam, a Mizfa. Ya zauna tare da shi a tsakiyar mutanen da aka bari cikin kasar.
7Yanzu wa su hafsoshin Yahuda waɗanda har yanzu su na a cikin harabar-- su da mutanensu-- su ka ji cewa sarkin Babila ya ɗora Gedaliya ɗan Ahikam, gwamna bisa ƙasar. Sun kuma sa ke ji cewa ya sa shi a matsayin mai kula da mazajen, mataye, da yara waɗanda su ne fakiran mutane a cikin ƙasar, waɗanda ba a kwashe ga hijira zuwa ƙasar Babila ba.8Sai su ka tafi wurin Gedaliya a Mizfa. Waɗannan mutane su ne Ishmayel ɗan Netaniya; Yohanan da Yonatan, 'ya'yan Kariya; da Seraya ɗan Tanhumet; su 'ya'yan Ifai mutumin Netofatiyawa; da Ya'azaniya ɗan Ma'akatiyawa-- su da mutanensu.
9Gedaliya ɗan Ahikam ɗan Shafan ya ɗauki alƙawari da su da 'ya'yansu ya ce masu, "Ka da ku ji tsoro da za ku bauta wa shugabannin Kaldiyawa. Ku zauna a cikin ƙasar ku kuma bauta wa sarkin Babila, da haka komai zai yi maku dai - dai.10Duba, ina zama a Mizfa domin in sami ganin Kaldiyawa da su ka zo gare mu. Sai ku girbe inabi, da kayan itatuwa na damuna, da kuma mai ku adana su a cikin dururruka. Ku zauna a biranen da ku ka mallaka."
11Sai dukkan mutanen Yahuda da ke a Mowab, a tsakanin mutanen Ammon, da kuma cikin Idom, da kuma a kowacce ƙasa su ka ji cewa sarkin Babila ya bar ragowar Yahuda su zauna, har ya aza Gedaliya ɗan Ahikam ɗan Shafan bisan su.12Saboda haka dukkan mutanen Yahuda su ka dawo daga dukkan wuraren da aka tarwatsa su. Su ka dawo zuwa ga ƙasar Yahuda, zuwa ga Gedaliya a Mizfa. Su ka girbe inabi da amfanin itatuwa na damina mai yawan gaske.
13Yohanan ɗan Kareya da dukkan shugabannin rundunar da su ke baje cikin ƙasar su ka zo wurin Gedaliya a Mizfa.14Su ka ce ma sa, "Ko ka sa ni da cewa Balis sarkin mutanen Ammon ya aiko Ishmel ɗan Netaniya da ya kashe ka?" Amma Gedaliya ɗan Ahikim bai yarda da su ba.
15Sai Yohanan ɗan Kareya ya yi magana a asirce da Gedaliya a Mizfa kuma ya ce, "Ka bar ni in tafi in kashe Ismayel ɗan Netaniya. Babu wanda zai sani. Don me za shi kashe ka? Don me za a bar Yahuda da aka tara maka su wartwatsu kuma ragowar Yahuda su hallaka?16Amma Gedaliya ɗan Ahikam ya ce wa Yohanan ɗan Kareya, "Kada ka aikata wannan abu, gama ka na faɗin ƙarya ne bisa Ismayel."

41

1Amma ya kasance a wata na bakwai Ismayel ɗan Netaniya ɗan Elishama, daga gidan sarauta, da waɗansu shugabanni na sarki, su ka zo su goma tare da shi wurin Gedaliya ɗan Ahikam, Mizfa. Su ka ci abinci tare a can Mizfa.2Amma Ismayel ɗan Netaniya da mutanen nan goma da ke tare da shi su ka tashi suka farmaki Gedaliya ɗan Ahikam ɗan Shafan da takobi. Ismayel ya kashe Gedaliya, wanda sarkin Babila ya sa ya mulki ƙasar.3Daga nan sai Ismayel ya kashe dukkan mutanen Yahudiya da ke goyon bayan Gedaliya a Mizfa da mayaƙan Kaldiyawan da ya samu a can.

4To a rana ta biyu bayan kisan Gedaliya, amma ba wanda ya sani.5Waɗansu mutane su ka zo daga Shekem, da kuma Shilo, da Samariya su tamanin waɗanda su ka aske gemunsu, su ka kuma kece tufafinsu, su ka yayyanka jikkunansu - ɗauke da baye - baye na abinci da turaren itacen lubban a hannuwansu don su je gidan Yahweh.
6Sai Ismayel ɗan Netaniya ya tafi daga Mizfa don ya sadu da su akan hanyarsu ta komawa, suna tafe su na kuka. A lokacin da ya gansu sai ya ce da su, "Ku zo wurin Gedaliya ɗan Ahikam!"7Sai ya zamana bayan sun zo birnin, sai Ismayel ɗan Netaliya ya yayyanka su ya zura su cikin rami, tare da mutanen da ke tare da shi.
8Amma akwai mutane goma daga cikinsu da su ka ce da Ismayel," kada ka kashe mu, don muna da tanaji a filin: da alkama, da sha'ir da mai da ruwan zuma." Don haka bai kashe su tare da abokan tafiyarsu ba.9Rijiyar da Ismayel ya zuba gawawwakin waɗanda ya kashe ta na da girma ita ce rijiyar da sarki Asa ya haƙa don kariya daga sarkin Ba'asha na Isra'ila. sai Ismayel ɗan Netaniya ya cikata da gawawwaki.
10Abu na gaba shi ne Ismayel ya kame dukkan mutanen da ke a Mizfa, da 'ya'yan sarki 'yan mata da duk sauran mutanen da su ka ragu a Mizfa waɗanda Nebuzzradan shugaban masu tsaro ya ba Gedaliya ɗan Ahikam. To sai Ismayel ɗan Netaniya ya kame su ya tafi ya ƙetare da suzuwa wurin mutanen Ammon.
11Amma Yohannan ɗan Kareya da dukkan hafsoshin da ke tare da shi suka ji dukkan muguntar da Ismayel ɗan Netaniya ya yi.12To sai su ka kwashi dukkan mutane don su yaƙi Ismayel ɗan Netaniya. su ka same shi a babban kwarin Gibeyon.
13Sai ya zamana a lokacin da dukkan mutanen da ke tare da Ismayel su ka ga Yohanan ɗan Kareya da dukkan hafsoshin da ke tare da shi, sai suka yi murna.14Sai dukkan mutanen da Ismayel ya kame a mizfa su ka juya suka koma ga Yohannan ɗan Kareya.
15Amma Ismayel ɗan Netaniya ya gudu tare da mutane takwas daga Yohannan. Ya je wurin mutanen Ammon.16Sai Yohannan ɗan Kareya da dukkan hafsoshin da ke tare da shi su ka kwashe mutanen daga Mizfa, suka kuɓutar da su daga Ismayel ɗan Netaniya. Hakan ya faru ne bayan Ismayel ya kashe Gedaliya ɗan Ahikan. Yohannan da abokan tafiyarsa su ka ɗauki ƙarfafan mazaje, da mayaƙa, da mata da yara, da bãbãnni waɗanda aka kuɓutar a Gibeyon.
17Daga nan sai su ka je su ka ɗan tsaya a Gerut Kimham, wanda ke kusa da Betelehem. Su na tafiya don su je Masar18saboda Kaldiyawa. Suna tsoron su tunda yake Ismayel ɗan Netaniya ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wanda sarkin Babila ya sa ya yi mulkin ƙasar.

42

1Daga nan dukkan hafsoshin da Yohanan ɗan Keriya, da Yezaniya ɗan Hoshayiya, da dukkan mutanen tun daga ƙanana ya zuwa manya suka zo wurin annabi Irmiya.2Su ka ce da shi, "bari kukanmu ya zo gareka.3Kayi addu'a zuwa ga Yahweh Allahnka a madadinmu da muka ragu tun da ya ke ba mu da yawa, kamar yadda ka gani. Ka roƙi Yahweh Allahnka ya faɗa mana abin da za mu yi da kuma hanyar da za mu bi"

4Annabi Irmiya ya ce da su, "Na ji ku. Duba, zan yi addu'a ga Yahweh Allahnku kamar yadda ku ka bukata. Kuma duk amsar da Yahweh ya bayar zan faɗa muku. Ba zan ɓoye muku komai ba."5Su ka cewa Irmiya, "Dama Yahweh ya zama amintaccen shaida na gaskiya a tsakaninmu, idan ba mu yi duk abin da Yahweh Allahn ka ya ce mu yi ba.6Ko da mai kyau ne ko kuma mara kyau, za mu yi biyayya da muryar Yahweh Allahnmu, wanda mu ke aiken ka wurinsa, don komai ya yi mana dai - dai a lokacin da muka yi biyayya da muryar Yahweh Allanmu."
7Bayan kwana goma, maganar Yahweh ta zo wurin Irmiya.8Sai Irmiya ya kira Yohanan ɗan Kareya da dukkan hafsoshin da ke tare da shi, da kuma dukkan mutane daga ƙanana zuwa manya.9Sai ya ce da su, "Wannan shi ne abin da Yahweh Allah na Isra'ila - wanda ku ka aike ni wurin sa don in kai roƙonku gare shi - ya ce,10Idan kun koma wannan ƙasar ku ka zauna to zan gina ku ba zan keta ku ba; Zan dasa ku ba zan tuge ku ba, don zan kawar da masifar da na aukar a kan ku.
11Kada ku ji tsoron sarkin Babila, wanda ku ke jin tsoro. Kada ku ji tsoron sa - wannan shi ne abin da yahweh ya furta - da shi ke Ina tare da ku don in cece ku in kuma kuɓutar da ku daga hannunsa.12Gama zan yi maku jinkai. Zan kuma ji tausayinku, zan kuma dawo da ku ƙasarku.
13Amma in kun ce "ba za mu zauna a wannan ƙasa ba" - in ba ku saurari muryata ba, muryar Yahweh Allanku.14In kun ce, "A a! Za mu je ƙasar Masar, inda ba za mu ga wani yaƙi ba, inda ba za mu ji ƙarar ƙaho ba, kuma ba zamu ji yunwa domin abinci ba, can za mu zauna."
15Yanzu sai ku saurari muryar Yahweh, ku da ku ka rage a Yahuda. Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, Ya faɗi wannan, 'In dai har ku ka je Masar, don ku je ku zauna a can,16To takobin da ku ke jin tsoro za ta kashe ku a can ƙasar Masar. Yunwar da ku ke damuwa a kanta yanzu za ta kora ku zuwa Masar, kuma za ku mutu a can.17Don haka duk waɗanda su ka gudu Masar don su zauna a can za su hallaka ta wurin takobi, da yunwa, ko annoba. Kuma ba wanda zai tsira daga wannan masifar da zan aukar masu.
18Domin Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: Kuma kamar yadda fushina ya yi ƙuna a kan mazauna Yeruselem, hakanan zan saukar da matsanancin fushina a kanku in ku ka je Masar. Za ku zama abin la'ana da reni, abin la'antawa, da abin ƙasƙantarwa, kuma ba za ku ƙara ganin wannan wurin ba.'"19Sai Irmiya ya ce,'" Yahweh ya faɗi wannan a kanku - ku da ku ka rage a Yahuda. Kada ku je Masar! Don tabbas kun san ni sheda ne a kanku a yau.
20Domin kun yaudari kanku sosai a lokacin da ku ka aike ni ga Yahweh Allahnku ku ka ce, ka yi addu'a ga Yahweh Allahnmu dominmu. Duk abin da Yahweh Allahnmu ya ce, ka faɗa mana, za mu yi shi.'21Domin yau na ba ku rahoto, amma ba ku saurari muryar Yahweh Allahnku ko kuma duk abin da ya aiko ni wurinku.22To yanzu sai ku san cewa tabbas zaku mutu ta wurin takobi, da yunwa, da annoba, a wurin da kuke son ku tafi ku zauna."

43

1Sai ya zamana bayan Irmiya ya gama shaidawa mutane dukkan maganar Yahweh Allahnsu wadda Yahweh Allahnsu ya faɗi masa ya faɗa.2Azariya ɗan Hosheya, Yohanan ɗan Kareya, da dukkan mutane kangararru su ka ce da Irmiya, '"ƙarya ka ke faɗi. Yahweh Allanhmu bai aiko ka ka faɗi cewa kada ku je Masar ku zauna a can ba'3Domin Baruk ɗan Neriya ya na zuga ka ka bada mu a hannun Kaldiyawa, don kaima ka jawo mana mutuwa ka kuma mai da mu kamammu a Babila."

4Domin haka Yohannan ɗan Kareya, da dukkan shugabannin mayaƙa da dukkan mutane su ka ƙi sauraron muryar Yahweh da ta ce su zauna a Yahuda.5Yohanan ɗan Kareya da shugabannin mayaƙa su ka kwashe dukkan waɗanda su ka rage a Yahuda waɗanda su ka dawo daga dukkan al'uman da aka warwatsa su su zauna a cikin ƙasar Yahuda.6Su ka kwashe maza da mata, da yara da 'ya'ya mata na sarki, da duk wanda Nebuzaradan, hafsan sarki da matsaran sarki, ya sa suka kasance tare da Gedeliya ɗan Ahikam ɗan Shafan. Hakannan su ka ɗauki Annabi Irmiya da Baruk ɗan Neriya.7Su ka tafi zuwa ƙasar Masar, a Tafenhes, saboda ba su saurari muryar Yahweh ba.
8To sai maganar Yahweh ta zo ga Irmiya a Tafanhes, cewa,9"Ka ɗauki manyan duwatsu a hannunka, da kuma a gaban mutanen Yahuda, ka ɓoye su a kankare a gefen hanyar zuwa ƙofar gidan Fir'auna a Tafanhes."10Daga nan sai ka ce da su, Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila ya faɗi wannan, 'Duba ina gab da aika manzannina zuwa Babila a matsayin bayina. Zan kafa mulkinsa akan waɗannan duwatsu wanda kai Irmiya ka binne. Nebukadzza zai kafa daularsa a kansu.
11Domin zai zo ya kawo hari ga ƙasar Masar. Duk wanda aka ƙaddara ga mutuwa zai mutu. Duk wanda aka ƙaddara ga bauta za a ɗauke shi zuwa bauta. Duk wanda aka ƙaddara ga takobi za a bada shi ga takobi.12Daga nan zan kunna wuta a haikalun allolin Masar. Nebukadnezza zai ƙone su ko kuma ya kwashe su. Zai tsarkake ƙasar Masar kamar yadda makiyaya ke tsabtace tufafinsu. Zai fita daga wurin nan da ɗaukaka.13Zai karye ginshiƙan nan na dutse na Heliyofolis a ƙasar Masar. Zai ƙone haikalun allolin Masar.'"

44

1Maganar ta zo ga Irmiya game da dukkan mutanen Yahudiya da ke zaune a ƙasar Masar, waɗanda ke zaune a Migdol, da Tafenhas, da Memfis, da ƙasar Fatros.2Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: Ku da kan ku kun ga duk waɗannan masifu da na aukar a Yeruselem da dukkan biranen Yahuda. Duba, yau sun zama kangaye. Ba wanda zai zauna a cikinsu.3Wannan saboda miyagun abubuwan da su ka yi domin su yi mani laifi ta wurin zuwa su ƙona turare da kuma bautawa waɗansu alloli. Waɗannan alloli ne da ko su da kansu, ko ku, ko kakanninku ba su sani ba.'

4Don haka na dinga aikawa da dukkan bayina annabawa gare su. Na aike su su ce, 'Ku dena aikata abubuwan ban ƙyamar da na ke ƙi.' ba su saurara ba.5Amma sun ƙi saurare. Suka ƙi maida hankali ko su juyo daga muguntarsu ta wurin ƙona turare ga wasu alloli.6Sai razanata da fushina su ka yi ƙuna a kan biranen Yahuda da titunan Yerusalem. Don haka suka zama kango da abin banzatarwa, kamar yadda ya ke a yau'
7To yanzu Yahweh, Allah mai runduna Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan, "Don me ku ke aikata babbar mugunta gãba da kanku? Don me ku ke jawowa kanku abin da zai sa a datse ku daga cikin Yahuda - mazaje da mataye, yara da jarirai? Ba za a rage ko ɗayanku ba.8Ta wurin aikin muguntarku kun yi ma ni laifi ta wurin ayyukan hannuwanku, ta ƙona turare ga waɗansu alloli a ƙasar Masar, inda ku ka je ku zauna. Kun je can ne don a hallaka ku, don ku zama la'antattu da abin reni a cikin dukkan al'umman duniya.
9Kun manta da ayyukan muguntar da kakanninku su ka yi da muguntar da sarakunan Yahuda da matansu su ka yi? Kun manta da muguntar da ku da kanku da matanku ku ka aikata a cikin ƙasar Yahuda da titunan Yerusalem?10Har ya zuwa yau, ba su yi tawa'li'u ba. Ba su girmama shari'una ba ko dokokina da na sanya a gabansu ba, su da kakanninsu, ba su kuma yi tafiya a cikinsu ba.'
11Don haka Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan, "Duba, ina gab da sa fuskata gãba da ku don in kawo muku masifa in kuma hallakar da dukkan Yahuda.12Don zan kwashe sauran mutanen Yahuda waɗanda su ka je Masar su zauna a can. Zan yi wannan don dukkan su su hallaka a ƙasar Masar. Za su faɗi ta wurin takobi da yunwa. Tun daga ƙaraminsu har zuwa babbansu za su faɗi ta wurin takobi da yunwa. Za su mutu su kuma zama abin reni da abin ƙyama.
13Don zan hori mutanen dake zaune a ƙasar Masar kamar yadda na hori mutanen Yeruselem da takobi, da yunwa. da annoba,14yadda ba wani ragowar Yahuda waɗanda su ka tafi su zauna a cikin ƙasar Masar da zai kucce ko ya tsira ko ya dawo ƙasar Yahuda, wadda su ke marmari su dawo su zauna; Ba waninsu da zai dawo, sai dai 'yan kima da su ka kutto a nan.'"
15Daga nan duk waɗanda su ka san matansu na ƙona turare ga waɗansu alloli, da kuma dukkan matayen da ke a babbar taruwa, da dukkan mutanen da ke zaune a ƙasar Masar ta kwari da tudu, a Fatros su ka amsa wa Irmiya.16Su ka ce, "Game da maganar da ka faɗa, mana a cikin sunan Yahweh ba za mu saurare ka ba.17Don hakika za mu yi duk abin da mu ka ce za mu yi - ƙona turare ga sarauniyar sama da zuba baye - baye na sha a gabanta Kamar yadda kakanninmu, da sarakunanmu, da shugabanninmu su ka yi a titunan Yerusalem. Daga nan za mu ƙoshi da abinci mu wadatu, ba tare da fuskantar wata masifa ba.
18Sa'ad da mu ka dena yin waɗannan wato ƙin miƙa baiko ga sarauniyar sama da kuma ƙin miƙa baye - baye na sha a gare ta, duk za mu talauce mu kuma mutu ta wurin takobi da yunwa."19Sai matayen suka ce, "lokacin da mu ke yin baye - baye na turare a gaban sarauniyar sama da zuba baye - baye na sha a gare ta, ashe saɓawa mazanmu muka yi da muka aikata waɗannan abubuwa, yin waina a cikin siffarta da kuma zuba baye - baye na sha gare ta?"
20Daga nan sai Irmiya ya ce da dukkan mutanen -ga maza da mata, kuma dukkan mutanen da su ka amsa masa - ya yi shela ya ce,21"Ashe Yahweh bai tuna da turaren da ku ka ƙona a biranen Yahuda da titunan Yerusalem - ku da kakanninku, da sarakunanku da shugabanninku, da kuma mutanen ƙasar ba? Domin Yahweh ya tuna da wannan; ya fãɗo cikin tunaninsa.
22Daga nan ba zai ƙara jurewa da shi ba saboda miyagun ayyukanku da ku ka yi, saboda ayyukan ban ƙyamar da ku ka aikata. Sai ƙasarku ta zama yassashiya, da abin reni, da la'anta ta zama ba wanda ke zaune a cikinta har ya zuwa yau.23Saboda kun ƙona turare kun kuma yi zunubi ga Yahweh, don kun ƙi sauraron muryarsa, da shari'unsa ba da kuma ƙa'idojinsa ba, ko alƙawaransa ba, da dokokinsa ba shi ya sa wannan masifar ta same ku kamar yadda ya ke a yau."
24Sai Irmiya ya ce da dukkan taron mutanen da kuma dukkan matayen, "Ku ji maganar Yahweh, dukkan mutanen Yahuda da ke ƙasar Masar.25Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila ya faɗi wannan, 'Ku da matayenku duk kun furta da bakinku kun kuma ɗauki duk abin da ku ka ce,"Hakika za mu aiwatar da alƙawuran da mu ka yi cewa za mu yi sujada ga sarauniyar sama, mu kuma zuba baye-baye na sha a gareta." Yanzu sai ku cika alƙawuranku, ku kuma aikatasu.'
26Don haka ku ji maganar Yahweh, ku dukkan mutanen Yahuda da ke a ƙasar Masar, duba na rantse da sunana mai girma - in ji Yahweh. Ba za a sa ke kiran sunana ta bakin wani daga cikin mutanen Yahuda ba a dukkan ƙasar Masar, ku da yanzu ke cewa, "Na rantse da ran Ubangiji Yahweh."27Duba, ina lura da su don in aukar masu da masifa ba abu na gari ba. Duk wani mutumin Yahuda da ke a Masar zai hallaka ta wurin takobi da yunwa har sai dukkan su sun ƙare.28Daga nan sai waɗanda su ka tsira daga takobin su dawo daga ƙasar Masar zuwa ƙasar Yahuda, 'yan kimansu kawai. Da haka dukkan waɗanda su ka ragu a Yahuda da suka je Masar don su zauna a can za su san ko maganar waye zata zama gaskiya - tawa ko tasu.
29Wannan zai zamar maku alama - wannan shi ne furcin Yahweh - da na ke shirya maku a wannan wurin, don ku san cewa maganata tabbas za ta hare ku tare da masifa.'30Yahweh ya faɗi wannan, duba ina gab da in bada Fir'auna Hofra sarkin Masar ga hannun maƙiyansa da kuma hannun masu so su hallaka shi. Zai zama kamar yadda na ba da Zedekiya sarkin Yahuda ga sarki Nebukadnezza sarkin Babila, maƙiyinsa wanda ya biɗi ransa.'"

45

1Wannan ita ce maganar annabi Irmiya da ya faɗawa Baruk ɗan Neriya. Wannan ya faru a lokacin da ya rubuta a cikin naɗaɗɗen littafi wanda Irmiya ya yi masa shifta - wannan ya faru a watan huɗu na sarautar Yahoaikim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, sai ya ce,2Yahweh Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan a gareku, ina faɗa maka wannan Baruk:3Ku ka ce, 'Kaito na, domin Yahweh ya ƙara ƙunci ga raɗaɗina. Da nishe - nishena sun gajiyar da ni; ban sami hutu ba.'

4Wannan shi ne abin da tilas za ka faɗa masa; Dubi abin da na gina, yanzu ina rushewa. Abin da na dasa, yanzu ina tumɓukewa - Zan yi wannan a dukkan duniya.5Amma ko kana begen manyan abubuwa domin kanka? Kada ka yi begen haka. Don duba, masifa za ta aukowa dukkan mutane - wannan furcin Yahweh ne - amma zan ba ka ranka a matsayin ganimarka a duk inda ka je.'"

46

1Wannan ita ce maganar Yahweh da ta zo wurin Irmiya annabi game da al'ummai.2Game da Masar: "Wannan game da sojan Fir'auna Neko ne, sarkin Masar da ke Karkemish a wajan kogin Yuferetis. Wannan shi ne sojan Nebudkadnezza sarkin Babila ya cinye a yaƙi a shekara ta huɗu ta mulkin Yehoyakim ɗan Yosiya, sarkin Yahuda:3A sami ƙananan garkuwoyi da manyan garkuwoyi a shirya su ka fita ka yi yaƙi.4Ka sa linzamin doki; Ka ɗaura sirdi ka kuma sa hular kwano; ka wasa mãshi ka ɗaura kayan yaƙi.

5Me nake gani a nan? sun cika da fargaba suna kuma guduwa, don an yi nasara da sojojinsu. Suna gudu don neman tsira basa kuma waigen baya. Fargaba na ko'ina - wannan shi ne abin da Yahweh ya furta -6masu hanzari baza su iya gudu ba, sojojin kuma ba za su tsira ba. Sun yi tuntuɓe a arewa suka faɗi a gefen Kogin Yuferetis.
7Wane ne wannan da ya tashi kamar Nilu, wanda ruwayensa ke tunbatsa sama da ƙasa kamar koguna?8Masar na tashi kamar Nilu, kamar kogunan da suke tumbatsa sama da ƙasa. Masar ta ce Zan tashi in rufe duniya. Zan hallakar da birane da mazaunansu.9Ku dawakai ku hau sama ku yi fushi, ku karusai. Bari sojoji su fita waje, Kush da Fut, mutanen da ke fasaha da garkuwa, da mutanen Ludim, mutanen da suka shahara a tanƙwara bakkunansu.'
10Wannan ranar zata zama ranar ramako ce ga Ubangiji Yahweh mai runduna, zai kuma sakawa kansa akan magaftansa. Takobi za ta ci ta ƙoshi. zata ƙoshi da jininsu. Don za a yi hadaya ga Yahweh Ubangiji mai runduna a arewacin ƙasar a gefen Kogin Yuferetis.
11Ku je Gileyad ku sami magani, budurwan Masar. A banza kuke sawa kanku magani mai yawa. Ba za ku warke ba.12Al'ummai sun ji labarin kunyarku. Duniya ta cika da makokinku, don sojoji suna tuntuɓe da juna, dukkansu su ka fãɗi tare."
13Wannan ita ce maganar da Yahweh ya faɗawa annabi Irmiya bayan Nebukadnezza sarkin Babila ya kawo wa Masar hari:14"Ka sanar a Masar, ka kuma yi shela a Migdol, da Memfis, da Tafanhes. Ku sami wurinku ku shirya kanku, don takobi zai haɗiye waɗanda ke kewaye da ku.'
15Don me jarumawanki fuskarsu a sunkuye ƙasa? Ba za su tsaya ba, saboda Ni, Yahweh, na ture su ƙasa.16Ya ƙara yawan waɗanda su ka yi tuntuɓe. Kowanne soja ya fãɗi kusa da ɗan uwansa. Su na cewa, 'Ku tashi. Bari mu tafi gida. Bari mu koma wurin mutanenmu, zuwa ainahin ƙasarmu. Bari mu bar wannan takobin da ya ke doddoke mu ƙasa.'17Su ka yi shela a can, 'Fir'auna sarkin Masar mai kwakazo ne kawai, wanda ya bar zarafinsa ya sille.'
18Na rantse da zatina inji Sarki, wanda sunansa shi ne Yahweh mai runduna - wani zai zo mai kama da Dutsen Tabor da Dutsen Karmel na bakin teku.19Ku kwaso wa kanku jakkuna don za ku tafi hijira, ku da ku ke zaune a Masar. Domin Memfis zata zama wofi, zata zama kango, ba kuma wanda zai zauna a can.
20Masar kyakkyawar maraƙa ce, amma ƙwaro mai harbi na zuwa daga arewa. Yana zuwa.21Sojojin hayar da ke cikinta kamar bijimi mai ƙiba suke, amma su ma za su juya su gudu. Ba za su iya tsayuwa tare ba, don ranar masifarsu na zuwa gãba da su, lokacin horonsu ne.22Masar ta fito kamar maciji tana kuma rarrafawa, don maƙiyanta suna tattaki gãba da ita. Suna tunkararta kamar masu yankan katako da gatura.
23Za su sassare dazuzzuka - wannan shi ne abin da Yahweh ya furta-duk da yake abin ya na da ban razana. Domin magabta za su zama da yawa sosai fiye da fara ba za su ƙidayu ba.24Za a kunyatar da Masar. Za a miƙa ta ga hannun mutane daga arewa."
25Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya ce, "Duba, ina gab da in hori Amon na Tebes, da Fir'auna, da Masar da allolinta, da sarakunanta wato masu mulkinta, da masu dogara da su.26Zan miƙa su ga wanda ke neman rayukansu, da kuma hannun Nebukadnezza sarkin Babila da bayinsa. Daga nan bayan wannan za a sake zama a Masar kamar a kwanakinta na can baya - wannan furcin Yahweh ne
27Amma kai, bawana Yakubu, kada ka ji tsoro. Kada ka razana, Isra'ila, don duba, Ina gab da in komo da ku daga manisanta wurare, zuriyarku kuma daga ƙasar bautarsu. Daga nan sai Yakubu ya dawo, ya sami salama, ya kuma sami tsaro, kuma ba sauran wanda zai razana shi.28Kai, bawana Yakubu, kada ka ji tsoro - wannan shi ne furcin Yahweh - don ina tare da kai, kuma zan halakar da dukkan al'ummai a inda na warwatsa ku. Amma ba zan hallaka ku dukka ba. Duk da haka zan hore ku da adalci hakika ba zan bar ku ba horo ba."

47

1Wannan ita ce maganar Yahweh da ta zo ga annabi Irmiya game da Filistiyawa. Wannan maganar ta zo gare shi kafin Fir'auna ya kai wa Gaza hari.2Yahweh ya faɗi wannan: Duba, tunbatsar ruwa na tasowa daga arewa. Zai zama kamar ambaliyar koguna! Daga nan za su share ƙasar da duk abin da ke cikinta, da biranenta da mazaunanta! Saboda haka kowa zai yi kukan neman taimako, kuma dukkan mazaunan ƙasar za su yi makoki.

3Da jin motsin sawayen ƙarfafan dawakansu 'kofatansu na ruri akan karusansu da kuma ƙarar gargarensu, ubanni ba za su taimaki 'ya'yansu ba saboda rashin ƙarfinsu.4Domin rana na zuwa da zata warwatsa dukkan Filistiyawa, ta datse daga Taya da kuma Sidom da kuma daga duk wanda ya tsira ya ke kuma so ya taimake su. Don Yahweh yana warwatsa Filistiyawa, waɗanda su ka ragu a tsibirin Kafto.
5Saiƙo zai aukawa Gaza. Ashkelon kuma mutanen da aka bari a kwarurrukansu za a sa su su yi shiru. Makokinku zai kai wanne lokaci?6Kaito, takobin Yahweh! Har yaushe za ta kasance har sai kun yi shiru? Ku koma ga watsewarku! Ku dena ku yi shiru.7Ta yaya zai huta, sa'ad da Yahweh ya umarce shi. Sa'ad da ya umarta a kaiwa Ashkelon hari da kuma ƙasashen da ke gefen teku?"

48

1Ga Mowab, Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan, "Kaiton Nebo, domin an warwatsa ta. An cinye KIriyata an ƙasƙantar da ita. An ɓalle hasumiyarta an wulaƙanta ta.2Mowab ba ta da sauran wata daraja. Maƙiyansu a Heshbon sun shirya mata masifa. Sun ce Ku zo mu hallakar da ita a matsayinta na ƙasa. Mahaukatanta suma za su hallaka - takobi za ta bi bayanku.'

3Ku saurara! Ƙarar kururuwa na tafe daga Horoniyam, inda akwai kango da kuma babbar hallakarwa.4An hallakar da Mowab. 'Ya'yanta sun yi kuka har aka ji su.5Sun je kan tsaunukan Luhit suna kuka, Domin akan hanya zuwa Horoniyam, an ji ƙara mai ban razana saboda hallakarwa.
6Tsere! Ku ceci rayukanku ku zama kamar dajin yunifa a jeji.7Domin saboda dogararku ga ayyukanku da dukiyarku, kuma za a kame ku. Daga nan sai Kemosh ya tafi zaman bauta, tare da firistocinsa da shugabanninsa.
8Domin mai hallakarwa zai zo kowanne birni; ba birnin da zai tsira. Don haka kwari zai lalace, filin ƙasa kuma za a ɓaɓɓata shi, Kamar yadda Yahweh ya faɗa.9Ku bada fukafukai ga Mowab, don tilas ne ta tashi ta gudu. Biranenta za su zama ɓatattun ƙasashe, inda ba mai zama a cikinsu.10Dama duk wanda ke ragwanci cikin aikin Yahweh ya zama la'ananne! Dama duk wanda ya janye takobinsa daga zubar da jini ya zama la'annanne!
11Mowab tana jin tana da tsaro tun tana matashiya. Ta zama kamar ruwan inabin da ba a taba canja masa gora ba. Ba ta taɓa zuwa bauta ba. Don haka yana jin komai dai - dai ne kamar dã; ɗanɗanonsa bai canza ba.12To duba, ranaku na zuwa - wannan shi ne abin da Yahweh ya furta - lokacin da zan aika masa da waɗanda za su juye shi su kuma juye dukkan tukwanensa su kuma farfasa butocinsa.
13Daga nan sai Mowab su ji kunyar Kemosh kamar yadda ya faru ga gidan Isra'ila, yadda su ka ji kunyar Betel, abin dogararsu.14Yaya za ku ce 'Mu sojoji ne, jarumawan yaƙi'?
15Za a washe Mowab za kuma a kai wa biranenta hari. Don kyawawan matasanta sun gangara mayanka. Wannan furcin sarki ne! Sunansa Yahweh mai runduna ne.16Masifar Mowab na gab da auko mata; bala'i ya kusa sauka da sauri.17Dukkan ku da ke kewaye da Mowab, ku yi kuka; da ku da kuka san ƙarfinta, ku yi sowar wannan, Kaiton, sanda mai ƙarfi, sandar daraja, an karye ta.'
18Sauko daga wurinki mai daraja ki zauna a busasshiyar ƙasa, ke ɗiya mai zama a Dibon. Domin wanda zai hallaka Mowab yana kawo ma ki hari, wanda zai hallakar da madogaranki.19Ku tsaya akan hanya ku yi tsaro, ku mutanen da ke a Arowa. Ku yi tambaya ga wanda ya ga wanda ke gudu don ya tsira. ku ce Me ya faru?'20Mowab ta kunyata, don an warwatsa ta. Ku kaɗa kai ku yi makoki; Ku yi ihun neman taimako. Ku faɗawa mutanen yankin kogin Arnon cewa an hallakar da Mowab.
21Yanzu horo ya sauko kan ƙasa mai duwatsu, ga Holon, da Jakza, da Mefat,22ga Dibon, ga Nebo, da Bet diblataim,23ga Kiriyataim, da Bet Gamul, da Bet Meyon,24ga Keriyot da Bozra, da kuma ga dukkan biranen da ke ƙasar Mowab - da manisanta, da biranen da ke nesa da kusa.25An kawar da ƙahon Mowab; an karya damtsenta - wannan furcin Yahweh ne.+
26Ka sa ya bugu, don ya yi girman kai gãba da Yahweh. Bari Mowab ta yi birgima a kan hararwarta, ka sa ta zama abin ba a.27Domin ko Isra'ila bata zama abin dariya a gare ku ba? An same shi cikin ɓarayi, saboda haka ku ka kaɗa kanku gare shi ku ka yi kuma ta yin magana a kansa?
28Ku yi watsi da birane ku tattaru a gefen gari, ku mazaunan Mowab. Ku zama kamar kurciyar da ke sheƙa a bakin rami a cikin duwatsu.29Mun ji labarin girman kan Mowab - da tayarwarta, da kumbura kanta, yadda ta ke ɗaukaka kanta da mugayen tunane tunanenta na zuciya.
30Wannan furcin Yahweh ne - Ni da kaina na san maganganunsa na banza, waɗanda ba komai ba ne, kamar ayyukansa.31Don haka zan kawo makoki ga Mowab, zan kuma tada muryar makoki ga dukkan Mowab zan yi makoki saboda mutanen Kir Hareset.32Zan yi kuka dominku fiye da yadda na yi don Yazer, da kuringar Sibmah! Rassanki sun zarce ƙetaren Tekun Gishiri sun kai har Yazer. masu hallakarwa sun kawo hari ga 'ya'yan itatuwan inabinki na damina.
33Don an kawar da biki da farinciki daga 'ya'yan itace da kuma ƙasar Mowab. Na kawo ƙarshen ruwan inabi daga wurin matsawarsu. Ba zasu matse su da sowace - sowacen farinciki ba. Duk wani sowace - sowace ba zai zama sowace - sowacen murna ba.
34Daga sowace - sowace a Heshbon tun daga can Eleyele, an jiwo ƙararsu a Yahaz, daga Zowar har zuwa Horoniyaim da Eglat Shelishiya, tun daga ma can rafuffukan Nimrim da suka bushe.35Don zan kawo ƙarshen kowa a Masar wanda ke miƙa hadayu a manyan wurare da ƙona turare ga allolinsa - wannan furcin Yahweh ne.
36Don haka zuciyata tana makoki domin Mowab kamar sarewa. Zuciyata tana makoki kamar gungume saboda mutanen Kir Hereset. Dukiyar da suka ribato ta ƙare.37Don dukkan kawuna sun yi saiƙo an kuma aske duk wani gemu. Tsage - tsage yana a kowanne hannu, sun kuma yafa tufafin makoki a kwankwasonsu
38A kwai makoki a ko'ina, a cikin dukkan gine-ginen Mowab da kuma Cibiyoyin kasuwancin Mowab. Don na hallakar da Mowab kamar tukwanen da ba wanda ke so - wannan furcin Yahweh ne.39Yadda aka farfasa su! Yadda su ka yi ruri cikin makokinsu! Mowab ta juya bayanta cikin kunya! Don haka Mowab zata zama abin ba a da firgita ga dukkan waɗanda suka kewaye shi."
40Gama Yahweh ya faɗi wannan, "Duba, maƙiyi zai zo yana jewa kamar gaggafa, yana buɗe fuka-fukansa a kan Mowab.41An kame Keriyot da dukkan hasumiyoyinta an ƙwance su. Don a waccan ranar zukatan sojojin Mowab za su zama kamar na zukatan matan da ke naƙuda a lokacin haihuwa.
42Don haka za a hallakar da Mowab ta zama ba sauran mutane, don ya mai da kansa ya zama babba gãba da yahweh.43Masifa da rami, da tarko suna zuwa kanku, ku mazauna Mowab - wannan furcin Yahweh ne.44Duk wanda ya gudu saboda firgita zai faɗa rami, kuma duk wanda ya fito daga rami tarko zai kama shi, don zan aukar masu da wannan a shekarar fushina na ramako a kansu - wannan furcin Yahweh ne.
45Waɗanda su ka tsere za su tsaya a inuwar Heshbon ba tare da wani ƙarfi, ba don wuta za ta tashi daga Heshbon, da harshen wuta daga tsakiyar Sihon. Zata cinye goshin Mowab da tsakiyar kawunan mutane masu ɗaga kai.
46Kaiton ki, Mowab! an hallakar da mutanen Kemosh, Don an kwashe 'ya'yanki maza a matsayin bayi, 'yan matanki kuma zuwa bauta.47Amma zan dawo da nasarar Mowab a kwanaki masu zuwa - wannan furcin Yahweh ne." Hukuncin Mowab ya ƙare a nan.

49

1Ga abin da Yahweh ya ce, game da mutanen Ammon, Isra'ila ba ta da 'ya'ya ne? Babu wanda zai gãji wani abu a Isra'ila? Me ya sa Molek ya ke zaune a Gad, mutanen sa kuma su na zaune a cikin biranen sa?2To duba, kwanaki su na zuwa - wannan furcin Yahweh ne - sa'ad da zan ba da alamar yaƙi gãba da Rabbah a cikin mutanen Ammon, za ta zama yasasshen tsibi kuma a ƙone ƙauyukanta da wuta. Gama Isra'ila zai mallaki waɗanda su ka mallake shi." cewar Yahweh.

3Yi ruri cikin makoki, da Heshbon, gama za a ragargaza Ai! Ɗiyar Rabba, ki yi kururuwa! Sa kayan makoki. Yi makoki da kai da kawowa a wofi, gama Molek zai tafi bauta, tare da firistocinsa da shuganninsa.4Me ya sa ki ke fahariya da kwarurrukanki, kwarurrukan masu ba da 'ya'ya sosai, ke kangararriyar ɗiya? Ke da ki ke dogara da dukiyarki kuma kin ce, "wane ne za ya iya zuwa ya yi gãba da ni?'
5Duba, na kusa kawo maki tsoro, wannan shi ne furcin Ubangiji Yahweh Mai Runduna - wannan abin tsoro zai zo daga dukkan waɗanda su ke maƙwabtanki. Zai watsar da kowanne ɗayan ku. Ba wanda zai tattaro waɗanda suka gudu.6Amma bayan haka zan dawo da kaddarorin mutanen Ammon - wannan shi ne furcin Yahweh."
7A kan Idom, Yahweh mai runduna ya ce haka, "Ba sauran hikimar da za a samu a Teman? Shawara mai amfani ta ƙare daga masu fahimta? Hikimar su ta lalace?8Ku gudu! Ku koma baya! Ku jira cikin ramummuka cikin ƙasa, mazauna Dedan. Gama zan kawo hallaka ga Isuwa, a kan shi lokacin da zan hore shi.
9Idan masu girbin inabi su ka zo wurin ku, ba za su rage kaɗan ba? Idan ɓarayi ne da daddare, ba za su saci abin da su ke so ba?10Amma na tuɓe Isuwa ya zama huntu, na tono wuraren ɓoyon sa domin kada ya ƙara ɓoye wa. 'ya'yansa da 'yan uwansa da maƙwabtansa an hallakar da su, shi kuma ya tafi.11Ku bar marayunku, zan lura da su rayukansu, gwaurayenku su dogara gare ni."
12Gama Yahweh ya faɗi haka, "Duba waɗanda ba su cancanta ba tabbas za su sha daga cikin ƙoƙon. Kai da kanka, ka na tsammani za ka tafi ba tare da horo ba? Ba zai yi wu ba, domin tabbas zaka sha.13Gama na rantse da kaina, wannan furcin Yahweh ne - Bozra za ta zama abin tsoro, abin reni, lalatatta, da abin la'antarwa. Dukkan biranenta za su lalace har abada.
14Na ji magana daga wurin Yahweh, an aika da manzo zuwa ga al'ummai, 'ku taru ku kai mata hari, ku yi shiri domin yaƙi.'15Duba, idan an gwada da sauran al'ummai na mai da ke 'yar ƙarama, abin reni ga mutane.
16Saboda tsoron ka, girman kan zuciyarka ya ruɗe ka, mazauna can ƙoli, ku da ku ke a can bisa tsaunuka masu tsawo domin ka sa sheƙar ka can sama kamar gaggafa. Zan dawo da kai ƙasa daga can - wannan ne furcin Yahweh.
17Idom za ta zama abin tsoro ga dukan mai wuce ta. Kowanne mutum zai yi rawar jiki da tsaki saboda dukkan masifunta.18Kamar yadda aka kaɓantar da Sodom da Gomora da maƙwabtansu," Yahweh ya faɗi, "ba wanda zai zauna a can; ba wanda zai tsaya a can.
19Duba, zai tashi kamar zaki daga jejin Yodan zuwa wuraren kiwo masu kyau. Domin nan da nan zan sa Idom ta gudu daga wurin ta, zan sa wani zaɓaɓɓe ya lura da ita. Gama wanene kama da ni, wane ne kuma zai yi mani sammaci? Akwai makiyayin da zai iya yin tsayayya da ni?"
20Ji shirye-shiryen da Yahweh ya yi gãba da Idom, shirye-shiryen da ya yi gãba da mazaunan Teman. Ba shakka za a janye su har ɗan ƙaramin garken dabbobi. Wuraren kiwon su za su zama rusasssun wurare.
21Duniya za ta girgiza da ƙarar faɗuwar su. An ji sowace - sowacen ƙunci daga Tekun Iwa.22Duba, wani zai kawo hari kamar gaggafa, ya kawo su-ra ya buɗe fuka-fukansa a kan Bozra. Daga nan a wannan rana zuciyar sojojin Idom za ta zama kamar zuciyar macen da ke cikin naƙuda."
23Game da Damaskus: "Hamat da Arfad za su ji kunya, saboda sun ji labarin hallaka. Sun narke! hankalin su ya ta shi kamar tekun da ya kasa kwantawa.24Damaskus ta raunana ƙwarai, ta juya ta gudu; tsoro ya kama ta. ‌Ƙ‌unci da ciwo ya kama ta kamar mace mai hafuwa.25Yaya birnin yabo ba a yashe shi ba, garin farincikina?
26Saboda haka samarinta za su faɗi a wuraren cinikaiyarsu, jarumawanta za su hallaka a rannar- wannan shi ne furcin Yahweh mai runduna"27"Gama zan kunna wuta a kan ganuwar Damsakus, za ta cinye kagara mai ƙarfi ta Ben Hadad."
28Game da Kedar da mulkokin Hazor, ga abin da Yahweh ya ce da Nebukadnezza, (gama Nebukadnezza sarkin Babila zai kai wa waɗannan wurare hari): "Tashi ka kai wa Kedar hari ka hallaka waɗannan mutanen na gabas.29Za a kwashe bukkokinsu da garkunansu, duk da labulen bukkokinsu da kayan aikinsu; za a kore raƙumansu daga wurinsu, mazaje za su yi masu ihu su ce, "Ga abin tsoro a kowanne gefe!"
30Ku gudu! Ku yi ragaita can nesa! Ku tsaya a cikin ramuka a ƙasa ku mazauna Hazor - wannan furcin Yahweh ne. Gama Nebukadnezza sarkin Babila ya ƙulla shiri gãba da ku. Ku gudu! Ku koma baya!31Tashi ka kai wa al'ummar da ke zaune lafiya hari cikin sauƙi, "Yahweh ya ce" Ba su da ƙofofi ko makarai, mutanen hakanan suke zaune su kaɗai.
32Gama raƙumansu za su zama ganima, kayansu masu yawa za su zama ganimar yaƙi. Sa'annan zan sa iska ta watsar da su, su waɗanda ke aske gefen gashinsu, zan kawo masu hallaka daga kowanne gefe - haka Yahweh ya furta.33Hazor za ta zama wurin kwanciyar diloli, ta lalace har abada. Ba wanda zai zauna a wurin, ba mutumin da zai tsaya a can.
34Wannan ce maganar Yahweh da ta zo ta wurin Irmiya annabi game da Elam. Wannan ya faru a farkon mulkin Zedekiya sarkin Yahuda, ya ce,35"Yahweh Mai runduna ya faɗi wannan: Duba, na kusa karya 'yan baka na Elam, a karfinsu mafi yawa.36Gama zan kawo iskoki huɗu daga kusurwoyi huɗu na sammai, zan watsar da mutanen Elam ga dukkan waɗannan iskokin. Waɗanda su ka watse daga Elam babu al'ummar da za su je.
37Zan ragargaza Elam a gaban abokan gãbar su da waɗanda ke neman ransu. Domin zan kawo masu hallaka da zafin fushina - haka Yahweh ya furta - Zan aika takobi a bayansu har sai na hallakar da su.38Sa'annan zan kafa kursiyina a Elam in hallakar da sarkinta da shugabanninta daga can - abin da Yahweh ya furta kenan -39Zai zama a cikin kwanaki masu zuwa zan dawo da martabar Elam - abin da Yahweh ya furta kenan."

50

1Ga abin da Yahweh ya furta game da Babila, ƙasar Kaldiyawa, ta hannun Irmiya annabi,2"Faɗawa al'ummai kuma ka sa su, su saurara. Ka sa alama kuma ka sa su saurara. kada ka rufe ta. Ka ce, 'An ɗauke Babila, an kuyatar da Bel. Marduk ta razana, an sa gumakanta cikin kunya; siffofinta sun razana.

3Wata al'umma daga arewa zata taso mata, domin ta mayar da ƙasarta kango. Ba wanda zai zauna cikinta ko mutum ko dabba, duk za su gudu.4Ga abin da Yahweh ya furta a cikin waɗannan kwanaki da wannan lokaci, mutanen Isra'ila da na Yahuda - zasu taru su je suna neman Yahweh Allahnsu da kuka.5Za su tambayi hanyar zuwa Sihiyona su nufi wurin ta suna cewa, za mu je mu haɗa kanmu da Yahweh da dauwamamman alƙawarin da ba za a manta ba."
6Mutane na sun zama garken da ya ɓace, makiyayansu sun bauɗar da su cikin duwatsu; suna juya su daga wannan tudu zuwa wancan. Sun tafi sun mance wurin da suka fito.7Kowa ya je wurin su yana cinye su. Abokan gãbar suna cewa, 'Ba mu yi zunubi ba gama sun yi zunubi ga Yahweh, gidansu na gaskiya -Yahweh begen kakanninsu.
8Ku fita daga tsakiyar Babila; ku fice daga ƙasar Kaldiyawa; ku zama kamar dan akuyan da ya tafi kafin sauran garke.9Duba, na kusa ta da ruɗami, in tada wata ƙungiya ta manyan al'ummai daga arewa su yi gãba da Babila. za su haɗa kan su gãba da ita. Za a ci Babila da yaƙi daga can. Kibiyoyinsu kamar na babban maharbin da ba ya dawowa hakanan.10Kaldiya za ta zama ganima. Dukkan waɗanda suka washe ta za su gamsu - haka Yahweh ya furta.
11Kun yi farinciki, kun yi shagali sa'ad da aka washe abin gãdona, kun yi tsalle kamar ɗan maraki a wurin kiwonsa, kun yi haniniya kamar ƙaƙƙarfan doki.12Saboda haka mahaifiyarku zata ji kunya ƙwarai; za a ƙasƙantar da wadda ta haife ku. Zata zama mafi ƙanƙanta cikin al'ummomi, ta zama jeji ta zama busasshiyar ƙasa ta zama hamada.13Saboda Yahweh ya yi fushi, Babila za ta zama kufai mai zama a cikinta, za ta lalace sarai. Dukkan wanda ya wuce zai yi mamakin lalacewar Babila, ya yi tsaki saboda dukkan raunukanta.
14Ku da ke kewaye da ita, ku shirya ku kai wa Babila hari. Dukkan wanda ya ɗana baka dole ya harbe ta, kada ku mayar da kibiyoyinku, gama ta yi wa Yahweh zunubi.15Ku yi mata ihu a ko'ina! Ta ba da kai, hasumiyoyinta sun faɗi; an rushe ganuwoyinta, wannan fansa ce da Yahweh ya ɗauka. Ku ɗauki fansa a kanta! Ku yi mata kamar yadda ta yi.
16Ku hallaka manoma, da wanda ya shuka iri da wanda ya yi amfani da lauje a lokacin girbi cikin Babila. Bari kowanne mutum ya koma wurin mutanensa ya gudu daga takobin mai azabtarwa; bari su gudu su koma ƙasarsu.
17Isra'ila tumaki ne da suka watse zakuna suka kore su. Da farko sarkin Asiriya ya cinye shi; sa'annan Nebukadnezza sarkin Babila ya karya ƙasusuwansa.18Saboda haka Yahweh Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi haka: Duba, na kusa in hori sarkin Babila da ƙasarsa, kamar yadda na hori sarkin Asiriya.
19Zan dawo da Isra'ila ƙasarsa; zai yi kiwo a Karmel da Bashan. Sa'annan za ya ƙoshi a ƙasar kan tudu ta Ifraim da Giliyad.20Yahweh ya ce, a cikin waɗanan kwanaki da wannan lokaci, za a nemi laifi a Isra'ila, amma ba za a samu ba. Zan biɗi zunubi game da Yahuda, amma ba zan samu ba, gama zan gafartawa waɗanda na keɓe."
21"A tasar wa ƙasar Meratayim, gãba da ita da mazaunan Fekod. Sa masu takobi, kuma a keɓe su domin hallakarwa - abin da Yahweh ya furta kenan-- ku yi dukkan abin da nake umurtarku.22Zizar yaƙi da mummunar hallakarwa suna cikin ƙasar.
23Yadda aka datse gudumar dukkan ƙasashe kuma aka hallakar. Yadda Babila ta zama rusasshen wuri cikin al'ummai.24Na ɗana maki tarko kuma kin kamu, ke Babila, kuma baki sani ba! An same ki kuma an kama ki, domin kin yi tsayayya da Yahweh.
25Yahweh ya buɗe wurin ajiyar kayan yaƙinsa kuma yana fito da kayan yaƙin domin aiwatar da fushinsa. Akwai aiki domin Ubangiji Yahweh mai runduna a ƙasar Kaldiyawa.26Ku kai ma ta hari daga nesa. Ku buɗe rumbunanta ku tara ta kamar tsibin hatsi. Ku keɓe ta domin hallakarwa. kada ku rage ma ta komi.
27Ku kashe dukkan bijimanta, ku kai su wurin yankawa. Kaiton su, ranarsu ta zo - lokacin horonsu.28Akwai motsin waɗanda suke gujewa, waɗanda suka rage, daga ƙasar Babila. Waɗannan za su ba da labarin ɗaukar fansa da Yahweh Allahnmu ya yi domin Sihiyona, da ɗaukar fansa domin haikalinsa."
29A kira maharba gãba da Babila - dukkan waɗanda su ka ɗana bakkunansu. Ku yi zango gãba da ita, kuma kada kowa ya tsira. Ku sãka mata kamar yadda ta yi. ku yi mata bisa ga ma'aunin da ta yi amfani da shi. Gama ta rena Yahweh, Mai Tsarki na Isra'ila.30Haka samarinta za su faɗi a cikin dandalin birni, kuma dukkan mayaƙanta zasu hallaka a wannan rana - Wannan shi ne furcin Yahweh."
31Duba, Ina gãba da ke, ke mai takama - wannan shi ne furcin Ubangiji Yahweh mai runduna - gama ranarki ta zo, ke mai taƙama, lokacin da zan hore ki.32Domin masu taƙama su yi tuntuɓe su faɗi. Ba wanda zai tashe su. Zan kunna wuta a cikin biranensu; za ta cinye komi da komi da ke kewaye da shi.
33Yahweh mai runduna ya ce wannan: An tsanantawa mutanen Isra'ila, tare da mutanen Yahuda. Dukkan waɗanda suka kamasu su na riƙe da su; sun hana su su tafi.34Mai kuɓutar da su mai ƙarfi ne. Yahweh mai runduna ne sunansa. Lallai zai duba matsalar su da gaskiya, domin ya kawo hutu a ƙasar, ya kuma kawo husuma ga mazaunan Babila.
35Takobi na gãba da Kaldiyawa, haka Yahweh ya furta, da kuma Babila da mazaunanta da shuganninta da masu hikimarta.36Takobi na gãba da masu faɗar maganganun banza! Za su zama wawaye! Takobi na gãba da sojojinta! za su cika da tsoro.37Takobi yana zuwa gãba da dawakansu, da karusansu da dukkan mutane mazauna cikin tsaƙiyar Babila, domin su zama kamar mataye. Takobi ya na zuwa gãba da ɗakunan ajiyarta, kuma za a washe su.
38Fari ya na zuwa kan ruwayenta domin su bushe. Domin ta zama ƙasar gumaka lalatattu, sun yi kamar mutane marasa hankali ta wurin gumakansu.39Ta zama hamada inda namun daji za su zauna da diloli da 'ya'yan jimina su zauna a cikinta. Ba lokacin da za a ƙara zama a cikinta. Ba za a ƙara zama cikinta ba daga tsara zuwa tsara.40Kamar yadda Yahweh ya kaɓantar da Sodom da Gomora da maƙwabtansu - abin da Yahweh ya furta ke nan - ba wanda zai zauna a can; ba mutumin da zai tsaya cikinta."
41Duba, wasu mutane suna zuwa daga arewa; babbar al'umma da sarakuna masu yawa an izo su daga manisantan wuraren duniya.42Zasu ɗauko bakkuna da mãsu. Su masu masifa ne ba su da tausayi. Tafiyar su tana kama da rurin teku, sun haye bisa dawakai, a jere bisa layi kamar mutane domin yaƙi, gaba da ke, ɗiyar Babila.
43Sarkin Babila ya ji rahoto game da su, sai hannayensa suka yi sanyi cikin ƙunci. Azaba ta kama shi kamar mace mai haihuwa.
44Duba! Ya fito kamar zaki daga tuddan Yodan zuwa wuraren kiwo. Gama nan da nan zan sa su gudu daga wurin, kuma zan sa wani zaɓaɓɓe ya lura da wurin. Gama wane ne kama da ni, kuma wa za ya ba ni sammaci? Wanne makiyayi ne zai iya tsayayya da ni?
45To saurari shirye-shiryen da Yahweh ya yi gãba da Babila, shirye-shiryensa da ya shirya gãba da ƙasar Kaldiyawa. Lallai za a janye su, har ma da ɗan karamin garke. Wuraren kiwon su za su zama kango.46Duniya za ta girgiza da rurin yaƙin yin nasara da Babila, al'ummai za su ji kukansa na ƙunci."

51

1Ga abin da Yahweh ya faɗi: Duba, na kusa tado da iskar mai hallakaswa a kan Babila da mazauna cikin Leb Kamai.2Zan aika da baƙi ga Babila, za su warwatsar da ita su lalata kasarta, gama za su auko mata ta kowanne gefe a ranar hallakarwa.

3Kada ku bari maharba su ɗana bakkunansu; kada ku bari su sa kibiya. Kada ku ƙyale samarinta, ku keɓe dukkan sojojinta domin hallakarwa.4Gama mutanen da suka sami rauni za su faɗi a ƙasar Kaldiyawa; matattu za su faɗi a cikin titunanta.
5Gama Isra'ila da Yahuda Allah bai yashe su ba, Yahweh mai runduna, ko da yake ƙasar ta na cike da laifofin da a ka yi wa Mai Tsarki na Isra'ila.6Ku gudu daga cikin Babila, kowa ya tsira da kansa. Kada ku hallaka cikin muguntarta. Gama lokacin ɗaukar fansar Yahweh ne. Zai rama komai a kanta.
7Dã Babila ƙoƙon zinari ce a hannun Yahweh wadda ta sa dukkan duniya suka bugu; dukkan al'ummai suka sha ruwan inabinta suka sami taɓin hankali.8Ba da jimawa ba Babila za ta fadi za a hallaka ta. Ku yi makoki dominta! Ku ba ta magani domin ciwonta; ko ƙila zata warke.
9Mun so mu warkar da Babila, amma ba ta warke ba. Bari mu barta, mu tafi kasarmu. Gama muguntarta ta kai har sama, ta taru a cikin giza-gizai.10Yahweh ya ce mu ba mu da laifi. Ku zo, mu faɗi ayyukan Yahweh Allahnmu a cikin Sihiyona.'
11Ku wãsa kibiyoyi ku kuma ɗauki garkuwoyi. Yahweh ya na zuga ruhun sarkin Medes a kan shirin hallaka Babila. Wannan fansa ce ta Yahweh, fansa saboda hallaka haikalinsa.12Ku tada tuta a kan ganuwoyin Babila, ku tsananta tsaro; ku sa masu tsaro ku shirya kwanton ɓauna; gama UBANGIJI zai aikata abin da ya ce game da mazaunan Babila.
13Ku mutanen da ke zaune a bakin rafuka masu ruwa da ku mutane masu arzikin dukiya, ƙarshenku ya zo. An rage tsawon zaren rayuwarku.14Yahweh mai ruduna ya rantse da ran sa, ' zan cika ku da mutane, kamar cincirindon fara, za kuma su tãda muryar yaƙi gãba da ku.'
15Ya yi duniya ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa. Ta wurin fahiminsa ya shimfiɗa sammai.16Idan ya yi tsawa, sai ruwaye su yi ruri a cikin sammai, gama ya kan kawo turiri daga ƙarshen duniya. Ya kan yi walƙiya domin ruwa ya kuma aiki iska daga cikin taskokinsa.
17Kowanne mutum ya zama marar fahimi, marar sani. Kowanne maƙerin tama gumakansa sun kunyatar da shi. Gama sifofinsa na zubi ƙarya ce kawai babu rai a cikin su.18Ba su da amfani, aikin ruɗi ne kawai, za su lalace a ranar horonsu.19Amma Yahweh, rabon Yakubu ba kamar waɗannan ya ke ba, gama shi ne ya cura dukkan abu. Isra'ila ne harshen gãdonsa; Yahweh mai runduna ne sunansa.
20Kai ne gudumata da kayan yaƙina. Da kai zan ragargaza al'ummai in hallaka mulkoki.21Da kai zan ragargaza dawakai da mahayansu; da kai zan ragargaza karusai da masu tuƙa su.
22Da kai zan ragargaza kowanne mutum da kowacce mace. Da kai zan ragargaza tsoho da yaro. Da kai zan ragargaza samari da budurwai.23Da kai zan ragargaza makiyayi da garkensa. Da kai zan ragargaza manoma da ƙungiyarsu, Da kai zan ragargaza gwamnoni da jami'ansu.
24Kana gani zan sakawa Babila da dukkan mazauna Kaldiya, bisa ga dukkan muguntar da suka yi a cikin Sihiyona - abin da Yahweh ya furta kenan.
25Duba, ina gãba da kai, dutsen hallakarwa - abin da Yahweh ya furta kenan - wanda ke hallaka dukkan duniya. Zan miƙa hannuna gãba da kai in gangarar da kai daga can ƙoli, in mai da kai ƙonannen dutse.26Yadda ba za su ɗauki wani dutse daga wurinka su kafa tushen gini da shi ba. Za ka lalace sarai har abada - haka Yahweh ya furta.
27A kafa tuta bisa duniya. A busa ƙaho bisa al'ummai, a kira al'ummai su kai mata hari: Ararat, Minni da Ashkenaz. A sa wani jarumi ya kai mata hari, a zo da dawakai kamar cincirindon fãri.28A shirya al'ummai su kai mata hari: Sarkin Medes da gwamnoninsa, da dukkan jami'ansa da dukkan ƙasashen da ke ƙarƙashin mulkinsa.
29Gama ƙasar za ta girgiza ta kasance cikin azaba, tun da shirye - shiryen Yahweh ya ci gaba a kan Babila, domin ya maida ƙasar Babila lalatacciyar ƙasa inda ba mazauna.
30Sojojin da ke Babila sun dena faɗa; sun koma cikin maɓoyarsu. ‌Ƙ‌arfinsu ya ƙare; sun zama mata - gidajenta suna cin wuta, an kakkarya makaran ƙofofinta.31Wani manzo ya tafi ya yi shela ga wani manzo, wani mai gudu ya tafi ya gaya wa wani mai gudu ya kai wa sarkin Babila rahoton an ƙwace birninsa tun daga ƙarshe har zuwa ƙarshe.32An ƙwace magangarin rafi an ƙone ciyawar fadamu, kuma mayaƙan Babila sun rikice.
33Gama Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi haka: ‌Ɗ‌iyar Babila ta zama kamar masussuka. Lokaci ya yi da za a tattake ta ƙasa. Da jimawa kaɗan lokacin girbi zai zo mata.
34Nebukadnezza sarkin Babila ya lanƙwame ni; ya kore ni cikin ruɗami ya kuma maishe ni tukunyar da ba komi a ciki. Ya haɗiye ni kamar dodo, ya cika cikinsa da abinci na mai kyau, ya share ni sarai.'35Shi wanda ya ke zaune a Sihiyona zai ce, '‌Ta'addancin da a ka yi mani da jikina ya koma kan Babila.'Yerusalem za ta ce, ' Bari jinina ya zauna a kan Kaldiya.'
36Saboda haka ga abin da Yahweh ya ce: Duba, ina kusa da goya ma ki baya cikin matsalar ki in ɗauki fansa domin ki. Duba zan busar da ruwayen Babila, in sa mabulbulolinta su ƙafe.37Babila za ta zama juji, kogunan diloli, wurin jin tsoro, abin tsãki, inda ba kowa a ciki.
38Mutanen Babila za su yi ruri tare kamar 'yan zakoki. Za su yi ƙara kamar 'ya'yan zaki.39Sa'ad da su ka ji zafi saboda haɗama, zan shirya masu liyafa; zan sa su bugu domin su yi murna, sa'annan su yi barci wanda ba za su ƙara tashi ba - abin da Yahweh ya furta kenan -40Zan tura su kamar ragunan yanka, kamar raguna da bunsura.
41An ci Babila da yaƙi! An kame yabon dukkan duniya. Abin da mamaki yadda Babila ta zama kango a cikin al'ummai.42Teku ya zo kan Babila! Rurin balalloƙan ruwa ya cika ta.
43Biranenta sun zama lalatattu, ƙasa busasshiya da kuma jeji, ƙasar da babu mai zama a ciki, ba talikin da ke wucewa ta wurin.44Saboda haka zan hori Bel cikin Babila; zan fitar daga bakinsa abin da ya haɗiye, al'ummai ba za su ƙara gangarowa wurinsa da baye - bayensu ba. Ganuwoyin Babila za su faɗi.
45Mutanena, ku fice daga cikin tsakiyarta. Bari kowanne ɗayanku ya tsira da ransa daga fushin hasalata.46Kada ku bari zuciyarku ta yi suwu saboda labarin da ku ka ji cikin ƙasar, gama labaran za su zo shekara ɗaya. Bayan wannan shekara mai zuwa akwai labarai, tashin hankali zai zo cikin ƙasar. Mai mulki zai yi gãba da mai mulki.
47Saboda haka, duba, kwanaki za su zo inda zan hori sassaƙaƙƙun gumaka na Babila. Dukkan ƙasarta za ta ji kunya, dukkan waɗanda a ka yanka za su faɗi cikin tsakiyarta.48Sa'annan sama da ƙasa, da dukkan abin da ke cikin su za su yi farin ciki a kan Babila. Gama masu hallakarwa za su zo dominta daga arewa - haka Yahweh ya furta.49Kamar yadda Babila ta kashe mutane su ka faɗi a Isra'ila, haka kuma za a kashe mutane su faɗi a cikin tsakiyar Babila.
50Masu tsira daga takobi, ku tafi! Kada ku tsaya cik. Ku tuna da Yahweh daga nesa; bari Yerusalem ta zo cikin lamirinku.51Mun ji kunya, domin mun ga wulaƙanci; kunya ta rufe fuskokinmu, gama bãƙi sun shiga wurare masu tsarki na gidan Yahweh.
52Domin haka, duba, kwanaki suna zuwa - haka Yahweh ya furta - sa'ad da zan hukunta sassaƙaƙƙun gumakanta, waɗanda suka ji rauni zasu yi nishi cikin ƙasarta dukka.53Ko da Babila zata hau cikin sammai ta inganta hasumiyarta, masu hallakarwa zasu auko mata daga wurina - haka Yahweh ya furta.
54Kukan baƙinciki ya fito daga Babila, babbar ribɗewa ta fito daga ƙasar Kaldiyawa.55Gama Yahweh ya na hallakar da Babila. Yana sa muryarta mai ƙara ta lalace. Abokan gabarsu su na ruri kamar balalloƙan ruwaye masu yawa; ƙarar su ta yi ƙarfi ƙwarai.56Gama masu hallakarwa sun zo kanta - a kan Babila! - kuma an kama jarumawanta. An kakkarya bakkunansu, gama Yahweh Allah ne mai ɗaukar fansa; ba shakka zai ɗauki fansa.
57Zan sa hakimanta da masu mulkinta da sojojinta su bugu, su yi barcin da ba za su tashi ba - wannan furcin sarki ne: Yahweh mai runduna ne sunansa.58Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Ganuwar Babila mai kauri za a rushe ta sarai, za a ƙone dogayen ƙofofinta. Sa'annan mutane masu kawo mata ɗauki za su yi aikin wofi; dukkan abin da al'ummai su ka yi ƙoƙarin yi mata za a ƙone shi."
59Wannan ita ce maganar da Irmiya annabi ya umurtawa Seraya dan Neriya dan Maseya, sa'ad da ya tafi da Zedekiya sarkin Yahuda zuwa Babila a cikin shekara ta hudu ta mulkinsa. A lokacin Seriya shi ne babban jami'i.60Irmiya ya riga ya rubuta a cikin naɗaɗɗen littafi dukkan hallakar da za ta zo a kan Babila - dukkan waɗannan maganganu da aka rubuta game da Babila.
61Irmiya ya ce da Seraiya, "Sa'ad da ka je Babila za ka gani kuma za ka karanta waɗannan maganganu da ƙarfi.62Sa'annan za ka ce, 'Yahweh, kai da kanka ka furta cewa za ka hallaka wannan wuri, kuma ba mutum ko dabba da zai zauna a cikinta, za ta zama lalatacciya har abada.'
63Sa'ad da ka gama karanta wannan naɗaɗɗen littafi, ka ɗaura masa dutse ka jefa shi cikin tsakiya Ifratis.64Ka ce, 'Haka Babila zata nitse. Ba zata tashi ba saboda bala'in da na ke aiko wa gãba da ita, kuma za su faɗi."' Nan maganganun Irmiya suka tsaya.

52

1Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa'ad da ya fara mulki; ya yi mulki a Yerusalem shekara goma sha ɗaya. Sunan mahaifiyarsa Hamutal ne; ita ɗiyar Irmiya ce daga Libna.2Ya yi mugunta a gaban Yahweh; ya yi dukkan abin da Yohoaikim ya yi.3Ta wurin fushin Yahweh dukkan waɗannan abubuwa suka faru a Yerusalem da Yahuda, har sai lokacin da ya kore su daga gabansa. Sa'annan Zedekiya ya yi wa sarkin Babila tawaye.

4Ya zama a cikin shekara ta tara ta mulkin Zedekiya, a cikin wata na goma, a cikin rana ta goma ga watan, Nebukadnezza sarkin Babila, ya zo da dukkan mayaƙansa gãba da Yerusalem. Suka yi zango daura da ita, suka kafa sansanin yaƙi kewaye da ita.5Suka kewaye birnin ba shiga ba fita, har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
6A cikin wata na hudu, a kan rana ta tara ga watan yunwa ta yi tsanani a cikin birnin har ma ba abin da mutane za su ci a ƙasar.7A ka ɓalle birnin aka shiga, dukkan mayaƙa su ka gudu su ka fice daga cikin birnin ta hanyar da ke tsakanin ganuwa biyu a cikin dare, ta lambun sarki, duk da ce wa Kaldiyawa su na kewaye da birnin. Su ka tafi wajen Arabah.8Amma sojojin Kaldiyawa su ka bi sarki su ka cimma Zedekiya a filin Kogin Yodan kusa da sararin kwarin Yariko. Dukkan mayaƙansa su watse daga wurinsa.
9Suka kama sarki suka kawo shi wurin sarkin Babila a Riblah cikin ƙasar Hamat, inda ya yanke ma sa hukunci.10Sarkin Babila ya yanka 'ya'yan sarki Zedekiya maza ya na gani, kuma a Riblah ya yanka dukkan shugabannin Yahuda.11Sa'annan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya, ya ɗaure shi da sarƙa ta jan ƙarfe ya kawo shi Babila. Sarkin Babila ya sa shi a kurkuku har zuwa ranar mutuwarsa.
12To, a cikin wata na biyar, a kan rana ta goma ga wata, a shekara ta goma sha tara ta mulkin Nebukadnezza sarki, sarkin Babila, Nebuzaradan ya zo Yeruselem. Shi ne jami'in masu tsaron sarki, shi kuma bawan sarkin Babila ne.13Ya ƙone gidan Yahweh, da fadar sarki da dukkan gidajen Yerusalem; ya kuma ƙone kowanne gini mai mahimmanci.14Ganuwar da ta kewaye Yerusalem kuma, mayaƙan Babiloniyawa da ke tare da jami'in masu tsaron sarki suka rushe su.
15Su marasa galihu da sauran mutanen da su ka ragu a cikin birni, waɗanda su ka bijire su ka tafi wurin sarkin Babila da sauran masu aikin hannu - Nebuzaradan jami'in masu tsaron sarki ya kwashe su ya kai su bauta.16Amma Nebuzaradan jimi'in masu tsaron sarki ya bar waɗansu cikin marasa galihu a ƙasar domin su yi aiki a garkar inabi da gonaki.
17Game da ginshikai na tagulla da ke na gidan Yahweh kuwa, da diraku, da babban bangaji na tagulla da ake kira "Teku" da su ke cikin gidan Yahweh, Kaldiyawa su ka kakkarya su gutsu - gutsu suka kwashe dukkan tagullan suka koma da su Babila.18Tukwanen, da ceburan, da tsinkunan gyara fitilu, da bangazai, da dukkan kayan aikin na tagulla waɗanda firistoci suka yi hidima da su a haikali - Kaldiyawa suka kwashe su dukka suka tafi da su.19Daruka da tasoshin ƙona turare, da bangazai, da tukwane, da maɗorin fitilu, da kaskuna, da darurruka da aka yi da su zinariya da waɗanda aka yi su da azurfa - jami'in masu tsaron sarki ya kwashe su dukka.
20Ginshiƙai guda biyu, da babban bangajin tagulla da aka sa ni da "Teku," da bijimai guda goma sha biyu na tagulla da su ke karkashin dirakun, abubuwan da Sulaiman ya yi domin gidan Yahweh, ɗauke da tagulla da ta wuce gaban aunawa.21Ginshikan kamu sha takwas ne kowannen a tsayi, da layikan da su ke kewaye da su kuma kowanne kamu goma sha biyu ne. Kowannen su kaurin yatsu hudu ne masu rami.
22Akwai gammon tagulla a bisan sa. Gammon tsawon kamu biyar ne, an yi masa aikin dajiya da siffofin 'ya'yan manta'uwa waɗanda a ka yi da tagulla. Ɗaya ginshikin da nashi 'ya'yan manta uwar dai - dai su ke da na farin.23Don haka akwai manta'uwa tasa'in da shida bisa gefen gammunan, da manta'uwa guda ɗari a bisa kewayen aikin dajiyar.
24Jami'in masu tsaron sarkin ya dauki Seraiya babban firist tare da Zafaniya da firist na biyu da masu tsaron ƙofa su uku a matsayin 'yan kurkuku.25Daga cikin birni kuwa ya kama jami'in da ke kula da sojoji da mutane bakwai masu ba sarki shawara, waɗanda suke cikin birni har wannan lokaci. Ya kuma kama jami'in sojojin sarki wanda shi ne ke shigar da mutane aikin soja, tare da waɗansu mahimmam mutane guda sittin waɗanda su ke cikin birni.
26Sai Nebuzaradan jami'in masu tsaron sarki ya ɗauko su ya kawo su wurin sarkin Babila a Ribla.27Sarkin Babila ya kashe su a Ribla cikin ƙasar Hamat. Ta haka Yahuda ta fita daga ƙasarta ta tafi bauta.
28Waɗannan su ne mutanen da Nebukadnezza ya kai bauta cikin shekara ta bakwai, mutanen Yahuda su 3,023.29A cikin shekara ta takwas ta Nebukadnezza, ya ɗauki mutane 832 daga Yerusalem.30A cikin shekara ta ashirin da uku ta Nebukadnezza, Nebuzaradan, jami'in masu tsaron sarki ya ɗauki mutum 745 cikin mutanen Yahudiya ya kai su bauta. Dukkan waɗanda a ka kai bauta su ne mutum 4,600.
31Ya zama kuma a cikin shekara ta talatin da bakwai ta hijira Yehoyacin, sarkin Yahuda, a cikin wata na goma sha biyu, a kan rana ta ashirin da biyar ga wata, sai Awel-Marduk, sarkin Babila ya saki Yehoyacin sarkin Yahuda daga kurkuku. Wannan ya faru ne a cikin shekarar da Awel-Marduk ya fara mulki.
32Ya yi masa maganar alheri, ya ba shi wurin zama da ya fi na sauran sarakunan da suke tare da shi daraja a Babila.33Awel-Marduk ya cire wa Yehoiyacin kayan 'yan sarƙa. Yehoyacin ya yi ta cin abinci a teburin sarki dukkan sauran rayuwarsa,34a kan ba shi kuɗin cin abinci kullum har mutuwarsa.

Littafin makoki

1

1Ƙasar da dã ke cike da mutane yanzu tana zaman kaɗaici. Ta zama kamar gwauruwa ko da ya ke babbar al'umma ce dã. Dã gimbiya ce a cikin al'ummai, amma yanzu an sa ta aikin bauta na dole.2Tana kuka da koke-koke da dare, kuma hawayenta sun rufe kumatunta. Babu masoyinta da ke yi mata taimako. Dukkan abokananta sun yashe ta. Sun zama maƙiyanta.

3Bayan talauci da ƙunci, Yahuda ta tafi zaman bauta. Tana zaune a cikin al'ummai kuma ta rasa samun hutawa. Dukkan masu korarta a guje sun wuce ta a cikin damuwarta.
4Hanyoyin Sihiyona na makoki saboda babu waɗanda suka zo bukukuwan da aka shirya. Dukkan ƙofofinta sun zama yasassu. Firistocinta na nishi. 'Yanmatanta na cikin da baƙinciki kuma ita kanta tana cikin cikakken ƙunci.5Magabtanta sun zama iyayengijinta; maƙiyanta sun azurta. Yahweh ya ƙuntata mata domin yawan zunubanta. An kai ƙananan 'ya'yanta bauta ga magabcinta.
6Kyau ya rabu da ɗiyar Sihiyona. 'Ya'yan sarakunanta sun zama kamar bareyin da ba za su iya samun abinci ba, kuma suna tafiya da ƙyar a gaban masu farautarsu.
7A kwanakin ƙuncinta da rashin wurin zamanta, Yerusalem zata tuna da dukiyoyinta masu daraja wadda take da su a kwanakin dã. Sa'ad da mutanenta suka faɗi a hannun abokan gãba, babu wanda ya taimaketa. Abokan gãba sun gan ta sun kuma yi dariya ga hallakarta.
8Yerusalem ta yi zunubi ƙwarai, saboda haka ta zama abin ƙi kamar wani abin ƙyama. Dukkan waɗanda ke girmama ta sun yashe ta tun da suka ga tsiraicinta. Tana nishi tana ƙoƙarin juyawa.9Ta zama marar tsabta a karkashin zannuwanta. Ba ta yi tunani a kan kwanakinta masu zuwa ba. Faɗuwarta abin takaici ne. Babu wanda zai ta'azantar da ita. Ta yi kuka cewa "Dubi wuyar da nake sha, Yahweh, gama makiyana sun ƙaru da yawa!"
10Abokin gãba yasa hannunsa a dukkan dukiyoyinmu masu daraja. Ta ga al'ummai sun shigo wurinta mai tsarki, ko da ya ke ka umarcesu kada su shiga wurin taruwar jama'arka.
11Dukkan mutanenta sun yi nishi sa'ad da suke neman abinci. Sun ba da dukiyoyinsu masu daraja domin abincin da zai rayar da su. Yahweh, ka dube ni ka kula da ni, gama na zama marar daraja.12Wato a wurinku ba komai ba ne, dukkanku da ke wucewa? Ku duba ku gani ko akwai wani mai shan azaba kamar ni, tun da Yahweh ya azabtar da ni a ranar fushinsa mai zafi.
13Daga can bisa ya aiko da wuta a ƙasusuwana, kuma ta cinye su. Ya yafa raga domin ƙafafuwana ya kuma maida ni baya. Ya maida ni kullum a yashe da somewa. Karkiyar laifofina a ɗaure suke a hannunsa.14An ɗaura su tare an sa su a kan wuyana. Ya sa ƙarfina ya ƙare. Ubangiji ya bashe ni a hanun maƙiyana, kuma ba zan iya tsayawa ba.
15Ubangiji ya tura majiya ƙarfina gefe waɗanda ke yi mani kariya. Ya kira taron jama'a găba da ni don su murƙushe jarumawana. Ubangiji ya tattake ɗiyar Yahuda budurwar nan, a wurin matse ruwan inabi.
16Saboda waɗannan abubuwa na yi kuka. Idanuwana, ruwa na zubowa ƙasa daga Idanuwana tun da mai ta'azantar da ni wanda zai 'yantar da raina yana nesa da ni. 'Ya'yana sun lalace saboda maƙiyin ya yi nasara.17Sihiyona ta shinfiɗa hannuwanta da făɗi; ba wanda zai ta'azantar da ita. Yahweh ya umarci waɗanda ke kusa da Yakubu su zama abokan găbarsa. Yerusalem ta zama abin rashin tsabta a garesu.
18Yahweh mai adalci ne, gama na tayar wa dokokinsa. Ku ji, dukkan mutane, ku kuma ga damuwata. Budurwaina da jarumawana sun tafi bauta.19Na yi kira ga abokaina, amma sun zama maciya amana a gareni. Firistocina da dattawana sun hallaka a cikin birnin, sa'ad da suke neman abinci na ceton ransu.
20Duba, Yahweh, gama ina cikin kunci; cikina ya ɗuri ruwa, sai na damu a cikin zuciyata, gama ni mai tayarwa ne sosai. A waje, takobi ya sa uwa makoki, a cikin gida kuma babu kome sai mutuwa.
21Sun ji nishina, amma ba mai ta'azantar da ni. Dukkan maƙiyana sun ji batun matsalata kuma sun yi murna cewa kai ka yi haka. Kã kawo ranar da ka alƙawarta; yanzu bari su zama kamar ni.22Bari dukkan muguntarsu ta zo gabanka. Ka yi masu yadda ka yi mani saboda laifofina. Nishe-nishe na da yawa kuma zuciyata ta some.

2

1Ubangiji yã rufe ɗiyar Sihiyona a karkashin gizagizan fushinsa. Ya jefar da darajar Isra'ila ƙasa daga sama zuwa duniya. Bai tuna da matashin sawunsa a ranar fushinsa ba.2Ubangiji yã haɗiye yã kuma ƙi jin tausayin dukkan garurruwan Yakubu. A ranar fushinsa ya jefar da ƙayatattun biranen ɗiyar Yahuda a ƙasa; a cikin rashin girmamawa ya saukar da mulkin da shugabaninsa ƙasa.

3Da zafin fushinsa ya datse kowanne ƙaho na Isra'ila. Ya cire hannun damansa daga gaban maƙiyi. Ya ƙone Yakubu kamar harshen wuta da ke cinye dukkan abin da ke kewaye da shi.4Kamar maƙiyansa ya ɗana bakansa gare mu, ya yi shirin harbi da hannun damansa. Ya yayyanke dukkan masu faranta masa rai a rumfar ɗiyar Sihiyona; Ya zuba fushinsa kamar wuta.
5Ubangiji ya zama kamar maƙiyi. Ya haɗiye Isra'ila. Ya haɗiye dukkan fadodinta. Ya hallakar da wuraren mafakarta. Ya ƙara baƙinciki da makoki cikin ɗiyar Yahuda.6Ya kai wa rumfar sujadarsa hari kamar bukkar gona. Ya rusa wurin tsattsarkan taron jama'a. Yahweh yasa a mance da tattsarkar Asabar da taron jama'a a Sihiyona, gama ya wofintar da sarki da firist cikin zafin fushinsa.
7Ubangiji ya ƙi bagadinsa ya kuma musanci tsarkakan haikalinsa. Ya ba da bangayen fadodinta ga hannun maƙiyi. Sai suka ta da ihu a gidan Yahweh, kamar ranar ayyanannen idi.
8Yahweh ya ƙudura ya hallakar da garun birnin ɗiyar Sihiyona. Ya miƙar da igiyar gwaji kuma bai ɗauke hannunsa daga rusar da garun ba. Ya sa kagara da garu suyi makoki; ya wofintar da su tare.9Ƙofofinta sun lume cikin ƙasa; ya rusar ya kuma karya shingayen kofofinta. Sarkinta da 'ya'yan sarkinta na cikin al'ummai, babu doka kuma, har anabawanta sun rasa wahayi daga Yahweh.
10Dattawan ɗiyar Sihiyona na zaune shiru a ƙasa. Sun watsa ma kawunansu ƙasa suna kuma sanye da tufafin makoki. 'Yan matan Yerusalem sun russunar da kawunansu ƙasa.
11Hawayen idanuwana sun gaji da zubowa; cikina ya kiɗime, dukkan raina na cike da baƙinciki saboda rushewar ɗiyar mutanena, yara da jarirai sun some a titunan birnin.12Suka cewa uwayensu, "Ina hatsi da ruwan inabi?" sa'ad da suka some kamar mutumin da ya ji ciwo a titunan birnin, rayukansu suka kasance cikin baƙinciki a hannuwan uwayensu
13Me zan ce maki, ɗiyar Yerusalem? Me zan kwatanta ta'aziyar da zan yi maki 'yar Sihiyona? Ciwonki na da girma kamar teku. Wa zai iya warkar da ke?14Anabawanki sun gano wahayin ƙarya dana wofi domin ki. Ba su fallasar da laifofinki har da farfaɗo da ke daga hasarar bauta ba, amma suka fitar da maganganun ƙarya dana kaucewa daga hanya.
15Dukkan waɗanda suka wuce a hanya suna tafa maki hannuwansu. Suna tsãki suna kaɗa kai gãba da 'yar Yerusalem suna cewa, "Ba wannan ne birnin da ake kira 'Cikakken Kyau,' 'Farin Cikin dukkan Duniya' ba?"16Dukkan maƙiyanki sun buɗe bakunansu suna maki ba'a. Suna gwalo da cizon baki da cewa, "Mun haɗiye ta! Wannan ce ranar da muke jira! Muna jiran ganinta!"
17Yahweh ya aikata abin da ya shirya zai yi. Ya cika maganarsa. Ya tumɓuke ki da rashin tausayi, gama ya bai wa maƙiya dama su yi farinciki a kan ki; ya ɗaga ƙahon maƙiyanki.
18Zuciyarsu ta yi kuka ga Ubangiji, garun 'yar Sihiyona! Ki sa hawayenki su kwararo ƙasa kamar kogi dare da rana. Kar ki ba kanki da idanunki hutu,19Tashi, yi kuka da dare, sau da yawa da almuru! Ki zubo da zuciyarki kamar ruwa a gaban fuskar Ubangiji. Ki ɗaga hannuwanki gareshi domin rayukan 'ya'yanki waɗanda suka some da yunwa a kowanne gefen titi.
20Duba, Yahweh, ka kula da waɗanda ka yi masu haka. Shin mata zasu iya cinye 'ya'yan cikinsu, 'ya'yan da suka yi renonsu? Yana yiwuwa a kashe firist da annabi a rumfar sujada ta Ubangiji?
21Matasa da tsofaffi na kwance a ƙurar titunan. "Yan mata da samari sun făɗi ta takobi; kã yanka su ba tare da tausayinsu ba.22Kã yi kira, kamar yadda kake kiran mutane a ranar idi, ina fargaba a kowanne gefe, a ranar fushin Yahweh, babu wanda zai kuɓuta ko ya rayu; waɗanda na lura na kuma tasar da su, maƙiyana sun hallakar da su.

3

1Ni ne mutumin da yaga wuya a ƙarƙashin sandar fushin Yahweh.2Ya kore ni waje ya kuma sanya ni in yi tafiya cikin duhu a maimakon haske.3Hakika ya juye hannuwansa gãba da ni ba sau ɗaya ba, ba sau biyu ba a dukkan rana.4Ya maida naman jikina da fatar jikina banza; ya karya kassusuwana.

5Ya kewaye ni kamar birnin da aka kawo masa hari, ya kuma kewaye ni da baƙinciki da matsananciyar wahala.6Yasa na zauna a wurare masu duhu, kamar waɗanda suka mutu da daɗewa.7Ya gina garu kewaye da ni kuma ba zan iya kuɓuta ba. Yasa sarƙoƙina sun nawaita8kuma ko da na yi kiran neman taimako, sai ya ƙi jin addu'ata
9Ya tare hanyata da garun sassaƙaƙƙun duwatsu; ya maida hanyoyina karkatattu.10Ya yi kamar damisa da ke mani kwanto, Zaki na boyewa;11ya bauɗar da hanyoyina, ya yashe ni.
12Ya ja bakansa ya sa na zama abin da kibiyarsa zata harba.13Ya soke ƙodojina da kiɓiyoyin kwarinsa.14Na zama abin dariya ga dukkan mutane, wani abin yi wa zambo a dukkan yini.15Ya cika ni da ɓacin rai ya kuma tilasta ni sha ruwan ɗaci.
16Ya haƙorana niƙa da tsakuwa; ya tura ni ƙasa cikin ƙura.17An raba raina da salama; Na mance da mene ne ma farinciki.18Saboda haka na ce, "jimirina ya ƙare haka kuma begena ga Yahweh"
19Tuna da azabata da yawace-yawacena, ɗacin rai da baƙinciki.20Ina ci gaba da tunawa da ita ina kuma russunawa ƙasa a cikin rai na.21Amma ina nazarin wannan a zuciyata saboda haka ina da bege:
22Kaunar Yahweh madawwamiya ba ta ƙarewa kuma tausayinsa baya zuwa ga ƙarshe,23suna sabuntuwa kowacce safiya; amincinka mai girma ne.24"Yahweh ne gãdona". Na ce, saboda haka zan yi bege a cikinsa.
25Yahweh managarci ne ga waɗanda ke jiransa, kuma ga mai nemansa.26Ya yi kyau a yi shiru a jira ceton Yahweh.27Abu nagari ne mutum ya jure karkiya a cikin ƙuruciyarsa.28Bari ya zauna shiru shi kaɗai sa'ad da aka ɗora masa shi.29Bari ya sa bakinsa a ƙura - mai yiwuwa akwai bege.
30Bari ya ba da kuncinsa ga mai marinsa, kuma bari ya cika da abin kunya.31Gama Ubangiji ba zai ƙi mu har abada ba,32Amma koda ya ke ya jawo ɓacin zuciya, zai ji tausayinmu bisa ga yawan kaunarsa marar ƙarewa,33Gama ba ya ƙuntatawa daga zuciyarsa, ko cakuna ga 'yan adam.
34Domin a rugurguza a karkashin kafafunsa dukkan ɗaurarrun duniya,35a hana yiwa mutum adalci a gaban maɗaukaki,36a hana adalci ga mutum - Ubangiji ba zai amince da abubuwa haka ba.
37Wa ya yi magana kuma ta cika, idan ba Ubangiji ya umarta ta ba?38Ba daga bakin Maɗaukaki ne masifu da nagargarun abubuwa ke fitowa ba?39Ta yaya wani rayayye zai yi gunaguni? Ta yaya mutum zai yi gunaguni game da hukuncin zunubansa?
40Bari mu auna hanyoyinmu mu gwada su, mu kuma juyo ga Yahweh.41Bari mu daga zukatanmu da hannuwanmu ga Allah a sammai.42"Mun yi laifofi da tayarwa, kuma baka gafarta ba.43Ka rufe kanka da fushi ka kuma kore mu, ka kashe kuma ba ka keɓe mu ba.
44Ka rufe kanka da giza-gizai yadda babu addu'ar da zata wuce ciki.45Ka maishe mu kamar ƙazantaccen juji na wofi a cikin al'ummai.46Dukkan maƙiyanmu sun la'anta mu,47fargaba da tsoro da lalacewa da hallaka sun auko mana.
48Idanuwana na fitar da maɓulɓulan hawaye saboda mutanena da aka hallaka.49Idanuwana za su zubar da hawaye marar ƙarewa; babu tsayawa,50har sai ya dubo ƙasa kuma Yahweh zai duba daga sama.
51Idanuwana sun sa ni matsananciyar wahala saboda dukkan 'yan matan birnina.52Maƙiyana na farauta ta kamar waɗanda ke kamun tuntsu; suna ta farauta ta ba dalili.53Sun jefa ni cikin rami suka kuma jefe ni da dutse,54har ruwa ya zuba a bisa kaina. Na ce, "An datse ni!'
55Yahweh, na kira sunanka daga rami mai zurfi.56Ka ji muryata sa'ad da na ce, 'Kada ka rufe kunnuwanka ga kukana na neman taimako.'57Ka zo kusa a ranar da na kira ka; ka ce, 'kada kaji tsoro.'
58Ubangiji, ka yi mani kariya, ka cece ni!59Yahweh, ka ga abu marar kyau da aka yi mani; ka zama alƙalina.60Ka ga zagi da ƙulle-ƙullen da suke yi mani.61Ka ji reninsu, Yahweh, da dukkan shirin da suke yi a kai na.
62Leɓunan waɗanda suke yi mani tayarwa, da zarginsu sun zo gãba da ni dukkan rana.63Duba yadda suke zama da tashi; suna yi mani ba'a da waƙoƙinsu.
64Yahweh, ka rama mani bisa ga abin da suka yi.65Za ka bar zukatansu a rashin kunya! Da ma hukuncinka ya auka masu!66Ka rarakesu a cikin fushinka ka hallaka su daga ƙarƙashin sammai, Yahweh!"

4

1Zinariyar ta zama gurbatacciya; tatacciyar zinariyar ta sake kamanni! An watsar da tsarkakakkun duwatsu a kwanar kowanne titi.2'Yan mazan Sihiyona masu daraja sun cancanci nauyin tacacciyar zinariya, amma yanzu ba suma cancanci tulunan yumɓu ba, aikin hannuwan maginin tukwane!

3Har ma diloli kan iya ba 'ya'yansu nono amma ɗiyar mutanena ta zama mai mummunan hali irin na garken jiminai da ke hamada.
4Harshen jariri saboda ƙishin ruwa ya liƙe a dasashinsa; yaran na neman abinci amma babu kome dominsu.5Waɗanda suka saba da idin abinci mai tsada sun gamu da yunwa a tituna; waɗanda aka san su da sa kyawawun kaya, yanzu suna kwance a juji wofi.
6Hukuncin ɗiyar mutanena ya fi na Sodom, wadda aka kawar da ita a ɗan lokaci kaɗan kuma babu wanda ya tada hannu na taimakonta
7Shugabaninta sun ɗara dusar ƙanƙara rashin aibi, sun kuma fi madara fari; jikunansu sun fi murjani kyau, fasalinsu kamar shudin saffiya.8Yanzu kammaninsu yafi kunkunniya baƙi. Ba sa ganuwa a tituna. Fatarsu ta liƙe a kasusuwansu; ta zama busasshiya kamar katako.
9Waɗanda aka kashe su da takobi suna da farinciki fiye da waɗanda aka kashe da yunwa, wanɗanda su ne suka zama lalatattun da aka sokesu da rashin wani girbi daga gona.10Hannuwan mata masu tausayi sun dafa 'ya'yansu; suka zamar masu abinci a lokacin da ake hallakar da ɗiyar mutanena.
11Yahweh ya nuna dukkan fushinsa; ya zubo zafin fushinsa. Ya kunna wuta a Sihiyona da ta cinye tushenta.
12Sarakunan duniya, ba su amince ba, da haka ma dukkan mazaunann duniya ba su amince ba cewa maƙiyan ko masu adawa za su iya shiga ƙofofin Yerusalem.13Wannan ya faru ne saboda zunuban annabawanta da laifofin firistocinta waɗanda suka zubar da jinin adalai a cikinta.
14Sun yi ta gararamba cikin makanta a tituna. Sun zama ƙazantattu sosai ta wurin jini da babu wanda aka yarda ya taba tufafinsu.15"Fita! Marar tsabta!" mutane na ta ihun kiransu. "Fita! Fita! Kar ku taɓa!" Haka suke gararamba; mutane faɗi a cikin al'ummai, "Ba za su ƙara zama a nan kuma ba."
16Yahweh da kansa ya watsar da su; bai sake kula da su kuma ba. Ba su girmama firistoci ba, kuma ba su nuna wani alheri ga dattawa ba.
17Idanuwanmu sun gaji da neman taimako a banza; daga wurin duban maƙiyanmu mun dubi al'ummar da ba za ta iya kuɓutar da mu ba.18Suka bi duk inda muka nufa, bamu iya tafiya a titunanmu ba. Ƙarshenmu ya kusato kuma an lisafta kwanakinmu, ƙarshenmu ya zo.
19Masu fafarar mu sun fi gaggafan sararin sama sauri. Suna korar mu zuwa duwatsu kuma suna yi mana kwanton ɓauna a cikin jeji.20Numfashin hancinmu - keɓaɓɓu na Yahweh - shi ne wanda aka cafko a ramukansu; wanda aka ce game da shi, "a ƙarkashin inuwarsa ne za mu zauna cikin al'ummai."
21Ki yi farinciki da murna, ɗiyar Idom, ke da kike zaune a ƙasar Uz. Amma a gare ki kuma za a fara shan ƙoƙon; za ki bugu har sai kin tuɓe kanki tsirara.22Ɗiyar Sihiyona, hukuncinki zai kawo ga ƙarshe, ba zai ƙara kwanakin bautarki ba. Amma zai hukunta ɗiyar Idom, zai hukunta; zai buɗe zunubanki

5

1Tuna, Yahweh, da abin da ya same mu. Ka duba ka ga abin ban kunyarmu.2Gãdonmu an bayar ga bãƙi, gidajenmu ga bãƙi.3Mun zama marayu, marasa ubanni, kuma waɗanda uwayensu sun zama kamar gwauraye.4Dole mu biya zinariya don ruwan shanmu, kuma dole mu biya zinariya kafin mu samu abincinmu.

5Waɗanda suke rarakarmu sun matso kusa da mu. mun gaji kuma ba mu samu hutu ba.6Mun ba da kanmu ga Masar da Asiriya don mu samu isasshen abinci.7Ubanninmu sun yi zunubi, kuma yanzu basu nan, kuma muna ɗaukar alhakin laifofinsu.
8Bãyi suna mulki a kanmu, kuma babu wanda zai kuɓutar da mu daga hannunsu.9Muna samun abincinmu ta sadaukar da ranmu ne kawai, saboda takobin cikin jeji.10Zafin fatarmu kamar zafin tanderu don tsananin yunwa.
11Ana yi wa mata fyaɗe a Sihiyona, har da 'yan mata ma a biranen Yahuda.12'Ya'yan sarakuna na rataya kansu da hannuwansu, kuma ba a nuna girmamawa ga dattawa.
13An sa samari su yi niƙan hatsi dole da dutsen niƙa, samari kuma suna jiri da kayan itace masu nauyi.14Dattawa sun bar kofar birnin kuma samarin sun bar raira waƙoƙinsu.
15Farincikinmu ya ƙare kuma rawarmu ta koma makoki.16Rawani ya faɗo ƙasa daga kanmu; kaiton mu, don mun yi zunubi!
17Domin wannan, zuciyarmu ta kamu da ciwo, kuma idanuwanmu sun dushe, saboda wannan idanuwanmu sun rage ƙarfi.18gama Tsaunin Sihiyona ya zama ƙango, diloli ke yawo a kansa.
19Amma kai, Yahweh, mulkinka har abada ne, kuma za ka zauna a kan kursiyinka daga tsara zuwa tsara.20Meyasa ka mance da mu har abada? Meyasa ka bar mu har tsawon kwanaki da yawa?21Ka komo da mu zuwa gare ka ya Yahweh, kuma zamu komo. ka sabunta kwanakinmu kamar yadda suke a dã -22har sai in ka ƙi mu ɗungum kuma ka yi fushi da mu fiye da misali.

Littafin ezekiyel

1

1A cikin shekara ta talatin, a wata na huɗu, rana ta biyar ga wata, ya kasance kuwa ina zaune cikin 'yan bauta a bakin Kogin Keba. Sai sammai suka buɗe, kuma Na ga wahayoyin Allah.2A rana ta biyar a wannan watan - shekara ta biyar kenan ta mijirar sarki Yehoyacin.3Maganar Yahweh ta zo ga Ezekiyel ɗan Buzi firist, a cikin ƙasar Kaldiyawa a hanyar Kogin Keba, hannun Yahweh kuma yana kansa a wurin.

4Daga nan sai na duba, sai ga iskar hadari na tasowa daga arewa; babban girgije mai wuta na haskakawa kewaye da shi da kuma a cikinsa, haske na kewaye da shi da cikinsa, kuma wutar tana da launin rawaya cikin girgijen.5Daga cikin tsakiyarsa siffar waɗansu masu rai huɗu. Wannan shi ne bayyanuwar su: suna da kamannin mutum,6amma kowannensu yana da fuskoki huɗu, kowacce halittar kuma nada fikafikai huɗu.
7Ƙafafunsu a miƙe suke, amma tafin sawayensu kamar kofaton ɗan maraƙi yana sheƙi kamar gogaggiyar tagulla.8Duk da haka suna da hannayen mutane a ƙarƙashin kowanne sashi huɗu na fukafukansu, dukkan su huɗun, fuskokinsu da fukafukansu haka suke:9fukafukansu na taɓa fukafukan ɗaya halittar, a cikin tafiyarsu ba su juyawa; maimakon haka, kowannensu a miƙe yake ɗoɗar.
10Kamannin fuskokinsu na kama da fuskar mutum. Su huɗun suna da fuskar zaki a sashin dama, su huɗun suna da fuskar bijimin sã sashin hagu. Su huɗun kuma suna da fuskar gaggafa.11Fukafukansu haka suke, fukafukansu kuma a shimfiɗe suke a sama, domin kowacce halitta nada fiffike biyu da ke taɓa fiffiken halittar, kuma fukafukan biyu sun rufe jikkunansu.12Kowanne ɗayansu ya tafi ɗoɗar, domin duk inda ruhu ya jagorance su suje, suna tafiya ba tare da sun juya ba.
13Game da kamannin rayayyun halittun nan kuwa, bayyanuwarsu na kama da garwashin wuta mai ci, kamar bayyanar cociloli; hasken wuta kuma na kai da komowa tsakanin halittun, kuma akwai haskawar walƙiya.14Rayayyun halittun nan suna matsawa da sauri gaba da baya, bayyanarsu kuma kamar walƙiya take!
15Daga nan sai na dubi rayayyun halittun nan, sai ga wani gargare a ƙasa a gefen rayayyun halittun tare da fuskokinsu huɗu.16Wannan shi ne bayyanuwa da tsarin gargarorin; kowanne gargare na kama da dutse mai tamani, dukkan su huɗun kamannin su ɗaya ne; bayyanuwarsu da ƙirarsu sai ka ce gargare mai ratsawa ta wani gargaren.
17Yayin da suke matsawa, suna tafiya ta kowanne kusurwarsu huɗu, ba tare da sun juya ba yayin da suke tafiya.18Zancen gammon gargarensu, masu tsawo ne da kuma ban tsoro, domin gammon gargaren na cike da idanu a kewaye.
19Duk sa'ad da rayayyun halittan nan suke matsawa, gargarorin na matsawa a gefensu. Sa'ad da rayayyun halittar suka tashi daga duniya, gargarorin suma su kan tashi sama.20Duk inda Ruhu zai tafi, sukan tafi, sai gargarorin su tashi a gefensu, gama ruhun rayayyun halittun yana cikin gargarorin.21Duk sa'ad da halittun suke matsawa, gargarorin suma suna matsawa; idan kuma halittun suka tsaya cik, gargarorin suma sukan tsaya cik; idan halittun suka tashi daga ƙasa, gargarorin sukan tashi a gefensu, saboda ruhun rayayyun halittun yana cikin gargarorin.
22A bisa kawunan rayayyun halittun nan akwai kamannin miƙaƙƙen sarari; yana kama da abu mai banmamaki da ƙyalli a miƙe bisa kawunansu sama.23A ƙarƙashin sararin, kowanne fukafukan halittun a miƙe suke sak kowanne yana taɓa fukafukan ɗaya rayayyen halittar. Kowannen rayayyen halittar kuma yana da fiffike biyu domin su rufe kansu; kowanne yana da biyu domin ya rufe jikinsa.
24Daga nan sai naji ƙarar fikafikansu. Kamar ƙarar ruwaye masu yawa. Kamar muryar mai Iko dukka a duk sa'ad da suke matsawa. Kamar ƙarar iskar hadari. Kamar ƙarar rundunar sojoji. Duk sa'ad da suka tsaya cik, sukan saukar da fukafukansu.25Sai murya ta zo daga saman sararin sama da kansu duk sa'ad da suka tsaya cik suka kuma sãki fukafukansu.
26A bisa sararin nan da ke sama da kansu akwai kamannin kursiyi da ke kama da bayyanuwar dutsen tama, a bisa kamannin kursiyin kuma akwai kamannin da ya yi kama da bayyanuwar mutum.
27Na ga siffa da bayyanuwar ƙarfe mai haskakawa da wuta a cikinsa tun daga bayyanuwar kwankwasonsa har sama; naga kuma daga bayyanuwar kwankwasonsa har zuwa ƙasa sai ka ce bayyanuwar wuta da haske ko'ina kewaye.28Kamar bayyanuwar bakangizo cikin giza-gizai a ranar da aka yi ruwa haka bayyanuwarar sheƙin hasken da ke kewaye da shi yake. Wannan kamar bayyanuwarar kamannin ɗaukakar Yahweh ne. Sa'ad da na gani, Na faɗi bisa fuskata, sai na ji murya tana magana.

2

1Ya ce mani, "Dan mutum, tashi bisa sawayenka; daga nan zan yi magana da kai."2Daga nan, da ya yi magana da ni, sai Ruhu ya shiga cikina, yasa na tsaya bisa sawayena, na kuma ji shi yana magana da ni.3Ya ce mani, "Dan mutum, ina aiken ka zuwa wurin mutanen Isra'ila, ga al'ummai masu tayarwa, da suka tayar mani. - da su da kakanninsu sun yi mani zunubi har ya zuwa yau!

4Zuriyarsu masu tsaurin fuskoki ne zukatansu kuma kangararru ne. Ina aiken ka wurinsu, kuma za ka ce masu, 'Wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh ya ce.'5Ko su saurara ko kada su saurara. Gama su gida ne mai tayarwa, amma a ƙalla za su sani cewa akwai annabi a tsakiyarsu.
6Kai, ɗan mutum, kada ka ji tsoron su ko maganganunsu. Kada ka ji tsoro, koda yake kana tare da sarƙaƙƙiya da ƙayayuwa koda yake kuma kana zaune da kunamai. Kada ka ji tsoron maganganunsu ko ka damu da irin fuskokinsu, da shike su gida ne mai tayarwa.
7Amma za ka faɗi maganganuna a gare su, ko su ji ko kada su ji, gama suna cika da tayarwa.8Amma kai, ɗan mutum, ka saurari abin da nake faɗa maka. Kada kayi tayarwa kamar wannan gidan mai tayarwa. Ka buɗe bakinka kaci abin da Na ke shirin ba ka!"
9Daga nan Na duba, sai a ka miƙo mani hannu; cikin sa rubutaccen littafi ne naɗaɗɗe.10Ya baza shi a gaba na; yana da rubutu cikinsa da bayansa, abubuwan da aka rubuta a kai sune koke-koke da makoki da kuma kaito.

3

1Sai ya ce mani, "Ɗan mutum, ka ci abin da ka samu. Ka ci littafin nan, daga nan ka tafi ka yi magana da gidan Isra'ila."2Sai na buɗe bakina, ya kuma ciyar da ni da littafin.3Ya ce mani, "Dan mutum, ka ciyar da tunbinka ka kuma ƙosar da cikinka da littafin da Na ba ka!" Sai na ci shi, a cikin bakina yana da zaƙi kamar zuma.

4Sai ya ce mani, "Ɗan mutum, ka tafi gidan Isra'ila ka faɗi maganganu na a gare su.5Gama ba'a aike ka wurin mutane masu bãƙon harshe ba, ko waɗanda harshensu yake da wahala ba, amma zuwa gidan Isra'ila -6ba wurin mutane masu yawa ba da bãƙon harshe ko waɗanda harshensu keda wuya ba, waɗanda ba za ka iya fahimtar kalmominsu ba. Tabbas idan da na aike ka wurinsu, da za su saurare ka.7Amma, gidan Isra'ila ba za su yadda su saurare ka ba, gama ba su yadda su saurare ni ba. Gama dukkan gidan Isra'ila masu taurinkai ne masu taurin zuciya kuma.
8Duba! Na sa fuskarka ta taurare kamar fuskokinsu girarka kuma ta taurare kamar girarsu.9Na maida girarka kamar lu'u-lu'u, yafi tsagewar dutse! kada ka ji tsoron su ko ka karaya da irin fuskokinsu, tunda gida ne mai tayarwa."
10Sai ya ce mani, "Ɗan mutum, dukkan kalmomin dana sanar da kai ka ɗauke su cikin zuciyarka ka kuma ji su da kunnuwanka!11Daga nan ka tafi wurin 'yan bauta mutanenka, ka yi magana da su. Ka ce masu, 'Wannan ne abin da Ubangiji Yahweh ya ce,' ko su ji ko kada su ji."
12Daga nan sai Ruhu ya ɗaga ni sama, a baya na kuma sai na ji babbar muryar girgizar ƙasa: "Albarka ta tabbata ga ɗaukakar Yahweh daga wurinsa!"13ƙarar fukafukan masu ran nan ne yayin da suke taɓa junansu, da ƙarar gargarorin da ke tare da su, da ƙarar babbar girgizar ƙasa.
14Sai Ruhu ya ɗauke ni sama ya tafi da ni, na kuma tafi da ɓacin rai cikin ruhuna da zafin fushi, gama hannun Yahweh yana danne ni da iko!15Sai na tafi wurin 'yan bauta a Tel-abib waɗanda suke zama a bakin kogin Keba, na zauna cikinsu har kwana bakwai, zugum cikin mamaki.
16Daga nan ya kasance bayan kwanaki bakwai ɗin sai maganar Yahweh ta zo gare ni, tana cewa,17"Ɗan mutum, Na maida kai mai tsaro domin gidan Isra'ila, domin haka sai ka ji maganar bakina, ka kuma ba su gargaɗi na.18Sa'ad da na ce da mugu, 'Hakika za ka mutu' kai kuma ba ka gargaɗe shi ba ko ka yi maganar gargaɗi ga mugu a kan miyagun ayyukansa ba, domin ya rayu - mugun za ya mutu saboda zunubinsa, amma zan biɗi haƙƙin jininsa a hannunka.19Amma idan ka gargaɗi mugun, kuma bai juya daga muguntarsa ba ko yabar miyagun ayyukansa ba, zai mutu domin zunubinsa, amma kai za ka ceci ranka.
20Kuma idan adali ya juya daga adalcinsa ya aikata ba abin da dai-dai ba, kuma na sa abin tuntuɓe a gabansa, zai mutu. Saboda ba kagargaɗe shi ba, zai mutu cikin zunubansa, ba kuwa zan tuna da ayyukansa na adalci da ya yi ba, amma zan biɗi haƙƙin jininsa a hannunka.21Amma idan ka gargaɗi adalin mutum ya daina yin zunubi shi kuwa bai ƙãra yin zunubi ba, lallai zai rayu tun da shi ke an gargaɗe shi; kai kuma ka ceci ranka."
22Hannun Yahweh yana kaina a wurin, sai ya ce mani, "Tashi! Ka fita zuwa sarari, a can kuma zan yi magana da kai!"23Sai na tashi na fita zuwa cikin sarari, a can ne ɗaukakar Yahweh na tsayawa, kamar ɗaukakar dana gani a gefen Kogin Keba; sai na faɗi a bisa fuskata.
24Sai Ruhu ya sauko mani ya tsaida ni bisa sawayena; sai ya yi magana da ni, ya ce mani, "Jeka ka kulle kanka cikin gidanka,25domin yanzu, ɗan mutum, za su sa igiyoyi a kanka su ɗaureka domin kada ka iya fita cikinsu.
26Zan sa harshenka ya liƙe wa rufin bakinka, za ka kasa yin magana, ba za ka iya tsauta masu ba, da shi ke su gidane masu tayarwa.27Amma sa'ad da na yi magana da kai, Zan buɗe bakinka za ka ce masu, 'Wannan shi ne abin da Yahweh ya faɗi,' Wanda ya ji, ya ji, Wanda ya ƙi ji ya ƙi ji, gama su gida ne mai tayarwa!"

4

1"Amma kai, ɗan mutum, sai ka ɗaukarwa kanka tubali ka sa a gabanka. Ka sassaƙa birnin Yerusalem a kansa.2Daga nan kayi sansani kewaye da shi, sai ka gina kagarai gãba da ita. A kuma tayar da masu kai mata hari, a kuma sa mata sansani kewaye da ita.3Daga nan ka ɗaukarwa kanka faifan ƙarfe ka kuma yi amfani da shi a matsayin katangar ƙarfe tsakaninka da birni ka kuma sa fuskarka gãba dashi, gama za a yi masa sansani, kuma kai zaka sa sansanin gãba dashi. Wannan zai zama alama ga gidan Isra'ila.

4Daga nan, sai ka kwanta a gefen hannunka na hagu sai ka sa zunubin gidan Isra'ila a kansa; za ka ɗauki zunubinsu bisa ga yawan kwanakin da kake kwantawa gãba da gidan Isra'ila.5Ni da kaina na sanya maka kwana ɗaya ya wakilci shekara ta hukuncinsu: kwanaki 390! Ta haka nan, za ka ɗauki zunubin gidan Isra'ila.
6Idan ka gama waɗannan kwanaki, sai ka sake kwanciya a sashin hannunka na dama kuma, gama za ka ɗauki zunubin gidan Yahuda har kwana arba'in. Na sanya maka kwana ɗaya domin shekara guda.7Ka sa fuskarka wajen sansanin Yerusalem, da hannunka marar rufi ka yi anabci gãba da ita.8Duba! I na sanya maɗaurai a kanka yadda ba za ka juya daga wannan sashi zuwa wancan ba har sai lokacin da ka gama kwanakin sansaninka.
9Ka ɗaukar wa kanka alkama, bali, wake, acca, gero da maiwa; ka sa su cikin tukunya ɗaya ka yi gurasa da su bisa ga yawan kwanakin da za ka kwanta a sashinka. Za ka ci su har kwanaki 390.10Abincin da za ka ci zai zama bisa ga awo, shekel ashirin kowacce rana, za ka ci bisa ga lokutan da a ka ƙaiyade kowacce rana.11Daga nan za ka sha ruwa, bisa ga aunawa sau shida bisa ga ka'ida za ka sha.
12Za ka ci a matsayin waina ta bali, amma za ka toya ta a kan idonsu da kãshin da ke fitowa daga jikin mutum!"13Gama Yahweh ya ce, "Wato abincin da 'ya'yan Isra'ila za su ci zai zama marar tsabta, a can cikin al'ummai inda na kora su."
14Amma, Na ce, "Kaito! Ubangiji Yahweh! Ban taɓa ƙazantuwa ba! Ban taɓa cin mushe ba ko abin da namun jeji suka kashe, tun ina matashi har yanzu, kuma ba wani ƙazantaccen nama da ya taɓa shiga bakina!"15Sai ya ce mani, "Duba, na baka kãshin shanu maimakon kãshin mutum a kansa za ka shirya abincinka."
16Ya sake ce mani, "Ɗan mutum! Duba! Ina karya sandar abincin da ke cikin Yerusalem, za su ci abinci suna aunawa cikin juyayi za kuma su sha ruwa lokacin da suke aunawa cikin rawar jiki.17Saboda za su rasa abinci da ruwa, kowanne mutum zai dubi ɗan'uwansa da damuwa su kuma lalace saboda laifinsu."

5

1"Daga nan kai, Ɗan mutum, ka ɗauki takobi mai kaifi kamar askar mai aski domin kanka, ka aske kanka da gemunka, daga nan ka ɗauki ma'auni ka raba gashin kanka uku.2Ka ƙone kashi ɗaya cikin wuta a tsakiyar birnin lokacin da kwanakin yiwa birnin sansani suka cika, ka ɗauki kashi ɗaya na gashin ka buge shi da takobi ko'ina kewayen birnin. Daga nan sai ka watsar da kashi ɗaya a iska, daga nan zan zare takobi in runtumi mutanen.

3Amma ka ɗibi gashi kaɗan daga cikinsu ka ɗaure su cikin rigarka.4Daga nan sai ka ɗebi gashi mafi yawa ka jefa cikin tsakiyar wuta; ka ƙone su cikin wuta; daga nan wuta za ta fito ta shiga dukkan gidan Isra'ila."
5Ubangiji Yahweh ya faɗi haka, "Wannan ita ce Yerusalem na sanya ta a tsakiyar al'ummai, na kuma kewaye ta da sauran ƙasashe.6Amma ta ƙi shari'ata yayin da ta aikata mugunta fiye da yadda sauran ƙasashe suka yi, ta tayarwa umarnaina fiye da ƙasashen da ke kewaye da ita. Mutanen sunƙi hukuntaina ba su kuma yi tafiya cikin farillaina ba."
7Domin wannan Yahweh ya ce, "Saboda kunfi al'ummai waɗanda ke kewaye daku taurinkai ba ku yi tafiya cikin umarnaina ba kuma ba ku kiyaye dokokina ba ko ma dokokin al'umman da ke kewaye daku,"8domin wannan Yahweh ya ce, "Duba! nima ina gãba da ke. Zan aiwatar da hukuntai a tsakiyarki domin al'ummai su gani.
9Zan yi maku abin da ban taɓa yi ba da kuma irin wanda ba zan sake yin irin sa ba, saboda dukkan ayyukan banƙyamarku.10Domin wannan a tsakiyarki ubanni za su ci naman 'ya'yansu, 'ya'ya kuma za su ci naman iyayensu, da shi ke zan aikata hukunci a kanku zan kuma watsar da dukkanku da kuka rage ko ina
11Na rantse da raina - Wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - hakika saboda kun tozartar da wurina mai-tsarki da dukkan kayanku na banƙyama da al'amuranku na banƙyama, domin wannan Ni da kaina zan rage yawanku; idona kuma ba zai dube ku da rahama ba, ba kuma zan bar ku ba.12Kashi ɗaya cikin ukunku za su mutu da annoba, da yunwa kuma za su ƙare a tsakiyarku. Kashi ɗaya cikin ukunku kuma za su faɗi da kaifin takobi kewaye daku. Sulusin na ukun kuma zan watsar da su a kowanne sashi, in kuma zare takobi in fafare su.
13Daga nan fushina zai kammala, zan kuma sa zafin hasalata akansu ya huce. Zan gamsu, kuma za su sani cewa Ni, Yahweh na yi magana cikin fushina sa'ad da na gama aikin hasalata gãba da su.14Zan maishe ku kango abin raini ga al'umman da ke kewaye daku, a kan idon duk wanda ke wucewa.
15Hakan nan Yerusalem za ta zama wani abin wulaƙantarwa da ba'a ga mutane, abin gargaɗi da tsoratarwa ga al'ummai da ke kewaye daku. Zan zartar da hukuntai gãba daku cikin fushi da hasala, da tsautawa mai zafi - Ni, Yahweh na furta wannan!16Zan aikar da kibau masu zafi na yunwa gãba daku da za su zama dalilin da zan hallaka ku. Zan ƙara maku yunwa zan kuma datse abincin da kuke dogara da shi.17Zan aikar da yunwa da bala'o'i gãba daku za ku zama marar 'ya'ya. Annoba da jini za su ratsa ta tsakiyarku, zan kawo takobi gãba daku - Ni, Yahweh na furta wannan."

6

1Maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, ka sa fuskarka gãba da tsaunukan Isra'ila ka yi anabci a kansu.3Ka ce, "Tsaunukan Isra'ila, ku ji maganar Ubangiji Yahweh! Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan ga tsaunuka da tuddai ga rafuffuka da kwarurruka: Duba! Zan kawo takobi gãba da ku, zan kuma hallaka wurarenku masu daraja.

4Daga nan bagadanku za su zama kangaye ginshiƙansu za a hallakar da su, zan jefar da gawarwakinku gaban gumakansu.5Zan jera gawarwakin mutanen Isra'ila a gaban gumakansu, in warwatsar da ƙasusuwanku wajen bagadanku.
6Duk inda kuka zauna, biranen za su zama marasa amfani, wuraren bisa kuma za su zama kufai, domin bagadanku su zama kufai su zama kangaye. Daga nan za'a farfashe su kuma za su ɓace, za a datse ginshiƙanku ayyukanku kuma za a shafe su kaf.7Matattu za su faɗi a tsakiyarku kuma za ku sani Ni ne Yahweh.
8Amma zan tsare ringi daga cikin ku, waɗansu kuma za su tsere wa takobi daga cikin al'ummai, sa'ad da aka warwatsar da ku ko'ina cikin ƙasashe.9Daga nan su da suka tsira za su tuna da ni cikin al'ummai inda za a kai su bauta, za su tuna yadda zuciyata tayi ƙũna ta wurin zuciyarsu mazinaciya wadda ta juya daga gare ni, ta idanunsu kuma da ke ƙara sasu bin gumakansu. Za su ji ƙyamar kansu suna duban dukkan muguntar da suka aikata da dukkan ƙazantarsu.10Za su sani cewa Ni ne Yahweh. Saboda wannan dalilin Na ce Zan kawo wannan muguntar a gare su.
11Ubangji Yahweh ya ce: Ka tãɓa hannayenka ka buga ƙafarka! Ka ce, 'Kaito!' saboda dukkan miyagun ayyukan ƙazanta na gidan Isra'ila! Gama za su faɗi ta kaifin takobi da yunwa da annoba.12Na nesa za su mutu ta annoba, na kusa zai faɗi ta wurin takobi. Waɗanda suka rage suka rayu za su mutu da yunwa. Ta haka ne zan cika hasalata a kansu.
13Daga nan za ku sani ni ne Yahweh, sa'ad da matattunsu suka kwanta wurin gumakansu, kewaye da bagadansu, a kan kowanne tudu mai bisa - kan dukkan ƙwanƙoli tsaunuka, da ƙarƙashin kowanne itace mai inuwa kuma da rimi mai kauri - da wurare inda suke ƙona turare ga dukkan gumakansu.14Da hannuna zan kai sãra in maida ƙasar kango da kufai, tun daga jeji har zuwa Dibla, ko'ina a dukkan wuraren zamansu. Daga nan za su sani cewa Ni ne Yahweh."

7

1Kalmar Yahweh ta zo wurina, cewa,2"Kai, Ɗan mutum - Ubangiji Yahweh ya faɗi haka ga ƙasar Isra'ila." 'ƙarshe! ƙarshe ya zo ga iyakoki huɗu na ƙasar.

3Yanzu ƙarshenki yana kanki, gama ina aikar da fushina a kanki, zan shar'anta ki bisa ga ayyukanki; zan kuma kawo dukkanharamtattun ayyukanki a kanki.4Gama idanuna ba za su tausaya maki ba, ba kuma zan keɓe ki ba. Maimakon haka, Zan kawo al'hakin al'amuranki a kanki, haramtattun ayyukanki kuma a cikinki, domin ki sani cewa Ni ne Yahweh.
5Ubangiji Yahweh ya ce: Bala'i! Bala'i na musamman! Duba, yana zuwa.6Lallai matuƙa tana zuwa. Matuƙa ta farka a kanki. Duba, tana zuwa!7hukuncinku zai zo maku ku mazaunan ƙasar. Lokaci ya zo; ranar hallaka ta kusa, tsaunuka kuma ba za su ƙara yin murna ba.
8Yanzu bada daɗewa ba zan zuba maku hasalata in cika fushina a kanku lokacin da nake hukunta ku bisa ga al'amuranku in kuma kawo dukkan al'hakin ƙazantarku a kanku.9Gama idanuna ba za su tausaya ba, ba kuma zan keɓe ku ba. Kamar yadda kuka yi haka zan yi maku; haramtattun ayyukanku za su kasance a tsakiyarku domin ku sani cewa Ni ne Yahweh wanda yake hukuntaku.
10Duba, ranar! Duba, tana zuwa! hukunci ya fita waje! Sandar tayi fure, girmankai ya yi toho!11Tashin hankali ya yi girma zuwa cikin sandar mugunta - babu wani daga cikinsu, ko wani daga cikin taronsu, ko daga cikin wadatarsu, babu wani abu nasu mai muhimmanci da zai dawwama!
12Lokaci na zuwa; lokaci ya zo kusa. Kada ka bari mai saye ya yi farinciki, ko mai sayarwa ya yi makoki, tunda fushina yana kan dukkan taronsu!13Gama mai sayarwa ba zai dawo ƙasar da ya yi sayarwa ba muddan dukkansu suna raye, saboda wahayin game da dukkan taron ba za a sauya ba; kuma saboda zunubansu, ba waninsu da zai ƙarfafa!
14Sun busa ƙaho sun shirya komai, amma ba bu mai takawa zuwa yaƙi; tunda fushina yana kan dukkan taron jama'ar.15Takobi na waje, yunwa kuma da annoba suna cikin ginin. Waɗanda ke cikin saura za su mutu da takobi, yayin da yunwa da annoba kuma za su cinye waɗanda ke cikin birnin.16Amma waɗansu za su tsira daga cikinsu, za su gudu zuwa tsaunuka. Kamar kurciyoyin kwarurruwa, dukkansu za su yi makoki - kowanne mutum saboda laifinsa.
17Kowanne hannu zai zama raunanne kowacce gwiwa kuma za ta zama marar ƙarfi kamar ruwa,18za su sa tsummoki, tsoro kuma zai rufe su; kunya za ta kasance a kowacce fuska, saiƙo kuma a dukkan kawunansu.19Za su jefar da azurfarsu cikin karafku zinariyarsu kuma za ta zama kamar juji. Azurfarsu da zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba a ranar fushin Yahweh. Rayukansu ba za su tsira ba, ba za a ƙosar da yunwarsu ba, domin laifofinsu sun zama dalilin tuntuɓe.
20A cikin taƙamarsu suka ɗauki Kyaun kayan duwatsun adonsa, da su kuma suka yi siffofinsu na gumaka da ƙazantattun abubuwansu. Domin wannan, Ina maida waɗannan abubuwa su zama marasa tsarki a gare su.21Daga nan zan bada waɗannan abubuwa a cikin hannun bãƙi a matsayin ganima ga kuma miyagun duniya a matsayin ganima, za kuma su ƙazantar da su.22Daga nan zan juyar da fuskata daga gare su sa'ad da suka ƙazantar da ƙaunataccen wurina; 'yan adawa za su shiga su ƙazantar da shi.
23Kayi sarƙa, saboda ƙasar ta cika da hukuncin jini, birnin kuma na cike da tashin hankali.24Domin in kawo ƙasashe mafi mugunta, za su kuma mallaki gidajensu, zan kuma kawo ƙarshen girmankan masu ƙarfi, gama za a ƙazantar da wurarensu masu tsarki!25Tsoro zai auko! Za su nemi salama, amma ba za a samu ba.
26Masifa biye da masifa za ta zo, kuma za a samu jita-jita bayan jita-jita. Sa'an nan za su nemi wahayi daga wurin annabi, amma shari'a za ta lalace daga Firist shawara kuma daga wurin dattawa.27Sarki zai yi makoki yarima kuma zai rufe kansa da fargaba, yayin da kuma hannayen mutanen ƙasar makyarkyata cikin tsoro. Bisa ga hanyoyinsu zan aikata masu wannan! Zan hukunta su bisa ga matakinsu har sai sun sani cewa Ni ne Yahweh.'"

8

1Ana nan a shekara ta shida cikin wata na shida, a rana ta biyar ga watan, Ina zaune cikin gidana dattawan Yahuda kuma suna zaune a gabana, sai hannun Yahweh ya sake saukowa a kaina a wurin.2Sai na duba, sai ga alamar wani mai kama da bayyanuwar mutum. Daga bayyanuwar ƙugunsa zuwa ƙasa akwai wuta. Daga kuma ƙugunsa zuwa sama akwai bayyanuwar wani abu mai ƙyalli, kamar ƙarfe mai sheƙi.

3Daga nan sai ya miƙa abu mai kama da hannu, ya ɗauke ni ta gashin kaina; Ruhun kuma ya ɗaga ni tsakanin duniya da sama, a kuma cikin wahayoyi daga wurin Allah, sai ya kawo ni Yerusalem, zuwa wurin shiga ƙofar arewa ta ciki, inda gunki mai cakuno babban kishi ke tsayawa.4Daga nan duba, ɗaukakar Allah na Isra'ila na wurin, bisa ga wahayin da na gani a sarari.
5Daga nan sai ya ce mani, "Ɗan mutum, ka ɗaga idanunka zuwa arewa." Sai na ɗaga idanuna zuwa arewa, daga arewacin ƙofar da ke bida wa zuwa bagadi, a ƙofar shigar, gunkin kishi ne.6Sai ya ce mani, "Ɗan mutum, ko ka ga abin da suke yi? Waɗannan sune haramtattun ayyuka masu girma da gidan Isra'ila ke yi da nufin su sani in tafi nesa da wurina mai tsarki. Amma za ka juya ka ga waɗansu haramtattun ayyukan mafi girma."
7Daga nan sai ya kawo ni bakin ƙofar farfajiya, sai na duba, sai kuma ga rami a jikin bango.8Sai ya ce mani, "Ɗan mutum, ka yi gini cikin bangon nan" Sai na gina cikin bangon, sai ga wata ƙofa.9Daga nan sai ya ce mani, "Je ka ka ga haramtattun ayyukan muguntar da suke yi a nan."
10Sai na shiga ciki na duba, kuma duba! Akwai kowanne abu mai rarrafe da ƙazantattun bisashe! Kowanne gunki na gidan Isra'ila an sasssaƙa siffarsa a jikin bangon kewaye ko'ina.11Dattawa saba'in na gidan Isra'ila suna wurin, Yãzaniya ɗan Shafan kuma na tsaye a tsakiyarsu. Suna tsaye a gaban siffofin, kowanne mutum na riƙe da kaskon ƙona turare a hannunsa yadda ƙanshin girgijen turaren kuma ya hau sama.
12Sai ya ce mani, "Ɗan mutum, ko ka ga abin da dattawan gidan Isra'ila ke aikatawa a cikin duhu? Kowannesu na aikata wannan a cikin ɓoyayyen wurin ɗakin gunkinsa, gama sun ce, 'Yahweh ba ya ganin mu! Yahweh ya yi watsi da ƙasar."13Daga nan sai ya ce mani, "Ka sake juyawa ka ga waɗansu manyan haramtattun ayyuka da suke yi."
14Gaba kuma sai ya kawo ni wajen ƙyauren ƙofar gidan Yahweh wadda ke gefen arewa, kuma duba! Mata na zaune suna makoki domin Tamuz.15Sai ya ce mani, "Ɗan mutum, ko ka ga wannan? Ka sake juyawa za ka ga manyan haramtattun ayyuka fiye da waɗannan."
16Ya kawo ni cikin farfajiya ta cikin gidan Yahweh, duba kuma! A ƙofar shiga haikalin Yahweh tsakanin harabar da bagadi, akwai maza ashirin da biyar sun juyawa haikalin Yahweh baya fuskokinsu na fuskantar gabas, suna kuma yiwa rana sujada.
17Sai ya ce mani, Ɗan mutum, ka ga wannan? Wannan ƙaramin abu ne ga gidan Yahuda, su yi waɗannan haramtattun ayyuka da suke yi a nan? Gama sun cika ƙasar da tashin hankali sun sake juyawa kuma sun cakune ni ga yin fushi, suna sanya reshe cikin hancinsu.18Ni ma zan yi aiki a cikinsu; Idanuna ba za su tausaya masu ba, ba kuwa zan raga masu ba. Koda za su yi kuka da babbar murya a kunnuwana, Ba zan ji su ba."

9

1Sa'an nan sai ya yi kuka da babbar murya a kunnena, ya ce, "Bari matsara su taso zuwa birni, kowanne da makamin hallakarwarsa a hanunsa."2Daga nan duba! Mutane shida suka zo daga hanyar ƙofa ta bisa, wadda ke fuskantar arewa, kowanne mutum da makamin yankansa a hanunsa. Akwai mutum ɗaya a tsakiyarsu saye da tufafin linin a jikinsa da abin rubutu a gefensa. Suka shiga ciki suka tsaya wajen bagadi na tagulla.

3Daga nan sai ɗaukakar Allah na Isra'ila ta hau daga wurin kerubim inda take a dã har zuwa bakin ƙofar gidan. Sai ya kira mutumin da ke saye da tufafun linin wanda yake da kayan rubuta a gefensa.4Yahweh ya ce masa, "Ka ratsa ta tsakiyar birnin - ta tsakiyar Yerusalem - ka sa shaida a goshin mutanen da ke nishi da tsaki game da dukkan haramtattun ayyukan da ake yi cikin tsakiyar birnin."
5Daga nan na ji ya yi magana da sauran ya ce, "Ku ratsa birnin ku bi bayansa ku yi kisa. Kada ku bari idanunku su tausaya, kada kuma ku raga wa kowa.6Ko tsoho, ko saurayi, ko budurwa, ko ƙananan yara, ko mata. Ku kashe dukkan su! Amma kada ku kusanci kowanne mutum da ke da shaida a goshinsa. Ku fara daga wurina mai tsarki!" Sai suka fara da dattawa waɗanda ke a gaban gidan.
7Sai ya ce masu, "Ku ƙazantar da gidan, ku cika harabunsa da matattu. Ku zarce gaba" Sai suka fita waje suka kai wa birnin hari.8Yayin da suke kai masa harin, sai na sami kaina ni kaɗai sai na faɗi a fuskata na yi kuka na ce, "Ah, Ubangiji Yahweh, za ka hallakar da dukkan sauran Isra'ila cikin hasalar fushin da kake zubawa kan Yerusalem?"
9Sai ya ce mani, "Zunubin gidan Isra'ila da na Yahuda ya ƙasaita ƙwarai. Ƙasar cike take da jini kuma birnin cike yake da ayyukan ƙazanta, tun da suka ce, 'Yahweh ya manta da ƙasar,' kuma Yahweh ba ya gani!'10To daga nan, ni ma idanuna ba za su duba da tausayi ba, kuma ba zan raga masu ba. Maimakon haka, zan kawo masu duk alhakinsu a kansu."11Duba! Mutumin da ke saye da tufafin linin wanda ke da kayan rubutu a gefensa ya dawo. Ya kawo rahoto ya ce, "Na aiwatar da dukkan abin da ka umarta."

10

1Da na duba ta sararin da yake bisan kawunan kerubobin; wani abu ya bayyana a samansu kamar yakutu da bayyanuwa mai kamannin kursiyi.2Daga nan Yahweh ya yi magana da mutumin da ke saye da tufafin linin ya ce, "Jeka tsakaningargarorin da ke ƙarƙashin kerubobin, ka cika hannuwanka biyu da garwashin wuta mai zafi daga tsakanin kerubobin ka watsa su bisa birnin." Daga nan mutumin ya tafi ni yayin da nake kallo.

3Kerubobin suna tsaya a gefen dama na gidan sa'ad da mutumin ya shiga ciki, sai girgije ya cika harabar da ke can ciki.4Ɗaukakar Yahweh ta taso daga kerubobin ta tsaya a ƙyauren gidan. ta cika gidan da girgijen, kuma harabar ta cika da hasken ɗaukakar Yahweh.5Aka kuwa ji ƙarar fukafukan kerubobin har can wajen harabar, kamar muryar Allah maɗaukaki sa'ad da yake magana.
6Ana nan kuma, sa'ad da Allah ya umarce mutumin da ke saye da tufafin linin ya ce, "Ka ɗebi wuta daga tsakanin gargarorin da ke tsakanin kerubobin," mutumin ya je ciki ya tsaya a gefen gargare ɗaya.7Kerubim ɗaya ya miƙa hannunsa tsakanin kerubobin zuwa wutar da ke tsakanin kerubobin, ya ɗiba ya zuba a hannun wanda ke saye da tufafin linin. Mutumin ya karɓa ya tafi waje.8Na kuwa gani a kerubobin wani abu kamar hannun mutum a ƙarƙashin fukafukansu.
9Saboda haka na duba, sai ga! gargarori huɗu a gefen kerubobin - gargare ɗaya a gefen kowanne kerubim guda - kuma fasalin gargarorin na kamar dutse mai daraja.10dukka huɗun fasalinsu dai-dai yake, kamar gargare na gittawa cikin wani gargaren.11Sa'ad da suke matsawa, suna tafiya a dukkan shiyyoyi huɗun. kuma ba tare da juyawa ga wata shiyyar ba, Maimakon haka, duk inda kan yake fuskanta, nan suke bin shi. Ba su kuwa juyawa ga wata shiyya sa'ad da suke tafiya.
12Dukka jikinsu - haɗe da bayansu da hannuwansu da fukafukansu - na rufe da idanuwa, kuma idanuwan sun rufe gargarori huɗun dukka kewaye kuma.13Sa'ad da nake saurarawa, gargarorin suna kira, "guguwa."14Kowanne ɗayansu na da fuskoki huɗu; fuska ta fari ta Kerubim ce, fuska ta biyu ta mutum ce, fuska ta uku ta zaki ce, fuska ta huɗu kuma ta gaggafa ce
15Daga nan kerubobin - waɗannan ne hallitu masu rai da na gani ta Kogin Keba - suka taso.16Duk sa'ad da Kerubobin suka matsa, gargarorin za su bi su gefensu, kuma duk sa'ad da kerubobin suka ɗaga fukafukansu su tashi daga ƙasa, gargarorin ba su juyewa. Suna dai tsaye a gefensu.17Sa'ad da kerubobin suka tsaya cik, gargarorin suma sai su tsaya cik, kuma idan suka tashi sama, gargarorin suma sai su tashi tare da su, gama ruhun halittar mai rai na cikin gargarorin.
18Sa'an nan ɗaukakar Yahweh ta fita daga ƙyauren gidan ta tsaya a kan kerubobin.19Kerubobin suka ɗaga fukafukansu suka tashi daga ƙasa a fuskata sa'ad da suka fita, gargarorin kuma suka yi kamarsu a gefensu. Suka tsaya a bakin kofar shiga ta wajen gabas, ta gidan Yahweh, sai ɗaukakar Allah na Isra'ila ta zo gare su daga sama.
20Waɗannan ne halittu masu rai dana gani a ƙarƙashin Allah na Isra'ila ta Kogin Keba, shi yasa na sani cewa su keruubobi ne!21Kowannen su na da fuskoki huɗu da fukafukai huɗu, da kamannin hannuwan mutum a ƙarƙashin fukafukansu,22kuma kamannin fuskokinsu na kama da wadda na gani a ruya a Kogin Keba, kuma kowannen su ya tafi gaba kai tsaye.

11

1Sai Ruhun ya ɗago ni sama ya kawo ni ƙyauren gabas na gidan Yahweh, yana kuma fuskantar gabas, a bakin ƙofar akwai mutum ashirin da biyar. Na ga Yãzaniya ɗan Azzu da Felatiya ɗan Benayya shugabanin mutanen, a cikinsu.

2Allah ya ce mani, "Ɗan mutum, waɗannan ne mutanen da ke ƙirkiro zunubai da kuma yin miyagun shirye-shirye a wannan birnin.3Suna cewa, 'Ba yanzu ne lokacin gina gidaje ba, wannan birnin shi ne tukunyar, kuma mu ne naman.'4Saboda haka ka yi annabci gãba da su. Ɗan mutum, ka yi annabci."
5Sai Ruhun Yahweh ya sauko mani ya kuma ce mani, "Ka ce: Ga abin da Yahweh ya ce, "Gidan Isra'ila wannan shi ne abin da kuke cewa; gama na san abin da ke tafiya a zuciyarku.6Kun yawaita mutanen da kuka kashe a wannan birnin kuma kun cika karafku da su.7Saboda haka, Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Mutanen da kuka kashe, waɗanda kuka sa jikunansu a tsakiyar UYerusalem, su ne naman, kuma wannan birnin ne tukunyar. Amma za a fitar daku daga tsakiyar wannan birnin.
8Kun ji tsoron takobi, saboda haka ina tahowa da takobi a kanku - wannan ne furcin Ubangiji Yahweh.9Zan fitar daku daga cikin birnin, in sa ku a hannun bãƙi, gama zan kawo hukunci a kanku.10Za ku faɗi ta takobi. Zan hukunta ku a cikin iyakar Isra'ila domin ku sani cewa Ni ne Yahweh.
11Wannan Birnin ba zai zama tukunyar dahuwarku ba, ko ku zama naman cikinta ba. Zan hukunta ku a kan iyakar Isra'ila.12Sa'an nan za ku sani cewa Ni ne Yahweh, wanda kuka ƙi yin tafiya bisa ga tafarkinsa wanda kuma kuka ƙi aikata umarninsa. Maimakon haka, sai kuka aikata dokokin al'umman da ke kewaye daku."
13Hakanan kuma sa'ada da nake annabci, Felatiya ɗan Benayya, ya rasu. Sai na faɗi fuskata a ƙasa na yi kuka da murya mai ƙarfi na ce, "Kash, ya Ubangiji Yahweh, za ka hallakar da ragowar Isra'ila ne kakaf?"
14Maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,15"Ɗan mutum, 'yan'uwanka! 'Yan'uwanka! Mutanen danginka da dukkan gidan Isra'ila! Dukkansu ne waɗanda a ka yi magana game da su ta wurin waɗanda ke zama cikin Yerusalem, 'Su na nesa da Yahweh! Wannan ƙasar an bada ita gare mu a matsayin mallakarmu.'
16Saboda haka ka ce, 'Ubangiji Yahweh ya ce haka: Koda shi ke na kai su nesa tsakanin al'ummai, kuma na warwatsar da su cikin ƙasahe, duk da haka na zama haikali a gare su na ɗan lokaci ƙaɗan cikin ƙasashen da suka tafi.'17Saboda haka ka ce, 'Ubangiji Yahweh ya ce haka: Zan tattaro ku daga mutane daban-daban, in jera ku daga ƙasashen da kuka warwatse, sai in ba ku ƙasar Isra'ila.18Sa'an nan za su je wurin su cire dukkan abin banƙyama da dukkan ayyukan banƙyama daga wancan wurin.
19Zan ba su zuciya ɗaya, kuma zan sa sabon ruhu a cikin su. Zan ɗauke zuciyar dutse daga jikinsu in ba su zuciyar tsoƙa,20domin su yi tafiya cikin tafarkina, za su kiyaye ka'idodina su kuma aikata su. Sa'an nan za su zama mutanena, Ni kuma in zama Allahnsu.21Amma ga waɗanda ke tafiya tare da sha'awar abin ƙyamarsu da taƙaicinsu, Zan kawo masu ayyukansu ga kawunansu - wannan ne furcin Ubangiji Yahweh."
22Kerubobin suka ɗaga fukafukansu da gargarorinsu da ke a gefensu, ɗaukakar Allah na Isra'ila kuma ta kasance a can sama bisansu.23Sa'an nan ɗaukakar Yahweh ta fito daga cikin tsakiyar birnin ta kuma tsaya a tsauni ta gabashin birnin.
24Ruhun ya ɗago ni ya kawo ni cikin Kaldiya, gun 'yan zaman ɓauta, a wahayi daga Ruhun Allah, kuma wahayin da na gani ya fito daga gare ni.25Sai na furtawa masu zaman bautar dukkan abubuwan Yahweh da na gani.

12

1Maganar Yahweh ta zo mani, cewa,2"Ɗan mutum, kana zama a cikin gidan tayarwa, inda suna da idanuwan gani amma ba su gani; inda kuma suna da kunnuwan ji amma ba su ji. Saboda su gidan tayarwa ne.

3Saboda haka kai ma, ɗan mutum, ka shirya kayanka domin zaman bauta, kuma ka tashi da rana a fuskarsu, domin zan sa kaje zaman bauta a fuskarsu daga wurin da kake zuwa wani wurin. Watakila za su fara gani, koda shi ke su gidan tayarwa ne
4Za ka fitar da kayayyakinka na zaman bauta da rana a fuskarsu; jeka waje da yamma a fuskarsu a hanyar da kowa ke zuwa zaman bauta.5Ka huda rami a bango a fuskarsu, kuma ka fita ta wurin.6A fuskarsu, ka ɗauki kayayyakinka kan kafaɗarka, ka kawo su waje a cikin duhu. Ka rufe fuskarka, gama lallai ba za ka ga ƙasar ba, tunda na sa ka kamar alama ne ga gidan Isra'ila."
7Sai na yi hakan, kamar dai yadda aka umarce ni. Na kawo kayan zaman bautata da rana, kuma da yamma na huda rami da hannu a bango. Na fitar da kayana waje a duhun, sai na sa su a kafaɗata na ɗaga sama a fuskarsu.
8Sai maganar Yahweh ta zo mani da safe, cewa,9"Ɗan mutum, ko gidan Isra'ila, gidan tayarwar nan, ba su tambaya, 'me ka ke yi?'10Ka ce masu, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Wannan aikin annabcin ya shafe ɗan sarki a Yerusalem ne, da dukkan gidan Isra'ila wanda a cikinsa suke.'
11Ka ce, 'Ni ne alama a gare ku. Kamar yadda na yi, haka za a yi masu; za su je zaman bauta da zaman talala.12Ɗan sarkin da ke a cikinsu zai ɗauki kayansa a kafaɗarsa da duhu, kuma ya fice ta bango. Za su huda bango su fita da kayansu. Zai rufe fuskarsa domin kar ya ga ƙasar da idanuwansa.13Zan shimfiɗa ragata a kansa kuma zai kamu a tarkona; sa'an nan zan kawo shi Babila, da ƙasar Kaldiyawa, amma ba zai gan su ba. Zai mutu a can.
14Ta kowacce shiyya kuma zan warwatsar da dukkan waɗanda ke kewaye da shi da za su taimaka masa da dukkan sojojinsa, kuma zan aikar da takobi biye da su.15Sa'an nan za su sani cewa Ni ne Yahweh, idan na warwatsar da su cikin al'umma na kuma tarwatsar da su ko'ina a ƙasashe.16Amma zan bar kaɗan daga cikinsu daga takobin da yunwa da annoba, saboda su bada rohoton dukkan abin ƙyamar da ke cikin ƙasar inda na ɗauke su, domin su sani Ni ne Yahweh."'
17Maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,18"Ɗan mutum, ka ci gurasarka a giggice, ka kuma sha ruwanka da rawar jiki da damuwa.
19Sa'an nan sai ka ce da mutanen ƙasar, ' Ubangiji Yahweh ya ce haka game da mazaunan Yerusalem, da ƙasar Isra'ila: Za su ci abincinsu da rawar jiki kuma su sha ruwa cikin fargaba, tun da za a washe ƙasar da dukkan abin da ke ciki saboda hargitsin dukkan waɗanda ke zaune a ciki.20Domin haka Biranen da ke da mazauna za su zama kufai, kuma ƙasar za ta zama kango; To za ku sani cewa Ni ne Yahweh."'"
21Karo na biyu kuwa, maganar Yahweh ta zo mani, cewa,22"Ɗan mutum, Mene ne wannan karin magana da kuke da shi a ƙasar Isra'ila da ke cewa, 'Kwanakin na da tsawo, kuma dukka wahayin bai gudana ba'?23Saboda haka, ka ce masu, 'Ubangiji Yahweh ya ce haka: Zan kawo ƙarshen wannan karin maganar, kuma mutanen Isra'ila ba za su ƙãra amfani da ita ba.' Ka ce masu, 'Kwanakin sun kusato sa'ad da dukkan wahayoyin za su cika.
24Gama ba za ƙãra samun wahayoyin ƙarya ba ko dũba ta neman suna cikin gidan Isra'ila ba.25Gama Ni ne Yahweh! Nakan faɗa, kuma ina aikata abin da na faɗa. Ba za a ƙãra ɓata lokaci a kan batun ba. Gama zan faɗi wannan magana a kwanakinku, gidan tayarwa, kuma tabbas zan aiwatar da shi! - wannan ne Ubangiji Yahweh ke furtawa."'
26Haka kuma maganar Yahweh ta zo mani, cewa,27"Ɗan mutum! Duba, gidan Isra'ila ya ce, 'Wahayoyin da yake gani na kwanaki da yawa ne daga yanzu, kuma yana annabcin lokutta masu nisa ne.'28Saboda haka ka ce da su, 'Ubangiji Yahweh ya ce: Maganganuna ba za su ƙãra yin jinkiri ba, amma maganar da na faɗa za ta cika - wannan ne furcin Ubangiji Yahweh.

13

1Bugu da ƙari, maganar Yahweh ta zo mani, cewa.2"Ɗan mutum, ka yi annabci gãba da annabawan da ke annabci a Isra'ila, kuma ka faɗa wa waɗanda ke annabci daga tsammace-tsammacensu, ' Ku saurari maganar Yahweh.3Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Kaiton wawayen annabawan da ke bin ruhun kansu, amma ba su ga komai ba!4Isra'ila, annabawanki sun zama kamar diloli a watsattsun gonaki.

5Ba ku je wurin tsagogin bango da ke kewaye da gidan Isra'ila domin ku gyara shi ba, domin ku yi tsayayya a yaƙi a ranar Yahweh ba.6Mutanen na ganin wahayoyin ƙarya kuma su na yin annabcin ƙarya, waɗanda ke cewa, "Wannan da wancan ne furcin Yahweh." Yahweh bai aike su ba, amma ko kaɗan ba su bar sanya mutane begen saƙonninsu za su zama gaskiya ba.7Ba ku yin wahayin ƙarya da annabcin ƙarya, ku da ke cewa, "abu kaza da abu kaza ne furcin Yahweh" sa'ad da Ni kaina ban yi magana ba?
8Saboda haka Ubangiji Yaweh ya faɗi wannan, 'Domin kun yi ƙarairayi a kan karɓar wahayi - Saboda haka Ubangiji Yahweh ya yi furcin gãba da ku:9Hannuna zai yi gãba da annabawa masu wahayoyin ƙarya da annabcin ƙarya. Ba za su kasance a taruwar jama'ata ba, ko a sa su a cikin lissafin gidan Isra'ila ba; Ba za su tafi ƙasar Isra'ila ba. Gama za ku san cewa Ni ne Ubangiji Yahweh!
10Domin wannan, kuma saboda sun sa mutanena su kauce daga hanya da cewa, "Salama!" sa'ad da babu salama, suna gini a bangon da za su shafa farar ƙasa.'11Ka cewa waɗanda ke shafen bangon da farar ƙasar,' zai faɗo ƙasa; za a yi ruwan sama, kuma zan aiko da guguwar da za ta sa ya faɗi, da iska mai ƙarfi da za ta rushe bangon.12Duba, bangon zai faɗo. Waɗansu ba su ce maku, "Ina farar ƙasar da kuka shafa wa bangon ba?"
13Saboda haka Ubangiji Yahweh ya ce: Zan kawo guguwar iska a fushina, kuma za a samu ambaliyar ruwan sama a hasalata! ƙurar fushina za ta hallaka shi kakaf.14Gama zan rushe bangon da kuka shafe da farar ƙasa, kuma zan ragargaza shi har ƙasa in bar ginshiƙan a fili. Domin ya faɗo, kuma ku hallaka a tsakiyarsa. Za ku kuwa sani cewa Ni ne Yahweh.
15Gama cikin fushina zan hallakar da bangon da waɗanda ke shafa masa farar ƙasa.16wato annabawan Isra'ila da ke yin annabci a kan Yerusalem waɗanda kuma ke ganin wahayoyin salama dominta. Amma babu salama!- wannan furcin Ubangiji Yaweh ne."'
17Saboda haka, ɗan mutum, ka sa fuskarka gãba da 'ya'ya mata na mutanenka da ke annabci daga nasu tunanin, kuma ka yi annabci gãba da su.18Ka ce, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Kaiton matayen da ke ɗinka layun dabo a dukkan ɓangarorin hannunsu suna kuma yin gyalulluka domin kawunansu da kowanne irin fasali, suna amfani da shi a farautar mutane. Za ku farauci mutanena amma ku ceci ranku?
19Kun ɓãta ni a cikin mutanena domin a ba ku ɗan danƙin bali da gutsiren gurasa, ku kashe mutanen da bai dace su mutu ba, da kuma barin waɗanda bai dace su rayu ba su rayu, saboda karairayi da kuke yiwa mutanena da ke jinku.
20Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Ina gãba da dabo da layun da kuka yi aiki da su domin ku yiwa rayukan mutane tarko kamar tsuntsaye. Hakika zan yayyage su daga hannuwanku; kuma mutanen da kuka cafko kamar tsuntsaye - Zan sake su su tafi.21Zan yayyage gyalullukanku na tsafi in ceci mutanena daga hannunku, saboda ka da su ƙara faɗawa a tarkon hannuwanku. Za ku kuwa sani cewa Ni ne Yahweh.
22Saboda kun karya zuciyar mutum mai adalci da ƙarairayi, koda yake Ni ban yi niyyar karya zuciyarsa ba, kuma domin kun ƙarfafa wa mugu gwiwa domin kar ya juyo daga hanyarsa ya ceci ransa -23to ba za ku ƙara ganin wahayoyin ƙarya ko ku ci gaba da yin annabcin ƙarya ba, gama Zan ceci mutanena daga hannunku. Za ku sani cewa Ni ne Yahweh,"'

14

1Waɗansu daga cikin dattawan Isra'ila suka zo wurina suka zauna a gabana.2Sa'an nan maganar Yahweh ta zo mani, cewa,3"Ɗan mutum waɗannan mazajen sun ɗauki gumakansu cikin zukatansu sun kuma sa tuntuɓen zunubansu a gaban fuskokinsu. Za su ma roƙe ni wani abu kuwa?

4Saboda haka ka sanar da wannan gare suka ce masu, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Duk mutumin gidan Isra'ila wanda ya ɗauki gumaka ya sa a zuciyarsa, ko ya sa tuntuɓen zunubansa a gaban fuskarsa, kuma ya zo gun Annabi - Ni, Yahweh, zan amsa masa bisa ga yawan gumakansa.5Zan yi wannan domin Zan iya ɗauke gidan Isra'ila daga cikin zukatansu da ke nesa da ni ta dalilin gumakansu.'
6Saboda haka ka cewa gidan Isra'ila. 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Ku tuba ku juyo daga gumakanku! Ku juya fuskokinku baya daga dukkan haramtattun ayyukanku.
7Domin duk wanda yake daga gidan Isra'ila da duk wanda ke cikin bãƙin da ke zaune a Isra'ila da suka rabu da ni, wanda ke ɗauke da gumaka cikin zuciyarsa ya sa abin tuntuɓe na zunubansa a furkarsa, kuma ya zo gun annabi ya roƙe ni - Ni, Yahweh, zan amsa masa da kaina.8Saboda haka zan sa fuskata gãba da mutumin nan in maida shi alama da karin magana, gama zan yanke shi daga tsakiyar mutanena, kuma za ku sani cewa Ni ne Yahweh.
9Idan a ka ruɗi annabi ya faɗi sãƙo, daga nan Ni, Yahweh, zan ruɗi annabin nan; Zan miƙa hannuna gãba da shi kuma in hallaka shi daga tsakiyar mutanena Isra'ila.10Za su ɗauki laifofinsu; laifin annabi zai zama dai-dai da laifin wanda ke zuwa nema daga gare shi.11Saboda wannan, gidan Isra'ila ba zai ƙara bijirewa ba daga bi na ko su ƙazamtar da kansu ta wurin bin dukkan laifofinsu. Za su zama mutanena, Ni kuma zan zama Allahnsu - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne,"'
12Sa'an nan maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,13"Ɗan mutum, Idan ƙasa ta yi zunubi gãba da ni ta aikata laifi har Na fitar da hannuna gãba da ita na karya sandar gurasarta, kuma Na aiko yunwa a kanta kuma na datse mutum da dabba daga ƙasar;14to ko mutanen nan guda uku - Nuhu da Daniyel da Ayuba - suna cikin tsakiyar ƙasar, za su dai iya ceton ransu ne kawai ta ayyukansu na adalci - wannan furcin Yahweh ne.
15Idan na aiko miyagun bisashe ta ƙasar na maida ita bakarariya saboda ta zama kufai inda ba mutum da zai iya wucewa saboda bisashen,16daga nan ko waɗannan mutum ukun kuma na ciki - Muddin ina raye, furcin Ubangiji Yahweh - ba za su iya su ceto ko da "ya'yansu maza ko mata ba; Rayukansu ƙadai za su iya cetowa, amma ƙasar za ta zama watsattsiya.
17Ko idan na kawo takobi gãba da ƙasar na ce, 'Takobi, je ta cikin ƙasar ki datse mutum da dabba daga cikinta,18daga nan ko waɗannan mutane ukun suna tsakiyar ƙasar- muddin Ina raye, furcin Ubangiji Yahweh - ba za su iya su ceto ko da ma 'ya'yansu maza ko mata ba; rayukansu ƙaɗai za su iya cetowa.
19Ko idan na aiko da annoba gãba da ƙasar nan kuma na zubo fushina gãba da ita ta wurin zubda jini, saboda in datse mutum da bisã,20daga nan ko da Nuhu da Daniyel da Ayuba na cikin ƙasar - muddin ina raye, furcin Ubangiji Yahweh - Ba za su iya su ceto ko da ma 'ya'yansu maza da mata ba; rayukansu ne kawai za su iya cetowa ta wurin ayyukan adalcinsu.
21Gama Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Zan maida abubuwa su fi haka ɓaci tabbas ta wurin aikowa da hukuntaina - yunwa da takobi da namomin jeji, da annoba - gãba da Yerusalem domin in datse mutum da bisã daga cikinta.
22Duba! duk da haka, Za a bar ragowa a cikinta, waɗanda suka rayu da za su fito da 'ya'ya maza da mata. Duba Za su fita zuwa wurinku, kuma za ku ga hanyoyinsu da ayyukansu sai ku ƙarfafa game da horon da Na aiko a Yerusalem, da a kan komai da na aiko gãba da ƙasar.23Waɗanda suka rayu za su ta'azantar da ke sa'ad da kika ga hanyoyinsu da ayyukansu, saboda ku san dukkan waɗannnan abubuwan da na yi gãba da ita, cewa ban yi su a banza ba! wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."

15

1Sa'an nan maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, yaya kuringar inabi ta fi kowanne itace mai rassa da ke kurmi kyau?3Mutane na ɗaukar katako daga kuringar inabi su yi wani abu da shi? Ko kuwa su yi maratayi daga gare ta su rataya wani abu a kai?4Duba! Idan aka jefa ta cikin wuta kuma idan wutar ta ƙone dukka sassa biyu na ƙarshenta da kuma na tsakiya, za a iya yin wani amfani?

5Duba! Sa'ad da ta kai ƙarshe, ba za ta iya yin komai ba; tabbas, sa'ad da wutar ta ƙona ta, to ba za ta yi wani abin amfani ba.6Domin haka Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Ba kamar itatuwan dazuzzuka ba, Na ba da kuringar inabi ta zama abin ƙonawa ga wuta; Kamar haka zan yi ga mazaunan Yerusalem.
7Gama zan sa fuskata gãba da su. koda yake sun fito daga wutar, duk da haka wutar ba za ta cinye su ba; da haka za ku sani cewa Ni ne Yahweh, sa'ad da na sa fuskata gãba da su.8Sa'an nan zan maida ƙasar watsattsen kufai domin sun aikata zunubi - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."

16

1Maganar Yahweh ta zo mani, cewa,2"Ɗan mutum, ka sanar da Yerusalem game da haramtattun ayyukanta,3ka kuma furta, 'Ubangiji Yahweh faɗi wannan ga Yerusalem: Farkonki da haihuwarki sun faru a ƙasar Kan'ana ne; Mahaifinki Ba'amore ne, mahaifiyarki Bahitiya ce.

4A ranar haihuwarki, mahaifiyarki bata yanke cibiyarki ba, balle ta tsabtace ki a ruwa ko ta shafe ki da gishiri, ko ta rufe ki da tsumma.5Babu idon da ya tausaya maki ya yi wani abu daga cikin waɗannan domin ki, ya ji tausayinki. Aranar da aka haife ki, domin ƙin jininki, an jefa ki waje a fili.
6Amma na bi ta wurinki, kuma na ga kina motsi cikin jininki; sai Na ce da ke a cikin jininki, "Ki rayu!" Na ce da ke a cikin jininki, "Ki rayu!"7Na sa kin yi girma kamar tsiro a fili. Kin yawaita kin kuma zama da girma, kika zama abin ƙauna sosai kuma kin kai ga sa kayan ado. Nonnanki sun tsaya tantsan-tantsan, kuma gashin kanki ya yi kauri, koda shi ke ki na tsirara tumɓur.
8Na bi ta wurin da kike kuma, na kuma gan ki. Duba! lokacin ƙauna ya zo maki, sai na rufe ki da bargo na rufe tsiraicinki. sa'an nan na yi maki rantsuwa na kawo ki ga alƙawari - kika kuma zama tawa - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.
9Sai na wanke ki da ruwa, na kuma wanke ki daga jini, sai na shafe ki da mai.10Na suturta ki da ɗinkakken tufafi na sa maki takalman fãta a ƙafafunki. Na naɗe ki da linin mai kyau na rufe ki da silki.11Biye da haka na yi maki ado da sarƙoƙi masu daraja, sai na sa maki sarƙar hannu, da sarƙa kewaye da wuyanki.12Na sa zoben hanci a hancinki, da 'yan kunne a kunnuwanki, da kambi a kanki.
13Saboda haka an yi maki ado da zinariya da azurfa, kuma an suturta ki da linin mai kyau da silki da ɗinkakkun kaya; kin ci gari mai kyau da zuma da mai, kuma kika zama kyakkyawa, sai kika zama sarauniya.14Shahararki ta kai ga al'ummai saboda kyaunki, gama cikakkiya ce a cikin darajar da na ba ki - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.
15Amma kin dogara ga kyaunki, kuma kin yi kamar karuwa saboda shahararki; kin zubo ayyukan karuwancinki ga duk wanda ke wucewa, saboda kyaunki ya zama nasa.16Sa'an nan kika ɗauki tufafinki kuma da su kika yiwa kanki masujadai masu ado da launuka daban-daban, a wurin kuma kika yi kamar karuwa. Bai kamata hakan ya faru ba. ko irin wannan abin ya kasance.
17Kin ɗauki kyawawan kayan adonki na zinariya da azurfa da na ba ki, sai kika yiwa kanki siffofin mazaje, sai ki ka yi da su kamar yadda karuwa ke yi.18Kika ɗauki tufafinki da a ka yi aikin ɗinki mai kyau kika rufe su, sai kika ajiye maina da turarena a gabansu.19Gurasata na ba ki - wanda aka yi da lallausan gari da maida zuma - kin ajiye su domin kamshi mai daɗi, gama abin da ya faru kenan - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.
20Sa'an nan kuka ɗauki 'ya'yanku maza da mata da kuka haifa mani, kuka kuma yi hadaya da su ga siffofin domin su lanƙwame kamar abinci. Ayyukan karuwancinku ƙaramin abu ne?21Kun yanka 'ya'yana kuka sa su a cikin wutar.22A cikin dukkan abin ƙyamarku da ayyukan karuwancinku ba ku yi tunani a kan kwanakin kuruciyarku ba, a sa'ad da kuke tsirara tumɓur sa'ad da kuke birgima cikin jininku.
23Kaito! Kaitonki! - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - saboda haka, a kan dukkan wannan muguntar,24kin gina wa kanki sãƙon tsafi a kowanne wurin taruwar jama'a.
25Ki ka gina wurin tsafi a kan kowacce hanya kuma kin wulaƙanta kyaunki, gama kin bada kanki ga kowanne mai wucewa kuma kika ƙara yin ayyukan karuwanci.26Kika yi kamar karuwa tare da Masarawa, makwabtanki masu sha'awace-sha'awace, kika kuma aikata ayyukan karuwanci da yawa, ki na ta sani fushi.
27Duba! Zan cake ki da hannuna in yanke abincinki. Zan miƙa ranki ga maƙiyanki, 'yan matan Filistiyawa, waɗanda suka ji kunyar halinki na lalata.28Kin yi kamar karuwa tare da Asiriyawa saboda ba ki ƙoshi ba. Ki ka yi kamar karuwa amma dai ba ki ƙoshi ba.29Kin ƙara aikata ayyukan karuwanci da yawa a ƙasar attajiran Kaldiya, kuma ko wannan ma bai ƙosar da ke ba.
30Yaya ciwon zuciyarki yake - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - cewa za ki yi dukkan waɗannan abubuwan, ayyukan bankunya na karuwanci?31Kin gina wurin tsafinki a kan dukkan tituna kuma ki ka sa sãƙon tsafinki a dukkan wurin taruwar jama'a. Duk da haka ke ba kamar karuwa ba ce saboda kin ƙi karbar biya.
32Ke mazinaciyar mace, kin amince da kwartaye a maimakon mijinki.33Mutane na biyan kowacce karuwa, amma ke kina bada ladarki ga dukkan masoyanki kina kuma ba su cin hanci su zo wurin ki daga ko'ina domin ayyukan karuwancinki.34Saboda haka akwai bambanci tsakaninki da waɗancan matayen, tun da ba mai zuwa wurinki ya sa ki kwana da shi, a maimakon haka kina biyan su. Babu mai biyan ki.
35Saboda haka, ke karuwa, ki ji maganar Yahweh.36Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Saboda kin zubo sha'awace-sha'awacenki waje kika kuma buɗe tsiraicinki ta wurin ayyukan karuwanci da dukkan masoyanki da dukkan ƙazaman gumakanki, kuma saboda jinin 'ya'yanki da kika miƙawa gumakanki,37saboda haka, Duba! Zan tara dukkan masoyanki da kika sadu da su, dukkan waanda kike so da waɗanda kike ƙi, kuma zan tara su gãba da ke a ko'ina. Zan fallasa tsiraicinki wurinsu domin su ga dukkan tsiraicinki.
38Gama zan hukunta ki saboda zina da zubda jini, kuma zan kawo maki zubda jinin fushina da shauƙi.39Zan bada ke a hannunsu saboda su jefar da sãƙon tsafiinki ƙasa su kuma rurrushe wuraren tsafinki su kuma tuɓe maki tufafinki su ɗauki dukkan kayan adonki. Za su bar ki tsirara tumɓur.
40Sa'an nan za su tara maki jama'a gãba da ke su jejjefeki da duwatsu, kuma su daddatsa ki da takkubansu.41Za su ƙone gidajenki su yi abubuwan hukuntawa da yawa a kanki a gaban mata da yawa, gama zan tsayar da karuwancinki, ba za ki kuma biya masoyanki ba.42Sa'an nan ne zan kwantar da fushina a kanki; fushina zai bar ki, gama zan gãmsu, kuma ba zan ƙara yin fushi ba.
43Saboda ba ki tuna da kwanakin kuruciyarki ba kuma kin sa na girgiza da fushi saboda dukkan waɗannan abubuwan, Domin haka, Duba! Ni kaina zan aiko hukunci a kanki domin abin da kika yi - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne. Ba za ki ƙara karuwanci da dukkan sauran kazamtattun ayyukanki ba?
44Duba! Duk mai faɗin karin magana game da ke zai ce, "Kamar yadda uwa take, haka ma 'yarta take."45Ke ɗiyar mahaifiyarki ce, wadda ta ƙi mijinta da 'ya'yanta, kuma ke 'yar'uwar 'yan'uwanki ne waɗanda suka ƙi mazajensu da 'ya'yansu. Mahaifiyarki Bahitiya ce, kuma mahaifinki Ba'amore ne.
46Yãyarki Samariya ce 'ya'yanta mata kuma su ne ke zama a Arewa, ƙanwarki kuma ita ce wadda ke zama a kudu da ke, wato Sodom da 'ya'yanta mata.
47Ba tafiya a hanyarsu da bin halayensu da ayyukansu kawai kika yi ba, amma a dukkan hanyoyinki kin zama fiye da yadda suke.48Da dawwamata - wannan furcin Yahweh ne - Yar'uwarki Sodom da 'ya'yanta mata, ba su yi yawan mugunta kamar yadda ke da 'ya'yanki mata suka yi ba.
49Duba! Wannan ne zunubin 'yar'uwarki Sodom: ta na da kumbura kai a cikin wadataccen jin daɗi da zaman sangarcewa da rashin kulawa da komai. Ba ta ƙarfafa hannun talakawa da masu buƙata ba.50Ta zama mai kumbura kai da aikata ayyukan ƙyama a gabana, saboda haka na ɗauke su kamar yadda kuka gani.
51Ko Samariya bata aikata rabin zunubanki ba; maimakon haka ma, kin yi ayyukan ƙyama da yawa fiye da yadda suka yi, kuma kin nuna cewa 'yan'uwanki sun fi ki kirki saboda dukkan abubuwan ƙyama da kika yi!52Ke musamman, kin nuna kunyar kanki; a wannan hanyar kin nuna cewa 'yan'uwanki sun fi ki kyau, saboda laifofin da kika aikata a dukkan hanyoyin banƙyaman nan. 'Yan'uwanki yanzu sun nuna alamar fin ki kyau. Ke musamman, kin nuna kunyar kanki, gama a wannan hanyar kin nuna cewa 'yan'uwanki sun fi ki kyau.
53Gama zan komo da wadatarsu - wadatar Sodom da'ya'yanta da wadatar Samariya da 'ya'yanta; amma wadatarki zata kasance a cikinsu.54A game da waɗannan abubuwan kuwa za ki nuna kunyarki; za a wulaƙanta ki saboda dukkan abubuwan da kika yi, kuma a sa'an nan ne za ki zama mai ta'azantarwa a gare su.55Saboda haka 'yar'uwanki Sodom da 'ya'yanta mata za a komo da su kamar yarda suke a dã. Samariya kuma da 'ya'yanta mata za a komo masu da matsayinsu na dã.
56Ba ki ambato 'yar'uwarki Sodom da bakin ki ba a kwanakin da kike fahariya.57kafin muguntarki ta bayyanu. Amma yanzu kin zama abar zargi ga 'ya'ya mata na Idom da kuma dukkan 'ya'ya mata na Filistiyawa kewaye da ita. Dukkan mutanen da ke kewaye na raina ki.58Za ki nuna kunyarki da aikin banƙyamarki! wannan furcin Yahweh ne!
59Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Zan yi da ke yadda kika cancanta, ke da kika raina rantsuwarki ta wurin karya alƙawari.
60Amma ni da kaina zan tuna da alƙawarin da na yi da ke a kwanakin kuruciyarki, kuma zan kafa madawamin alƙawari da ke.61Sa'an nan ne za ki tuna da hanyoyinki ki kuma ji kunya a sa'ad da kika ƙarɓi yãyarki da ƙanwarki. Zan ba ki su a matsayin 'ya'yanki mata, amma ba saboda alƙawarinki ba
62Ni da kaina zan ƙulla alƙawarina da ke, kuma za ki san cewa ni ne Yahweh.63Saboda waɗannan abubuwan, za ki tuna da komai ki kuma ji kunya, saboda haka ba za ki sake buɗe bakinki ki yi magana ba saboda kunya, sa'ad da na gafarce ki a kan dukkan abin da kika yi - wannan furcin Yahweh ne."'

17

1Maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, faɗi kacici-kacici da kuma misali ga mutanen Isra'ila.3Ka ce, 'Ubangiji Yahweh ne ya faɗi wannan: Wani babban gaggafa mai manyan fikafikai da dogayen gasusuwan fikafikai da gasusuwa da yawa masu launi iri-iri ya je Lebanon ya kama saman kan itacen sida.4Ya karya kan tohonsa mafi tsawo ya ɗauko su zuwa ƙasar Kan'ana; ya shuka su a birnin fatake.

5Sai kuma ya ɗauki wani iri na ƙasar ya dasa shi a wuri mai dausayi kusa da ruwa mai yawa kamar itacen warɗi.6Sai ya yi toho ya zama kuringa mai yaɗuwa har ƙasa. Rassansa suka tanƙwasa wajensa, saiwoyinsa suka kama ƙasa sosai. Domin haka ya zama kuringa ya yi rassa da toho.
7Amma akwai wani babban gaggafa mai manyan fikafikai da gashi mai yawa. Sai wannan kuringa ta tanƙwasa saiwoyinta zuwa wajen gaggafan, ta kuma miƙe rassanta zuwa wajensa tun daga inda aka dasa ta domin ya rika yi ma ta ban ruwa.8An dasa ta a wuri mai kyau da danshi inda akwai ruwa da yawa domin ta yi rassa ta kuma ba da 'ya'ya, ta zama kuringar inabi ta ƙwarai.'
9Ka cewa mutanen, 'Ubangiji Yahweh ne ya faɗi wannan: Ko za ta wadatu? Ba za a iya cire ta a kuma ɗebe 'ya'yanta domin kada su yi yaushi, kuma dukkan ganyayenta masu kyau su yanƙwane ba? Babu wani abu ko mutane masu yawa da a ke buƙata da su cire ta daga jijiyoyinta.10To duba! bayan an sake dasa ta, za ta sake yin girma? Ba za ta yanƙwane ba idan iskar gabas ta hura ta? Babu shakka za ta yanƙwane ga baki ɗaya daga tushenta.'"
11Sai maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,12"Ka yi magana da 'yan tawayen gidan, 'Ba ku san mene ne waɗannan abubuwa ke nufi ba? Duba! Sarkin Babila ya zo Yerusalem ya kuma tafi da sarkinta da yarimanta ya kai su zuwa gare shi Babila.
13Sai ya ɗauki wani daga zuriyar sarauta, ya yi alƙawari da shi, ya kuma ɗauki rantsuwa da shi. Ya ɗauke mutane na ƙasar masu iko,14domin mulkin ya zama da rauni har ƙasar ta kasa ɗaga kanta. Ta wurin kiyayye alƙawarinsa ƙasar za ta tsira.
15Amma sarkinYerusalem ya yi masa tawaye ta wurin aikawa da jakadai zuwa Masar domin a ba shi dawakai da sojoji. To, zai yi nasara? Wanda ya yi irin waɗannan abubuwa zai tsira? Idan ya karya alƙawari, zai iya tsira?16Da dawwamata -wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - babu shakka zai mutu a cikin ƙasar sarki wanda ya naɗa shi sarauta, sarkin da ya rena rantsuwarsa, wanda kuma ya karya alƙawarinsa. Zai mutu a tsakiyar Babila.
17Fir'auna da sojojinsa masu ƙarfin yaƙi da kuma jama'arsa masu yawa domin yaƙi ba za su tsare shi ba a wannan yaƙin, sa'ad da Babilawa suka gina hasumiyoyi da kagarai don su kashe rayuka masu yawa.18Gama sarkin bai cika rantsuwar alƙawarinsa ba. Duba ya miƙa hannunsa ga yin alƙawari duk da haka ya aikata dukkan waɗannan abubuwa. Ba zai kuɓuta ba.
19Domin haka ni Ubangiji Yahweh na faɗi wannan: Da dawwamata, ba rantsuwata da alƙawarina ya rena ya kuma karya ba? Saboda ha ka zan ɗora hukuncinsa a kansa!20Zan kafa masa tarko in kama shi, kuma za a kama shi a tarkon farautata. Sa'an nan zan kai shi Babila inda zan yi masa shari'a saboda cin amana da kuma tayawar da ya yi mani!21Dukkan 'yan gudun hijira cikin sojojinsa za a kashe su da takobi, sauran da suka ragu za a watsar da su ko'ina. A sa'an nan ne za su sani cewa Ni ne Yahweh; Na furta wannan zai faru."
22Ubangjji Yahweh ya faɗi wannan, 'Saboda haka ni kaina zan cire toho a kan itacen sida mai tsawo, zan kuma sake dasa shi daga sashen jikin rassansa. Zan karye shi, ni da kaina kuma zan dasa shi a tsauni mai tsayi.23Zan dasa shi a kan tsaunukan Isra'ila domin ya fito da rassa, ya bada 'ya'ya, ya kuma zama itacen sida na gaske saboda kowanne tsuntsu mai fiffike ya zauna a ƙarƙashinsa. Za su yi sheƙa a cikin inuwar rassansa.
24Sa'an nan dukkan itatuwan jeji za su sani cewa Ni ne Yahweh. Na kan kawo manyan itatuwa ƙasa sa'an nan in tada ƙananan itatuwa sama. Zan sa ɗanyen itace ya bushe in kuma sa busashen itace ya zama ɗanye. Ni ne Yahweh, Na furta wannan zai faru; na kuma yi shi.

18

1Maganar Yahweh ta sake zuwa gare ni, cewa,2"Me kuke nufi, ku da kuka yi amfani da wannan karin magana a kan ƙasar Isra'ila cewa, 'Mahaifa sun ci 'ya'yan inabi masu tsami, hakoran 'ya'yansu kuma sun dakushe'?

3Da dawwamata - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - ba za a ƙara samun wani dalili da za ka sake amfani da wannan karin magana a Isra'ila ba.4Ga shi! Kowanne rai nawa ne - ran mahaifi duk da na ɗan, dukka nawa ne! Wanda ya yi zunubi shi zai mutu!
5Me za a ce a kan mutum wanda yake shi adali ne yana kuma aikata shari'a da adalci--6idan ba ya cin abinci a kan tsaunuka ko ya sa idanunsa a kan allolin da ke gidan Isra'ila, bai kuma kwana da matar maƙwabcinsa ba, ko ya Kwana da mace a lokacin hailarta, wannn mutum adali ne?
7Me za a ce a kan mutum wanda ba ya ƙuntatawa kowa, wanda yakan mayar wa wanda ya ba shi jingina abin da ya jinginar masa, wanda ba ya ƙwace amma ya kan bada abinci ga mayunwanci, yakan ba huntu tufa, wannan mutum adali ne?
8Me za a ce da mutumin da ba ya bada bashin kuɗi da ruwa; ko tare da wani ƙari a kan abin da ya sayar? Haka yake ce da shi yana goyon bayan gaskiya a tsakanin masu gaskiya, yana kuma tabbatar da adalci a tsakanin mutane.9Amma idan mutumin yana tafiya cikin farillaina yana kuma bin ka'idodina da gaskiya, daga nan alƙawarin wannan mutum mai adalci shi ne: hakika zai rayu! - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.
10Amma da a ce yana da ɗa wanda ya zama ɗan fashi mai kisankai yana kuma yin waɗannan abubuwa masu yawa kamar yadda a ka nuna su a nan,11koda mahaifinsa ba ya yin ɗaya daga waɗannan abubuwa, amma yana cin abinci a kan tsaunuka ya kuma kwana da matar maƙwabcinsa, me za a ce game da shi?
12Wannan mutum yana cin zalin matalauta da masu buƙata, yana kuma yin ƙwace da fashi, ba ya mayar da abin da a ka jinginar masa, yana bautawa gumaka yana kuma aikata abubuwa masu banƙyama,13yana bada rancen kuɗi da ruwa, yana cin riba ta fitar hankali a kan abin da ya sayar, shin wannan mutum zai rayu? Babu shakka ba zai tsira ba! Lallai ne zai mutu kuma alhakin jininsa yana a kansa domin ya yi munanan abubuwa.
14Amma idan akwai mutum da ya haifi ɗa, kuma ɗan nasa ya ga dukkan zunuban nan da mahaifinsa ya yi, koda ya gan su, amma shi bai yi waɗannan abubuwa ba.15Wannan ɗa bai ci abinci a kan tsaunuka ba, bai kuma sa idanunsa ga gumakan gidan Isra'ila ba, bai kwana da matar maƙwabcinsa ba, me za a ce game da shi?
16Wannan ɗa bai ci zalin kowa ba, ko ya ƙarbi jingina, ko ya saci wasu abubuwa, amma a maimakon haka yana bada abincinsa ga mayunwaci, yana ba huntu tufafi.17Wannan ɗan ba ya zaluntar kowa ko ya bada bashi da ruwa ko kuma ya ci ƙazamar riba a kan bashin, amma yana bin ka'idodina, yana kuma tafiya bisa ga farillaina; wannan ɗa ba zai mutu ba saboda zunubin mahaifinsa: Lallai za ya rayu.
18Mahaifinsa kuwa, da yake ya ƙuntatawa wasu ta wurin zaluntarsu, ya yiwa ɗan'uwansa ƙwace, ya kuma aikata abubuwa marasa kyau a cikin mutanensa - zai mutu saboda muguntarsa.
19Amma kun ce, 'Me ya sa ɗa ba zai ɗauki laifin mahaifinsa ba?' Domin ɗan ya bi shari'a da adalci kuma ya bi dukkan umarnaina; ya yi su dai-dai. Babu shakka za ya rayu!20Shi wanda ya yi zunubi, shi ne wanda zai mutu. Ɗa ba zai ɗauki laifin mahaifinsa ba, haka nan mahaifi ba zai ɗauki laifin ɗansa ba. Adalcin wanda ya yi dai-dai ai nasa ne, muguntar azzalumi zata kasance a kansa.
21Amma idan mugu ya juya daga dukkan zunubansa wanda ya aikata ya kiyaye umarnaina ya bi shari'a da adalci, lallai za ya rayu ba zai mutu ba.22Dukkan muguntar da ya aikata ba za a neme su a kansa ba. Zai rayu saboda adalcin da ya yi.
23Ina murna da mutuwar mugu ne - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - ba juyowa daga muguwar hanyarsa ba domin ya rayu?
24Amma idan adalin mutum ya bar yin adalcinsa, ya aikata haramtattun ayyuka kamar dukkan haramtattun ayyuka waɗanda wannan mugun mutum ya aikata, daga nan sai ya rayu? Dukkan adalcin da ya aikata ba za a tuna da su ba idan ya ci amanata da laifin da ya aikata. To zai mutu a cikin zunuban da ya aikata.
25Amma kun ce, 'Hanyar Ubangiji ba dai-dai ba ce!' Ku ji ya ku gidan Isra'ila! Hanyata ba dai-dai ba ce? Ashe ba hanyarku ce ba dai-dai ba?26Sa'ad da mutum adali ya bar adalcinsa, ya kuwa aikata mugunta zai mutu saboda su, zai mutu a cikin muguntar da ya aikata.
27Amma idan mugun mutum ya bar muguntar da ya yi ya zo ya aikata gaskiya da adalci, za ya rayu.28Domin ya gani kuma ya bar dukkan laifofin da ya aikata. Babu shakka za ya rayu, ba zai mutu ba.
29Amma gidan Isra'ila suka ce, 'Hanyar Ubangiji ba dai-dai ba ce! Gidan Isra'ila yãyã hanyata ta zama ba dai-dai ba? Ai hanyarku ce ba dai-dai ba.30Saboda haka zan shar'anta kowanne mutum a cikinku gwargwadon ayyukansa, ya gidan Isra'ila! - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne. Ku tuba daga dukkan muguntarku domin kada su zamar maku dalilin hallaka.
31Ku rabu da dukkan laifofin da kuka aikata; ku samo wa kanku sabuwar zuciya da sabon ruhu. Me ya sa za ku mutu, gidan Isra'ila?32Gama ba na murna da mutuwar wanda ke mutuwa - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - saboda haka sai ku tuba domin ku rayu!"

19

1"Yanzu kai, sai ka yi makoki a kan shugabanin Isra'ila2ka ce, 'Wace ce mahaifiyarka? Zakanya, tana zaune tare da ɗan zaki; a cikin tsakiyar 'yan zakoki, ta yi renon 'ya'yanta.3Ita ce ta goyi ɗaya daga cikin 'ya'yanta ya zama ɗan zaki wanda ya koyi kamun nama, har ya cinye mutane.4Sai al'ummai suka ji labarinsa. Sai aka kama shi cikin tarkonsu, suka ja shi da ƙugiyoyi zuwa ƙasar Masar.

5Daga nan ta ga cewa koda yake ta jira dawowarsa, sa begenta a kansa yanzu ya ƙare, sai ta ɗauki ɗaya daga cikin 'ya'yanta, ta goye shi ya zama sagari.6Wannan sagari yana ta kai da kawowa a cikin zakoki. Ya zama sagari yana kuma koyan kamun nama; ya cinye mutane.7Ya lalatar da kagarunsu ya kuma maida biranensu kufai. ƙasar da mazaunan cikinta an bar su saboda jin rurinsa
8Amma al'ummai suka kafa masa tarko daga kowanne waje; suka baza masa tarunsu a kansa. Suka kama shi cikin tarkunansu.9Suka sa masa ƙugiyoyi, sa'an nan suka kawo shi ga sarkin Babila. Suka kawo shi cikin matsaran wurare domin kada a ƙara sake jin muryarsa a kan tsaunuka Isra'ila.
10Mahaifiyarka tana kamar kuringar inabi da aka dasa a cikin jininka a gefen ruwa. Ta yi 'ya'ya da rassa da yawa saboda isasshen ruwa.11Tana da rassa masu ƙarfi da a ke amfani da su domin sandunan masu mulki, tsayinta zuwa sama da dukkan rassan, ta yi tsayi sosai daga nesa ana iya hangen ganyenta.
12Amma aka tumɓuke kuringar inabin da fushi aka jefar da ita a ƙasa, iskar gabas ta busar da ita. Rassanta masu ƙarfi suka kakkarye suka bushe, wuta kuwa ta cinye su.13Yanzu an dasa ta a cikin jeji, cikin busasshiyar ƙasa mai ƙishi da fari.
14Sai wuta ta fito daga manyan rassanta ta kuwa cinye 'ya'yanta, babu reshe mai ƙarfi a kanta, babu sandar da zan yi mulki.' Wannan makoki ne, kumaza a raira shi a matsayin makoki."

20

1Ya zamana a kan shekara ta bakwai, a rana ta goma ga watan biyar, sai dattawan Isra'ila suka zo domin su yi roƙo a wurin Yahweh suka kuma zauna a gabana.

2Daga nan maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,3"Ɗan mutum, ka faɗa wa dattawan Isra'ila ka ce da su, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Kun zo ku yi roƙo a wurina? Da dawwamata, ba za ku taɓa tuntuɓa ta ba! -wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.'
4Za ka shar'anta su? Za ka shar'anta, ɗan mutum? Bari su san haramtattun ayyukan da ubanninsu suka aikata.5Ka ce masu, 'Ubangiji Yahweh ne ya faɗi wannan: A ranar da na zaɓi Isra'ila na ta da hannuna na rantse wa zuriyar gidan Yakubu, na kuma bayyana kaina a gare su cikin ƙasar Masar, sa'ad da na ta da hannun rantsuwa a gare su. Na ce, "Ni ne Yahweh Allahnku"-6a wannan rana na ta da hannuna na rantsuwar alƙawari a gare su cewa zan fito da su daga ƙasar Masar zuwa cikin ƙasar dana zaɓa dominsu. Mai malalowa da madara da zuma; tana da abubuwa masu kyau da babu irinsu a dukkan ƙasashe.
7Na ce da su, "Bari kowanne ɗayanku ya yi watsi da abubuwan banƙyama daga idanunsa, da gumakan Masar. Kada ku ƙazantar da kanku; Ni ne Yahweh Allahnku."
8Amma sun yi mani tawaye, ba su da niyyar sauraro na. Kowanne mutum ya ƙi watsi da abubuwan banƙyama daga idanunsa ko ya rabu da gumakan Masar, sai na shirya zan zubo masu da fushina domin in cika hasalata a cikinsu a kuma tsakiyar ƙasar Masar.9Amma saboda sunana ban yi haka ba a idanun al'ummai da suke zama a cikinsu. Na sanar da kaina a gare su, a idanunsu, ta wurin fito da su daga ƙasar Masar.
10Sai na fitar da su daga ƙasar Masar na kawo su cikin jeji.11Sa'an nan na ba su farillaina na sa su san ka'idodina a gare su, waɗanda idan mutum ya kiyaye su zai rayu.12Na kuma ba su Asabatai a matsayin alama tsakanina da su, domin kuma su sani cewa Ni ne Yahweh wanda ke tsarkake su.
13Amma gidan Isra'ila suka tayar mani a cikn jeji. Suka ƙi su yi tafiya cikin farillaina; maimakon haka, sai suka ƙi ka'idodina, waɗanda ta wurinsu ne mutum zai rayu idan ya yi biyayya da su. Sun ɓata Asabataina ƙwarai, saboda haka na ce zan zubo masu da fushina a cikin jeji domin in ƙarar da su.14Amma sabili da sunana ban yi haka ba saboda kada a saɓi sunana a idanun al'ummai, waɗanda a kan idanunsu ne na fitar da su daga ƙasar Masar.
15Sai na kuma tada hannuna na rantse masu a cikin jeji ba zan kai su cikin ƙasar da na ba su ba, ƙasar da ta ke cike da yalwar madara da zuma, wadda tafi kyau a cikin dukkan ƙasashe.16Nayi rantsuwa a kan wannan domin sun ƙi ka'idodina kuma sun ƙi yin tafiya cikin farillaina, sun ɓata Asabataina, gama zuciyarsu ta fi so ta bauta wa gumakai.17Amma na kawar da idanuna daga hallakasu ban kuma hallakar da su a cikin jeji ba.
18Sai na ce da 'ya'yansu a jeji, "Kada ku yi tafiya a kan farillan ubanninku; ko ku kiyaye sharuɗɗansu ko ku ɓata kanku da gumakansu.19Ni ne Yahweh Allahnku, ku yi tafiya a kan farillaina, ku kuma kiyaye ka'idodina, ku yi biyayya da su.20Ku kiyaye Asabataina da tsarki domin su zama alama tsakanina da ku, domin ku sani cewa Ni ne Yahweh Allahnku."
21Amma 'ya'yansu maza da mata suka tayar mani, ba su yi tafiya a cikin farillaina ko su kiyaye ka'idodina ba, ta haka idan mutum ya yi biyayya da su zai rayu. Sai kuma suka ɓata Asabataina, domin haka na yi tunani zan zubo masu da fushina a kansu in kuma huce fushina a kansu a jeji.22Amma na yi hakuri sabili da sunana, domin kada a saɓi sunana a gaban idanun al'ummai waɗanda a idanunsu ne na fito da Isra'ilawa.
23Ni da kaina na ɗaga hannuna bisa na rantse masu a jeji, zan warwatsar da su cikin al'ummai in kuma raba su a sauran ƙasashe.24Na yi shawara zan yi wannan domin sun ƙi yin biyayya da ka'idodina, sun kuma ƙi bin farillaina, sun lalata Asabar ɗina. Idanuwansu na mamarin bauta wa gumakan kakanninsu.
25Sai kuma na ba su farillai waɗanda ba su da kyau, da ka'idodi marasa amfani da ba za susa su rayu ba.26Na furtasu ƙazantattu ta wurin kyaututtukansu - sunyi hadayunsu na kowanne ɗan fãri daga mahaifa sunsa su ratsa ta cikin wuta - domin in cika su da fargaba su kuma sani cewa Ni ne Yahweh!"
27Saboda haka, ɗan mutum, yi magana da gidan Israila ka ce da su, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: A wannan kuma ubanninku suka saɓe ni ta wurin rashin aminci a gare ni.28Sa'ad da na kawo su cikin ƙasar da na rantse zan ba su, daga nan kuma dukkan sa'ad da suka hango wani tudu da itace mai ganye, sai su miƙa hadayunsu, suka tsokane ni ta wurin baye-bayensu, a wurin kuma suka ƙona turare mai ƙanshi da zuba baye-bayensu na sha.29Daga nan na ce da su, "Wanne wurin ne wannan da kuke miƙa baye-baye a can?" Domin haka aka kira sunan wurin Bama har zuwa wannan rana.'
30Saboda haka ka cewa gidan Isra'ila, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Me ya sa kuka ƙazantar da kanku da hanyoyin ubanninku? To me ya sa kuke haka kamar karuwai, ku na neman abubuwan banƙyama?31Duk sa'ad da ku ke miƙa kyaututtukanku - kuma duk sa'ad da kuke sanya 'ya'yanku maza su bi ta cikin wuta - har ya zuwa wannan rana kuna ƙazantar da kanku ta wurin dukkan gumakanku. To me ya sa zan barku ku neme ni, gidan Isra'ila? Da dawwamata - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - ba zan bari ku neme ni ba.32Tunanin nan da kuke yi a zuciyarku ba zai faru ba. Kuka ce, "Bari mu zama kamar sauran al'ummai, kamar dangogin sauran ƙasashe waɗanda ke bauta wa katako da dutse."
33Da dawwamata - wannan furcin Yahweh ne - tabbas zan yi mulki a bisan ku da hannu mai ƙarfi, da ɗagaggen damtse, da fushina zan zubo a kanku.34Zan fitar da ku daga sauran mutane zan kuma tattaro ku daga sauran ƙasashe inda aka warwatsar da ku. Zan yi wannan da ikona ta wurin fushina mai zafi.35Sa'an nan zan kawo ku cikin jejin mutane, a wurin ne zan yi maku shari'a fuska da fuska.
36Kamar yadda na yi wa ubanninku shari'a a jeji a ƙasar Masar, haka nan kuma zan yi maku shari'a - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.37Zan sa ku wuce ta ƙarƙashin sandata, in kuma sa ku yi biyayya da abubuwan da alƙawari ya wajabta.38Zan fitar da 'yan tawaye daga cikinku da waɗanda ke yi mani laifi. Zan fito da su daga ƙasar da suke zaune kamar bãƙi, gama ba za su shiga ƙasar Isra'ila ba. Sa'an nan ne za ku sani cewa Ni ne Yahweh.
39To ku, gidan Israila, Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: kowannen ku zai tafi wurin bautar gukinsa. Ku bauta ma sa tun da ya ke ba za ku saurare ni ba, amma ba za ku sake ɓata sunana mai tsarki da hadayunku da gumakanku.
40Gama a kan dutsena mai tsarki, a bisa ƙwanƙolin dutsen Israila--wannan furcin Yahweh ne--dukkan gidan Israila za su bauta mani a ƙasar. Zan yi murna in bukaci hadayunku a wurin, da kuma nunar 'ya'yan farin gandunku na dukkan abubuwanku masu tsarki.41Zan karɓe ku kamar turare mai ƙanshi sa'ad da na fito da ku daga cikin sauran mutane, na tattaro ku daga ƙasashen da aka warwatsar da ku. Zan nuna kaina mai tsarki a cikinku domin sauran al'ummai su gani.
42Gama idan na kawo ku a ƙasar Isra'ila, a ƙasar da na ɗaga hannuna sama na rantse zan bada ita ga ubanninku, za ku sani cewa Ni ne Yahweh.43A nan za ku tuna da mugayen hanyoyinku da dukkan ayyukanku da kuka ɓata kanku da su, za ku ji ƙyamar kanku a idanunku saboda mugayen abubuwa da kuka aikata.44Za ku sani cewa Ni ne Yahweh sa'ad da na yi maku wannan saboda sunana, ba kuma saboda gurɓatattun ayyukanku ba, ya gidan Isra'ila - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.'"
45Sai maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa.46"Ɗan mutum, ka fuskanci ƙasashen kudu, ka yi maganar gãba da kudu; ka yi annabci a kan kurmin Negeb.47Ka cewa kurmin Negeb, 'Wannan furcin Yahweh ne - Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Duba, zan kunna wuta a cikinka. Za ta kuwa cinye kowanne ɗanyen itace da kowanne busashen itace da ke cikinta. Ba za a iya kashe harshen wutar ba, kowacce fuska daga kudu da arewa za su ƙone.
48Gama dukkan masu rai za su sani cewa Ni ne Yahweh idan na sa wutar, ba kuma za a iya kashewa ba.49Sai na ce, "Ya Ubangiji Yahweh, suna cewa da ni, wannan ba maganar misalai kawai yake yi ba?'"

21

1Sai maganar Yahweh ta zo ga gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, ka fuskanci Yerusalem, ka yi maganar gãba da masujadarta; ka kuma yi annabci a kan ƙasar Isra'ila.3Ka ce da ƙasar Isra'ila, 'Yahweh ya faɗi wannan: Ina gãba da ita! Zan zare takobina daga cikin kubanta in datse adalin mutum da mugun mutum daga cikinta!

4Da yake ni zan daddatse adalai da mugaye daga gare ki, takobina zata fito daga cikin kubenta gãba da dukkan mutane daga kudu da kuma arewa.5Dukkan mutane kuwa za su sani Ni, Yahweh, na zare takobina daga kubenta. Ba kuwa za a sake mayar da ita a kubenta ba!'
6Kai kuma, ɗan mutum, sai ka yi nishi da ajiyar zuciya yayin da ƙugunka ya karye! cikin ɗacin rai kayi nishi a gaban idanunsu!7Idan har za su tambaye ka, 'Donme ya sa kake nishi?' Sai ka ce masu, 'Saboda labarin abin da ke zuwa, domin kowacce zuciya za ta narke, kuma kowanne hannu zai yi lakwas! Kowanne ruhu zai some, kuma kowace gwiwa zata malale kamar ruwa. Duba! Abin yana zuwa kuma zai kasance kamar haka! - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.'"
8Sai maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,9"Ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, 'Ubangiji ya faɗi haka: "Ka ce Takobi! Takobi! Za a wãsa ta sosai a kuma goggoge ta!
10Za a wãsa ta domin a yi babban kisa, an goge ta domin ta yi walwal kamar walƙiya! Shin mũyi murna a kan sandar girma ta ɗana? Takobi mai zuwa na gãba da kowacce sanda!11Saboda haka za a bada takobin a goge ta, sa'an nan a cafke ta da hannu! Takobin an wãsa ta an kuma goge ta za a kuma bada ita a hannun wanda ke yin kisa!""'
12Ɗan mutum ka yi kiran neman taimako da makoki! Gama takobi ta zo ta yi gãba da mutanena! Ta na gãba da dukkan shugabannin Isra'ila. An bada su ga takobi tare da mutanena. Saboda haka, ka buga cinyarka!13Gama akwai gwaji, amma idan sandar girman bata daɗe ba fa? - wannan furcin Yahweh ne.
14Yanzu kai, ɗan mutum, ka yi annabci ka buga hannuwanka biyu tare, don takobi zata kai hari har sau uku! Takobi domin waɗanda za a yanka! Ita ce takobin da zata datse mutane da yawa, za a yi masu gunduwa-gunduwa a ko'ina!
15Domin a narkar da zukatansu a kuma ruɓanya faduwarsu, na aika da takobi domin yanka a ƙofofinsu. Ah! An yi ta kamar walƙiya, an cafko ta domin yanka!16Ke, takobi! ki sara dama! ki kuma sara hagu! Ki kuma je duk inda kika juya fuskarki.17Gama ni ma zan buga hannuwana biyu, Sa'an nan kuma zan kwantar da fushina, Ni, Yahweh na furta haka.
18Maganar Yahweh ta sake zuwa gare ni, cewa,19"Yanzu kai, ɗan mutum, ka nuna hanyoyi biyu domin takobin sarkin Babila ta zo. Hanyoyin biyu kuwa za su fara a ƙasar, alama kuma za ta nuna ɗaya daga ckinsu da ke kaiwa zuwa birnin.20Ka kuma sa alamar ɗaya hanyar domin sojojin Babila da za su zo Rabba, birnin Ammonawa. Ka kuma sa ɗaya alamar ta kai sojoji Yahuda da kuma birnin Yerusalem, wadda aka katange.
21Gama sarkin Babila zai tsaya a mararrabar hanyoyi, inda hanyar ta rabu biyu, domin ya yi tsãfi. Yana girgiza waɗansu kiɓau yana kuma neman bayani daga waɗansu gumaka zai kuma binciki hanta.22A hannun damarsa zai riƙe wani abun sihiri game da Yerusalem, zai kafa mata dundurusai, ya buɗe bakinsa domin ya bada umarnin yanka, a yi kururuwar yaƙi, a rurrushe ƙofofinta ya kuma gina mahaurai da gina hasumiyoyin sansani.23Zai kasance kamar abin banza ne a idanuwan waɗanda suke a Yerusalem, waɗanda suka rantse ga Babiloniyawa! Amma sarkin zai zarge su da karya yarjejeniyarsu domin mamaye su!
24Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Saboda kun sa a tuna da laifinku, kuka kuma sa a bayyana kurakuranku, domin a ga zunubanku a dukkan ayyukanku - saboda kun yi haka za a kame ku a hannu.
25Kai kuma, ƙazantacce da mugun shugaban Isra'ila, wanda ranar hukuncinsa ta zo, wanda kuma lokacin aikata laifofinsa ya zo karshe,26Ubangiji Yahweh ne ya faɗi haka zuwa gare ka: Ka cire rawani ka kuma cire kambi! Abubuwa ba za su sake zama dai-dai ba! A ɗaukaka marasa martaba a kuma ƙasƙantar da masu girmankai!27Kufai! Kufai! Zan maida ita kufai! ba za a komar da ita ba, har sai shi wanda aka sa ya zartar da hukunci ya zo.
28To Kai, ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan ga mutanen Ammonawa a kan zuwan kaskancinsu: Takobi! an zare takobi! An wãsa ta domin yanka domin ta lanƙwame, haka zata zama kamar walƙiya!29Annabawa kuma suna ganin holoƙan wahayoyi domin ku, sa'ad da suke yin bukukuwan addini domin su zo maku da karairayi, wannan takobin zata kwanta a wuyan mai mugunta wanda aka kusan kashewa, wanda ranar hukuncinsa ta zo wanda kuma lokacin zunubinsa ya kusa ƙarewa.
30Maida takobi a cikin kubenta. A wurin da aka hallice ka, a cikin ƙasarka ta ainihi, zan hukunta ka!31Zan zubo da hasalata a kanka! Zan kunna wutar fushina gãba da kai in kuma sa ka a cikin hannun mugayen mutane masu dabarar hallakarwa!
32Za ka zama abincin wuta! Jininka zai kasance a tsakiyar ƙasar. Ba za a tuna da kai ba, gama Ni, Yahweh na furta wannan!'"

22

1Sai maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa2"Yanzu, kai ɗan mutum, za ka shar'anta? Za ka shar'anta birni mai jini? Kasa ta san dukkan ayyukanta na banƙyama.3Dole ne ka ce, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Wannan shi ne birnin da ke zubar da jini a tsakiyarsa domin lokacinsa ya zo; birnin da ya yi gumaka domin ya kazantar da kansa.

4Ka zama mai laifi ta wurin jinin da ka zubar, ka ƙazantar da kanka ta wurin gumakan da ka yi. Domin ka jawo kwanakinka kusa, ƙarshen shekarunka kuma ya zo. Domin haka zan maida kai abin reni ga dukkan al'ummai, abin ba'a kuma a dukkan ƙasashe.5Da waɗanda ke kusa da waɗanda ke nesa da kai za su yi maka ba'a, kai ƙazantaccen birni - da aka sani a ko'ina cike da rudami.
6Duba! Masu mulki na Isra'ila, kowannen su da ikonsa, ya zo wurin ka domin ya zubar da jini.7Sun rena ubanni da uwaye a cikin ka, kuma suka yiwa baƙi danniya a cikin tsakiyar ka.8Sun wulaƙanta marayu da gwauraye a cikinka ka rena abubuwana masu tsarki, ka tozarta Asabataina.9Masu yankan baya sun zo cikin ka domin su zubar da jini, kuma sun ci abinci a kan tsaunuka. Sun yi mugunta a tsakiyarka.
10Mazaje sun buɗe tsiraicin mahaifinsu a cikin ka. Sun kuma tozarta mata masu haila a cikin ka a lokacin hailarsu.11Mutanen da suka yi aikin kazanta da matan makwabtansu, mutanen da suka sa surukansu cikin kunya da kazanta; mazajen da suka ɓata 'yan'uwansu mata - 'ya'ya matan ubanninsu - dukkan waɗannan suna cikin ka.12Waɗannan mutane sun karɓi toshi a cikin ka domin su zubar da jini. Ka karɓi kuɗinka da ruwa, kaci riba mai yawa, ka ɓata maƙwabtanka da danniya, ka mance da ni - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.
13Duba! Da hannuna na bugi kazamar ribar da kaci, da kuma zubar da jinin da ke a tsakiyarka.14Zuciyarka zata tsaya, hannuwanka suyi ƙarfi a kwanakin da ni da kaina zan ɗauki mataki a kan ka? Ni Yahweh ni ne ke furta wannan, kuma zan aikata.15Zan watsar da kai cikin al'ummai in sa ka ɗaiɗaice cikin ƙasashe. Ta haka zan wanke ƙazantarka.16Ta haka za ka zama mai ƙazanta a cikin al'ummai. Sa'an nan za ka sani cewa Ni ne Ubangiji Yahweh."
17Sai kuma maganar Yahweh ta zo gare ni cewa,18"Ɗan mutum, gidan Isra'ila sun zama a yamutse a gare ni. Dukkan su sun zama ragowar tagulla da tãma da ƙarfe da dalma a cikin tsakiyar ka. Za su zama kamar gurɓatacciyar azurfa a cikin kaskonka.19Saboda haka Ubangiji Yahweh ya ce, 'Saboda ku dukka kun zama kamar gauraye, duba, saboda haka na kusa tattara ku a cikin tsakiyar Yerusalem.
20Kamar yadda mutane ke tara azurfa da tagulla da ƙarfe da tãma da dalma a maƙera su narke, su kuma hura wuta a kan su domin su narkar da su, to haka zan tattara ku cikin fushina da hasalata, zan kuma sa ku a wurin in narkar da ku.21Zan tattara ku in hura wutar hasalata a kanku, za ku kuma narke a cikin tsakiyarta.22Kamar yadda a ke narka azurfa a cikin tsakiyar maƙera, za ku narke a cikin ta, sa'an nan za ku sani cewa Ni, Yahweh na zubo da hasalata a kan ku.
23Maganar Yahweh ta zo gare ni cewa,24"Ɗan mutum ka ce da ita ke ƙasa ce wadda ba a tsabtace ba. Ba ruwan sama a cikin ranar hasala!25Akwai haɗaɗɗiyar maƙida ta annabawanta a cikinta kamar zaki mai ruri yana yaga nama. Suna kashe rai su kwashi dukiya mai daraja, suka sa gwauraye su yi yawa a cikin ta!
26Firistocinta suna yiwa shari'ata tayarwa, sun ɓata abubuwa masu tsarki. Ba su banbanta abu mai tsarki da lalatacce ba, bãsa koyar da banbanci tsakanin abu mai tsabta da marar tsabta. Sukan kawar da idanunsu daga ranakun Asabar ɗina, saboda haka suka tozarta ni a cikin su.27Hakiman da ke cikin ta kamar kerketai suke lokacin da suke yayyaga nama. Sukan kashe rai, su zubar da jini domin suci riba ta rashin gaskiya.28Annabawanta sun shafe su da farar ƙasa; suna ganin wahayoyin ƙarya suna kuma faɗa masu ƙarya. Sukan ce, "Ubangiji Yahweh ya faɗi haka" Sa'ad da Yahweh bai yi magana ba.
29Mutanen ƙasar suna yin zalunci, suna karɓar toshi, suna yin fashi, suna wulaƙanta mabuƙata da masu talauci, suna ƙwarar bãƙo da rashin adalci.
30Sai na nemi mutum ɗaya a cikin su wanda zai gina ganuwa, ya tsaya a gabana a cikin tsagar domin kada in hallaka ta, amma ban samu ba.31Saboda haka zan zuba fushin hasalata a kan su. Zan gama da da su da fushin hasalata in maida masu ayyukansu a kansu - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."

23

1Maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, akwai mata guda biyu, mahaifiyarsu kuma ɗaya.3Sun yi aikin karuwanci a Masar sa'ad da suke matasa. Sun yi aikin karuwanci a can. A can aka lagwaigwaita nonnansu, aka daƙuna kan nonnan budurcinsu.4Sunayensu su ne Ohola - ita ce babba - da Oholiba kuma ƙanwarta. Daga nan suka zama nawa suka haifi 'ya'ya maza da mata. Ga ma'anar sunayensu: Ohola tana nufin Samariya, Oholiba tana nufin Yerusalem.

5Ohola ta yi karuwanci ko sa'ad da take tawa; ta yi sha'awar masoyanta, su Asiriyawa waɗanda suke da yawa a wurin.6Gwamna mai saye da shuɗi, da jami'ansa kyawawa majiya ƙarfi, da dukkan waɗanda ke a kan dawakai.7Ta bayar da kanta karuwa a gare su, da dukkan mahimman mazaje na Asiriya, ta ƙazantar da kanta da dukkan waɗanda ta yi sha'awar su - da dukkan gumakansu.
8Gama ba ta bar halinta na karuwanci a Masar ba, sa'ad da suka kwana da ita lokacin da take yarinya, sa'ad da suke taɓa nonnanta na kuruciya, lokacin da suka fara zuba mata halinsu na lalata.9Saboda haka na miƙa ta a hannun masoyanta, a hannun Asiriyawa waɗanda ta yi sha'awar su.10Suka yi mata tsirara sun kwashe 'ya'yanta maza da mata, kuma suka kashe ta da kaifin takobi, ta zama abin kunya ga sauran mata, suka yi mata hukunci.
11Oholiba 'yar'uwarta ta ga haka, amma ta yi sha'awa fiye da ita, ta yi aikin karuwanci fiye da 'yar'uwarta.12Ta yi sha'awar Asiriyawa da gwamnoni da jami'ai waɗanda suke sa kaya masu kyau, masu hawan dawaki. Dukkan su kyawawa ne kuma ƙarfafan mutane ne.13Na ga ta kazamtar da kanta. Dukkan su sun zama ɗaya.
14Sai kuma ta ƙaru cikin karuwancinta, ta ga sifofin mazaje a kan ganuwa, waɗanda a ka zãna da siffar Kaldiyawa da jar kala,15suna ɗaure da ɗamara a gindinsu, da rawunna masu lilo a kansu. Dukkan su sun yi kama da jami'ai masu karusai, kamanninsu na 'ya'yan Babiloniyawa ne, waɗanda asalin ƙasarsu Kaldiya ce.
16Da dai idanunta suka gan su, sai ta yi sha'awar su, sai ta aiki waɗansu wurin su a cikin Kaldiya.17Sai Babiloniyawa suka zo wurin ta, wurin gadon sha'awarta, suka kazantar da ita da lalatarsu. Abin da ta yi ya kazantar da ita, sai ta ɓatar da kama ta rabu da su.
18Ta bayyana aikin karuwancinta ta nuna tsiraicinta, raina ya yi ƙyamar ta kamar yadda raina ya yi kyamar 'yar'uwarta.19Sa'an nan ta ƙara tunawa da aikin karuwanci, kamar yadda ta yi kwanakin ƙuruciyarta, sa'ad da ta zama kamar karuwa a cikin ƙasar Masar.
20Ta yi sha'awar masoyanta waɗanda mazakuttarsu ke kamar na jakuna, waɗanda kuma maniyinsu kamar na dawaki ne.21Haka ki ka yi aikin kunya a lokacin ƙuruciyarki, sa'ad da Masarawa suka taɓa kan nonnanki suka lagwaigwaita nonnanki da ke tsaye.
22Saboda haka, Oholiba, Ubangiji Yahweh ya faɗi haka, 'Duba! Zan sa mãsu ƙaunar ki su yi gãba da ke. Waɗanda kika gudu daga wurin su, za su taso maki daga kowanne sashi:23Babiloniyawa da dukkan Kaldiyawa da Fekod da Shoya da Koya da dukkan Asiriyawa tare da su da ƙarfafa da kyawawan mutane da gwamnoni da jami'ai, dukkan su jami'ai ne da mazaje masu muƙami, dukkan su suna kan dawakai.
24Za su auko maki da kayan yaƙi, da karusai da kekuna da taron mutane da yawa. Za su ta da garkuwoyi manya da ƙanana da hulunan ƙarfe kewaye da ke ko'ina. Zan ba su zarafi su hore ki, za su hore ki da ayyukansu.25Gama zan sa kishin fushina a kan ki, za su lallasa ki da fushinsu. Za su yanke hancinki da kunnuwanki, waɗanda suka tsira kuma za su faɗi da kaifin takobi. Za su kwashe 'ya'yanki maza da mata, waɗanda suka tsira kuma wuta za ta cinye su.
26Za su tuɓe kayanki su bar ki tsirara, su kwashe kayan adonki dukka.27Ta haka zan cire halinki na abin kunya da aikin karuwancinki daga ƙasar Masar. Ba za ki ƙara ɗaga idonki wajen su da marmarin ki gan su ba, ba za ki ƙara yin tunanin Masar ba.
28Gama Ubangiji ya faɗi haka. Duba! zan bayar da ke a hannun waɗanda kika ƙi su, ki koma hannun waɗanda kika juyawa baya.29Za su azabtar da ke cikin zafin ƙiyayya, za su ɗauke dukkan kayayyakinki su bar ki huntuwa. Huntancinki na karuwanci zai bayyana, halinki na kunya da lalatarki za su bayyana.
30Za a yi maki waɗannan abubuwa saboda aikinki na karuwanci, sha'awarki ta al'ummai wadda ta ƙazamtar da ke da gumakansu.31Kin yi tafiya cikin hanyar 'yar'uwarki, saboda haka zan sa ƙoƙon horona a cikin hannunki.'
32Ubangiji Yahweh ya faɗi haka, 'Za ki sha ƙoƙon 'yar'uwarki mai faɗi da zurfi. Za ki zama abin dariya da abin ba'a - cikin wannan ƙoƙon akwai abubuwa da yawa.
33Za ki cika da maye da baƙinciki, ƙoƙon fargaba da lalacewa; ƙoƙon 'yar'uwarki Samariya.34Za ki shanye shi dukka ki farfasa shi ki tsattsaga nononki da gutsattsarinsa. Gama na furta shi - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.
35Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi haka, 'Saboda kin manta da ni kin jefar da ni bayanki, ke kuma za ki ɗauki alhakin halinki na kunya da lalata."
36Yahweh ya ce da ni, "Ɗan mutum, za ka hukunta Ohola da Oholiba? To ka nuna masu ayyukansu na banƙyama,37tun da yake sun yi zina, tun da yake akwai jini a hannuwansu. Sun yi zina da gumakansu, sun sa 'ya'yansu cikin wuta, a matsayin abinci ga gumakansu.
38Sa'an nan sun ci gaba da yi mani haka, sun ɓata gidana mai tsarki, sun tozarta Asabataina.39Gama sa'ad da suka yanka 'ya'yansu ga gumakansu, rannan kuma suka zo gidana mai tsarki suka ɓata shi! To duba! Wannan shi ne abin da suka yi a tsakiyar gidana.
40Kin yi aike wurin mutanen da suka zo daga nesa, an aika manzanni - duba yanzu. To sun zo su waɗanda kika yi wanka domin su, kin yi wa idanunki kwalliya kin sa kayan adonki.41Can kika zauna a kan gado mai kyau wanda aka shirya teburi a gabansa inda kika ajiye turarena da maina.
42To ga hayaniyar babban taro kewaye da ita; ciki akwai mutane iri-iri har da masu maye daga cikin jeji, sun sa sarƙoƙi a hannuwansu da kambuna kyawawa a kawunansu.
43Sa'an nan na ce da ita, ita wadda ta tsofe a wurin karuwanci, 'Yanzu za su ƙazantu da zinarta, ita kuma da su.'44Suka je wurin ta suka kwana da ita kamar yadda mutum zai je wurin karuwa. Ta wannan hanya suka kwana da Ohola da Oholiba, kazantattun mata.45Amma mazaje masu adalci za su yi masu hukuncin mazinata, kuma za su yi masu hukunci na mãsu zubar da jini, saboda su mazinata ne kuma jini yana hannuwansu.
46To Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: zan sa taron mutane su auko masu da ta'addanci su washe su.47Sa'an nan waɗannan mutane za su jejjefe su da duwatsu su daddatsu da takubbansu. Za su karkashe 'ya'yasu maza da mata, su ƙone gidajensu.
48Gama zan cire halayen kunya daga ƙasar, in hori dukkan mataye domin kada su ƙara yin rayuwa kamar karuwai.49Haka za su sa maki halinki na kunya. Za ki ɗauki hakin zunubanki da gumakanki, ta haka za ki sani cewa Ni ne Ubangiji Yahweh."

24

1Maganar Yahweh ta zo gare ni a cikin shekara ta tara, a cikin wata na goma, a kan rana ta goma ga watan, cewa,2"Ɗan mutum, ka rubuta wa kanka sunan wannan rana, ranar nan ta yau, gama a dai-dai wannan ranar ne sarkin Babila ya ƙwace Yerusalem.

3To sai ka yi magana da misali gãba da wannan gida mai tayarwa, a misali. Ka ce da su Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Ɗora tukunyar girki. Ɗora ta ka zuba ruwa a cikin ta.4Ka tattara gutsattsarin abinci a cikin ta, kowanne yanka mai kyau - kamar su cinya da karfata - ka cika ta da ƙasusuwa zaɓaɓɓu.5A cikin garke ka ɗauki dabba zaɓaɓɓiya ka jera kasusuwan a ƙarƙashin ta. Ka sa ta tafasa ka dafa ƙasusuwan a cikin ta.
6Saboda haka, Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Kaiton birni mai jini, tukunyar girki mai tsatsa kuma tsatsar ba za ta fita daga cikin ta ba. Ka ɗauki yanka bayan yanka daga cikin ta, amma kada ka jefa ƙuri'a kan ta.
7Gama jininta yana cikin tsakiyarta, ta sa shi a kan dutse mai laushi; ba ta zubar da shi a ƙasa ta rufe shi da turɓaya ba,8ta kawo hasala dai-dai ta ɗaukar fansa. Na sa jininta a kan dutse mai laushi domin kada ya rufu.
9Saboda haka, Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Kaiton birni mai jini. Zan ƙara sa itace da yawa.10Iza itacen ka sa wuta. Ka dafa naman ya dafu sosai ka gauraye da kayan yaji ka kuma bari kasusuwan su gashe.
11Sa'an nan ka ɗora tukunyar a kan garwashi ba komai a ciki, domin ta yi zafi tagullarta ta rikiɗe, domin ƙazantar da ke cikinta ta narke, tsatsarta ta ƙone.12Ta zama gajiyayya saboda aiki, amma tsatsarta ba ta fita daga cikin ta da wuta ba.
13Halinki na kunya yana cikin ƙazantarki. Saboda nayi ƙoƙari in tsabtace ki amma har yanzu ba ki tsabtatu daga ƙazantarki ba, ba za ki sake tsabtatuwa ba sai na ƙosar da fushina a kan ki.
14Ni, Yahweh, na furta, kuma zan aikata. Ba zan janye ba, ba zan huta ba. Yadda hanyoyinki suke, yadda kuma ayyukanki suke, su za su hukunta ki! - Wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."
15Sa'an nan maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,16"Ɗan mutum! Duba zan ɗauke maka muradin idanunka daga gare ka da annoba, amma kada ka yi baƙinciki ko kuka, kada hawayenka su zubo.17Ka yi nishi a hankali. kada kayi jana'izar matattu. Ka ɗaura rawaninka a jikinka ka sa takalmanka a ƙafafunka, amma kada ka lulluɓe gashin bakinka, kada ka ci gurasar waɗanda ke makoki saboda sunyi rashin matayensu."
18Domin haka na yiwa mutane magana da safe, da yamma kuma matata ta mutu. Da safe na yi abin da aka umarce ni in yi.
19Mutanen suka tambaye ni, "Ba za ka gaya mana ma'anar waɗannan abubuwa ba, abubuwan da kake yi?"20To sai na ce da su, "Maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,21'Ka ce da gidan Isra'ila, ga abin da Ubangiji Yahweh ya fadi: Duba! Zan ƙaskantar da gidana mai tsarki - girmankan ikonku da muradin idanunku, da marmarin ranku da na 'ya'yanku maza da mata da kuka baro, za su faɗi da kaifin takobi.
22Sa'an nan za ku yi dai-dai yadda na yi: Ba za ku lulluɓe kanku ba, ba za kuci gurasar mazajen da ke yin makoki ba!23Maimakon haka rawunanku za su kasance a kan ku takalmanku kuma a ƙafafunku; ba za ku yi baƙinciki ka kuka ba, gama za ku narke cikin muguntarku, kowanne mutum zai yi nishi saboda ɗan'uwansa.24Domin haka Ezekiyal za ya zamar maku misali, yadda idan wannan abu ya zo za ku yi dukkan abin da ya yi. Sa'an nan za ku sani cewa Ni ne Ubangiji Yahweh."
25"Amma kai ɗan mutum, ran da na ƙwace haikalinsu, wanda shi ne farincikinsu, da fahariyarsu da abin da suke gani suna jin daɗi - sa'ad da kuma na ɗauke 'ya'yansu maza da mata -26a wannan rana mai gudun hijira zai zo ya ba ka labari!27A wannan rana ne bakinka zai buɗe ga wannan mai gudun hijira za ka yi magana - ba za ka ƙara yin shiru ba. Za ka zama misali a gare su domin su sani cewa Ni ne Yahweh."

25

1Sa'an nan maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, ka sa fuskar ka gãba da mutanen Amon ka yi anabci gãba da su.

3Ka ce da mutanen Amon, 'Ku ji maganar Yahweh. Wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh ya faɗi: Saboda kun ce, "Aha!" a kan wurina mai tsarki sa'ad da aka ɓata shi, da kuma gãba da ƙasar Isra'ila sa'ad da ta zama kango, da kuma gidan Yahuda sa'ad da suka tafi bauta,4saboda haka, duba, zan bashe ku ga mutanen gabas su mallake ku. Za su kafa sansani gãba da ku su kafa rumfuna a cikin ku. Za su ci 'ya'yan itatuwanku su sha madararku.5Zan maida Rabba wurin kiwon raƙuma mutanen Amon kuma saura domin garkuna. Sa'an nan za su sani cewa Ni ne Yahweh.
6Gama Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Da yake kun tafa hannuwanku kun buga ƙafafunku kun yi farinciki da ƙiyayya a cikin ku gãba da ƙasar Isra'ila.7Saboda haka, duba! Zan buge ku da hannuna in bashe ku ganima ga al'ummai. Zan datse ku daga cikin mutane in sa ku lalace daga cikin al'ummai! Zan hallaka ku, kuma za ku sani cewa Ni ne Yahweh.'
8Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan, 'Saboda Mowab da Siya sun ce, "Duba! Gidan Yahuda ya zama kamar kowacce al'umma."9Saboda haka, Duba! Zan buɗe magangarin Mowab in fara daga biranensa a kan iyaka - martabar Bet Yeshimot, Ba'al Miyon da Kiriyattayim -10domin mutanen gabas waɗanda ke gãba da mutanen Amon. Zan bayar da su a mallake su yadda ba za a ƙãra tunawa da mutanen ba a cikin al'ummai.11Haka zan yi hukunci a kan Mowab, za su kuma sani cewa Ni ne Yahweh.
12Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan, 'Idom ta ɗauki fansa a kan gidan Yahuda kuma ba ta yi dai-dai ba da ta yi haka.13Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Zan bugi Idom da hannuna in hallaka kowanne mutum da kowacce dabba a can. Zan maida su kufai, yasasshen wuri tun daga Teman har zuwa Dedan. Za su faɗi da kaifin takobi.
14Zan ɗora ramakona a kan Idom ta hannun mutanena Isra'ila, za su yi wa Idom bisa ga fushina da hasalata, kuma za su gane ramako na ne - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.'
15Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan, 'Tun da Filistiyawa sun ɗauki fansa da reni a cikin su, sun yi ƙoƙari su rushe Yahuda ba sau ɗaya ba.16To ga abin da Ubangiji Yahweh ya faɗi: Duba! Zan kai hannuna a kan Filistiyawa, zan datse Keretiyawa in hallaka waɗanda suka rage a gefen teku.17Gama zan ɗauki fansa a kan su da fushi mai zafi da horo, saboda su sani cewa Ni ne Yahweh, sa'ad da na ɗauki fansata a kan su."

26

1Ya zama a cikin wata na goma sha ɗaya, a kan rana ta fari ga watan, Maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, saboda Taya ta ce, 'Aha! A kan Yerusalem, ƙofofin mutanen yanzu an ɓalle su! ta dawo wurina; zan cika saboda ta zama kango.'

3Saboda haka, Ubangiji Yahweh ya faɗi haka, 'Duba! Ina gãba da ke Taya, zan taso da al'ummai da yawa a kan ki kamar yadda teku ya kan tada raƙuman ruwansa.4Za su rushe ganuwoyin Taya, su farfasa hasumiyoyinta. Zan share ƙurarta in sa ta zama kamar huntun dutse.
5Za ta zama wurin da a ke shimfiɗa taru ya bushe a tsakiyar teku, tun da shi ke na furta - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - kuma za ta zama ganima ga al'ummai.6'Ya'yanta waɗanda suke cikin gona za a datse su da takobi; kuma za su sani cewa Ni ne Yahweh.'
7Gama wannan shi ne abin da Yahweh ya faɗi: Duba, daga arewa zan kawo Nebukadnezza sarkin Babila, sarkin sarakuna gãba da Taya, da dawakai da karusai da masu hawan dawakai da mutane da yawa.8Za ya kashe 'ya'yanki mata a gona. Ya kafa sansani ya gina wuraren hawan ganuwarki ya tada garkuwoyi gãba da ke.
9Zai sa mabugi ya bubbuge ganuwarki, ya rushe hasumiyoyinka da kayan aikinsa.10Dawakinsa za su yi yawa har ƙurar su za ta rufe ki. Ganuwarki za ta girgiza da ƙarar mahayan dawakai da kekunan yaƙi da karusai. Sa'ad da zai shiga ƙofofinki zai shiga kamar yadda mutane ke shiga birnin da aka rushe ganuwarsa.11Kofatun dawakinsa za su yi tafiya a cikin dukkan hanyoyinki. Zai kashe mutanenki da takobi, ginshiƙanki na dutse masu ƙarfi za su faɗi har ƙasa.
12Za su kwashe dukiyarki da kayan cinikinki, za su farfasa ganuwarki su rushe gidajenki na jin daɗi. Duwatsunki da katakonki da ɓaragwazanki za su zubar da su a cikin ruwaye.13Zan tsayar da ƙarar waƙoƙinki. Ba za a ƙara jin ƙarar molayenki ba.14Zan maida ke huntun dutse, za ki zama wurin da za a shanya taru ya bushe. Ba za a sake gina ki ba, gama Ni, Ubangiji Yahweh na faɗi - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.
15Ubangiji Yahweh ya faɗawa Taya haka, 'Tsibirai ba za su girgiza ba da ƙarar faɗuwarki, da nishin waɗanda aka yiwa rauni sa'ad da wannan kisa mai muni ya zo cikin ki?16Sa'an nan dukkan yarimai na bakin teku za su sauka daga mulkokinsu su tuɓe tufafinsu, su jefar da rigunansu masu aiki. Za su rufe kansu da rawar jiki, za su zauna a ƙasa suna rawar jiki kowanne lokaci, kuma za su yi nukura saboda ke.
17Za su yi makoki a kanki su ce da ke, yaya haka, ke da kike wurin zaman masu tukin jirgin ruwa aka rushe ki. Sanannen birni mai ƙarfin gaske - yanzu ba shi a bakin teku. Su da suke zaune cikin ta suka baza labarin fargabarsu ga waɗanda ke zaune kusa da su.18Yanzu ƙasashen tudu sun girgiza da ranar faɗuwarki. Tsibirai na cikin teku sun firgita saboda kin rabu da wurin ki..
19Gama Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Sa'ad da na mayar da ke kangon birni, kamar biranen da ba kowa. Sa'ad da na taso da zurfafa a kan ki, sa'ad da manyan ruwaye suka rufe ki,20sa'ad da zan saukar da ke wurin mutanen dã, kamar waɗanda suka gangara cikin rami; gama zansa ki zauna can ƙarƙashin ƙasa kamar irin kango na zamanin dã. Saboda haka ba za ki ƙara dawowa ki tsaya a cikin ƙasar masu rai ba.21Zan saukar maki da masifa, kuma ba za ki ƙara wanzuwa ba har abada. Sa'an nan za a neme ki, kuma ba za a ƙara samun ki ba - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."

27

1Kuma maganar Yahweh ta sake zuwa gare ni cewa,2"Yanzu kai, ɗan mutum, sai ka soma makoki game da Taya,3ka kuma cewa Taya, wadda take zama kurkusa da ƙofofin teku, masu kasuwancin mutane ne ga Tsibirai da yawa, Ubangiji Yahweh ya faɗa maki haka: Taya, Kin ce, 'Ni kammalalliya ce mai kyau.'

4Iyakokinki suna cikin tsakiyar zuciyar tekuna; maginanki sun kamalla kyaunki;5Sun yi katakan ki da siferas daga Tsaunin Hamon; sun ɗauko sida daga Lebanon domin su yi maki sandar tukin jirgi.
6Sun sarrafa sandar tukin jirginki da itace na Bashan; suka yi matakalar ki da katakan siferas daga Saifrus, suka kuma lulluɓe ta da hauren giwa.7Mayafanki mayafai masu ƙawa ne daga Masar da ke a matsayin tutarki; launin shuɗi da shunayya daga gaɓar Elisha a na amfani da su domin kare jirgin ruwanki.
8Waɗanda suka zauna cikin Sidon da Abad su ne matuƙanki; masu hikima na Taya na cikin ki; su ne masu yi maki jagora.9Ƙwararru masana masu aikin hannu daga Baibilos sun gyarta tsagaggun wurarenki; dukkan jiragen teku da matuƙansu da ke cikin ki suna ɗaukar kayan fatauci domin kasuwanci.
10Fãsha da Lidiya da kuma Libiya suna cikin rundunarki, mayaƙãnki sun rataye garkuwa da ƙwalƙwali a cikin ki; suka bayyana darajarki.11Mazajen Abad da Helek da ke cikin rundunarki sun zama katanga zagaye da ke, kuma mutanen Gammad su ne hasumiyoyinki. Sun rataye garkuwoyinsu a kan katangu zagaye da ke! Suka kammala kyaunki.
12Tarshish abokiyar kasuwancinki ce saboda yawan wadatar dukiyarki ta sayarwa: da azurfa, da baƙin ƙarfe, da tãma, da dalma. Suka saya suka kuma sayar da kayayyakin ki!13Yaban da Tubal da kuma Meshek-sun sayar da bayi da kuma kayayyaki na tagulla. Suka sarrafa kayan fataucinki.
14Bet Togama ta tanadi dawakai, da dawakan yaƙi da alfadarai a matsayin kayan fataucinki.15Mazajen Rodes suka zama yan kasuwarki a tsibirai masu yawa. Fatauci na cikin hannunki; suka kuma aiko maki ƙaho da hauren giwa da katakai masu ƙarfi a matsayin kyautai.
16Aram babbar 'yar kasuwa ce da kayayyakin ki masu yawa; suka tanada koren dutse mai daraja da shunayya, kaya mai launuka, da yãdi mai kyau da tsakiya da sauran kayan ado a matsayin kayan fataucinki.17Yahuda da Isra'ila abokan kasuwancin ki ne. Suka tanada alkama daga Minit, waina da zuma, da mai, da ƙãro a matsayin kayan fataucinki.18Dimaskus dillaliyar dukkan kayayyakin da kika sarrafa ce, ta hamshaƙiyar dukiyarki, da kuma ruwan inabi na Helbon da ulun Zaha.
19Dan da Yaban daga Izal suka yi maki fataucin ɗanyen ƙarfe da ɓawon ƙirya, da ƙansa-ƙansa. Wannan ya zama abin fatauci domin ki.20Dedan ce mai samar maki da mashinfiɗai na sirdin dawakai masu kyau.21Arebiya da dukkan shugabannin Keda suna ciniki da ke; sun samo maki 'yan raguna da raguna da awaki.
22'Yan kasuwa na Sheba da Rama suka zo su sayar maki da kowanne irin kayan ƙamshi mafiya daraja da kowanne irin dutse mai daraja; suka yi safarar zinariya domin fataucinki.23Haran da Kane da Iden su ne abokan kasuwancinki, tare da Sheba da Ashu da kuma Kilmad.
24Waɗannan su ne dillalanki waɗanda ke sayar da kayan ƙawa (kayayyaki masu daraja na sãƙaƙƙun kayan ãdo), da kuma cikin barguna masu zane iri-iri da sãƙaƙƙun kaya a cikin kasuwannin ki.25Jiragen ruwa na Tarshish su ne masu kawo maki kayayyakin fataucinki! Domin haka ki ka cika, aka loda maki kaya masu nauyi a tashoshin jiragen ruwanki.
26Matuƙan jiragen ruwanki suka kawo ki ga manyan tekuna; iskar gabas ta karya ki a tsakiyar su.27Dukiyarki, da abin fataucinki da kuma kayan kasuwancinki; matuƙan jiragenki, da mãsassaƙa jiragen ruwa; abokan cinikinki da dukkan mayaƙan da ke cikin ki da dukkan ma'aikatan jiragenki- za su nutse cikin zurfin teku a ranar hallakarki.
28Biranen kusa da teku za su yi rawar jiki da jin ƙarar kukan masu yin jagoran jiragen ruwanki;29Dukkan matuƙan jiragen za su sauko daga jiragensu; ma'aikata da majayan hanya za su sauka su tsaya kan ƙasa.30Sa'an nan za susã ki saurari muryarsu za su kuma yi kuka mai zafi; za su watsa ƙura a kawunansu. Za su kwanta suna birgima cikin toka.
31Za su aske sumar kansu dominki su kuma ɗaure kansu da tsummokin makoki, kuma za su yi kuka mai zafi su kuma tãda murya ƙwarai.32Za su tãda muryarsu ta makoki mai zafi dominki su kuma furta kalamai na habaici a kanki, wane ne kamar Taya, wadda yanzu aka sa tayi shiru a tsakiyar teku?33A lokacin da fataucinki ya kai bakin teku, yana biyan buƙatar mutane masu yawa; kin azurtar da sarakunan duniya da dukiyarki da fataucinki!
34Amma lokacin da teku ya ragargaza ki, ta zurfafan ruwaye, fataucinki da dukkan ma'aikatanki suka nutse!35Mazaunan tsibirai suka gan ki suka tsorata da ke, kuma sarakunansu suka yi rawar jiki mai ban razana! Fuskokinsu suka gigice!36Fatake suka yi maki tsãki, kin zama abin razana, kuma ba za a sake ganin ki ba har abada."

28

1Sai maganar Yahweh ta zo mani, cewa,2"Ɗan mutum, ka yi magana da shugaban Taya, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: zuciyarka tunƙaho! Kãce, 'Ni allah ne! zan zauna a cikin mazaunin alloli a tsakiyar tekuna!" koda shi ke kai mutum ne ba allah ba, ka maida zuciyarka kamar ta allah;3kana tunanin ka fi Daniyel hikima, kuma babu asirin da ke ba ka mamaki!

4Ka maishe da kanka mawadaci da hikima da fasaha, ka kuma tara zinariya da azurfa cikin ma'ajin ka!5Ta wurin babbar hikima da kuma kasuwanci, ka ruɓanɓanya wadatarka, sai zuciyarka ta kumbura saboda dukiyarka.
6Saboda haka, Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: domin ka maida zuciyarka kamar zuciyar allah,7Zan kawo bãƙi gãba da kai, Mazaje masu ban razana daga waɗansu al'ummai. Za su kawo takubba gãba da kyakkawar hikimarka, kuma za su wulaƙanta darajarka.
8Za su tura ka cikin rami, kuma za ka mutu mutuwa irin ta masu mutuwa cikin tsakiyar tekuna.9Ka iya cewa, 'Ni allah ne' a fuskar mai kashe ka? Kai mutum ne ba Allah ba, kuma za ka zama a hannun wanda yake caccakar ka.10Za ka yi mutuwar marasa kaciya ta hannun bãƙi, gama na furta haka - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."
11Maganar Yahweh ta sake zuwa gare ni karo na biyu, cewa,12"Ɗan mutum, ka tãda makoki domin sarkin Taya kace da shi, "Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: ka zama misalin kammala, cike da hikima da kammalanlen kyau.13Kana cikin Iden, lambun Allah. Kowanne dutse mai daraja ya rufeka; da rubi, da tofaz, da imeral, da kiraisolet, da oniks, da yasfa, da saffiya, da tokwayis, da beril. Tsare-tsarenka da haɗuwarka anyi su ne da zinariya. A ranar da aka hallice ka ne aka shirya su.
14Na ajiye ka a bisa tsauni mai tsarki na Allah a matsayin kerubim da na shafe domin ya yi tsaron 'yan adam. Kana cikin tsakiyar dutse ma wuta inda ka yi yawo.15Kana da aminci a tafarkunka tun daga ranar da aka hallice ka har sai da aka sami rashin adalci cikin ka.
16Ta wurin girman kasuwancinka ka cika da ta'addanci, domin haka ka yi zunubi. Saboda haka sai na jefar da kai daga tsaunin Allah, kamar wadda ya ƙazanta, kuma sai na hallakar da kai, kerubim mai tsaro, na kore ka daga cikin duwatsu masu wuta.17Zuciyarka ta cika da tunƙaho domin kyaunka; ka wofintar da hikimarka saboda darajarka. Na koro ka ƙasa. Na sanya ka a gaban sarakuna domin su gan ka.
18Saboda zunubanka masu yawa da kuma rashin amincin kasuwancinka, ka ƙazantar da wurarenka masu tsarki. Domin haka na sa wuta ta fito daga gare ka; zata cinye ka. Zan maishe ka toka a fuskar dukkan waɗanda suke kallon ka.19Dukkan waɗanda suka san ka cikin mutanen za su girgiza kai; za su yi fargaba, kuma ba za a sake ganinka ba har abada."'
20Sai maganar Yahweh ta zo mani, cewa,21"Ɗan mutum, ka sa fuskar ka gãba da Sidon ka kuma yi annabci gãba da ita.22Ka ce, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Duba! Ina gãba da ke, Sidon! Gama za a ɗaukaka Ni a tsakiyarki domin mutanenki su sani cewa Ni ne Yahweh a lokacin da zan zartar da adalci a cikin ki. Za a nuna ni mai tsarki cikin ki.
23Zan aika da annoba cikin ki da jini cikin titunanki, kuma waɗanda aka kashe za su faɗi a tsakiyarki. A lokacin da takobin zata tashi gãba da ke ta ko'ina, sa'an nan za ki sani cewa Ni ne Yahweh.24Daga nan ba za a sami wata sarƙaƙiya da ƙaya mai azaba domin gidan Isra'ila ba daga dukkan waɗanda ke zagaye da ita waɗanda ke raina mutanenta ba, haka za su sani cewa Ni ne Ubangiji Yahweh!'
25Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan, 'Lokacin da na tara gidan Isra'ila daga cikin mutane waɗanda aka tarwatsa su, kuma lokacin da na keɓe cikin su, domin al'ummai su gani, sa'an nan za su gina gidajensu a cikin ƙasar da zan ba bawana Yakubu.26Sa'an nan za su zauna lafiya cikin ta su kuma gina gidaje, su shuka gonakin inabi, su kuma zauna lafiya a lokacin da zan shar'anta dukkan waɗanda suka rena su yanzu daga dukkan kewaye; Da haka za su sani Ni ne Yahweh Allahnsu!"'

29

1A cikin shekara ta tara, a watan goma a ran sha biyu ga wata, maganar Yahweh ta zo mani, cewa,2"Ɗan mutum, ka juya fuskar ka gãba da Fir'auna, sarkin Masar; ka yi annabci gãba da shi da kuma gãba da dukkan Masar.3Ka furta ka ce, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Duba! Ina gãba da kai, Fir'auna, sarkin Masar. Kai, babbar dabbar teku da ke ɓuya cikin tsakiyar kogi, da ke cewa, "Kogi nawa ne. Na yi shi domin kaina."

4Gama zan sa ƙugiya a cikin bakinka, kuma kifaye na cikin Nilunka za su liƙe bisa ɓawonka; Zan tãda kai sama tare da dukkan kifayen kogin da suka manne wa ɓawonka.5Zan jefar da kai cikin hamada, kai da dukkan kifaye daga koginka. Zaka faɗi a buɗaɗɗen fili; ba za a tãra ka ko a tãda kai sama ba. Zan bada kai abinci ga hallitun ƙasa da kuma tsuntsayen sammai.
6Sa'an nan dukkan mazaunan Masar za su sani cewa Ni ne Yahweh, domin sun zama sandar matsala ga gidan Isra'ila.7A lokacin da suka riƙe ku da hannunsu, kun karye kun kuma yage kafaɗarsu; da suka jingina a kanku, sai kuka karye, sai kuma kuka sa ƙafafunsu suka kasa tsayawa.
8Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Duba! Zan kawo takobi gãba da kai. Zan datse mutum da dabba daga gare ka.9Sai ƙasar Masar ta zama yasasshiya da kuma kufai. Sa'an nan za su sani cewa Ni ne Yahweh, domin dabbar teku ta ce, "Kogin nawa ne, gama ni na yi shi."10Domin haka, duba! Ina gãba da kai kuma ina gãba da koginka, don haka zan bayar da ƙasar Masar ga hallakarwa da lalacewa, kuma za ta zama lalatacciyar ƙasa daga Migdol zuwa Sãyin da kuma iyakokin Kush.
11Babu ƙafafun mutum da za shi wuce ta cikin ta, kuma babu ƙafar naman jeji da za shi wuce cikin ta. Ba za a zauna cikin ta ba har shekaru arba'in.12Gama zan maida Masar ƙango a tsakiyar ƙasar da ba a zama cikin ta, kuma biranenta a tsakiyar lalatattun birane za su zama kufai har shekaru arba'in; sa'an nan zan tarwatsa Masar cikin al'ummai, in kuma watsa su cikin ƙasashe.
13Gama Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: a ƙarshen shekara arba'in zan tara Masar daga cikin mutanen da aka watsar da su.14Zan dawo da abin da ke na Masar in kuma dawo da su zuwa ga yankin Fatros, zuwa ga ƙasar su ta asali. Sa'an nan za su zama masarauta marar muhimmanci a can.
15Zata zama ƙasƙantacciyar masarauta cikin masarautu, kuma ba za a ɗaga ta sama ba cikin al'ummai. Zan ƙasƙantar da su domin kada su yi mulkin al'ummai.16Masarawa ba za su ƙara zama dalilin ƙarfin zuciya ga gidan Isra'ila ba. Maimakon haka, za su zama abin tunawa da zunubin da Isra'ila ta aikata a lokacin da suka juya ga Masar neman taimako. Sa'an nan za su sani cewa Ni ne Ubangiji Yahweh."'
17Sai ya zama a cikin shekara ta ashirin da bakwai a ranar farko ta watan ɗaya, maganar Yahweh ta zo mani, cewa,18"Ɗan mutum, Nebukadneza sarkin Babila ya shirya rundunarsa su yi aiki mai wuya gãba da Taya. Kowanne kai an murje shi har sai ya yi saiƙo, kuma kowacce kafaɗa ta gogu. Duk da haka shi da rundunarsa ba su karɓi lada daga wurin Taya domin aiki mai wuyar da ya yi gãba da ita ba.
19Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: 'Duba! Ina bayar da Masar ga sarki Nebikadneza sarkin Babila, kuma zai kwashe dukiyarta, ya kwashe mallakarta, ya tafi da duk abin da ya iske a can; wannan zai zama ladar rundunarsa.20Na ba shi ƙasar Masar domin aikin da suka yi mani - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.
21A wannan rana zan sa ƙaho ya taso domin gidan Isra'ila, kuma na sa ku yi magana a tsakiyarsu, domin su san cewa Ni ne Yahweh."

30

1Maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Ku yi kururuwa, "Kaiton ranar mai zuwa."3Ranar ta kusa. Ranar ta gabato domin Yahweh. Za ta zama rana ce ta hadarai, lokaci na masifa ga al'ummai.

4Sa'an nan takobi zata zo gãba da Masar, kuma za a yi ƙunci a cikin Kush a lokacin da mutanen da aka kashe suka fǎɗi a Masar - a lokacin da suka ɗauki dukiyarsu, da kuma lokacin da ginshiƙanta aka warwatsar.5Kush da Libiya, da kuma Lidiya, da dukkan Arebiya, tare da mutanen da ke na alƙawari - dukkan su za su fãɗi ta dalilin takobi.
6Yahweh ya faɗi wannan: Waɗanda suka tsaya tare da Masar za su fǎɗi, kuma girman ƙarfin ta zai fǎɗi ƙasa. Daga Migdol zuwa Siyen sojojinsu za su fǎɗi da takobi - wannan furcin Yahweh ne.7Za su zama wofi a tsakiyar yasassun ƙasashen, kuma biranen su za su zama cikin dukkan rusassun biranen.
8Sa'an nan za su san cewa Ni ne Yahweh, yayin da na cinna wuta cikin Masar, kuma lokacin da aka hallaka dukkan mataimakanta.9A wannan ranar 'yan saƙo za su fito daga gare ni cikin jirage su addabi tsararrar Kush, kuma za a yi azaba a cikin su a wannan rana ta azabar Masar. Duba! Tana zuwa.
10Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Zan kawo ƙarshen taron jama'ar Masar ta hannun Nebukadneza, sarkin Babila.11Shi da rundunarsa tare, ta'addar al'ummai, za a hallakar da ƙasar; za su zare takobinsu gãba da Masar su kuma cika ƙasar da gawawwakin mutane.
12Zan maishe da rafuffuka busassun ƙasa, zan kuma sayar da ƙasar cikin hannun mugayen mutane. Zan maishe da ƙasar da dukkan cikarta kufai ta hannun bãƙi- Ni, Yahweh, na yi magana.
13Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: zan hallakar da gumaka, kuma zan kawo iyakar gumakan Memfis marasa amfani. Ba za a sake samun yarima cikin ƙasar Masar ba, kuma zan sa ta'adda a bisa ƙasar Masar.14Sa'an nan zan sa Fatros ta zama kufai in kuma cinna wuta a Zowan, kuma zan aiwatar da ayyukan shari'a a kan Tebes.
15Gama zan zubo da fushi na a bisa Felusiyom, kangararren wuri na Masar, in kuma datse taron jama'ar Tebes.16Sa'an nan zan cinna wuta a Masar; Felusiyom za ta zama da azaba mai tsanani, Tebes za ta kakkarye, Memfis kuma za ta fuskanci magabta a kowacce rana.
17Majiya ƙarfi cikin Heliyofolis da Bubastis za su fǎɗi ta takobi, kuma birninsu zai tafi bauta.18A Tafahes, rana za ta ƙi bada haskenta sa'ad da na karya karkiyar Masar a nan, za a ƙarar da alfarmar ikonta. Girgije zai rufe ta, kuma 'ya'yanta mata za su tafi bauta.19Zan aiwatar da ayyukan shara'a a Masar, domin su sani cewa Ni ne Yahweh.'"
20Sai ya kasance a cikin shekara ta sha ɗaya, cikin wata na farko, a cikin kwana na bakwai na watan, da maganar Yahweh ta zo mani, cewa,21"Ɗan mutum, na karya hannun Fir'auna, sarkin Masar. Duba! Ba a rigaya an ɗaure masa ciwon ba, ko a shirya shi ya warke da bandeji, saboda ya yi ƙarfi ya kama takobi.
22Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: 'Duba, ina gãba da Fir'auna, sarkin Masar. Gama zan karya hannunsa, da mai ƙarfin da wanda aka karye, kuma zan sa takobin ya fǎɗi daga hannunsa.23Sa'an nan zan tarwatsa su cikin Masar cikin al'ummai in kuma watsa su cikin ƙasashe.24Zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babila in kuma ɗibiya takobina a cikin hannunsa domin in hallaka hannun Fir'auna. Zai yi nishi a gaban sarkin Babila da nishi kamar na mutum mai mutuwa.
25Gama zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babila, amma hannun Fir'auna zai faɗi. Sa'an nan za su sani cewa Ni ne Yahweh, a lokacin da zan sa takobina cikin hannuwan sarkin Babila; gama zai kai wa Masar farmaki da ita.26Don haka zan watsar da Masar cikin al'ummai In kuma tarwatsa su a cikin ƙasashe. Sa'an nan za su sani cewa Ni ne Yahweh."'

31

1Sai ya zama a cikin shekara ta sha ɗaya, a wata na uku, a rana ta farko ta watan, da maganar Yahweh ta zo mani, cewa,2"Ɗan mutum, ka ce da Fir'auna, sarkin Masar, da kuma ga taron jama'arsa da ke kewaye da shi, 'girman kujerarka, kama da wa kake?

3Duba! Asiriya ta zama sida a cikin Lebanon da kyawawan rassa, ta na bada inuwa ga jejin, kuma doguwa ce, kuma rassanta suka zama ƙoƙuwar itace.4Ruwaye masu yawa suka sa tayi tsayi; zurfafan ruwaye suka sa tayi faɗi. Rafuka suka gangara dukka kewaye da sashenta, gama hanyoyinsu sun bi ta dukkan hanyoyi zuwa ga dukkan itatuwan fili.
5Tsawonsa mai girma yafi sauran itatuwa da ke a filin, kuma rassanta sun zama da yawa; rassanta suka yi tsayi sabili da ruwaye masu yawa sa'ad da suke girma.6Kowanne tsuntsun sammai na zama cikin rassanta, haka kuma kowacce halita mai rai na cikin filin suna haifar 'ya'yansu a ƙarƙashin inuwarsa. Dukkan al'ummai masu yawa suna zama a ƙarƙashin inuwarsa.7Gama yana da kyau a cikin girmansa da kuma tsayi a rassansa, gama saiwarsa na cikin ruwaye masu yawa.
8Sida na cikin gonar Allah ba su kai shi ba. A cikin itatuwan gora babu waɗanda suka kai rassansa, kuma itacen durumi bai kai shi rassa ba. Babu wani itace a cikin lambun Allah da ke kamar sa cikin kyaunsa.9Na yi shi da kyau da rassansa masu yawa kuma dukkan itatuwan Iden da ke cikin lambun Allah suka yi kishinsa.
10Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Saboda yana da tsawo, kuma ya sa dogayen rassansa a tsakanin rassansa, ya ɗaukaka zuciyarsa sabili da tsawonsa.11Na rigaya na bayar da shi cikin hannuwan jarumi na al'ummai, ya yi masa dai-dai da muguntarsa. Na wurga shi waje.
12Bãƙi waɗanda ke ta'addanci a dukkan al'ummai suka datse shi suka bar shi ya mutu. Rassansa suka fãɗi a kan tsaunuka da kuma dukkan kwari, rassansa suka kakkarye a cikin dukkan magudanun ruwaye na ƙasar. Sai dukkan al'ummai na duniya suka fito daga ƙarƙashin inuwarsa suka kuma tafi suka bar shi.
13Dukkan tsuntsayen sararin sama suka sauka bisa tushen itacen da ya fãɗi, kuma kowacce dabba ta fili ta zo rassansa.14Wannan ya faru ne domin kada wata itaciyar ta tsiro kusa da ruwayen ta ɗaga ganyayesu zuwa ga itatuwa mafiya tsawo, kuma kada waɗansu itatuwa su yi girma gefen ruwayen su kai tsayinta. Dukkan su an sa sun mutu, a can ƙasa, a cikin 'ya'yan mutane, tare da waɗanda suka gangara cikin rami.
15Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: A ranar da sida ya gangara zuwa Lahira na kawo makoki cikin duniya. Na rufe zurfafan ruwaye bisanta, na kuma tsayar da ruwayen teku. Na tsai da ruwaye masu girma, na kuma kawo makoki ga Lebanon dominsa. Saboda haka dukkan itatuwan saura suka yi makoki sabili da shi.
16Na kawo rawar jiki ga al'ummai ta dalilin ƙarar faɗuwarsa, a lokacin da na wurga shi cikin lahira tare da waɗanda suka gangara zuwa cikin rami. Sai na ta'azantar da dukkan itatuwan da ke a Iden a cikin wuraren duniya a ƙasa. Waɗannan su ne da zaɓaɓɓu da kuma mafi kyaun itatuwa na Lebanon; itatuwan da suka sha ruwan.
17Gama suma suka gangara tare da shi zuwa Lahira, zuwa ga waɗanda aka kashe da takobi. Waɗannan su ne ƙarfin hannunsa, waɗannan al'umman da suka zauna cikin inuwarsa.18Wacce itaciya ce dai-dai da ke a ɗaukaka da girma? Gama za a kawo ki ƙasa tare da itatuwan Iden zuwa ƙarkashin ƙasa a tsakanin marasa kaciya; za ka zauna tare da waɗanda aka kashe da takobi.' Wannan shi ne Fir'auna tare da dukkan taronsa - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."

32

1Sa'an nan ya kasance a cikin wata na sha biyu ta shakara ta sha biyu, a rana ta farko ga watan, da maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, tãda makoki domin Fir'auna sarkin Masar; ka ce masa, 'Ka na kamar ɗan zaki a cikin al'ummai, amma ka zama kama da dodon ruwa na cikin teku; ka na dama ruwa, ka na dãma ruwaye da ƙafafunka ka kuma yamutsa ruwayensu.

3Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Haka zan warwatsa tãruna bisan ka cikin mutane da yawa, kuma za su ɗaga ka cikin tãruna.4Zan yashe ka cikin ƙasar. Zan wurga ka cikin fili in kuma sa dukkan tsuntsayen sammai su zauna bisanka; yunwar dukkan dabbobi masu rai a duniya za su ƙoshi ta wurin ka.
5Gama zan sa naman ka a bisa tsaunuka, zan kuma cika kwarurruka da gawarka cike da tsutsotsi.6Sa'an nan zan watsar da jininka a bisa tsaunuka, ruwayen ƙarƙarshin ƙasa za su cika da jininka.
7Bayan na katse ka, Zan rufe sammai in kuma baƙantar da taurarinsu; Zan rufe rana da giza-gizai, wata kuma ba zai bada haskensa ba.8Dukkan haske masu haskakawa a sammai zan baƙanta su bisan ka, zan kuma sa duhu bisa ƙasarka - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.
9Da haka zan tsoratar da zuciyar mutane da yawa a cikin ƙasashen da ba ka sani ba, a lokacin da na kawo rushewarka a tsakiyar al'ummai, cikin ƙasashen da ba ka sani ba.10Zan firgita mutane da yawa saboda kai; sarakunansu za su girgiza cikin tsoro saboda kai a lokacin da zan jujjuya takobina a gabansu. A kowacce sa'a kowa zai yi rawar jiki saboda kai, a ranar faɗuwar ka.
11Gama Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Takobin sarkin Babila zai auko gãba da kai.12Zan sa taron jama'arka mutanenka su faɗi ta hannun takobin jarumi - kowanne jarumi ɗan ta'adda ne ga al'ummai. Waɗannan jarumawa za su lalatar da fahariyar Masar su kuma lalata dukkan tarurrukanka.
13Gama zan lalatar da dukkan garkunan da ke a bakin magudanun ruwaye masu yawa; tafin ƙafar mutum ba zai ƙara dãma ruwan ba, ko kuma kofatun dabbobi su dãma su.14Sa'an nan zan kwantar da ruwansu in sa ƙogunansu su zubo kamar mai - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.
15A sa'ad da na maida Masar yasasshiyar ƙasa, lokacin da aka maida ƙasar abin wofi sarai da dukkan cikarta, bayan na kai hari ga mazaunanta, za su san cewa Ni ne Yahweh.16Za a yi makoki; 'ya'ya mata na al'ummai za su yi makoki domin ta; za su yi makoki domin Masar, domin dukkan taruwar jama'arta za su yi makoki - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."'
17Hakanan ya faru a cikin shekara ta sha biyu, a ranar sha biyar ga wata, da maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,18"Ɗan mutum, ka yi kuka domin taron jama'ar Masar ka kuma jawo su ƙasa - ita da 'ya'yanta mata masu daraja na al'ummai-- zuwa cikin ƙarƙashin ƙasa tare da sụ waɗanada suke gangarawa cikin rami.
19'Ki na da kyau fiye da wani? Je ƙasa ki kwanta da marasa kachiya.'20Za su faɗi daga cikin waɗanda aka kashe da takobi. An zare takobin! An miƙa ki ga takobin; za su kama ta tare da taron jama'arta.21Mafi ƙarfi daga cikin jarumawa a Lahira zai yi magana game da Masar da kuma abokan amanarta. Sun gangaro zuwa nan! Za su kwanta tare da marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.'
22Asiriya ta na can tare da dukkan jama'arta. Kaburburanta suna zagaye da ita; dukkansu an kashe su da takobi.23Su waɗanda kaburburansu na can cikin wuri mai zurfin rami su na can, da dukkan jama'arta. Kaburburanta sun zagaye dukkan waɗanda aka kashe, su da suka faɗi ta wurin takobi, su da suka jawo masifa a bisa ƙasar masu rai.
24Ilam na wurin tare da dukkan taron. kaburburanta na zagaye da ita; dukkan su aka kashe su. Waɗanda suka faɗi ta wurin takobi, su da suka gangara ƙasa babu kaciya zuwa wurin zurfafa na iyakar ƙasa, su da suka kawo ta'addancin su bisa ƙasar masu rai kuma su waɗanda suke ɗauke da kunyarsu, tare da waɗanda suke gangarawa cikin rami.25Suka shirya wa Ilam makara da dukkan taron ta cikin tsakiyar waɗanda aka kashe; kaburburanta sun zagaye ta. Dukkan su marasa kaciya ne, an sha zararsu da takobi, domin sun kawo ta'addancinsu cikin ƙasar masu rai. Domin haka suna ɗauke da kunyarsu, tare da su waɗanda suke gangarawa zuwa cikin rami a tare da dukkan waɗanda aka kashe, waɗanda suke gangarawa zuwa cikin rami. Ilam na cikin dukkan waɗanda aka kashe.
26Meshek, Tubal, da dukkan taron suna wurin! Kaburburansu na kewaye da su. Dukkansu marasa kaciya ne, aka kashe da takobi, domin sun kawo ta'addancinsu cikin ƙasar masu rai.27Ba su kwanta da jarumawan da suka faɗi na marasa kaciya waɗanda suka gangara zuwa Lahira da dukkan makamansu na yaƙi ba, kuma da dukkan makamansu ƙarƙashin kawunansu da kuma kurakuransu bisa ƙasusuwansu. Gama su ne 'yan ta'adda na jarumawa a cikin ƙasar masu rai.
28To ke, Masar, za a kakkarya ki a cikin takiyar marasa kaciya! Za ki kwanta tare da waɗanda aka sare su da takobi.29Idom na wurin tare da sarkinta da kuma dukkan shugabanninta. An sanya su cikin ƙarfinsu tare da waɗanda aka kashe da takobi. Tare da marasa kaciya suka kwanta, tare da waɗanda suka gangara cikin rami.
30Sarakunan arewa suna wurin - dukkansu da kuma dukkan Sidoniyawa waɗanda suka gangara ƙasa tare da waɗanda aka sare su. Suna da matuƙar karfi kuma suka sanya waɗansu jin tsoro, amma yanzu suna wurin cikin kunya, marasa kaciya tare da waɗanda aka sare da takobi. Sun ji kunyarsu, tare da waɗanda suke gangarawa cikin rami.
31Fir'auna zai gani ya kuma karfafa game da dukkan taron jama'arsa waɗanda aka sare da takobi - Fir'auna tare da dukkan sojojinsa - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.32Na sa shi a matsayin mai ban tsoro a cikin ƙasar masu rai, amma za a ajiye shi ƙasa a tsakiyar marasa kaciya, cikin waɗanda aka sare da takobi, Fir'auna da dukkan taron jama'arsa - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."

33

1Sa'an nan maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Dan mutum, ka faɗa wa mutanenka wannan; ka ce masu, 'Sa'ad da na kawo takobi gãba da wata ƙasa, sai mutanen wannan ƙasar suka ɗauki ɗaya da ga cikin su suka maishe shi mai tsaro domin su.3Zai riƙa duba idan takobi ya taso wa ƙasar sai ya busa ƙahonsa ya faɗakar da mutane!4Idan mutanen suka ji ƙarar ƙaho amma ba su yi lura ba, idan kuma takobi ya zo ya kashe su, to kowanne ɗayansu alhakin jininsa na kansa.

5Idan wani ya ji ƙarar ƙaho amma ya ƙyale, alhakin jininsa na kansa; amma idan ya kula, zai ceci na sa ran.6Idan kuwa, mai tsaro ya ga takobi yana tasowa, amma bai busa ƙaho ba, sakamakon bai faɗakar da mutane ba, takobi ya zo ya ɗauki ran wani, wannan mutum ya mutu cikin zunbinsa, zan biɗi alhakin jininsa daga hannun mai tsaro.'
7Yanzu kai da kanka, ɗan mutum! Na saka ka zama mai tsaron gidan Isra'ila; za ka ji maganganu daga bakina kayi gargaɗi a madadi na.8Idan na cewa mugun mutum, 'Kai mugu, hakika za ka mutu!' Amma idan ba ka faɗakar da wannan ba domin a gargaɗi mugu game da hanyarsa, mugun nan zai mutu cikin zunubinsa, amma zan biɗi alhakin jininsa a hannun ka!9Amma idan kai, ka gargaɗi mugu game da hanyarsa, domin ya juyo ya bar ta, idan bai juyo yabar hanyarsa ba, to zai fa mutu cikin zunubinsa, amma kai da kanka ka riga ka ceci ranka.
10Saboda haka, ɗan mutum, ka cewa gidan Isra'ila, 'Kuna cewa haka, 'Kurakuranmu da zunubanmu suna kanmu, muna kuma ruɓewa a cikin su! Ƙaƙa za mu rayu?'"11Ka ce masu, 'Muddin ina raye - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - ba na farinciki da mutuwar mugu, domin idan mugu ya tuba daga hanyarsa, zai rayu! Ku Tuba! Ku Tuba daga mugayen hanyoyinku! Donme ne ne za ku mutu, gidan Isra'ila?'
12Yanzu kai, ɗan mutum, ka cewa mutanenka, 'Ayyukan adalcin adali ba zai cece shi ba idan ya yi zunubi! Muguntar mugun mutum ba za ta sa shi ya hallaka ba, idan ya tuba daga zunubinsa! Domin mai adalci ba zai iya rayuwa ba saboda adalcinsa idan ya yi zunubi.13Idan na cewa adali, "Ba shakka za ka rayu!" idan kuwa ya dogara ga adalcinsa sa'an nan ya aikata rashin gaskiya, ba zan tuna da adalcinsa ba ko guda ɗaya. Zai mutu saboda muguntar da ya yi.
14Idan na cewa mugu, "Ba shakka za ka mutu," amma kuma sai ya tuba daga zunubinsa ya aikata abin adalci da gaskiya -15idan ya mayar da ƙwacen da ya yi da sunan jingina, ko kuma ya mayar da abin da ya sata, kuma idan ya yi tafiya a cikin farillan rai ya dena yin laifi - ba shakka zai rayu. Ba zai mutu ba.16Ba za a kuma tuna masa da laifofinsa waɗanda ya aikata ba. Gama ya aikata gaskiya da adalci, saboda haka, zai rayu!
17Amma mutanenka suka ce, "Hanyar Ubangiji ba dai-dai take ba!" alhali hanyoyinku ne ba dai-dai ba!18Sa'ad da adali ya juya daga adalcinsa ya yi zunubi, zai mutu cikinsa!19Sa'ad da mugu ya juya ya bar muguntarsa ya yi abin da ke gaskiya da adalci, zai rayu saboda waɗannan abubuwa!20Amma ku mutane kun ce, '"Hanyar Ubangiji ba dai-dai ba ce!" Zan shar'anta kowannenku bisa ga hanyarsa, gidan Isra'ila.'"
21Wannan ya faru a shekara ta goma sha biyu, a rana ta biyar ga watan goma na bautar talalarmu, wani ɗan gudun hijira ya zo guna da ga Yerusalem ya ce, "An ci birnin!"22Hannun Yahweh yana bisana da maraice kafin ɗan gudun hijiran ya zo, bakina kuma ya rigaya ya buɗe kafin lokacin zuwansa da safe. Bakina kuwa ya buɗe; ban ƙara yin shuru ba!
23Sa'an nan maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,24"Ɗan mutum, waɗanda suke zaune cikin kango a ƙasar Isra'ila suna magana suna cewa, 'Ibrahim kaɗai ne ya gaji ƙasar, amma mu, muna da yawa! An riga an ba mu ƙasar a matsayin mallaka.'
25Saboda haka ka ce masu, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi: Kuna cin nama da jini, kuna bautar gumakanku sa'an nan kuna zubda jinin mutane. Lallai sai kun mallaki ƙasar?26Kun kafa dogararku ga takubba, kunyi abubuwan banƙyama; kowannenku yana zina da matar maƙwabcinsa. Ya kamata ku mallaki ƙasar kenan?'
27Za ka faɗa masu haka, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Muddin ina raye, 'hakika waɗanda ke kufai za a kashe su da takobi, zan kuma bada waɗanda ke jeji ga hallitu masu rai su zama abincinsu, waɗanda ke cikin kagaru da koguna annoba za ta kashe su.28Sa'an nan zan maida ƙasar kufai da kuma abin tsoro, ƙarfinta na taƙama zai ƙare, gama za a bar duwatsun Isra'ila, ba wanda zai ratsa ta cikinsu.'29Gama za su sani Ni ne Yahweh, sa'ad da na maida ƙasar kufai a lalace saboda dukkan abubuwan banƙyamar da suka aikata.
30Yanzu kai, ɗan mutum - mutanenka suna faɗin abubuwa game da kai a jikin garu da ƙofofin gidaje, suna cewa junansu - kowanne mutum ga ɗan'uwansa, 'Bari mu je mu saurari maganar annabi wadda ta zo daga Yahweh!'31Mutanena za su zo wurinka, kamar yadda suka saba yi, za su zauna a gabanka su saurari maganganunka, amma ba za su yi biyayya da su ba. Maganganu masu kyau suna bakinsu, amma zukatansu na bin ƙazamar riba.
32Gama kai kamar waƙa mai daɗi ne a gare su, ƙyakkyawar murya da a ke rairawa a kan garaya, lallai za su kasa kunne ga maganarka, amma ba ko ɗaya da zai yi biyayya da ita.33Saboda haka idan duk waɗannan sun faru - duba! haka kuwa zai faru! - sa'an nan ne za su sani annabi ya kasance a tsakanin su."

34

1Sai maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, ka yi annabci gãba da makiyayan Isra'ila. Yi annabci ka ce masu, 'Ubangiji Yahweh ya cewa makiyaya: Kaiton makiyayan Isra'ila masu kiwon kansu. Bai kamata masu kiwo su tsare garke ba?3Kuna cin rabo mai tsoka kuna kuma sa tufafi na ulu. Kuna yanka masu ƙiba cikin garke. Baku yin kiwo ko kaɗan.

4Ba ku ƙarfafa waɗanda ke da cututtuka ba, ko ku warkar da marasa lafiya. Waɗanda suka karye, ba ku ɗori su ba, waɗanda aka kora ba ku dawo da su ba ko ku nemo ɓatattu. Maimakon haka, kun mallaƙesu ƙarfi da yaji.5Sai suka warwatse saboda ba makiyayi, suka zama nama ga kowanne mai rai a jeji bayan an warwatsar da su.6Tumakina suka yi makuwa a kan duwatsu da tsaunuka, suka kuma warwatsu a dukkan faɗin duniya. Duk da haka ba wanda ya ke neman su.
7Saboda haka, makiyaya, ku ji maganar Yahweh:8Da dawwamata - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - saboda tumakina sun zama ganima da abinci ga kowanne naman jeji, saboda rashin makiyayan kirki, kuma masu kiwon garkena ba su nemo tumakin ba, amma makiyayan sun kãre kansu, ba su yi kiwon garkena ba.
9Saboda haka, makiyaya, ku ji maganar Yahweh:10Ubangiji Yahweh ya faɗi: Duba! Ina găba da masu kiwon tumakina, zan nemi tumaki na a hannunsu. Sa'an nan zan sallame su daga kiwon garkena; makiyayan ba za su ƙara kiwon kansu ba tunda zan ƙwace garkena daga bãkinsu, domin kada tumakina su ƙara zama abincinsu.
11Gama Ubangiji Yahweh ya faɗi: Duba! Ni da kaina zan nemo garkena in kuma lura da su,12kamar yadda makiyayi yakan nemi tumakinsa da suka watse daga cikin garkensa. Haka zan nemo tumakina, zan kuma cecesu daga dukkan wuraren da aka warwatsa su a ranar hadari da duhu.13Sa'an nan zan fito da su daga cikin al'ummai; zan tattaro su daga ƙasashe dabam dabam in kawo su ƙasarsu. Zan saukar da su a wurin kiwo mai dausayi a gefen duwatsu na Isra'ila, a maɓugɓugai, a dukkan wuraren da mutane ke zaune a ƙasar.
14Zan sa su a makiyaya mai kyau; manyan duwatsun Isra'ila za su zama wurin kiwonsu. Za su kwanta a wurin kiwo mai kyau, inda akwai ciyawa da yawa, za su yi kiwo a tsaunukan Isra'ila.15Ni da kai na zan yi kiwon garkena, Ni da kaina kuma zan sa su kwanta - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne -16Zan nemo ɓatattu in kuma dawo da waɗanda aka watsar da su. Zan ɗora karyayyun tumaki, in warkar da marasa lafiya amma masu ƙiba da ƙarfafa zan hallaka su. Zan yi kiwo da adalci.
17Yanzu dai ku, garkena - ga abin da Ubangiji Yahweh ya faɗa - duba, zan shar'anta tsakanin tunkiya da tunkiya, tsakanin raguna da bunsurai.18Bai isa ba ku ci ciyawa mai ƙyau, sai kun tattake ragowar da ƙafafunku; ku kuma sha ruwa mai kyau, sai kuma kun gurɓata rafin dukka da ƙafafunku?19Dole ne tumakina suci abin da kuka tattake da ƙafafunku, su kuma sha abin da kuka gurɓata da ƙafafunku?
20Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗa masu haka: Duba! Ni da kaina zan shar'anta tsakanin tumaki masu ƙiba da ramammu,21domin kun tunkuɗe su da kwankwasonku da kuma kafaɗunku, kun kuma tunkuɗe dukkan marasa ƙarfi da ƙahonninku har sai da kuka warwatsar da su daga ƙasar.
22Zan ceci garkena ba za su ƙara zama ganima ba, zan shar'anta tsakanin tunkiya da tunkiya!23Zan ɗora makiyayi guda a bisansu, bawana Dauda. Shi zai yi kiwon su, zai ciyar da su, zai kuma zama makiyayinsu.24Gama Ni, Yahweh, zan zama Allahnsu, kuma bawana Dauda zai zama sarki a cikin su - Ni, Yahweh, na furta wannan.
25Sa'an nan zan yi alƙawarin salama da su in fitar da mugayen dabbobi a ƙasar, domin su zauna lafiya a jeji su kuma yi barci lafiya a kurmi.26Zan kuma kawo albarku a bisan su da kuma wurare kewaye da tuddaina, domin zan aiko da ruwan sama a lokacinsa. Zai zama ruwan albarka.27Sa'an nan itatuwan saura za su bada 'ya'yansu, ƙasa za ta bada amfaninta. Tumakina za su zauna lafiya a ƙasarsu; sa'an nan ne za su sani cewa Ni ne Yahweh, sa'ad da zan karya gungumen kãrkiyarsu, in kuma cece su daga hannun waɗanda suka bautar da su.
28Ba za su ƙara zama ganima ga al'ummai ba, mugayen namomin jeji a bisa ƙasa ba za su cinye su ba. Gama za su zauna lafiya, ba kuma wanda zai tsoratasu.29Gama zan ƙebe masu mazaunin salama domin kada a ƙara zama da yunwa a cikin ƙasar, al'ummai kuma ba za su kawo zargi a kansu ba.
30Sa, an nan za su sani cewa Ni, Yahweh Allahnsu, ina tare da su. Su jama'ata ne, gidan Isra'ila - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.31Gama ku tumakina ne, garken makiyayata, mutanena, ni kuma Allahnku ne - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.'"

35

1Sa'an nan maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2'‌Ɗan mutum, kasa fuskarka gãba da Tsauna Seyir ka yi annabci gãba da shi.3Ka ce masa, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi: Duba! Ina gãba da kai, Tsauni Seyir, kuma zan buge ka da hannuna in maishe ka kufai abin watsarwa.

4Zan maida biranenka kufai, kai kuma da kanka za ka zama kango; sa'an nan za ka sani cewa Ni ne Yahweh.5Domin kullum kana ƙiyayya da mutanen Isra'ila, kuma domin ka bashesu a hannun takobi a lokacin ƙuncinsu, a lokacin da hukuncinsu yake da zafi.6Saboda haka, Muddin ina raye - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - zan shiryaka domin zubar da jini, alhakin jini zai bi ka! Tun da ba ka ƙi zubar da jini ba, alhakin jini zai bi ka.
7Zan maida Tsaunin Seyir kufai gaba ɗaya sa'ad da na datse mai shiga cikinsa da mai fita.8Sa'an nan zan cika duwatsunsa da gawawwakinsa. Da tuddansa da kwarurukansa da dukkan rafuffukansa, waɗanda aka kashe da takobi za su fǎɗa.9Zan sa ka yi ta zama kufai. Ba za a zauna cikin biranenka ba, amma za ka sani cewa Ni ne Yahweh.
10Ka ce, "Waɗannan al'ummai biyu da ƙasashen nan biyu za su zama nawa, zan kuma mallakesu," koda yake Yahweh yana tare da su.11muddin ina raye - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - zan sãka maka gwargwadon fushinka da gwargwadon kishi da ƙiyayyar da ka yiwa Isra'ila, kuma zan bayyana kaina gare su sa'ad da na shar'anta ka.
12Sa'an nan za ka sani cewa Ni ne Yahweh. Na ji ɓatancin da ka yi gãba da duwatsun Isra'ila, sa'ad da ka ce, "An lalatar da su; an rigaya an ba mu su mu cinye."13Ka ɗaukaka kanka gãba da ni da abin da ka faɗa, ka yi maganganu da yawa gãba da ni; na kuma ji su dukka.
14Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Zan maishe ka kufai, dukkan duniya za suyi murna.15Kamar yadda ka yi murna da gãdon mutanen Isra'ila saboda ta zama kufai, kai ma zan yi haka da kai. Za ka zama kufai, Tsaunin Seyir da dukkan Idom - dukkanta! Sa'an nan za ka sani cewa Ni ne Yahweh."'

36

1Yanzu dai, ɗan mutum, ka yi annabci ga tsaunukan Isra'ila ka ce, "Tsaunukan Isra'ila, ku saurari maganar Yahweh.2Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Magabci ya ce a kanka, "Aha!" kuma "Daɗaɗɗun tuddai na dã sun zama mallakarmu.'"3Saboda haka ka yi annabci kace, Ubangiji Yahweh ya ce: Saboda an maishe ka kufai an kuma murƙushe ka ta kowacce fuska, ka zama abin mallaka ga sauran al'ummai; ka zama abin ɓatanci a leɓuna da harsuna, a kuma labaran mutane.

4Saboda haka, Tsaunukan Isra'ila, ku kasa kunne ga maganar Ubangiji Yahweh: Ubangiji Yahweh ya faɗi haka ga tsaunuka, da tuddai, da rafuffuka da kwarurruka, da kufafan da ba kowa da yasassun biranen da aka washe su sun zama ganima da abin ba'a ga sauran al'umman da ke kewaye da su -5saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Hakika nayi magana cikn zafin fushina da hasalata gãba da sauran al'ummai, gãba da Idom da dukkan waɗanda suka ƙwace ƙasata suka maisheta mallakarsu, gãba da dukkan masu murna a zuciyarsu ko reni a ruhunsu, yadda suka ƙwace ƙasata domin su mallaki wuraren kiwo su zama nasu.'6Saboda haka, ka yi annabci a kan ƙasar Isra'ila ka cewa tsaunuka da kuma tuddai, da rafuffuka da kwarurruka, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Duba! A cikin fushina da hasalata nake furta wannan domin ka jure da zage-zagen al'ummai.
7Saboda haka, Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Ni da kaina zan ɗaga hannuna in rantse cewa al'ummai da ke kewaye daku tabbas za su sha tasu kunyar.
8Amma ku, tsaunuka Isra'ila, za ku yi rassa ku haifi 'ya'ya domin mutanena Isra'ila, domin bada daɗewa ba za su komo wurinku.9Ku duba, Ni naku ne, na yi maku tagomashi; za a huɗe ku a kuma shuke ku da iri.
10Saboda haka zan ruɓanya maku yawan mutanenku, koda dukkan gidan Isra'ila ne. Birane za su kasance da mazauna, za a sake gina rusassun wurare.11Zan riɓaɓɓanya mutum da dabba a kanku ku tsaunuka saboda su ruɓaɓɓanya su hayayyafa. Sa'an nan Zan sa a zauna a cikin ku kamar yadda kuke dã, zan sa ku yalwata fiye da dã, domin ku sani cewa Ni ne Yahweh.12Zan kawo mutane, jama'ata Isra'ila, su tattaka ku. Za su mallakeku, za ku zama gãdonsu, ba za ku ƙara sa 'ya'yansu su mutu ba.
13Ubangiji Yaweh ya faɗi haka: Saboda suna ce maku, "Ku na cinye mutane, kuna sa 'ya'yan al'ummarku suna mutuwa,"14saboda haka ba za ku ƙara cinye mutane ba, ba za ku ƙara sa al'ummarku ta yi makokin mutuwarsu ba. Wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.15Ba zan ƙara bari ku sake sauraren zage-zagen al'ummai ba, ba za ku ƙara jin kunyan mutane ba ko ku sa al'ummarku ta faɗi - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.'"
16Sa'an nan maganar Yahweh ta zo wuri na, cewa,17"‌Ɗan mutum, sa'ad da gidan Isra'ila suka gaji ƙasarsu, suka ƙazamtar da ita ta wurin hanyoyinsu da ayyukansu. Hanyoyinsu a gabana kamar ƙazantar hailar mace suke.18Saboda haka na zuba hasalata gãba da su, domin zubar da jini da suka yi a ƙasar da kuma ƙazantarsu ta wurin gumakansu.
19Na warwatsa su cikin al'ummai; suka warwatsu cikin ƙasashe. Na hukunta su gwargwadon hanyoyinsu da ayyukansu.20Sai suka tafi cikin al'ummai, duk inda suka tafi, sai suka ɓata sunana mai tsarki sa'ad da mutane suka ce masu: 'Da gaske waɗannan mutanen Yahweh ne? Gama an fitar da su daga ƙasarsa.'21Amma ina da juyayi saboda sunana mai tsarki wanda gidan Isra'ila ya ƙazantar cikin al'ummai lokacin da suka tafi can.
22Saboda haka ka cewa gidan Isra'ila, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: 'Ba saboda ku nake wannan ba, gidan Isra'ila, amma saboda sunana mai tsarki, wanda kuka ɓata a cikin al'ummai dukkan inda kuka tafi.23Gama zan sa sunana mai girma ya zama da tsarki, wanda kuka ɓata a cikin al'ummai - a tsakiyar al'ummai, kuka ɓata shi. Sa'an nan al'ummai za su sani cewa Ni ne Yahweh - wannan furcin Ubagiji Yahweh ne - sa'ad da za ku ga Ni mai tsarki ne.
24Zan kwasoku daga cikin al'ummai, in tattaro ku daga kowacce ƙasa, zan kawo ku ƙasarku.25Sa'an nan zan yayyafa maku tsabtataccen ruwa domin ku tsarkaka daga dukkan ƙazantarku, zan kuma tsarkake ku daga gumakanku.
26Zan ba ku sabuwar zuciya da sabon ruhu a cikinku, zan ɗauke zuciyar dutse daga cikinku. Gama zan ba ku zuciyar tsoka.27Zan sa Ruhuna a cikinku in sa ku kuyi tafiya a cikin farillaina da kiyaye umarnaina, domin ku yi su.28Sa'an nan za ku zauna a ƙasar da na ba kakanninku; za ku zama mutanena, ni kuma in zama Allahnku.
29Gama zan ceceku daga dukkan ƙazantarku. Zan sa hatsi ya yawaita. Ba zan ƙara nawaitaku da yunwa ba.30Zan yawaita 'ya'yan itatuwa da amfanin gona domin kada ku ƙara jin kunya a wurin al'ummai saboda yunwa.31Sa'an nan za ku yi tunani a kan mugayen hanyoyinku da ayyukanku masu banƙyama, za ku nuna naɗama a fuskokinku sabili da zunubanku da kuma mugayen ayyukanku.
32Ba dominku nake yin wannan ba - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - yakamata ku san wannan. Saboda haka, ku kunyata ku ƙasƙanta, saboda hanyoyinku ku gidan Isra'ila.33Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: A ranar da na tsarkake ku daga dukkan kurakuranku, zan sa ku zauna a birane, ku kuma gina rusassun wurare.34Gama za ku noma ƙasa wadda take kufai a dã masu wucewa wurin ba za su gane ta ba.
35Sa'an nan za su ce, "Wannan ƙasa wadda dă kufai ce yanzu ta zama kamar lambun Iden; rusassun birane da rusassun wurare waɗanda suka zama kufai an yi masu garu a na kuma zama a cikin su."36Sa'an nan sauran al'ummai da ke kewaye daku za su sani cewa Ni ne Yahweh, mai gina rusassun wurare da mai zaunar da mutane a yasassun wuri. Ni ne Yahweh. Ni na faɗi haka, zan kuma aiwatar da shi.
37Ubangiji Yahweh ya faɗi: Gidan Isra'ila za su roƙe ni in yi masu haka, in riɓaɓɓanya su kamar garken mutane.38Kamar garken da aka keɓe domin hadayu, kamar garke a Yerusalem a lokacin bukukuwan idi, haka rusassun birane za su cika da ɗumbun mutane za su kuma sani cewa Ni ne Yahweh."'

37

1Hannun Yahweh yana bisa na, ya fito da ni waje ta wurin Ruhun Yahweh kuma ya zaunar da ni a tsakiyar wani kwari; yana cike da ƙasusuwa.2Daga nan ya sani na bi ta tsakiyar su ina ta zagayawa, Duba! Da yawansu birjik suna cikin kwarin. Duba! Ga su busassu ƙayau.3Sai ya ce mani, "'Dan mutum, ƙasusuwan nan za su iya rayuwa kuma?" Sai na ce, "Ubangiji Yahweh, kai kaɗai ka sani."

4Daga nan ya ce mani, "'Ka yi annabci a kan waɗannan ƙasusuwa ka ce masu, 'Busassun ƙasusuwa. Ku saurari maganar Yahweh.5Ubangiji Yahweh ya cewa ƙasusuwan nan: Duba! Zan sa numfashi a cikinku, za ku kuma rayu.6Zan sa jijiyoyi a jikkunanku in kuma sa tsoka. Zan rufe ku da fata in hura numfashi a cikinku domin ku rayu. Daga nan za ku sani cewa Ni ne Yahweh.'"
7Sai na yi anabci kamar yadda ya umarce ni; da na ke anabcin, duba, sai wata ƙara ta fito, mai girgiza. Sai ƙasusuwan suka marmatso ga junansu - ƙashi ya haɗu da ƙashi a mahaɗinsu.8Da na duba, ai kuwa, sai ga jijiyoyi a kansu, tsoka kuma ta fito fata kuma ta rufe su. Amma ba numfashi a cikinsu tukuna.
9Daga nan Yahweh ya ce mani, "Yi anabci a kan numfashi, yi anabci, ɗan mutum, ka ce da numfashi, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Numfashi, ka zo daga kusurwai huɗu, ka hura a kan waɗannan da aka kashe, domin su rayu.'"10Sai na yi anabci kamar yadda aka umarce ni; numfashi ya shiga cikinsu suka rayu. Daga nan suka miƙe a kan ƙafafunsu, babbar rundunar mayaƙa.
11Daga nan Yahweh ya ce da ni, "Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwan gidan Isra'ila ne dukka. Duba! Suna cewa, 'Kasusuwanmu sun bushe, zuciyarmu ta karai. An datse mu.'12Saboda haka ka yi anabci ka ce masu, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Duba! Zan buɗe kabarbarunku in tashe ku daga cikinsu, ya ku mutane na. Zan dawo daku ƙasar Isra'ila.
13nan za ku sani cewa Ni ne Yahweh, sa'ad da na buɗe kabarbarinku na tashe ku daga cikin su, mutane na.14Zan sa Ruhuna a cikin ku domin ku rayu, zan sa ku huta a ƙasarku sa'ad da kuka sani ni ne Yahweh. Ni na faɗa kuma zan aikata - wannan furcin Yahweh ne.'"
15Sa'an nan maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,16"Yanzu dai, ɗan mutum, ka ɗauki sanda guda domin kanka ka yi rubutu a kan sa, 'Domin Yahuda da mutanen Isra'ila abokan tarayya.' Sa'an nan ka ɗauki wata sandar ka yi rubutu a kansa, 'Domin Yosef reshen Ifraim kuma domin dukkan mutanen Isra'ila, abokan tarayya.'17Haɗa biyun su zama sanda guda, domin su zama ɗaya a hannunka.
18Sa'ad da mutanenka za su yi maka magana, su ce, 'Ba za ka gaya mana abin da kake nufi da waɗannan ba?'19sai ka ce masu, 'Ubangiji Yahweh ya ce: Duba! Ina ɗauke reshen Yosef da ke hannun Ifraim da kabilar Isra'ila abokan tarayyarsa domin in haɗa shi da Yahuda, domin su zama sanda guda, za su kuma zama ɗaya a hannuna.'20Ka riƙe sandunan da ka yi rubutu a kansu a hannunka a kan idanunsu.
21Ka furta masu, Ubangiji Yahweh yafaɗi wannan: Duba! Ina gab da fitar da mutanen Isra'ila daga cikin al'ummai inda suka tafi. Zan tattaro su daga ƙasashen kewaye in kuma dawo da su ƙasarsu.22Zan tattaro su al'umma ɗaya a ƙasar, a kan tsaunukan Isra'ila, sarki guda ne zai yi sarauta bisansu dukka, ba za su ƙara zama al'umma biyu ba. Ba za a ƙara raba su zuwa masarautai biyu ba.23Daga nan ba za su ƙara ƙazantar da kansu da gumakansu ba, da abubuwansu na ban ƙyama, ko kowanne irin zunubansu ba. Gama zan cece su daga dukkan ayyukan rashin aminci waɗanda da su suka yi mani zunubi, zan kuma tsarkake su, domin su zama mutanena ni kuma in zama Allahnsu.
24Bawana Dauda zai zama sarki bisansu. Domin su kasance da makiyayi ɗaya a bisansu dukka, za su yi tafiya bisa ga dokokina su kuma kiyaye farillaina su yi biyayya da su.25Za su zauna a ƙasar da na ba bawana Yakubu, inda ubanninku suka zauna. Za su zauna cikin ta har abada - da su, da 'ya'yansu, da jikokinsu, gama bawana Dauda zai zama sarkinsu har abada.
26Zan kafa alƙawarin salama da su. Zai zama madawwamin alƙawari ne da su. Zan kafa su in ruɓanɓanya su, in kuma kafa wurina mai tsarki a tsakaninsu har abada.27Mazaunina zai kasance tare da su; zan zama Allahnsu, su kuma za su zama mutanena.28Daga nan al'ummai za su sani cewa Ni ne Yahweh da na ƙeɓe Isra'ila da bam, sa'ad da wurina mai tsarki yana cikinsu har abada.'"

38

1Maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2Ɗan mutum, ka juya ka fuskanci Gog, ƙasar Magog, babban yariman Meshek da Tubal; ka kuma yi anabci gãba da shi.3Ka ce, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Duba! ina gãba da kai, Gog, babban yariman Meshek da Tubal.

4Domin in juya ka in kuma sa maka ƙugiya a muƙamuƙinka; Zan fitar da kai da dukkan sojojinka, da dawakai, da mahaya dawakan, dukkansu sun sa kayan yaƙi sosai, babbar runduna da manyaan garkuwoyi da ƙananan garkuwoyi, dukkan su suna riƙe da takubba!5Fasiya, Kush, da Libiya suna tare da su, dukkan su da garkuwoyi da hulunan kwano!6Goma da dukkan rundunarta, da Bet Togama, daga arewa mafi nisa, da dukkan rundunarta! Mutane da yawa na tare da kai!
7shiri!, ka shirya kanka da tawagarka da suka yi layi tare kai, ka zama kwamandansu.8Bayan waɗansu kwanaki da waɗansu za a kiraka, kuma bayan waɗansu shekaru za ka je wata ƙasa da ta farfaɗo daga takobi wadda kuma aka tattaro daga mutane masu yawa, tattare aka koma tsaunin Isra'ila wanda ya ci gaba da zama kango. Amma mutanen ƙasar za a fito da su daga mutanen, kuma za su zauna cikin tsaro, dukkan su!9Saboda za ka tashi sama kamar yadda hadari ke yi; za ka zama kamar girgijen da yake rufe ƙasar, da duk rundunar sojojinka, da sojoji masu yawa da ke tare da kai.
10Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: zai kuma faru a wannan ranar da aka tsara wannan shiri a zuciyarka, kuma za ka ɓata mugayen shirye-shirye.'11Daga nan za ka ce, zan je can buɗaɗɗiyar ƙasa; zan je wurin mutane masu natsuwa da ke zama cikin tsaro, dukkan su da ke rayuwa a inda babu garu ko danga, inda babu ƙofofin birane.12Zan kwaso kayayyaki in saci ganima, domin in kawo hannuna gaba da kangayen da yanzu mutane suka fara zama, da kuma gaba da al'ummai waɗanda ke samun dabbobi da kayayyaki, waɗanda kuma ke zama a tsakiyar duniya.'
13Sheba da Dedan, da 'yan kasuwar Tarshish haɗe da matasan mayaƙanta za su ce da kai, Kun zo ne domin ku kwashi ganima? Kun tattara sojoji ne domin ku kwashi ganima, domin ku kwashi azurfa da zinariya, ku kuma kwashi dabbobinsu da kayayyaki ku kuma kwashi garar ganimar yaƙi?'
14Saboda haka, ɗan mutum ka yi anabci, ka ce da Gog, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: A wannan rana, lokacin da mutanena Isra'ila na zama cikin tsaro, ba za ku koyi wani abu ba game da su?15Za ku fito daga wurarenku a can arewa mafi nisa tare da babbar rundunar sojoji, dukkan su suna kan dawakai, babbar runduna, manyan mayaƙa.16Za ka kai hari ga mutanena Isra'ila kamar girgijen da ya rufe ƙasar. A kwanaki masu zuwa zan kawo ka gãba da ƙasata, domin ƙasashe su san ni a lokacin da na nuna kaina ta wurinka, Gog, ka zama da tsarki a idanunsu.
17Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Ba ku ba ne waɗanda na yi magana a kan ku a waɗancan kwanaki ta hannun bayina, annabawan Isra'ila, waɗanda suka yi anabci a nasu lokuttan game da shekarun da zan kawo ku gãba da su?18Haka zai faru a waɗancan kwanaki bayan Gog ya kai hari ƙasar Isra'ila - wannan furcin Yahweh ne - fushina zai yi ƙuna a cikin hasalata.
19A cikin himmata da kuma cikin wutar fushina, na furta cewa za'a yi babbar girgizar ƙasa a ƙasar Isra'ila.20Za su girgiza a gabana - da kifayen teku da tsuntsayen sama, da dabbobin saura, da dukkan dabbobi masu rarrafe a duniya, da kowanne mutum da ke a doron ƙasa. Za'a ragargaza duwatsu ɓallin zai faɗi, har sai kowacce kusurwa ta faɗi a kan duniya.
21Zan kawo takobi a kansu a kan dukkan duwatsu -wannan shi ne furcin Ubangiji Yahweh - kowanne mutum zai juya takobinsa gãba da ɗan'uwansa.22Bayan wannan zan hukunta shi da annoba da jini; da kuma ambaliyar ruwa da aman duwatsu da tattatsin wuta zan saukar a kansa shi da rundunarsa da dukkan al'umman da ke kewaye da shi.23Domin zan nuna girmana da tsarkina zan kuma sa al'ummai da yawa su san ni, za su kuma sani cewa Ni ne Yahweh.'"

39

1"Yanzu, kai ɗan mutum, ka yi annabci gãba da Gog ka ce, Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Duba! ina gãba da kai Gog, sarkin Meshek da Tubal.2Zan juya ka in bi da kai; Zan kawo ka daga can arewa in kawo ka tsaunukan Isra'ila.3A sa'an nan ne zan bugi bakanka daga hannunka na hagu in kuma sa kibiya ta faɗi daga hannunka na dama.

4Za ka fãɗi ƙasa matacce a kan tsaunukan Isra'ila -kai da tawagar da ke tare da kai da kuma sojojin da ke tare da kai. Zan miƙa ka ga tsuntsayen sama da dabbobin dawa ka zama abincinsu.5Za ka faɗi ƙasa a saura, domin ni da kaina na furta haka - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.6Daga nan zan aika da wuta a kan Magog a kan kuma masu zama cikin tsaro a wurare masu nisa, za su kuma sani cewa Ni ne Yahweh.
7Domin zan sa su san sunana mai tsarki a tsakiyar mutanena Isra'ila, kuma ba zan taɓa yadda sunana ya ɓaci ba; al'ummai za su sani cewa Ni ne Yahweh, mai Tsarki na Isra'ila.8Duba! Rana na zuwa, kuma za ta zo - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.
9Masu zama a biranen Isra'ila za su fita za su mori makamai su kunna wuta su ƙone su - ƙananan garkuwoyi, da manyan garkuwoyi, da bakkuna, da kibau, da kwarin mashi; za su wuta da su har tsawon shekaru bakwai.10Ba za su tattara itatuwa daga saura ba ko su sassaro bishiyoyi daga dawa, tun da ya ke za su ƙona makamansu; za su ɗauka daga wurin waɗanda ke son su ɗauka daga gare su; za su baje waɗanda suka so su baje su - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."
11Kuma zai zamana a wannan rana zan tanada wuri domin Gog - maƙabarta a Isra'ila, kwari ga waɗanda ke tafiya cikin gabashin kwarin teku. Zai toshe waɗanda ke son ƙetarewa su haye. A can za su binne Gog da dukkan mutane masu yawa da ke tare da shi. Za su kira shi kwarin Hamon Gog.
12Har tsawon watanni bakwai gidan Isra'ila za su binne su domin su tsarkake ƙasar.13Domin dukkan mutanen ƙasar za su binne su; za su zama abin tunawa a gare su a lokacin da na sami ɗaukaka - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.
14A sa'an nan ne za su keɓe mutanen da za su ci gaba da tafiya a cikin ƙasar, domin su sami waɗanda ke tafiya a ciki, amma waɗanda suka mutu gangar jukkunansu kuma na waje a ƙasar za su iya su binne su, domin su tsarkake ƙasar. A ƙarshen shekarun nan bakwai za su fara bincikensu.15A lokacin da mutanen nan ke tafiya a cikin ƙasar, bayan sun ga ƙashin mutum za su sa alama a gefenta, har sai masu haƙar kabari sun zo domin su binne su a kwarin Hamon Gog.16Za'a sami wani birni a can ta wurin sunan Hamona. A wannan hanya za su tsarkake ƙasar.
17Yanzu a gare ka, ɗan mutum, Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Ka faɗi wannan ga dukkan tsuntsayen sama da dukkan dabbobin daji, 'Ku taru wuri ɗaya ku zo. Ku tattaru daga ko'ina ku kewaye hadayar da ni kaina nake miƙawa a kan tsaunukan Isra'ila, domin ku ci gangar jiki ku kuma sha jini.18Za ku ci jikkunan mayaƙa ku kuma sha jinin shugabannin duniya; za su zama raguna, da 'yan raguna, da awaki. da bijimai, duk sun yi ƙiba a Bashan.
19Daga nan za ku ci wadataccen kitse ku ci ku ƙoshi; ku kuma sha jini har sai kun bugu; wannan ita ce hadayar da zan yanka dominku.20A kan teburina za ku ƙoshi da dawakai, da karusai, da mayaƙi, da dukkan jaruman yaƙi - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.'
21Zan sa ɗaukakata a cikin al'ummai, kuma dukkan al'ummai za su ga hukuncina da nayi da kuma hannuna da na sa nake gãba da su.22Gidan isra'ila za su sani cewa Ni ne Yahweh Allansu daga wannan rana zuwa gaba.
23Al'ummai za su sani cewa gidan Isra'ila sun je bauta saboda laifofinsu wanda ta wurinsu suka bashe ni, domin haka na ɓoye fuskata daga gare su, na kuma miƙa su ga abokan gãbarsu domin a hallaka dukkan su da takobi.24Na yi masu gwargwadon ƙazantarsu da zunubansu, a lokacin da na kawar da fuskata daga gare su.
25Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan; Yanzu zan komo da damar Yakubu, kuma zan ji tausayin dukkan gidan Is'raila, a lokocin da na yi haka da himmar sunana mai tsarki.26A lokacin za su sha kunyarsu a cikin dukkan cin amanar da suka bashe ni. Za su manta da duk wannan a lokacin da suka huta a cikin ƙasarsu cikin tsaro, inda ba wanda zai firgita su.27lokacin da na komo da su daga cikin jama'a na kuma tattaro su daga ƙasar maƙiyansu, zan nuna kaina a matsayin mai tsarki a idon al'ummai masu yawa.
28Sa'an nan za su sani cewa Ni ne Yahweh Allahnsu, domin na aika su zuwa bauta a cikin al'ummai, amma zan sake tattara su a ƙasarsu. Ba zan rage ko ɗaya daga cikinsu ba a cikin al'ummai.29Ba zan sake ɓoye fuskata daga garesu ba a lokacin da na huro Ruhuna a kan gidan Isra'ila - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."

40

1A cikin shekara ta ashirin da biyar ta bautar talalarmu a farkon shekara a rana ta goma ga wata, A shekara ta sha huɗu bayan an kame birnin a wannan dai ranar, hannun Yahweh na bisana ya kuma ɗauke ni zuwa can.2A cikin wahayai daga Allah sai ya kawo ni zuwa ƙasar Isra'ila. Ya kawo ni in huta a kan tsauni mai tsawo sosai; a ɓangaren kudu inda abin da ya bayyana ya zama gine-ginen birni.

3Sai ya kawo ni can. Sai ga wani mutum! Bayyanuwarsa kamar bayyanuwar tagulla. Yana ɗauke da igiyar linin da sandar awo a hannunsa, sai ya tsaya a bakin ƙofar birnin. Mutumin ya ce da ni,4"Dan mutum, ka duba da idanunka ka kuma saurara da kunnuwanka, ka kuma maida hankali ga dukkan abin da nake bayyana maka, domin an kawo ka nan ne domin in bayyana maka su. Ka bada rahoton duk abin da za ka gani ga gidan Isra'ila."
5Akwai katangar da ta kewaye haikali. Tsawon sandar awon a hannun mutumin kamu shida ne. Dukkan mizanan tsawonsu iri ɗaya. Sai ya auna katangar; ta kai kamu ɗaya da rabi na tsawon sandar awon.6Daga nan sai ya tafi ƙofar haikali da ke fuskantar gabas. Sai ya hau kan matakansa ya auna ginshiƙin ƙofar tsawonsa shi ne dai-dai tsawon sandar gwajin a zurfi.7Ɗakunan tsaron dukkan su kamun sandar awon ɗaya a tsawo kuma ɗaya ne a fãɗi; akwai tsawon kamu biyar a tsakanin kowanne ɗakuna biyu, kuma daga dankarin shirayin haikalin akwai kwararo mai tsayi da aka kafa ƙasa.
8Sai ya auna kwararon ƙofar; faɗinsa ya kai kamu guda na sandar awon.9Ya auna kwararon ƙofar. Zurfinsa ya kai kamu guda na sandar awo. Madogaran ƙofofin sun kai kamu biyu a fãɗi. Wannan shi ne kwararon ƙofar da ke fuskantar haikali.10Akwai ɗakunan tsaro guda uku a kowacce kwana a ɓangaren gabas, kuma dukkan su suna da awo iri ɗaya ne, kuma katangar da ta raba su ita ma awo iri ɗaya ne.
11Daga nan mutumin ya auna faɗin ƙofar shiga - aka sami kamu goma; kuma faɗin ƙofar shiga - ya kai kamu goma sha uku.12Sai ya auna katangar da ke iyaka da ɗakuna na gaba - tsayinta kamu guda ne. Aka auna ɗakunan kowannen su ya kai kamu shida a kowanne gefe.13Daga nan sai ya auna ƙofar shiga daga rufin ɗaya daga cikin ɗakin har zuwa ɗaki na gaba - aka sami kamu ashirin da biyar, daga ƙofar farko ta shiga ɗakin har ya zuwa ta biyun.
14Daga nan ya auna katangar da ta bi ta tsakanin ɗakunan tsaron - tsawonsu ya kai kamu sittin; ya auna har ya zuwa kwararon ƙofar.15Mashigi daga ƙofar gaba har ya zuwa kwararon ƙofar ƙarshen kamu hamsin.16Akwai kullallun tagogi a kusa da ɗakunan da kuma kusa da madogaran da ke cikin dukkan ƙofofin da ke kewayen; hakannan kuma zaurukan. Akwai tagogin da ke kewaye a ciki, kuma kowanne ƙyaure an yi masa ado da itacen kwakwa.
17Sai mutumin ya kawo ni harabar waje da haikalin. Duba, ga ɗakuna, akwai gefen hanya a harabar, da kuma ɗakuna sittin a gaban harabar, da ɗakuna talatin gaba da gefen hanyar.18Gefen hanyar ya bi ta gefen ƙofofin, kuma fasalinsu ɗaya ne da tsawon ƙofofin. Wannan shi ne gefen hanya mafi kwari.19Sai mutumin ya auna nisan daga gaban ƙaramar ƙofa zuwa gaban ƙofofi na ƙurya; kamu ɗari ne daga bangon gabas, haka kuma yake a bangon arewa.
20Daga nan sai ya auna tsawo da fadin ƙofar da ke arewa a can cikin harabar waje21Akwai ɗakuna guda uku a kowanne gefe na ƙofar, ƙofar da kwararonta duk suma an auna su kamar yadda aka auna babbar ƙofar - tsawonta dukka kamu hamsin ne sai fadinta kuma kamu ashirin da biyar ne
22Tagogin, da kwararon, da ɗakunan, da bishiyoyin dabinon da aka sa a ƙofar da ke fuskantar gabas. Taki bakwai su ne suka kai kwararonsa.23Akwai kuma wata ƙofar daga ciki wadda ke fuskantar arewa, kamar dai yadda akwai ƙofa a gabas; mutumin ya auna daga ƙofa ɗaya zuwa ƙofa ɗaya - ya sami kamu dari na nisa.
24A gaba sai mutumin ya kawo ni ƙofar shiga ta kudu, kusurwarta da tsawonta suma ya auna su kamar yadda ya auna sauran ƙofofin.25Akwai tagogi da ke a kulle a kan hanyar ƙofar da kwararonta kamar dai irin na waccan ƙofar. Kofar kudu da kwararonta tsawonta kamu hamsin ne faɗinta kuma kamu ashirin da biyar ne.
26Akwai kuma ƙofa zuwa can ƙuryar harabar daga bangon kudu tsawonta kamu ɗari ne.27Akwai matakai bakwai da ake hawa zuwa ƙofar da kwararonta akwai kuma itacen dabino da aka kewaye katangar da su a kowanne gefe.
28Sai mutumin ya kawo ni ƙuryar harabar ta hanyar ƙofarsa ta kudu, wadda ke da awo irin na sauran ƙofofin.29da bangayen, da kwararon duk awonsu dai-dai ne da na sauran ƙofofin; kuma akwai tagogi a ko'ina a kwararon. ƙofar ciki da girmanta kamu hamsin ne na tsawo kuma faɗinta kamu ashirin da biyar ne.30Kuma akwai kwararo da suka kewaye katangar ta ta ciki a ko'ina; waɗannan ne ma su kamu ashirin da biyar a tsawo da kuma kamu biyar na faɗi.31Wannan kwararo ya fuskanci harabar waje da aka kewaye da sassaƙaƙƙun itatuwan dabino a bangonta kuma akwai matakai takwas da a ke takawa a hau samanta.
32Daga nan sai mutumin ya kawo ni cikin haraba ta ƙurya ta bangon gabas ya kuma auna ƙofar, ita ma awonsu ɗaya da sauran ƙofofin.33Ɗakunansa, da bangayen, da kwararon suma an auna su kamar yadda aka auna sauran ƙofofin, kuma awonsu dai-dai, kuma akwai tagogi a kewaye a ko'ina. Ƙofar ciki da kwararonta an auna tsawonsu kamu hamsin, faɗinsu kuma kamu ashirin da biyar.34Kwararonta na fuskanci harabar waje; kuma tana da itatuwan dabino a kowanne gefe kewaye da matakai takwas na hawa bisansa.
35A gaba sai mutumin ya kawo ni ƙofar arewa ya kuma auna ta; awonta dai-dai ne da sauran ƙofofin.36Ɗakunanta, da bangayenta, da kwararonta duk ɗaya suke da sauran ƙofofin, akwai kuma tagogi a kewaye a ko'ina. ƙofar shiga da kwararonta an auna kamu hamsin na tsawo, sai kamu ashirin da biyar na faɗi.37Kwararonta na fuskantar harabar waje; tana kuma da itatuwan dabino a kowacce kusurwarsa da kuma matakai takwas na hawa samansa.
38Akwai ɗaki da ƙofa a kowanne gefe na hanyoyin shiga da ke ciki. Wannan ne wurin da suke ɗauraye baye-baye na ƙonawa.39Da tebura guda biyu a kowanne gefen kowanne kwararo, inda a ke yanka baikon ƙonawa a kai, haka kuma baiko na zunubi da kuma baiko na laifi.
40Bangon harabar, da ya bi ta ƙofa zuwa arewa, akwai tebura guda biyu. Hakan nan a ɗaya gefen shi ma akwai tebura guda biyu a kwararon ƙofar.41Akwai kuma tebura guda huɗu a kowanne gefe wurin ƙofa; su na yanka dabbobi a kan teburan nan guda takwas.
42Akwai kuma tebura huɗu na yakkakken dutse domin baye-baye na ƙonawa, tsawonsu kamu ɗaya da rabi, sanan faɗinsa rabin kamu ne, tsayinsa kuma kamu guda ne. A kansu suke ɗora kayayyakin da suke yanka baye-baye na ƙonawa da su.43Aka kakkafa matsirai guda biyu tsawonsu kamun hannu ne a kwararon kewaye da ko'ina, domin a dinga ƙyafe naman baye-bayen da za'a miƙa a kan teburan.
44A waje da ƙofar ciki, a cikin harabar ciki, akwai ɗakuna na mawaƙa, ɗaya daga gefen arewa yana fuskantar kudu, ɗayan kuma daga gefen kudu yana fuskantar arewa.45Bayan haka sai mutumin ya ce da ni, "Wannan ɗakin da ke fuskantar kudu domin firistoci ne waɗanda ke kan aiki a cikin haikali.
46Ɗakin da ke duban arewa na firistocin da ke kan aiki ne a bagadi. Waɗannan sune 'ya'yan Zadok da suka zuwa kusa da Yahweh domin su bauta masa; suna cikin 'ya'yan Lebi."47A gaba sai ya auna harabar - tsawo kamu dari faɗi kuma kamu ɗari ne, tare da bagadi a gaban gidan.
48Sai mutumin ya ɗauko ni ya kawo ni kwararon gidan ya kuma auna madogaran ƙofofin - kaurinsu ya kai kamu biyar a kowanne gefe. Hanyar shiga ita kanta kuma sha huɗu ne a faɗi, kuma bangayen kowanne gefe faɗinsu kamu uku ne.49Tsawon kwararon ya kai kamu ashirin, kuma zurfinsa ya kai kamu sha ɗaya. Akwai matakai da suka nufe shi sama da lungunan da ke a kowanne gefen gini.

41

1Sai mutumin ya kawo ni cikin wuri mai tsarki na haikali, sai ya auna madogaran ƙofofin - faɗinsa kamu shida ne ta kowanne gefe.2faɗin hanyar ƙofar ya kai kamu goma; bagon a kowanne gefe ya kai kamu biyar a tsawo. Daga nan sai mutumin ya auna fasalin wuri mai tsarki - tsawonsa kamu arba'in da faɗinsa kamu ashirin.

3Daga nan mutumin ya tafi ya shiga wuri mafi tsarki ya auna madogaran hanyar ƙofar - aka sami awo biyu, hanyar ƙofar kuma kamu shida ne faɗinsa. Bangayen ta kowanne gefe kamu bakwai ne a faɗi.4Daga nan sai ya auna tsawon ɗaki - awo ashirin ne. Faɗinsa kuma - kamu ashirin ne zuwa gaban sararin haikalin. Daga nan sai ya ce mani, "Wannan shi ne wuri mafi tsarki."
5Sai mutumin ya auna bangon gidan - kaurinsa kamu shida ne. Faɗin kowanne gefen ɗaki kewaye da gidan kamu huɗu ne a faɗi.6Akwai ɗakuna a gefe bisa hawa ku, ɗaki ɗaya bisa ɗaya, akwai ɗakuna talatin a kowanne hawa. Akwai ginshiƙai kewaye da bangon gidan, domin su zama makarai na dukkan ɗakunan da ke gefe, domin babu makarin da aka sa a bangon gidan.7To ɗakunan gefen suka faɗaɗa suka kewaya suka nufi sama, domin gidan ya zama bene kan bene a kewaya; ɗakunan suna faɗaɗa yayin da gida ke yin sama, hawan benen ya hau zuwa mataki mafi bisa, ta cikin mataki na tsakiya.
8Sa'an nan na ga sashen da aka ɗaga dukkan kewayen gidan, da harsashe domin ɗakunan gefe; an auna shi kamun tsayin sanda - wato awo shida.9Faɗin bangon ɗakunan gefe ta waje awo biyar ne. Akwai kuma wuri buɗaɗe a wajen waɗannan ɗakunan a masujada.
10A ɗaya gefen na wannan buɗaɗɗen fili akwai ɗakunan firistoci da ke waje; wannan filin faɗinsa ya kai awo ashirin a dukkan kewayen masujadar.11Akwai ƙofofi a cikin ɗakunan gefe daga wani buɗaɗɗen filin -akwai kuma wata hanyar ƙofar daga bangon arewa, da kuma wata daga kudu. Faɗin wannan buɗɗaɗen fili dukka kamu biyar ne.
12Ginin da ya fuskanci harabar daga yamma ya kai kamu saba'in a faɗi. Bangonsa kuma da aka auna ya kai kamu biyar a kauri a kewaye da ko'ina, tsawonsa kuma ya kai kamu tasa'in.13Daga nan sai mutumin ya auna masujadar - tsawonsa kamu ɗari ne. Ginin da ke ware, da bangonsa, da harabar duk suma an auna su tsawonsu kuma ya kai kamu ɗari.14Faɗin gaban harabar a gaban masujadar shi ma kamu ɗari ne.
15Sai mutumin ya auna tsawon ginin da ke bayan masujadar, zuwa yammacinsa, da ɗakunan ajiya da ke a dukkan gefen - aka sami awo ɗari. Wuri mai tsarki da kwararon,16da bangayen ciki da tagogi da duk da ƙananan tagogi, da ɗakunan ajiya kewaye da dukkan hawa ukunnan, duk an ƙayata su da katako17A saman hanyar shiga zuwa masujada ta ciki da kuma filin da ke wurin shi ma duk an auna shi.
18An yi masa ado da kerubim da itatuwan dabino a tsakanin kowanne kerubim da kerubim, kuma kowanne kerubim na da fuskoki biyu:19fuskar mutum na duban itacen dabino ta gefe ɗaya da kuma fuskar sagarin zaki da ke duban ɗaya gefen. Sun kewaye ko'ina na gidan,20Doga ƙasa har zuwa saman hanyar ƙofa, an kewaye shi da kerubim da kuma itatuwan dabino a dukkan bangon gidan
21Madogaran ƙofar wuri mai tsarki an yi masu zagaye. Kammanninsu kamar kamannin22bagadin katako ne a gaban wuri mai tsarki, wanda bisansa kamu uku ne, tsawonsa kuma kamu biyu ne ta kowanne gefe. Madogaran kusurwa, da harsashen, da matokaranta, da katako aka yi su. Sai mutumin ya ce da ni, "Wannan shi ne teburin da ke tsaye a gaban Yahweh."23Akwai ƙofofi ruɓi biyu manne domin wuri mai tsarki da kuma wuri mafi tsarki.24Waɗannan ƙofofin suna da maƙalatun ƙofa guda biyu, maƙalatun ƙofa biyu domin kowacce ƙofa.
25Aka sassaƙa a kansu - a kan ƙofofin wuri mai tsarki - kerubim ne da itatuwan dabino, kamar dai yadda aka yi wa bango ado, kuma an yi rufin katako a kan kwararon daga gaba.26Akwai kuma tagogi da itatuwan dabino a gefen kwararon waɗannan su ne ɗakunan da ke gefen gidan, suma kuma suna da rufi a sama.

42

1A gaba sai mutumin ya aike ni waje zuwa harabar ciki daga wajen arewa, sai ya kawo ni ɗakuna a gaban harabar waje da kumabangon waje daga kudu.2Waɗannan ɗakunan sun kai kamu ɗari a tsawonsa a gaba sai kuma kamu hamsin na faɗi.3Waɗansu daga cikin ɗakunan sun fuskanci harabar ciki nisansu daga masujadar ya kai kamu ashirin. Akwai ɗakuna hawa uku waɗanda ke sama suna duban ƙasa na waɗanda ke ƙasa da su, an kuma bubbuɗe masu ƙofofin da a ke bi. Waɗansu ɗakunan kuma suna duban haikalin.

4Sararin wucewa kamu goma ne na faɗi da kuma kamu ɗari na tsawo su ne a gaban ɗakunan. Ƙofofin ɗakunan na duban arewa.5Amma ɗakunan taro na sama ƙanana ne daga nan ne a ke samun hanyar wucewa, ƙofofin suna da faɗi fiye da filin da ke a ƙasa da kuma tsakiyar matakai na ginin.6Domin ɗakunan taron da ke hawa na uku ba su da shingaye. Ba kamar harabar ba, da ke da shingaye. To benayen da ke can sama ƙanana ne in kwatanta da girman ɗakunan da ke ƙarƙas da kuma benaye na hawan tsakiya.
7Bangon da ke waje ya bi ta kusa da harabar ciki, harabar da ke gaban ɗakunan. Wannan bangon ya kai kamu hamsin a tsayi.8Tsawon ɗakunan ya kai kamu hamsin, ɗakunan da ke fuskantar masujada kamunsu kamu ɗari ne a tsawo.9Akwai hanyar shiga ta ɗakunan da ke kwari da ke gefen gabas, da suka fito daga wajenharabar waje.
10A gefen bangon harabar waje da ke gefen gabas da harabar waje, a gaban harabar ciki na masujada, akwai kuma waɗansu ɗakunan11da hanyar wucewa a gabansu. Suna kama da bayyanuwar ɗakunan a gefen arewa. Suna da tsawo da faɗi iri ɗaya kuma kasancewar iri ɗaya ne da jerin da ƙofofin.12A gefen kudu akwai ƙofofin zuwa cikin ɗakuna waɗanda suke dai-dai da da na gefeb arewa. Sararin wucewa daga ciki yana da ƙofa bisa kansa, kuma sararin wucewar ya buɗe zuwa cikin ɗakuna daban-daban. A gefen gabas akwai hanya da ke zuwa sararin wucewar a ƙarshe ɗaya.
13Daga nan sai mutumin ya ce da ni, "Ɗakunan da ke arewa da kuma ɗakunan da ke kudu waɗanda ke a gaban harabar waje ɗakuna ne masu tsarki inda firistocin da ke aiki kusa da Yahweh za su iya cin abinci mafi tsarki. Za su ajiye abubuwa mafiya tsarki a can - baiko na abinci, da baiko na zunubi, dabaiko na laifi - domin wannan wuri mai tsarki.14Sa'ad da firistoci suka shiga can, ba za su fita daga wuri mai tsarki ba zuwa harabar waje, ba tare da sun ajiye tufafin da suea yin hidima da su ba, tun da ya ke waɗannan masu tsarki ne. To dole ne su sa waɗansu tufafin na da ban kafin su kusanci mutane."
15Mutumin ya gama auna gida na ciki daga nan sai ya ɗauke ni zuwa waje zuwa ƙofar da ke duban gabas ya auna dukkan filayen da ke kewaye a can.
16Ya auna gefen gabas da sandar awo - ya sami kamu ɗari biyar da sandar awon.17Ya auna gefen arewa - awo ɗari biyar da sandar awo.18Hakannan ya auna gefen kudu - awo ɗari biyar da sandar awo.19Ya kuma juya ya auna gefen yamma - awo ɗari biyar da sandar awo.
20Ya auna sassan guda huɗu. Akwai bango a kewaye da shi tsawonsa kamu ɗari biyar, da kuma kamu ɗari biyar a faɗi, domin ya raba tsakanin wuri mai tsarki da kuma dandali.

43

1Sai mutumin ya kawo ni ƙofar da ta buɗe zuwa gabas.2Duba! ɗaukakar Allah na Isra'ila na zuwa daga gabas; muryarsa kamar rurin ruwaye masu yawa, duniya kuma ta haskaka da ɗaukakarsa.

3Bisa ga bayyanuwar wahayin dana gani ne, bisa ga wahatin dana gani sa'ad da yazo domin ya lalatar da birnin, wahayoyin kuma sun yi kama da wahayin dana gani a Kogin Keba - sai na faɗi da fuskata.4Sai ɗaukakar Yahweh ta zo gidan daga ƙofar da ta buɗe zuwa gabas.5Sai Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni cikin harabar ciki. Duba! ɗaukakar Yahweh ta cika gidan.
6Mutumin na tsaye a gefena, sai na ji muryar wani mutumin da ban na magana da ni daga gidan.7Ya ce mani, "‌Ɗan mutum, wannan ne wurin kursiyina da kuma wurin sawayen ƙafafuna, inda zan zauna a tsakiyar mutanena Isra'ila har abada. Gidan Isra'ila ba za su ƙara rena sunana mai tsarki ba - su ko sarakunansu - da rashin amincinsu ko kuma da gawayen sarakunansu bisa dogayen wurarensu ba.8Ba za su sake rena sunana mai tsarki ba ta wurin kafa dankarin gidansu, da dankarin gidana ba, da kuma madogaran ƙofofinsu da madogaran ƙofofina ba, babu wani abu sai katanga kawai tsakanina da su. Suka rena sunana mai tsarki da ayyukansu na ƙazanta, sai na cinye su cikin fushina.
9Yanzu bari su kawar da rashin amincinsu da gawarwakin sarakunansu daga gabana, daga nan in zauna a tsakiyarsu har abada.
10‌Ɗan mutum, kai da kanka dole ka gaya wa gidan Isra'ila game da wannan gida domin su ji kunyar kurakuransu. Su yi tunani game da wannan kwatancin.11Gama idan suka ji kunyar abin da suka yi, dagaan sai ka bayyana masu zanen gidan, da dukkan abin da ya ƙunsa, da wanzuwarsa, da hanyoyin shiga cikinsa, dukkan dokoki da ka'idodinsa. Daga nan sai ka rubuta wannan a gaban idanunsu domin su kiyaye dukkan tsarinsa da dukkan dokokinsa, domin su yi biyayya da su.
12Wannan ne ka'idar gidan: Daga ƙololuwar tudu zuwa dukkan kewayen kan iyakar da ta kewaye shi, za ya zama mafi tsarki. Duba! wannan ce ka'idar gidan.
13Waɗannan ne za su zama gwaje-gwajen bagadin bisa ga kamu-kamun kuwa dai-dai kamun tafin hannu a tsawonsa. To ramin da ke kewaye da bagadin zurfinsa za ya zama kamu ɗaya, faɗin sama kamu ɗaya. Kan iyakar da ke kewaye da gefensa zaya zama taƙi daya. Wannan ne za ya zama ƙasan bagadin.14Daga ramin daɓen ƙasa zuwa hawa na farko na bagadin kamu biyu ne, hawa na farkon kansa faɗinsa kamu ɗaya ne. Daga ƙaramin hawan kuma zuwa babban hawan bagadin kamu huɗu ne, babban hawan kuma faɗinsa kamu ɗaya ne.
15Murhun bagadin kuma domin baye-baye na ƙonawa bisansa kamu huɗu ne, akwai kuma ƙahonni huɗu da suka fuskanci sama a bisa murhun.16Tsawon murhun kamu sha biyu ne faɗinsa kuma kamu sha biyu ne, a kewaye.17Kan iyakarsa kuma tsawonsa kamu sha huɗu fadinsa kamu sha huɗu a fannoninsa huɗu, gefensa kuma rabin kamu a faɗi. Ramin kuwa faɗinsa kamu ɗaya ne a dukkan kewayen da matakalunsa na fuskantar gabas.
18Daga nan sai ya ce mani, "‌Ɗan mutum, Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Waɗannan ne ka'idoji domin bagadi a ranar da aka yi su, domin ɗaga baikon ƙonawa a kansa, da kuma yayyafa jini a kansa.19Za ku bada maraƙi daga cikin garken shanu a matsayin baikon zunubi domin Lebiyawa firistoci waɗanda ke na zuriyar Zadok, waɗanda ke zuwa kusa da ni su yi mani bauta - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.
20Sai ka ɗauki jinin ka sa a ƙahonnin huɗu na bagadin, da fannoni huɗu na hawan da kewayen gefen kuma; za ka tsaftace shi ka kuma yi kaffara domin sa.21Sai ka ɗauki maraƙin baikon zunubin ka ƙona a wurin da aka zaɓa a sashen harabar haikalin da ke waje da masujadar.
22A rana ta biyu sai ka miƙa bunsuru marar aibi daga garken awaki a matsayin baikon zunubi; Firistocin za su tsaftace bagadin da shi kamar yadda suka tsaftace shi da maraƙin.23Idan kuka gama tsaftace shi, sai ku miƙa maraƙi marar aibi daga garken shanu da rago marar aibi daga garken tumaki.24Ku miƙa su a gaban Yahweh; Firistocin za su barbaɗa masu gishiri su ɗaga su sama a matsayin baikon ƙonawa ga Yahweh.
25Dole ku shirya bunsuru a matsayin baikon zunubi kullum har kwanaki bakwai, Firistoci kuma dole su shirya maraƙi marar aibi daga garken shanu da rago marar aibi daga garken tumaki.26Dole su yi kaffara ta kwana bakwai domin bagadin su tsarkake shi, ta wannan hanya dole su keɓe shi.27Dole su kammala waɗannan kwanaki, a rana ta takwas kuma da nan gaba za ya kasance Firistocin za su shirya baye-baye na ƙonawa da baye-baye na salama a kan bagadin, kuma zan karɓe ku - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."

44

1Sai mutumin ya dawo da ni ƙofar masujadar da ke fuskantar gabas; an rufe ta gam.2Yahweh ya ce mani, "An datse wannan ƙofar gam; ba za a buɗe ta ba. Babu wanda za ya bi ta cikin ta, gama Yahweh, Allah na Isra'ila, ya bi ta cikin ta, domin haka an rufe ta gam.3Shugaban Isra'ila za ya zauna a kai ya ci abinci a gaban Yahweh. Za ya shiga ta rumfar ƙofar ya kuma fita ta cikin ta."

4Daga nan sai ya kawo ni ta hanyar ƙofar arewa da ke fuskantar gidan. Sai na gani na kuma duba, ga ɗaukakar Yahweh ta cika gadan Yahweh, sai na faɗi bisa fuskata.5Sai Yahweh ya ce mani, "‌Ɗan mutum, ka shirya zuciyarka ka kuma duba da idanunka ka saurara kuma da kunnuwanka dukkan abin da na ke furta maka. Ga dukkan farillai na gidan Yahweh da dukkan ka'idodin. Yi tunani game da ƙofofin shiga gidan dana fitarsa.
6Sai ka faɗa wa kangararrun nan, gidan Isra'ila, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Bari dukkan ayyukanku na ƙazanta su ishe ku, gidan Isra'ila -7Da kuka kawo baƙi marasa kaciyar zuciya da kaciyar jiki su kasance a Haikalina, suna rena gidana, yayin da kuke miƙa mani abinci, kitse da Jini - Kun karya alƙawarina da dukkan ayyukanku na ƙazanta.
8Ba ku aiwatar da ayyukanku ba game da abubuwana masu tsarki, amma kuka zaɓi wasu suyi ayyukanku, kuka kuma sanyasu su lura da wurina maitsarki.9Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Ba bu wani baƙo, marar kaciyar zuciya da jiki, a cikin dukkan waɗanda ke zaune tare da mutanen Isra'ila, da za ya shiga wurina mai tsarki.
10Amma Lebiyawa suka tafi nesa da ni - suka kauce daga gare ni, suka tafi ga gumakansu - amma za su biya domin zunubinsu.11Su bayi ne a haikalina, suna lura da ƙofofin gidan suna kuma yin bauta a cikin gidan suna kuma yanka baye-baye na ƙonawa da hadayun mutane, za su tsaya a gaban mutane su bauta masu.12Amma saboda sun miƙa hadayu ga gumakansu, sai suka zama abin sa tuntuɓe domin zunubi ga gidan Isra'ila. Saboda haka zan ɗaga hannuna in furta rantsuwa game da su - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - zasu ɗauki nauyin horonsu.
13Ba za su zo kusa da ni ba su yi aikin firistoci ko kuma su kusanci abubuwana masu tsarki, abubuwa mafi tsarki ba. Maimako haka, za su ɗauki zarginsu da laifofinsu domin ayyukan ƙazanta da suka aiwatar.14Amma zan maishe su masu tsaron aikin cikin gidan, domin dukkan ayyukansa da dukkan abin da a ke yi a cikinsa.
15Daga nan su Lebiyawa firistoci, su waɗannan 'ya'ya maza na Zadok waɗanda suka cika ayyukan masujadata sa'ad da mutanen Isra'ila suke bauɗewa daga gare ni - za su zo kusa da ni su yi mani sujada. Za su tsaya a gabana su miƙa mani kitse da jini - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.16Za su zo masujadata; za su kusanci teburina su yi mani sujada su kuma cika ayyukansu a gare ni.
17Hakanan za ya kasance sa'ad da suka zo ƙofofin harabar ciki, dole su yi sutura da kayan linin, dole ne kuma ba za su zo cikin ƙofofin harabar ciki da gidansa ba a cikin suturar ulu.18Za su sa rawwunan linin a kawunansu da kuma bujen linin a kwankwasonsu. Ba za su yi sutura da kayan da za susa su yi zufa ba.
19Idan suka fita zuwa harabar waje, zuwa harabar waje domin suje wurin mutanen, dole su tuɓe kayan da suka sa sa'ad da suke yin hidima; dole su tuɓe su su kuma ajiye su a cikin ɗaki mai tsarki, domin kada su maida sauran mutane masu tsarki ta wurin shafar suturarsu ta musamman.
20Dole ne kuma ba za su aske kawunansu ba ko su bar gashinsu a rataye ba yana lilo, amma dole su yiwa gashin kawunansu saisaya.21Kada wani firist ya sha ruwan inabi idan za ya shiga harabar ciki,22ko kuma ya ɗaukarwa kansa gwauruwa ko bazawara a matsayin matar aure, sai dai budurwa kaɗai daga zuriyar gidan Isra'ila ko kuma gwauruwar da ta auri firist.
23Gama za su koyawa mutanena bambanci tsakanin abu mai tsarki da abun reni; za su sanya su su san abu mai tsafta daga marar tsafta.24A wurin saɓani za su tsaya su yi hukunci da dokokina; dole su kasance masu adalci. Za su kiyaye shari'ata da farillaina a cikin kowanne buki, kuma su yi shagalin Asabataina masu tsarki.
25Ba za su je ga wanda ya mutu ba domin su zama marasa tsarki, sai dai ko mahaifinsu ne ko mahaifiyarsu, ko ɗa ko ɗiya, ko ɗan'uwa ko 'yar'uwar da ba ta taɓa kwana da namiji ba; idan kuwa ba haka ba, za su zama marasa tsafta.26Bayan da firist ya zama marar tsafta, za su lissafa warewar tsawon kwana bakwai domin sa.27A ranar da za ya shiga wuri mai tsarki, a cikin harabar ciki domin ya yi bauta a wuri mai tsarki, dole ne ya kawo baikon zunubi domin kansa - wannan ne furcin Ubangiji Yahweh.
28Wannan za ya zama gãdonsu: Ni ne gãdonsu, tilas kuma ba za ku ba su kaddara ba a Isra'ila; Ni ne zan zama kaddararsu!29Za su ci baye-baye na abinci, da baye-baye na zunubi, da kuma baye-baye na laifi, da kuma dukkan abin da aka keɓe domin Yahweh a Isra'ila, za ya zama nasu.
30Mafi kyau na 'ya'yan fari na dukkan abubuwa da kuma dukkan baiko, kowanne abu daga dukkan baye-baye za ya zama na firistoci, za ku kuma bayar da mafi kyau na baye-bayen abincinku ga firistoci domin albarka ta sauka bisa gidanku.31Firistoci kuma ba za su ci wani mushe ba ko dabbar da naman daji ya yaga, ko tsuntsu ne ko bisa ne.

45

1Idan kuka jefa ƙuri'u domin raba ƙasar a matsayin gãdo, dole ku bayar da baiko domin Yahweh; wannan baiko za ya zama fanni mai tsarki na ƙasar, kamu dubu ashirin da biyar a tsawonsa, faɗinsa kuma kamu dubu goma. Za ya zama mai tsarki, da dukkan lardin da ke kewaye da shi.2Daga wannan za a ɗibi wuri kamu ɗari biyar na tsawo da kamu ɗari biyar na faɗi a kusurwa huɗu kewaye da wuri mai tsarki, da kuma kewayen kan iyakarsa kamu hamsin a faɗinsa.

3Daga wannan lardin za ka ɗibi wuri kamu dubu ashirin da biyar a tsawo da kamu dubu goma a faɗi; shi ne za ya zama masujada, wuri mafi tsarki.4Za ya zama wuri mai tsarki a ƙasar domin firistoci da ke yiwa Yahweh bauta, waɗanda ke zuwa kusa da Yahweh su bauta masa. Za ya zama wuri domin gidajensu da kuma lardi mai tsarki domin wuri mai tsarki.5Saboda haka za ya zama kamu dubu ashirin da biyar a tsawonsa da kamu dubu goma a faɗinsa, za ya kuma zama garurruka domin Lebiyawa da ke bauta a gidan.
6Zaku keɓe lardi domin birnin, kamu dubu biyar a faɗi da kamu dubu ashirin da biyar a tsawo, wanda zaya zama a gaba da lardin da aka keɓe domin wuri maitsarki; wannan birni zaya zama na dukkan gidan Isra'ila.7‌Ƙasar shugaban zata kasance a ɓarayi biyu na lardin da aka keɓe domin wuri maitsarki da kuma birnin. Zaya zama a yamma da su da kuma gabas da su. Tsawonsa zaya zama dai-dai da tsawon ɗaya daga cikin wuraren da aka keɓe, daga yamma zuwa gabas.
8Wannan ƙasa zata zama kaddarar shugaba a Isra'ila. Shugabannina ba zasu sake muzgunawa mutanenaba; Maimako, zasu bayar da ƙasar ga gidan Isra'ila, domin kabilunsu.
9Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Ya isheku, shugabannin Isra'ila! Ku kawar da ta'addanci da rigima; kuyi hukunci da adalci! ku daina kawar da mutanena! - wannan ne furcin Ubangiji Yahweh.10Dole kuyi ma'aunai na gaskiya, da jarka ta gaskiya, da daro na gaskiya!11Awon jarkar da daron su zama ɗaya, saboda daro ɗaya ya zama kashi ɗaya cikin goma na durom; jarkar kuma ta zama kashi ɗaya cikin goma na durom. Ma'auninsu zaya zama dai-dai da durom.12Shekel zaya zama gerori ashirin; shekel sittin zaya zama maina a gare ku.
13Wannan ne baikon da ya zama tilas ku gabatar: kashi shida na jarka domin kowanne durom na alkama, zaku kuma bayar da kashi shida na jarka domin kowanne durom na bãli.14Baikon ka'ida na mai zaya zama kashi goma na daro wanda ya ke durom ɗaya (wanda ya ke darurruka goma), ko kuma kowanne durom, tunda ya ke durom ɗinma darurruka goma ne.15Tunkiya ɗaya ko akuya ɗaya daga cikin garken kowanne dabbobi ɗari biyu daga shiyyoyin ruwa na Isra'ila za a yi amfani da su domin baikon ƙonawa da baikon salama ayi kaffara domin mutanen - wannan ne furcin Ubangiji Yahweh.
16Dukkan mutanen ƙasar zasu bayar da wannan baiko ga shugaban Isra'ila.17Zaya zama aikin shugaban ya shirya dabbobin domin baye-baye na ƙonawa, da baye-baye na hatsi, da baye-baye na abin sha a lokacin shagulgula da bukukuwan sabon wata, da ranakun asabaci - dukkan kafaffun shagulgulan gidan Isra'ila. Zaya bayar domin baye-baye na zunubi, da baye-baye na hatsi, da baye-baye na ƙonawa, da baye-baye na salama domin kaffara a madadin gidan Isra'ila.
18Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: A wata na farko, a rana ta farko ga watan, zaku ɗauki maraƙi marar cikas daga garke kuyi baikon zunubi domin masujadar.19Firist zaya ɗiba daga cikin jinin baikon zunubin sai ya sanya a dawakan ƙofar gidan da kuma kusurwa hudu na kan iyakar bagadin, da kuma dawakan ƙofar shiga harabar ciki.20Zakuyi wannan a rana ta bakwai na watan domin zunubin kowanne mutum da a kayi cikin kuskure ko jahilci; ta wannan hanya zakuyi kaffara domin haikalin.
21A cikin wata na farko a rana ta sha huɗu ga watan, akwai shagali dominku, shagali na kwana bakwai. Za kuci gurasa marar gami.22A wannan rana, shugaban zaya shiryawa kansa da dukkan mutanen maraƙi a matsayin baikon zunubi.
23A kwanaki bakwai na bukin, shugaban zaya shirya baiko na ƙonawa ga Yahweh: maraƙai bakwai da raguna bakwai marasa cikas kowacce rana har ranaku bakwai, da kuma bunsuru kowacce rana a matsayin baikon zunubi.24Daga nan shugaban za ya yi baikon abinci na jarka ɗaya domin kowanne maraƙi da kuma jarka ɗaya domin kowanne rago da gwajin mai domin kowacce jarka.
25A cikin wata na bakwai a rana ta sha biyar ga watan, a wurin shagalin, shugaban za ya yi baye-baye cikin waɗannan kwanaki bakwai: baye-baye na zunubi, baye-baye na ƙonawa, baye-baye na abinci, da baye-baye na mai.

46

1Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: ‌Ƙofar harabar ciki, da ke fuskantar gabas, za a rufe ta a cikin kwanaki shida na aiki, amma a ranar Asabaci za a buɗe ta, ranar sabon wata kuma za a buɗe ta.2Shugaban za ya shiga harabar waje ta hanyar ƙofar da rumfarta da ke waje, za ya kuma tsaya a dawakan ƙofa na ƙofar ciki yayin da firistocin ke shirya masa baikon ƙonawa da baikon salama. Daga nan sai ya yi sujada a dankarin ƙofar ciki sai ya fita, amma ba za a rufe ƙofar ba sai da yamma.

3Mutanen ƙasar kuma za suyi sujada a gaban Yahweh a wurin shiga wannan ƙofa a ranakun asabaci da sabobbin watanni.4Baikon ƙonawa da shugaban zaya miƙa ga Yahweh a ranar asabaci zaya zama 'yan tumaki shida marasa cikas da kuma rago ɗaya marar cikas.5Baikon hatsi tare da ragon zaya zama jarka ɗaya, baikon hatsin dana 'yan ragunan zaya bayar bisa ga ra'ayinsa, da kuma gwajin mai ga kowacce jarkar hatsin.
6A ranar sabon wata tilas ne ya miƙa maraƙi marar cikas daga garke, 'yan tumaki shida, da rago marar cikas.7Tilas ya miƙa baikon hatsi na jarka ɗaya domin maraƙin da kuma jarka ɗaya domin ragon, da abin da ya yi niyyar bayar wa domin 'yan tumakin, da kuma gwajin mai ga kowacce jarkar hatsi.8Idan shugaban ya shiga ta hanyar ƙofar da rumfarta, tilas ya fita ta hakan.
9Amma idan mutanen ƙasar suka zo gaban Yahweh a lokacin shagulgulan da aka kafa, duk wanda ya shiga ta ƙofar arewa domin ya yi sujada tilas ya fita ta ƙofar kudu; duk kuma wanda ya shiga ta ƙofar kudu tilas ya fita ta ƙofar arewa. Babu wanda za ya koma baya ta ƙofar da ya shiga, tilas ya miƙe ya fita ta gabansa.10Tilas shugaban ya kasance a tsakanin su; yayin da suke shiga, tilas ya shiga, yayin da suke fita, tilas ya fita.
11A lokacin shagulgulan, baikon hatsin tilas ya zama jarkar hatsi ɗaya domin maraƙin da jarka ɗaya domin ragon, da kuma duk abin da ya yi niyyar bayarwa domin 'yan tumakin, da gwajin mai domin kowacce jarka.12Idan shugaban ya bayar da baikon yaddar rai, kodai baiko na ƙonawa ko baiko na salama ga Yahweh, za a buɗemashi ƙofar da ke fuskantar gabas. Zaya miƙa baikonsa na ƙonawa da baikonsa na salama kamar yadda ya ke yi a ranar asabaci. Daga nan tilas ya fita, bayan kuma daya fita sai a kulle ƙofar.
13Bugu da ƙari, za ku bayar da ɗan rago marar cikas ɗan shekara ɗaya a matsayin baikon ƙonawa ga Yahweh kullum; za ku yi wannan safiya bayan safiya.14Za ku bayar da baikon hatsi tare da shi safiya bayan safiya, ka shi shida na garwar da kashi uku na gwajin mai domin a murtsike garin baikon hatsin ga Yahweh, bisa ga madawwamin farilla.15Za su shirya ɗan ragon, da baikon hatsin, da kuma mai safiya bayan safiya, baikon ƙonawa madawwami.
16Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: idan shugaban ya bayar da kyauta ga ɗaya daga cikin 'ya'yansa maza, gãdonsa ne. Za ya zama kadarar 'ya'yansa maza, gãdo ne.17Amma idan ya bayar da kyauta daga gãdonsa ga ɗaya daga cikin bayinsa, za ya zama na bawannan har zuwa shekarar 'yantarwa, sai kuma a maida shi ga shugaban. Gãdonsa lallai za ya zama na 'ya'yansa maza ne.18Shugaban ba za ya ɗauke gãdon mutanen daga kadararsu ba; dole ya bayar ga 'ya'yansa maza daga kadararsa domin kada mutanena su warwatse, kowanne mutum daga kadararsa."'
19Daga nan sai mutumin ya kawo ni ta hanyar shiga ɗakuna masu tsarki domin firistoci, masu fuskantar arewa duba kuma! Akwai wani wuri kuma zuwa yamma.20Ya ce mani, "Wannan ne wurin da tilas firistoci su dafa baikon laifofi da baikon zunubi inda kuma tilas su gasa baikon hatsi. Tilas kuma ba za su kawo baye-bayen ba zuwa harabar waje, domin mutanen za su zama keɓaɓɓu."
21Daga nan ya kawo ni harabar waje ya bida ni na bi ta kusurwoyi huɗu na harabar, sai kuma na ga cewa a kowacce kusurwar harabar akwai wata harabar.22A kusurwoyi huɗu na harabar waje akwai waɗansu ƙananan harabai huɗu, kamu arba'in a tsawo da kamu talatin a faɗi. Dukkan harabobin huɗu gwajinsu ɗaya ne.23Akwai layin da aka yi da dutse kewaye da dukkan su huɗun, kuma murahun girki na ƙarƙashin dutsen.24Sai mutumin ya ce mani, "Waɗannan ne wuraren da bayin haikali za su dafa hadayun mutane."

47

1Sai mutumin ya maida ni baya hanyar shiga haikalin, sai ga ruwa na ɓulɓulowa daga ƙarƙashin dankarin haikalin gidan zuwa gabas - gama gaban haikalin na fuskantar gabas - kuma ruwan na ɓulɓulawa ɓangaren kudu na haikalin, zuwa dama da bagadin.2Sai ya fito da ni ta hanyar ƙofar arewa ya kuma bi da ni zagaye da ƙofar da ke fuskantar gabas, a nan ruwan yana ta malalawa daga wannan ƙofa zuwa kudu da ita.

3Yayin da mutumin ke tafiya zuwa gabas, yana riƙe da magwaji a hannunsa; sai ya gwada kamu dubu ya kuma kawo ni ta cikin ruwan inda zurfinsa ya kai idon ƙafa.4Ya sake gwada kamu dubu ya kuma kawo ni ta cikin ruwan inda zurfinsa yakai gwiwa; ya sake gwada kamu dubu ya kuma kawo ni inda zurfin ruwan ya kai kwankwaso.5Sai ya sake gwada wani kamu dubu, amma ruwan ya zama kogi wanda bazan iya bi ta cikin ba gama ruwan ya taso sama zurfinsa kuma ya isa ayi iwo a ciki - ya zama kogin da ba a iya ƙetarewa.
6Daga nan mutumin ya ce mani, "‌Ɗan mutum, ka ga wannan?" sai ya fito da ni waje ya kuma sa na tafi na koma baya ina tafiya ta gefen kogin.7Yayin da nake komawa baya sai na ga gefen kogin nada itatuwa da yawa a wannan gefe da kuma wancan gefe.8Mutumin ya ce mani, "Wannan ruwan na tafiya lardin gabas ne da ƙasa zuwa Araba; wannan ruwan yana gudu ne zuwa cikin tekun gishiri za ya kuma sabunta ta.
9Za ya zama kuma duk wata halitta mai rai da ke iwo za ta kasance inda ruwan ya tafi; za ayi kifaye masu yawa, gama wannan ruwan za ya malala zuwa can. Za ya maida ruwan gishirin mai daɗi. Komai za ya rayu a duk inda ruwan ya je.10Daga nan za ya kasance masu kamun kifi na Engedi za su tsaya bakin ruwan, za a sami wurin shanya tarurrukan kamun kifin su bushe a En Egilayim. Za a sami kifaye daban-daban a Tekun Gishiri, kamar kifayen babbar teku domin tsananin yawansu.
11Amma kududdufai da tafkunan Kogin Gishirin ba za a maida su masu daɗi ba; za su zama wurin samun gishiri.12Gefen wannan kogin a bakunansa, a gefensa biyu, itatuwa daban-daban masu bada abinci za su fito. Ganyayensu ba za su yi yaushi ba kuma ba za su taɓa dena bada 'ya'ya ba. Kowanne wata itatuwan za su bada 'ya'ya, saboda ruwa daga haikalin yana malalawa zuwa gare su. 'Ya'yansu za su zama domin abinci, ganyayensu kuma za su zama domin warkaswa.
13Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Wannan ce hanyar da za ku raba ƙasar ga kabilu sha biyu na Isra'ila: Yosef za ya sami kaso biyu.14Za ku raba dai-dai abin da na ɗaga hannu na rantse wa ubanninku zan ba su. Wannan ƙasa za ta zo maku a matsayin gãdo.
15Wannan ne za ya zama kan iyakar ƙasar a gefen arewa dagaBabbar Teku zuwa hanyar Hetlon, daga nan kuma zuwa Zedad.16Daga nan kan iyakar za ya tafi Berota, da Sibirayim, wadda ke tsakanin Damaskus da Hamat, daga nan kuma zuwa Haza Hattikon, wadda ke gefen kan iyakar Hauran.17Saboda haka kan iyakar za ya tafi daga teku zuwa Haza Enan kan iyaka da Damaskus da Hamat zuwa arewa. Wannan ne za ya zama ɓarayin arewa.
18A gefen gabas, a tsakanin Hauran da Damaskus da kuma tsakanin Giliyad da ƙasar Isra'ila za ya zama Kogin Yodan. Tilas ka gwada daga kan iyaka zuwa tekun gabas; dukkan wannan za ya zama kan iyakar gabas.19Daga nan gefen kudu kan iyakar zai kama daga Tama zuwa ruwayen Meriba Kadesh, gulbin Masar zuwa BabbarTeku. Wannan zai zama kan iyakar gefen kudu.20Daga nan kan iyakar yamma za ya zama daga BabbarTeku zuwa inda ya tafi daura da Hamat. Wannan ne za ya zama gefen yamma.
21Ta wannan hanyar za ku raba ƙasar a tsakaninku, domin kabilun Isra'ila.22Sai ku rarraba gãdon domin ku da kuma baƙin da ke zaune a tsakanin ku, su waɗanda suka haifi 'ya'ya a tsakanin ku, tare daku, kamar haihuwar 'yan asalin mutanen Isra'ila. Za ku jefa ƙuri'u domin gãdo a tsakanin kabilun Isra'ila.23Daga nan za ya zama cewa baƙo za ya kasance tare da kabilar da ke zaune tare da su. Tilas ku ba shi gãdo - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."

48

1Waɗannan ne sunayen kabilun. Kabilar Dan za su karɓi kaso ɗaya na ƙasar; Kan iyakarsu za ya tafi dai-dai da kan iyakar Isra'ila ta arewa ta hanyar Hetlon da Lebo Hamat. Kan iyakar za ya tafi har zuwa Hazar Enan ya kuma tafi kan iyaka da Damaskus zuwa arewa daga nan har zuwa Hamat. Kan iyakar Dan za ya tafi daga gabas har zuwa Babbar Teku.2Haɗe da kan iyakar Dan, daga gefen gabas zuwa yamma, Asha za ya sami kaso ɗaya.3Haɗe da kan iyakar Asha, daga gefen gabas zuwa yamma, Naftali za ya sami kaso ɗaya.

4Haɗe da kan iyakar Naftali daga gefen gabas zuwa yamma, Manasse za ya sami kaso ɗaya.5Haɗe da kan iyakar Manasse daga gefen gabas zuwa yamma, Ifraim za ya sami kaso ɗaya.6Haɗe da kan iyakar Ifraim daga gefen gabas zuwa yamma, Ruben za ya sami kaso ɗaya.7Haɗe da kan iyakar Ruben daga gefen gabas zuwa yamma, Yahuda za ya sami kaso ɗaya.
8Baikon ƙasa da zaku bayar za ya kasance daga kan iyakar Yahuda ya zarce daga gefen gabas zuwa gefen yamma; Faɗin ta za ya zama kamu dubu ashirin da biyar. Tsawonta kuma za ya zama dai-dai da kason kabila ɗaya daga gefen gabas zuwa gefen yamma, Haikalin kuma za ya kasance a tsakiyarsa.9Wannan ƙasa da za ku miƙa baiko ga Yahweh za ta zama kamu dubu ashirin da biyar a tsawo da kuma kamu dubu goma a fãɗi.
10Waɗannan ne za su zama ayyukan kason wannan ƙasa mai tsarki: za a ɗeba wa firistoci ƙasar a gwada kamu dubu ashirin da biyar bisa gefen arewa; kamu dubu goma a fãɗi bisa gefen yamma; kamu dubu goma a fãɗi bisa gefen gabas; kamu dubu ashirin da biyar kuma bisa gefen kudu, tare da wuri mai tsarki na Yahweh a tsakiyarta.11Wannan za ya zama domin keɓewar firistoci zuriyar Zadok, waɗanda suka bauta mani da aminci ba su kuma kauce ba a lokacin da mutanen Isra'ila suka kauce, yadda Lebiyawa suka yi.12Baiko dominsu za ya kasance kason wannan ƙasa mafi tsarki, ya zarce zuwa kan iyakar Lebiyawa.
13‌Ƙasar Lebiyawa da ke kan iyaka da ƙasar firistoci za ta kasance kamu dubu ashirin da biyar a tsawo da kamu dubu goma a fãɗi. Tsawon gabaɗaya na tsagawar ƙasar biyu za ya kasance kamu dubu ashirin da biyar da kuma kamu dubu ashirin a fãɗi.14Dole ba za su sai da ba ko su yi musanya da ita; 'Ya'yan fari na ƙasar Isra'ila dole ba za a taɓa ware su ba daga waɗannan karkasawar, gama dukkan ta mai tsarki ce ga Yahweh.
15Sauran ƙasar, kamu dubu biyar a fãɗi da kamu dubu ashirin da biyar a tsawo, za ta zama abin amfanin birnin gabaɗaya, da gidajen, da saurar kiwo, birnin za ya kasance a tsakiya.16Waɗannan ne za su zama gwaje-gwajen birnin: Gefen arewa za ya zama kamu 4,500 a tsawo; gefen kudu za ya zama 4,500 a tsawo; gefen gabas za ya zama 4,500 a tsawo; gefen yamma za ya zama 4,500 a tsawo.
17Za a fidda saura domin birnin wajen arewa, kamu 250 a zurfi; wajen kudu, kamu 250 a zurfi; wajen gabas, kamu 250 a zurfi; wajen yamma, kamu 250 a zurfi.18Sauran lardin domin baiko mai tasrki za ya zarce ya kai kamu dubu goma zuwa gabas da kamu dubu goma zuwa yamma. Za ta zarce har zuwa kan iyaka da baiko mai tsarki, amfanin ta kuma za ya zama abinci domin masu aiki cikin birnin.
19Mutanen da ke aiki cikin birnin, mutanen da suka fito daga dukkan kabilun Isra'ila, za su noma wannan ƙasar.20Dukkan ƙasar baikon za a gwada kamu dubu ashirin da biyar da kamu dubu ashirin da biyar. Ta wannan hanyar za ku bada baikon mai tsarki da ƙasa, domin birnin.
21Sauran ƙasar daga kowanne gefe na baiko mai tsarki da lardin birnin za ya zama domin shugaban. Tsagin ƙasar shugaban zuwa gabas za ta zarce ta kai kamu dubu ashirin da biyar daga kan iyakar baiko mai tsarki zuwa gabashin kan iyakar - tsagin nasa kuma daga yamma za ta zarce ta kai kamu dubu ashirin da biyar zuwa yammacin kan iyakar. Tsakiyar za ta zama baiko mai tsarki, wuri mai tsarki kuma na haikalin za ya kasance a tsakiyarta.22‌Ƙasar za ta zarce daga kadarar Lebiyawa da kuma lardin birnin da ke tsakiya zaya zama na shugaban; za ta kasance tsakanin kan iyakar Yahuda da kuma kan iyakar Benyamin - wannan ƙasa za ta zama ta shugaban.
23Sauran kabilun kuwa, na su kashi-kashinsu ma za ya fara daga gefen gabashi zuwa gefen yamma. Benyamin za ya karɓi kaso ɗaya.24Haɗe da kan iyakar Benyamin daga gefen gabas zuwa yamma, Simiyon za ya sami kaso ɗaya.25Haɗeda kan iyakar Simiyon daga gefen gabas zuwa yamma, Issaka za ya sami kaso ɗaya.26Haɗe da kan iyakar Issaka daga gefen gabas zuwa yamma, Zebulun za ya sami kaso ɗaya.
27Daga kudancin kan iyakar Zebulun, ya kamo daga gefen gabas zuwa yamma, za ya zama ƙasar Gad - kaso ɗaya.28Kan iyakar kudancin Gad za ya zarce daga Tama zuwa Meriba Kadesh da kuma nesa daga tafkin Masar, daga nan kuma zuwa babbar teku.29Wannan ce ƙasar da za ku jefa ƙuri'u; za ta zama gadon kabilun Isra'ila. Waɗannan ne za su zama rabonsu. Wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.
30Waɗannan ne za su zama wuraren fita daga birnin: a gefen arewa, wanda za a gwada kamu 4,500 a tsawo,31za ya zama ƙofofi uku, waɗanda za a yi wa suna domin kabilun Isra'ila: ƙofa ɗaya domin Ruben, ƙofa ɗaya domin Yahuda, ƙofa ɗaya kuma domin Lebi.32A gefen gabas, wanda za a gwada kamu 4,500 a tsawo, za ya zama ƙofofi uku: ƙofa ɗaya domin Yusufu, ƙofa ɗaya domin Benyamin, ƙofa ɗaya kuma domin Dan.
33A bangon kudu, wanda za a gwada kamu 4,500 a tsawo, za ya zama ƙofofi uku: ƙofa ɗaya domin Simiyon, ƙofa ɗaya domin Issaka, ƙofa ɗaya kuma domin Zebulun.34A gefen yamma, wanda za a gwada kamu 4,500 a tsawo, za ya zama ƙofofi uku: ƙofa ɗaya domin Gad, ƙofa ɗaya domin Asha, ƙofa ɗaya kuma domin Naftali.35Tazarar kewaye da birnin za ya zama kamu dubu sha takwas; daga ranar nan zuwa nan gaba, sunan birnin za ya zama "Yahweh yana wurin."

Littafin daniyel

1

1A cikin shekara ta uku ta mulkin Yehoyakim sarkin Yahuda, Nebukadnezza sarkin Babila ya zo Yerusalem ya kewaye birnin domin ya yanke dukkan abin da zai shigo cikinsa.2Ubangiji ya ba Nebukadnezza nasara akan Yehoyakim sarkin Yahuda, ya ba shi waɗansu keɓaɓun abubuwa daga gidan Allah. Ya kawo su cikin ƙasar Babila, zuwa gidan allahnsa, kuma ya sa keɓaɓun abubuwan a cikin ma'ajin allahnsa.

3Sarkin ya yi magana da Ashfenaz, baban jami'insa, ya kawo waɗansu daga cikin mutanen Isra'ila, waɗanda su ke daga iyalin sarauta da kuma manyan mutane -4samari waɗanda ba su da cikas, kyawawa, ƙwararru a kowacce hikima, cike da ilimi da ganewa, waɗanda suka cancanci su yi aiki a fãdar sarki. Shi ne zai koya masu adabin mutanen Babila da harshensu.5Sarki ya ɗibar masu abinci daga abincinsa da ruwan inabi wanda ya ke sha. Za a horar da waɗannan samari har shekaru uku, bayan haka, za su yi wa sarki hidima.
6A cikin su akwai Daniyel da Hananiya da Mishayel da Azariya, daga cikin mutanen Yahuda.7Babban jami'in ya ba su sunaye, Daniyel ya kira shi Beltishazza, ya kira Hananiya Shadrak, ya kira Mishayel, Meshak Azariya kuma ya kira shi Abednego.
8Amma Daniyel ya yi niyya a ransa, cewa ba zai ɓata kansa da abincin sarki ba ko da ruwan inabin da ya ke sha. Sai ya roƙi alfarma daga wurin babban jami'in saboda ba ya so ya ɓata kansa.9Sai Allah ya ba Daniyel tagomashi da tausayi daga babban jami'in ta wurin girmamawar da da ya ke yi masa.10Babban jami'in ya ce da Daniyel, "Ina jin tsoro shugabana sarki. Ya bada ummurni akan abincin da za ku ci da abin shan da za ku sha. Me ya sa zai gan ku da rãma da samari abokanku? Sarki zai fille kaina saboda ku."
11Sa'annan Daniyel ya yi magana da mai aikin da babban jami'in ya sa ya kula da su Daniyel, Hananiya, Meshayel da Azariya.12Ya ce, "Idan ka yarda ka gwada mu bayinka na kwana goma, ka riƙa ba mu kayan lambu mu ci da kuma ruwa mu sha.13Sa'annan ka gwada baiyanarmu da baiyanar samarin da ke cin abincin sarki, ka yi mana mu bayinka, bisa ga abin da ka gani."
14Sai mai hidimar ya yarda ya yi haka, ya gwada su kwana goma.15A ƙarshen kwanaki goman sai baiyanarsu ta fi lafiya, kuma suka fi duk samarin da ke cin abincin sarki annuri.16Sai mai hidimar ya ɗauke abincinsu da ruwan inabinsu ya ba su kayan lambu kawai.
17Waɗannan samari huɗu, Allah ya ba su ilimi da ganewa da fahimtar dukkan adabi da hikima, Daniyel kuma ya na iya gane kowanne irin wahayi da mafarkai.18Da lokacin da sarki ya bayar a kawo su wurinsa ya yi, sai babban mai hidimar ya kawo su ciki gaban Nebukadnezza.
19Sarki ya yi magana da su, a cikin dukkan taron babu wanda za a iya kwatanta shi da Daniyel, Hananiya, Meshayel da Azariya. Suka tsaya a gaban sarki, a shirye su yi masa hidima.20A cikin kowacce tambaya ta hikima da ganewa da sarki ya tambaye su, ya tarar sun fi dukkan masu dũba da masu magana da kurwa waɗanda ke cikin dukkan mulkinsa har sau goma.21Daniyel ya zauna can har shekara ta fari ta Sairus.

2

1A cikin shekara ta biyu ta mulkin Nebukadnezza, sai ya yi mafarkai. Hankalinsa ya tashi, bai iya yin barci ba.2Sarki ya umarta cewa masu dũba da masu cewa suna magana da kurwa su zo. Haka kuma ya kira masu sihiri da mutane masu hikima. Ya so su ba shi bayanin mafarkansa. Sai suka zo suka tsaya a gaban sarki.

3Sarki ya ce da su, "Na yi mafarki, kuma raina ya ƙagara ya san ma'anar mafarkin."4Sai mutanen masu hikima suka yi wa sarki magana cikin harshen Aremiyanci, "Ranka ya dade ya sarki! Ka gaya mana mafarkin, bayinka kuwa za su baiyana maka ma'anarsa."
5Sai sarki ya amsawa masu hikimar da cewa, "Wanann maganar a yanke take. Idan ba ku baiyana mani mafarkin da fassararsa ba, za a yayyaga jukkunanku a mayar da gidajenku kufai.6Amma idan kun baiyana mani mafarkin da ma'anarsa, za ku karɓi kyautai daga gare ni, da lada da ɗaukaka. To sai ku gaya mani mafarkin da ma'anarsa."
7Suka sake amsawa suka ce, "Bari sarki ya gaya mana mafarkin, mu bayinsa mu kuwa za mu baiyana maka ma'anarsa."8Sai sarki ya amsa, "Tabbas na sani kuna bukatar ƙarin lokaci, saboda kun ga shawarata ta yi tsauri akan wannan abu.9Amma idan ba ku faɗa mani mafarkin ba, hukunci ɗaya ne a kanku. Kun shirya ku gaya mani ƙaryar da kuka shirya ku ka yarda a kanta da maganganu na ruɗi, har sai na canza shawarata. To ku gaya mani mafarkin, sa'annan zan sani za ku ba ni bayaninsa."
10Masu hikima suka amsa wa sarki, "Ba wani mutum a duniya da zai iya biyan bukatar sarki. Ba wani babban sarki mai iko da ya taɓa bukatar irin wannan abu daga masu dũba, ko daga wani mai magana da kurwa, ko mutum mai hikima.11Abin da sarki ya ke bukata yana da wuya, ba wanda zai iya gaya wa sarki shi sai dai alloli, su kuma ba a cikin mutane suke zama ba."
12Wannan ya sa sarki ya ji haushi ya hasala ƙwarai, ya bada ummurni a hallaka dukkan masu hikima na Babila.13Shela ta fita a kashe dukkan waɗanda aka sani su masu hikima ne. Saboda wannan doka, aka nemo Daniyel da abokansa domin a kashe su.
14Sai Daniyel cikin ladabi da hikima ya amsa wa Ariyok shugaban masu tsaron sarki, wanda ya zo ya kashe dukkan waɗanda aka san masu hikima ne a cikin Babila.15Daniyel ya tambayi jami'in sarkin, "Me ya sa shelar sarki ta zo da sauri haka?" Ariyok ya gaya wa Daniyel abin da ya faru.16Sai Daniyel ya roƙi a ba shi lokaci ya zo wurin sarki domin ya kawo wa sarki fassara.
17Sai Daniyel ya koma gida ya gaya wa su Hananiya, Meshayel da Azariya, abin da ya faru.18Ya roƙe su su nemi jinƙai daga Allah na sama akan wannan asiri domin kada a kashe su tare da sauran mutanen Babila waɗanda aka sani saboda da hikimarsu.
19A wannan daren a ka baiyana wa Daniyel asirin a cikin ruya. Sa'annan Daniyel ya yabi Allah na sama20ya ce, "A yabi sunan Allah har abada abadin; gama hikima da iko nasa ne.
21Shi ne mai canza lokatai da zamanai; ya kan cire sarakuna ya sa waɗansu sarakunan akan mulkokinsu. Ya kan ba da hikima da ilimi ga masu fahimta.22Yakan baiyana ɓoyayyun abubuwa masu zurfi gama shi ya san abin da ke cikin duhu, haske kuwa tare da shi ya ke zama.
23Allah na ubannina, na gode maka na yabe ka saboda hikima da iko da ka ba ni. Yanzu ka sanar da ni abin da muka roƙe ka; ka kuma sa mun san abin da ya dami sarki."
24Sai Daniyel ya shiga wurin Ariyok (wanda sarki ya sa ya kashe kowanne mai hikima a cikin Babila). Ya je ya ce masa, "Kada ka kashe masu hikima na cikin Babila. Ka kai ni wurin sarki zan nuna masa fassarar mafarkinsa."
25Nan da nan kuwa Ariyok ya kawo Daniyel gaban sarki ya ce, "Na samo wani daga cikin 'yan bauta na Yahuda wanda zai baiyana wa sarki ma'anar mafarkinsa."26Sarki ya cewa Daniyel (wanda a ke kira Beltishazza), "Ko ka iya gaya mani mafarkin da na gani da ma'narsa?"
27Daniyel ya amsa wa sarki ya ce, "Asirin da sarki ya tambaya game da shi masu hikima ba zasu iya baiyana shi ba, ko masu magana da kurwa da masu dũba, ko masana taurari.28Duk da haka, akwai Allah wanda ya ke zaune a cikin sammai, wanda ya ke baiyana asirai, kuma ya sanar da kai, ya sarki Nebukadnezza, abin da zai faru a cikin kwanaki masu zuwa. Wannan shi ne mafarkinka da ruyar ranka lokacin da ka ke kwance akan gadonka.
29Amma kai, ya sarki, zace-zacenka sa'ada ka ke kan gadonka game da abubuwan da zasu faru nan gaba ne, kuma shi wanda ya ke baiyana asirai ya sanar da kai abin da ya kusa faruwa,30A gare ni ba a baiyana mani wannan asiri domin na fi kowanne mutum da ke rayuwa hikima ba. An baiyana mani asirin ne domin, kai, sarki ka gane ma'anar, domin kuma ka gane zurfin tunanin da ke cikin tunane-tunanenka da ke da zurfi a cikinka.
31Sarki, ya dubi sama ya ga siffa mai girma. Wannan siffa mai girma da haske, ta tsaya a gabanka. Haskenta yana da ban tsoro.32Kan sifar an yi shi da zinariya mai kyau. Ƙirjinta da hannuwanta na azurfa ne. Tsakiyarta da cinyoyinta an yi su da tagulla,33ƙafafunta kuma an yi su da ƙarfe. Tafin sawunta kuma an yi su rabi da ƙarfe rabi da yumɓu.
34Da ka duba sama, an saro wani dutse, ko da ya ke ba da hannun mutum ba ne, ya kuma bugi siffar ya farfasa ƙafafunta na ƙarfe da na yumɓu.35Sa'annan ƙarfen da yumɓun da baƙin ƙarfen da azurfar da zinariyar aka farfasa su gaba ɗaya suka zama kamar ɗan maraƙi a masussuka lokacin kaka. Iska ta kwashe su ba ta rage komai ba. Amma dutsen da ya faɗo ya farfasa siffar ya zama babban dutse ya cika duniya.
36Wannan shi ne mafarkinka. Yanzu zamu gaya maka ma'anarsa.37Kai, sarki, kai ne sarkin sarakuna waɗanda Allah na sama ya ba su mulki, da iko da ƙarfi da martaba.38Ya bayar da wurin da mutane ke zaune a hannunka. Ya kuma bada dabbobi da tsuntsayen sama a cikin hannunka, ya sa ka yi mulki akan su dukka. Kai ne kan zinariya na siffar nan.
39Bayanka, wani mulki zai taso wanda bai kai kamar ka ba, daga nan mulki na uku na baƙin ƙarfe zai yi mulkin dukkan duniya.
40Mulki na huɗu zai zo, mai ƙarfi kamar ƙarfe, saboda ƙarfe ya farfasa kome ya lalata su. Zai farfasa duk waɗannan abubuwa ya lalata su.
41Kamar yadda ka gani an yi tafin ƙafafun rabi da yumɓu rabi da ƙarfe, mulkin zai rabu kenan; wani sashi zai sami ƙarfi kamar ƙarfe, kamar yadda ka ga an gauraya ƙarfe da yumɓu mai taushi.42Kamar yadda aka yi yatsun ƙafafun rabi da ƙarfe, rabi da yumɓu, haka mulkin zai zama wani sashi da ƙarfi wani sashi da rauni.43Kamar yadda ka ga ƙarfe gauraye da yumɓu mai taushi, haka mutanen za su zama a gauraye; ba za su tsaya tare ba kamar yadda ƙarfe ba zai gaurayu da yumɓu ba.
44A cikin kwanakin waɗannan sarakunan, Allah na sama zai tayar da wani mulkin da ba za a iya rushe shi ba, waɗansu mutane ba zasu iya cin nasara akan sa ba. Zai farfasa sauran mulkokin gutsu-gutsu ya kawo ƙarshensu, shi kuwa zai kasance har abada.45Kamar yadda ka ga an saro dutse daga babban dutse, amma ba da hannuwan mutum ba. Ya farfasa ƙarfen da baƙin ƙarfe da yumɓu da azurfa da zinariya gutsu-gutsu. Allah Mai Girma ya sanar da kai, ya sarki, abin da zai faru bayan wannan. Mafarkin gaskiya ne, wannan bayanin kuma tabbas ne."
46Nebukadnezza sarki ya faɗi da fuskarsa a ƙasa a gaban Daniyel ya girmama shi; ya ba da ummurni a yi bayarwa dominsa a ba shi turare.47Sarkin ya cewa Daniyel, "Hakika Allahnka shi ne Allahn alloli, Ubangijin sarakuna, wanda ya ke baiyana asirai, gama ka iya ka baiyana wannan asiri."
48Sai sarki ya sa Daniyel ya zama mai martaba sosai, ya ba shi kyautai da yawa na mamaki. Ya mai da shi mai mulki a bisa dukkan gundumar Babila. Daniyel ya zama babban gwamnan masu hikima na Babila.49Daniyel ya roƙi sarki, sarkin kuma ya naɗa Shadrak, Meshak da Abednego su zama masu gudanarwa a gundumar Babila. Amma Daniyel ya zauna a fãdar sarki.

3

1Nebukadnezza sarki ya yi siffa ta zinariya wadda tsawonta ƙafa tasa'in ne fadinta kuma ƙafa tara, ya ƙafa ta a Filin Dura wanda ke a gundumar Babila.2Sai Nebukadnezza ya aika da 'yan kai saƙo, a tattaro shugabanni, masu riƙe da sassa da yankuna da gundumomi da masu ba da shawara da masu ajjiya da masu shari'a da alƙalai da dukkan manyan jami'an gundumomi, su zo wurin ƙaddamar da siffar da ya kafa.

3Sai shugabannin sassa da yankuna da gundumomi da masu bada shawara da masu ajjiya da masu shari'a da alƙalai da dukkan manyan jami'an gundumomi, suka tattaru domin ƙaddamar da siffar da Nebukadnezza ya kafa. Suka tsaya a gaban siffar.4Sa'annan aka yi shela mai ƙarfi, "An ummurce ku, ku mutane da al'ummai da harsuna,5a lokacin da ku ka ji ƙarar kahonni da sarewa da garaya da molo da caki da kuge da algaita da kowanne irin kayan kiɗa, sai ku faɗi warwas a gaban siffar zinariya wadda Nebukadnezza sarki ya kafa.
6Duk wanda bai faɗi ya yi sujada ba, a wannan lokacin, za a jefa shi cikin tanderu mai ci da wuta."7To lokacin da dukkan mutane suka ji ƙarar ƙahonni da sarewa da garaya da molo da caki da kuge da algaita da kowanne irin kayan kiɗa, dukkan mutane da al'ummai da harsuna suka faɗi warwas a wurin siffar zinariya wadda Nebukadnezza sarki ya kafa.
8To sai waɗansu Kaldiyawa suka zo suka kawo sãra akan Yahudawa.9Suka ce da Nebukadnezza sarki, "Ranka ya daɗe, ya sarki!10Kai sarki, kai ne ka ba da ummurni, dukkan wanda ya ji ƙarar ƙahonni da sarewa da garaya da molo da caki da kuge da algaita da kowanne irin kayan kiɗa, dole ya faɗi warwas a gaban siffar zinariya.
11Duk wanda bai faɗi ya yi sujada ba, dole za a jefa shi cikin tanderu mai ci da wuta.12To akwai waɗansu Yahudawa da ka naɗa su lura da harkokin gundumar Babila; sunayensu kenan, Shadrak, Meshak da Abednego. Sarki, waɗannan mutane ba su damu da kai ba. Ba za su yi wa allolinka sujada ba, balle su bauta masu, ko kuma su faɗi warwas a gaban siffar zinariya wadda ka kafa."
13Sai Nebukadnezza cike da fushi da hasala, ya ummurta a kawo su Shadrak, Meshak da Abednego a wurin sa. Sai aka kawo waɗannan mutane gaban sarki.14Nebukadnezza yace da su, "Ko kun yi shawara, ya Shadrak, Meshak da Abednego, ba za ku yi sujada ga allolina ba ko ku faɗi warwas a gaban siffar zinariya wadda na kafa ba?
15Yanzu idan kuna shirye -lokacin da ku ka ji ƙarar ƙahonni da sarewa da giraya da caki da kuge da algaita da kowanne irin kayan kiɗa - ku faɗi warwas a gaban siffa wadda na kafa, ba komai. Amma idan ba za ku yi sujada ba, yanzun nan za a jefa ku cikin tanderu mai ci da wuta. Wanne allah ne zai iya kuɓutar da ku daga hannuna?"
16Shadrak, Meshak da Abedinego suka amsa wa sarki, "Nebukadnezza, ba mu da bukata mu amsa maka a kan wannan magana.17Idan da wata amsa ita ce, Allahn da muke bauta wa zai iya tsare mu lafiya daga cikin tanderu mai ci da wuta, kuma zai kuɓutar da mu daga hannunka, ya sarki.18Amma idan ma ba haka ba, bari ka sani ya sarki, ba za mu bauta wa allolinka ba, kuma ba za mu faɗi warwas a gaban siffar zinariya wadda ka kafa ba."
19Sai Nebukadnezza ya cika da hasala; yanayin fuskarsa ya canza game da Shadrak, Meshak da Abednego. Ya ba da ummurni a zuga tanderun har sau bakwai fiye da yadda aka saba zugawa.20Sa'annan ya ummurci waɗansu ƙarfafa cikin sojojinsa su ɗaure su Shedrak, Meshak da Abedinego, su jefa su cikin tanderun mai ci da wuta.
21Aka ɗaure su saye da tufafinsu da alkyabbunsu da rawunansu da sauran kayan jikinsu, aka jefa su cikin tanderun mai ci.22Saboda ummurnin sarki ya yi tsauri kuma haka aka yi, tanderun ya yi zafi ƙwarai, harshen wuta ya kashe mutanen da suka ɗauki su Shedrak da Meshak da Abednego.23Waɗannan mutane uku, wato, Shedrak, Meshak da Abednego, suka faɗa a cikin tanderun mai ci da wuta a ɗaure.
24Sai Nebukadnezza ya cika da mamaki, ya tashi da sauri. Ya tambayi mashawartansa, "Ba mutane uku mu ka jefa a ɗaure cikin wuta ba?" Suka amsa wa sarki suka ce, "Tabbas haka ne, ya sarki."25Ya amsa ya ce, "Na ga mutane huɗu ba a ɗaure ba suna yawo a cikin wutar, kuma ba abin da ya same su. Hasken na huɗun kamar na ɗan alloli."
26Sai Nebukadnezza ya zo kusa da ƙofar tanderun mai ci da wuta ya yi kira, "Shedrak, Meshak, da Abednego bayin Allah Mafi Ɗaukaka, ku fito! Ku zo nan!" Sai su Shadrak, Meshak da Abednego suka fito daga cikin wutar.27Shugabannin sassa da yankuna da gundumomi da suka taru a wurin suka ga waɗannan mutane. Wuta ba ta ƙona jukkunansu ba; gashin kansu bai taɓu ba; kuma ba abin da ya sami tufafinsu; kuma babu ƙaurin wuta a jikinsu.
28Nebukadnezza yace, "Bari mu yabi Allah na Shadrak, Meshak da Abednego wanda ya aiko ɗan saƙonsa ya ba bayinsa saƙo. Sun gaskata da shi lokacin da ba su bi dokata ba, sun ba da jikkunansu a maimakon su yi sujada ga wani allah ko su faɗi warwas a gabansa sai dai Allahnsu kaɗai.
29Saboda haka na ba da ummurni ko dukkan mutane ko al'umma ko harshen da ya yi magana gãba da Allah na Shadrak, Meshak da Abednego dole za a yayyaga su a mai, da gidajensu juji saboda ba wani allah da zai iya yin ceto kamar wannan."30Sa'annan sarki ya ƙara wa su Shadrak, Meshak da Abednego girma a cikin gundumar Babila.

4

1Sarki Nebukadnezza ya aika wannan umarni ga dukkan mutane da al'ummai, da harsuna waɗanda ke zaune a duniya: "Bari salamarku ta ƙaru.2Na ga ya yi kyau in faɗa maku akan waɗansu abubuwan alamu da al'ajabai da Maɗaukaki ya yi mani.3Ya ya girman alamunsa, kuma ya ya girman al'ajabansa! Sarautarsa har abada ce kuma mulkinsa daga zamani zuwa zamani ne."

4Ni, Nebukadnezza ina zaune cike da murna a cikin gidana, ina nishaɗi a fãdata.5Sai na yi mafarki wanda ya sa na ji tsoro. lokacin da na ke kwance, kamanni da wahayin da na gani ya dami tunanina ƙwarai.6Saboda haka sai na ummarta a kirawo mani dukkan masu hikima na Babila don su yi mani fassarar mafarkin.
7Sai masu sihiri da waɗanda ke cewa suna magana da matattu da masu hikima da masu duba suka zo. Na faɗa masu mafarkin, amma ba su iya fassara mani ba.8Sai daga baya Daniyel ya zo - wanda a kira Beltishazza wato irin sunan allahna, a gare shi kuwa akwai ruhun alloli tsarkaka-- na faɗa masa mafarkin.9Beltishazza, shugaban masu sihiri, na sani ruhun alloli tsarkaka yana cikinka kuma ba wani asirin da zai fi ƙarfin ganewarka. Ka faɗa mani mene ne na gani a mafarkina kuma me ya ke nufi.
10Waɗannan su ne alamun da na gani a cikin tunanina lokacin da nake kwance akan gadona: Na duba, akwai wani itace a tsakiyar duniya, yana da tsayi ƙwarai da gaske.11Itacen ya yi girma ya zama mai ƙarfi. ƙwanƙolinsa ya kai sammai, kuma ana iya ganinsa har duk ƙarshen duniya.12Yana da ganyaye masu kyau, 'ya'yansa kuwa suna da yawa, a kansa kuma akwai abinci domin kowa. Namomin jeji suka sami inuwa a ƙarƙashinsa, tsuntsayen sama kuma suka zauna a rassansa. Dukkan masu rai suna ci daga gare shi.
13A tunaninna da nake kwance akan gadona na ga wani tsattsarkan mai saƙo ya sauko daga sammai.14Sai ya yi magana da ƙarfi, ya ce, 'A sare itacen, a kuma daddatse rassansa, a zage ganyayensa kakaf, a kuma warwatsar da 'ya'yansa. Bari namomin jeji su yi gudu daga ƙarƙashinsa, tsutsaye kuma su tashi daga rassansa.
15A bar kututturen da saiwoyinsa a cikin ƙasa, ɗaure da sarƙar baƙin ƙarfe da tagulla, a cikin tsakiyar ɗanyar ciyawar saura. A bar shi ya jiƙe da raɓa daga sammai. A bar shi ya zauna da namomi a cikin tsirai na ƙasa.16Bari tunaninsa ya canja daga tunanin mutum, a kuma ba shi tunanin irin na dabba zai zauna a wannan hali har shekaru bakwai.
17Wannan ita ce shawara da hukuncin da ɗan saƙon ya faɗa. Shawarar da masu tsarki suka zartar don waɗanda ke da rai su sani Maɗaukaki ne ke sarautar mulkokin 'yan adam, ya kan kuma ba da ita ga wanda ya ga dama a maimakonsu, har ma da mutane masu tawali'u.'18Ni, sarki Nebukadnezza, na yi wannan mafarki. Yanzu kai, Beltishazza, ka faɗa mani ma'anarsa, domin dukkan masu hikima na cikin mulkina ba su iya faɗa mani ma'anar ba. Amma kai za ka iya yi, gama ruhun alloli tsakaka yana cikinka."
19Sai Daniyel, wanda aka lakaba wa suna Beltishazza, ya tsaya zugum da ɗan daɗewa, tunaninsa ya ba shi tsoro. Sarki yace, "Beltishazza, kada ka bar mafarkin ko ma'anarsa ya ba ka tsoro." Beltishhazza ya amsa, "Ya shugabana, bari mafarkin ya zama domin waɗanda ke gãba da kai ne; bari ma'anarsa kuma ta zama ta masu gãba da kai.
20Itacen nan da ka gani - wanda ya yi girma ya kuma yi ƙarfi, wanda ƙwanƙolinsa kuma ya kai sammai, har ma wanda za a iya ganinnsa daga ko'ina a duniya -21wanda ke da ganyaye masu kyau, wanda kuma har ya yi 'ya'ya jingim, don a cikinsa akwai abinci domin kowa, har ma namomin jeji sun sami inuwa a ƙarƙashinsa, wanda tsuntsaye sammai kuma suka zauna a kai -22wannan itacen kuwa kai ne, ya sarki, kai ne ka yi girma ka ƙasaita. Girmanka kuma ya kai har sammai, mulkinka kuma ya kai har iyakar duniya.
23Kai, sarki, ka ga tsattsarkan ɗan saƙo na saukowa daga sama yana cewa, 'A sare itacen nan, a ragargaje shi, amma a bar kututturen da saiwoyinsa cikin ƙasa, a ɗaure da sarƙar ƙarfe da kuma tagulla, a tsakiyar ɗanyar ciyawar saura. A bar shi can ya jiƙe da raɓa daga sammai. Bari ya zauna tare da namomin jeji har shekaru bakwai.'
24Wannan ita ce fassarar, sarki. Wannan hukunci ne na Maɗaukaki ya same ka, shugabana sarki.25Za a kore ka daga cikin mutane, zaka kuma zauna tare da namomin jeji. Za ka ci ciyawa kamar sa, zaka jiƙe da raɓa daga sammai, har shekaru bakwai sun cika lokacin nan za ka sani Maɗaukaki ne ke sarautar mulkin 'yan adam, kuma ya kan ba da ita ga kowa yadda ya ga dama.
26Kamar yadda aka ummarta a bar kututturen itace da saiwoyinsa, a wannan hanyar mulkinka zai dawo gare ka daga lokacin da ka san Mai sama ne ke mulki.27Saboda haka, ya sarki, bari shawarata ta sami karɓuwa gare ka. Ka daina zunubi, ka yi abin da ke da kyau. Ka juyo daga muguntarka ta wurin aikata alheri ga waɗanda ake wulaƙantawa, wataƙila za a ƙara maka tsawon kwanakinka da salama."
28Dukkan waɗannan abubuwa sun kasance ga sarki Nebukadnezza.29Bayan wata goma sha biyu lokacin da ya ke tafiya akan benen fãdar Babila,30sai ya ce, "Ashe wannan ba ita ce babbar Babila ba, wadda ni da kaina na gina domin zama fãdar sarauta, don darajar ɗaukakata ba?"
31Lokacin da kalmomi ke fita daga leɓunan sarki, sai ga murya daga sama: "Sarki Nebukadnezza, ana sanar da kai an ɗauke wannan mulkin daga gare ka.32Za a kuma kore ka daga cikin mutane, gidanka kuwa zai kasance tare da namomin jeji. Za ka ci ciyawa kamar sa. Shekaru bakwai cur zasu wuce sa'an nan za ka gane Maɗaukaki ne ke mulkin mulkokin mutane, yana kuma ba da su ga wanda ya ga dama."
33Wannan hukuncin akan Nebukadnezza ya tabbata nan take. An kore shi daga cikin mutane. Ya shiga cin ciyawa kamar sa, jikinsa kuwa ya jiƙe da raɓa daga sammai. Gashinsa kuma ya yi tsawo kamar gashin gaggafa, farotansa kuma suka yi tsawo kamar na shaho.
34A ƙarshen kwanakin ni, Nebukadnezza, sai na ɗaga idanuna sama, hankalina ya komo gare ni. "Na ɗaukaka Maɗaukaki, na yi yabo na kuma ɗaukaka shi wanda ke rayayye har abada. Gama mulkinsa madawwamin mulki ne, sarautarsa kuwa daga dukkan zamanai zuwa zamanai ne.
35Dukkan mazaunan duniya yana ɗaukan su kamar ba a bakin kome suke a gare shi ba; yakan yi yadda ya nufa a cikin rundunar sama da mazaunan duniya abin da ya yi masa dai-dai. Babu wanda zai iya hana wa ko ya ƙalubalance shi. Ba wanda zai ce da shi, 'Me ya sa ka yi wannan?"
36A lokacin nan hankalina ya komo gare ni, an mayar mani da sarautata da darajar mulkina. 'Yan majalisata da fãdawana suka dawo da mutuncina. Aka maido ni kan gadon sarautata, har ma an darajanta ni fiye da dã.37Yanzu ni, Nebukadnezza, na ba da yabo da girma da ɗaukaka ga Sarkin samaniya, domin dukkan abubuwan da ya aikata masu kyau ne, al'amuransa kuma gaskiya ne. Ya kan ƙasƙantar da waɗanda ke da girmankai.

5

1Sarki Belshazza ya yi babban liyafa domin manyan mutanensa, ya kuwa sha ruwan inabi a gaban dukkan su su dubu.2A lokacin da Belshazza ya kurɓi ruwan inabin, sai ya umarta a kawo tasoshi na zinariya da na azurfa waɗanda Nebukadnezza ubansa ya ɗauko daga cikin haikali a Yerusalem, daga waɗanda shi kansa, da manyan mutanensa da matansa da ƙwaraƙwaransa za su sha.

3Barorinsa kuwa suka ɗauko waɗannan kayyayaki da aka kwaso su daga cikin haikali, gidan Allah, a Yerusalem. Sarki da manyan mutanensa da matansa da ƙwaraƙwarnsa suka sha a cikin su.4Sun sha ruwan inabin sun yabi allolinsu waɗanda aka yi da zinariya da azurfa da tagulla da baƙin ƙarfe da katako da kuma dutse.
5A dai- dai wannan lokaci sai ga yatsun hannun mutum suka bayyana a gaban fitila da rubutu a kan shafen bangon fadar sarki. Sarki ya ga rabin hannun na rubutu.6Sai fuskar sarki ta turɓune, tunaninsa ya razanar da shi; gaɓoɓinsa kuwa suka saki, gwiwoyinsa suka soma bugun juna.
7Sarki ya yi umarni da babbar murya a kawo masu cewa suna iya magana da matattu, da masu dabo da bokaye, da masu duba. Sarki ya ce da waɗannan da aka san su masu hikima ne a Babila, "Wanda duk ya bayyana wannan rubutu ya kuma faɗi ma'anarsa za a sa masa rigar shunayya, a kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa. Zai zama da iko ya kuma zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar."
8Sai dukkan waɗanda aka san masu hikima na sarki ne suka shigo, amma babu wanda ya iya karanta rubutun balle ya faɗa wa sarki ma'anarsa.9Sarki Belshazza kuwa ya firgita ƙwarai, fuskarsa ta turɓune. Fãdawansa kuma duk suka ruɗe.
10Yanzu da sarauniya ta zo wurin babban liyafa domin abin da sarki da manyan fãdawansa suka ce. Sarauniya ta ce "Ran sarki, ya daɗe! Kada ka bar tunaninka ya sami damuwa. Kada kuma ka bar fuskarka ta turɓune.
11Ai, akwai wani mutum a cikin mulkinka wanda ke da ruhun alloli tsarkaka. A kwanakin ubanka, an iske haske da fahimi da hikima da ganewa kamar na alloli a cikinsa. Sarki Nebukadnezza, ubanka sarki, ya naɗa shi shugaba na masu sihiri, da kuma shugaban masu magana da matattu, da bokaye da masu dũba.12Ya na da ruhu nagari, da ilimi da ganewa da fassarar mafarkai da bayyana ma'anar ka-cici-ka-cici, da warware al'amura masu wuya - waɗannan ƙwarewa aka sami wannan mutum wato Daniyel da su, wanda sarki ya lakaɓa wa suna Beltishazza. Yanzu sai ka kirawo Daniyel, shi kuwa zai faɗa maka ma'anar abin da aka rubuta."
13Sai aka kawo Daniyel a gaban sarki. Sarki ya cewa Daniyel, "Kai ne Daniyel ɗin nan, ɗaya daga cikin waɗanda aka ɗauko a Yahuda, wanda ubana sarki ya kawo daga Yahuda.14Na ji labarinka, ruhun alloli tsarkaka na cikinka, haske da ganewa da mafificiyar hikima aka samu a cikinka tare.
15Yanzun nan mutanen da aka san su da hikima da waɗanda ke magana da matattu an kawo su gabana don su karanta wannan rubutu su kuma yi mani fassara, amma sun kasa faɗar ma'anar rabutun.16Amma na ji kai kana iya fassara, ka kuma iya warware al'amura masu wuya. Yanzu idan fa ka iya karanta rubutun nan, har kuma ka iya faɗa mani ma'anarsa, za a sa maka rigar shunayya, a kuma sa maka sarƙar zinariya a wuyanka, za ka zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar."
17Sai Daniyel ya amsa a gaban sarki, "Bar kyautarka don kanka, ka ba wani ladan. Duk da haka zan karanta rubutun a gare ka, ya sarki, zan kuma faɗa maka ma'anarsa.18Ya sarki, Allah Maɗaukaki ya ba Nebukadnezza ubanka sarauta, da girma, da daraja, da martaba.19Saboda girman da Allah ya ba shi, dukkan mutane, da al'ummai, da harsuna suka ji tsoronsa suna rawar jiki a gabansa. Ya kashe duk waɗanda ya ke so ya kashe, ya kuma bar waɗanda ya ke so ya bar su su rayu. Haka nan kuma ya kan ɗaukaka waɗanda ya ke so, ya kuma ƙasƙantar da waɗanda ya ga dama.
20Amma sa'ad da zuciyarsa ta kumbura, ruhunsa kuma ya taurare don haka sai ya yi girmankai, sai aka kore shi daga gadon sarautarsa, aka raba shi kuma da darajarsa.21Aka kore shi daga cikin mutane, aka ba shi hali irin na dabba, ya kuma zauna tare da jakunan jeji. Yana ta cin ciyawa kamar sã. Jikinsa ya jiƙe da raɓa daga sammai har zuwa lokacin da ya gane ashe Allah Maɗaukaki ne ke mulkin 'yan'adam, ya kan kuma ba da shi ga wanda ya ga dama.
22Kai kuma ɗansa, Belshazza, ba ka ƙasƙantar da zuciyarka ba, duk da ka san wannan dukka,23Sai ka ɗaukaka kanka kana nuna wa Ubangiji na sama girmankai. Tun daga gidansa suka kawo maka waɗannan abubuwa kai da fãdawanka, da matanka da ƙwaraƙwaranka ku ka sha ruwan inabi daga ciki, kuna yabon gumakan da aka yi da zinariya da na azurfa da na tagulla da baƙin ƙarfe da itace da dutse - gumakan da ba sa gani, ba su ji, ko su gane kome. Ba ka girmama Allah wanda ya ke riƙe da numfashinka a hannunsa ba, wanda kuma ya san dukkan hanyoyinka.24Saboda haka ne Allah ya aiko da hannun da ya yi wannan rubutun.
25Wannan shi ne rubutun da aka yi: 'Mene, Mene, Tekel, da Pharsin.'26Wannan ita ce ma'anar: 'Mene,' 'Allah ya sa kwanakin mulkinka sun ƙare.'27'Tekel' 'an auna ka a ma'auni, aka tarar ka kasa.'28'Peres,' 'an raba mulkinka, an kuma ba Mediyawa da Fashiyawa.'"
29Sai Belshazza ya ba da umarni, suka sawa Daniyel rigar shunayya. Aka sa masa sarkar zinariya a wuyansa, sarki kuma ya yi shela a kansa cewa yanzu shi ne mai iko na uku cikin masu mulkin ƙasar.30A wannan dare aka kashe Belshazza, sarkin Babila,31Dariyos Bamediye ya karɓi mulkin ya na da shekaru sittin da biyu.

6

1Ya gamshi Dariyos ya naɗa dagatai 120 a masarautar domin su yi mulkin dukkan masarautar.2Sama da su kuma ya naɗa manyan hakimai uku, Daniyel kuma na ɗaya daga cikin su. Waɗannan manyan hakimai an zaɓe su ne domin su riƙa duba ayyukan dagatan, domin kada sarki ya yi asara.3Daniyel ya yi fice daga cikin manyan hakiman da kuma dagatan saboda yana da nagartaccen ruhu. Sarki yana shirin ya sanya shi bisa dukkan masarautar.

4Sai manyan hakiman da dagatan suka duba domin su sami kuskure a cikin aikin da Daniyel ya ke yiwa masarautar, amma ba su sami wata rashawa ko kasawa ba saboda shi mai aminci ne. Ba a sami wani kuskure ko watsi da aiki a cikinsa ba.5Sai waɗannan mutane suka ce, "Bamu sami wani dalilin da zamu yi ƙarar wannan Daniyel ɗin ba sai dai ko mu sami wa ni abin tsayayya da shi game da shari'ar Allahnsa."
6Daga nan waɗannan hakimai da Dagatai suka kawo wani shiri a gaban sarki. Suka ce da shi, "Sarki Dariyos, ranka ya daɗe!7Dukkan manyan hakiman masarautar, da dagatan gudumomi, da dagatan lardi, da mashawarta, da gwamnoni sun yi shawara a tsakaninsu sun ɗauki mataki cewa kai, sarki, ka fito da doka kuma ka tilastata, yadda duk wanda ya yi wani roƙo ga wa ni allah ko mutum cikin kwana talatin, sai dai gare ka kaɗai, sarki, wannan mutum tilas a jefa shi cikin ramin zakuna.
8Yanzu dai, sarki, ka fito da doka ka kuma sanya hannu a takardar yadda ba za a iya canza ta ba, kamar yadda aka umarta bisa ga shari'un Medeyawa da Fashiyawa, domin baza a iya sauya ta ba."9Sai sarki Dariyos ya sa hannu a takardar ya maida dokar ta zama shari'a.
10Da Daniyel ya fahimci cewa an sanya hannu a takardar ta zama shari'a, sai ya tafi cikin gidansa (tagoginsa dai a buɗe suke a ɗakinsa na saman bene suna fuskantar Yerusalem), sai ya durƙusa bisa gwiwoyinsa, yadda ya saba sau uku a rana, ya yi addu'a ya kuma bada godiya a gaban Allahnsa, yadda ya ke yi a dã.11Daga nan waɗannan mutane waɗanda suka shirya makircin tare suka ga Daniyel yana yin roƙe-roƙe da neman taimako wurin Allah.
12Sai suka zo wurin sarki suka yi masa magana game da dokarsa: Ashe ba ka kafa doka ba cewa duk wanda ya yi roƙo ga wani allah ko mutum a cikin kwanaki talatin, in ba gare ka kaɗai ba, ya sarki, tilas a jefa shi cikin ramin zakuna?" Sarkin ya amsa, "Al'amarin zaunannne ne, kamar yadda aka umarta bisa ga shari'ar Medeyawa da Fashiyawa; baza a iya sokewa ba."
13Sai suka amsa wa sarki, "Wannan Daniyel ɗin, wanda ke ɗaya daga cikin 'yan bauta da daga Yahuda, bai kula da kai ba, sarki, ko dokar da ka sa hannu. Yana addu'a ga Allahnsa sau uku a rana."14Da sarkin ya ji haka, sai hankalinsa ya tashi sosai, sai ya ƙudura a ransa ya ceci Daniyel daga wannan hukunci. Ya yi ƙoƙari har zuwa faɗuwar rana ya ga ya ceci Daniyel.
15Sai waɗannan mutane waɗanda suka shirya makircin suka tattaru tare da sarki suka ce masa, "Ka sani, sarki, cewa shari'a ce ta Medeyawa da Fashiyawa, cewa babu wata doka ko umarni da sarki ya fito da shi da za a iya canzawa."
16Daga nan sarkin ya bada umarni, sai aka kawo Daniyel, aka kuma jefa shi cikin ramin zakunan. Sarkin ya cewa Daniyel, "Bari Allahnka, wanda ka ke bautawa babu fasawa, ya kuɓutar da kai."
17Aka kawo dutse aka rufe ramin, sai sarkin ya hatimce shi da zobensa na sanya hannu da kuma zobunan sanya hannun 'yan, majalisarsa yadda babu wani abin da za a canza game da Daniyel.18Daga nan sarki ya koma fãdarsa ya yi azumi tsawon dare. Babu wani abin annashuwa da aka kawo a gabansa, barci kuma ya guje daga gare shi.
19Da gari ya waye sarkin ya tashi da sauri ya tafi ramin zakunan.20Da ya matso kusa da ramin, ya yi kira ga Daniyel da muryar baƙinciki, "Daniyel, bawan Allah mai rai, ko Allahnka, wanda ka ke bautawa babu fasawa, ya iya cetonka daga zakunan?"
21Daga nan Daniyel ya ce da sarki, "Ran sarki, ya daɗe!22Allahna ya aiko da manzonsa ya rufe bakunan zakunan, ba su kuma cutar da ni ba. Gama an same ni marar laifi a gabansa da kuma gabanka, sarki, ban kuma cutar da kai ba."
23Daga nan sarki ya yi murna ƙwarai. Ya bada umarni a fito da Daniyel daga ramin. Sai aka ciro Daniyel daga ramin. Babu wani abin cutarwa da ya same shi, saboda ya dogara ga Allahnsa.
24Sarkin ya bada umarni, sai aka kawo mutanen nan da suka zargi Daniyel aka kuma jefa su cikin ramin zakunan - dukka, da 'ya'yansu, da kuma matansu. Kafin su kai ƙasa, zakunan suka sha ƙarfinsu suka kakkarya ƙasusuwansu suka yi ragargaza su.25Sai Sarki Dariyos ya rubuta zuwa ga dukkan mutane, da al'ummai da kuma harsuna da ke zaune a cikin dukkan duniya: "Bari salama ta ƙaru gare ku.
26Yanzu na kafa doka a dukkan mulkin masarautata mutane su yi rawar jiki su kuma ji tsoro a gaban Allahn Daniyel, gama shi ne Allah mai rai kuma ya dawwama har abada, sarautarsa kuwa ba za a rushe ba; mulkinsa kuwa za ya kasance har ƙarshe.27Yana kiyaye mu yana kuɓutar da mu, yana yin alamu da al'ajibai a sama da kuma duniya; Ya kiyaye Daniyel daga ƙarfin zakuna."
28Daniyel kuwa ya wadata a zamanin mulkin Dariyos da mulkin Sairus bafashiye.

7

1A shekara ta farko ta Belshazza sarkin Babila, Daniyel ya yi mafarki da wahayoyi a ransa da ya ke kwance bisa gadonsa. Sai ya rubuta abin da ya gani a mafarkin. Ya rubuta al'amura mafi muhimmanci:2Daniyel ya bayyana cewa, "A cikin wahayina na dare sai na ga iskokin sama huɗu suna motsa babban teku.3Manyan dabbobi huɗu, kowanne ya sha daban da ɗayan, suka fito daga cikin tekun.

4‌Ɗayan ya yi kama da zaki amma yana da fukafukai kamar gaggafa. lokacin da nake kallo, sai aka yage fukafukansa aka kuma ɗaga shi sama aka sa ya tsaya bisa ƙafafu biyu, kamar mutum.5Daga nan akwai dabba ta biyu, kamar damisa, a sunkuye kuma; tana da haƙarƙari uku a tsakiyar haƙoranta a cikin bakinta. Aka ce mata, 'Tashi ki lanƙwame mutane da yawa.'
6Bayan wannan na sake dubawa. Akwai wata dabbar kuma, kamanninta kamar damisa. Bisa bayanta tana da fukafukai huɗu kamar fukafukan tsuntsu, tana kuma da kawuna huɗu. Aka ba ta ikon yin mulki.7Bayan wannan kuma na gani a wahayina na dare dabba ta huɗu, mai ban razana, da ban tsoro, kuma mai ƙarfi ƙwarai. Tana da babban haƙorin ƙarfe; tana haɗiyewa, tana karyawa rugu-rugu, tana kuma tattake abin da ya rage da ƙafafunta. Ta bambanta da sauran dabbobin, kuma tana da ƙahonni goma.
8Yayin da nake yin la'akari da ƙahonnin, dana duba sai naga wani ƙaho ya fito daga cikinsu, ƙaramin ƙaho. Uku daga cikin ƙahonnin aka daga jijiyoyinsu. A wannan ƙaho na ga idanu kamar idanun mutum da kuma bakin da ke fahariya game da manyan abubuwa.
9Da na duba, sai na ga an shirya kursiyoyi a waje ɗaya, sai Mai dogon zamani ya zauna. Suturarsa fari fat kamar ƙanƙara, gashin kansa kuwa kamar farin ulu. Kursiyinsa harsunan wuta ne, gargarensu kuwa suna ci da wuta.
10‌Ƙoramar wuta na fitowa daga gabansa; miliyoyi na bauta masa, miliyan ɗari kuma na tsaye a gabansa. Ana zaman kotu, aka kuma buɗe litattafai.
11Na ci gaba da dubawa saboda maganganun fankama da ƙahon ke furtawa. Ina kallo lokacin da aka kashe dabbar, aka lalatar da jikinta, aka kuma miƙa ta domin a ƙone ta.12Sauran dabbobin huɗu kuwa, ikonsu na yin mulki aka ɗauke shi, amma aka ƙarawa rayukansu tsawon kwanaki na wani lokaci.
13A cikin wahayoyina na daren nan, sai na ga wani na zuwa da gizagizan sama kamar ɗan mutum; ya zo wurin Mai dogon zamani ya gabatar da kansa a gabansa.14Ikon yin mulki da ɗaukaka da ikon sarauta aka bayar a gare shi yadda dukkan mutane, da al'ummai, da harsuna zasu bauta masa. Ikonsa na mulki madawwamin iko ne da ba zai shuɗe ba, masarautarsa kuwa ba za a taɓa iya rusawa ba.
15Ni kuwa, Daniyel, ruhuna ya damu a cikina, wahayoyin da na gani kuwa a cikin raina suka dame ni.16Sai na kusanci ɗaya daga cikin waɗanda ke tsaye a wurin na kuma tambaye shi ya nuna mani ma'anar waɗannan abubuwa.
17Waɗannan manyan dabbobin, guda huɗu, sarakuna huɗu ne da zasu taso a duniya.18Amma tsarkakan mutanen Mafi Girma zasu karɓi masarautar, zasu kuma mallake ta har abada abadin.'
19Sai kuma na so in ƙara sani game da dabbar nan ta huɗu - ta bambanta sosai da sauran kuma tana da ban razana da haƙoranta na ƙarfe da kofatun tagulla; tana cinyewa, tana karyawa rugu-rugu, ta kuma tattake abin da ya rage da ƙafafunta.20Na so in sami sani game da ƙahonnin goma da ke a kanta, game kuma da ƙahon ɗaya da ya tsiro, wanda kuma a gabansa ƙahonni uku suka faɗi. Na so in sami sani game da ƙahon da ke da idanu da kuma game da bakin da ke fahariyar manyan abubuwa wanda kuma ya ke ganin kamar ya fi abokan tarayyarsa girma.
21Lokacin da nake kallo, sai wannan ƙaho ya yaƙi tsarkakan mutane yana kuma kayar da su22har sai da Mai dogon zamani ya zo, an kuma bayar da hukunci ga tsarkakan mutane na Mafi Girma. Daga nan lokaci ya zo inda tsarkakan mutanen suka karɓi sarautar.
23Wannan ne abin da mutumin nan ya faɗa, 'Dabbar nan ta huɗu kuwa, zata kasance masarauta ta huɗu a duniya wadda zata sha bamban da dukkan sauran masarautun. Za ta cinye dukkan duniya, ta tattake ta ta kuma karya ta rugu-rugu.24‌Ƙahonnin goma kuwa, daga cikin wannan masarauta sarakuna goma ne za su taso, wani kuma zai taso bayan su. Zai sha bamban da waɗanda suka wuce, zai kuma yi nasara da sarakunan uku.
25Zai furta maganganun tsayayya da Mafi Girma zai kuma tsananta wa tsarkaka mutanen Allah Mafi Girma. Zai yi ƙoƙarin canza shagulgula da kuma shari'a. Za a bayar da waɗannan abubuwa cikin hannunsa har shekara ɗaya, shekaru biyu, da kuma rabin shekaru.26Amma zaman kotu zai ci gaba, za a kuma ɗauke ikon sarautarsa domin a gama da shi a kuma lalatar da shi a ƙarshe.
27Masarautar da mulkin, da kuma girman masarautun da ke ƙarƙashin dukkan sama, za a bayar ga mutane waɗanda ke tsarkakan mutanen Mafi Girma. Masarautarsa madawwamiyar masarauta ce, dukkan sauran masarautu kuma za su bauta masa su kuma yi masa biyayya.'28Ga ƙarshen al'amarin. Ni kuwa, Daniyel, tunane-tunanena sun motsa ni sosai fuskata kuwa ta canza kamanni. Amma na ajiye waɗannan abubuwa a gare ni."

8

1A cikin shekara ta uku ta mulkin Sarki Belshazza, Ni, Daniyel, wahayi ya bayyana a gare ni (baya ga wanda ya bayyana a gare ni da farko).2A cikin wahayin na gani, yayin da nake dubawa, cewa ina cikin fãdar Susa a gundumar Ilam. Na gani a wahayi cewa ina bakin Rafin Ulai Kanal.

3Na duba sama sai na ga rago a gabana mai ƙahonni biyu, yana tsaye bakin rafin. ‌Ƙaho ɗaya ya fi ɗaya tsawo, amma wanda ya fi tsawon girmansa a hankali ne fiye da gajeren har ya zo ya zarce shi a tsawo.4Sai na ga ragon na bankawa yamma, daga nan arewa, daga nan kuma kudu; babu wata dabbar da ke iya tsayawa a gabansa. Babu waninsu da ke iya kuɓuto da wani daga hannunsa. Yana yin abin da ya ga dama, ya kuma zama babba.
5Yayin da nake tunani game da wannan, sai na ga bunsuru ya fito daga yamma, wanda ya tafi cikin sararin dukkan duniya, yana gudu da sauri, ya yi kamar baya taɓa ƙasa. Bunsurun yana da babban ƙaho a tsakanin idanunsa.6Ya zo wurin ragon mai ƙahonni biyu - naga ragon yana tsayawa a bakin rafin - bunsurun kuwa ya ruga wurin ragon cikin matsanancin fushi.
7Na ga bunsurun ya zo kusa da ragon. Yana cikin fushi sosai da ragon, sai kuma ya tunkuyi ragon ya ɓalle masa ƙahonnin biyu. Ragon kuwa bai da ƙarfin tsayawa a gabansa. Bunsurun ya fyaɗa shi ƙasa ya take shi. Babu wani da ke iya kuɓuto da ragon daga ikonsa.8Sai bunsurun ya zama mai girma sosai. Amma da ya zama mai ƙarfi, sai babban ƙahon ya ɓalle, a gurbinsa kuwa ƙahonni manya huɗu suka fito suka fuskanci kusurwoyin iskoki huɗu na sammai.
9Daga kan ɗaya daga cikin su wani ƙahon ya tsiro, da farko dai ƙarami ne, amma ya zama babba sosai a kudu, a gabas, a kuma ƙasa mai kyau.10Ya yi girma sosai har ya shiga yaƙi da mayaƙan sama. Waɗansu daga cikin mayaƙan da waɗansu daga cikin taurarin aka watso su ƙasa cikin duniya, ya kuma tattake su.
11Ya maida kansa ya zama da girma kamar shugaban mayaƙan. Ya ɗauke baiko na ƙonawa da aka saba yi, wurin haikalinsa kuma aka gurɓata shi.12Saboda tawaye za a miƙa mayaƙan ga ƙahon bunsurun, kuma za a tsai da baikon ƙonawa. ‌Ƙahon zai watsar da gaskiya ƙasa, zai kuma yi nasara cikin dukkan abin da ya yi.
13Sai na ji wani mai tsarki na magana wani kuma mai tsarkin na amsa masa, "Har yaushe waɗannan abubuwa za su kasance, wannan wahayin game da baikon ƙonawa, zunubin da ya kawo rusarwa, miƙawar haikalin, da kuma tattakawar mayaƙan sama?"14Ya ce mani, "Za su kasance har yamma-yamma da safiya-safiya 2,300. Bayan wannan za a maido da haikalin dai-dai."
15Lokacin da ni, Daniyel, na ga wahayin, na yi ƙoƙari in fahimce shi. Sai ga wani ya tsaya a gabana mai kamannin mutum.16Sai na ji muryar mutum na kira daga tsakiyar bakin Rafin Ulai. Ya ce, "Jibra'il, ka taimaki mutumin nan ya fahimci wahayin."17Sai ya zo kusa da inda na tsaya. Da ya zo, sai na tsorata na rusuna ƙasa. Ya ce mani, "Ka fahimta, ɗan mutum, wahayin domin lokacin ƙarshe ne."
18Da ya yi mani magana, sai na faɗa cikin barci mai nauyi da fuskata a ƙasa. Daga nan ya taɓa ni ya sa na miƙe a tsaye.19Ya ce, "Duba, zan nuna maka abin da zai faru daga bisani a lokacin hasala, saboda wahayin ya shafi zaɓaɓɓen lokacin ƙarshe.
20Game da ragon da ka gani, wanda ke da ƙahonni biyu - sune sarakunan Mediya da Fashiya.21Bunsurun shi ne sarkin Girka. Babban ƙahon tsakanin idanunsa shi ne sarkin farko.
22Game da ƙahon da ya ɓalle kuwa, wanda a gurabunsa huɗu kuma suka taso - masarautai huɗu ne za su taso daga al'ummarsa, amma bada babban ikonsa ba.23A ƙarshen lokacin waɗannan masarautai, lokacin da masu kurakurai suka ƙure iyakarsu, wani sarki marar sakin fuska, mai basira sosai, zai taso.
24Ikonsa zai zama babba - amma ba da ikonsa ba. Zai zama da ban mamaki cikin abin da ya ke rusarwa; zai aikata ya kuma yi nasara. Zai lalatar da manyan mutane, mutane daga cikin tsarkakan.25Da dabararsa zai sa yaudara ta yi nasara a hannunsa. Zai zama babba a cikin tunaninsa. Kamar yadda aka zata zai lalatar da mutane da yawa. Zai kuma yi tsayayya da Sarkin sarakuna, za a kuma karya shi, amma ba da hannun mutum ba.
26Wahayi game da yammaci da safiya da aka faɗa gaskiya ne. Amma ka rufe wahayin, gama yana magana ne akan kwanaki masu yawa nan gaba."
27Daga nan ni, Daniyel, aka sha ƙarfina na kwanta da kasala har kwanaki da yawa. Daga nan na tashi, na kuma ci gaba da hidimomin sarki. Amma na razana game da wahayin, babu kuma wani wanda ya fahimce shi.

9

1Dariyos ɗan Ahazurus ne, daga zuriyar Medeyawa. Ahazurus ne aka naɗa sarki a dukkan ƙasar Babiloniyawa.2To a shekara ta farko ta mulkin Dariyos ni, Daniyel, ina binciken litattafai da ke ɗauke da maganar Yahweh, maganar da tazo wa Irmiya annabi. Sai na lura za ayi shekaru saba'in har watsarwar Yerusalem ta kai ƙarshe.

3Sai na juya fuskata ga Ubangiji Allah, na biɗe shi cikin addu'a da roƙe-roƙe, tare da azumi, ina sanye da tsumma, ina zaune kuma cikin toka.4Nayi addu'a ga Yahweh Allahna, na kuma furta zunubanmu. Na ce, "Ina roƙon ka, Ubangiji - kai ne Allah Mai Girma Mai Ban mamaki - kai ne mai riƙe alƙawari kana kuma da aminci da ƙaunar masu ƙaunarka suna kuma kiyaye dokokinka.
5Mun yi zunubi kuma mun yi abin da ba dai-dai ba. Mun aikata mugunta kuma mun kangare, mun kauce daga umarnanka da dokokinka.6Ba mu saurari bayinka annabawa ba waɗanda suka yi magana cikin sunanka ga sarakunanmu, da shugabanninmu, da ubanninmu, da kuma dukkan mutanen ƙasar.
7A gare ka, Ubangiji, adalci ya tabbata. Ko da ya ke, a gare mu yau, kunya ce ta tabbata a fuskokinmu-ga mutanen Yahuda, da mazauna Yerusalem, da kuma dukkan mutanen Isra'ila. Wannan ya haɗa da waɗanda ke kusa da waɗanda ke nesa a cikin dukkan ƙasashen da ka warwatsa su. Wannan ya zama haka saboda babban tawayen da muka yi maka.8A gare mu, Yahweh, kunya a fuskokinmu ta tabbata-ga sarakunanmu, ga shugabanninmu, ga kuma ubanninmu - saboda mun yi maka zunubi.
9Jinƙai da gafartawa sun tabbata ga Ubangiji Allahnmu, gama mun yi maka tawaye.10Ba mu yi biyayya ga muryar Yahweh Allahnmu ba ta wurin tafiya bisa ga shari'unsa waɗanda ya ba mu ta wurin bayinsa annabawa ba.11Dukkan Isra'ila sun karya shari'arka su ka juya gefe ɗaya, suka ƙi biyayya da muryarka. La'ana da rantsuwar da aka rubuta cikin shari'ar Musa, bawan Allah, an zubo ta a kanmu, gama mun yi masa zunubi.
12Yahweh ya tabbatar da maganganun da ya furta game da mu da kuma masu mulki a kanmu, ta wurin kawo babban bala'i a kanmu. Gama a ƙarƙashin sama dukka babu wani abu da za a iya kwatantawa da abin da a kayi wa Yerusalem.13Kamar yadda aka rubuta a shari'ar Musa, duk wannan bala'i ya sauka akan mu duk da haka ba mu roƙi jinƙai ba daga wurin Yahweh Allahnmu ta wurin kaucewa daga laifuffukanmu da mai da hankali ga gaskiyarka.14Saboda haka Yahweh ya ajiye bala'i a shirye ya kuma kawo shi a kanmu, gama Yahweh Allahnmu mai adalci ne cikin dukkan abin da ya yi, duk da haka ba mu yi biyayya da muryarsa ba.
15Yanzu, Ubangiji Allahnmu, ka fito da mutanenka daga ƙasar Masar da hannu mai iko, ka yi wa kanka sanannen suna, kamar yadda ya ke a yau. Amma duk da haka mun yi zunubi; mun yi abubuwan mugunta.16Ubangiji, domin dukkan ayyukanka na adalci, bari fushinka da hasalarka su kawu daga birninka Yerusalem, tsauninka mai tsarki. Saboda zunubanmu, saboda kuma laifuffukan ubanninmu, Yerusalem da mutanenka sun zama abin ba'a ga dukkan waɗanda ke kewaye da mu.
17Yanzu, Allahnmu, ka saurari addu'ar bawanka da roƙe-roƙensa domin jinƙai; Ubangiji, ka sa fuskarka ta haskaka akan haikalinka da ya zama kufai.18Allahna, ka buɗe kunnuwanka ka saurara; ka buɗe idanunka ka duba. Mun wulaƙantu; kalli birnin da ake kira da sunanka. Ba muna roƙon taimakonka ba ne saboda adalcinmu, amma saboda jinƙanka mai girma.19Ubangiji, ka saurara! Ubangiji, ka gafarta! Ubangiji, ka kula ka ɗauki mataki! Saboda kai, kada ka yi jinkiri, Allahna, saboda birninka da kuma mutanenka ana kiran su da sunanka."
20Yayin da na ke magana - ina addu'a da furta zunubina da zunubin mutanena Isra'ila, ina kuma gabatar da roƙe-roƙena a gaban Yahweh Allahna a madadin dutsen Allah mai tsarki -21yayin da nake addu'a, mutumin nan Jibra'il, wanda na gani a wahayin da farko, ya taso zuwa wurina da gaggawa, a lokacin hadayar maraice.
22Ya ba ni fahimi ya kuma ce mani, "Daniyel, yanzu na zo in ba ka masaniya da fahimta.23Da ka fara roƙo domin jinƙai, an bayar da umarni na kuma zo in faɗa maka amsar, gama an ƙaunace ka sosai. Domin haka ka yi la'akari da wannan magana ka fahimci wahayin.
24Bakwai-bakwai sau saba'in na shekaru aka zartar domin mutanenka da birninka mai tsarki domin a kawo ƙarshen laifofi a kuma kawo ƙarshen zunubi, a yi kaffara domin mugunta, a kuma kawo madawwamin adalci, a kuma aiwatar da wahayin da anabcin, a kuma keɓe wuri mafi tsarki.25Ka sani kuma ka fahimci cewa daga zartar da umarnin maidowa da sake ginin Yerusalem har ya zuwan shafaffen nan (wanda za ya zama shugaba), za a sami bakwai-bakwai sau bakwai da kuma bakwai sittin da biyu. Za a sake gina Yerusalem da tituna da ramin ganuwa, duk da cewa lokutan tsanani ne.
26Bayan bakwai-bakwai sittin da biyu na shekaru, za a rugurguza shafaffen zai zama kuma zama ba komai. Mayaƙan shugaba mai zuwa za su rugurguza birnin da kuma wuri mai tsarki. ‌Ƙarshen shi zai zo da ambaliya, za a kuma yi yaƙi har zuwa ƙarshe. An zartar da abubuwan ban ƙyama.
27Zai tabbatar da alƙawari da mutane da yawa na bakwai ɗaya. A tsakiyar bakwai ɗin zai kawo ƙarshen hadaya da baiko. A tsakiyar haramtattun al'amura wani mai hallakarwa zai zo. Cikakkken ƙarshe da rusarwa aka zartar da za a zubo akan wanda ya kawo hallakarwar."

10

1A cikin shekara ta uku ta Sairus sarkin Fasiya, an bayyana wa Daniyel wani saƙo, wanda kuma ake kira Beltishazza. Wannan saƙon gaskiya ne. Game da babban yaƙi ne. Daniyel ya gane saƙon ya kuma sami fahimta daga wahayin

2A cikin waɗannan kwanaki ni, Daniyel ina cikin makoki har sati uku.3Ban ci abincin da nake marmari ba, ban ci nama ba, ban sha ruwan inabi ba, ban kuma shafe kaina da mai ba har sai da mako uku ɗin suka cika.
4A rana ta ashirin da huɗu ga watan fari, lokacin da nake bakin babban kogi (wato Tigris),5Sai Na duba sama sai ga mutum saye cikin linin, ƙugunsa na ɗaure da ɗammara na tsattsarkar zinariya daga Ufaz.6Jikinsa na kama da tofaz, fuskarsa tana kamar walƙiya. Idanunsa kamar fitilu na wuta, ƙafafunsa da hannuwan sa kamar gogagiyar tagulla. Muryar kalmominsa tana kama da muryar babban taro.
7Ni, Daniyel, kaɗai na ga wahayin, gama mutanen da ke tare da ni ba su ga wahayin ba. Duk da haka, babban tsoro ya sauko masu, suka ruga don su ɓoye kansu.8Ni kaɗai aka bari sai na ga wannan babban wahayin. Babu sauran ƙarfi da ya rage a cikina; bayyanata mai haske ta juya ta za ma kallon lalatarwa, ba sauran ƙarfi da ya rage a cikina.9Daga nan sai na ji kalmominsa - da na ji su, sai na faɗi kan fuskata cikin barci mai nauyi da fuskata a ƙasa.
10Sai hannu ya taɓa ni, ya sa jikina ya yi ta rawa a cikin gwiwoyina da dantsen hannuwana.11Mala'ika ya ce mani, "Daniyel, ƙaunataccen mutum na ƙwarai, Ka fahimci maganar da nake faɗa maka. Ka tashi tsaye, gama an aiko ni wurin ka." Sa'ad da ya faɗa mani wannan saƙon, na miƙe tsaye, ina rawar jiki.
12Daga nan sai ya ce mani, "Kada ka ji tsoro, Daniyel. Tun ran da ka fara ƙwallafa ranka ka fahimta kuma ka ƙasƙantar da kanka gaban Allahnka, an ji maganganunka, nima na zo ne saboda maganganunka.13Sarkin mulkin Fasiya ya yi mani tsayayya, an ajiye ni a can tare da sarakunan Fasiya har kwanaki a shirin da ɗaya. Amma Makyal, ɗaya daga cikin manyan sarakuna, ya zo domin ya taimake ni.
14Yanzu na zo in taimake ka fahimtar abin da zai faru da mutanenka a kwanakin ƙarshe. Gama wahayin domin kwanakin da ba su zo ba ne tukuna."15Lokacin da ya ke magana da ni yana morar waɗannan kalmomin, sai na juya fuskata wajen ƙasa ban iya yin magana ba.
16Wani mai kama da 'ya'ya maza na mutum ya taɓa laɓunana; sai na buɗe bakina na yi magana da shi wanda ke tsaye a gabana. "Ya shugabana, I na cikin tsanani saboda wahayin nan; Ba ni da sauran ƙarfi.17Ni bawanka ne. Ta ya ya zan yi magana da shugabana? Gama ba ni da ƙarfi, kuma ba sauran numfashin da ya ragu a cikina."
18Har yanzu sai shi mai bayyana irin ta mutum ya taɓa ni ya ƙarfafa ni.19Ya ce, "Kada ka ji tsoro, ƙaunataccen mutum na ƙwarai, Salama a gareka! Ka yi ƙarfin hali yanzu, ka yi ƙarfin hali!" Lokacin da ya ke magana da ni, Na sami ƙarfi, Na ce, "Bari shugabana ya yi magana, gama ka ƙarfafa ni."
20Ya ce, "Ko ka san dalilin da ya sa na zo gare ka? Ba da jimawa zan dawo in yaƙi sarkin Fasiya. Idan na tafi, sarkin Girka zai zo.21Amma zan faɗa maka abin da a ka rubuta cikin Littafin Gaskiya. Ba wanda ya nuna kansa cewa yana da ƙarfi tare da ni gãba da su, sai Makyal sarkinku."

11

1Cikin shekara ta fari ta Dariyos Bamedeya, ni da kaina na zo domin in goyi baya in kuma kãre Makyal.2Yanzu kuma zan bayyana maka gaskiya. Sarakuna uku zasu tashi daga cikin Fasiya na huɗun zai fi sauran wadata nesa. Yayin da ya sami iko ta wurin wadatarsa, zai zuga mutane su tayarwa mulkin Girka.

3Sarki mai girma zai tashi wanda zai yi mulkin masarauta mai girma, zai kuma aikata bisa ga yadda ya so.4Sa'ad da ya tashi sama, mulkinsa zai karye za a raba su wajen iskoki huɗu na sama, amma ban da zuriyarsa, ba kuma zai zama da iko kamar lokacin da ya ke mulki ba. Gama za a tunɓuke mulkinsa a raba shi ga waɗansu ba ga zuriyarsa ba.
5Sarkin kudu zai zama da ƙarfi, amma ɗaya daga cikin jarumawansa zai fi shi ƙarfi zai yi mulkin masarautarsa da babban iko.6Bayan 'yan shekaru idan lokaci ya yi, za su yi ƙawance. ‌Ɗiyar sarkin kudu za ta zo wurin sarkin arewa domin tabbatar da yarjejiniyarsu. Amma ba za ta riƙe da ƙarfin hanunta ba shi kuwa ba zai tsaya ba ko 'ya'yansa. Za a yãshe ta - tare da waɗanda suka kawo ta, da mahaifinta, da shi wanda ya goyi bayanta a waɗancan kwanaki.
7Amma reshe daga cikin sauyoyinta zai tashi a maimakonta. Zai kai wa rundunar hari ya shiga sansanin sarkin Arewa. Zai yaƙe su, kuma zai yi nasara da su.8Za ya ɗauke su ya kai su Masar bauta. allolinsu da siffofinsu na zubi tare da kyawawan kayansu na azurfa da na zinariya. Har waɗansu shekaru zai janye da ga sarkin Arewa.9Daga nan sarkin Arewa zai mamaye daular sarkin Kudu, amma zai janye ya koma ƙasarsa.
10'Ya'yansa za su yi shiri su kuma tara babbar rundunar yaƙi. Za su ci gaba da zuwa su yi ambaliyar kowanne abu; za su ratsa ta duk hanyar zuwa kagararsa.
11Daga nan sarkin Kudu zai ji haushi ƙwarai; zai je ya yi yaƙi da shi, wato sarkin Arewa. Sarkin Arewa zai tara manyan mayaƙa, amma za a bayar da rundunar a cikin hanunsa.12Za a kwashe rundunar, zuciyar sarkin kudu kuma za ta ɗaukaka, zai sa dubbun-dubbai su faɗi amma ba zai yi nasara ba.
13Daga nan sarkin Arewa zai tãda wata rundunar, da suka fi ta fari girma. Bayan waɗansu shekaru, lallai sarkin Arewa zai zo da babbar runduna waɗanda sun tănaji kayayyaki masu yawa.
14Cikin waɗancan lokatai da yawa za su ṭashi gãba da sarkin kudu. 'Yan tada zaune tsaye daga cikin mutanenka za su shirya kansu domin su cika wahayin, amma za su faɗi.
15Sarkin Arewa zai zo, zai zuba ƙasa kewaye domin yin matakalu, ya kuma ci birni tare da sansanonin. Ko zaɓaɓɓun sojojinsu. Ba su da sauran karfin tsayawa.16Maimakon haka, shi wanda ya zo zai aikata bisa ga manufofinsa gãba da shi; Ba wanda zai tsaya cikin hanyarsa. Zai tsaya cikin ƙasa mai kyau, hallakarwa kuwa zata kasance cikin hanunsa.
17Sarkin Arewa zai ƙudurta ya zo da dukkan ƙarfin mulkinsa, tare da shi kuma zai zama akwai yarjejeniya da sarkin Kudu. Zai ba shi 'ya mace ya aura domin ya lalata mulkin Kudu. Amma dabarar ba za ta taimake shi ba ba kuwa zai yi nasara ba.18Bayan wannan, sarkin Arewa zai maida hankali ga ƙasashen bakin teku zai kama da yawa daga cikin su. Amma wani Jarumi zai kawo ƙarshen girmankansa zai sa girmankansa ya koma kansa.19Sa'annan zai mai da hankalinsa ga sansanoni na ƙasarsa, amma zai yi tuntuɓe ya faɗi; ba za a ƙara ganinsa ba.
20Amma wani zai tashi a madadinsa zai sa mai karɓar haraji ya ratsa saboda darajar mulkinsa. Amma cikin kwanaki masu zuwa za a karya shi, ba cikin fushi ko cikin yaƙi ba.21A maimakonsa kuma wani zai tashi mutum abin raini wanda mutane ba za su ba shi darajar sarauta ba; zai zo ba tsammani zai karɓi mulki ta wurin yaudara.22Za a share rundunar yaƙi kamar ambaliya a gabansa. Dukan su da rundunar yaƙi da shugaban alƙawari za a hallakar da su.
23Daga lokacin da a ka yi ƙawance da shi, zai yi aikin yaudara; da kimanin mutane 'yan kaɗan zai yi ƙarfi.24Ba tare da gargaɗi ba zai zo cikin waɗansu lardunan da suka fi wadata, zai yi abin da mahaifinsa ko kakansa bai yi ba. Zai baza wa mabiyansa ganima, ganimar yaƙi, da dukiya. Zai shirya juyar da sansanoni, amma na ɗan lokaci ne.
25Zai ta da ikonsa da zuciyarsa gãba da sarkin Kudu da babbar rundunar yaƙi. Sarkin Kudu kuma zai ja dagar yaƙi, da babbar rundunar yaƙi, ba zai iya tsayawa ba saboda waɗansu zasu shirya masa makirci.26Har su da suke cin abincisa mai kyau za su yi ƙoƙarin hallaka shi. Rundunarsa za'a share su kamar ambaliya, da yawan su zasu faɗi kisassu.27Dukansu sarakunan nan, da zukatansu da ke nufin mugunta gãba da juna, za su zauna a teburi ɗaya suna yiwa juna ƙarya, amma ba za ta zama da amfani ba. Gama matuƙa za ta zo a ƙayadadden lokaci.
28Sa'an nan sarkin Arewa zai koma ƙasarsa da dukiya mai yawa, ya sa zuciyarsa ta yi gãba da alƙawari mai tsarki. Zai aikata abin da ya so daga nan ya koma ƙasar sa.
29A cikin sanyayyen lokaci zai sake dawowa gaba da Kudu. Amma a wannan lokacin ba zai zama kamar na farin ba.30Gama jiragen Kittim za su kawo masa hari, zai tsorata kuma ya koma baya. Zai ji haushin alƙawari mai tsarki, zai nuna amincewa ga waɗanda suka watsar da alƙawari mai tsarki.
31Dakarunsa zasu tashi su tozartar da kagarun wuri mai tsarki. Zasu kawar da baikon ƙonawa na kullum, za kuma su kafa abin banƙyama da zai sa hallakarwa.32Gare su da suke aikata mugunta saɓanin alƙawari, zai yaudare su ya ɓata su. Amma mutanen da suka san Allahnsu zasu yi ƙarfi su kuma ɗauki mataki.
33Su da ke da hikima cikin mutane zasu sa da yawa su fahimta. Amma zasu faɗi ta kaifin takobi da harshen wuta; zasu faɗi cikin bauta da yi masu fashi kwanaki da yawa.34Cikin faɗuwarsu, za a taimake su da taimako ƙanƙane. Cikin munafunci da yawa za su haɗa kai da su.35Daga cikin masu hikima waɗansu zasu faɗi domin a tace su, a wanke su, a tsarkake su, har kwanakin ƙarshe. Amma lokacin da aka ƙayyade bai yi ba tukuna.
36Sarki zai aikata bisa ga son ransa. zai ɗaukaka kansa ya maida kansa babba bisan kowanne allah. Zai faɗi abubuwan ban mamaki gãba da Allahn alloli, zai yi nasara har lokacin da fushi ya cika. Gama abin da aka wajabta zai faru.37Ba zai kula da allolin kakanninsa ba ko allahn da mata ke marmari. Ba zai kula da kowanne allah ba. Gama zai maida kansa babba a bisa kowannen su.
38Maimakon waɗannan, zai girmama allahn ganuwoyi. Shi ne allahn da ubanninsa ba su sani ba zai girmama shi da zinariya da azurfa da duwatsu masu daraja da kyaututtuka masu amfani.39Zai kai hari ga ganuwoyi masu ƙarfi ta wurin taimakon baƙon allah. Ga duk wanda ya yarda da shi, zai ƙara mai ɗaukaka. Zai maishe su masu mulkin mutane da yawa. Zai raba masu ƙasa a matsayin lada.
40A kwanakin ƙarshe kuma sarkin Kudu zai kai hari. Sarkin Arewa kuma zai tasar masa da karusan yaƙi da mahaya dawakai, da jirage da yawa. Zai shiga cikin ƙasashe, ya kwarara, ya ratsa.41Zai shiga cikin ƙasa mai kyau dubbun-dubban Isra'ilawa za su faɗi. Amma waɗannan zasu tsira daga hanunsa: Idom, Mowab da sauran mutanen Amon.
42Zai ƙara miƙa hanunsa cikin ƙasashen; ƙasar Masar ba za ta tsira ba,43Zai sami iko bisa kan taskar zinariya da azurfa da kan dukkan wadatar Masar; Libiyawa da Kushawa zasu bi tafin sawayensa.
44Amma labari daga gabas da arewa zai tsoratar da shi, zai fita da babbar hasala domin ya hallakar gaba ɗaya ya kuma keɓe da yawa domin hallaka.45Zai kafa rumfar fãdarsa tsakanin teku da kyakkyawan dutse mai tsarki. Zai kawo ƙarshen sa, ba kuwa mai taimakon sa.

12

1"A wannan lokaci Makyal, babban yarima mai kare mutanenka, zai tashi. Za a yi kwanakin wahala irin waɗanda ba a taɓa yi ba tun da aka yi kowacce al'umma har ya zuwa lokacin nan. A lokacin nan za a ceci mutanenka, duk wanda aka iske sunansa a cikin littafi.2Da yawa waɗanda suke barci cikin turɓayar ƙasa za su tashi, waɗansu zuwa rai na har abada waɗansu kuma zu wa kunya da ƙasƙanci marar matuƙa.

3Waɗanda suke da hikima zasu haskaka kamar walƙiya ta sararin sama, waɗanda suka juya mutane da yawa zuwa ga adalci za su haskaka kamar taurari har abada abadin.4Amma kai Daniyel, ka kulle maganganun nan; ka hatimce littafin har sai kwanakin ƙarshe. Da yawa zasu yi ta gudu nan da can, ilimi kuma zai ƙaru".
5Sa'an nan, ni, Daniyel, na duba, akwai waɗansu biyu suna tsaye. ‌Ɗaya yana tsaye a bakin kogi ɗaya kuma yana tsaye a bakin ƙetaren wancan kogin.6‌Ɗ‌aya daga cikin su ya ce da mutumin da ke saye da linin, wanda ya ke kan magudanar kogin ya ce, "Har yaushe zai zama ƙarshen waɗannan al'amura na al'ajabi?"
7Na ji mutumin da ke sanye da linin, wanda ya ke bisa magudanar kogin - ya ɗaga hanunsa na dama da na hagu sama ya yi rantsuwa ga shi wanda ya ke rayuwa har abada za a yi lokaci da lokatai, da rabin lokaci. Sa'ad da ikon mutane masu tsarki ya karye a ƙarshe, dukkan waɗannan al'amura zasu cika.
8Na ji amma ban fahimta ba. Sai na tambaya, "Ya shugabana, ina mafitar waɗannan al'amura?"9Ya ce, "Tafi yi tafiyarka, Daniyel, gama an kulle maganganun nan an hatimce su har sai kwanakin ƙarshe.
10Waɗansu da yawa zasu tsarkaka, tsabtattu, su zama tatattu, amma miyagu za su aikata mugunta. Babu wani a cikin mugaye da zai fahimta, amma masu hikima zasu fahimta.11Daga lokacin da aka kawar da baiko na ƙonawa aka kuma kafa abin ƙyama mai sa hallakarwa, za'a yi kwanaki 1,290.
12Mai albarka ne shi wanda ya jira har ƙarshen kwanaki 1,335.13Dole ka yi tafiyarka har ƙarshen, kuma za ka huta. Za ka tashi a cikin wurin da aka keɓe maka, a ƙarshen kwanaki."

Littafin hosiya

1

1Wannan ita ce maganar Yahweh da ta zo wurin Hosiya ɗan Biri a kwanakin Uziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, sarakunan Yahuda, da kuma kwanakin Yerobowam ɗan Yoash, sarkin Isra'ila.2Sa'ad da Yahweh ya yi magana da fari ta wurin Hosiya, ya ce masa, "Jeka ka ɗaukar wa kanka mata wadda karuwa ce. Za ta sami 'ya'ya ta wurin karuwancinta. Domin ƙasar tana aikata matuƙar karuwanci ta wurin yashe da Yahweh."

3Sai Hosiya ya tafi ya auro Gomar ɗiyar Diblayim, sai ta yi ciki ta haifa masa ɗa namiji.4Yahweh ya cewa Hosiya, "Ka kira sunansa Yeziril, gama a ɗan lokaci kaɗan zan hukunta gidan Yehu saboda ya zubda jini a Yeziril, zan kuma kawo ƙarshen mulkin gidan Isra'ila.5Wannan zai faru randa zan karya bakãr Isra'ila a Kwarin Yeziril."
6Sai Gomar ta sake yin ciki ta haifi 'ya mace. Sai Yahweh yace wa Hosiya, "Ka raɗa mata suna Lo Ruhama, gama ba zan ƙara yi wa gidan Isra'ila jinƙai ba, har da zan gafarta masu.7Duk da haka zan yi wa gidan Yahuda jinƙai, zan cece su ni da kaina, Yahweh Allahnsu. Ba zan cece su da baka, da takobi, da yaƙi, da dawakai da mahayansu ba,"
8Bayan da Gomar ta yaye Lo Ruhama, sai ta yi ciki ta haifi ɗa namiji kuma,9Sa'an nan Yahweh yace, "Ka raɗa masa suna, Lo Ammi, domin ku ba mutanena ba ne, ni kuma ba Allahnku ba ne.
10Duk da haka yawan mutanen Isra'ila za su zama kamar yashi a bakin teku, wanda ba za a iya aunawa ko ƙirgawa ba. Zai zamana inda aka ce masu, 'Ku ba mutanena ba ne, za a ce masu, "Ku mutanen Allah mai rai ne.'11Mutanen Yahuda da mutanen Isra'ila za su taru wuri ɗaya. Za su naɗa wa kansu shugaba ɗaya, za su haura su tafi daga ƙasar, gama ranar Yezril zata zama da girma.

2

1Ku cewa 'yan'uwanku maza, 'Mutanena!' ga 'yan'uwanku mata, 'An ji tausayin ku.'"

2Ku kawo ƙarar mahaifiyarku, ku kawo ƙara, gama ita ba matata ba ce, ni kuma ba mijinta ba ne. Ta kawar da karuwancinta daga gare ta da halinta na zina daga tsakanin nonnanta.3Idan ba haka ba, zan maishe ta tsirara in nuna tsiraicinta kamar a ranar da aka haife ta. Zan maishe ta kamar hamada, kamar busasshiyar ƙasa, in sa ta mutu da ƙishiruwa.
4Ba zan nuna jinƙai kan 'ya'yanta ba ko kaɗan, gama 'ya'yan fasikanci ne.5Domin uwarsu dăma karuwa ce, ita wadda ta ɗauki cikinsu ta yi abin kunya. Ta ce, "Zan bi masoyana, domin suna bani abincina, da ruwa, da ulu, da gyale, da mai da abin sha."
6Sabo da haka zan gina shinge in tare hanyarta da ƙayayuwa. Zan gina katanga gãba da ita don kada ta gane hanyarta.7Zata bi masoyanta, amma ba za ta cim masu ba. Zata neme su, amma ba za ta same su ba. Sa'annan za ta ce, "Zan koma wurin mijina na farko, gama a dã ya fiye mani da yanzu."
8Gama ba ta sani dama ni ne na ba ta hatsi ba, da sabon ruwan inabi da mai, na kuma yawaita ta da azurfa da zinariya, wanda suke amfani da shi ga Ba'al.9Saboda haka zan karɓe hatsinta da kaka, da sabon ruwan inabina a lokacin girbi. Zan karɓe uluna da gyaluluwana da aka mora don a rufe tsiraicinta.
10Zan buɗe tsiraicinta a idanun masoyanta, ba wanda zai cece ta daga hannuna.11Zan sa dukkan shagulgulanta su ƙare - bukukuwanta, shagalin tsayawar sabon wata, Asabatai, da dukkan ayyanannun bukukuwa.
12"Zan lalatar da kuringar inabinta da itatuwan ɓaurenta, da ta ce, "Waɗannan su ne ladar da masoyana suka bani.' Zan maishe su jeji, namun jeji kuma za su cinye su.13Zan hore ta domin ranakun bukukuwan Ba'aloli, lokacin da ta ƙona masu turare, sa'ad da ta yiwa kanta ado da zobba da duwatsu masu daraja, ta bi masoyanta ta manta da ni -- wannan shi ne furcin Yahweh."
14Saboda haka zan lallashe ta in dawo da ita. Zan kai ta cikin jeji in yi mata tattausar magana.15Zan mayar mata da gonakin inabinta, Kwarin Akor zai zama kofar bege. Nan za ta amsa mani kamar kwanakin ƙuruciyarta, kamar ranar da ta fito daga ƙasar Masar.
16"Zaya zamana a ranan nan - wannan furcin Yahweh ne - za ki kira ni, 'Mijina,' kuma ba za ki ƙara kira na 'Ba'al Nawa' ba.17Gama zan fitar da sunayen Ba'aloli daga bakinta, ba za a ƙara tunawa da sunayensu ba."
18A ranan nan zan yi alƙawari domin su da namun jeji, da tsuntsayen sama, da masu rarrafe a ƙasa. Zan kori bakã, da takobi, da kuma yaƙi daga ƙasar, in sa ku zauna lafiya.
19Zan yi alƙawari in zama mijinki har abada. Zan yi alƙawari in zama mijinki cikin gaskiya, da adalci, da alƙawarin aminci, da jinƙai.20Zan ɗaukar wa kaina alƙawarin aminci da ke, za ki kuma san Yahweh.
21A ranar nan zan amsa - wannan furcin Yahweh ne - Zan amsa wa sammai, su kuma za su amsa wa ƙasa.22Ƙasa kuma za ta amsa wa hatsi, sabon ruwan inabi da kuma mai, za su amsa wa Yeziril.
23Zan dasa ta domin kaina a ƙasar, zan nuna jinkai akan Lo Ruhama, Zan cewa Lo Ammi, 'Ke ce Ammi Attah,' sa'annan za su ce mani, 'Kai ne Allahnmu."'

3

1Yahweh yace mani, "Jeka har wa yau, ka ƙaunaci wata mata wadda kaunatacciya ce ga mijinta, amma mazinaciya ce. Ka ƙaunaceta kamar yadda Ni, Yahweh, na ke ƙaunar mutanen Isra'ila, ko da yake sukan juya zuwa ga bin waɗansu alloli, suna ƙaunar wainar 'ya'yan itatuwa."2Sai na saye ta domin kaina a bakin azurfa sha biyar da hatsi tiya guda da rabin bali.3Na ce mata, "Dole ne ki zauna da ni kwanaki da yawa. Ba za ki zama karuwa ba, ko ki zama ta wani mijin ba. Haka nima kuma zan kasance a gare ki."

4Gama mutanen Isra'ila za su kasance kwanaki da yawa ba sarki, ba kuma ɗan sarki, ba hadaya, ba bagadin dutse, ba falmara ko gumakan gida.5Daga baya mutanen Isra'ila za su juyo su nemi Yahweh Allahnsu da sarkinsu Dauda, kuma a kwanakin ƙarshe, za su zo da rawar jiki gaban Yahweh da alheransa.

4

1Ku ji maganar Yahweh, ku mutanen Isra'ila. Yahweh yana da ƙara game da mazaunan ƙasar, domin babu gaskiya ko alƙawarin aminci, babu sanin Allah a ƙasar.2Akwai la'antarwa, ƙarya, kisa, sata da zina. Mutanen sun zarce dukkan iyaka, ana zubda jini kan zubda jini.

3Saboda haka ne ƙasar take bushewa, dukkan mazaunanta kuma suna yanƙwanewa; dabbobin jeji da tsuntsayen sama, har ma da kifayen dake a teku, ana kawar dasu.
4Amma kada ka bari ko guda ɗaya ya kawo ƙara; kada ka bari wani ya zargi wani. Domin ku firistoci kune nake zargi.5Ku firistoci za ku yi tuntuɓe da rana, annabawa kuma za su yi tuntuɓe tare da ku da dare, zan kuma hallaka mahaifiyarku.
6Ana hallaka mutanena saboda rashin ilimi. Saboda ku firistoci kun ƙi ilimi, nima zan ƙi ku zama firistocina. Domin kun manta da dokokina, ko da yake ni Allahnku ne, nima zan manta da 'ya'yanku.7Yadda firistocin suke ƙaruwa, haka ma zunuban da suke yi mani. Sukan misanya ɗaukakarsu da kunya.
8Suna ci daga zunuban mutanena; suna da zarin mugunta da yawa.9Zai zama ɗaya saboda mutane da kuma firistoci: Zan hukunta su dukka saboda al'amuransu, zan saka masu saboda ayyukansu.
10Za su ci amma ba zai ishe su ba; za su yi karuwanci, amma ba za su ƙaru ba, domin sun yi nisa da Yahweh.
11Suna ƙaunar fasiƙanci, ruwan inabi, da sabon ruwan inabi, wanda yake ɗauke fahimtarsu.12Mutanena suna neman shawara daga gumakun itacensu, sandar tafiyarsu kuma na basu anabce - anabce. Domin tunanin fasiƙanci ya ɓadda su, sun aikata karuwanci maimakon su zama da aminci ga Allahnsu.
13Suka miƙa hadayu a ƙwanƙolin duwatsu, suka ƙona turare bisa tuddai, ƙarƙashin rimaye, foflas da tsamiya, domin inuwar tana da daɗi. Sai 'ya'yanki mata suka yi lalata, surukanki mata kuma suka yi zina.14Bazan hori 'ya'yanki mata ba sa'ad da suka zaɓi suyi fasiƙanci, ko surukanki mata idan suka yi zina. Domin maza ma suna bada kansu ga karuwai, suna miƙa hadayu domin su yi lalata da keɓaɓɓun karuwai. Waɗannan mutane da basu da ganewa zan fyaɗa su ƙasa.
15Koda yake Isra'ila kin yi zina, bari Yahuda ma kada ta yi saɓo. Ku mutane, kada ku tafi Gilgal, kada ku haye zuwa Bet Aben, kada kuma ku rantse kuna cewa, "Yahweh hakika mai rai ne."16Gama Isra'ila ta yi taurin kai, kamar karsana mai gardama. Ƙaƙa Yahweh zai kawosu makiyaya kamar 'yan tumaki wurin kiwo?
17Ifraim ya haɗa kansa da gumaka; ku ƙyale shi.18Harma idan barasarsu ta ƙare, sukan ci gaba da zinarsu, masu mulkinsu suna amincewa da kunyarsu ƙwarai.19Iska za ta nannaɗe ta cikin fukafukanta; za su kuma ji kunya saboda hadayunsu.

5

1Ku ji wannan ku firistoci! Ku natsu, gidan Isra'ila! Ku kasa kunne, gidan sarki! Domin hukunci na zuwa bisa kanku dukka. Kun zama tarko a Mizfa tarun da aka baza akan Tabor.2'Yan tawaye sun dage da hallakarwa, amma zan hukunta dukkansu.

3Na san Ifraim, Isra'ila kuma ba a ɓoye take a gare ni ba. Ifraim yanzu kin zama kamar karuwa; Isra'ila ta ƙazantu.4Ayyukansu ba za su barsu su juyo ga Allah ba, domin tunanin zina yana cikinsu, ba su kuwa san Yahweh ba.
5Girman kan Isra'ila yana shaida a kansu, saboda haka Isra'ila da Ifraim za suyi tuntuɓe cikin laifinsu. Yahuda ma zai yi tuntuɓe tare dasu.6Zasu tafi tare da garkunansu na tumaki dana shanu su biɗi Yahweh, amma baza su same shi ba, gama ya rigaya ya janye kansa daga gare su.7Sunyi rashin aminci ga Yahweh, domin sun haifi 'ya'yan haram. Yanzu bukukuwan sabon wata zai cinyesu dasu da gonakinsu.
8Ku busa ƙaho a Gibiya, da kakaki a Rama. Ku tada kururuwar yaƙi a Bet Aben: 'Za mu bi ki Benyamin!'9Ifraim zata zama kango a ranar hukuncinta. Na yi shelar abin da zai faru lallai a cikin ƙabilar Isra'ila.
10Shugabannin Yahuda suna kama da masu kawar da dutsen kan iyaka, zan zuba hasalata a kansu kamar ruwa.11An murƙushe Ifraim; an danne shi a shari'a domin da yardar rai ya bi gumaka.
12Saboda haka zan zama kamar asu ga Ifraim, kuma kamar tsatsa ga gidan Yahuda.13Da Ifraim ya ga cutarsa, Yahuda ma ya ga rauninsa, sai Ifraim ya tafi Asiriya, Yahuda kuwa ya aiki jakadu wurin babban sarki. Amma bai iya warkar da mutanen ku ba, bai kuma iya warkar da raunukanku ba.
14Saboda haka zan zama kamar zaki ga Ifraim, kuma kamar dan zaki ga gidan Yahuda. Ni, I, Ni' kaina zan kekketasu in yi tafiya ta; zan kwashe su; ba kuma wanda zai cecesu'15Zan tafi in koma wurina, har sai sun yarda su karɓi laifinsu su kuma biɗi fuskata, sai kuma sun biɗe ni da aniya cikin ƙuncinsu."

6

1"Zo, mu koma gun Yahweh, gama ya yayyaga mu, amma zai warkar da mu; ya ji mana rauni, amma zai ɗaure mana raunukanmu.2Bayan kwana biyu, zai farkar da mu; zai tashemu a rana ta uku, zamu rayu kuma a gabansa.3Bari mu san Yahweh, bari mu ƙara nacewa mu san Yahweh. Zuwansa tabbataccene kamar wayewar gari. Zai zo wurinmu kamar ruwan sama, kamar ruwan ƙarshe mai jiƙa ƙasa.

4Ifraim me zan yi da ke? Yahuda, me zan yi da ke? Amincinki kamar gajimaren safe ne, kamar raɓar da take kaɗewa da wuri.5Saboda haka na daddatse su ta wurin annabawansu, na kashesu da maganganun bakina. Umarninka kamar haske ne mai sheƙi.
6Gama ina biɗar aminci ne ba hadaya ba, da kuma sanin Allah fiye da hadayun ƙonawa.7Kamar Adamu sun karya alƙawari; sun yi mani rashin aminci.
8Giliyad birnin mugaye ne mai sawun jini.9Kamar yadda taron mafasa suke wa mutum kwanto haka ƙungiyar firistoci suke haɗa kai su yi kisa a hanya zuwa Shekem; sun aikata laifofi masu ban kunya.
10A cikin gidan Isra'ila na ga mummunan abu; karuwancin Ifraim na nan, Isra'ila kuma ta ƙazantu.11Ke kuma, Yahuda, an ƙaddara miki girbi, sa'ad da zan mayar wa mutanena albarkunsu.

7

1Duk lokacin da nake so in warkar da Isra'ila, sai zunuban Ifraim su bayyana, haka kuma mugayen ayyukan Samariya, domin suna shirya yaudara; ɓarawo ya kan shigo, mafasa kuwa su kai hari a titi.2Basu sani ba a zukatansu ina sane da dukkan mugayen ayyukansu. Yanzu ayyukansu sun kewayesu; suna nan a fuskata.

3Da muguntarsu suke faranta wa sarki rai, hakimai kuma da ƙarairayi.4Dukkansu mazinata ne, kamar tanderun wuta da mai tuya ya dena zuga wutar daga lokacin kwaɓa curi zuwa lokacin sa gami.5A ranar sarki, hakimai suka sa wa kansu ciwo da ƙunar barasa. Ya miƙa hannunsa ga masu yin ba'a.
6Da zuciya kamar tanderu suna ƙirƙiro dabarun ƙarya. Fushinsu; na ƙuna da dare, da safe yakan tashi kamar harshen wuta.7Duk suna da zafi kamar tanderu, suna kuma hallakar da masu mulkinsu. Dukkan sarakunansu sun faɗi; ba wanda yake kira na.
8Ifraim ya na cuɗanya da al'umma. Ifraim waina ne mai faɗi da ba a juya shi ba.9Bãƙi sun cinye ƙarfinsa, amma bai sani ba. An yayyafa furfura a kansa, amma bai sani ba.
10Girman kan Isra'ila na shaida gãba akansa a; duk da haka basu dawo ga Yahweh Allahnsu ba, basu kuma neme shi ba duk da waɗannan abubuwa.11Ifraim kamar kurciya yake, mara wayo, ba hankali, yana kiran Masar yana firiya zuwa Asiriya.
12Sa'ad da suka tafi, zan baza ragata a kansu, zan jawo su ƙasa kamar tsutsayen sama. Zan hukunta su a tarayyarsu.13Kaiton su! Domin sun gudu daga gare ni. Hallaka tana zuwa kansu! Sun yi mani tawaye! Dã na cece su, amma sun yi mani ƙarya.
14Basu yi mani kuka da dukkan zuciyarsu ba, amma a kan gadajensu suke rusa kuka. Suna taruwa domin hatsi da sabon ruwan inabi, sun juya daga gareni.15Ko da yake ni na koyar dasu na kuma ƙarfafa hannuwansu, amma yanzu suna ƙulla mani mugunta.
16Sun dawo, amma ba su dawo wurina ba, Mafi ‌Ɗaukaka. Suna kama da bakan da ya saki. Hakimansu za su fãɗi da kaifin takobi, saboda hasalar harshensu. Wannan zai jawo masu ba'a cikin kasar Masar.

8

1Ka sa ƙaho a leɓunanka! Gaggafa na zuwa bisa kan gidan Yahweh domin mutane sun karya alƙawarina sun kuma bijirewa dokokina.2Sun yi kuka gare ni, 'Ya Allahna, mu a Isra'ila mun san ka.'3Amma Isra'ila taƙi abin dake mai kyau, maƙiyi kuma zai tasar masa.

4Sun naɗa sarakuna, amma ba dani ba, sun yi hakimai, amma bada sani na ba. Da zinariyar su da azurfa suka yi wa kansu gumakai, amma lallai za a datse su."5"An ƙi ɗan maraƙinki ya Samariya. Fushina yana ƙuna akan waɗannan mutane. Har yaushe zasu kasance cikin laifi?
6Gama wannan gunki daga wurin Isra'ila ya fito; mutum ne yayi shi; ba Allah ba ne! Za a farfashe ɗanmaraƙin Samariya.7Gama mutane sun shuka iska sun girbe guguwa. Hatsin dake tsaye ba shi da tsaba; bai bada gari ba. Ko da ya nuna, bãƙi ne zasu cinye shi.
8An haɗiye Isra'ila; yanzu sun kwanta tare da ƙasashe sai kace abin da ba shi da amfani.9Gama sun hau zuwa Asiriya kamar jakin jeji shi ka ɗai. Ifraim tayi hayar masoya domin kanta.10Ko da zasu yi hayar masoya daga cikin al'ummai, yanzu zan tara su. Zasu fara lalacewa, saboda danniyar sarkin sarakuna.
11Saboda Ifraim ya ruɓanya bagadai domin miƙa baye-baye na zunubi, amma a maimakon haka sai suka zama bagadan aikata zunubi.12Ko da zan rubuta masu dokata sau dubu goma, zasu dube ta a matsayin baƙon abu a gare su.
13Game da maganar hadayun baye-bayena, suna hadaya da nama su kuma ci. Amma ni, Yahweh, ban karɓe su ba. Yanzu zan tuna da muguntarsu in hukunta zunubansu. Za su koma Masar.14Isra'ila ya manta da ni, Mahaliccinsa, ya kuma gina masarautai. Yahuda ya gina garu masu yawa, amma zan aikar da wuta bisa biranen su; zai hallakar da kagara.

9

1Isra'ila, kada ka yi farinciki, tare da murna kamar sauran mutane. Gama ka yi ta rashin aminci, ka yashe da Allahnka. Kana son biyan haƙƙoƙin karuwa a dukkan masussukai.2Amma masussuka da wurin matsewar inabi ba zasu ciyar da su ba; sabon ruwan inabi kuma zai ƙare.

3Ba zasu ci gaba da zama a ƙasar Yahweh ba; maimakon haka, Ifraim zai koma Masar, wata rana zasu ci ƙazantaccen abinci a Asiriya.4Ba zasu zuba hadayun inabi ga Yahweh ba, ba kuma zasu zama abin karɓa gare shi ba. Hadayunsu zasu zama kamar abincin makoki: duk wanda ya ci shi zai ƙazantu. Domin abincinsu zai zama nasu ne kaɗai; ba zai zo cikin gidan Yahweh ba.
5Me za ku yi a ranar da aka keɓe don taruwa, a ranar idi ta Yahweh?6Gama, duba, idan sun kubcewa hallaka, Masar zata tara su, Memfis kuma za ta bizne su, kayayyakin daraja na azurfa - abubuwa masu tsini zasu mallake su, ƙayayuwa kuma za su cika rumfunansu.
7Kwanakin hukunci suna zuwa; kwanakin sakamako suna zuwa. Bari dukkan Isra'ila su san waɗannan abubuwa. Annabin wawa ne, masanin kuma taɓaɓɓe ne, saboda girman muguntarka da yawan zafin ranka.
8Annabi mai tsaro ne domin Allahna akan Ifraim. Amma tarkon tsuntsu yana kan dukkan hanyoyinsa, rashin jituwa kuma na cikin gidan Allahnsa.9Sun ƙazantar da kansu ƙwarai kamar a cikin kwanakin Gibiya. Allah zai tuna da muguntarsu, zai kuma hukunta zunubansu.
10Yahweh yace, "Lokacin da na samo Isra'ila, kamar samun 'ya'yan inabi ne a cikin jeji. Kamar nunan farin itacen ɓaure a lokacinsa, na samo ubanninku. Amma suka je wurin Ba'al Fiyo, suka kuma miƙa kansu ga wannan gunki abin kunya. Suka zama abin ƙyama kamar gunkin da suke ƙauna.
11Amma ga Ifraim darajarsu zata tashi kamar tsuntsu. Ba mai haihuwa, ba mai juna biyu, ko mai daukar ciki.12Ko da yake sun goyi 'ya'ya, zan ɗauke su daga gare su ba wanda zai ragu. Kaiton su sa'ad da na juya daga gare su!
13Na ga Ifraim, kamar Taya, an dasa ta a wuri mai dausayi, amma Ifraim zai kawo 'ya'yansa wurin wani wanda zai yayyanka su."14Ka ba su, Yahweh - me zaka ba su? Ka ba su mahaifa mai yin ɓari, da nonon da baya ba da madara.
15"Saboda muguntarsu a Gilgal, a can ne na fara ƙinsu. Saboda mugayen ayyukansu, zan kore su daga cikin gidana. Bazan ƙara ƙaunarsu ba; dukkan shugabanninsu 'yan tawaye ne.
16Ifraim na da cuta, sauyarsa kuma ta bushe; basu ba da 'ya'ya. Ko da zasu sami 'ya'ya, zan kashe ƙaunattatun 'ya'yansu."17Allahna zai ƙi su saboda ba suyi masa biyayya ba. Zasu zama masu kai wa da komowa cikin al'ummai.

10

1Isra'ila kuringa ce mai yabanya dake ba da 'ya'yansa. Gwargwadon yawan 'ya'yansa gwargwadon yawan gina bagadansa. Bisa ga albarkar ƙasarsa, yakan inganta ginshiƙansa.2Zuciyarsu da yaudara; yanzu dole su ɗauki laifinsu. Yahweh zai rushe bagadansu; zai lalatar da ginshiƙansu.

3Sa'annan zasu ce, "Bamu da sarki, domin ba mu jin tsoron Yahweh, sarki kuma -- me zai yi mana?"4Maganganunsu na wofi ne, su kan ɗauki wa'adodi ta wurin rantsewa kan ƙarya. Domin wannan adalci ya tsuro kamar tsire - tsire masu dafi cikin gona.
5Mazaunan Samariya zasu tsorata saboda 'yan'maruƙan Bet Aben. Mutanenta zasu yi makoki a kanta, kamar yadda mazinatan firistoci suka yi murna a kansu da darajarsu, amma yanzu ba su nan.6Za a kai su Asiriya a matsayin kyauta ga babban sarki. Za a kunyatar da Ifraim, Isra'ila kuma za ta ji kunya saboda gumakanta.
7Za'a hallakar da sarkin Samariya, kamar sassaƙen itace a bisa ruwa.8Za a hallakar da wurin zaman mugunta. Wannan shi ne zunubin Isra'ila! Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya zasu fito bisa bagadansu. Mutane zasu cewa duwatsu, "Ku rufe mu!" tuddai kuma, "Ku faɗo mana!"
9Isra'ila kayi zunubi tun kwanakin Gibiya; a can ka tsaya. Ko yaƙi ba zai iske 'ya'yan kurakurai a Gibiya ba?
10A lokacin da na so, zan horar dasu. Al'ummai zasu taru su ɗaure su saboda laifofinsu.11Ifraim horarriyar karsana ce dake son sussukar hatsi, zan sa karkiya a bisa kyakkyawan wuyanta. Zan sa karkiya a wuyan Ifraim; Yahuda zai yi huɗa; Yakubu kuma zai ja garma da kansa.
12Ku shuka wa kanku adalci, za ku girbi ɗiyan alƙawarin aminci. Kuyi kaftun saurar ƙasarku, gama lokaci ya yi da za a nemi Yahweh, har lokacin da zai zo ya zuba adalci a kanku.13Kun shuka mugunta; kun girbe rashin adalci. Kun ci 'ya'yan yaudara saboda kun dogara ga shirye-shiryenku da kuma yawan sojojinku.
14Domin wannan hargitsin yaki zai tashi daga cikin mutanenku, za a kuma lalatar da dukkan garuruwanku masu kagara, zai za ma kamar yadda Shalman ya lalatar da Bet Arbel a ranar yaƙi, aka datse uwaye da 'ya'yansu gunduwa-gunduwa.15Haka zai faru dake, Betel, saboda muguntar ki mai yawa. Da wayewar gari za a datse sarkin Isra'ila gaba ɗaya."

11

1Lokacin da Isra'ila yake yaro na ƙaunace shi, na kuma kira ɗana daga cikin Masar.2Yawan kiran su, yawan gujewar su daga gare ni. Sun miƙa hadaya ga Ba'aloli, suka ƙona turare ga gumaka.

3Duk da haka ni na koyawa Ifraim tafiya. Ni ne na ɗaga su da hannuwansu, duk da haka basu sani na kula dasu ba.4Na bishe su da linzamin mutune, da ragamar ƙauna. Na zama kamar mai kwance masu karkiya a muƙamuƙinsu, na sunkuya masu na ciyar dasu kuma.
5Baza su koma ƙasar Masar ba? Ko Asiriya ba za suyi mulkinsu saboda sunƙi juyowa gare ni ba?6Takobi zai faɗa wa biranensu ya hallaka ƙarafan ƙofofinsu; zai hallaka su saboda shirye-shiryensu.7Mutanena sun ƙudurta juyawa daga gareni. Ko da sun yi kira ga Maɗaukaki, ba wanda zai taimake su.
8Ta yaya zan iya rabuwa da kai, ya Ifraimu? Ta yaya zan mika ka, ya Isra'ila? ‌‌‌Ƙaƙa zan maishe ka kamar Adma? Yaya zan maishe ka kamar Zeboyim? A gare ni zuciyata ta canza; dukkan jinƙaina ya harzuƙa.9Bazan tabbatar da zafin fushina ba; bazan hallakar da Ifraim ba. Gama Ni Allah ne ba mutum ba; Ni ne Mai Tsarki wanda ke tsakiyar ku, ba kuwa zan zo cikin hasala ba.
10Zasu bi Yahweh; shi kuma zai yi ruri kamar zaki. Idan yayi ruri, 'ya'yansa za su zo suna rawar jiki daga yamma.11Zasu zo da rawar jiki kamar tsuntsu daga Masar, kamar kurciya daga ƙasar Asiriya. Zan maishe su su zauna a gidajensu - wannan furcin Yahweh ne.
12Ifraim ya kewaye ni da ƙarairayi, gidan Isra'ila kuma da yaudara. Amma Yahuda har yanzu yana tare da ni, Allah, yana yi mani aminci, Mai Tsarkin nan."

12

1Ifraim yana ci daga iska, ya na bin iskar gabas. Kullum yana yawaita ƙarairayi da ta'addanci. Sun yi alƙawari da Asiriya suna ɗaukar man zaitun zuwa Masar.2Yahweh kuma yana da ƙara gãba da Yahuda kuma zai hukunta Yakubu saboda abin da ya yi; zai sãka masa gwargwadon ayyukansa.

3A cikin ciki Yakubu ya kama duddugen ɗan'uwansa, a cikin balagarsa kuma yayi kokowa da Allah.4Yayi kokowa da mala'ika kuma ya yi nasara. Ya yi kuka ya roƙi tagomashinsa. Ya sadu da Allah a Betel; a can Allah yayi magana da shi.
5Wannan shi ne Yahweh, Allah Mai runduna; "Yahweh" shi ne sunansa da za a dinga kira6Domin wannan ka juyo wurin Allahnka. Ka kiyaye alƙawarin jinƙai da adalci, kana cigaba da sauraron Allahnka.
7'Yan kasuwa na riƙe da ma'aunin algus a hannunsu; suna son yin algus.8Ifraim yace, "Hakika na zama mai arzaƙi sosai; na samarwa kaina dukiya. A cikin dukkan aikina ba za a sami laifi a ciki na ba, ko duk wani abin da zai zama zunubi."
9"Ni ne Yahweh Allahnku tun daga ƙasar Masar. Zan kuma sa ku sake zama cikin rumfuna, kamar cikin kwanakin ayyanannen idi.10Na yi magana da annabawa, na kuma basu wahayi da yawa domin ku. Ta hannun annabawa kuma na ba da misalai."
11Idan akwai mugunta a Giliyad, hakika mutane sun zama marasa amfani. A Gilgal sun yi hadayar bajimai; bagadansu zasu zama kamar tsibi -tsibin dutse a cikin gonaki.12Yakubu ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra'ila ya yi aiki domin ya sami mata; ya yi kiwon garkunan tumaki domin ya sami mata.
13Yahweh ya fitar da Isra'ila daga Masar ta wurin annabi, ta hannun annabi kuma ya kula dasu.14Ifraim ya baƙanta wa Yahweh rai. Domin wannan Ubangijinsa zai bar jininsa a kansa, zai kuma sãka masa akan duk abin kunyarsa.

13

1"Sa'ad da Ifraim ya yi magana, akwai razanarwa. Ya ɗaukaka kansa a Isra'ila, amma ya zama da laifi wajen bautar Ba'al, kuma ya mutu.2Yanzu, sai ƙara zunubi suke tayi, suna yiwa kansu sifofi na zubi daga azurfarsu, gumaka ne da masu hikima suka ƙera, dukkan su aikin gwanayen masu sana'a ne. Mutane suka ce masu, 'Waɗannan mutane masu miƙa hadaya sunyiwa 'yanmaruƙa sumba.'

3Domin wannan zasu zama kamar gizagizan safe, kamar raɓa mai kaɗewa da sauri, kamar ƙai-ƙayi wanda iska ke hurewa daga masussuka, kamar hayaƙi daga cikin mafitarsa.
4Amma ni ne Yahweh Allahnka tun daga ƙasar Masar, dole ka sani cewa ba bu wani Allah sai ni, dole kuma ka amince cewa banda ni babu wa ni mai ceto.5Na san ka a cikin jeji, cikin ƙasa mai tsananin fari.6Da kuka sami makiyaya, kun zama ƙosassu; amma bayan da kuka ƙoshi, kun ɗaukaka kanku. Saboda wannan dalili kuka manta da ni.
7Zan zama kamar zaki a gare su; kamar damisa zan yi fako a kan hanya.8Zan faɗa masu kamar damisa da aka ƙwace mata 'ya'yanta, zan tsaga haƙarƙarin ƙirjin su, a can ne zan cinye su kamar zaki, kamar naman jeji zan yayyage su gunduwa-gunduwa.
9Zan hallaka ku, ya Isra'ila; wanene zai iya taimakon ku?10Yanzu ina sarkinku, da za ya iya ceton ku daga cikin dukkan biranenku? Ina shugabanninku waɗanda kuka ce mani, 'Ka bamu sarki da hakimai'?11Na baku sarki cikin fushina, na kuma kawar da shi cikin hasalata.
12Laifin Ifraim a ajiye yake; an kuma ajiye kurakuransa,13Zafin naƙudar haihuwa za ta afko masa, amma ɗa ne mara hikima, domin idan lokacin haihuwarsa ya yi, ba zai fita daga cikin mahaifa ba.
14̀̀̀̀̀Zan cece su daga hannun Lahira? Zan cece su daga mutuwa? Mutuwa, ina, annobanki? Lahira, ina hallakarwarki? Babu sauran tausayi daga idanuna."
15Koda Ifraim ya azurta cikin 'yan'uwansa, iskar gabas za ta zo; guguwar Yahweh za ta buga daga hamada. Maɓulɓular Ifraim za ta bushe, rijiyarsa ba zata ba da ruwa ba. Abokan gãbarsa zasu washe ɗakin ajiyar dukkan kayansa masu daraja.
16Samariya za ta ji kunya, domin ta tayarwa Allahnta. Zasu faɗi ta kaifin takobi; ƙananan 'ya'yansu za a yayyankasu, matansu masu ciki za a farke su.

14

1Isra'ila, ka juyo wurin Yahweh Allahnka, gama ka faɗi saboda laifinka.2Ka ɗauki maganganun tare da kai ka juyo wurin Yahweh. Ka ce masa, "Ka kawar da dukkan laifinmu ka kuma karɓi abin da ke mai kyau, domin mu iya miƙa maka ɗiyan leɓunanmu.

3Asiriya ba za su cece mu ba; ba za mu hau dawakai mu yi yaƙi ba. Ba kuwa zamu ƙara ce da aikin hannuwanmu, 'Ku ne allolinmu,' gama a cikinku marayu ke samun jinƙai."
4"Zan warkar da bauɗewarsu; zan ƙaunacesu a yalwace, domin na kawar da fushina daga gare shi.5Zan zama kamar raɓa ga Isra'ila; zai yi fure kamar auduga, ya kuma kafu kamar itacen sida a Lebanon.6Rassansa zasu yaɗu waje; kyaunsa zai zama kamar itatuwan zaitun, ƙanshinsa kuma kamar itatuwan sida a Lebanon.
7Mutanen da ke zaune ƙarƙashin inuwarsa zasu dawo; zasu farfaɗo kamar hatsi zasu yi fure kamar kuringar inabi. Shahararsa za ta zama kamar inabin Lebanon.8Ifraim, me zan yi kuma da gumaka? Zan amsa masa in lura da shi. Ni kamar itacen bakin rafi ne wanda kullum ganyayensa kore ne; daga wurina kuke samun 'ya'ya."
9Wane ne mai hikima da zai fahimci waɗannan abubuwa? Wane ne ya fahimci waɗannan abubuwa domin ya san su? Gama hanyoyin Yahweh dai-dai suke, adali kuwa zaya yi tafiya cikinsu, amma masu tayarwa zasu faɗi a cikinsu.

Littafin yowel

1

1Wannan ita ce maganar Yahweh da ta zo ga Yowel ɗan Fetuwel.2Ku ji wannan ku dattawa, ku kuma kasa kunne dukkan ku mazauna ƙasar. Ko wannan ya taɓa faruwa a kwanakinku ko a kwanakin iyayenku?3Ku faɗa wa 'ya'yanku labarinsa, 'ya'yanku kuma su fada wa tsara mai zuwa.

4Abin da bãbe ya rage fara ta ci; abin da da fara ta bari burdunnuwa ta ci; abin da burdunnuwa ta rage; ganzari ya cinye.
5Ku mashaya, ku tashi, ku yi ta kuka! Ku yi ta baƙin ciki, ku dukkan mashayan ruwan inabi, don an datse inabinku mai zaƙi daga gare ku.6Don wata al'umma ta zo kan ƙasata, ƙaƙƙarfa mara ƙidayuwa. Haƙoransu haƙoran zãki ne, kuma suna da haƙoran zãkanya.7Sun mayar da kuringar inabina abar wofi. Sun yayyage dangar itacen ɓaurena, sun yayyage dangar sun watsar; rassan sun koɗe sun yi fari.
8Ku yi makoki kamar amaryar da ke makokin mutuwar angonta.9An dena miƙa baikon hatsi da na abin sha daga gidan Yahweh. Firistoci, bayin Yahweh suna makoki.10Filaye sun bushe, ƙasa tana makoki saboda an hallakar da hatsi. Sabon ruwan inabi ya ƙare, mai ya kasa.
11Ku manoma ku ji kunya, ku yi baƙinciki, hakan nan ku wuraren matse ruwan inabi, saboda alkama da sha'ir. Don abin da aka girbe ya lalace.12Inabi sun kaɗe, itatuwan ɓaure kuma sun bushe, itacen ruman, da kuma na dabino, da gawasa duk da sauran itatuwa sun bushe. Don farinciki ya ƙare daga cikin mutane
13Ku firistoci ku sa tufafin makoki, ku firistoci ku yi bakin ciki, ku masu hidima a bagadi ku kwanta cikin tufafin makoki har safiya, ku bayin Allahna. Don an hana miƙa baikon hatsi da na abin sha daga gidan Allahnku.14Ku yi kira a yi azumi mai tsarki, ku kuma yi kira a yi tattaruwa mai tsarki. Ku tattara dattatawa da dukkan mazaunan ƙasar zuwa gidan Yahweh Allahnku, ku yi kuka ga Yahweh.
15Kaito saboda ranar! Gama ranar Yahweh ta ƙarato. Tare da ita akwai hallakarwa daga Mai iko dukka.16Ba a ɗauke abinci daga gabanmu ba, an kuma ɗauke farinciki da fara'a daga gidan Allahnmu ba?17Iri ya lalace a kofensa, an wulaƙanta hatsi, an banzantar da wuraren ajiya don hatsi ya yanƙwane.
18Yaya dabbobi ke nishi! Makiyayan dabbobi kuma ke shan wahala saboda ba wurin kiwo. Hakannan kuma garken tumaki na shan wahala.19Yahweh, ina kuka gare ka. Don wuta ta cinye makiyayar dake jeji, harshen wuta kuma ya ƙone bishiyoyin dake cikin filayen.20Har da dabbobin jeji suna yi maka kuka, don ƙoramun ruwa sun bushe, wuta kuma ta cinye makiyayar jeji.

2

1Ku hura ƙaho a Sihiyona, ku kuma kaɗa kararrawa a kan duwatsuna masu tsarki! Bari dukkan mazaunan ƙasar su gigice don tsoro, Don hakika ranar Yahweh tana tafe, hakika ta kusa.2Rana ce ta duhu baƙiƙƙirin, rana ce ta giza-gizai da baƙin duhu. Kamar yadda duhu ke rufe duwatsu, babbar rundunar sojoji tana kusantowa. Ba a taɓa samun soja kamarta ba, ba kuma za a sake samun kamar ta ba, Koma a bayan tsararraki da yawa.

3Wuta na cinye duk abin da ke gabanta, bayanta kuma harshen wutar yana ƙuna. ƙasar ta zama kamar gonar Adnin a gabanta, amma a bayanta akwai jejin da ba komai. Ba kuma abin da zai tsira daga gare ta.
4Bayyanuwar sojojin kamar ta dawakai ce, kuma su na gudu kamar mahayan dawakai.5Suna tsalle da ƙara kamar na masu karusa a kan duwatsu, kamar kuma ƙarar wutar da ke cin tarin yayi, kamar ta Sojoji masu iko dake shirye domin yaƙi.
6A gabansu jama'a na cikin ƙunci, dukkan fuskokinsu kuma suka yi suwu.7Suna gudu kamar na jarumawa masu iko; suka hau katanga kamar sojoji; suna tafiya a jere kowanne dai-dai a kan sawu, basu kauce matsayinsu ba.
8Ba wanda ya tunkuɗe wani a gefe, kowa yana tafiya a gefensa, suka kutsa ta cikin kariyar basu kuma kauce layi ba.9Suka ruga kan birnin, suna gudu a kan ganuwa, suka haura cikin gidaje, suka shiga ta tagogi kamar ɓarayi.
10Duniya ta girgiza a gabansu, sammai kuma suka firgita, rana da wata sun duhunta, taurari kuma sun dena haskakawa.11Sai Yahweh ya tada muryarsa a gaban sojojinsa, don sojojinsa suna da yawa sosai, suna kuma da ƙarfi, waɗanda ke karɓar umarninsa. Don ranar Yahweh tana da girma da kuma ban tsoro sosai. Wa zai iya jure mata?
12"Amma ko yanzu ma, "Yahweh yace, "Ku juyo wurina da dukkan zuciyarku. Ku yi azumi da kuka, da makoki."13Ku keta zuciyarku ba tufafinku kawai ba, ku komo wurin Yahweh Allahnku. Don shi mai alheri ne da jinƙai, marar saurin fushi kuma ya na cike da alƙawari mai aminci, kuma zai so ya kawar da aiwatar da hukunci.
14Wa ya sani? Ko zai juyo ya ji tausayi, ya kuma sa masa albarka, da baiko na hatsi da na abin sha saboda Ubangiji Allahnku?
15A hura ƙaho a Sihiyona, a kira ayi azumi mai tsarki, a kuma yi kira ayi tattaruwa mai tsarki.16A tattara jama'a don tattaruwa mai tsarki, a tattara dattawa, a tattara 'yan yara da jarirai masu shan nono. Sai anguna su fito daga ɗakunansu, amare kuma daga kagararsu ta amarcinsu.
17Sai firistoci bayin Yahweh su yi kuka a tsakanin bagadi da shirayi. Sai su ce, "Ya Yahweh, ka ceci mutanenka, kada kuma ka mai da gãdonka abin ba a, har al'ummai su yi musu ba a. Me ya sa za su faɗa a cikin al'umai cewa, 'Ina Allahnsu?'"
18Sai ya yi kishin ƙasarsa, ya kuma ji tausayin mutanensa.19Yahweh ya amsa wa mutanensa, "Duba zan aiko maku da hatsi, da sabon ruwan inabi, da mai. Zasu wadace ku, kuma ba zan ƙara mai da ku abin wulaƙanci ba a cikin al'ummai.
20Zan kawar da maharan nan na arewa daga gare ku, kuma za ku kore su zuwa yasassun wurare. jagoran sojojinsu zai fuskanci gabashin teku. Bãshinta zai tashi, mumunan warinta kuma zai tashi.' Hakika, ya yi manyan abubuwa.
21Ƙasa kada ki tsorata, ki yi murna da farinciki, domin Yahweh zai yi manyan abubuwa.22Kada ku ji tsoro, namomin jejin da ke cikin saura, gama tsire-tsiren dake cikin saura zasu tohu, itatuwa zasu bada 'ya'ya, kuma itacen ɓaure da na inabi za su bada "ya'yansu sosai.23Mutanen Sihiyona ku yi murna, kuma ku yi farinciki cikin Yahweh Allanhnku. Don zai baku ruwan sama da bazara ya kuma buɗe sakatun sama dominku, ruwan bazara da na koramunku kuma kamar dã.
24Masussuka za ta cika da alkama, wurin matsar inabi kuma zai cika da sabon ruwan inabi da mai.25"Zan komo maku da shekarun da kuka yi asarar hatsinku wanda fãra ta cinye wato wannan farar mai hallakarwa da na aiko cikinku.
26Za ku ci ku ƙoshi sosai, ku yabi sunan Yahweh Allahnku, wanda ya aikata abubuwan al'ajabi a cikinku, kuma ba zan taɓa sake kawo abin kunya akan mutane na ba.27Za ku san cewa ina cikin Isra'iila, kuma ni ne Yahweh Allahnku, kuma babu wani sai ni, kuma ba zan ƙara kawo kunya akan mutanena ba.
28Bayan wannan kuma zan zubo da Ruhuna ga dukkan mutane, 'ya'yanku maza da mata za su yi anabci. Tsofaffinku zasu yi mafarkai, samarinku kuma zasu ga wahayi.29Kuma ga bayi da mata bayi, a waɗancan kwanaki zan zubo musu da Ruhuna.
30Zan nuna al'ajabai a sama da kuma a duniya, jini, da wuta, da murtukewar hayaƙi.31Rana zata duhunta, wata kuma zai zama jini, kafin babbar ranar nan ta Ubangiji mai ban tsoro ta zo.
32Zai zama kuma dukkan wanda ya yi kira ga sunan Yahweh zai tsira. Don a dutsen Sihiyona da kuma a cikin Yerusalem za a sami waɗanda suka tsira, kamar yadda Yahweh ya ce, da kuma cikin waɗanda suka rayu, wato waɗanda Yahweh ya kira.

3

1A waɗannan kwanaki da lokatai, sa'ad da na komar da masu zaman talalar Yahuda da Yerusalem,2Zan tattara dukkan al'ummai in kuma kawo su kwarin Yehoshafat. A can zan yi masu shari'a, saboda jama'ata da abin gãdona Isra'ila, waɗanda suka warwatsar cikin al'ummai, saboda kuma sun raba ƙasata.3Sun kuma jefa ƙuri'a kan mutanena, sun sayar da yaro saboda da karuwa, sun kuma sayar da yarinya saboda ruwan inabi don su sha.

4Yanzu don me kuke fushi da ni, ku Taya, da Sidon da dukkan yankin Filistiya? Ko za ku sãka mani? Ko da ma kun sãka mani nan da nan zan komo muku da ramuwarku a kanku.5Don kun ɗauke zinariyata da azurfata, kun kuma kawo kayayyakina masu daraja zuwa cikin masujadanku.6Kun sayar da mutanen Yahuda da na Yerusalem ga Girkawa, don ku cire su can nesa da ƙasarsu.
7Duba, ina gab da in tayar da su, daga inda kuka sayar dasu, ku ne kuma za ku biya kuɗin fansa da kanku.8Zan sayar da 'ya'yanku maza da mata ta hannun mutanen Yahuda. Za su sayar da su ga Sabiyawa, ga al'umma mai nisa, Don Yahweh ne ya furta.
9Yi wannan shela a cikin al'ummai, 'Ku shirya kanku domin yaƙi, ku horar da manyan mutane, ku bar su su zo kusa, ku bar dukkan jarumawan yaƙi su hauro nan.10Ku mayar da dumɓayen garemaninku takkuba, ku kuma mayar da wuƙaƙenku mãsu. Sai raunana su ce "muna da ƙarfi."
11Ku yi sauri ku zo ku makusantan ƙasashe, ku tara kanku wuri ɗaya a can. Yahweh ya kawo ƙarshen mayaƙanku masu iko.'
12Bari al'ummai su tada kansu tsaye su zo kwarin Yehoshafat. Don a can zan zauna don in yi wa dukkan al'umman da ke kewaye shari'a.13Ku ɗauki lauje don girbi ya nũna. Ku zo, ku mãtsi abin sha, don tulunan ruwan inabi sun cika. sun cika suna zuba, saboda muguntarsu tana da yawa sosai."
14Akwai hayaniya, a cikin Kwarin Hukunci. Gama ranar Yahweh ta kusa a cikin Kwarin Hukunci.15Rana da wata sun zama baƙi, taurari kuma sun dena bada haskensu.
16Yahweh zai yi ruri daga Sihiyona, ya kuma tada murya daga Yerusalem. Duniya da sammai za su girgiza, amma Yahweh zai zama mafaka ga mutanensa, da kuma kagara ga mutanen Isra'ila.17"Da haka za ku sani cewa ni ne Yahweh Allahnku wanda ke a Sihiyona, dutsena mai tsarki. Daga nan Yerusalem zata tsarkaka, kuma ba wani sojan da zai ƙara ratsa ta.
18A wannan rana kuma duwatsu zasu cika da ruwan inabi mai zaƙi, tuddai kuma za su kwararo da madara, dukkan ƙoramun Yahuda za su ɓulɓulo da ruwa, magudanu za su zo daga gidan Yahweh su jiƙe kwarin Shittim.19Masar zata zama yasasshiya, Idom kuma ta zama jejin da a ka yi watsi da shi, saboda tayarwar da a ka yi wa mutanen Yahuda, saboda an zubar da jinin marasa laifi a ƙasarsu.
20Gama za a zauna a Yahuda har abada, Yerusalem kuma zata zama wurin zama na dukkan zamanai.21Zan yi ramuwar da ban yi ba tukuna a kan jininsu," don Yahweh yana zaune a Sihiyona.

Littafin amos

1

1Waɗannan sune abubuwa game da Isra'ila wanda Amos, ɗaya daga cikin makiyaya a Tekowa ya karɓa a wahayi. Ya karɓa waɗannan abubuwa a kwanakin da Azariya ke mulkin Yahuda, da kuma kwanakin Yerobowam ɗan Yehowash ke sarautar Israila, shekaru biyu kafin girgizar ƙasa.2Ya ce, "Yahweh zai yi ruri daga Sihiyona; zai yi tsawa da murya mai ƙarfi daga Yerusalem. Wuraren kiwo na makiyayan za su bushe; ƙwanƙolin Karmel zai yi yaushi."

3Wannan shi ne abin da Yahweh yace: "Domin zunubai uku na Damasku, har don huɗu ma, Ba zan janye hukuncin ba, domin sun zalunci mutanen Gileyad da maƙamai na ƙarfe.4Zan aika da wuta a kan gidan Hazael, kuma za ta cinye kagarar Ben-hadad.
5Zan karya makaran kyamran Damasku zan kuma kau da mutumin da ke rayuwa a Kwarin Aben, da kuma mutumin da yake rike da sandar girma a Bet Iden. Mutanen Aram za su tafi bauta a Kir," inji Yahweh.
6Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Domin zunubai uku na Gaza har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, domin su ne suka ɗauke kamammun mutane dukka, don su miƙa su ga mutanen Idom.7Zan aika da wuta akan garun Gaza, za ta kuma lakume kagarorinta.
8Zan yanke mutumin da yake rayuwa a Ashdod da kuma mutumin da ya ke riƙe da sandar girma daga Ashkelon. Zan juya hannu na gãba da Ekron, kuma sauran Filistiyawa za su hallaka," inji Ubangiji Yahweh.
9Wannan shi ne abin da Yahweh yace: "Domin zunubai uku na Taya, har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, don sun miƙa dukkan mutanen zuwa Idom, kuma sun karya yarjejeniyar yan'uwantakarsu.10Zan aika da wuta akan garun Taya, kuma za ta ƙone kagarorinta."
11Wannan shi ne abin da Yahweh yace, Domin zunubai uku na Idom, har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, don ya farauci 'ɗan'uwansa da takobi ya kuma kawar da dukkan tausayi. Ya cigaba da fushi, fushinsa ya ɗore har abada.12Zan aika da wuta akan Teman, kuma za ta cinye fadodin Bozra."
13Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Domin zunubai uku na mutanen Ammon, har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, don sun farke mata masu ciki na Gileyad, saboda su ƙara faɗaɗa yankinsu.
14Zan kunna wuta a garun Rabba, kuma za ta cinye fadodin, tare da ihu a ranar yaƙi, tare da rugugin hadari a ranar guguwar.15Sarkinsu zai tafi zuwa bauta, tare da sauran jami'ansa," inji Yahweh.

2

1Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Domin zunubai uku na Mowab, har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, don ya ƙone ƙasusuwan sarkin Idom zuwa toka.

2Zan aika da wuta akan Mowab, kuma za ta cinye kagarorin Keriyot. Mowab zai mutu a hargitsi, tare da sowa da kuma busa ƙaho.3Zan lalata mai shari'a a cikinta, zan kuma kashe dukkan 'ya'yan sarki tare da shi," inji Yahweh.
4Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Domin zunubai uku na Yahuda, har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, domin sun ƙi dokar Yahweh kuma sun ƙi dokokinsa. Ƙarerayinsu sun jawo su yin tafiya ba dai dai ba, kamar yadda ubanninsu su ka yi tafiyar.5Zan aika da wuta akan Yahuda, kuma za ta cinye kagarorin Yerusalem."
6Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Domin zunubai uku na Isra'ila, har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, domin sun sayar da salihai don azurfa da kuma masu bukata akan takalma.
7Sun tattake kawunan talakawan kamar mutane na taka ƙura a ƙasa; suna ture matalauta a gefe. Mutum da ubansa su kwanta a wurin budurwa ɗaya kuma su na ɓata sunana mai tsarki.8Sun kwanta a gefen kowanne bagadi akan tufafin da aka bayar jingina don bashi, kuma a cikin gidajen Allahnsu sukan sha ruwan inabin waɗanda aka yi wa tãra.
9Ga shi na hallakar da Ba'amore a gaban ku, dogaye masu tsawo kamar itatuwan sida; ya na da ƙarfin kamar rimaye. Ga shi na lalata 'ya'yan itatuwansa na sama da jijiyoyin ƙasa.10Kuma na fito da ku daga ƙasar Masar na kuma bi da ku a cikin daji shekaru arba'in, na kuma ba ku ƙasar Amoriyawa.
11Na ta da annabawa daga cikin 'ya'yanku, waɗansu kuma daga cikin samarin sun zama Naziriyawa. Ko ba haka ba ne, ya ku mutanen Israila? Yahweh ne ya faɗa12Amma kun sa Naziriyawa shan ruwan inabi kun kuma umarci annabawa da kada su yi anabci.
13Duba, zan ragargaza ku kamar yadda amalanke cike da hatsi yake ragargaza mutum.14Ko wani mai gudu ma ba zai tsere ba, mai ƙarfi ba zai ƙara wa kansa ƙarfi ba; ko mai iko ya ceci kansa.
15Mai baka ba zai iya tsayawa ba; mai saurin gudu ba zai tsira ba; mahayin doki ba zai ceci kansa ba.16Ko ma sojojin da suka fi jaruntaka za su gudu tsirara a ranan nan - wannan furcin Yahweh ne.

3

1Ku saurari maganar da Yahweh ƙe faɗa akan ku, ku mutanen Isra'ila, akan dukkan iyalinku, na fito da ku daga ƙasar Masar. Ku kaɗai na zaɓa daga kowanne iyalai a duniya.2"Saboda haka zan hukunta ku don zunubanku."

3Zan yiwu mutanen biyu su yi tafiya tare, ba tare da yarda ba?4Zai yiwu zaki yayi ruri a daji ba tare da ya sami kome ba? Zai yiwu ƙaramin zaki yayi gurnani a kogonsa idan bai kama kome ba?
5Zai yiwu tsuntsu ya faɗi akan ƙasa idan ba a kafa masa tarko ba? Zai yiwu tarko ya zargu daga ƙasa idan bai kama wani abu ba?6Zai yiwu mutane su rasa firgita idan suka ji ƙarar ƙaho a birni? Zai yiwu wata masifa ta auko wa birnin amma Yahweh bai aiko ta ba?
7Hakika Ubangiji Yahweh ba zai aikata komai ba ba tare da ya baiyana wa bayinsa annabawa ba.8Zaki yayi ruri wane ne ba zai ji tsoro ba? Ubangiji Yahweh yayi magana; wane ne ba zai yi anabci ba?
9A yi shelar wannan a kagarar Ashdod da kuma kagarar ƙasar Masar; a ce, "Ku tara kanku akan duwatsun Samariya ku ga babban shashanci a cikinta, da kuma irin danniyar da ke cikinta.10Domin ba su san abin da ya ke dai dai ba - wannan furcin Yahweh ne. Sun cika da tashin hankali da barnar kagarorinsu."
11Saboda haka, wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh yace, "Abokin gãba zai kewaye ƙasar. Zai nuna ƙarfinsa ya rushe kagarorinka."12Wannan ne abin da Yahweh yace: "Kamar yadda makiyayi ya kan ceci ƙafafu biyu kadai na tunkiya daga bakin zaki, ko gutsarin kunne, hakanan kuma ke ma daga cikin mutanen Isra'ila wanda yake zama cikin Samariya, a gefen taragon jirgi kaɗai ko a gefen gado."
13Ku ji ku kuma shaida game da gidan Yakubu - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne, Allah mai runduna,14"A ranar da zan hukunta Isra'ila saboda zunubai, zan kuma hukunta bagadodin Betel. ƙahonin bagadi za su kakkarye su kuma fadi a ƙasa.
15Zan lalata gidan hunturu tare da na bazara. Gidajen da aka yi da hauren giwa zasu lalace, babban gidan shi ma zai lalace, - wannan furcin Yahweh ne.

4

1Ku ji wannan maganar, ku shanun Bashan, ku na cikin dutsen Samariya, ku dake danne matalauta, ku dake hallaka mabukata, ku dake cewa da mazajenku, "Kawo mana abin sha."2Ubangiji Yahweh ya rantse da sunansa mai tsarki, "Ku duba, ranaku na zuwa akan ku da za a tafi da ku da ƙugiya, na ƙarshenku tare da fatsar kifi.

3Za ku fita ta wurin da ya tsage a jikin garun birnin, kowannenku zai tafi ta cikin tsaguwar, za a jefar da ku waje wajen Harmon - wannan furcin Yahweh ne."
4Ku tafi Betel ku yi zunubi, tafi Gilgal ku ƙara zunubi, ku kawo hadayarku kowacce safiya, zakkarku kowane kwanaki uku.5Ku mika gurasarku shaidar haɗayar godiya; ku yi shelar baikon yaddar rai, ku sanar da su, wannan dai dai ne, gare ku mutanen Isra'ila - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.
6Na ba ku tsabtatattun hakora a cikin dukkan biraninku da kuma ƙarancin gurasa a dukkan wurarenku. Duk da haka ba ku juyo gare ni ba - wannan furcin Yahweh ne.7Na kuma hana ruwan sama daga gare ku a lokacin da akwai sauran watanni uku a yi girbi. Na sa a yi ruwa a birni daya, kuma na sa ka da a yi ruwa a wani birnin. Ɗaya daga cikin sashen ƙasar an yi ruwa amma ɗaya sashen ba a yi ruwa ba ya bushe.
8Birane biyu ko uku suna ƙishi har ma sun tafi neman ruwa a birnin, amma ba su ƙoshi ba. Amma duk da haka ba ku komo wurina ba - wannan furcin Yahweh ne.9Na sa ma ku ƙunci tare da darɓa da raɓa. Yawan lambunanku da gonakin inabinku da itatuwan ɓaurenku da itatuwan zaitun ɗinku fari sun laƙume su dukka. Duk da haka ba ku juyo gare ni ba - wannan furcin Yahweh ne.
10Na aika ma ku da annoba irin wanda na aika wa Masar. Na kashe samarinku da takobi, an ɗauke dawakanku, an cika hancinku da ɗoyi. Amma duk da haka kun ki juyo wa gare ni - wannan furcin Yahweh ne.11Na hallakar da biraninku kamar yadda Allah ya hallakar da Saduma da Gwamrata. Kamar sandar da aka fizge daga wuta. Duk da haka ba ku juyo gare ni ba - wannan furcin Yahweh ne.
12Domin haka zan yi wani abu mummuna a kanki, ya Isra'ila; shirya don ki sadu da Allahnki, Isra'ila!13Ku duba, wanda ya yi duwatsu ya kuma halicci iska, ya baiyana tunaninsa ga mutum, ya maida safiya duhu, ya auna wurare na Duniya. Yahweh, Allah mai runduna, shi ne sunansa."

5

1Ku ji wannan maganar dana ɗauke ta kamar ta makoki da zan yi a kanku, gidan Israi'la.2Budurwa Isra'ila kin faɗi, ba za ki ƙara tashi ba, an yasheta a ƙasarta; ba wanda zai ta da ita.

3Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Birnin da ya fita tare da dubu zai dawo da ɗari kaɗai, kuma wanda ya tafi da ɗari amma goma kaɗai za su rage na gidan Isra'ila."
4Wannan shi ne abin da Yahweh ya ce da gidan Isra'ila: "Ku neme ni ku kuma tsira!5Kada ku nemi Betel; ko ku shiga Gilgal; ka da ku tafi Biyasheba. Gama babu shakka ita ma za ta tafi bauta, kuma Biyasheba za ta zama wofi.
6Ku nemi Yahweh ku rayu, ko ya taso ma gidan Yosef kamar wuta. Zai kuwa laƙume, ba kuma wanda zai kashe ta a Betel.7Mutanen nan na juya adalci zuwa abu mai ɗaci kuma suna jefar da ayyukan adalci a ƙasa!"
8Allah ya yi manyan taurari tare da haskensu; ya maida duhu haske; ya maida rana dare shi ne kuma ya kira ruwan teku; ya ƙwararo shi a fuskar duniya. Sunansa Yahweh ne!9Ya kawo hallaka a kan ƙarfafa don lalacewar ta kai kan kagarori.
10Ku na ƙin duk wanda ya ƙwabe ku a ƙofar birnin, kuma tare da duk wanda zai faɗi gaskiya.11Domin kun matsa wa talakawa kuna ƙwace alkama daga gare su - koda yake kun gina gidajenku da dutse, ba za ku zauna a cikinsu ba. Kuna sha'awar gonakin inabinsu, kuma ba za ku sha ruwan inabin ba.
12Domin na san yawan laifofinku, kuma da girman zunubanku - kuna wulakanta masu kirki, ku na karɓar rashawa ku na hanawa talakawa adalci a wurin shari'a.13Saboda haka mai hikima shiru yake a waɗanan lokatai, don mugun lokaci ne.
14Ku nemi yin nagarta ba mugunta ba, saboda ku rayu. Don Yahweh, Allah mai runduna, ya kasance tare da ku, kamar yadda ku ka ce ya ke.15Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta, ku yi adalci a cikin majalisa. Watakila Yahweh, Allah mai runduna, zai yi wa sauran da su ka ragu na Yosef alheri.
16Saboda haka wannan shi ne abin da Yahweh yace, Allah mai runduna, Ubangiji, "Za a yi kuka da kururuwa a kowanne wurin taruwa za su kuma ce a dukkan tituna, 'Kaito! Kaito!' Za su kira manoma su yi makoki kuma masu makokin su yi kuka mai zafi.17A cikin dukkan gonakin inabinku za a yi kuka da kururuwa, don zan wuce a tsakiyar ku," inji Yahweh.
18Kaito ga ku dake marmarin zuwan ranar Yahweh! Me ya sa ku ke jiran ranar Yahweh?19Za ta zama baƙa bakikirin kuma babu haske, kamar wanda ya gujewa zaki ya fada a bakin damisa, ko kuwa kamar wanda ya komo gida ya sa hannunsa a bango, maciji kuma ya sare shi.20Ko ranar Yahweh za ta zama haske ne ba duhu ba? Almuru ne ba haske ba?
21Na ki bukukuwanku ba na murna da tarurukanku.22Ko da ya ke kun kawo mani baikon ƙonawa da baikonku na hatsi ba zan karɓe su ba, ba kuma zan dubi tarurukan baye-bayenku na manyan dabbobinku ba.
23Ku kawar mani da hargowar waƙoƙinku; ba zan saurari kaɗe-kaɗenku da bushe-bushenku ba.24Maimakon haka ku sa adalci ya kwararo kamar ruwa, adalci kuma ya zama kamar kogin da ba ya ƙafewa.
25Gidan Isra'ila ko kun kawo mani hadaya da baye-baye a cikin jeji har shekaru ariba'in?26Duk da haka ku ka ɗauki siffofin Sakkut sarkinsu da Kaiwan, allolinku na taurari- gumakan da kuka yi wa kanku.
27Saboda haka zan sa ku yi ƙaura gaba da Damaskus," inji Yahweh, wanda sunansa Allah mai runduna ne.

6

1Kaiton waɗanda ke zama sake a Sihiyona, da ke da kariya a tudun ƙasar Samariya, da ku da kuke sanannun mutane da suka fi na kowacce al'umma, ga waɗanda gidan Isra'ila ke zuwa don taimako!2Shugabaninku sun ce, "Mu je Kalne mu duba, daga wurin ku je Hamat, babban birnin, sa'an nan har zuwa Gat ta Filistiyawa. Sun fi mulkokinku biyu daraja ne? Ko kuwa, yankin ƙasarsu ya fi naku ne?"

3Kaiton waɗanda suka kawar da ranar masifa suka kuma sa mulkin hargitsi ya zo kusa.4Suna kwance kan gadajen hauren giwa suna jin daɗin miƙe jiki a dogayen kujerunsu. Sun ci naman 'yan raguna daga garke da naman 'yan maruƙa daga turke.
5Suna raira waƙokin wofi da giraya; kuna amfani da kayan aiki kamar Dauda.6Suna shan ruwan inabi daga manyan kwanoni sa'an nan su shafe jikinku da mai mafi kyau, amma ba su yin makoki saboda lalacewar Yosef.
7To yanzu sune na fari da zasu tafi bauta, kuma bukukuwanku da shagulgulanku zasu wuce.8Ni, Ubangiji Yahweh na rantse da kai na - wannan furcin Ubangiji Yahweh, Allah mai runduna, na ƙi girman kan Yakubu; ba na son kagaransa. Saboda haka zan miƙa birnin da duk abin dake ciki.
9Ko da zai zama mutane goma ne suka rage a gida ɗaya, zasu mutu dukka.10Sa'ad da dangin mamacin ya zo don ya ɗauki gawar mamatan -wanda zan ƙone su bayan ya fitar da gawarwaki daga gidan - sai yayi kira ga wanda ya ke a cikin gidan, ko akwai wani kuma a nan? Idan wannan mutum zai ce, "A'a." Sai ya ce, "Ka yi shuru, don ba za mu ambaci sunan Yahweh ba."
11Duba, Yahweh zai ba da umarni, babban gida buge shi za a yi ya ragargaje, ƙaramin gida kuma ya rushe.
12Dawakai sukan yi gudu a ƙonƙolin duwatsu? ko da wanda zai iya huɗa da shanu a can? Duk da haka ku ka mai da adalci dafi kuma ku ka mai da nagarta mugunta.13Ku da kuke murna akan Lo Dibar, wanda yace, "Ba mu ɗauke Karnaim ta wurin ƙarfinmu ba?"
14Ku duba zan ta da wata al'umma ta yi gãba da ku, gidan Isra'ila -- wannan shi ne furcin Ubangiji Yahweh, Allah mai runduna. Zasu ƙuntata ma ku tun daga Lebo Hamat zuwa kwarin Araba."

7

1Wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh ya nu na mani. Duba, ya sa fari sun yi cincirindo lokacin da aka fara yankan hatsi, duba lokacin girbin baya ne bayan an cire na sarki.2Bayan sun gama cinyen kowanne ɗanyen ganye a ƙasar, sai na ce, "Ubangiji Yahweh, idan ka yarda ka yi gafara, yaya Yakubu zai tsira? Don shi ƙarami ne ainun."3Yahweh kuwa ya dakatar da nufinsa. Ya ce, "Ba zai faru ba."

4Wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh ya nuna mani: Duba, Ubangiji Yahweh ya yi kira akan wuta ta shari'a. An busar da fili mai yawan gaske, ruwa mai zurfi a ƙarƙashin duniya an kuma lalata ƙasa.5Amma na ce, "Ubangiji Yahweh, idan ka yarda ka tsaya; Yaya Yakubu zai tsira? Don shi ƙarami ne."6Yahweh kuwa ya dakatar da wannan. "Wannan ma ba zai faru ba," inji Ubangiji Yahweh.
7Wannan shi ne abin da aka nuna mani: Duba, Ubangiji ya tsaya gefen bango, yana rike da magwaji a hannunsa.8Yahweh yace da ni, "Amos, me ka gani? Sai na ce, "Magwaji." Sai Ubangiji yace, "Duba, zan sa magwaji a wurin mutanena Isra'ila. Ba zan sake barin su ba.
9Wurare masu bisa na Ishaku za a lalace, wuraren sujada na Israila za su zama kufai, kuma zan yi gãba da gidan Yerobowam da takobi."
10Sai Amaziya, firist na Betel, ya aika da saƙo zuwa Yerobowam sarkin Isra'ila: "Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a cikin gidan Isra'ila. Ƙasa ba za ta iya ɗaukan dukkan maganganunsa ba.11Wannan shi ne abin da Amos yace, 'Yerobowam zai mutu ta takobi, kuma babu shakka Isra'ila zai tafi bauta daga ƙasarsa.'"
12Amaziya yace da Amos, "Mai gani, tafi da gudu. koma ƙasar Yahuda, a can za ka nemi gurasa ka ci ka kuma yi annabci.13Amma kada ka ƙara yin annabci a nan Betel don nan wurin yin sujadar sarki ne kuma gidan sarauta ne."
14Sai Amos yace wa Amaziya, "Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi. Ni makiyayi ne, kuma mai lura da itatuwan ɓaure.15Amma Yahweh ya ɗauke ni daga kiwo sai ya ce da ni, 'Tafi, yi annabci ga mutanena Isra'ila.'
16Yanzu ji maganar Yahweh. Ka ce; "Ka da ka yi annabci gãba da Isra'ila, kuma kada ka yi magana gãba da gidan Ishaku.'17Saboda haka ga abin da Yahweh yace, 'Matarka za ta zama karuwa a birni, za a karkashe 'ya'yanka maza da mata da takobi; ƙasarka za a gwada ta a kuma rarraba; kai kanka za ka mutu a cikin ƙasa marar tsarki, kuma babu shakka Isra'ila zai tafi bauta daga ƙasarsa.'"

8

1Wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh ya nuna mani. Duba, ga kwandon itacen ɓaure na kaka!2Ya ce, "Me ka gani, Amos?" Na ce "Kwandon itacen ɓaure na bazara." Sai Yahweh yace da ni, "ƙarshen mutanena Israila ya zo; Ba zan sake barin su ba.3Waƙoƙin haikali za su zama na makoki. A wannan rana -- wannan furcin Ubangiji Yahweh ne -- gawawwaki zasu yawaita, a ko'ina za a jefar dasu waje. Shuru!"

4Ku saurari wannan, ku da ku ke tattake masu bukata ku na fitar da matalautan ƙasar.5Sun ce, yaushe ne sabon wata zai wuce, saboda ko ma sake sayar da amfanin? Yaushe ne Asabar za ta ƙare, ko ma sake sayar da alkama? Za mu rage girman ma'aunin mu kuma ƙara farashi, yayin da muke zalunci da ma'aunin ƙarya.6Wannan zai sa mu sayar da alkama mara kyau, mu saye talakawa da zinariya, kuma masu bukata da takalma."
7Yahweh ya rigaya ya rantse ta wurin fahariyar Yakubu, "Babu shakka ba zan manta da kowanne aikinsu ba.8Shin ƙasar ba za ta girgiza a kan wannan ba, dukkan wanda ke cikinta zai yi baƙinciki? Dukkan ƙasar za ta hau ta sauka kamar Kogin Nilu, kuma za ta juya ta kuma sake dulmiyewa, kamar kogin Masar.
9Za ya zama kuwa a wannan rana - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - zan mai da rana ta faɗi da tsakar rana, zan kuma sa duniya ta duhunta a rana kata.10Zan mai da bukukuwanku makoki kuma waƙoƙinku su zama makoki. Zan sa maku tufafin makoki, in kuma sa kowa ya aske kansa. Zan sa ku yi makoki kamar iyayen da suka rasa ɗan su tilo, kuma ranar mai daci ce har karshen ta.
11Duba, ranaku na zuwa - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - da zan aiko da yunwa a ƙasar, ba yunwa don gurasa ba, ko kishin ruwa, amma domin rashin samun sakon magana daga wurin Yahweh.12Zasu yi ta tangaɗi daga teku zuwa teku; zasu yi gudu daga arewa zuwa gabas suna neman sakon maganar Yahweh, amma ba kuma zasu samu ba.
13A wannan rana kyawawan 'yan'mata da samari zasu faɗi saboda ƙishi.14Waɗanda suka yi rantsuwa da zunubin Samariya suka kuma ce, 'Muddin allahnku na raye, Dan,' 'Muddin hanyar zuwa Biyasheba nanan' -- za su faɗi kuma ba zasu ƙara tashi ba."

9

1Na ga Ubangiji tsaye wajen bagadi, sai yace, "Bugi saman ginshiƙan don harsasan dukka su girgiza. Farfasa su gunduwa-gunduwa akan kowannen su, ni kuma zan kashe su da takobi. Babu ɗaya daga cikinsu da zai tsere.2Ko da za su nutse cikin Lahira, can hannu na zai kamo su. Ko da sun hau sama, zan sauko da su.

3Ko da sun ɓuya a bisa kololuwar Karmel, can ma zan neme su in cafko su. Ko da sun ɓoye daga ganina a karkashin teku, can ma zan bada umarni ga maciji, shi kuma zai sare su.4Ko da sun tafi bauta ta hannun abokan gãbarsu, can ma zan bada umarni ga takobi, takobi kuwa za ya kashe su. Zan sa idanuna a kansu don azaba ba nagarta ba."
5Ubangiji Yahweh mai runduna ya taɓa ƙasa har ta narke, dukkan waɗanda suke cikinta suna baƙinciki; dukkan abin da ke cikinta zasu tashi kamar Kogi, za ta kuma nutse kamar kogin Masar.6Shi ne ya gina matakansa a sammai, ya kafa maɓoyarsa a bisa duniya. Ya kira ruwan teku ya ƙwararo a bisa fuskar duniya, sunansa Yahweh ne.
7"Ku ba kamar mutanen Kush ba ne gare ni, mutanen Isra'ila? - wannan furcin Yahweh ne. Ba na fito da Isra'ila daga ƙasar Masar da Filistiyawa daga Krit da Aramiyawa kuma daga Kir ba?8Duba, idanuwan Ubangiji Yahweh suna kan mulkin nan mai zunubi, kuma zan lalata su daga fuskar duniya, sai dai ba zan hallaka gidan Yakubu kakaf ba -wannan furcin Yahweh ne.
9Duba, zan ba da umarni, zan kuma rairayi gidan Isra'ila a cikin al'ummai, kamar wanda yake tankaɗan hatsi, don kada a rage ko ɗan ƙaramin dutse ya faɗi a ƙasa.10Dukkan masu zunubi daga cikin mutanena za su mutu ta wurin takobi, waɗansu za su ce, 'Masifa ba za ta auko mana ko ta kusan ce mu ba!'
11A wannan rana zan ta da rumfar Dauda wanda ta faɗi, zan toshe kafafe. Zan ta da lalatattun wurarenta, in kuma sake gina ta kamar kwanakin dă.12Ta haka zasu ci nasara ga waɗanda su ka ragu a Idom, da kuma dukkan al'ummai da suke kira da sunana - wannan furcin Yahweh ne - shi ne ya yi wannan.
13Duba, kwanaki na zuwa - wannan furcin Yahweh ne - sa'ad da mai huɗa zai riga mai girbi, mai matse ruwa inabi kuma zai riga mai shuka iri nan da nan. Duwatsu zasu zubo da ruwan inabi mai zaƙi, dukkan tuddai kuma su kwararo da shi.
14Zan dawo da mutanena Isra'ila daga bauta. Za su giggina biranensu da su ka rurrushe su kuma zauna a ciki, zasu dasa gonakin inabi su kuwa sha ruwan inabinsu, za su yi lambuna su kuma ci amfanin 'ya'yansu.15Zan dasa su a ƙasarsu, ba kuwa za a ƙara tumbuke su daga ƙasar da na ba su ba," inji Yahweh Allahnku.

Littafin obadiya

1

1Wahayin Obadiya. Ubangiji Yahweh ya faɗi haka a kan Idom: Mun ji bayani daga wurin Yahweh cewa an aika da jakada a cikin al'ummai, da cewa, "Tashi tsaye! Bari mu tashi mu kai mata hari!"2Ga shi zan mayar dake 'yar ƙarama a cikin al'ummai, za a rena ki ƙwarai.

3Girman kai na zuciyarki ya ruɗe ki, ke da ki ke zaune a can cikin kogunan dutse, cikin ƙayataccen gidanki; a cikin zuciyarki, kin ce, "Wane ne zai saukar da ni can ƙasa?"4Ko da zaki tashi sama kamar gaggafa, ko da zaki kai sheƙarki cikin taurari, zan sauko dake ƙasa, inji Yahweh.
5Idan ɓarayi suka zo wurinki, idan 'yan fashi suka zo wurinki da daddare - dubi yadda za a maishe ki kufai! - ba za su saci abin da suke buƙata ba ne kawai? Idan masu tattara inabi suka zo, ba zasu rage kala ba?6Yadda aka bincike Isuwa, harma da abin da ya ɓoye dukka an bincike!
7Dukkan mazajen da suka ƙulla amana da ke zasu kore ki har kan iyaka, mazajen da suke zaune lafiya da ke sun ruɗe ki, sun ci nasara a kan ki. Waɗanda suka ci abincinki sun ɗana maki tarko. Babu fahimta a cikinsa.8Yahweh yace a waccan rana, "Ba zan ce a hallaka ma su hikima daga cikin Idom ba, da masu ganewa daga cikin dutsen Isuwa ba?"9Jarumawanki zasu karaya, Teman, domin a datse kowanne mutum daga dutsen Isuwa ta wurin yankawa.
10Saboda ta'addancin da aka yi wa ɗan'uwanki Yakubu, kunya za ta rufe ki, za a datse ki har abada.11A ranar da ki ka tsaya a ware ke kaɗai, a ranar da bãƙi suka kwashe dukiyarsa, bãƙi suka shiga ƙofofinsa, suka jefa ƙuri'a a kan Yerusalem, kema ki na kamar su.
12Amma kada ki yi murna a cikin ranar ɗan'uwanki, a ranar da ya yi asara, kuma kada ki yi farinciki a kan mutanen Yahuda a ranar hallakarsu; kada ki yi fahariya a ranar baƙincikinsu.13Kada ki shiga ƙofar mutanena a ranar masifarsu; kada ki yi murna a cikin ƙuncinsu a ranar bala'insu; kada ki washe dukiyarsu a ranar rushewarsu.14Kada ki tsaya a mararrabar hanyoyi, domin ki datse masu neman tsira da miƙa kuɓutattun mutanensa a ranar ƙuncinsu.
15Gama ranar Yahweh ta kusa a kan dukkan al'ummai. Kamar yadda ki ka yi, haka za a yi maki, abin da kika yi zai dawo kanki.16Kamar yadda kika sha a kan dutsena mai tsarki, haka dukkan al'ummai za suyi ta sha. Za su sha su haɗiye su zama kamar basu taɓa kasancewa ba.
17Amma a Dutsen Sihiyona za a sami waɗanda suka tsira, kuma zai zama da tsarki; gidan Yakubu kuma zasu mallaki mallakarsu.18Gidan Yakubu zai zama wuta, gidan Yosef kuma zai zama harshen wuta mai ci, gidan Isuwa kuma zai zama tattaka, za a ƙone su a hallakar da su. Ba wanda zai tsira daga gidan Isuwa, gama Yahweh ya faɗi."
19Waɗanda suke daga Negeb zasu mallaki dutsen Isuwa, na Sefilah kuma za su mallake ƙasar Filistiyawa. Za su mallaki ƙasar Ifraim da ƙasar Samariya; shi kuma Benyamin zai mallaki Giliyad.
20Masu zaman bauta na mutanen Isra'ila masu yawa zasu mallaki ƙasar Kan'ana har zuwa Zerefat. Masu zaman bauta na Yerusalem, waɗanda ke Sefarad zasu mallaki biranen Negeb.21Masu kuɓutarwa za su hau zuwa Dutsen Sihiyona za su yi mulki a ƙasar kan tudu ta Isuwa, mulkin kuma zai zama na Yahweh.

Littafin yona

1

1Maganar Yahweh ta zo ga Yona ɗan Amittai, cewa,2"Ka tashi ka tafi Nineba, babban birnin nan, ka yi magana gãba da shi, saboda muguntarsa ta zo gare ni."3Amma Yona ya tashi ya gudu daga gaban Yahweh ya tafi Tarshish. Ya tafi Yofa ya sami jirgin da zai tafi Tarshish. Ya biya kuɗin tafiya Tarshish. Domin ya gudu daga fuskar Yahweh.

4Amma sai Yahweh ya aika da babbar iska a kan teku wadda ta zama hadari mai ƙarfi ta sa jirgin ya yi ta kaɗawa kamar zai fashe.5Sai masu tuƙin jirgin su ka ji tsoro sosai mutanen suka yi ta addu'a kowanne ga allahnsa. Sai suka zubar da kayan da ke cikin jirgin a cikin teku domin su rage nauyin jirgin. Amma Yona yana can cikin ƙarshen jirgi yana barci mai nauyi.
6Sai mai tuƙin jirgin ya zo ya same shi yace da shi, "Barci ka ke yi? Tashi! Ka kira ga allahnka! Ko allahnka zai ji ya cece mu daga hallaka."7Sai suka ce da junansu, "Ku zo mu jefa ƙuri'a mu gani ko wane ne ya sa muka shiga wannan masifa." Da suka jefa ƙuri'a sai ta faɗa kan Yona.
8Sai suka ce da Yona, "In ka yarda ka gaya mana wane ne ya sa wannan masifa ta same mu. Mene ne aikinka, daga ina ka ke? Daga wacce ƙasa ka ke, kai ɗan wacce kabila ne?"9Yona yace da su, "Ni Ba'ibrane ne; kuma ina jin tsoron Yahweh, Allah na sama, wanda ya halitta sama da teku da busasshiyar ƙasa."10Sai mutanen suka ƙara jin tsoro suka ce da Yona, "Me ka yi kenan?" Sun sani cewa ya gudu ne daga wurin Yahweh, gama ya faɗa masu.
11Sai suka ce da Yona, "Me za mu yi maka domin tekun ya kwanta?" Saboda tekun na ƙara yin hauka.12Sai Yona yace masu, "Ku ɗauke ni ku jefa cikin tekun. Tekun kuwa zai yi shiru domin ku, gama na sani saboda ni ne wannan babban hadari ya same ku."13Amma duk da haka, mutanen suka yi ta ƙoƙari domin su mallako jirgin ya dawo bakin gãɓa, amma suka kasa saboda tekun yana ta ƙara yi masu hauka.
14Sai suka yi kuka ga Yahweh suka ce, "Mun roƙe ka, Yahweh, mun roƙe ka, kada ka bari mu hallaka saboda wannan mutum, ya Yahweh, kada ka ɗora alhakin mutuwarsa a kan mu, saboda kai Yahweh ka yi adalci ka kuma yi kamar yadda ya gamshe ka."15Sai suka ɗauki Yona suka jefa shi cikin teku sai tekun ya daina hauka.16Sai mutanen suka ji tsoron Yahweh ƙwarai da gaske. Suka miƙa hadayu ga Yahweh suka kuma yi alƙawura.
17Yahweh kuwa ya shirya wani babban kifi don ya haɗiye Yona, Yona kuma ya kasance a cikin cikin kifi har yini uku da kwana uku.

2

1Daga can cikin kifi sai Yona ya yi addu'a ga Yahweh Allahnsa.2Ya ce, "Na yi kira ga Yahweh game da ƙuncina ya kuwa amsa mani; daga can cikin Lahira na yi kuka na neman taimako! Ka ji muryata.

3Ka jefa ni can cikin ƙarƙashin ƙasa, cikin zurfin tekuna, rigyawa da ambaliya, raƙuman ruwa sun bi ta kaina.4Na ce, 'An kore ni daga fuskarka; amma duk da haka zan sake duban haikalinka mai tsarki.'
5Ruwaye sun sha kaina har zuwa wuyana; zurfi ya kewaye ni ta ko'ina, rigyawa ta sha kaina.6Na shiga ƙarƙashin duwatsu; duniya da makullanta sun rufe ni har abada. Amma duk da haka ka tsamo raina daga rami, Yahweh, Allahna!
7Lokacin da raina ya sume a cikina, sai na tuna da Yahweh a cikin raina; sai addu'ata ta zo gare ka, a haikalinka mai tsarki.8Waɗanda suka juya ga alloli marasa amfani sukan ƙi amincinka zuwa gare su.
9Amma ni zan miƙa maka hadaya da murya ta godiya, zan cikasa abin da na alƙawarta. Daga wurin Yahweh ceto yake zuwa!"10Sai Yahweh ya yi magana da kifin, sai kifin ya amayar da Yona a gãɓar tekun.

3

1Maganar Yahweh ta zo wurin Yona karo na biyu, cewa,2"Ka tashi, ka tafi Nineba, babban birnin nan, ka yi shelar saƙon da na umarce ka ka bayar."3Sai Yona ya tashi, ya tafi Nineba ya yi biyayya da maganar Yahweh. Nineba dai birni ne babba, kuma tafiya ce ta kwana uku.

4A yini guda Yona ya fara shiga birnin ya yi kira ya ce, "A cikin kwana arba'in za a rushe Nineba."5Mutanen Nineba suka gaskata Allah, suka yi shelar yin azumi. Dukkan su suka sanya tsummokara, daga manyansu har ya zuwa ƙananansu.
6Nan da nan labari ya kai ga sarkin Nineba. Shi kuwa ya tashi daga kursiyinsa, ya tuɓe alkyabbarsa, ya rufe kansa da tsummokara, ya zauna cikin toka.7Sai ya aika ayi shelar cewa, "A cikin Nineba, bisa ga ikon sarki da majalisarsa, kada wani mutum ko dabba, ko garken shanu da tumaki, ko na awaki ya ɗanɗana wani abu. Kada su ci abinci ko su sha ruwa.
8Amma sai mutum da dabba su rufa da tsummokara kuma su yi kuka mai ƙarfi zuwa ga Allah. Sai kowanne mutum ya juya daga hanyarsa ta mugunta da kuma ta'addancin dake cikin hannuwansa.9Wa ya sani? Ko Allah zai iya yin jinkiri kuma ya canza ra'ayinsa ya kuma juya daga fushinsa mai zafi domin kada mu hallaka."
10Allah ya ga abin da suka yi, yadda suka juya daga hanyoyinsu na mugunta. Sai Allah ya canza ra'ayinsa game da hukuncin da ya ce zai zartar a kansu, bai kuma zartar da shi ba.

4

1Amma hakan bai yi wa Yona daɗi ba, sai ya ji haushi ƙwarai.2Saboda haka, Yona ya yi addu'a ga Yahweh ya ce, "Yahweh, ashe ba abin da na ce ba kenan tun ban baro ƙasata ba? Shi ya sa tun da farko na yi ƙoƙarin gudu zuwa Tarshish - domin na san kai Allah ne mai alheri, mai tausayi, mai jinkirin fushi, cike da aminci, ka kan kuma fasa aiko da bala'i.3Saboda haka yanzu, Yahweh, na roƙe ka, ka ɗauke raina daga gare ni, gama ya fiye mani in mutu, da in rayu."

4Yahweh yace, "Ya dace da ka yi fushi haka?"5Sai Yona ya fita daga birnin ya zauna daga gabas da birnin. Can ya yi rumfa ya kuma zauna a ƙarƙashinta domin ya ga abin da zai faru da birnin.
6Yahweh Allah ya shirya wata 'yar itaciya ya sa ta yi girma ta kere Yona, domin ta zama inuwa a saman kansa ta sauƙaƙa ƙuncinsa. Yona kuwa ya yi murna sosai sabo da wannan 'yar itaciyar.7Amma Allah ya shirya tsutsa da gari ya waye rana ta ɗaga. Tsutsar kuwa ta kawo hari ga 'yar itaciyar, ta cinye 'yar itaciyar, 'yar itaciyar kuma ta bushe.
8Kashegari sa'ad da rana ta fito, Allah ya shirya wata iska daga gabas mai zafin gaske. Ranar kuwa, ta yi zafi matuƙa bisa Yona har ya some. Sai Yona ya gwammace ya mutu. Ya ce wa kansa, "Gara ma in mutu da in rayu."9Sai Allah yace wa Yona, "Ya dace da ka yi fushi game da 'yar'itaciyar? Sai Yona yace, "Ya dace da in yi fushi, har ma ga mutuwa."
10Yahweh yace, "Ka ji tausayin 'yar itaciyar, wadda ba ka yi aiki a kai ba, ba ka kuma sa ta yi girma ba. 'Yar Itaciyar ta yi girma cikin dare ɗaya ta kuma mutu cikin dare ɗaya.11To ashe, Ni, ba zan tausayawa Nineba, wannan babban birni, wanda akwai fiye da mutane dubu ɗari da ashirin, da ba su san bambanci tsakanin hannunsu na dama da hannunsu na hagu ba, da kuma dabbobi masu yawan gaske?"

Littafin mika

1

1Wannan ita ce maganar Yahweh wadda ta zo wurin Mika, Bamorashtite a cikin kwanakin Yotam, da Ahaz, da Hezekiya, sarakunan Yahuda, abin da ya gani game da Samariya da Yerusalem.

2Dukkan jama'a ku saurara, ke duniya ki saurara da dukan abin dake cikinki. Bari Ubangiji Yahweh ya zama shaida a kan ki daga haikalinsa mai tsarki.3Duba, Yahweh ya sauko daga kursiyinsa, zai bi ta wurare masu tudu a bisa ƙasa.4Duwatsu zasu narke a ƙarƙashinsa, kwarurruka kuma zasu farfashe kamar saƙar zuma a gaban wuta, kamar an zubar da ruwa a kan wuri mai tsauri.
5Dukkan wannan saboda tawayen Yakubu ne, kuma saboda zunubin gidan Isra'ila ne. Mene ne dalilin tawayen Yakubu? Ba Samariya ba ce? Mene ne dalilin wurare masu tsawo na Yahuda? Ba Yerusalem ba ce?
6"Zan maida Yahuda ta zama kamar kufai kawai kamar wurin dasa itatuwan inabi. Zan tura gininta na duwatsu cikin rami, zan kware harsasanta.7Za a farfasa sifofinta, dukkan kyaututtukanta za a ƙone su. Dukkan gumakanta zan rushe su. Gama daga wurin karuwancinta ta tattara su, zasu zama kamar abin da aka biya ta saboda karuwanci."
8Domin wannan zan yi makoki in yi kuka, zan fita tsirara ba takalma; zan yi kuka kamar dila, zan yi makoki kamar mujiya.9Domin rauninta marar warkewa, domin ta zo Yahuda. Ta kawo ƙofar mutanena, wato Yerusalem.10Kada a yi maganar ta a Gat; kada a yi mata kuka. A Bet Lefra na yi birgima a ƙura.
11Ki wuce ta mazaunan Shafir, a tsiraice cikin kunya. Mazauna Za'ana basu fito waje ba. Bet Ezel tana makoki saboda an ɗauke kariyarta.12Mutanen Marot suna da marmarin jin labari mai daɗi, saboda masifa daga Yahweh ta zo har ƙofofin Yerusalem.
13Ku mutanen Lakish ku haɗa karusai na dawaki. Ke, Lakish, ke ce kika zama sanadin zunubin ɗiyar Sihiyona, saboda an sami kurakuran Isra'ila a cikinki.14To za ki bada kyauta ta ban kwana ga Morashet Gat; garin Akzib zai ba sarakunan Isra'ila kunya.
15Zan sake kawo wanda zai mamaye ku, ku mazaunan Maresha, martabar Isra'ila zata dawo Adullam.16Ki aske kanki ki share gashinki saboda 'ya'yan da ki ke jin daɗin su. Ki sa kanki ya yi saiƙo kamar na gaggafa, domin 'ya'yanki za su tafi bauta daga wurinki.

2

1Kaiton masu shirya mugunta, ga waɗanda ke shirya mugunta a kan gadajensu. Idan gari ya waye sukan aikata ta domin suna da iko.2Sukan yi sha'awar gonaki su kuma ƙwace su; sukan yi sha'awar gidaje su kuma ƙwace su. Suna tsanantawa mutum da gidansa, da kuma abin gãdonsa.

3Saboda haka Yahweh yace, "Duba, na kusa kawo bala'i ga wannan kabila, wadda ba zaku cire kanku daga ciki ba. Ba zaku yi tafiya da taƙama ba, gama zaya zama mugun lokaci.4A wannan rana abokan gãbarku zasu rera waƙa game da ku, zasu yi makoki da makoki mai zafi. Zasu yi waƙa, 'Mu Isra'ilawa mun hallaka sarai, Yahweh ya canza gundumar mutanena.' Ya ya zaya ɗauke shi daga wurina? Ya bayar da filayanmu ga maciya amana!"'5Saboda haka, ku masu arziki baza ku sami zuriyar da za a raba gundumominku a cikin taruwar mutanen Yahweh ba.
6"Sun ce, "kada ka yi anabci." "Ba zasu yi anabcin waɗannan abubuwa ba; reni ba zaya zo ba."7Ko lallai za a iya faɗin gidan Yakubu, "Ko Ruhun Yahweh ya ji haushi ne?" Ko waɗannan su ne ainihin ayyukansa?" Ko kalmomina ba su yi wani aikin kirki ga kowa ba ne?8A makare mutanena suka tashi kamar abokan gãba. Kun tuɓe sutura, da riga, daga masu wucewa ba tare da tsarguwa ba, kamar sojoji suna dawowa daga yaƙi zuwa wurin da suke tsammani lafiyayye ne.
9Kun kori matan mutanena daga gidajen da suke jin daɗi, kun ɗauke albarkuna daga wurin 'ya'yansu har abada.10Tashi ka tafi, nan ba wurin da za ka iya zama ba ne, saboda rashin tsafta; hallakakke ne sarai.11Idan wani ya zo da ruhun ƙarya ya yi ƙarya ya ce, "Zan yi maka anabci a kan ruwan inabi da abin sa maye," zasu ɗauke shi annabi domin wannan jama'a.
12Tabbas, zan tattara dukkan ku, Yakubu. Tabbas zan tattara sauran mutanen Isra'ila. Zan kawo su kamar garken tumaki a cikin tsakiyar wurin kiwonsu. Saboda yawan mutanen za a ji ƙara mai ƙarfi.13Wanda ya fara ɓalle ƙofa shi ne zai yi masu jagora. Sun ɓalle ƙofa sun fita; sarkinsu zai wuce gabansu. Yahweh zai kasance a gabansu.

3

1Na ce, "Yanzu ku saurara, ku shugabannin Yakubu da masu mulki na gidan Isra'ila: Ashe ba dai-dai ba ne a gare ku ku fahimci adalci?2Ku da ke ƙin nagarta kuke kuma ƙaunar mugunta? Ku da ke yayyage fatarsu, da namansu daga ƙasusuwansu --3ku da ke cin naman mutanena, kun yage fatarsu, kun kakkarya ƙashinsu, kun daddatsa su gunduwa-gunduwa kamar naman da za a sa a tukunya, kamar nama domin dafawa.

4Sa'an nan ku shugabanni zaku yi kuka ga Yahweh, shi kuwa ba zai amsa maku ba. Zai ɓoye fuskarsa daga gare ku, da yake kun yi aikin mugunta.
5Yahweh ya faɗi haka, "Game da annanbawan da suke ɓatar da mutanena, idan wani ya basu wani abu su ci, sukan yi shelar 'Salama'. Amma ga waɗanda ba su sa komi a bakinsu ba, sai su fara yaƙi da su.6Saboda haka zai zama duhu a gare ku, babu ruya domin ku, zai zama duhu sosai har da ba zaku yi duba ba. Rana za ta faɗi a kan annabawa, yini zai yi masu duhu.7Masu duba zasu ji kunya, masu sihiri zasu rikice. Dukansu zasu rufe leɓunansu, domin babu amsa daga gare ni."
8Amma ni ina cike da iko ta wurin Ruhun Yahweh, kuma ina cike da adalci da ƙarfi, don in furtawa Yakubu kuskurensa, Isra'ila kuma zunubinsa.
9Yanzu ku ji wannan, ku shugabanni na gidan Yakubu, da masu mulki na gidan Isra'ila, ku da ke ƙyamar adalci, kuna wulaƙanta kowanne abu mai kyau.10Kun gina Sihiyona da jini, Yerusalem kuma da mugunta.11Shugabanninku suna hukunci da cin hanci, firistocinku suna koyarwa don a biya su, kuma annabawanku suna dubã saboda kuɗi. Duk da haka kun dogara ga Yahweh kun ce, "Ba Yahweh yana tare da mu ba? Ba masifa da za ta same mu."
12Domin haka, saboda ku za a huɗe Sihiyona kamar gona, Yerusalem za ta zama juji, tudun haikali zai zama tsaunin daji.

4

1Amma zaya zama a rana ta ƙarshe dutsen gidan Yahweh zaya kafu a bisa sauran duwatsu. Zai ɗaukaka bisa sauran tuddai mutane kuma za su yi tururuwa wurinsa.

2Al'ummai da yawa zasu ce, "Ku zo, mu je bisa dutsen Yahweh, zuwa gidan Allah na Yakubu. Zaya koya mana hanyoyinsa, kuma zamu yi tafiya cikin tafarkunsa." Gama daga Sihiyona shari'a zata fito, maganar Yahweh kuma daga Yerusalem.3Shi zaya hukunta tsakanin mutane da yawa, ya kuma yanke hukunci a kan mulkoki masu yawan gaske masu nisa kuma. Zasu maida takubbansu su zama garmuna mãsun su kuma su zama lauzuna. Wata al'umma baza ta ɗaga takobi gãba da wata al'umma ba, baza su ƙara koyar da yaƙi ba.
4Maimakon haka kowanne mutum zai zauna ƙarƙashin kuringar inabinsa ko ƙarƙashin itacen ɓauransa. Ba wanda zai ƙara basu tsoro, gama bakin Yahweh mai runduna ne ya faɗi.5Gama dukkan mutane suna tafiya, kowanne ɗaya cikin sunan allahnsu. Amma mu zamu yi tafiya cikin sunan Yahweh Allahnmu har abada abadin
6"A waccan ranar" - wannan furcin Yahweh ne - "Zan tattaro guragu da korarru, da waɗanda na tsanantawa.7Zan sa guragun su zama su ne saura, waɗanda a ka kora su zama al'umma mai ƙarfi, ni kuma Yahweh zan yi mulki a bisansu, a kan Dutsen Sihiyona daga yanzu da har abada.8Ke fa, hasumiya ta tsaron garke, tsaunin ɗiyar Sihiyona, mallakarki ta dã za ta dawo gare ki, da mulki na ɗiyar Yerusalem.
9Yanzu, me yasa kuke ihu da ƙarfi haka? Babu sarki a cikinku ne? Mai shawararku ya mutu ne? Wannan shi ne yasa ciwo ya kama ku kamar mace mai naƙuda?10Ki zama da ciwo da naƙuda ta haifuwa, ke ɗiyar Sihiyona, kamar mace mai naƙuda. Gama yanzu ke zaki fita waje daga birnin, ki zauna a waje, kuma ki tafi Babila. A can za a kuɓutar da ke. A can Yahweh zaya kuɓutar da ke daga hannun abokan gãbarki.
11Yanzu al'ummai da yawa sun taru gãba da ke; sun ce, 'Bari ta ƙazance; bari idanunmu su yi murna a kan Sihiyona'12Basu san tunanin Yahweh ba, basu gane shirye-shiryansa ba, gama ya tara su kamar dammai a masussuka.
13Tashi ki yi shiƙa ɗiyar Sihiyona, gama zan maida ƙahonki ya zama ƙarfe, kofatanki kuma su zama jan ƙarfe. Zaku hallaka mutane da yawa kuma zaku miƙa dukiyarsu ta zilama ta zama ta Yahweh, mallakarsu kuma ga Ubangijin dukan duniya."

5

1Yanzu ku taru da shirin yaƙi, ɗiyan sojoji; sojoji sun yi sansani sun kewaye birni, zasu bugi alƙalin Isra'ila da sanda a kunci.

2Amma ke Betlehem Ba'ifrata, ko da yake ke ƙanƙanuwa ce a cikin dangi Yahuda, wani daga cikinki zaya zo gare ni ya yi mulkin Isra'ila, wanda farkonsa tun daga lokacin dã ne, tun daga can farko.3Saboda haka zaya bashe su, har sai wadda ta ke naƙuda ta haifi ɗa, kuma sauran 'yan'uwansa su dawo wurin mutanen Isra'ila.
4Zaya tashi ya yi kiwon mutanensa cikin ƙarfin Yahweh, a cikin darajar sunan Yahweh Allahnsa. Zasu kasance, sa'annan shi zaya zama babba har iyakar duniya.5Zaya zama salamarmu. Sa'ad da Asiriyawa suka shigo cikin ƙasarmu, sa'ad da suka yi gangami gãba da kagarunmu, sa'an nan zamu tashi gãba da su, makiyaya bakwai da shugabanni takwas a kan mutane.
6Zasu kiwaci ƙasar Asiriya da takobi, ƙasar Nimrod kuma a cikin ƙofofinta. Zaya kuɓutar da mu daga Asiriyawa, sa'ad da suka shiga cikin ƙasarmu, sa'ad da suka yi gangami cikin iyakokinmu.7Waɗanda suka rage na wajen Yakubu zasu zama cikin tsakiyar mutane da yawa, kamar raɓa daga wurin Yahweh, kamar ruwa a kan ciyawa, wadda ba mutum take jira ba, ba kuma 'ya'yan mutane take jira ba.
8Waɗanda suka rage na wajen Yakubu zasu zama a cikin al'ummai, cikin mutane da yawa, kamar zãki a cikin namomin jeji masu yawa, kamar ɗan zaki a cikin garken tumaki. Sa'ad da ya shiga cikinsu zai tattaka su, ya daddatsa su, ba wanda zaya cece su.9Za a ɗaga hannunka gãba da abokan gãbarka, zaya kuma hallaka su.
10"Haka zaya kasance a wannan rana" - wannan furcin Yahweh ne -- "zan hallakar da dawakanka a gabanka in narkar da karusanka.11Zan hallakar da biranen ƙasarka in lalatar da wuraren ɓoyewarka dukka.
12Zan hallakar da maita da ke wurinka, baza ka ƙara samun masu duba ba.13Zan hallakar da sassaƙaƙƙun sifofinka da ginshiƙai na duwatsu daga wurinka. Baza ka ƙara bautawa aikin hannuwanka ba.14Zan tumɓuke ginshiƙan Asherarka daga wurinka, kuma in hallakar da biranenka.15Zan ɗauki fansa cikin fushi da hasala a kan al'umman da basu saurara ba."

6

1Yanzu ji abin da Yahweh ya faɗi, "Ka tashi ka kai ƙararka ga duwatsu; bari tsaunuka su ji muryarka.2Ku ji ƙarar Yahweh, ku duwatsu, da ku ginshiƙan duniya masu juriya. Gama Yahweh yana da shari'a da mutanensa, zai yi faɗa da Isra'ila a kotu."

3Mutanena, me na yi ma ku? Ta yaya na gajiyar da ku? Ku faɗi laifin da na yi!4Gama na fito da ku daga ƙasar Masar na kuɓutar da ku daga gidan bauta. Na aiki Musa da Haruna da Miriyam zuwa wurinku.5Mutanena, ku tuna abin da Balak sarkin Mowab ya ƙulla, da yadda Bala'am ɗan Biyo ya amsa masa sa'ad da kuke tafiya daga Shittim zuwa Gilgal, ta haka za ku san aikin adalci na Yahweh."
6Me zan kawo gaban Yahweh, sa'ad da na durƙusa gaban Allah mai girma? Na zo da hadayu na ƙonawa, da ɗan maraƙi bana ɗaya?7Yahweh zai yi murna da dubban raguna, ko da dubban rafukan mai? Zan ba da ɗan farina saboda laifina, ɗiyan jikina domin zunubina?8Ya dai gaya maka, mutum, abin da ke mai kyau, abin da Yahweh ke nema daga wurinka: Aikin adalci, jinƙai da tafiya cikin tawali'u tare da Allahnka.
9Yahweh, yana yin furci da muryarsa zuwa ga birnin - ko yanzu hikima ta san sunanka: "Ku saurari sandar, da wanda ya ajiye ta a wurin.10Akwai dukiya a gidajen masu mugunta wannan rashin aminci ne, mudun ƙarya abin ƙyama.
11Ko zan lura da mutumin daya yi amfani da ma'auni mara kyau, da bahu wanda nauyinsa na cuta ne?12Masu arziki sun zama cike da ta'addanci, mazaunan sun faɗi ƙarairayi, kuma harshensu da bakinsu na cike da ruɗi.
13Saboda haka na buge ku da ciwo mai zafi, na mai da ku kango saboda zunubanku.14Za ku ci ba za ku ƙoshi ba, yunwarku za ta zauna a cikinku, za ku ajiye kayayyaki amma ba za ku adana su ba, abin da kuka adana zan bayar ga takobi.15Za ku yi shuka amma ba za ku yi girbi ba; za ku sawo zaitun amma ba za ku shafe kanku da mai ba; za ku matse kuringar inabi amma ba za ku sha ruwan ba.
16Farillan da Omri ya bayar an kiyaye su, haka kuma dukkan abin da gidan Ahab suka yi. Kun yi tafiya bisa ga shawararsu. To haka zan mai da birnin kango, mazauna ciki kuma abin ƙi, ku mazaunan za ku yi ta fama da ba'a a matsayinku na mutanena."

7

1Kaito na! Gama a gare ni ya zama kamar an riga an gama girbi na kaka, har ma da kalar abin da ya rage na kuringar inabi a gonaki: Ba sauran 'ya'yan itatuwan da za a samu, babu nunar fari na 'ya'yan ɓaure waɗanda rai na ke so.2Babu sauran amintattun mutane a ƙasar, babu sauran na kirki a cikin dukkan 'yan adam. Dukkan su sun yi kwanto domin su zãbar da jini, kowanne ɗayansu yana farautar ɗan'uwansa da tãru.

3Hannayensu sun iya yin ɓarna sosai: sarki yana nema a ba shi kuɗi, alƙali yana shirye ya karɓi cin hanci, ƙaƙƙarfan mutum yana gaya wa waɗansu abin da yake so ya samu. Haka suke rigima tare.4Mafi kyau a cikinsu kamar laka yake, mafi aminci a cikinsu yana kamar shingen ƙaya. Dãma masu tsaronmu sun yi magana a kan wannan rana, ranar da za a hore ku. Ranar ruɗewarsu ta zo.
5Kada ka amince da kowanne maƙwabci, kada ka dogara ga kowanne aboki. Ka yi hankali da abin da za ka faɗi ko ma ga matar da ke kwance a kafaɗunka.6Gama ɗa yana rena ubansa, ɗiya kuma tana tayarwa uwatta, suruka tana tayarwa uwar mijinta. Abokan gabar mutum, mutanen gidansa ne.
7Amma ni zan duba wajen Yahweh, zan jira ga Allah na cetona, Allahna zai ji ni.8Kada ka yi murna a kaina kai maƙiyina, ko na faɗi zan tashi. Sa'ad da na zauna cikin duhu, Yahweh zai zama haske a gare ni.
9Saboda na yi wa Yahweh zunubi, zan jure da fushinsa har yayi mani shari'a, yayi mani hukunci. Zai kawo ni cikin haske, zan gan shi yana kuɓutar da ni cikin adalcinsa.
10Sa'an nan maƙiyina zai gani, kunya za ta rufe wanda yake ce da ni, "Ina Yahweh Allahnka?" Idanuna zasu gan ta, za a tattake ta kamar taɓo a kan hanyoyi.
11Ranar da za ka gina ganuwarka tana zuwa; a ranar nan za a faɗaɗa iyakokinka da nisa ƙwarai.12A ranar nan mutanenka zasu zo wurinka daga Asiriya da biranen Masar, daga Masar har zuwa babban Kogi, daga teku zuwa teku, daga dutse zuwa dutse.13Waɗancan ƙasashen za a watsar da su saboda mutanen da ke zaune, a wurin yanzu, saboda sakamakon ayyukansu.
14Ka yi kiwon mutanenka da sandarka, garke abin gãdonka. Suna zaune su kaɗai a jeji, a tsakiyar fadama. Bari su yi kiwo a Bashan da Giliyad kamar kwanakin dã.15Kamar rana da ka fito daga kasar Masar, zan basu mamaki.
16Al'ummai zasu gani su ji kunya a kan dukkan ikonsu. Zasu sa hannuwansu a bakinsu, kunnuwansu zasu toshe.17Zasu lashi ƙasa kamar macizai, kamar hallittun dake rarrafe a ƙasa. Zasu fito daga cikin kogunansu da tsoro, zasu zo wurinka da tsoro, Yahweh Allahnmu, kuma za su ji tsoro saboda kai.
18Wane ne Allah kamar ka, kai da kake ɗauke zunubi, wanda yake ƙetare kurakuran mutanensa da suka rage, abin gãdonsa? Ba ka riƙe fushinka har abada, saboda kana ƙaunar ka nuna mana amincin alƙawarinka.
19Za ka sake jin tausayinmu, kuma; za ka take muguntarmu a ƙarƙashin sawayenka. Za ka jefa dukkan zunubanmu cikin zurfin teku.20Za ka bada gaskiya ga Yakubu alƙawari da aminci kuma ga Ibrahim, kamar yadda ka rantsewa kakanninmu tun kwanakin dã.

Littafin nahum

1

1Furci game da Nineba. Littafin wahayin Nahum, mutumin Elkosh.

2Yahweh Allah Mai kishi ne da sakayya; Yahweh mai sakayya ne da fushi mai zafi; Yahweh na ɗaukar fansa a kan abokan gãbarsa, kuma yana ci gaba da fushinsa a bisa maƙiyansa.3Yahweh na da jinkirin fushi da iko mai girma; ba zai ƙyale miyagu ba hukunci ba. Yahweh na shirya hanyarsa a cikin guguwa da hadari, gizagizai kuma ya maishe su ƙurar tafin sawayensa.
4Yana tsauta wa teku ya kuma busar da ita; ya busar da dukkan koguna. Bashan ta yi rauni, haka kuma Karmel; furannin Lebanon sun yi yaushi.5Duwatsu suna girgiza a gabansa, tuddai kuma suna na narkewa; duniya tana rushewa a gabansa, hakika, dukkan duniya da mazaunanta.
6Wane ne zai iya tsayawa a gaban hasalarsa? Wane ne zai iya tsayayya da zafin fushinsa? Hasalarsa na zubowa kamar wuta, kuma yana farfasa duwatsu.
7Yahweh nagari ne, mafaka ne mai ƙarfi a ranar masifa; mai aminci ne kuma ga dukkan masu fakewa a cikinsa.8Amma zai hallakar da maƙiyansa kakaf da babbar ambaliya; zai kora su can cikin duhu.
9Ku mutane mene ne ku ke shiryawa gãba da Yahweh? Zai kawo ƙarshensa dukka; Masifa ba za ta sake tasowa karo na biyu ba.10Gama zasu zama a harɗe kamar sarƙaƙiya; abin shansu zai gundure su; wuta zata cinye su sarai kamar busasshiyar ciyawa.11Wani ya tashi daga cikin ki, Nineba, wanda ya yi shirin mugunta game da Yahweh, wani wanda ya haɓaka aikin mugunta.
12Ga abin da Yahweh ya faɗi, "Ko da suna cike da ƙarfinsu da kuma yawansu, duk da haka za a datse su; jama'arsu za su ƙare sarai. Amma kai, Yahuda; ko da ya ke na wahalshe ka, ba zan ƙara wahalsheka ba.13Yanzu zan karya karkiyar mutanen nan daga gare ka; Zan tsinke sarƙoƙinka."
14Nineba, Yahweh ya ba da umarni game da ke; "Babu wata sauran zuriyar da za a kira ta da sunanki. Zan datse sassaƙaƙƙun gumaka da kuma gumakan ƙarfe daga gidajen allolinki. Zan haƙa kaburburanki, gama ke abin raini ce."
15Duba, a bisa duwatsu, akwai sawayen wani mai kawo labarai masu daɗi, wanda ya ke shelar salama! Yahuda, yi murnar bukukuwanka, ka kuma cika wa'adodinka, gama mugu ba zai ƙara mamaye ka ba, don an datse shi sarai.

2

1Shi wanda zai daddatsa ku yana zuwa gãba da ku. Ku tsare ganuwar birnin, ku yi tsaron hanyoyi. Ku ƙarfafa kan ku, ku shirya sojojinku.2Don Yahweh zai dawo da darajar Yakubu, kamar darajar Isra'ila, ko da ya ke maharan sun washe su sun kuma ɓaɓɓata rassan kuringar inabinsu.

3Garkuwoyin jarumawansa jajaye ne, kuma sojojinsa sun sa jajayen tufafi, ƙarafan karusansu na walƙiya tun ranar da a ka shirya su, kuma suna karkaɗa mãsunsu masu ƙotar katako a iska4Karusai na ta yin gudu a tituna suna kai wa suna kawowa a manyan tituna. Suna kama da harsunan wuta, kuma suna gudu kamar walƙiya.
5Wanda zai daddatsa ku gutsu-gutsu ya kira jarumawansa, cikin tafiyarsu suna cin karo da juna, su na sauri don su kawo hari a kan ganuwar birnin. An shirya babbar garkuwa don ta kare masu kawo hari.
6An buɗe ƙofofin bakin koguna ta ƙarfi da yaji, fadar kuma ta zama kufai.7An tuɓe wa Huzzab tufafinta an kuma tafi da ita; bayinta mata suna makoki kamar kurciyoyi, suna bugun ƙirjinsu.
8Nineba ta zama kamar tafki mai maguda, tare da mutanenta suna gudu kamar ruwa mai kwarara. Waɗansu na ihu "ku tsaya, ku tsaya", amma ba wanda ya waiga baya.9Ku ɗauki ganimar azurfa, ƙu ɗauki ganimar zinariya don bata da iyaka, kan dukkan abubuwa kyawawa masu daraja na Nineba.10Nineba ta zama kango da kufai. Zuciyar kowa ta karaya, gwiwoyin kowa na gugar juna, kowa na cikin baƙinciki; fuskokinsu sun yanƙwane.
11Yanzu kuma ina kógon zakokin, inda ake ciyar da 'ya'yan zăki, wurin da zãki da zãkanya ke tafiya da 'ya'yansu ba su tsoron komai?12Zãki ya yayyaga abin da ya kama don 'ya'yansa, ya murɗe abin da ya kamo wa zãkanyarsa, ya cika kógonsa da waɗanda ya kamo, ya cika raminsa da yagaggen mushen waɗanda ya yayyaga.
13"Duba, ina gãba da ku - wannan furcin Yahweh mai runduna ne. Zan ƙone karusanku, a cikin hayaƙi, takobi kuma zai cinye ƙananan zakunanku. Zan datse ganima daga ƙasarku, kuma ba za a ƙara jin muryoyin masu kawo saƙonku ba."

3

1Kaiton birni wanda ke cike da jini! Wanda ke cike da ƙarairayi da kayan sata; a kullum waɗanda aka ƙwara suna cikinsa.2Ƙarar bulala na cikinsa, da ƙarar karusan yaƙi da haniniyar dawakai da sukuwar karusai.

3Akwai mahayan dawakai masu kawo hari, da walƙiyar takubba da ƙyallin mãsu da tarin gawaye da tsibin jukkuna. Gawarwaki ba su da iyaka; maharan sun yi tuntuɓe a kan su.4Wannan na faruwa ne saboda mummunar sha'awa ta ayyuka kyakkyawar karuwar, ƙwararriya a maita, mai sayar da al'ummai ta wurin karuwancinta, ta wurin ta kuma mutane na aikata maitanci.
5"Duba, ina gãba da ke - wannan furcin Yahweh mai runduna ne - Zan kware zanen ki in sa ki zama tsirara a gaban al'ummai, ki zama abin kunya ga masarautu.6Zan kawo ƙazanta a kan ki, in sa ki zama abin reni; zan mayar dake abin kallo.7Zai zama dukkan wanda ya dube ki zai koma da baya, ya ce 'Nineba ta rushe; wa zai yi kuka domin ta?' Ina zan sami wanda zai yi maki ta'aziya?"
8Nineba, kin fi Tebes ne wadda aka gina ta kusa da Kogin Nilu, wadda ruwaye ke kewaye da ita, wadda kariyarta teku ne, wadda teku ta yi mata dajiya?9Kush da Masar ne ƙarfinta, kuma ba shi da iyaka; Fut da Libiya suka yi amana da ita.
10Duk da haka an kwashe Tebes, ta tafi bauta; an fyaɗa 'ya'yanta a ƙasa a kan hanyoyi, abokan gabarta sun jefa ƙuru'u a kan manyan mutanenta, kuma an ɗaure ƙarfafan mutanenta da sarƙoƙi.11Ke ma za ki bugu, za ki yi ƙoƙarin ɓoyewa ki nemi mafaka daga abokan gãbarki.
12Dukkan hasumiyoyinki zasu zama kamar itacen ɓauren da yake da 'ya'yan fari: idan an girjiza su, zasu faɗo a bakin mai cinyewa.13Duba, mutanen dake tare dake mata ne; ƙofofinki suna bude ga abokan gãbarki; wuta ta cinye makaranki.
14Ki je ki ɗebo ruwa domin za a kewaye ki, ki ƙarawa kagarorinki ƙarfi, ki je wurin magina ki samo yunɓu ki yi tubula.15Wuta zata same ki a wurin, takobi zai hallaka ki. Zai cinye ki kamar yadda fãra ta kan cinye komi da komi. Ki maida kanki kamar 'ya'yan fãra, ki yi yawa kamar fãrin da suka yi ƙwari sosai.
16Kin riɓanya abokan cinikayyarki da yawa kamar taurarin sammai; amma suna kamar 'ya'yan fãri sukan washe ƙasa su tashi.17'Ya'yan sarakunanki suna da yawa kamar fãrin da suka yi girma sosai, jarumawanki kuma na kamar fãrin da suka yi cincirindo a bango lokacin sanyi. Amma idan rana ta yi sai su tashi su tafi wurin da ba'a sani ba.
18Sarkin Asiriya, masu tsaronka sun yi barci; masu mulkinka sun kwanta suna hutawa. Mutanenka sun warwatsu a kan duwatsu ba wanda za ya tattarosu.19Raunukanka ba zasu warke ba. Raunukanka sun yi zafi sosai. Dukkan wanda ya ji labarinka zai tafa hannu domin murna a kanka. Wane ne ya tserewa muguntarka ta ko yaushe?

Littafin habakuk

1

1Saƙon da annabi Habakuk ya karɓa,2"Yahweh, har yaushe zan yi kukan neman taimako, ba za ka ji ni ba? Na yi kuka gareka cikin 'husuma'! amma ba za ka cece ni ba.

3Donme kake bari na in kalli mugunta, in kuma dubi rashin gaskiya? Hallaka da tashin hankali na gabana; akwai jayayya, kuma gardama ta taso.4Saboda haka shari'a ta yi rauni, adalci kuma bai ɗore ba ko da na ɗan lokaci. Domin muguye sun kewaye masu adalci; shi yasa shari'a ta karkace." Yahweh ya amsa wa Habakuk.
5Ka dubi al'ummai ka bincike su; ka yi mamaki da al'ajibi! Domin lallai na kusa in yi wani abu a kwanakin ka da ba za ka gaskata ba idan an faɗa maka.6Ka duba! Na kusa ta da Kaldiyawa - waɗannan al'ummai - masu zafin rai da kuma garaje - zasu ratsa dukkan faɗin ƙasar, su ƙwace wurare da ba nasu ba.7Masu ban razana ne da kuma ban tsoro; hukunci da darajassu daga gare su suke fitowa.
8Dawakansu sun fi damisa gudu, sun fi kyarketan maraice sauri. Dawakan su su na tattakawa, mahayansu sun zo daga nesa sosai - Su kan tashi kamar gaggafar da ke niyyar ci.9Duk sun zo domin husuma; rundunarsu sukan tafi kamar iskar hamada, sukan tara bayi kamar yashi.
10Suna yi wa sarakuna ba'a, masu mulki kuma abin ba'a ne a gare su. Suna ma duk kagara dariya, domin sukan tula ƙasa su hau su washe su.11Sa'an nan iska za ta buga mugayen mutane ta wuce da sauri, waɗanda ƙarfinsu allahnsu ne." Habakuk ya sake tambayar Yahweh
12"Kai ba tun fil'azal ka ke ba, Yahweh Allahna, Mai Tsarkin nan? Ba za mu mutu ba. Yahweh ya ƙaddara su ga hukunci, kai kuma, Dutse, ka kafa su domin gyara.
13Idanuwanka masu tsarki ne ba za su duba mugunta ba, ba za ka kuma dubi mugun aiki da tagomashi ba; to don me kake duban masu cin amana da tagomashi? Don me ka yi shuru sa'ad da mugaye suke haɗiye waɗanda suka fi su adalci?14Ka maida mutane kamar kifi a teku, kamar abubuwa masu rarrafe da basu da shugaba.
15Ya kan kawo su dukka da ƙugiyar kamun kifi; yakan ja mutane a tarun kifi su tara su a tãrunsu. Wannan ne ya sa suke murna suna sowa mai yawa.16Shi ya sa suke miƙa hadayu ga tarun kama kifinsu suna ƙona wa tarunsu turare, domin dabbobi masu ƙiba ne rabonsu, nama mai kitse ne abincinsu.17Saboda wannan ne zasu juye tarun kama kifinsu su ci gaba da yanka al'ummai, ba jin tausayi?"

2

1Zan tsaya wurin tsarona in kuma tsaya kan hasumiya, in duba da kyau in ji abin da dai zai faɗi mani da yadda zan amsa masa game da ƙarata.

2Yahweh ya amsa mani ya ce, "Ka rubuta wannan ruyar, ka rubuta ta da kyau a kan alluna domin duk wanda ke karanta su ya gudu.3Domin ruyar lokacinta ya na gaba a ƙarshe lallai za ta cika ba zata fasa ba. Ko da ta yi jinkiri, ku jira. Tabbas zata zo ba za ta yi jinkiri ba.
4Duba! Shi wanda sha'awace sha'awacensa ba dai-dai suke a cikinsa ba hurarra ne. Amma adali ta wurin bangaskiyarsa zai rayu.5Gama ruwan inabi abin yaudara ne ga mutum mai fahariya domin kada ya kiyaye, amma ya yawaita marmarinsa, kamar kabari, kuma kamar mutuwa, ba ya ƙoshi. Ya kuma tattara wa kansa kowacce ƙasa ya kuma tattaro wa kansa dukkan mutane.
6Ashe ko waɗannan ba zasu sa a ƙirƙiro masa maganganun reni da waƙa da zanbo suna cewa, 'Kaiton wanda yake ƙarawa kansa abin da ba nasa ba! Har yaushe zaka yi ta ƙara wa kanka nauyin al'ƙawuran da ka ɗauka?'7Masu cizonka ba zasu tashi farad ɗaya ba, su da ke tsoratar da kai sun farka? Za ka zama ganima a gare su.8Saboda ka washe mutane da yawa, dukkan sauran al'ummai za su washe ka. Saboda ka zubar da jinin mutane tare da tashin hankali a ƙasa, da birane da duk waɗanda ke zaune a cikinsu.
9'Kaitonsa mai cin ƙazamar riba domin gidansa, yakan gina sheƙarsa a sama domin ya tsare kansa daga hanun mugunta.'10Ka jawo wa gidanka kunya ta wurin dạtse mutane da yawa, ka kuma yi wa kanka zunubi.11Gama daga cikin katanga duwatsu zasu tada murya, katako kuma daga cikin itatuwan jinka zai amsa masu,
12'Kaiton wanda ya gina birni da jini, da wanda ya kafa gari da mugunta.'13Ashe ba daga Yahweh mai runduna ba ne mutane ke wahala domin su sami wuta, sauran ƙasashe kuma suna gajiyar da kansu domin abin wofi?14Har yanzu ƙasar zata cika da sanin darajar ɗaukakar Yahweh, kamar yadda ruwaye ke rufe teku.
15'Kaiton wanda ke tilasta maƙwabcinsa ya sha, ka na nuna fushinka, kana kuwa sa su bugu, domin ka dubi tsiraicinsu.'16Maimakon ɗaukaka za ka cika da kunya. Yanzu lokacinka ne! Kai ma ka sha zaka kuma bayyana tsiraicinka. Ƙoƙon hannun dama na Yahweh zai juyo gare ka, kunya kuma zata rufe darajarka.
17Tashin hankalin da aka yi wa Lebanon zai komo maka, hallakar dabbobi kuma zata tsoratar da kai. Domin ka zubar da jinin mutane, ka aikata tashin hankali gãba da ƙasa, da birane, da waɗanda ke zaune a cikinsu.
18Ina amfanin sassaƙaƙƙiyar siffa a gare ka? Ko gare shi wanda ya sassaƙa ta, gunki na zubi, mai koyar da ƙarairayi; gama ya na sa dogararsa ga aikin hannuwansa sa'ad da ya ke yin waɗannan alloli bebaye.19'Kaiton wanda ke ce wa itace, 'Ka farka!' Ko ya ce wa beben dutse, 'Ka tashi!' Waɗannan abubuwa suna koyarwa ne? Duba, an dalaye su da zinariya da azurfa amma ba numfashi ko kaɗan a cikinsa.20Amma Yahweh yana cikin haikalinsa mai-tsarki! Ku yi shiru dukkan ƙasa a gabansa."

3

1Addu'ar annabi Habakuk a waƙance:2Yahweh na ji labarinka, kuma na tsorata. Yahweh, ka farfaɗo da aikinka a cikin waɗannan lokatai; a cikin waɗannan lokatai ka bayyana shi; ka tuna da yin tausayi cikin fushinka.

3Allah ya zo daga Teman, kuma Mai Tsarki daga Dutsen Faran. Selah. Ɗaukakarsa ta rufe sammai, kuma duniya na cike da yabonsa.
4Sheƙi biyu na hannunsa na haskakawa kamar walƙiya, inda ƙarfinsa yake a ɓoye.5Cuta mai hallakarwa ta tafi a gabansa, annoba kuma ta biyo sawunsa.
6Ya tsaya ya auna duniya; ya duba kuma ya girgiza al'ummai. Harma daɗaɗɗun duwatsu suka rugurguje, madawwaman tsaunuka kuma suka rusuna ƙasa. Tafarkinsa madawwami ne.
7Na ga runfunan Kushan cikin ƙunci, kuma bargunan runfunan cikin ƙasar Midiyan suna raurawa.8Yahweh ya fusata da kogunan ne? fushinka a kan kogunan ne, ko hasalarka kan teku ne, da ka yi sukuwa bisa dawakanka da karusanka masu nasara?
9Kã fito da bãkanka a ɗane; kạ sa kibiyoyinka ga băkanka! Selah. Kạ raba duniya da koguna.10Duwatsu sun gan ka sun murɗe cikin zafi. Ambaliyar ruwa ta bi ta kansu; Teku mai zurfi ya yi ruri. Ya yi tsalle da raƙuman ruwansa.
11Rana da wata suka tsaya cik can sama wurarensu masu nisa suka gudu daga hasken kibiyoyinka, daga kuma hasken walƙiyar sheƙin mashinka.12Ka tattaka duniya da zafin fushi. A cikin fushi ka sussuke al'ummai.
13Ka fita domin ceton mutanenka, domin ceton zaɓaɓɓenka. Ka rugurguza kan gidan mai mugunta domin a kware shi daga ƙasa har zuwa wuyansa. Selah.
14Da kibiyoyinsa ka soke kan mayaƙansa tun da sun taho kamar hadari domin su watsar da mu, marmarinsu kamar masu lanƙwame matalauta a ɓoyayyen wuri ne.15Ka yi tafiya zuwa ƙetaren teku da dawakanka, ka kuma tattara manyan ruwaye.
16Na ji, kuma can cikin gaɓoɓina na yi rawar jiki! Da jin ƙarar leɓunana sun girgiza. Ruɓewa ta shigo cikin ƙasusuwana, a cikina ina rawar jiki yayin da nake jira shiru domin ranar ƙunci da zata zo a kan mutanen da suka mamayemu.
17Koda itacen ɓaure bai yi toho ba kuma inabi bai ba da 'ya'ya ba; kuma itacen zaitun bai ba da amfani mai kyau ba kuma gonaki basu ba da abinci ba; koda a ce garke ya tsinke babu shanu a maɗauri, ga abin da zan yi.
18Duk da haka, zan yi farinciki cikin Yahweh. Zan cika da murna saboda Allahn cetona.19Ubangiji Yahweh shi ne ƙarfina ya kuma maida sawayena kamar na barewa. Yana sa in tafi gaba bisa wurarena na ɗaukaka. - Ga shugaban mawaƙa, bisa kayan kaɗe-kaɗena masu tsarkiya.

Littafin zafaniya

1

1Wannan maganar Yahweh ce da ta zo ga Zafaniya ɗan Kushi ɗan Gedaliya ɗan Amariya ɗan Hezekiya, a kwanakin Yosiya ɗan Amon, sarkin Yahuda.2"Zan hallakar da kome da kome daga doron duniya - wannan furcin Yahweh ne.3Zan hallakar da mutum da dabba; Zan hallakar da tsuntsayen sammai da kuma kifayen teku, rusasssun wurare tare da miyagu. Domin zan datse mutum daga sararin duniya - wannan furcin Yahweh ne.

4Zan miƙa hannuna kan Yahuda da dukkan mazaunan Yerusalem. Zan datse kowanne ragowar Ba'al daga wannan wurin da kuma sunayen masu bautar gumaka daga cikin firistoci,5mutanen da a saman gidaje suke bautawa hallitun sammai, da mutanen da ke sujada da rantsuwa ga Yahweh amma kuma suna rantsuwa ta wurin sarkinsu.6Zan kuma datse waɗanda suka juye baya daga bin Yahweh, waɗanda basu neman Yahweh basu kuma neman bishewarsa."
7Ku yi shiru a gaban Ubangiji Yahweh! Gama ranar Yahweh ta kusato; Yahweh ya shirya hadaya ya kuma keɓe baƙinsa.8"Zai zama kuma a ranar hadayar Yahweh, zan hori hakimai da 'ya'yan sarakuna, da duk wanda ke sanye da baƙin tufafi.9A ranan nan zan hukunta masu tsallake dankarin ƙofa, masu cika gidan shugabansu da ta'addanci da yaudara.
10Haka zai zama a ranar nan - wannan furcin Yahweh ne - lallai za a ji kukan baƙinciki daga Kofar Kifi, da ƙarar kuka daga Gundumar Biyu, da gagarumar ƙarar farfashewa daga tuddai.11Kuyi kuka da ƙarfi, ku mazaunan Gundumar Kasuwa, gama za a rugurguje dukkan fatake; za a datse dukkan masu awon azurfa.
12Zai zama a gabatowar lokacin nan ne zan binciki Yerusalem da fitilu in kuma hukunta mutanen da suka kafu a kan ruwan inabinsu suka ce a zuciyarsu, 'Yahweh ba zai yi kome ba, ko nagari ko mugu.'13Dukiyarsu zata zama ganima, kuma gidajensu za a maida su kufai da aka yi watsi da shi! Zasu gina gidaje amma baza su zauna a cikinsu ba, zasu dasa gargunan inabi amma baza su sha ruwansu ba.
14Babbar ranar Yahweh ta yi kusa, tayi kuma kurkusa da sauri! ‌Ƙarar ranar Yahweh zata zama kukan mayaƙi na ɓacin rai!15Ranar nan zata zama ranar tsananin fushi, ranar damuwa da baƙinciki, ranar baƙin hadari da rushewa, ranar duhu da baƙin ƙunci, ranar giza-gizai da baƙin duhu.16Zata zama ranar hura kakaoki da ƙararrawa gãba da ƙayatattun birane masu manya manyan wuraren ɓuya da ganuwoyi.
17Gama zan kawo ƙunci ga mutane, saboda suyi tafiya kamar makafin mutane tunda sun yiwa Yahweh zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura, a kuma cire kayan cikinsu kamar kashin dabba.18A ranar hasalar Yahweh zinariyarsu ko azurfarsu ba zasu iya kuɓutar dasu ba. A cikin wutar kishinsa dukkan duniya zata hallaka, gama zai kawo cikakken mummunan ƙarshen dukkan mazaunan duniya."

2

1Ku jero kanku tare ku taru, al'umma marar kunya -2kafin ranar aiwatar da dokokin kuma waccan ranar ta wuce kamar ƙaiƙayi, kafin zafin fushin hasalar Yahweh ta auko muku, kafin ranar hasalar Yahweh ta zo kanku.3Ku nemi Yahweh, ku mutane masu tawali'u da biyayya ga dokokinsa! ku nemi adalci Ku nemi tawali'u, ko wataƙila a yi maku kariya a ranar hasalar Yahweh.

4Gama za a yashe da Gaza, kuma Ashkelon zata zama rusasshiya. Zasu kori Ashdod da rana, kuma zasu tunɓuke Ekron!5Kaiton mazaunan gaɓar teku, al'ummar Kiritiyawa! Yahweh ya yi magana gãba da ku, Kan'ana, ƙasar Filistiyawa. Zan hallakar dake har sai ba mazaunan da suka ragu.
6Yankin gaɓar teku zai zama saurar makiyaya da makwantar dabbobi. Yankin gaɓar zai zama na ragowar mutanen gidan Yahuda, waɗanda zasu yi kiwon garkensu a wurin.7Da yamma mutanensu zasu kwanta a gidajen Ashkelon, gama Yahweh Allahnsu zai lura da su ya kuma mayar masu da mallakarsu.
8Na ji cakunar Mowab da wulaƙancin mutanen Amon sa'ad da suke cakunar mutanena suna ci masu kan iyaka.9Don haka na rantse da kaina - wannan ne furcin Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, - Mowab zai zama kamar Saduma, mutanen Amon kuma kamar Gomora; wurin ciyayi masu dafi da ramin gishiri da aka yi watsi da shi har abada. Amma ragowar mutanena zasu washe su, ragowar al'ummata kuma zasu mallake su."
10Wannan zai faru da Mowab da Amon saboda girman kansu, tunda suka cakuni suka kuma yi ba'a ga mutanen Yahweh mai runduna.11Sa'an nan zasu ji tsoron Yahweh, don zai cakuni dukkan allolin duniya. Kowannensu zai yi masa sujada, kowanne daga wurinsa, daga kowacce gaɓar teku.
12Ku Kushiyawa kuma za a soke ku da takobina,13Hannun Allah kuma zai kawo hari ga arewa ya hallaka Asiriya, don Nineba zata zama rusasshen wurin da aka watsar, busshiya kuma kamar hamada.14Sai garkuna su kasance kwance a nan, kowacce dabba ta kowacce al'umma, mujiyar hamada da mujiya mai tsuwwa ma zasu huta a samman ginshiƙanta. Za a yi waƙoƙin kira daga tagogi; Juji zai kasance a bakin ƙofofin; sassaƙaƙƙun ginshiƙanta na sidar za a bayyana su.
15Wannan ne maɗaukakin birnin da ya zauna cikin rashin tsoro, da yace a zuciyarsa," Ni ne kuma ba wanda ya kai ni." To Yaya ya zama mafi muni, wurin da dabbobin jeji ke kwance ciki. Duk wanda ya wuce ta wurinsa zai yi tsaki ya kaɗa kai.

3

1Kaiton ki birni mai tayarwa! Birni mai ta'addanci ya ƙazantu.2Bata saurari muryar Allah ba, ko ta karɓi gyara daga Yahweh. Bata dogara ga Yahweh ba kuma ba zata kusanci Allahnta ba.

3Sarakunanta zakuna ne masu ruri a tsakiyarta. Alƙalanta kyarketan yamma ne da basa barin abin yin tuƙa da safe.4Annabawanta marasa biyayya ne masu cin amana. Firistocinta sun wulaƙanta abin da ke mai tsarki kuma sun yi ta'addanci ga shari'a.
5Yahweh adali ne a cikinta. Ba zai yi kuskure ba. Daga safiya zuwa safiya zai aiwatar da adalci! Ba zai ɓoyu ba cikin haske, duk da haka mutane marasa adalci basu san kunya ba.
6Na hallakar da al'ummai; an lalatar da kagarorinsu. Na mai da titunansu kufai, don kar kowa ya bi kan su. An hallakar da biranensu har babu mutumin dake zaune cikinsu.7Na ce, 'Hakika zaku ji tsoro na. Ku karɓi gyara don kada a datse ku daga gidajenku ta wurin dukkan abubuwan da na shirya in yi maku.' Amma suna ƙagara su fara kowacce safiya da lalata ayyukansu.
8Saboda haka ku jira ni - wannan furcin Yahweh ne. Har sai ranar da zan tashi domin ƙwace wahalallun. Gama ƙudurina shi ne in tara al'ummai, in taro masarautu, in kuma zuba masu fushina-dukkan hasalata mai zafi; domin a cikin wutar kishina za a cinye dukkan duniya.
9Amma zan bada leɓuna masu tsarki ga mutanen, a kira dukkan su cikin sunan Yahweh su bauta mani suna tsaye kafaɗa da kafaɗa.10Daga ƙetaren kogin Kush masu yi mani sujada - mutanena dake warwatse - zasu kawo baye-bayen dake nawa.11A ranan nan baza ku kunyata ba game da dukkan abubuwan da kuka yi mani. Tun da a wannan lokaci zan kawar da waɗanda suka yi bikin girman kanku daga cikinku, saboda kuma baza ku ƙara yin rashin hankali ba a bisa dutsena mai tsarki.
12Amma zan bar ku ƙaskantattu matalautan mutane, zaku kuma fake a cikin sunan Yahweh.13Ragowar Isra'ila kuma baza su ƙara aikata rashin adalci ba ko su faɗi ƙarairayi ko kuma a sami yaudara a bakin su ba; saboda haka zasu yi kiwo su kwanta, babu kuma wanda zaya tsoratar dasu."
14Yi waƙa 'ɗiyar Sihiyona! Yi ihu, Isra'ila. Yi murna da farinciki da dukkan zuciyarki, ɗiyar Yerusalem.15Yahweh ya ɗauke hukuncinki; Ya kori maƙiyanki! Yahweh shi ne sarkin Isra'ila a tsakiyarku. Baza ki ƙara jin tsoron mugunta ba!16A ranar nan zasu cewa Yerusalem, "Kada ki ji tsoro, Sihiyona. Kada ki bari hannuwanki suyi sanyi.
17Yahweh Allahnku yana tsakiyarku, mai ƙarfin nan da zai cece ku. Zai ji daɗin ku da farinciki kuma zai yi shuru a kanku cikin ƙaunarsa. Zai yi murna a kanku kuma zai yi sowa ta farinciki a kanku,18Zan tattara waɗanda ke ɓacin, waɗanda baza su iya kasancewa a zaɓaɓɓun bukukuwa ba, domin haka baza ku ƙara jin kunya dominsa ba.
19Duba, Ina gab da horon masu tsananta maku. A lokacin nan, zan ƙwato guragu in tattaro waɗanda aka watsar. Zan maishe su kamar yabo, zan musanya kunyarsu zuwa sanannu a dukkan duniya.20A lokacin nan zan bi daku; a lokacin nan zan tara ku tare. Zan sa dukkan al'umman duniya su girmama su kuma yabe ku, lokacin kuka gana dawo da ku," inji Yahweh.

Littafin haggai

1

1A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyos, a wata na shida, a rana ta fari ga watan, maganar Yahweh ta zo ta hannun annabi Haggai ga gwamnan Yahuda, wato Zerubabel ɗan Shiltiyel, da kuma babban firist Yoshuwa ɗan Yehozadak cewa2"Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Waɗannan mutanen na cewa, 'lokaci bai yi ba da za mu zo ko mu gina wa Yahweh gida.'"

3Sai maganar Yahweh ta zo ta hannun annabi Haggai, cewa,4"Lokaci ya yi da za ku zauna a shiryayyun gidajenku, amma kuma wannan gidan na kwance a lalace?5To Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Ku lura da hanyoyinku!6Kun shuka iri da yawa amma kun girbi kaɗan, kun ci amma bai ishe ku ba, kun sha amma ba ku ƙoshi ba. Ku na sa tufafi amma ba ku ji ɗumi ba, kuma mai ƙarbar albashi yana ƙarba kawai ya sa shi cikin jakka mai hudoji!
7Yahweh mai runduna ya faɗi haka: "Ku lura da hanyoyinku!8Ku hau bisa tudu, ku kawo katako ku gina mani gida, ta haka zan ji daɗi, kuma za a ɗaukaka ni!- in ji Yahweh."9"Kun nema da yawa amma duba kun kawo gida kaɗan, don na hure shi! Don me?" Yahweh mai runduna ya furta. "Saboda gidana na kwance a lalace, alhali kowanne ɗayan ku na aiki a nasa gidan.
10Saboda haka sammai sun riƙe raɓa, ƙasa kuma ta riƙe amfaninta,11Ni na kawo ƒãri ga ƙasar kuma ga tuddai, ga ƙwayar hatsi, kuma ga sabon ruwan inabi, ga mai kuma ga girbin ƙasa, ga mutane da kuma ga dabbobi, kuma ga dukkan ayyukan hannuwanku!"
12Sai Zarubabel ɗan Shaltiyel da babban firist Yoshuwa ɗan Yehozadak, tare da dukkan sauran mutanen, suka yi biyayya da muryar Yahweh Allahnsu da kuma kalmomin annabi Haggai, saboda Yahweh Allahnsu ya aiko shi kuma mutanen sun ji tsoron fuskar Yahweh.13Sai Haggai, mai kawo saƙon Yahweh, ya faɗi saƙon Yahweh zuwa ga mutanen ya ce, "Ina tare da ku! - wannan furcin Yahweh ne!"
14Yahweh ya zuga ruhun gwamnan Yahuda, wato Zerubabel ɗan Shiltiyel, da kuma ruhun babban firist Yoshuwa ɗan Yehozadak, da kuma ruhun dukkan sauran mutanen, domin haka suka je su ka yi aiki a gidan Yahweh mai runduna, Allahnsu15a rana ta ashirin da hudu ta watan shida, a shekara ta biyu ta mulkin sarki Dariyos.

2

1A wata na bakwai ranar ashirin da ɗaya a watan, maganar Yahweh ta zo ta hannun annabi Haggai, cewa,2"Yi magana da gwamnan Yahuda, Zerubabel ɗan Shiltiyel, da babban firist Yoshuwa ɗan Yehozadak, da dukkan mutane da aka rage. Ka ce,

3"Wa ya rage a cikinku wanda ya ga wannan gida da darajarsa ta dã? Ya ya ku ka ganshi a yanzu? Shin kamar ba kome ya ke a idanunku ba?4Yanzu, sai ka yi ƙarfin hali, Zerubabel! - wannan furcin Yahweh ne, kai ma Yoshuwa ɗan Yehozadak babban firist sai ku yi ƙarfin hali, dukkan mutanen cikin ƙasar! - wannan furcin Yahweh ne, kuma ku yi aiki, domin ina tare da ku! - wannan furcin Yahweh mai runduna ne.5Wannan shi ne alƙawarin da na yi da ku sa'ad da kuka fito daga ƙasar Masar, kuma Ruhuna na tare da ku. Kada ku ji tsoro!
6Domin Yahweh mai runduna ya faɗi wannan: Ba da jimawa ba zan girgiza sammai da ƙasa, da teku da duk abin da ke a busarshiyar ƙasa!7Zan kuma girgiza kowacce al'umma, kuma kowacce al'umma za ta kawo abubuwa ma su daraja a gare ni, kuma zan cika wannan gidan da ɗaukaka, in ji Yahweh mai runduna.
8Azurfa da zinariya nawa ne! - wannan furcin Yahweh mai runduna ne.9Ɗaukakar wannan gidan ta zama da girma a nan gaba fiye da farkonsa, inji Yahweh mai runduna, zan ba da salama ga wannan wuri! - wannan furcin Yahweh mai runduna ne."
10A rana ta ashirin da hudu ga watan tara a shekara ta biyu ta Dariyos, maganar Yahweh ta zo ga annabi Haggai cewa,11"Yahweh mai runduna ya faɗi wannan: A tambayi firistoci a kan shari'a, a ce,12"Idan mutum ya ɗauki nama da aka keɓe don Yahweh a rigarsa, sa'an nan ta taɓa gurasa, ko miya, ko ruwan inabi ko mai, ko kowanne irin abinci, ko wannan zai sa abin ya tsarkaka?" Firistoci suka amsa suka ce, "A'a."
13Sai Haggai yace, "Idan wani wanda ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, daga cikin waɗannan, sun zama ƙazantattu? Sai firistoci suka amsa suka ce, "I sun ƙazantu.14Sai Haggai ya amsa yace, "Haka ya ke da mutane da al'umma da ke gabana! - wannan furcin Yahweh ne - haka ya ke game da dukkan abin da suke yi da hannuwansu. Da kuma abin da suke miƙawa a gare ni marar tsarki ne!
15To yanzu, sai ku yi tunani a cikin lamirinku a kan abin da ya wuce har zuwa wannan rana. Kafin a ɗora dutse a kan dutse na haikalin Yahweh,16yaya ya ke? Lokacin da ku ka zo tarin da aka auna maku mudu ashirin na hatsi, sai aka iske mudu goma kaɗai; idan kuma kun zo wurin matsar ruwan inabi don a ɗebo mudu hamsin, sai aka tarar da mudu ashirin kawai.17Na aika maku da bala'i a aikin hannuwanku ta wurin darɓa da raɓa amma duk da haka ba ku komo wurina ba - wannan furcin Yahweh ne.
18Lura tun daga wannan rana zuwa gaba, daga rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, tun daga ranar da aka aza harsashin ginin haikalin Yahweh. Ku lura da shi!19Akwai sauran iri a rumbun? Inabin da itacen ɓauren, da ruman, da itacen zaitun ba su bada amfani ba! Amma daga wannan rana zan albarkace ku!"
20Sai maganar Yahweh ta zo a karo na biyu ga Haggai a rana ta ashirin da huɗu ga watan ya ce,21"Yi magana da gwamnan Yahuda, Zerubabel, ka ce, 'Zan girgiza sammai da ƙasa.22Zan kuma hamɓare kursiyin mulkoki in kuma lalata ƙarfin mulkokin al'ummai! Zan kuma hamɓare karusai da mahayansu; dawakai da mahayansu zasu faɗi ƙasa, kowanne saboda takobin ɗan'uwansa.
23A wannan rana - wannan furcin Yahweh mai runduna ne - Zan ɗauke ka, Zerubabel ɗan Shiltiyel, bawana - wannan furcin Yahweh ne. Zan mai da kai kamar zoben hatimi, gama na zaɓe ka!' - wannan furcin Yahweh mai runduna ne!"

Littafin zakariya

1

1A cikin wata na takwas na shekara ta biyu na mulkin Dariyos maganar Yahweh ta zo ga Zakariya ɗan Berekaya ɗan Iddo, annabi, yana cewa,2"Yahweh ya ji haushin ubanninku ƙwarai!3Ka faɗi masu, 'Yahweh mai runduna ya faɗi haka: ku juyo gare ni! - wannan furcin Yahweh mai runduna ne - ni ma zan dawo gare ku, Yahweh mai runduna ya faɗa.

4Kada ku zama kamar ubanninku waɗanda Annabawa suka yi wa shela a lokatan baya, suna cewa, "Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Ku juyo daga miyagun hanyoyinku da ayyukanku na mugunta!" Amma basu ji ba ko kuma su saurare ni - wannan ne furcin Yahweh.'5Ubanninku, ina suke? Ina Annabawan, suna nan ne har abada?6Amma maganganuna da dokokina da na umarci bayina Annabawa, ba sun zarce ubanninku ba? Sai suka tuba suka ce, 'Kamar yadda Yahweh mai runduna ya shirya ya yi mana abin da ya yi wa hanyoyinmu da ayyukanmu dai-dai, hakanan ya yi da mu.'"
7A cikin rana ta ashirin da huɗu na watan sha ɗaya, wanda shi ne watan Shibat, cikin shekara ta biyu na mulkin Dariyos, maganar Yahweh tazo wurin Annabi Zakariya ɗan Berekaya ɗan Iddo, cewa,8"Da dare na gani, na duba kuma! ga mutum na sukuwa bisa jan doki, yana tsakiyar itatuwan cizaƙi dake cikin kwari; bayan shi kuma akwai dawakai da ja da jaja-jaja-ruwan ƙasa-ƙasa da kuma farare."9Na ce, "Ubangiji mene ne waɗannan?" Sai mala'ikan da ke magana da ni yace mani, "zan nuna maka ko mene ne waɗannan."
10Sai mutumin dake tsaye tsakiyar itatuwan cizaƙi ya amsa yace, "Waɗannan su ne Yahweh ya aika su yi yawo cikin duniya duka."11Suna ba da amsa ga mala'ikan Yahweh wanda ke tsaye a tsakiyar itatuwan cizaƙi; suna ce masa, "Muna ta yawatawa cikin duniya dukka; duba, dukkan duniya na zaune tsit kuma cikin hutawa."
12Sai mala'ikan Yahweh ya amsa yace, "Yahweh mai runduna, har yaushe ne ba za ka nuna tausayi ga Yerusalem ba da kuma biranen Yahuda da suka sha wahalar zafin fushi shekarun nan saba'in?"13Yahweh ya amsa wa mala'ikan da ya yi magana da shi, da kalmomi masu daɗi, kalmomin ta'aziya.
14Sai mala'ikan dake magana da ni yace mani, "Ka yi kira ka ce, 'Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Ina kishi game da Yerusalem da Sihiyona da babban kishi!15Ina jin haushi ƙwarai game da al'umman dake zaune cikin hutu. Yayin da haushina kaɗan ne game da su, sai suka maida bala'in ya zama da tsanani.
16Saboda haka Yahweh mai runduna ya faɗi wannan: Na komo ga Yerusalem tare da jinkai. Za a sake gina gidana cikinta - wannan furcin Yahweh mai runduna ne - kuma za a ja layin gwaji bisa Yerusalem!'17Ka sake kira, kuma, ka ce, 'Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Biranena zasu sake malala da nagarta, Yahweh kuma zai sake yi wa Sihiyona ta'aziya, zai kuma sake zaɓen Yerusalem.'"
18Sai na ɗaga idanuna na ga ƙahonni huɗu!19Sai na yi magana da mala'ikan dake magana da ni, "Mene ne waɗannan?" Ya amsa mani, "Waɗannan ne ƙahonnin da suka warwatsa Yahuda, da Isra'ila, da Yerusalem."
20Sai Yahweh ya nuna mani masassaƙa huɗu.21Na ce, "Me waɗannan mutanen suka zo yi?" Ya amsa, yace, "Waɗannan ne ƙahonnin da suka warwatsa Yahuda har ba mai iya ɗaga kansa. Amma waɗannan mutane sun zo ne su kore su, su kakkarya ƙahonnin al'ummai waɗanda suka ɗaga ƙahon tsayayya da ƙasar Yahuda domin watsar da ita."

2

1Daga nan na ɗaga idanuna sai na ga mutum da ma'auni a hannunsa.2Na ce, "Ina zaka?" Sai ya ce mani, "Domin in auna Yerusalem, a tantance faɗinta da tsawonta."

3Sai mala'ikan da yake magana da ni ya yi tafiyar sa sai wa ni mala'ika kuma ya tafi domin ya same shi.4Mala'ikan na biyu yace masa, "Yi gudu ka yi magana da saurayin can; ka ce, 'Yerusalem zata zauna a buɗaɗɗiyar ƙasa saboda yawan mutane da dabbobi dake cikinta.5Gama ni - wannan furcin Yahweh ne - zan zama katangar wuta kewaye da ita, kuma zan zama ɗaukakar dake cikinta.
6Tashi! Tashi! Ku gudu daga ƙasar arewa - wannan furcin Yahweh ne - gama na warwatsa ku kamar kusurwoyin iska huɗu a sasarin sama! - wannan furcin Yahweh ne.7Tashi! Ku tsere zuwa Sihiyona, ku da kuke zaune tare da ɗiyar Babila!'"
8Gama bayan da Yahweh mai runduna ya darajantani ya kuma aike ni ga al'umman nan da suka washe ku - gama duk wanda ya taɓa ku, ya taɓa ƙwayar idon Allah! - bayan da Yahweh ya yi wannan, sai ya ce,9"Ni da kaina zan girgiza hannuna a bisansu, kuma za a washe su domin bayinsu. "Daga nan zaku sani Yahweh mai runduna ne ya aiko ni.
10"Ki raira waƙa domin farinciki, ke ɗiyar Sihiyona, gama ni da kaina ina gaf da zuwa in kafa sansani a cikinki! - wannan ne furcin Yahweh."11Daga nan manyan al'ummai zasu haɗu da juna zuwa ga Yahweh a wannan rana. Ya faɗi, "Daga nan zaku zama mutanena; kuma zan kafa sansani a cikinku," daga nan kuma zaku sani Yahweh mai runduna ya aiko ni zuwa gare ku.
12Gama Yahweh zai gãji Yahuda a matsayin mai 'yancin gãdonta cikin ƙasa mai tsarki kuma zaya sake zaɓen Yerusalem domin kansa.13Ku yi tsit, dukkanku masu rai, a gaban Yahweh, domin an zugo shi daga wurinsa mai tsarki!

3

1Sai Yahweh ya nuna mani Yoshuwa babban firist a tsaye a gaban mala'ikan Yahweh ga kuma Shaiɗan a tsaye a hannun damansa domin ya zarge shi da zunubi.2Mala'ikan Yahweh yace da Shaiɗan, "Bari Yahweh ya tsauta ma, Shaiɗan; bari Yahweh, wanda ya zaɓi Yerusalem, ya tsauta maka! Wannan ba reshe ba ne da aka ciro daga wuta?"3Yoshuwa dai na sanye da ƙazantattun tufafi yayin da yake tsaye a gaban mala'ikan.

4Sai mala'ikan ya yi magana yace da waɗanda ke tsaye a gabansa, "Ku tuɓe ƙazantattun tufafin daga jikinsa." Sai yace da Yoshuwa, "Duba! na sa laifuffukanka su kawu daga gare ka kuma zan sanya maka kaya masu tsafta."5Sai yace, "Bari a sa rawani mai tsafta a bisa kansa!" Sai suka sa rawani mai tsafta a bisa kan Yoshuwa kuma suka sanya masa tufafi masu tsafta yayin da mala'ikan Yahweh ke tsaye tare dasu.
6Daga nan sai mala'ikan Yahweh ya yi umarni mai juyayi ga Yoshuwa yace,7"Yahweh mai runduna ya faɗi wannan: Idan za ka yi tafiya cikin hanyoyina, ka kuma kiyaye dokokina, to za ka yi mulkin gidana kuma ka yi tsaron harabaina, domin zan ba ka dama ka shiga ka fita a tsakiyar waɗannan dake tsayawa a gabana.
8Ka saurara, Yoshuwa babban firist, kai da masu tarayya da kai dake zaune tare da kai! Domin waɗannan mutane alama ne, gama ni da kaina zan taso da bawana Reshen.9Yanzu ka duba dutsen da na sa a gaban Yoshuwa. Akwai idanu bakwai a kan wannan dutse ɗaya, kuma zan sassaƙa hatimi -wannan ne furcin Yahweh mai runduna - kuma zan cire zunubin daga wannan ƙasa a rana ɗaya.
10A wannan rana - wannan furcin Yahweh mai runduna ne - kowanne mutum zai gayyaci maƙwabcinsa ya zauna a gindin inabinsa da gindin itacen ɓaurensa."

4

1Sai mala'ikan dake magana da ni ya juya ya farko da ni kamar mutumin dake farkarwa daga barci.2Ya ce da ni, "Me ka gani?" na ce, "Na ga mazaunin fitila da aka yi da zinariya baki ɗaya, da kwano a bisansa. Yana da fitilu bakwai a bisansa da kuma lagwanin fitilu bakwai a kan kowacce fitila.3Akwai itatuwan zaitun biyu a kowanne gefensa, ɗaya na gefen dama da kwanon ɗaya kuma na gefen hagu."

4Sai na ƙara magana da mala'ikan dake magana da ni. Na ce, "Mene ne ma'anar waɗannan abubuwa ya shugabana?"5Mala'ikan dake magana da ni ya amsa yace da ni, "Baka san ma'anar waɗannan abubuwa ba?" Na ce, "A'a, ya shugabana."
6Sai ya ce ma ni, "Wannan ce maganar Yahweh ga Zerubabel: Ba ta ƙarfi ba, ba ta iko ba amma ta Ruhuna, Yahweh mai runduna ya faɗa.7Kai wane ne, babban dutse? A gaban Zerubabel za ka zama sarari, zai kuma kawo dutsen dake sama tare da sowace - sowacen 'Alheri! Alheri a gare shi!'"
8Maganar Yahweh tazo gare ni, cewa,9"Hannun Zerubabel ya ɗora harsashen ginin wannan gida hannunsa kuma zai kammala shi. Daga nan zaku sani Yahweh mai runduna ya aiko ni gare ku.10Wane ne ya rena ranar ƙananan abubuwa? Waɗannan mutane zasu yi farinciki kuma zasu ga dunƙulen dutsen a hannun Zerubabel. (Waɗannan fitilu bakwai idanun Yahweh ne dake dubawa ko ina cikin duniya)."11Daga nan na tambayi mala'ikan, "Mene ne waɗannan itatuwan zaitun biyu dake hagu da dama na mazaunin fitilar?"
12Na sake tambayar shi kuma, "Mene ne waɗannan rassan zaitun biyu dake gefen bututun zinari biyu dake ɓulɓulo da mạn zinariya daga cikinsu?"13Sai ya ce ma ni, "Baka san ko mene ne waɗannan ba?" Na ce, "A'a, ya shugabana."
14Sai ya ce, "Waɗannan 'ya'ya maza ne na sabon man zaitun dake tsaye a gaban Ubangijin dukkan duniya."

5

1Daga nan na juya na ɗaga idanuna, sai na gani, duba, ga littafi naɗaɗɗe na shawagi a sama!2Sai mala'ikan yace mani, "Me ka gani?" Na amsa, "Na ga littafi naɗaɗɗe na shawagi a sama, tsawonshi kamu ashirin fadinshi kamu goma."

3Sai ya ce da ni, "Wannan ce la'anar dake yawo a fuskar dukkan ƙasar, za a datse kowanne ɓarawo bisa ga yadda ya faɗa a gefe ɗaya, dukkan wanda kuma ya yi rantsuwa da alƙawarin ƙarya za a datse shi bisa ga yadda ya faɗa a gefe ɗayan, bisa ga maganganunsu.4"Zan aika da ita - wannan shi ne furcin Yahweh mai runduna - saboda haka zata shiga gidan ɓarawo da gidan wanda ya yi rantsuwar ƙarya da sunana. Zata zauna a gidanshi ta cinye katakan da duwatsun."
5Daga nan sai mala'ikan dake magana da ni ya fita ya ce mani, "Ɗaga idanunka ka ga abin dake tahowa!"6Sai na ce, "Mene ne?" Ya ce, "Wannan kwando ne dake ɗauke da garuwa dake zuwa. Wannan laifuffukansu ne cikin dukkan ƙasar."7Sai aka ɗauke murfin ƙarfen dake rufe da kwandon sai ga wata mace a cikinsa zaune!
8Mala'ikan yace, "Wannan mugunta ce!" Sai ya sake jefa ta cikin kwandon, kuma ya sake rufe shi da murfin ƙarfen.9Na ɗaga idanuna sai na ga mata biyu na zuwa wurina, kuma iska na cikin fukafukansu - gama suna da fukafukai kamar fukafukan shamuwa. Suka ɗaga kwandon nan tsakanin duniya da sama.
10Sai na ce da mala'ikan nan dake magana da ni, "Ina zasu kai kwandon?"11Ya ce da ni, "Zasu gina mashi haikali a ƙasar Shina, domin idan suka gama ginin haikalin, sai su ɗora kwandon a dai-dai wurinda suka shirya dominshi."

6

1Sai na juya na hango karusai huɗu suna zuwa sun fito daga tsakanin duwatsu biyu; duwatsun nan biyu kuwa an yi su daga tagulla ne.2Karusa na farko dawakansa jajaye ne, karusa na biyu dawakansa baƙaƙe ne,3karusa na uku dawakansa farare ne, karusa na huɗu dawakansa dabbare - dabbaren ruwan toka ne.4Sai na amsa na ce da mala'ikan dake magana da ni, "Mene ne waɗannan, ya shugabana?"

5Sai mala'ikan ya amsa yace ma ni, "Waɗannan su ne iskoki huɗu na sararin samaniya waɗanda ke fitowa daga wurin da suke tsayawa a gaban Ubangijin dukkan duniya.6Mai baƙaƙen dawakai na tafiya zuwa ƙasar arewa; fararen dawakan na tafiya zuwa ƙasar yamma; dawakai masu dabbare-dabbaren ruwan toka na tafiya zuwa ƙasar kudu."
7Waɗannan dawakai masu ƙarfi suka tafi suka nemi su kewaye dukkan duniya, sai mala'ikan yace, "Ku tafi ku kewaye bisa duniya!" Sai suka tafi domin dukkan duniya.8Sai ya kira ni ya yi magana da ni ya ce, "Dubi waɗanda ke tafiya zuwa ƙasar arewa; zasu tausar da ruhuna game da ƙasar arewa."
9Sai maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,10"Ka karɓi baiko daga 'yan gudun hijirar - daga Heldai, da Tobiya, da Yedaya - sai ka tafi dai-dai cikin wannan ranar ka kai cikin gidan Yosaya ɗan Zafaniya, wanda ya zo daga Babila.11Sai ka ɗauki azurfar da zinarin, sai ka yi rawani dasu ka ɗora bisa kan Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.
12Ka yi magana da shi ka ce, 'Yahweh mai runduna ya faɗi wannan: Wannan mutum, sunansa Reshe! Zai yi girma inda ya ke sa'an nan kuma ya gina haikalin Yahweh!13Shi ne wanda zai gina haikalin Yahweh sa'an nan ya ɗaga darajarsa; daga nan zai zauna ya yi mulki akan kursiyinsa. Zai zama firist a bisa kursiyinsa kuma fahimtar salama za ta kasance tsakanin su biyun.
14Za a bayar da rawani ga Heldai, da Tobiya da Yedaya da Hen ɗan Zakariya a matsayin abin tunawa a cikin haikalin Yahweh.15Daga nan waɗanda ke daga nesa zasu zo su gina haikalin Yahweh, domin ku sani Yahweh mai runduna ne ya aiko ni zuwa gare ku; wannan zai faru idan da gaske kun saurari muryar Yahweh Allahnku!'"

7

1Da sarki Dariyos ya yi mulki shekaru huɗu, a ranar huɗu ga watan Kisleb (wanda shi ne watan tara), maganar Yahweh ta zo ga Zakariya.2Mutanen Betel suka aika da Shareza da Regem Melek da kuma mazajensu domin su yi roƙo gaban fuskar Yahweh.3Suka yi magana da firistocin dake gidan Yahweh mai runduna da kuma annabawan; suka ce, "Ko zan yi makoki cikin watan biyar ta wurin yin azumi, kamar yadda na yi cikin shekarun nan masu yawa?"

4Sai maganar Yahweh mai runduna ta zo gare ni, cewa,5"Yi magana da dukkan mutanen ƙasar da firistocin ka ce, 'Da kuka yi azumi da makoki watan biyar da watan bakwai cikin shekarun nan saba'in, da gaske ni kuka yi wa azumi?6Da kuka ci ku ka sha, ba don kanku ku ka ci kuka sha ba?7Waɗannan ba sune maganganun da Yahweh ya yi shela ba ta bakin annabawan dã, sa'ad da kuke zaune a Yerusalem da biranen kewaye cikin wadata kuma kuka yi zamanku a Negeb, da gefen tsaunukan yamma?'"
8Maganar Yahweh ta zo wurin Zakariya, cewa,9"Yahweh mai runduna ya faɗi haka, 'Ku zartar da hukunci mai gaskiya, da amintaccen alƙawari, da kuma jinƙai. Bari kowanne mutum ya yi wa ɗan'uwansa haka.10Game da gwauruwa da maraya, da kuma baƙo, da matalauci-- kada ku ƙuntata masu, kada kuma wani ya shirya wani mugun abu game da ɗan'uwansa a cikin zuciyarsa.'
11Amma suka ƙi maida hankali kuma suka ɗaga kafaɗunsu cikin taurinkai. Suka toshe kunnuwansu domin kada su ji.12Suka maida zukatansu taurara kamar dutse domin ka da su ji shari'a ko maganganun Yahweh mai runduna. Ya aika da saƙonnin nan ga mutanen ta wurin Ruhunsa a lokatan farko, ta bakin annabawa. Amma mutanen suka ƙi saurare, domin wannan Yahweh mai runduna ya ji haushin su ƙwarai.
13Sai ya kasance da ya yi kira, basu saurara ba. Ta haka kuma," Yahweh mai runduna yace, "Zasu yi kira zuwa gare ni, amma ba zan saurare su ba.14Gama zan warwatsasu da guguwa cikin dukkan al'umman da basu taɓa gani ba, ƙasar za ta zama kufai bayansu. Gama ba wanda zai iya ratsawa ta cikin ƙasar ko ya dawo gareta tun da mutanen sun maida ƙasarsu ta farinciki zuwa watsartsiyar ƙasa."

8

1Maganar Yahweh mai runduna ta zo gare ni cewa,2"Yahweh mai runduna ya faɗi wannan: Ina kishi domin Sihiyona da kuma babban kishi da hasala mai zafi ƙwarai!3Yahweh mai runduna ya faɗi wannan: Zan komo wurin Sihiyona in kuma zauna a tsakiyar Yerusalem, gama za a kira Yerusalem Birnin Gaskiya kuma dutsen Yahweh mai runduna za a ce da shi Dutse Mai Tsarki!

4Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Tsofaffi maza da mata zasu ƙara kasancewa a titunan Yerusalem, kowannensu za shi buƙaci sanda a hannunsa domin yạ tsufa.5Titunan birnin zasu cika da matasa maza da mata, masu wasanni a cikinsu.
6Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Idan wani al'amari ya zama mai wuya a ganin mutanen nan da suka rage, a wannan kwanaki, shi ma za shi zama abu mai wuya a idanuna? -- wannan furcin Yahweh ne.7Yahweh mai runduna ya fa‌ɗ‌i wannan; Duba, Ina gaf da kuɓutar da mutanena daga ƙasashe na fitowar rana da na faɗuwar rana!8Gama zan dawo dasu, kuma zasu zauna a tsakiyar Yerusalem, haka zasu zama mutanena kuma, ni kuma zan zama Allahnsu cikin gaskiya da adalci!
9Yahweh mai runduna ya fa‌ɗi haka: Ku da kuka ci gaba da sauraron maganganuna daga bakin annabawa tun farkon kafa harsashen ginin wannan haikali, - wannan gida nawa, Yahweh mai runduna: Ku ƙarfafa hannayenku domin a gina haikalin.10Domin kamin wannan lokaci babu hatsin da aka tara daga wurin wani, babu wata riba domin mutum ko dabba, kuma ba a sami salama ba daga magabci ko ga mai shiga ko mai fita. Na maishe da kowanne mutum magabci ga makwabcinsa.
11Amma yanzu baza shi kasance kamar kwanakin baya ba, zan zauna tare da mutanena wa‌ɗ‌anda suka rage - wannan ne furcin Yahweh mai runduna.12Gama za a shuka irin salama; kuringa mai haurawa sama zata ba da 'ya'ya, duniya kuwa zata ba da amfanin ƙasa; sammai zasu ba da raɓarsu, gama zan sa sauran jama'ar da suka rage su gãji dukkan waɗannan abubuwa.
13Kun zama misali na la'ana ga al'ummai, gidan Yahuda da na Isra'ila. Yanzu fa zan kuɓutar da ku da haka kuma zaku zama albarka. Kada ku ji tsoro; amma bari hannuwanku su ƙarfafa!14Gama Yahweh mai runduna ya faɗi wannan: kamar yadda na shirya yi maku lahani a lokacin da kakanninku suka cakuneni - Yahweh mai runduna ya fadi wannan - kuma bai fasa ba,15haka kuma zan yi shiri mai kyau a wannan kwanaki zuwa ga Yerusalem da kuma gidan Yahuda! Kada ku ji tsoro!
16Ga abubuwan da dole ku aikata: ku faɗi gaskiya, kowanne mutum ga makwabcinsa. Ku yi shari'a da gaskiya, da adalci, da kuma salama a ƙofofinku.17Kada ku yi shirin aikata mugunta a cikin zuciyarku ga junanku, kuma kada ku ƙaunaci alƙawaran ƙarya -- gama waɗannan sune abubuwan da na ƙi! - wannan furcin Yahweh ne."
18Sa'an nan maganar Yahweh mai runduna ta zo gareni, cewa,19"Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Azumi na watan huɗu, da na watan biyar, da na watan bakwai, da na watan goma, duk zasu zama lokatan farinciki, da jin daɗi, da bukukuwan murna na gidan Yahuda! Saboda haka ku ƙaunaci gaskiya da salama!
20Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Mutane zasu sake zuwa, harma da waɗanda suke zama a birane daban - daban.21Mazaunan birni ɗaya zasu je wani birnin su ce, "Mu yi sauri mu je mu yi roƙo a gaban fuskar Yahweh mu kuma nemi Yahweh mai runduna! Mu ma zamu tafi da kanmu.22Mutane dayawa da manyan al'umma zasu zo Yerusalem su nemi Yahweh mai runduna kuma su roƙi tagomashin Yahweh!
23Yahweh mai runduna ya faɗi haka: A wannan kwanakin, maza goma daga kowanne harshe da kuma al'umma zasu kama haɓar rigarku su ce, "Bari mu tafi tare da ku, gama mun ji cewa Allah na tare da ku!"'

9

1Wannan furcin maganar Yahweh ne game da ƙasar Hadrak da Damaskus. Gama idanun Yahweh na bisan dukkan 'yan'adam, da kuma bisa dukkan kabilun Isra'ila.2Furcin nan kuma ya shafi Hamat wadda take maƙwabciya da Damaskus, ta kuma shafi Taya da Sidon, ko da shi ke suna da hikima ƙwarai.

3Taya ta gina wa kanta mafaka mai karfi ta kuma lafta azurfa kamar ƙura da kuma tatacciyar zinariya kamar laƙa a bisa titunanta.4Duba! Ubangiji za ya kawar da ita ya kuma lallata karfinta na teku, da haka zata hallaka da wuta.
5Ashkelon zata gani ta kuma ji tsoro! Gaza kuma zatayi rawar jiki ƙwarai! Ekron, begenta ba zai tabbata ba! Sarkin zaya hallaka daga Gaza, ba kuma za a sake zama cikin Ashkelon ba!6Baƙi zasu gina gidaje a Ashdod, zan kuma datse girman kan Filistiyawa.7Gama zan fitar da jininsu daga bakinsu, abubuwan banƙyamarsu kuma daga tsakiyar haƙoransu. Da haka zasu zama ragowa ga Allahnmu kamar zuriya a Yahuda, Ekron kuma zata zama kamar Yebusawa.
8Zan kafa sansani kewaye da ƙasata gãba da sojojin maƙiya domin kada wani ya ratsa ta cikinta ko ya je ko ya dawo, domin ba bu mai tsanantawar da zai ƙara shigowa ta cikin ƙasata. Yanzu dai zan kula da ƙasata da idanuna!
9Yi sowa da farinciki mai girma, ɗiyar Sihiyona! Yi sowa da murna, ɗiyar Yerusalem! Duba! Sarkinki na zuwa gare ki da adalci yana kuma kuɓutar dake. Mai tawali'u ne yana bisa kan jaki, a bisa kan ɗan jaki.10Daga nan zan datse karusa daga Ifraimu doki kuma daga Yerusalem, Za a kuma datse baka daga yaƙi; gama za ya yi maganar salama ga al'ummai, mulkinsa kuma za ya zama daga teku zuwa teku, kuma daga ‌Ƙogi har zuwa ƙarshen duniya!
11Amma ke, saboda jinin alƙawarina dake, zan fitar da 'yan sarƙarki daga ramin da babu ruwa.12Ku dawo cikin mafaka mai ƙarfi dukkan ku 'yan kurkukun bege! Ko yau ina shaida maku zan maido maku ruɓi biyu,13gama na lanƙwasa Yahuda kamar baka na. Na cika ƙwarina da Ifraimu. Na motso da 'ya'ya mazanki, Sihiyona, gãba da 'ya'ya mazanki, Giris, kuma na yi ki, Sihiyona, kamar takobin mayaƙi!
14Yahweh za ya bayyana gare su, kuma kibiyoyinsa zasu harba kamar walƙiya! Gama Ubangijina Yahweh za ya busa ƙahon kuma za ya cigaba cikin hadari daga Teman.15Yahweh mai runduna zai kare su, zasu kuma haɗiyesu, su kuma ci nasara da duwatsun majaujawa. Sa'an nan zasu sha suna sowa kamar mutanen da suka bugu da ruwan inabi, zasu kuma cika da ruwan inabi kamar dãro, kamar kusurwoyin bagadi.
16Yahweh Allahnsu zai cece su a wannan rana; zasu zama kamar garke mai ɗauke da mutanensa, gama zasu zama duwatsun kambi, wanda aka ɗaukaka bisa ƙasarsa.17Duba yadda zasu zama da kyau da kuma ban sha'awa! Samarin zasu yalwata kan hatsi, budurwan kuma bisa inabi mai zaƙi!

10

1Ku roƙi Yahweh ruwan sama a lokacin bazara -Yahweh shi ne mai yin hadarun-aradu -- kuma yana ba da ruwan sama ga kowa da kuma dukkan tsire tsiren gona.2Gama ƙarya kawai gumakan gãdo ke faɗi; masu sihiri kuma suna ƙirƙiro ƙarya; suna faɗin mafarkai na ruɗani su kuma yi ta'aziyar wofi, da haka suke yawo kamar tumaki suna shan azaba domin babu makiyayi.

3Fushina na ƙuna akan makiyayan; sune bunsuran -- shugabannin -- waɗanda zan hora. Yahweh mai runduna za ya kuma lura da garkensa, gidan Yahuda, za ya mai dasu kamar dokin yaƙinsa a yaƙi!
4Daga gare su dutsen kusurwar gini zaya fito; daga gare su turken rumfar za ya fito; bakan yaƙi za shi fito daga nan; daga can dukkan shugabanni zasu fito tare.5Zasu zama kamar jarumawa masu tattaka maƙiyansu a cikin laka a bisa titunansu a yaƙi; zasu ja dagar yaƙi, gama Yahweh na tare da su, zasu kuma kunyatar da mahayan dawakan yaƙi.
6Zan ƙarfafa gidan Yahuda in kuma ceci gidan Yosef; gama zan maido dasu in kuma nuna masu jinƙai. Ba za su yi kamar na yashe su ba, gama ni ne Yahweh Allahnsu, kuma zan amsa masu.7Daga nan Ifraim zaya zama kama da mayaƙi, zuciyarsu kuma zata yi farinciki kamar da inabi; 'Ya'yansu zasu gani su yi farinciki. Zuciyarsu zata yi farinciki a ciki na!
8Zan yi masu busa in kuma tara su, gama zan kuɓutar dasu, kuma zasu zama da girma kamar yadda suke a dã!9Na shuka su cikin al'ummai amma zasu tuna da ni a ƙasashe masu ni sa, su da 'ya'yansu zasu rayu su kuma dawo gida.10Gama daga Asiriya zan tattara su in kuma maido dasu daga Masar. Zan dawo dasu ƙasar Giliyad da Lebanon har sai ba sauran wuri dominsu.
11Zan bi ta cikin tekun azabarsu; Zan tsautawa igiyoyin tekun nan in kuma busar da dukkan zurfafun Nilu. Za a saukar da ƙasaitar Asiriya, sandar mulkin Masar kuma zata tafi daga Masarawa.12Zan ƙarfafa su a cikina, za su yi tafiya kuma cikin sunana - wannan furcin Yahweh ne.

11

1Ki buɗe ƙofofinki, Lebanon, don wuta ta cinye itatuwanki na sida!2Yi makoki, itatuwan siferes, gama itatuwan sida sun faɗi! Abin da yake ƙasaitacce ya lalace sarai! Yi makoki, ku rimaye na Bashan, gama babban kurmi dukka ya faɗi.3Makiyaya suna ta kururuwa, gama an lalatar da ɗaukakarsu! Muryar 'ya'yan zakuna na ruri, gama an lallatar da fahariyar Kogin Yodan!

4Wannan ne abin da Yahweh Allahna ya faɗi: "Kamar makiyayi, mai kiwon garken da aka ƙaddara domin yanka!5(Su waɗanda suka sayesu suka yankasu kuma ba a yi masu horo ba, kuma waɗanda suka sayar da su sukace; "Mai albarka ne Yahweh! Na zama mai arziƙi! gama makiyayan dake yi wa masu garken aiki basu jin tausayinsu).6Gama ba zan ƙara jin tausayin mazaunan ƙasar ba! --- wannan furcin Yahweh ne. Duba! Ni da kaina ina gaf da bayar da kowanne mutum cikin hannun makwabcinsa da kuma cikin hannun sarkinsa, zasu kuma lallatar da ƙasar ba bu wanda zan kuɓutar daga hannunsu."
7Don haka na zama makiyayin garken da aka ƙaddara domin yanka, ga masu cinikin tumaki. Na ɗauko sanduna biyu; ɗaya na kira ta "tagomashi" ɗayar kuma na kira ta "haɗin kai." da haka na yi kiwon garken.8A cikin wata ɗaya na hallaka makiyayan uku, gama hakurina ya gaza a kansu, haka su ma suka ƙi ni.9Sai na cewa masu garken, "Ba zan sake yi maku aikin makiyayi ba. Tumakin da ke mutuwa-- bari su mutu; tumakin da ke hallaka --- bari su hallaka. Bari tumakin dasu ka rage kowanne ya ci naman maƙwabcinsa."
10Sai na ɗauki sandata "tagomashi" sai na karyata domin in karya alƙawarina da nayi da dukkan kabiluna.11A wannan ranar aka karya alƙawarin, masu cinikin tumaki da waɗanda ke kallona suka sani cewa Yahweh ya yi magana.12Na ce masu, "Idan kun ga ya dace ku biya ni ladata. Amma idan ba haka ba, kada kuyi." Sai suka auna mani ladata --- sulallan azurfa talatin.
13Sai Yahweh yace dani, "Zuba azurfar cikin ma'aji, darajar farashin da aka kimantaka!" Sai na ɗauki sulallan azurfar talatin na zuba su cikin ma'aji a gidan Yahweh.14Sa'an nan na karya sandata ta biyu "Haɗin kai," domin a karya 'yan'uwantakar dake tsakanin Yahuda da Isra'ila.
15Yahweh yace da ni, "Ka sake, ɗaukarwa kanka kayan aiki irin na wawan makiyayi,16gama duba, ina gaf da naɗa makiyayi a ƙasar. Ba za ya kula da tumakin dake hallaka ba. Ba za ya tafi neman ɓatattun tumaki ba, ko ya warkar da tumakin da suka gurgunce ba. Ba zaya ciyar da lafiyayyun tumakin ba, amma za ya cinye naman tumaki masu ƙiba, ya kuma saɓe ƙofatunsu.
17Kaiton makiyayi mara amfani da ya yi watsi da garken! Bari takobi ta yi tsayayya da hannusa da kuma idonsa na dama! Bari hannunsa ya shanye idonsa na dama ya makance!"

12

1Wannan furcin maganar Yahweh game da Isra'ila - furcin Yahweh, shi wanda ya shimfiɗa sararin sammai ya kuma kafa harsashen duniya, wanda ya sa ruhun ɗan adam cikin mutum,2"Duba, ina gaf da sa Yerusalem ta zama kofi mai sa maƙwabtanta tangaɗi. Haka kuma za shi zama ga Yahuda a lokacin da aka yiwa Yerusalem sansani.3A wannan rana, Zan maida Yerusalem dutse mai nauyi domin dukkan mutane. Duk wanda ya yi ƙoƙarin ɗaga wannan dutse za ya ji wa kansa rauni mai tsanani, dukkan al'umman duniya kuma zasu tattaru yin gãba da wannan birni.

4A ranan nan --- wannan ne furcin Yahweh --- zan bugi kowanne doki da firgita da kuma kowane mahayi da hauka. Zan dubi gidan Yahuda da tagomashi in kuma bugi kowanne dokin sojojin da makanta.5Daga nan shugabannin Yahuda zasu ce cikin zuciyarsu, 'Mazaunan Yerusalem sune ƙarfinmu saboda Yahweh mai runduna, Allahnsu.'
6A wannan rana zan mai da shugabannin Yahuda kamar tukunyar wuta a tsakiyar itatuwa da kuma fitila mai ci balbal a cikin hatsin dake tsaye, gama zasu hallaka dukkan mazauna kewaye dasu dama da hagu. Yerusalem zata sãke zaunawa a wurinta."
7Yahweh zai ceci rumfunan Yahuda da farko, don kada darajar gidan Dauda da kuma na mazaunan Yerusalem su fi na sauran mazaunan Yahuda.8A wannan ranar Yahweh zaya zama kariyar mazaunan Yerusalem, kuma a wannan ranar, waɗanda basu da ƙarfi cikinsu zasu zama kamar Dauda, yayin da gidan Dauda zaya zama kamar Allah, kamar mala'ikan Yahweh a gabansu.9"A ranan nan da zan fara hallaka dukkan al'umman dasu ka yi tsayayya da Yerusalem.
10Amma zan zubo da ruhun tausayi da na roƙo a bisa gidan Dauda da mazaunan Yerusalem, domin su dube ni, wanda suka soke. Zasu yi makoki domina, kamar wanda ke makoki domin tilon ɗansa; za su yi matuƙar makoki dominsa kamar waɗanda su ke makokin mutuwar ɗan fari.11A wannan ranar makokin cikin Yerusalem za shi zama kamar makokin da aka yi cikin Hadad Rimon cikin kwarin Megido.
12Ƙasar zata yi makoki, kowacce zuriya daban da wasu zuriyoyin. Zuriyar gidan Dauda zata zama a ware matayensu kuma zasu zama a ware daga mazajen. Zuriya daga gidan Natan zasu zama a ware matayensu kuma zasu zama a ware da mazajen.13Zuriyar gidan Lebi zasu zama a ware, matayensu kuma a ware da mazajen. Zuriyar Shimeyawa zasu zama a ware matayensu kuma a ware daga mazajen.14Kowacce zuriya ta sauran zuriyar da suka ragu - kowacce zuriya zata zama a ware matayensu kuma zasu zama a ware daga mazajen."

13

1"A wannan rana za a buɗe wa gidan Dauda magudanar ruwa da kuma mazaunan Yerusalem, saboda zunubansu da rashin tsarkinsu.2A wannan ranar -- wannan furcin Yahweh mai runduna ne - cewa zan datse sunayen gumaka daga ƙasar don kada a ƙara tunawa dasu. Zan kuma sa dukkan annabawan ƙarya da ƙazamin ruhunsu su fita daga ƙasar.

3Idan wani mutum ya ci gaba da yin annabci, mahaifinsa da mahaifiyarsa waɗanda suka haifeshi zasu ce masa, 'Ba za ka rayu ba, don kana ƙarya da sunan Yahweh! Sa'an nan mahaifinsa da mahaifiyarsa waɗanda suka haife shi zasu soke shi yayin da yake anabce-anabce.
4A wannan ranar kowanne annabi zayaji kunyar wahayinsa yayinda yake gaf da yin annabci. Waɗannan annabawan ba zasu ƙara sanya rigar gashi ba don su ruɗi jama'a.5Gama kowanne zai ce, 'Ni ba annabi ba ne! Ni manomi ne, na fara aikin gona tun ina yaro!'6Amma wani zai ce masa, 'ina ka samo waɗannan raunukan a hannuwanka? shi kuwa za ya amsa, 'An yi mani rauni tare da waɗanda ke gidan abokaina."'
7"Takobi! Motsa kanki gãba da makiyayina, mutumin da ya tsaya kusa da ni -- wannan furcin Yahweh ne - mai runduna. Bugi makiyayin, tumakin kuma zasu warwatse! Gama zan juya hannuna gãba da ƙasƙantattun.
8Daga nan zaya kasance game da wannan a cikin dukkan ƙasar --- wannan furcin Yahweh ne --- kashi biyu cikin uku za a datse! Waɗannan mutane zasu hallaka; kashi ɗaya cikin uku kawai zaya rage a wurin.9Kashi ɗayan da ya rage zan bi dasu ta cikin wuta in tãcesu kamar yadda ake tãce azurfa; zan gwada su kamar yadda ake gwada zinariya. Zasu kira bisa sunana, ni kuwa zan amsa masu in ce, 'Waɗannan mutanena ne!' su kuma zasu ce, 'Yahweh ne Allahna!"'

14

1Duba! Ranar Yahweh na zuwa da za a raba ganimarku a tsakiyarku.2Gama zan tattara dukkan al'umma tsayayya da Yerusalem domin yaƙi kuma za a ci birnin. Za a warwashe gidajensu kuma za a yiwa matayensu fyaɗe. Rabin birnin za ya tafi zuwa bautar talala, amma ragowar mutanen ba za a datse su ba daga birnin.

3Amma Yahweh zaya fita ya kuma jãdagar yaƙi da waɗannan al'ummai kamar yadda ya jãgadar yaƙi a ranar yaƙi.4A wannan rana tafin sawayensa zasu tsaya bisa Dutsen Zaitun, wanda yake gefen Yerusalem maso gabas. Za a raba Dutsen Zaitu kashi biyu tsakanin gabas da yamma ta kwari mai girma kuma sashe ɗaya na dutsen za shi janye zuwa arewa ɗaya sashen kuma za shi janye zuwa kudu.
5Sa'an nan zaku tsere zuwa cikin kwarin tsakanin duwatsun Yahweh, domin kwarin dake tsakanin duwatsun za ya kai har Azel. Zaku yi ta gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa a kwanakin Uzaya, sarkin Yahuda. Sa'an nan Yahweh Allahna za ya zo kuma dukkan tsarkaka zasu kasance tare dashi.
6A wannan ranar da ba za a sami haske ba, babu sanyi ko ƙanƙara.7A wannan ranar, Yahweh kaɗai ya san ta, ba za a sake yin rana ko dare ba, gama maraice za ya zama lokacin haske.8A wannan rana ruwayen rai za su ɓulɓulo daga Yerusalem. Rabin ruwan za shi yi gudu zuwa tekun gabas rabin kuwa zuwa tekun yamma, damina da lokacin sanyi.
9Yahweh zai zama sarki a bisa dukkan duniya. A wannan rana Yahweh kaɗai zai zama, Allah ɗaya, babu wani suna sai na sa.10Dukkan ƙasa za ta zama kamar Arabah, daga Geba har zuwa Rimon kudu da Yerusalem. Yerusalem zata ci gaba da haurawa bisa a mazamninta, daga Ƙofar Benyamin zuwa inda kofar ta ke a dã, zuwa Ƙofar Kusurwa, kuma zuwa Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsewar ruwan inabin sarki.11Mutane zasu zauna cikin Yerusalem kuma babu sauran hallaka da zata zo gare su daga wurin Allah. Yerusalem zata zauna cikin kariya.
12Wannan ita ce annobar da Yahweh zai hari dukkan al'umman da suka tayarwa Yerusalem da yaƙi: Naman jikinsu zai ruɓe lokacin da suke a tsaye bisa sawayensu. Idanunsu zasu ruɓe cikin kwarminsu kuma harsunansu zasu ruɓe daga cikin bakunansu.13A wannan rana babban tsoro daga Yahweh za shi abko masu. Kowannensu zai kama hannun wani, kuma hannun wani zai ɗaga hannunsa domin tsayayya da hannun wani.
14Yahuda kuma zai yi yaƙi da Yerusalem. Zasu tara dukiya daga al'umman dake zagaye dasu - zinariya, da azurfa da kuma kyawawan riguna tuli.15Annoba zata faɗo wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakai, da dukkan dabbobin da suke a sansaninsu zasu wahala da wannan annobar.
16Za shi zama kuma dukkan waɗanda suka rage cikin ƙasashen da suka zo yaƙi da Yerusalem a maimako zasu zo kowacce shekara domin su yi wa sarki sujada, Yahweh mai runduna, sụ kuma kiyaye Idin Bukkoki.17Za shi zama kuma idan wani daga cikin al'umman duniya ya kasa zuwa Yerusalem don ya yi sujada ga sarki, Yahweh mai runduna, daga nan Yahweh kuma ba zai aiko masu da ruwan sama ba.18Idan al'ummar Masar basu je ba, to ba zasu sami ruwan sama ba. Annoba daga Yahweh zata abko wa duk mutanen dasu ka ƙi zuwa domin su yi Bikin Idin Bukkoki.
19Wannan zai zama horon da za a yi wa Masar da kuma horo ga kowacce al'ummar da ba ta zo Yerusalem ta halarci Bikin Idin Bukkoki ba.
20Amma a wannan ranar, ƙararrawar dawakai zasu ce, "ku keɓe ga Yahweh," kuma darurrukan da suke gidan Yahweh zasu zama kamar darurruka a gaban bagadi.21Gama kowacce tukunya a Yerusalem da Yahuda za a ƙeɓeta ga Yahweh mai runduna kuma duk wanda zai kawo hadaya zai ci daga cikinsu ya kuma tafasa a cikinsu. A wannan rana 'yan kasuwa ba zasu ƙara kasancewa a cikin gidan Yahweh mai runduna ba.

Littafin malakai

1

1Furcin maganar Yahweh ga Isra'ila ta hannun Malakai.2"Na ƙaunace ku," inji Yahweh. Amma ku kun ce, "Ta yaya ka ƙaunace mu?"3"Ashe Isuwa ba ɗan'uwan Yakubu ba ne?" Yahweh ya furta. "Amma na ƙaunaci Yakubu, na ƙi Isuwa. Na maida tuddansa banza abin ƙi, kuma na maida gãdonsa muhallin diloli na daji."

4Idan Idomawa suka ce, "An buge mu har ƙasa, amma za mu sake tashi," Yahweh mai runduna zai ce, "Zasu sake tashi kuma su gina, zan kuma sake rushewa. Wasu zasu kirasu, 'Ƙasar masu mugunta' kuma 'Mutanen da Yahweh ya la'anta har abada.'5Idanuwanku zasu ga wannan, kuma zaku ce, Yahweh mai girma ne har ma a gaban iyakokin Isra'ila.'"
6Ɗa yana girmama ubansa, kuma bawa yana girmama ubangijinsa. Idan ni uba ne, ina ku ka girmama ni? Idan ni ubangijinku ne, me yasa ba ku ba ni daraja, inji Yahweh mai runduna ga ku firistoci, da ku ka rena sunana. "Amma kun ce ta yaya mu ka rena sunanka?'7Ta wurin miƙa ƙazantacciyar gurasa da kuke kawo wa bagadina. Amma kun ce, "Ta yaya mu ka ƙazantad da kai?"' Ta cewa teburin Yahweh marar daraja ne.
8A lokacin da kuka miƙa hadayun makafin dabbobi ashe wannan ba mugunta ba ce? Duk lokacin da ku ka miƙa hadayun guragun dabbobi da marasa lafiya, wannan ba mugun abu ba ne? Kwa ba da wannan ga gwamnanku! Zai karɓa ko zaku sami tagomashi a wurinsa?" inji Yahweh mai runduna.9Yanzu kuna ta neman fuskar Allah, domin ya yi mana alheri. Amma Yahweh mai runduna yace da irin wannan baikon a hannunku, zaku sami tagomashinsa?
10"Kash, ina ma da akwai wani daga cikinku wanda zai rufe ƙofofin haikali, don kada ku kunna wuta akan bagadina a banza! Domin ba na jin daɗinku," inji Yahweh mai runduna, "kuma ba zan karɓi kowanne baiko daga hannunku ba.11Daga fitowar rana har zuwa faɗuwarta sunana zai zama da girma a cikin al'ummai a dukkan wuraren da ake ƙona turare da kuma baye-baye masu tsabta da za a miƙa da sunana. Domin sunana zai zama da girma a cikin al'ummai," inji Yahweh mai runduna.12Amma kuna ɓata shi sa'ad da kuka ce teburi na Ubangiji ya ƙazance, kuma 'ya'yan itacensa da abincinsa abin reni ne.
13Kun kuma ce, 'kai wannan abin gajiyarwa ne,' kuma kun wulaƙanta shi," inji Yahweh mai runduna. "kun kawo dabbar da naman daji ya kama ko gurguwa ko marar lafiya; kuma wannan ku ka kawo a matsayin hadayarku. Ko zan karɓi wannan daga hannunku? inji Yahweh.14"Bari mayaudari ya zama la'ananne wanda ke da dabba namiji a garkensa kuma ya yi wa'adi zai bayar da ita gare ni, amma duk da haka, Ni da na ke Ubangiji, ya kawo mani hadayar nakasashiya! Gama ni babban sarki ne," inji Yahweh mai runduna, "kuma za a girmama sunana a cikin al'ummai."

2

1Yanzu ku firistoci, wannan umurni domin ku ne.2"Idan ba zaku saurara ba, kuma in ba zaku yi niyya a zuciyarku ku bani girma ba," inji Yahweh mai runduna, "lallai zan aiko da la'ana zuwa gare ku, kuma zan la'anta albarkunku. Hakika, na la'antar da su, domin ba ku sa dokokina a zuciyarku ba.

3Duba, ina shirin tsauta wa zuriyarku, kuma zan watsa kashin dabbobi a fuskokinku, wato kashin dabbobin bukukuwanku, kuma zan kore ku daga gare ni.4Za ku sani cewa ni na aiko da wannan umarni gare ku, kuma alƙawarina zai ci gaba da kasancewa tare da Lebi," inji Yahweh mai runduna.
5Alƙawarina da shi na rai da salama ne, kuma ni na ba dasu gare shi; Na sa ya girmama ni, kuma ya ji tsoro na, kuma ya darajanta sunana.6Umurnin gaskiya ya kasance a bakinsa, kuma ba a sami ƙarya a leɓunansa ba. Ya yi tafiya da ni a cikin salama da daidaituwa kuma ya juyo da yawa ga tuba daga zunubi.7Domin ya kamata leɓunan firist su kasance da sani kuma mutane su nemi koyarwa daga bakinsa, domin shi ɗan saƙon Yahweh mai runduna ne.
8Amma kun kauce daga hanyar gaskiya. Kun sa da yawa sun yi tuntuɓe game da koyarwar shari'a. Kun karya alƙawarin Lebiyawa," inji Yahweh mai runduna.9Haka ni ma na maishe ku marasa daraja kuma abin reni ga dukkan mutane, domin baku bi hanyoyina ba, maimakon haka kuka nuna son kai game da abin da aka umurta."
10Ashe dukkanmu ba uba ɗaya muke ba? Ba Allah ɗaya ne ya hallicce mu ba? Me ya sa muka zama marasa aminci kowanne ga ɗan'uwansa, mu na ƙazantar da alƙawarin iyayenmu?11Yahuda ya kasance marar aminci. An aikata mummunan abu cikin Isra'ila da Yerusalem. Gama Yahuda ya ƙazantar da wuri mai tsarki na Yahweh da yake ƙauna, kuma ya aure 'yar baƙon allah.12Bari Yahweh ya datse irin wannan mutum daga alfarwar Yakubu, ko wane ne shi, ko da ma mai kawo hadaya ga Yahweh mai runduna ne.
13Kuna kuma yin wannan: wato kuna rufe bagadin Yahweh da hawaye da kuka da ajiyar zuciya, domin ba ya kula da hadayunku ko karɓar su daga hannunku da tagomashi.
14Amma ku ka ce "Don me ya ƙi?" Domin Yahweh shaida ne tsakaninka da matarka ta ƙuruciya, wadda ka yi mata rashin aminci, ko da yake abokiyar tarayyarka ce da matarka ta alƙawari.15Ba shi ne ya yi su ɗaya daga ruhunsa ba? To me yasa ya maishe ku ɗaya? Saboda ya na neman 'ya'ya daga Allah. Don haka ku lura da kanku a cikin ruhunku, kada ka zama marar aminci ga matarka ta ƙuruciya.16"Gama na ƙi kisan aure," inji Yahweh, Allah na Isra'ila, "da kuma wanda ya rufe tufafinsa da husuma," inji Yahweh mai runduna. "To sai ku yi lura da kanku cikin ruhu don kada ku zama marasa aminci."
17Kun gajiyar da Yahweh da maganganunku. Amma kun ce "Ta yaya muka gajiyar da shi?" Ta cewa "Duk wanda ya yi mugunta managarci ne a idanun Yahweh, kuma yana jin daɗin su, ko "Ina Allah na adalci?"

3

1"Duba, na kusa aiko da manzona, kuma zai shirya mani hanya a gabana. Sa'an nan Ubangiji da kuke nema, zai zo haikalinsa ba zato. Manzon da aka alƙawarta, da kuke farinciki da shi, duba, zai zo," inji Yahweh mai runduna.2Amma wa zai jure ranar zuwansa? Wa zai iya tsayawa sa'ad da ya bayyana? Domin zai zama kamar wutar maƙera, kamar sabulun wanki.3Zai zama kamar mataci mai tace azurfa, zai tsarkake 'ya'yan Lebiyawa. Zai tace su kamar zinariya da azurfa, sa'an nan ne zasu kawo baikon adalci ga Yahweh.

4Sa'an nan ne baikon Yahuda da na Yerusalem zai gamshi Yahweh, kamar a kwanakin dă, a shekarun baya.5"Sa'an nan zan zo gare ku domin hukunci. Nan da nan zan zama shaida gãba da masu sihiri, da mazinata, da masu shaidar zur, da masu zaluntar ma'aikata wajen albashinsu, da masu cutar gwauraye, da marayu, da masu korar baƙi, da marasa girmama ni," inji Yahweh mai runduna.
6Domin ni Yahweh ban canza ba; saboda haka ne ku 'zuriyar Yakubu ba ku ƙare ba.7Tun daga zamanin ubanninku kun kauce daga bin farillaina ba ku kuma kiyaye su ba. Ku dawo gare ni, ni ma zan dawo gare ku," inji Yahweh mai runduna, "Amma kun ce, 'Ƙaƙa zamu dawo?'
8Mutum zai iya yi wa Allah fashi? Duk da haka kuna yi mani fashi. Amma kun ce, 'Ta yaya muka yi maka fashi?' A zakkoki da baye-baye.9La'anannu ne ku da la'ana, domin kuna yi mani fashi, dukkan al'umma.
10Ku kawo dukkan zakka a cikin ma'aji, domin a sami abinci a cikin gidana, ku gwada ni a wannan," inji Yahweh mai runduna, "idan ba zan buɗe maku tagogin sama, in zubo da albarku a kan ku, har ba wurin tara su.11Zan kwaɓi masu ɓarnata maku amfani domin su dena lalatar maku da amfanin ƙasarku. Gonakin inabinku ba zasu kakkaɓe 'ya'yansu ba, inji Yahweh mai runduna.12"Dukkan al'ummai zasu ce da ku masu albarka. Zaku zama ƙasa mai ban sha'awa," inji Yahweh mai runduna.
13"Maganganunku a kaina suna da ƙarfi," inji Yahweh. "Amma kuka ce, 'Me muka ce a tsakaninmu gãba da kai?'14Kun ce, "Ba amfani a bauta wa Allah. Wacce riba ce muka samu da yin biyayya da dokokinsa ko kuma da tafiya rai ɓace a gaban Yahweh mai runduna?15Yanzu muna kiran masu girman kai masu albarka. Masu aikata mugunta bama azurta kaɗai suke ba, amma har ma suna gwada Allah su kuɓuta."'
16Sai waɗanda ke jin tsoron Yahweh suka yi magana da junansu. Yahweh kuma ya ji su ya saurare su, sai aka rubuta littafin tunawa a gabansa game da waɗanda ke jin tsoron Yahweh masu girmama sunansa.
17"Zasu zama nawa," inji Yahweh mai runduna, dukiyata mai tamani, a ranar da zan yi wannan. Zan yi masu jinƙai, kamar yadda uba ya kan yi wa ɗansa jinƙai wanda yake bauta masa.18Sa'an nan ne kuma zaku bambance tsakanin adalai da miyagu da tsakanin masu bauta wa Allah da marasa bauta masa.

4

1Duba rana na zuwa, mai ƙuna kamar tanderu, inda dukkan masu girman kai da masu aikata mugunta zasu zama tattaka. Ranar dake zuwa zata ƙone su, "inji Yahweh mai runduna, "Baza ta bar masu tushe ko reshe ba"2Amma a gare ku ku dake tsoron sunana, ranar adalci zata fito da warkarwa a fukafukanta. Zaku fita, ku yi ta tsalle kamar 'yan maruka a dangwali.3A wannan rana zaku tattake mugaye, zasu zama tattaka a ƙarƙashin sawayenku a ranar da zan aikata wannan", inji Yahweh mai runduna.

4"Ku tuna da koyarwar bawana Musa wadda na ba shi a Horeb domin dukkan Isra'ila, farillai ne da dokoki.5Duba, zan aiko ma ku da annabi Iliya kafin babbar ranar nan mai tsoratar wa ta Yahweh.6Zai juyar da zuciyar ubanni zuwa wajen 'ya'ya, da zuciyar 'ya'ya zuwa ga ubanninsu, domin kada in kawo hari in hallakar da ƙasar ɗungum."

Matiyu

1

1Littafin asalin Yesu Almasihu Dan Dauda, Dan Ibrahim. 2Ibrahim shine mahaifin Ishaku, Ishaku shine mahaifin Yakubu, Yakubu shine mahaifin Yahuza da 'yan'uwansa. 3Yahuza shine mahaifin Farisa da Zera, ta wurin Tamar. Farisa kuma shine mahaifin Hasruna, Hasruna kuma shine mahaifin Aram.

4Aram shine mahaifin Amminadab, Amminadab shine mahaifin Nashon, Nashon shine mahaifin Salmon. 5Salmon shine mahaifin Bo'aza ta wurin Rahab, Bo'aza shine mahaifin Obida ta wurin Rut. Obida shine mahaifin Yesse, 6Yesse shine mahaifin sarki Dauda. Sarki Dauda shine mahaifin Sulaimanu ta wurin matar Uriya.
7Sulaimanu shine mahaifin Rehobo'am, Rehobo'am shine mahaifin Abija, Abija shine mahaifin Asa. 8Asa shine mahaifin Yehoshafat, Yehoshafat shine mahaifin Yoram, Yoram kuma shine mahaifin Uziya.
9Uziya shine mahaifin Yotam, Yotam shine mahaifin Ahaz, Ahaz shine mahaifin Hezekiya. 10Hezekiya shine mahaifin Manassa, Manassa shine mahaifin Amon, sannan Amon shine mahaifin Yosiya. 11Yosiya shine mahaifin Yekoniya da 'yan'uwansa, dai dai locacin da aka kwashe su zuwa kasar Babila.
12Bayan kwasar su zuwa kasar Babila, Yekoniya shine mahaifin Sheyaltiyel, Sheyaltiyel shine mahaifin Zarubabel. 13Zarubabel shine mahaifin Abihudu, Abihudu shine mahaifin Eliyakim, sannan Eliyakim shine mahaifin Azuru. 14Azuru shine mahaifin Saduku. Saduku shine mahaifin Akimu, sannan Akimu shine mahaifin Aliyudu
15Aliyudu shine mahaifin Ali'azara, Ali'azara shine mahaifin Matana, sannan Matana shine mahaifin Yakubu. 16Yakubu shine mahaifin Yusufu maigidan Maryamu, wadda ta wurin ta ne aka haifi Yesu, wanda ake ce da shi Almasihu.17Tun daga Ibrahim zuwa Dauda, an yi tsara goma sha hudu ne, daga Dauda zuwa lokacin da aka kwashe su zuwa Babila, tsara goma sha hudu ne, sannan daga lokacin da aka kwashe su zuwa Babila zuwa Almasihu tsara goma sha hudu ne
18Ga yadda haihuwar Yesu Almasihu ta kasance. Mahaifiyarsa, Maryamu, tana tashi da Yusufu, amma kafin su yi aure, sai aka same ta da juna biyu ta wurin Ruhu Mai Tsarki. 19Mijinta, Yusufu, adalin mutum ne, amma ba ya so ya kunyatar da ita a sarari. Sai ya yi shawara ya sake ta a asirce.
20Yana cikin tunanin wadannan al'amura, sai mala'ikan Ubangiji ya bayyana gareshi a mafarki, ya ce masa, "Yusufu, dan Dauda, kada ka ji tsoron daukar Maryamu a matsayin matarka. Gama abinda ke cikinta, ta wurin Ruhu Mai Tsarki aka same shi. 21Za ta haifi Da, za ka kira sunansa Yesu, domin za ya ceci mutanensa daga zunubansu."
22Duk wannan ya faru ne domin a cika abinda aka fada ta bakin annabin, cewa, 23"Duba, budurwa za ta sami juna biyu sannan za ta haifi da, za su kira sunansa Immanuel"-ma'ana, "Allah tare da mu."
24Yusufu ya farka daga barci, ya yi kamar yadda mala'ikan Ubangiji ya umarce shi, sai ya dauke ta a matsayin matarsa. 25Amma Yusufu bai sadu da ita ba sai bayan da ta haifi da. Ya kira sunansa Yesu.

2

1Bayanda aka haifi Yesu a Baitalami ta kasar Yahudiya, a zamanin sarki Hirudus, sai ga wadansu masana daga gabas suka zo Urushalima, suna cewa, 2"Ina wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Mun ga tauraronsa a gabas mun kuma zo mu yi masa sujada." 3Da sarki Hirudus ya ji haka, sai ya damu kwarai, haka kuma dukan mutanen Urushalima.

4Hirudus ya tara dukan manyan firistoci da marubuta na jama'a, ya tambaye su, "Ina za a haifi Almasihun?" 5Suka ce masa, "A Baitalami ne ta kasar Yahudiya, domin haka annabin ya rubuta, 6'Ke kuma, Baitalami, ta kasar Yahudiya, ba ke ce mafi kankanta ba a cikin shugabanin Yahudiya, domin daga cikin ki mai mulki zai fito wanda zai zama makiyayin jama'a ta Isra'ila.'"
7Sai Hirudus ya kira masanan a asirce ya tambaye su aininhin lokacin da tauraron ya bayyana. 8Ya aike su Baitalami, ya ce, "Ku je ku binciko mani dan yaron da kyau. Idan kun same shi, ku kawo mani labari, don ni ma in je in yi masa sujada."
9Bayan sun ji maganar sarkin, sai suka yi tafiyar su, ga shi kuwa, tauraron da suka gani a gabas yana tafe a gaban su, har ya zo ya tsaya bisa inda dan yaron nan yake. 10Da suka ga tauraron, sai suka yi matukar farin ciki.
11Sai suka shiga gidan, suka ga dan yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka rusuna gabansa suka yi masa sujada. Sa'an nan suka kwance kayansu, suka mika masa kyautar su ta zinariya da lubban, da mur. 12Allah kuma ya gargade su a mafarki kada su koma wurin Hirudus, sai suka koma kasarsu ta wata hanya dabam.
13Bayan sun tashi, sai ga wani mala'ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusufu a mafarki, ya ce, "Tashi, ka dauki dan yaron da mahaifiyarsa, ka gudu zuwa kasar Masar, ka zauna a can sai na fada maka, don Hirudus yana shirin binciko dan yaron ya hallaka shi." 14A wannan dare fa Yusufu ya tashi ya dauki dan yaron da mahafiyarsa ya tafi Masar. 15Ya zauna a can har mutuwar Hirudus. Wannan kuwa domin a cika abin da Ubangiji ya fada ne ta bakin annabin, "Daga Masar na kirawo Da na."
16Da Hirudus ya ga masanan nan sun shashantar da shi, sai ya hasala kwarai, ya aika a karkashe dukan 'yan yara maza da suke Baitalami da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa kasa, gwargwadon lokacin da ya tabbatar a gun masanan.
17A lokacin ne aka cika fadar Annabi Irmiya, 18"An ji wata murya a Rama, tana kuka da bakin ciki mai zafi, Rahila ce take kuka saboda 'ya'yanta, kuma ta ki ta ta'azantu, domin ba su.
19Sa'adda Hirudus ya mutu, sai ga mala'ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusufu a mafarki a Masar ya ce, 20"Tashi ka dauki dan yaron da mahaifiyarsa, ka tafi kasar Isra'ila, domin masu neman ran dan yaron sun mutu." 21Yusufu ya tashi, ya dauki dan yaron da mahaifiyarsa, ya zo kasar Isra'ila.
22Amma da ya ji Arkilayus ya gaji mahaifinsa Hirudus, yana mulkin kasar Yahudiya, sai ya ji tsoron isa can. Bayan da Allah ya yi masa gargadi a mafarki, sai ya ratse zuwa kasar Galili 23sai ya je ya zauna a wani gari da ake kira Nazarat. Wannan ya cika abin da aka fada ta bakin annabawa, cewa, za a kira shi Banazare.

3

1A kwanakin nan Yahaya Mai baftisma ya zo, yana wa'azi a jejin Yahudiya yana cewa, 2"Ku tuba, domin mulkin sama ya kusa." 3Wannan shine wanda annabi Ishaya ya yi maganarsa, ya ce, "Muryar wani mai kira a jeji yana cewa, 'Ku shirya wa Ubangiji hanyarsa, ku daidaita tafarkunsa."

4Yahaya kuwa yana sanye da tufa ta gashin rakumi, yana kuma daure da damarar fata, abincinsa kuwa fara ne da zuman jeji. 5Sai mutanen Urushalima, da na dukan Yahudiya, da na duk kasashen bakin Kogin Urdun, suka yi ta zuwa wurin sa. 6Ya yi masu baftisma a Kogin Urdun, yayinda suke furta zunubansu.
7Amma da ya ga Farisawa da Sadukiyawa da yawa, suna fitowa domin a yi masu baftisma, sai ya ce masu, "Ku 'ya'yan macizai masu dafi, wa ya gargade ku ku guje wa fushi mai zuwa? 8Ku ba da 'ya'ya da za su nuna tubanku. 9Kada kuwa ku dauka a ranku cewa, 'Ibrahim ne ubanmu.' Domin ina gaya maku, Allah yana da iko ya ta da wa Ibrahim 'ya'ya daga cikin duwatsun nan.
10Ko yanzu ma an sa gatari a gindin bishiyoyin. Saboda haka duk bishiyar da ba ta ba da 'ya'ya masu kyau ba, sai a sare ta a jefa a wuta. 11Na yi maku baftisma da ruwa, zuwa tuba. Amma mai zuwa baya na, ya fi ni girma, wanda ko takalmansa ma ban isa in dauka ba. Shi ne zai yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki, da kuma wuta. 12Kwaryar shikarsa na hannunsa, zai kuwa share masussukarsa sarai, ya tara alkamarsa ya sa a rumbunsa, amma zai kona buntun da wutar da ba za a iya kashewa ba."
13Sai Yesu ya zo daga kasar Galili, ya je Kogin Urdun wurin Yahaya, domin ya yi masa baftisma. 14Amma Yahaya ya yi ta kokarin ya hana shi, yana cewa, "Ni da nake bukatar ka yi mani baftisma, ka zo gare ni?" 15Yesu ya amsa masa ya ce, "Bari ya zama haka a yanzu, domin a cika dukan adalci." Sai Yahaya ya yarje masa.
16Bayan da aka yi masa baftisma, Yesu ya fito nan da nan daga cikin ruwan, sai kuma sammai suka bude masa. Ya ga Ruhun Allah yana saukowa kamar kurciya, ya sauko a kansa. 17Duba, wata murya daga sammai tana cewa, "Wannan shi ne kaunataccen Da na. Wanda ya gamshe ni sosai."

4

1Sa'an nan Ruhu ya bi da Yesu zuwa cikin jeji, domin Ibilis ya gwada shi. 2Da ya yi azumi kwana arba'in dare da rana, daga baya yunwa ta kama shi. 3Sai mai jarabtar nan ya zo, ya ce masa, "Idan kai Dan Allah ne, ka umarci duwatsun nan su zama gurasa." 4Amma Yesu ya amsa ya ce masa, "A rubuce yake cewa, 'Ba da gurasa kadai mutum zai rayu ba, sai dai da kowace magana da ta ke fitowa daga wurin Allah.'"

5Sa'an nan Ibilis ya kai shi tsattsarkan birni ya dora shi can kan kololuwar ginin haikali, 6ya ce masa, "In kai Dan Allah ne, to dira kasa. Domin a rubuce yake cewa, 'Zai ba mala'ikunsa umarni game da kai,' kuma, 'Za su daga ka da hannuwansu, domin kada ka yi tuntube da dutse.'"
7Yesu ya ce masa, "kuma a rubuce yake, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'" 8Kuma, sai Ibilis ya kai shi kan wani dutse mai tsawo kwarai, ya nuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu. 9Ya ce masa, "Dukan wadannan zan baka idan ka rusuna ka yi mani sujada."
10Sai Yesu ya ce masa, "Tafi daga nan, Shaidan! Domin a rubuce yake, 'Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kadai za ka bauta wa.'" 11Sa'an nan Ibilis ya rabu da shi, sai kuma mala'iku suka zo suka yi masa hidima.
12To, da Yesu ya ji an kama Yahaya, sai ya tashi zuwa kasar Galili. 13Ya bar Nazarat, ya koma Kafarnahum da zama, can bakin tekun Galili, kan iyakar kasar Zabaluna da Naftali.
14Wannan ya faru domin a cika fadar annabi Ishaya cewa, 15"Kasar Zabaluna da kasar Naftali, ta bakin teku, da hayin Kogin Urdun, Galili ta al'ummai! 16Mutane mazauna duhu suka ga babban haske, sannan ga wadanda ke zaune a yankin da inuwar mutuwa, haske ya keto masu."
17Daga lokacin nan, Yesu ya fara wa'azi, yana cewa, "Ku tuba domin mulkin sama ya kusa."
18Yana tafiya a bakin tekun Galili, sai ya ga wadansu 'yan'uwa biyu, Saminu da ake kira Bitrus, da dan'uwansa Andarawas, suna jefa taru a teku, domin su masunta ne. 19Yesu ya ce masu, "Ku zo, ku biyo ni, zan mai da ku masuntan mutane." 20Nan da nan sai suka bar tarunsu, suka bi shi.
21Da Yesu ya ci gaba da tafiya, sai ya ga wadansu mutum biyu, su kuma 'yan'uwa ne, Yakubu dan Zabadi, da dan'uwansa Yahaya, suna cikin jirgi tare da mahaifinsu Zabadi, suna gyaran tarunsu. Sai ya kira su. 22Nan take suka bar mahaifinsu da jirgin, suka bi shi.
23Yesu ya zazzaga dukan kasar Galili, yana koyarwa a majami'unsu, yana shelar bisharar mulkin, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiya a cikin mutane. 24Labarinsa ya bazu a cikin dukan kasar Suriya, kuma mutanen suka kakkawo masa dukan marasa lafiya, masu fama da cuta iri iri, da masu shan azaba, da kuma masu aljannu, da masu farfadiya, da shanyayyu. Yesu ya warkar da su. 25Taro masu yawa suka bi shi daga kasar Galili, da Dikafolis, da Urushalima, da kasar Yahudiya, har ma daga hayin Urdun.

5

1Da Yesu ya ga taron jama'ar, sai ya hau saman dutse. Sa'adda ya zauna, almajiransa suka zo wurinsa. 2Ya bude bakinsa kuma ya koyar da su, yana cewa, 3"Albarka ta tabbata ga masu talauci a ruhu, domin mulkin sama nasu ne. 4Albarka ta tabbata ga masu makoki, domin za a ta'azantar da su.

5Albarka ta tabbata ga masu tawali'u, domin za su gaji duniya. 6Albarka ta tabbata ga masu yunwa da kishin adalci, domin za a kosar da su. 7Albarka ta tabbata ga masu jinkai, domin za su samu jinkai. 8Albarka ta tabbata ga masu tsabtar zuciya, domin za su ga Allah.
9Albarka ta tabbata ga masu kawo salama, domin za a ce da su 'ya'yan Allah. 10Albarka ta tabbata ga wadanda ake tsananta masu saboda adalci, domin mulkin sama nasu ne.
11Masu albarka ne ku sa'adda mutane suka zage ku, suka kuma tsananta maku, ko kuwa suka zarge ku da dukan miyagun abubuwa iri iri na karya, saboda ni. 12Ku yi murna da matukar farin ciki, domin sakamakonku mai yawan gaske ne a sama. Ta haka ne mutane suka tsananta wa annabawa da suka yi rayuwa kafin ku.
13Ku ne gishirin duniya, amma idan gishiri ya sane yaya za a mai da dandanonsa? Ba zai kara anfani ga komai ba, sai ko a zubar da shi, a tattake a karkashin kafafun mutane. 14Ku ne hasken duniya, birnin da ke kan tudu ba shi boyuwa.
15Mutane ba za su kunna fitila su sa ta karkashin kwando ba, sai ko a dora ta a mazaunin ta, domin ta ba da haske ga kowa da ke gidan. 16Bari hasken ku ya haskaka gaban mutane yadda za su ga kyawawan ayyukanku su kuma yabi Ubanku da ke cikin sama.
17Kada ku yi tsammanin na zo ne domin in rushe shari'a ko annabawa. Ban zo domin in rushe su ba, amma domin in cika su. 18Domin gaskiya ina gaya maku, har sama da kasa su shude, amma digo ko wasali daya ba za ya shude ba a cikin shari'ar, sai an cika dukan al'amura.
19Saboda haka duk wanda ya karya mafi kankanta daga cikin dokokin nan ko kuwa ya koya wa wasu su yi haka, za a kira shi mafi kankanta a cikin mulkin sama. Amma dukan wanda ya kiyaye su ko kuwa ya koyar da su, za a kira shi mafi girma a cikin mulkin sama. 20Gama ina gaya maku cewa idan adalcin ku bai zarce adalcin marubuta da Farisawa ba, babu yadda za ku shiga mulkin sama.
21Kun ji dai an ce wa mutanen da, 'Kada ka yi kisan kai,' kuma 'Duk wanda ya yi kisan kai yana cikin hatsarin hukunci.' 22Amma ina gaya muku, duk wanda ya yi fushi da dan'uwansa, yana cikin hatsarin hukunci. Kuma duk wanda ya ce da dan'uwansa, 'Kai mutumin banza!' yana cikin hatsarin tsayawa gaban majalisa, kowa kuma ya ce da dan'uwan sa 'Kai wawa!' yana cikin hatsarin shiga wutar jahannama.
23Saboda haka idan za ka yi baiko a bagadi sai ka tuna cewa dan'uwanka yana da damuwa da kai, 24ka bar baikon ka a gaban bagadin, ka yi tafiyarka. Da farko dai, ka sasanta da dan'uwanka kafin ka zo ka mika baikon.
25Ka yi sulhu da mai karar ka tun kana hanyar zuwa gaban shari'a, domin kada mai karar ka ya mika ka ga alkali, alkali kuwa ya mika ka ga dogarai, za a kuwa jefa ka a kurkuku. 26Gaskiya ina gaya maka, ba za ka taba fita daga can ba sai ko ka biya dukan kudin da ya ke binka.
27Kun dai ji an ce, 'Kada ka yi zina'. 28Amma ina gaya maku, duk wanda ya dubi mace, da muguwar sha'awa, ya riga ya yi zina da ita a zuciyarsa.
29Idan idonka na dama zai sa ka tuntube, kwakule shi ka jefar daga gareka. Don gara daya daga cikin gabobinka ya halaka, da a jefa dukan jikin ka a jahannama. 30Ko kuwa idan hannunka na dama zai sa ka tuntube, ka yanke shi ka jefar daga gare ka. Domin gara daya daga cikin gabobin ka ya halaka, da a jefa dukan jikinka a jahannama.
31An sake fada, 'Duk wanda ya kori matarsa, sai ya ba ta takaddar saki.' 32Amma ina gaya maku ko wa ya saki matarsa, idan ba a kan laifin lalata ba, ya mai da ita mazinaciya kenan. Kuma duk wanda ya aure ta bayan sakin, ya yi zina kenan.
33Kun sake ji an ce wa wadan da suke a zamanin da, 'Kada ku yi rantsuwar karya, amma ku yi rantsuwar ku ga Ubangiji.' 34Amma ina gaya maku, kada ku yi rantsuwa sam, ko da sama domin kursuyin Allah ne; 35ko kuwa da duniya, domin mazaunin kafafunsa ne, ko da Urushalima, domin birnin babban sarki ne.
36Ko ma ace ku yi rantsuwa da kanku, domin ba za ku iya mai da gashin kanku baki ko fari ba. 37Amma bari maganarku ta zama 'I, I', ko kuwa 'A'a, a'a.' Duk abin da ya wuce wannan, daga mugun yake.
38Kun dai ji an ce, "Ido a maimakon ido, hakori kuma a maimakon hakori.' 39Amma ina gaya maku, kada ku yi jayayya da wanda ke mugu, a maimakon haka, ko wa ya mare ku a kuncin dama, ku juya masa dayan ma.
40Idan wani yana da niyyar kai kararku gaban shari'a saboda ya karbi rigarku, ku ba wannan mutumin mayafinku ma. 41Duk wanda ya tilasta ku ga tafiyar mil daya, ku je da shi biyu. 42Ku ba kowa da ya tambaye ku, kuma kada ku hana kowa da ke neman rance a wurinku.
43Kun ji abin da aka fada, 'Za ka kaunaci makwabcin ka ka ki magabcin ka.' 44Amma ina gaya maku, ku kaunaci magabtan ku, ku yi addu'a domin masu tsananta maku, ku albarkaci wadanda suka la'ance ku, ku yi alheri ga wadanda suke kin ku, 45domin ku zama 'ya'yan Ubanku da ke cikin sama. Domin yakan sa rana ta haskaka wa mugu da mutumin kirki, kuma yakan aiko da ruwan sama ga adali da azzalumi.
46Domin idan kuna kaunar wadanda suke kaunarku, wanne lada kuka samu? Ba haka masu karban haraji ma suke yi ba? 47Kuma in kun gaida 'yan'uwanku kadai, me kuke yi fiye da sauran? Ba hakanan al'ummai ma suke yi ba? 48Saboda haka, lalle ne ku zama cikakku, kamar yadda Ubanku na sama yake cikakke.

6

1Ku yi hankali kada ku yi ayyukan adalcinku gaban mutane domin su ganku, idan kun yi haka, ba za ku sami sakamako a wurin Ubanku da yake sama ba. 2Saboda haka, in za ku yi sadaka, kada ku busa kaho yadda munafukai suke yi a majami'u da kuma akan tituna domin mutane su yabesu. Gaskiya ina gaya maku, sun samu ladansu.

3Amma in za ku yi sadaka, kada hannunku na hagu ya san abin da hannunku na dama yake yi, 4domin sadakarku ta zama a asirce. Ubanku kuwa da yake ganin abin da ake yi a asirce, zai saka maku.
5Sa'adda za ku yi addu'a kuma, kada ku zama kamar munafukai, domin sun cika son yin addu'a a tsaye a majami'unsu da kuma a gefen tituna, domin mutane su gansu. Gaskiya ina gaya maku, sun sami ladarsu kenan. 6Amma ku, idan za ku yi addu'a, sai ku shiga cikin daki. Ku rufe kofa, ku yi addu'a ga Ubanku wanda yake a asirce, Ubanku kuwa da ke ganin abin da ake yi a asirce, zai saka maku. 7Idan za ku yi addu'a, kada ku yi ta maimaici marar anfani, kamar yadda al'ummai suke yi, domin a tunanin su za a saurare su saboda yawan maganganunsu.
8Domin haka, kada ku zama kamarsu, domin Ubanku ya san bukatar ku tun kafin ku roke shi. 9Saboda haka sai ku yi addu'a kamar haka: 'Ubanmu da ke sama, bari a tsarkake sunanka. 10Bari mulkinka shi zo. Bari nufinka ya yiwu a duniya kamar yadda ake yi a sama.
11Ka ba mu yau abincinmu na kullum. 12Ka gafarta mana basussukanmu, kamar yadda mu ma muke gafarta ma wadanda muke bi bashi. 13Kuma kada ka kawo mu cikin jaraba, amma ka kubutar da mu daga Mugun.' 1
14Domin in kun yafe wa mutane laifuffukansu, Ubanku na Sama shima zai yafe maku. 15In kuwa ba ku yafe wa mutane laifuffukansu ba, Ubanku ma ba zai yafe muku laifuffukanku ba."
16Haka kuma, in za ku yi azumi, kada ku zama da fuska kamar masu makoki yadda munafukai ke yi, domin sukan yankwane fuskokinsu, domin su bayyana ga mutane kamar suna azumi. Gaskiya, ina gaya maku, sun sami ladansu ke nan. 17Amma in kuna azumi, ku shafa mai a ka, ku kuma wanke fuska, 18don kada mutane su gane kuna azumi, sai dai Ubanku da yake a asirce. Kuma Ubanku da ke ganin abinda ke a asirce, zai saka maku."
19"Kada ku tara wa kanku dukiya a duniya, inda asu da tsatsa ke batawa, inda barayi kuma ke fasawa su yi sata. 20Maimakon haka, ku tara wa kanku dukiya a sama, inda babu asu da tsatsa da za su bata, inda kuma ba barayi da za su fasa su yi sata. 21Domin inda dukiyar ka take, a nan zuciyar ka ma take.
22Ido shi ne fitilar jiki. Saboda haka, idan idonka na da kyau, dukan jiki na cike da haske. 23Amma in idonka na da lahani, dukan jiki na cike da duhu. Saboda haka, in hasken da yake cikinka duhu ne, ina misalin yawan duhun! 24Ba mai iya bauta wa iyayengiji biyu, ko dai ya ki daya, ya so daya, ko kuma ya amince wa dayan ya raina dayan. Ba dama ku bauta wa Allah da kuma dukiya.
25Saboda haka ina gaya maku, kada ku damu a kan rayuwarku, game da abin da za ku ci, da abin da za ku sha- ko kuwa jikinku, abin da za ku yi tufafi da shi. Ashe rai bai fi abinci ba, jiki kuma bai fi tufafi ba? 26Ku dubi tsuntsayen da ke sararin sama. Ai, ba su shuka, balle girbi, ba su kuma tarawa a cikin rumbuna, amma Ubanku na Sama na ciyar da su. Ashe, ba ku fi su martaba ba?
27Kuma wanene a cikinku, don damuwarsa, zai iya kara ko taki ga tsawon rayuwarsa? 28To, don me kuke damuwa a kan tufafi? Ku dubi furannin jeji, yadda suke girma. Ba su aiki, kuma ba su sakar kaya. 29Duk da haka ina gaya maku, ko Sulaimanu ma, cikin dukan daukakar sa bai yi ado kamar daya daga cikin wadannan ba.
30Idan Allah yayi wa ciyawar jeji ado, wadda yau tana wanzuwa, gobe kuwa a jefa ta cikin murhu, ina misalin adon da za ya yi maku, ya ku masu karancin bangaskiya? 31Don haka kada ku damu, kuna cewa, 'Me za mu ci? ko, Me za mu sha?' ko kuwa, 'Wadanne tufafi za mu sa?'
32Ai, al'ummai ma suna neman dukan irin wadannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa ya san kuna bukatarsu. 33Amma ku nemi mulkinsa da farko da adalcinsa, kuma dukan wadannan abubuwa za a baku. 34"Saboda haka kada ku damu don gobe, ai, gobe za ta damu da kanta. Kowace rana ta na cike da wahalarta".


1Mafi kyawun kwafin kwafi ba su da Gama mulki da iko da daukaka naka ne har abada. Amin .

7

1Kada ku yi hukunci, domin ku ma kada a hukunta ku. Domin da irin hukuncin da ku kan hukunta da shi za a hukunta ku. 2Mudun da kukan auna, da shi za a auna maku.

3Don me kake duban dan hakin da ke idon dan'uwanka, amma ba ka kula da gungumen da ke naka idon ba? 4Ko kuwa yaya za ka iya ce wa dan'uwanka, 'Bari in cire maka dan hakin da ke idon ka,' alhali ga gungume a cikin naka idon? 5Kai munafiki! Ka fara cire gungumen da ke idonka, sa'annan za ka iya gani sosai yadda za ka cire dan hakin da ke idon dan'uwanka.
6Kada ku ba karnuka abin da ke tsattsarka. Kada kuma ku jefa wa aladu, lu'u lu'anku. Idan ba haka ba za su tattake su a karkashin sawunsu, su kuma juyo su kekketa ku.
7Roka, kuma za a ba ku. Nema, kuma za ku samu. Kwankwasa kuma za a bude maku. 8Ai duk wanda ya roka, zai karba, kuma duk wanda ya nema zai samu, wanda ya kwankwasa kuma za a bude masa. 9Ko, kuwa wane mutum ne a cikin ku, dan sa zai roke shi gurasa, ya ba shi dutse? 10Ko kuwa in ya roke shi kifi, zai ba shi maciji?
11Saboda haka, idan ku da ku ke miyagu, kun san yadda za ku ba da kyautai masu kyau ga 'ya'yanku, ina kimanin yadda Ubanku na sama zai ba da abubuwa masu kyau ga duk wadanda suke rokon sa? 12Saboda haka, duk abinda ku ke so mutane su yi maku, ku ma sai ku yi masu, domin wannan shi ne dukan shari'a da koyarwar annabawa.
13Ku shiga ta matsattsiyar kofa, don kofar zuwa hallaka na da fadi, hanyar ta mai saukin bi ce, masu shiga ta cikin ta suna da yawa. 14Domin kofar zuwa rai matsattsiya ce, hanyar ta mai wuyar bi ce, masu samun ta kuwa kadan ne.
15Ku kula da annabawan karya, wadanda su kan zo maku da siffar tumaki, amma a gaskiya kyarketai ne masu warwashewa. 16Za ku gane su ta irin "ya'yansu. Mutane na cirar inabi a jikin kaya, ko kuwa baure a jikin sarkakkiya? 17Haka kowanne itace mai kyau yakan haifi kyawawan 'ya'ya, amma mummunan itace kuwa yakan haifi munanan 'ya'ya.
18Kyakkyawan itace ba zai taba haifar da munanan 'ya'ya ba, haka kuma mummunan itace ba zai taba haifar da kyawawan 'ya'ya ba. 19Duk itacen da ba ya ba da 'ya'ya masu kyau, sai a sare shi a jefa a wuta. 20Domin haka, ta irin 'ya'yansu za a gane su.
21Ba duk mai ce mani, 'Ubangiji, Ubangiji,' ne, zai shiga mulkin sama ba, sai dai wanda ya yi nufin Ubana da yake cikin sama. 22A ranar nan da yawa za su ce mani, 'Ubangiji, Ubangiji,' ashe ba mu yi annabci da sunanka ba, ba mu fitar da aljanu da sunanka ba, ba mu kuma yi manyan ayyuka masu yawa da sunanka ba?' 23Sa'annan zan ce masu 'Ni ban taba saninku ba! Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta!'
24Saboda haka, dukan wanda yake jin maganata, yake kuma aikata ta, za a kwatanta shi da mutum mai hikima, wanda ya gina gidan sa a bisa dutse. 25Da ruwa ya sauko, ambaliyar ruwa ta zo, iska ta taso ta buga gidan, amma bai fadi ba, domin an gina shi bisa dutse.
26Amma duk wanda ya ji maganar nan tawa, bai aikata ta ba, za a misalta shi da wawan mutum da ya gina gidansa a kan rairayi. 27Ruwa ya sauko, ambaliyar ruwa ta zo, sai iska ta taso ta buga gidan. Sai kuma ya rushe, ya kuwa yi cikakkiyar ragargajewa."
28Ya zama sa'adda Yesu ya gama fadin wadannan maganganu, sai taro suka yi mamakin koyarwarsa, 29Domin yana koya masu da iko, ba kamar marubuta ba.

8

1Da Yesu ya sauko daga dutsen, sai taro masu yawa suka bi shi. 2Sai wani kuturu ya zo gunsa ya yi masa sujada, ya ce, "Ubangiji, in dai ka yarda, za ka iya tsarkake ni." 3Yesu ya mika hannunsa ya taba shi, ya ce, "Na yarda, ka tsarkaka." Nan da nan aka tsarkake shi daga kuturtarsa.

4Yesu ya ce masa, 'Ka tabbata, ba ka gaya wa kowa komai ba. Sai dai ka je ka nuna kan ka ga firist, ka kuma bayar da baiko da Musa ya umarta domin shaida garesu?
5Da Yesu ya shiga kafarnahum, sai wani hafsa ya zo gunsa ya roke shi, 6Ya ce, Ubangiji, bawana na kwance shanyayye a gida, yana shan azaba kwarai." 7Yesu ya ce masa, "Zan zo in warkar da shi."
8Sai hafsan, ya ce, "Ubangiji, ban isa har ka zo gida na ba, amma sai ka yi magana kawai, bawana kuwa zai warke. 9Domin ni ma ina karkashin ikon wani ne, ina kuma da sojoji a karkashina, sai in ce wa wannan, 'je ka,' sai ya je, wani kuma in ce masa, 'zo,' sai ya zo, in ce wa bawa na, 'yi abu kaza,' sai ya yi," 10Da Yesu ya ji haka, sai ya yi mamaki, har ya ce wa mabiyansa, "Gaskiya, ina gaya maku, ko a cikin isra'ila ban taba samun bangaskiya mai karfi irin wannan ba.
11Na gaya maku, da yawa za su zo daga gabas da yamma, su zauna cin abinci tare da Ibrahim da Ishaku, da Yakubu a cikin mulkin sama. 12Amma 'ya'yan mulkin kuwa sai a jefa su cikin matsanancin duhu. Can za su yi kuka da cizon hakora." 13Yesu ya ce wa hafsan, "Je ka! Bari ya zamar maka gwargwadon bangaskiyar da ka yi," A daidai wannan sa'a bawansa ya warke.
14Da Yesu ya shiga gidan Btrus, sai ya ga surukar Bitrus tana kwance da zazzabi. 15Yesu ya taba hannunta, zazzabin ya sake ta, ta kuma tashi ta fara yi masa hidima.
16Da maraice ya yi, sai mutanen suka kakkawo wa Yesu masu aljanu da yawa. Da magana kawai ya fitar da aljanun, ya kuma warkar da dukan marasa lafiya. 17Ta haka kuwa maganar annabi Ishaya ta samu cika cewa, "Shi da kansa ya debe rashin lafiyar mu, ya dauke cututtukan mu."
18Sa'adda Yesu ya ga taro masu yawa kewaye da shi, sai ya ba da umarni su tafi su koma wancan hayi na tekun Galili. 19Sai wani marubuci ya zo ya ce masa, "Malam, zan bi ka duk inda za ka je." 20Yesu ya ce masa, "Yanyawa suna da ramukansu, tsuntsayen sama kuma da shekunan su, amma Dan mutum ba shi da wurin da zai kwanta."
21Wani cikin almajiran ya ce masa, "Ubangiji, ka bar ni tukuna in je in binne mahaifina." 22Amma Yesu ya ce masa, "Bari matattu su binne matattunsu."
23Da Yesu ya shiga jirgi, almajiransa suka bi shi. 24Sai ga wata babbar iska ta taso a tekun, har rakuman ruwa suka fara shan kan jirgin. Amma Yesu yana barci. 25Sai almajiran sa suka je suka tashe shi, suka ce, "Ubangiji, ka cece mu, za mu hallaka!"
26Yesu ya ce masu, "Don me kuka firgita haka, ya ku masu karancin bangaskiya?" Sa'annan ya tashi, ya tsauta wa iskar da tekun. Sai wurin gaba daya ya yi tsit. 27Mutanen suka yi al'ajibi, suka ce, "Wanne irin mutum ne wannan, wanda har iska da teku ma suke masa biyayya?".
28Da Yesu ya zo daga wancan hayin a kasar Garasinawa, mutane biyu masu al'janu suka fito suka same shi. Suna fitowa daga makabarta kuma suna da fada sosai, har ma ba mai iya bin ta wannan hanya. 29Sai suka kwala ihu suka ce, "Ina ruwanka da mu, kai dan Allah? Ka zo nan ne ka yi mana azaba tun kafin lokaci ya yi?"
30To akwai wani garken aladu masu yawa na kiwo, babu nisa da su. 31Sai al'janun suka roki Yesu suka ce, "In ka fitar da mu, tura mu cikin garken aladun nan." 32"Yesu ya ce masu, "To, ku je." Sai aljanun suka fita, suka shiga cikin aladun. Sai kuwa duk garken suka rugungunta ta gangaren, suka fada cikin tekun, suka hallaka a ruwa.
33Mutanen masu kiwon aladun suka gudu, suka shiga gari, suka yi ta ba da labarin komai da komai, musamman abin da ya faru da masu al'janun. 34Sai duk jama'ar gari suka fito su sami Yesu. Da suka gan shi, suka roke shi ya bar kasarsu.

9

1Yesu ya shiga jirgi ya haye ya je birninsa. 2Sai gashi, sun kawo masa wani mutum shanyayye kwance a tabarma. Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce wa shanyayyen, "Da, ka yi farin ciki. An gafarta maka zunuban ka."

3Sai wadansu marubuta suka ce a tsakaninsu, "Wannan mutum sabo yake yi." 4Yesu kuwa da yake ya san tunaninsu, yace, "Don me kuke mugun tunani a zuciyarku? 5Wanne ya fi sauki, a ce, 'An gafarta maka zunubanka,' ko kuwa a ce, 'Tashi ka yi tafiya'? 6Amma domin ku sani Dan mutum yana da ikon gafarta zunubai a duniya,..." Sai ya ce wa shanyayyen, "Tashi, ka dauki shimfidarka ka tafi gida."
7Mutumin kuwa ya tashi ya tafi gida. 8Da taron suka ga haka sai suka yi mamaki, suka daukaka Allah, wanda ya ba mutane irin wannan iko. 9Da Yesu ya yi gaba, ya ga wani mutum mai suna Matiyu a zaune, yana aiki a wurin karbar haraji. Yace masa, "Ka biyo ni." Ya tashi ya bi shi.
10Sa'adda kuma Yesu yake cin abinci a gida, sai ga masu karbar haraji da masu zunubi da yawa sun zo, sun zauna tare da shi da almajiransa. 11Da Farisawa suka ga haka, sai suka ce wa almajiransa, "Don me malamin ku ya ke ci tare da masu karbar haraji da masu zunubi?"
12Amma da Yesu ya ji haka ya ce, "Ai, lafiyayyu ba ruwansu da likita, sai dai marasa lafiya. 13Sai ku fahimci ma'anar wannan tukuna, 'Ni kam, ina bukatar jinkai ba hadaya ba.' Ba domin in kira masu adalci su tuba na zo ba, sai dai masu zunubi.
14Sai almajiran Yahaya suka zo wurinsa, suka ce, "Don me mu da Farisawa mu kan yi azumi a kai a kai, amma naka almajiran ba su yi?" 15Sai Yesu ya ce masu, "Masu hidimar buki za su yi bakin ciki tun ango yana tare da su? Ai, lokaci yana zuwa da za a dauke masu angon. A sa'annan ne fa za su yi azumi."
16Babu mutumin da zai sa sabon kyalle a kan tsohuwar tufa, domin kyallen zai yage daga tufar, har ma yagewar ta fi ta da.
17Mutane kuma ba su dura sabon ruwan inabi a tsofaffin salkuna. Idan sun yi haka, sai salkunan kuma su fashe inabin ya tsiyaye, sai salkunan su lalace. A maimakon haka, ana sa sabon inabi cikin sababbin salkuna, ta haka an tsirar da duka biyun kenan."
18Yesu kuwa yana cikin yi masu magana sai ga wani shugaban jama'a ya zo ya yi masa sujada, ya ce, "Yanzun nan 'yata ta rasu, amma ka zo ka dora mata hannu, za ta rayu." 19Sai Yesu ya tashi ya bi shi tare da almajiransa.
20Sai ga kuma wata mace wadda ta yi shakaru goma sha biyu tana zubar da jini sosai, ta rabo ta bayan Yesu, ta taba gezar mayafinsa. 21Domin ta ce a ran ta, "Ko da mayafinsa ma na taba, sai in warke." 22Sai Yesu ya juya, ya gan ta ya ce, '"Yata, ki karfafa. Bangaskiyarki ta warkar da ke." Nan take matar ta warke.
23Da Yesu ya isa gidan shugaban jama'ar, ya kuma ga masu busar sarewa da taro suna ta hayaniya sosai. 24Sai ya ce, "Ku ba da wuri, ai, yarinyar ba matacciya take ba, barci ta ke yi." Sai suka yi masa dariyar raini.
25Sa'adda aka fitar da taron waje, ya shiga ya kama hannunta, sai kuwa yarinyar ta shi. 26Labarin kuwa ya bazu a duk yankin.
27Da Yesu ya yi gaba daga nan, sai wadansu makafi biyu suka bi shi, suna daga murya suna cewa, "Ya Dan Dauda, ka ji tausayinmu." 28Da Yesu ya shiga wani gida sai makafin suka zo gareshi. Yesu ya ce masu, "Kun gaskata ina da ikon yin haka?" Sai suka ce masa. "I, ya Ubangiji."
29Sai Yesu ya taba idanunsu, ya ce, "Ya zama maku gwargwadon bangaskiyarku." 30Sai idanunsu suka bude. Amma Yesu ya umarce su kwarai, ya ce, "Kada fa kowa ya ji labarin nan." 31Amma suka tafi suka yi ta baza labarinsa a duk yankin.
32Da makafin biyu suka tafi, sai aka kawo wa Yesu wani bebe mai aljani. 33Bayan da an fitar da aljanin, sai beben ya yi magana, taron kuwa suka yi mamaki, su ka ce, "Kai, ba a taba ganin irin wannan a cikin Isra'ila ba!" 34Amma sai Farisawa suka ce, "Ai, da ikon sarkin aljanu ya ke fitar da aljanu."
35Sai Yesu ya zazzaga dukan garuruwa da kauyuka, yana koyarwa a majami'unsu, yana yin bisharar mulkin Allah, yana kuma warkar da kowace irin cuta da rashin lafiya. 36Amma da ya ga taro masu yawa sai ya ji tausayinsu, domin suna shan wahala kuma sun karaya. Suna nan kamar tumaki da babu makiyayi.
37Sai ya ce wa almajiransa, "Girbin yana da yawa, amma ma'aikatan kadan ne. 38Saboda haka sai ku yi sauri ku roki Ubangijin girbin ya turo ma'aikata cikin girbinsa."

10

1Yesu ya kira almajiransa goma sha biyu, ya kuma ba su ikon fitar da kazaman ruhohi, su warkar da kowacce irin cuta da rashin lafiya.

2To yanzu ga sunayen manzanin nan goma sha biyu. Na farkon shine, Saminu, wanda ake kira Bitrus, da dan'uwansa Andarawas, da Yakubu dan Zabadi, da dan'uwansa Yahaya; 3Filibus, da Bartalamawus, da Toma da Matiyu mai karbar haraji da Yakubu dan Halfa, da Taddawus; 4Saminu Bakairawane, da kuma Yahuza Iskariyoti wanda ya bashe shi.
5Sha biyun nan su ne Yesu ya aika, ya yi masu umarni ya ce, "Kada ku shiga wajen al'ummai, ko kuma kowane garin Samariyawa. 6Sai dai ku je wurin batattun tumaki na gidan Isra'ila. 7Sa'adda kuna tafiya, kuna wa'azi, kuna cewa, 'Mulkin Sama ya kusato'.
8Ku warkar da marasa lafiya, ku tada matattu, ku tsarkake kutare, ku kuma fitar da aljanu. Kyauta kuka samu ku ma ku bayar kyauta. 9Kada ku rike zinariya, ko azurfa, ko tagulla a jakarku. 10Kada kuma ku dauki zabira a tafiyarku, ko taguwa biyu, ko takalma, ko sanda, don ma'aikaci ya cancanci abincin sa.
11Kowanne birni, ko kauyen da kuka shiga, ku nemi mai mutunci a cikinsa, ku kuma zauna a wurin har lokacin da za ku tashi. 12In za ku shiga gida ku ce, salama a gareku. 13Idan gidan akwai dan salama, salamarku za ta ta tabbata a gare shi. Idan kuwa babu, salamarku za ta komo maku.
14Ga wadanda su ka ki karbar ku ko sauraron ku, idan za ku fita garin ko gidan, sai ku karkade kurar kafafunku. 15Hakika, ina gaya maku, a ranar shari'a za a fi rangwanta wa kasar Saduma da ta Gwamrata a kan wannan birni.
16"Duba, na aike ku kamar tumaki a tsakiyar kyarketai, don haka sai ku zama masu wayo kamar macizai, da kuma marasa barna kamar kurciyoyi. 17Ku yi hankali da mutane, don za su kai ku gaban majalisa, su kuma yi maku bulala a majami'unsu. 18Za su kuma kai ku gaban mahukunta da sarakuna saboda ni, domin ku bada shaida a gabansu, da kuma gaban al'ummai.
19Idan har sun bada ku, kada ku damu da yadda za ku yi magana, ko kuwa abin da za ku fada, domin za a ba ku abin da za ku fada a lokacin. 20Domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhun Ubanku ne yake magana ta bakinku.
21Dan'uwa zai ba da dan'uwansa a kashe shi, uba kuwa dansa. 'Ya'ya kuma za su tayarwa iyayensu, har su sa a kashe su. 22Kowa kuma zai ki ku saboda sunana. Amma duk wanda ya jure har karshe, zai tsira. 23In sun tsananta maku a wannan gari, ku gudu zuwa na gaba. Hakika ina gaya maku, kafin ku gama zazzaga dukan garuruwan Isra'ila, Dan Mutum zai zo.
24Almajiri ba ya fin malaminsa, bawa kuma ba yafin ubangijinsa. 25Dai dai ne almajiri ya zama kamar malaminsa, bawa kuma kamar ubangijinsa. In har sun kira mai gida Ba'alzabuba, za su kuma bata mutanen gidansa!
26Don haka kada kuji tsoron su, domin ba abin da yake boye da ba za a bayyana ba. 27Abin da nake fada maku a asirce, ku fada a sarari. Abin da kuma kuka ji a cikin rada, ku yi shelarsa daga kan soraye.
28Kada ku ji tsoron masu kisan jikin mutum, amma ba sa iya kashe rai. Sai dai ku ji tsoron wannan da yake da ikon kashe jiki ya kuma jefa rai cikin jahannama. 29Ba 'yan tsuntsaye biyu ake sayarwa akan kobo ba? Ba ko daya a cikin su da zai fadi kasa ba tare da yardar Ubanku ba. 30Ai, ko da gashin kan ku ma duk a kidaye yake. 31Kada ku ji tsoro. Gama darajarku ta fi ta tsuntsaye masu yawa.
32"Saboda haka duk wanda ya shaida ni a gaban mutane, ni ma zan yi shaidar sa a gaban Ubana wanda ya ke cikin Sama. 33Amma duk wanda ya yi musun sani na a gaban mutane, ni ma zan yi musun sanin sa a gaban Ubana da yake cikin Sama."
34"Kada ku zaci na zo ne in kawo salama a duniya. Ban zo domin in kawo salama ba, sai dai takobi. 35Domin na zo ne in hada mutum da ubansa gaba, 'ya da uwatarta, mata da kuma surukarta. 36Zai zama na kuma magabtan mutum su ne mutanen gidansa.
37Dukan wanda ya fi son mahaifinsa ko mahaifayarsa fiye da ni, bai cancanci zama nawa ba. Wanda kuma ya fi son dansa ko 'yarsa fiye da ni, bai cancanci zama nawa ba. 38Wanda kuma bai dauki gicciyensa ya biyo ni ba, bai cancanci zama nawa ba. 39Dukan mai son ya ceci ransa, zai rasa shi. Duk kuwa wanda ya rasa ransa saboda ni, yana ceton sa ne.
40"Wanda ya marabce ku, ya marabce ni ke nan. 41Wanda ya marabce ni kuwa, ya marabci wanda ya aiko ni. Wanda ya marabci annabi domin shi annabi ne, zai karbi lada kamar na annabi. Wanda kuma ya marabci mai adalci saboda shi mai adalci ne, zai sami lada kamar na mai adalci.
42Kowa ya ba daya daga cikin 'yan kananan nan, ko da kofin ruwan sanyi ya sha, domin shi almajirina ne, hakika, Ina gaya maku, ba zai rasa ladarsa ba."

11

1Bayan Yesu ya gama yi wa almajiransa gargadi, sai ya bar wannan wuri, ya tafi biranensu domin yayi koyorwa, da wa'azi. 2Da Yahaya mai baftisma ya ji daga kurkuku irin ayyukan da Yesu ke yi, sai ya aika sako ta wurin almajiransa. 3Ya ce masa. "Kai ne mai zuwa"? ko mu sa ido ga wani.

4Yesu ya amsa ya ce masu, "Ku je ku gaya wa Yahaya abin da ku ka gani da abin da ku ka ji. 5Makafi suna samun ganin gari, guragu na tafiya, ana tsarkake kutare, kurame na jin magana kuma, ana tada matattu, mabukata kuma ana ba su bishara. 6Kuma mai albarka ne wanda baya tuntube sabili da ni.
7Bayan wadannan sun tafi, sai Yesu ya fara wa jama'a jawabi game da Yahaya mai baftisma, yana cewa, "Me ake zuwa gani a jeji - ciyawa ce da iska ke busawa? 8Shin menene kuke zuwa gani a jeji - mutum mai sanye da tufafi masu laushi? Hakika, masu sa tufafi masu laushi suna zaune ne a fadar sarakuna.
9Amma me ku ke zuwa gani, annabi? Hakika ina fada maku, fiye ma da annabi. 10Wannan shine wanda aka rubuta game da shi, 'Duba, ina aika manzona, wanda za ya tafi gabanka domin ya shirya maka hanya inda za ka bi'.
11Ina gaya maku gaskiya, cikin wadanda mata suka haifa, babu mai girma kamar Yahaya mai baftisma. Amma mafi kankanta a mulkin sama ya fi shi girma. 12Tun daga kwanakin Yahaya mai baftisma zuwa yanzu, mulkin sama yana shan gwagwarmaya, masu husuma kuma su kan kwace shi da karfi.
13Gama dukan annabawa da shari'a sun yi annabci har zuwa lokacin Yahaya. 14kuma in zaku karba, wannan shine Iliya wanda za ya zo. 15Wanda ke da kunnuwan ji, ya ji.
16Da me zan kwatanta wannan zamani? Ya na kamar yara masu wasa a kasuwa, sun zauna suna kiran juna 17suna cewa mun busa maku sarewa baku yi rawa ba, mun yi makoki, baku yi kuka ba.
18Gama Yahaya ya zo, baya cin gurasa ko shan ruwan inabi, sai aka ce, "Yana da aljannu". 19Dan mutum ya zo yana ci yana sha, sai aka ce, 'Duba, ga mai hadama, mashayi kuma, abokin masu karbar haraji da masu zunubi!' Amma hikima, ta wurin aikin ta ake tabbatar da ita.
20Sannan Yesu ya fara tsautawa biranen nan inda ya yi yawancin ayukansa, domin ba su tuba ba. 21"Kaiton ki Korasinu, kaiton ki Batsaida! In da an yi irin ayuka masu ban mamaki a Taya da Sidon! Yadda aka yi a cikinku, da tuni sun tuba suna sanye da tsumma da yafa toka. 22Amma zai zama da sauki a kan Taya da Sidon a ranar shari'a fiye da ku.
23Ke kafarnahum, kina tsammani za a daukaka ki har zuwa sama? A'a za a saukar da ke kasa zuwa hades. Gama in da an yi irin al'ajiban da aka yi a cikin ki a Sodom, da tana nan har yanzu. 24Amma ina ce maku, za a saukaka wa Sodom a ranar shari'a fiye da ku."
25A wannan lokaci Yesu ya ce, "Ina yabon ka, ya Uba, Ubangijin sama da kasa, domin ka boye wa masu hikima da fahimta wadannan abubuwa, ka bayyana wa marasa sani, kamar kananan yara. 26I, ya Uba gama wannan shine ya yi daidai a gare ka. 27An mallaka mani dukan abu daga wurin Ubana. Sannan babu wanda ya san Dan, sai Uban, babu kuma wanda ya san Uban, sai Dan, da duk wanda ya so ya bayyana masa.
28Ku zo gare ni, dukanku masu wahala da fama da nauyin kaya, ni kuma zan ba ku hutawa. 29Ku dauki karkiya ta ku koya daga gare ni, gama ni mai tawali'u ne da saukin hali a zuciya, sannan zaku sami hutawa ga rayukanku. 30Gama karkiyata mai sauki ce, kaya na kuma ba shi da nauyi."

12

1A wannan lokaci, Yesu ya tafi a ranar Asabaci, ya bi cikin gonar hatsi. Almajiransa na jin yunwa, sai suka fara zagar hatsi suna ci. 2Amma da Farisawa suka gan su, sai su ka ce wa Yesu. "Duba, almajiranka su na yin abin da doka ta haramta a ranar Asabaci."

3Amma Yesu ya ce masu, "Baku karanta abin da Dauda ya yi ba, lokacin da ya ke jin yunwa, tare da mazan da ke tare da shi? 4Yadda ya shiga gidan Allah, ya ci gurasar alfarwa da doka ta hana shi ko mazan da ke tare da shi su ci, sai dai Firistoci ne kawai doka ta basu damar ci?
5Sa'annan ba ku karanta cikin shari'a cewa, a ranar Asabaci, Firistoci da ke cikin haikali na sabawa ranar Asabaci, amma kamar ba su yi laifi ba? 6Amma ina tabbatar maku da cewa, wani wanda ya fi haikali girma yana nan.
7In da kun san ma'anar wannan 'Na fi son jinkai fiye da hadaya,' da baku shari'anta wa marar laifi ba. 8Gama Dan mutum shine Ubangijin Asabaci."
9Sa'annan Yesu ya bar wannan wuri, ya shiga majami'ar su. 10Sai ga wani mutum wanda hannun sa ya shanye, sai Farisawa suka tambayi Yesu, cewa, "Doka ta halarta a yi warkarwa a ranar Asabaci?" Domin su zarge shi a kan zunubi.
11Yesu ya ce masu, "Wanene a cikin ku, wanda idan ya na da tunkiya guda, sa'annan tunkiyar nan ta fada a rami mai zurfi a ranar Asabaci ba zai kamo ta ya fitar da ita ba? 12Yaya za a kwatanta darajar mutum da tunkiya! Saboda haka ya halarta a yi alheri ranar Asabaci."
13Sai Yesu ya ce wa mutumin nan "Mika hannun ka." Ya mike hannunsa, sai hannun nan ya dawo lafiyaye kamar dayan hannunsa. 14Amma Farisawa su ka fita waje su ka fara mugun shiri domin sa. Su na neman hanyar da za su kashe shi.
15Da Yesu ya fahimci wannan, sai ya janye kan sa daga nan. Mutane da dama su ka bi shi, ya warkar da su duka. 16Ya dokace su da kada su bayyana shi ga kowa, 17domin ya zama gaskiyar abin da aka fada ta wurin annabi Ishaya, cewa,
18"Dubi, bawa na zababbe; kaunatacce na, wanda ya ke faranta mani raina sosai. Zan sa Ruhu na bisan sa, za ya furta hukunci zuwa al'ummai.
19Ba za ya yi jayayya ko tada murya ba, babu wanda za ya ji muryar sa a karabku. 20Ba zai karya kara da ya tankwashe ba; ba zai kashe fitilar da ta kusa mutuwa ba; sai ya kawo hukunci ga nasara. 21Sa'annan al'ummai za su dogara a ga sunansa.
22Sa'annan wani mutum, makaho ne, kurma kuma, aljannu kuma na cikinsa, an kawo shi wurin Yesu. Ya warkar da shi, ya sami ganin gari ya kuma yi magana. 23Jama'a su ka yi mamaki kwarai, su na cewa, "Ko wannan ne Dan Dawuda?"
24Amma da Farisawa su ka ji wannan al'ajibi, sai su ka ce, "Mutumin nan yana fitar da aljannu ta wurin Bahalzabuba sarkin aljannu ne." 25Amma Yesu ya san tunanin su, sai ya ce. "Duk mulkin da ya rabu gaba da kan sa, ba zaya tsaya ba, duk wani birni da ya rabu ba zai tsaya ba, ko gida da ya tsage, za ya rushe.
26Idan Shaidan ya fitar da Shaidan, ya rabu gaba da kansa. Yaya mulkin sa za ya tsaya? 27Idan Ina fitar da aljannu da ikon Ba'alzabuba, ta wurin wa masu bin ku su ke fitar da su? Saboda haka, su za su shari'anta ku.
28Amma idan ina fitar da aljannu da Ruhun Allah ne, hakika mulkin Allah ya zo gare ku. 29Kuma ta yaya mutum za ya shiga gidan mai karfi ya kwashe masa kaya ba tare da ya fara daure shi ba? Sa'annan ne za ya iya satar masa kaya daga gidansa. 30Wanda baya tare da ni yana gaba da ni ke nan, wanda kuma baya tarawa tare da ni, yana watsarwa ne.
31Saboda haka ina ce maku, kowanne zunubi da sabo, za a gafarta wa mutum, amma sabon Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta shi ba. 32Duk wanda yayi batanci ga Dan Mutum, za a gafarta masa. Amma duk wanda yayi batanci game da Ruhu Mai Tsarki ba za a gafarta masa ba, a nan duniya da har abada.
33Ko dai a mai da itace mai kyau 'ya'yansa kuma su yi kyau, ko a mai da itace marar kyau 'ya'yansa kuma marasa kyau, gama ana sanin itace ta wurin 'ya'yansa. 34Ku 'ya'yan macizai, tun da ku miyagu ne, yaya za ku iya fadin abubuwa nagari? Gama daga cikar zuciya baki ke magana. 35Mutumin kirki daga ajiyar zuciyarsa ya kan fitar da abubuwa masu kyau, mugun mutum kuma daga mummunar ajiyar zuciyarsa ya kan fitar da abubuwan mugunta.
36Sa'annan ina ce maku a ranar shari'a, mutane za su bada lissafin abubuwan banza da su ka fadi. 37Gama ta wurin maganganun ku, za a 'yantar da ku, ta wurin maganganun ku kuma za a kashe ku."
38Sa'annan wadansu Malaman Attaura, da Farisawa suka amsa suka ce wa Yesu, "Mallam, muna so mu ga wata alama daga gare ka."39Amma Yesu ya amsa ya ce masu, "Mugun zamani da mazinaciyar tsara, su na bukutar alama. Amma babu alamar da za a ba su, sai dai alamar annabi Yunusa. 40Gama yadda Yunusa ya yi kwana uku da dare uku a cikin babban kifi, haka ma Dan Mutum zaya yi kwana uku da dare uku a cikin zuciyar kasa.
41Mutanen Nineba za su tsaya a ranar shari'a da wannan zamani sannan su kashe su. Domin sun tuba da suka ji wa'azin Yunusa, amma duba wanda ya fi Yunusa yana nan.
42Sarauniyar Kudu za ta tashi da mutanen wannan zamani ta kuma kashe su. Ta zo daga karshen duniya domin ta ji hikimar Sulaimanu, kuma duba, wanda ya fi Sulaimanu yana nan.
43Idan kazamin ruhu ya rabu da mutum, ya kan wuce ya nemi wuraren da ruwa yake domin ya huta, amma bai samu ba. 44Sai ya ce, 'zan koma gidana inda na fito'. Bayan ya dawo, sai ya tarar da gidan nan an share shi ya zama da tsabta. 45Sai ya koma ya kawo wadansu ruhohi guda bakwai, wadanda su ka fi shi mugunta, sa'annan dukan su su zo su zauna a nan. Sa'annan yanayin mutumin nan na karshe ya fi na farko muni. Haka zaya kasance ga wannan mugun zamani.
46Sa'adda Yesu ya ke yi wa Jama'a jawabi, sai mahaifiyarsa da 'yan'uwansa su ka zo su ka tsaya a waje, suna neman su yi magana da shi. 47Sai wani ya ce masa, "Duba, mahaifiyarka da 'yan'uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai".
48Amma Yesu ya amsa ya ce wa shi wanda ya gaya masa, "Wacece mahaifiyata? Kuma su wanene 'yan'uwana?" 49Sai ya mika hannu ya nuna almajiransa ya ce, "Duba, ga mahaifiyata da 'yan'uwana! 50Gama duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda ya ke cikin sama, shine dan'uwana, da 'yar'uwata da mahaifiyata."

13

1A waccan rana Yesu ya fito daga gida ya zauna a gefen teku. 2Taro mai yawan gaske kuwa suka kewaye shi, sai ya shiga cikin kwalekwale ya zauna. Dukan taron kuwa na tsaye a bakin tekun.

3Sai Yesu ya fada masu abubuwa da yawa cikin misalai. Ya ce, "Wani mai shuka, ya tafi yayi shuka. 4Da yayi shukar, wadansu irin suka fadi a kan hanya, sai tsunsaye suka zo suka cinye su. 5Wadansu irin kuwa suka fadi a kan duwatsu, wurin da babu kasa. Nan da nan sai suka tsira, domin kasar babu zurfi. 6Amma da rana ta taso, sai suka yankwane domin ba su yi saiwa ba, suka kuwa bushe suka zube.
7Wasu irin kuwa suka fada a cikin kayayuwa. Kayayuwan kuwa suka shake su. 8Wasu irin kuwa suka fada a wuri mai kyau suka ba da tsaba, wani ya ba da dari, wasu sitin, wasu kuma talatin. 9Duk mai kunnen ji, bari ya ji.
10Almajiran suka zo suka ce ma Yesu, "Don me ka ke yi wa taron magana da misali?" 11Yesu ya amsa ya ce masu, "An baku 'yanci ku fahimci asiran mulkin sama, amma gare su ba a bayar ba. 12Domin wanda yake da shi, za a kara masa, zai kuma samu dayawan gaske. Amma duk wanda ba shi da shi, sai a dauke har ma abin da yake dashi.
13Saboda haka na yi masu magana cikin misalai, amma ko da ya ke sun gani, duk da haka ba su gani ba. Kuma ko da yake sun ji, hakika ba su ji ba, balle ma su fahimta. 14A gare su ne annabcin Ishaya ya cika, wanda yake cewa, "Game da sauraro zaku saurara, amma ba za ku fahimta ba. Game da gani kuma za ku kalla, amma ba za ku gane ba.
15Domin zuciyar mutanen nan ta duhunta, sun taurare ga saurare, kuma sun rufe idanunsu domin kada su gani da idanunsu, ko kuwa su ji da kunnuwansu, ko kuwa su fahimta da zukatansu, saboda su juyo kuma in warkar da su'.
16Amma idanunku masu albarka ne, domin sun gani, haka ma kunnuwanku, domin sun ji. 17Hakika ina gaya muku, annabawa da mutane dayawa masu aldalci sun yi marmarin ganin abin da kuka gani, amma ba su sami ganin su ba. Sun yi marmarin jin abin da kuka ji, ba su kuwa ji su ba.
18Ku saurari misalin nan na mai shuka. 19Idan wani ya ji maganar mulkin sama amma bai fahimce ta ba, sai mugun nan ya zo ya kwace abinda aka shuka a zuciyarsa. Wannan shine irin da aka shuka a kan hanya.
20Shi wanda aka shuka akan duwatsu, shine wanda ya ji maganar ya kuma karbe ta da murna nan da nan. 21Duk da haka, bai yi karfi cikin ta ba kuma nan ba da dadaiwa ba. Da wahala da tsanani suka taso saboda maganar, sai ya yi tuntube nan da nan.
22Shi wanda aka shuka a cikin kayayuwa wannan shine wanda ya ji maganar, amma dawainiyar duniya da kuma yaudarar dukiya suka shake maganar, sai ya kasa ba da 'ya'ya. 23Shi wanda aka shuka a kasa mai kyau, wannan shine wanda ya ji maganar, ya kuma fahimce ta. Wannan shine wanda ba da 'ya'ya da gaske; wadansu ribi dari, wadansu sittin, wasu kuma talatin."
24Yesu ya sake ba su wani misali, yana cewa "Za a kwatanta mulkin sama da wani mutum wanda ya shuka iri mai kyau a gona. 25Amma da mutane suka yi barci, magabcin sa ya zo ya shuka ciyayi a cikin alkamar, ya kuwa yi tafiyarsa. 26Sa'adda suka yi toho suka kuma ba da tsaba, sai ciyayin suka bayyana.
27Bayin mai gonar kuwa suka zo suka ce masa, maigida, ashe ba iri mai kyau ka shuka a gonarka ba? ya ya aka yi ta kasance da ciyayi? 28Ya ce masu, "Magabci ne ya yi wannan". Sai bayin suka ce masa, 'kana so mu je mu tuge su ne?'
29Mai gonar ya ce, 'A'a, kada a garin tuge ciyayin, ku tuge tare da alkamar. 30Bari dukan su su girma tare har lokacin girbi, a lokacin girbin zan gaya wa masu girbin, "Ku tuge ciyayin da farko a daura su dami dami sai a kona su, amma a tara alkamar a kai rumbunana.'"
31Sai Yesu ya sake yin magana da su cikin misalai, yana cewa "Za a kwatanta mulkin sama da kwayar mustad, wanda wani mutum ya shuka a lambunsa. 32Wannan iri shine mafi kankanta cikin dukan iri. Amma bayan ya yi girma, sai ya fi dukan ganyaye dake lambun. Ya zama itace, har ma tsuntsayen sama su yi sheka a rassansa."
33Yesu ya sake fada masu wani misali. "Za a kwatanta mulkin sama da yisti da mace takan dauka ta kwaba gari da shi mudu uku har sai ya yi kumburi."
34Duk wadannan abubuwa Yesu ya fada wa taron cikin misalai. Babu abinda ya fada masu da ba a cikin misali ba. 35Wannan ya kasance ne domin abinda annabin ya fada ya zama gaskiya, da ya ce, "Zan buda bakina da misali. In fadi abubuwan da ke boye tun daga halittar duniya."
36Sai Yesu ya bar taron ya shiga cikin gida. Amajiransa suka zo wurin sa suka ce, "Ka fasarta mana misalan nan a kan ciyayin da ke gonar" 37Yesu ya amsa kuma ya ce, "Shi wanda ya shuka iri mai kyau Dan Mutum ne. 38Gonar kuwa duniya ce; iri mai kyau kuma sune 'ya'yan mulkin. Ciyayin kuma sune 'ya'yan mugun, 39magabcin da ya shuka su kuma shaidan ne. Girbin shine karshen duniya, kuma masu girbin sune mala'iku.
40Saboda haka, kamar yadda aka tara ciyayin aka kona su da wuta, haka ma zai faru a karshen duniya. 41Dan Mutum zai aiki mala'ikunsa, kuma su tara dukan abubuwan da ke sa zunubi daga cikin mulkinsa, da kuma wadanda su ka yi aikin mugunta. 42Za su jefa su cikin korama ta wuta, inda za a yi kuka da cizon hakora. 43Sa'an nan ne mutane masu adalci za su haskaka kamar rana a mulkin Ubansu. Bari mai kunnen ji, ya ji.
44Mulkin sama kamar dukiya ce da ke boye a gona. Mutum ya samu sai ya boye ta, ya tafi cikin murna, ya sayar da mallakarsa kuma ya sayi filin. 45Haka ma za a kwatanta mulkin sama da wani attajiri mai neman Lu'ulu'ai masu daraja. 46Da ya sami lu'ulu'u daya mai darajar gaske, ya je ya sayar da dukan mallakarsa ya kuma saye shi.
47Haka kuma, za a kwatanta mulkin sama da taru da aka jefa cikin teku, ya kuwa tara hallitu iri-iri. 48Da ya cika, sai masuntan suka jawo shi bakin tekun. Sai suka zauna suka tara kyawawan abubuwan a taska, amma munanan abubuwan, suka watsar da su.
49Haka zai kasance a karshen duniya. Mala'iku za su zo su ware miyagu daga cikin masu adalci. 50Za su jefa su cikin korama ta wuta, inda za a yi kuka da cizon hakora.
51Kun fahimci dukan wadannan abubuwa? Amajiran suka ce da shi, "I". 52Sai Yesu ya ce masu, "Saboda haka kowane malamin attaura da ya zama almajirin mulkin sama, yana kamar mutum mai gida wanda ya zaro tsoho da sobon abu daga taskarsa." 53Daga nan, sa'adda Yesu ya kammala ba da wadanan misalai, sai ya tafi ya bar wurin.
54Sai Yesu ya shiga yankinsa ya koyar da mutane a masujadarsu. Saboda haka suka yi mamaki suna cewa, "Daga ina wannan mutumin ya sami hikimarsa da al'ajibai? 55Wannan mutumin ba dan masassakin nan ba ne? Ba kuma sunan mahaifiyarsa Maryamu ba? Ba Kuma 'yan'uwansa sune, Yakubu da Yusufu da Saminu da kuma Yahuza ba? 56Ba 'yan'uwansa mata na tare da mu ba? To daga ina wannan mutumin ya sami dukan wadannnan abubuwa?
57Suka bata rai saboda shi. Amma Yesu ya ce masu, "Ai annabi bai rasa daraja sai dai ko a garinsa da kuma cikin iyalinsa. 58Kuma bai yi al'ajibai dayawa a can ba saboda rashin bangaskiyarsu.

14

1A lokacin nan ne, Hiridus mai mulki ya ji labarin Yesu. 2Ya ce wa barorinsa, "Wannan Yahaya mai baftisma ne; ya tashi daga matattu. Saboda haka wadannan ikoki na aiki a cikinsa".

3Domin Hiridus ya kama Yahaya, ya daure shi, kuma ya jefa shi a kurkuku saboda Hirudiya, matar dan'uwansa Filibus. 4Ya ce masa, "Bai kamata ka dauke ta a matsayin matarka ba." 5Da Hirudus ya kashe shi, amma yana tsoron jama'a, domin sun dauke shi a matsayin annabi.
6Amma da ranar bikin haihuwar Hirudus ta kewayo, diyar Hirudiya tayi rawa a lokacin har ta burge Hirudus. 7Sai ya yi mata alkawari har da rantsuwa cewa ta roki komenene ta ke so, zai ba ta.
8Bayan ta amshi umurni daga wurin mahaifiyarta, ta ce, "Ka bani kan Yahaya mai baptisma a kan tire. 9Sarki ya husata da rokonta, amma domin rantsuwar da ya yi kuma domin mutanen da ke a wurin bukin tare da shi, sai ya umurta a yi haka.
10Ya aika aka yanke kan Yahaya acikin kurkuku. 11Sai aka kawo kansa bisa tire, aka mika wa yarinyar, ta kuwa kai wa mahaifiyarta. 12Sai almajiransa suka zo, su ka dauki gawar su ka je su ka yi jana'iza. Bayan haka, su ka je su ka fada wa Yesu.
13Sa'adda da Yesu ya ji haka, ya fita daga cikin kwale-kwale zuwa wani kebabben wuri. Da taron suka ji haka, suka bi shi da kafa daga biranen. 14Sai Yesu ya zo gabansu, ya kuma ga babban taron. Ya tausaya masu ya kuwa warkar da marasa lafiya dake cikinsu.
15Da maraice ya yi, almajiransa su ka zo su ka ce masa, "Wannan wuri jeji ne, dare kuwa ya riga ya yi. Ka sallami taron domin su je cikin kauyukan nan, su sayo wa kansu abinci."
16Amma Yesu ya ce masu, "Babu amfanin tafiyar su, ku basu abin da za su ci." 17Suka ce masa, "Muna da gurasa guda biyar da kifi biyu ne kawai." 18Yesu ya ce, "Ku kawo mani su."
19Sai Yesu ya umarci taron su zauna akan ciyawa. Ya dauki gurasa biyar da kifi biyun. Ya dubi sama, ya sa albarka ya gutsuttsura ya kuma ba almajiran. Almajiran suka ba taron. 20Dukansu suka ci suka koshi. Sai suka dauki gutsattsarin gurasa da kifin, kwanduna goma sha biyu cike. 21Wadanda su ka ci kuwa kimanin maza dubu biyar ne, ban da mata da yara.
22Nan take sai ya sa almajiran suka shiga kwale-kwalen su haye zuwa dayan gefen kafin shi, domin ya sallami taron. 23Bayan ya sallami taron sun tafi, sai ya haura kan dutse domin yayi addu'a. Da dare yayi, yana can shi kadai. 24Amma yanzu fa kwale-kwalen na tsakiyar tekun, kuma da wuyar sarrafawa saboda rakuman ruwa da iska na gaba da su.
25Da asuba (wajen karfe uku na dare) Yesu ya nufo su yana tafiya akan teku. 26Da almajiran suka ganshi yana tafiya akan tekun, sai suka firgita suna cewa, "Fatalwa ce," suka yi kururuwa cikin tsoro. 27Amma Yesu yayi magana da su nan da nan yace, "Ku yi karfin hali! Ni ne! Kada ku ji tsoro."
28Bitrus ya amsa masa cewa, "Ubangiji, idan kai ne, ka umarce ni in zo wurin ka bisa ruwan." 29Yesu yace, "Zo" Sai Bitrus ya fita daga jirgin yana tafiya akan ruwan zuwa wurin Yesu. 30Amma da Bitrus ya ga iska, sai ya tsorata. Yayin da ya fara nutsewa, sai ya tada murya ya ce, "Ubangiji, ka cece ni!"
31Nan take Yesu ya mika hannunsa, ya kama Bitrus ya ce masa, "Kai mai karancin bangaskiya, meyasa ka yi shakka?" 32Bayan da Yesu da Bitrus suka shiga cikin kwale-kwalen, sai iska ta daina kadawa. 33Sai almajiran dake cikin kwale-kwalen su ka yi wa Yesu sujada suna cewa, "Hakika kai Dan Allah ne."
34Da suka haye, sun iso kasar Janisarata. 35Da mutanen wurin suka gane Yesu, sai suka aika da sako zuwa dukan yankin, kuma suka kawo masa dukan marasa lafiya. 36Suka roke shi don su taba gezar rigarsa, kuma dukan wadanda suka taba shi sun warke.

15

1Sai wadansu Farisawa da malamai suka zo wurin Yesu daga Urushalima. Su ka ce, 2"Meyasa almajiranka suke karya al'adar dattawa? Don ba su wanke hannayen su kafin su ci abinci." 3Yesu ya amsa masu ya ce, "Kuma don me ku ke karya dokar Allah saboda al'adunku?

4Domin Allah ya ce, 'Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka; 'Shi wanda ya yi muguwar magana ga mahaifinsa ko mahaifiyarsa, lallai zai mutu. 5Amma kun ce, "Duk wanda ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, "Kowanne taimako da za ka samu daga gare ni yanzu baiko ne ga Allah,'" 6wannan mutum ba ya bukatar ya girmama mahaifinsa. Ta wannan hanya kun maida maganar Allah wofi saboda al'adunku.
7Ku munafukai, daidai ne Ishaya ya yi annabci akan ku da ya ce, 8" Wadannan mutane girmama ni da baki kawai suke yi, amma zukatansu nesa suke da ni. 9Suna mani sujada a banza, domin suna koyar da dokokin mutane a matsayin rukunansu."
10Sai ya kira taron mutane zuwa gare shi ya ce masu, "Ku saurara ku fahimta, 11ba abin da ke shiga baki ke kazantar da mutum ba. Sai dai, abin da ke fitowa daga baki, wannan shi ya ke kazantar da mutum."
12Sai al'majiran suka zo suka ce masa, "Ka san Farisawa ba su ji dadi ba da suka ji maganan nan?" 13Yesu ya amsa ya ce, "Kowace shuka wadda ba Ubana na sama ya shuka ba za a tuge ta. 14Ku kyale su kawai, su makafin jagora ne. In makaho ya ja wa wani makaho gora dukan su za su fada rami."
15Bitrus ya amsa ya ce wa Yesu, "Ka bayyana wannan misali a garemu," 16Yesu ya ce, "Ku ma har yanzu ba ku da fahimta? 17Ko baku gani ba duk abin da ke shiga baki zuwa ciki ta haka yake fita zuwa salga?
18Amma abubuwan da ke fita daga baki suna fitowa ne daga zuciya. Su ne abubuwan da ke kazantar da mutum. 19Domin daga zuciya mugayen tunani suke fitowa, kisan kai, zina, fasikanci, sata, shaidar zur, da zage-zage. 20Wadannan su ne abubuwan da ke kazantar da mutum. Amma ci da rashin wanke hannu baya kazantar da mutum."
21Sai Yesu ya tafi daga nan ya nufi yankin biranen Taya da Sidon. 22Sai wata mace Bakan'aniya ta zo daga wannan yanki. Ta daga murya ta ce," Ka yi mani jinkai, Ubangiji, Dan Dauda; 'yata tana cikin bakar azaba da aljani." 23Amma Yesu bai ce mata kome ba. Almajiransa suka zo suka roke shi, suna cewa, "Ka sallame ta, domin tana bin mu da ihu."
24Amma Yesu ya amsa ya ce, "Ba a aike ni gun kowa ba sai dai ga batattun tumakin gidan Isra'ila." 25Amma ta zo ta durkusa a gabansa, tana cewa, "Ubangiji ka taimake ni." 26Ya amsa ya ce, "Ba daidai bane a dauki gurasar yara a jefa wa kananan karnuka.
27Ta ce, "I, Ubangiji, amma ko kananan karnuka suna cin barbashin da ke fadowa daga teburin maigida." 28Sai Yesu ya amsa ya ce mata, "Mace, bangaskiyarki tana da girma. Bari ya zamar maki yadda ki ke so." 'Yarta ta warke a lokacin.
29Yesu ya bar wurin ya tafi kusa da tekun Galili. Sai ya hau tudu ya zauna a can. 30Taro mai yawa suka zo gunsa. Suka kawo masa guragu, makafi, bebaye da nakasassun mutane da yawa, da wadansu marasa lafiya. Suka kawo su gaban Yesu, sai ya warkar da su. 31Don haka mutane da yawa suka yi mamaki a lokacin da suka ga bebaye suna magana, nakasassu sun warke, guragu suna tafiya, makafi suna gani. Sai suka daukaka Allah na Isra'ila.
32Yesu ya kira almajiransa zuwa gun sa sai ya ce, "Ina jin tausayin taron, sun kasance tare da ni kwana uku ke nan kuma ba su da abin da za su ci. Bana so in sallame su ba tare da sun ci abinci ba, domin kada su suma a hanya." 33Almajiran suka ce masa, "A ina zamu sami isasshiyar gurasa a wannan wuri da babu kowa har ta ishi babban taron nan." 34Yesu ya ce masu, "Gurasa nawa ku ke da ita?" Suka ce, "Bakwai da 'yan kifi marasa yawa." 35Sai Yesu ya umarci taron su zauna a kasa.
36Ya dauki gurasar nan bakwai da kifin, bayan ya yi godiya, ya kakkarya gurasar ya bada ita ga almajiran Sai almajiran suka ba taron. 37Jama'a duka suka ci suka koshi. Suka tattara gutsattsarin abincin da ya rage, kwando bakwai cike. 38Wadanda suka ci su dubu hudu ne maza, banda mata da yara. 39Sai Yesu ya sallami taron ya shiga cikin jirgin ruwa ya tafi yankin Magadan.

16

1Sai Farisawa da Sadukiyawa suka zo su gwada shi suka roke shi ya nuna masu alama daga sama. 2Amma ya amsa ya ce masu, "Lokacin da yamma ta yi, sai ku ce, 'Za a yi yanayi mai kyau, domin sama ta yi ja,'

3Kuma da safe ku ce, 'Zai zama yanayi mara kyau a yau, domin sama ta yi ja ta kuma gama gari, kun san yadda za ku bayyana kammanin sararin sama, amma ba ku iya bayyana alamun lokaci ba. 4Mugun zamani, maciya amana suna neman alama, amma babu wata alama da za a nuna sai ta Yunusa." Daga nan sai Yesu ya tafi.
5Almajiran suka zo daga wancan gefe, amma sun manta su dauki gurasa, 6Yesu ya ce masu, "Ku kula ku kuma mai da hankali da yisti na Farisawa da Sadukiyawa." 7Sai almajiran suka fara magana da junansu suka ce, "Ko saboda bamu kawo gurasa bane." 8Yesu yana sane da wannan sai ya ce, "Ku masu karancin bangaskiya, don me ku ke magana a tsakaninku cewa ko don bamu kawo gurasa bane?
9Ba ku gane ko tuna da gurasa guda biyar da aka ciyar da mutum dubu biyar, kuma kwando nawa kuka tara ba? 10Ko gurasa bakwai ga mutum dubu hudu, da kuma kwanduna nawa kuka dauka ba?
11Yaya kuka kasa fahimta cewa ba game da gurasa nake yi maku magana ba? Ku yi hankali ku kuma lura da yistin Farisawa da Sadukiyawa." 12Sa'annan suka fahimta cewa ba yana gaya masu su yi hankali da yistin da ke cikin gurasa ba ne, amma sai dai su yi lura da koyarwar Farisawa da Sadukiyawa.
13A lokacin da Yesu ya zo yankin Kaisariya Filibbi, ya tambayi almajiransa, cewa, "Wa mutane ke cewa Dan Mutum yake? 14Suka ce, "Wadansu suna cewa Yahaya mai baftisma; wadansu Iliya, saura suna cewa Irmiya, ko daya daga cikin annabawa." 15Ya ce masu, "Amma ku wa kuke ce da ni?" 16Sai Saminu Bitrus ya amsa ya ce, "Kai ne Almasihu, Dan Allah mai rai."
17Yesu ya amsa ya ce masa, "Mai albarka ne kai, Saminu dan Yunusa, don ba nama da jini ba ne ya bayyana maka wannan, amma Ubana wanda ke cikin sama. 18Ina kuma gaya maka cewa kai ne Bitrus, a kan wannan dutse zan gina ikilisiya ta. Kofofin hades ba za su yi nasara da ita ba.
19Zan ba ka mabudan mulkin sama. Duk abin da ka kulla a duniya zai zama abin da an kulla a cikin sama, kuma duk abinda ka warware a duniya a warware yake cikin sama," 20Sai Yesu ya umarci almajiransa kada su gaya wa kowa cewa shi ne Almasihu.
21Daga lokacin nan Yesu ya fara gaya wa almajiransa cewa dole ne ya tafi Urushalima, ya sha wahala mai yawa a hannun dattawa, da manyan firistoci da malaman attaura, a kashe shi, a tashe shi zuwa rai a rana ta uku. 22Sai Bitrus ya kai shi a gefe ya tsauta masa, cewa, "Wannan ya yi nesa da kai, Ubangiji; wannan ba zai taba faruwa da kai ba." 23Amma Yesu ya juya ya ce wa Bitrus, "Ka koma bayana, Shaidan! Kai sanadin tuntube ne gare ni, domin ba ka damuwa da abubuwan da suke na Allah, amma sai abubuwan mutane."
24Sa'annan Yesu ya ce wa almajiransa, "Duk wanda yake so ya bi ni, lallai ne ya ki kansa, ya dauki gicciyensa, ya bi ni. 25Domin duk wanda yake so ya ceci ransa zai rasa shi. Duk wanda ya rasa ransa domina zai same shi. 26Domin wace riba mutum zai samu in ya sami dukan duniya ya rasa ransa? Me mutum zai iya bayarwa a maimakon ransa?
27Domin Dan Mutum zai zo ne cikin daukakar Ubansa tare da mala'ikunsa. Sa'annan ne zaya biya kowane mutum bisa ga ayyukansa. 28Gaskiya ina gaya maku, akwai wadansun ku da ke tsaye a nan, da ba za su dandana mutuwa ba sai sun ga Dan Mutum na zuwa cikin mulkinsa."

17

1Bayan kwana shida Yesu ya dauki Bitrus da Yakubu, da Yahaya dan'uwansa, ya kai su kan wani dutse mai tsawo su kadai. 2Kamanninsa ya canja a gabansu. Fuskarsa ta haskaka kamar rana, kuma rigunansa suka yi kyalli fal.

3Sai ga Musa da Iliya sun bayyana garesu suna magana da shi. 4Bitrus ya amsa ya ce wa Yesu, "Ubangiji, ya yi kyau da muke a wurin nan. In kana so, zan yi bukkoki uku daya dominka, daya domin Musa, daya domin Iliya."
5Sa'adda yake cikin magana, sai, girgije mai haske ya rufe su, sai murya daga girgijen, tana cewa, "Wannan kaunattacen Dana ne, shi ne wanda yake faranta mani zuciya. Ku saurare shi." 6Da almajiran suka ji haka, suka fadi da fuskokinsu a kasa, saboda sun tsorata. 7Sai Yesu ya zo ya taba su ya ce, "Ku tashi, kada ku ji tsoro." 8Amma da suka daga kai ba su ga kowa ba sai Yesu kadai.
9Yayin da suke saukowa daga dutsen, Yesu ya umarce su, ya ce, "Kada ku fadawa kowa wannan wahayin, sai Dan Mutum ya tashi daga matattu." 10Almajiransa suka tambaye shi, suka ce, "Don me marubuta ke cewa lallai ne Iliya ya fara zuwa?"
11Yesu ya amsa ya ce, "Hakika, Iliya zai zo ya maido da dukan abubuwa. 12Amma ina gaya maku, Iliya ya riga ya zo, amma ba su gane shi ba. A maimakon haka, suka yi masa abin da suka ga dama. Ta irin wanan hanya, Dan Mutum kuma zai sha wuya a hannunsu. 13Sa'annan almajiransa suka fahimci cewa yana yi masu magana a kan Yahaya mai Baftisma ne.
14Da suka iso wurin taron, wani mutum ya zo gunsa, ya durkusa a gaban sa, ya ce, 15"Ubangiji, ka ji tausayin yarona, domin yana da farfadiya, kuma yana shan wuya kwarai, domin sau da yawa yana fadawa cikin wuta ko ruwa. 16Na kawo shi wurin almajiran ka, amma ba su iya su warkar da shi ba."
17Yesu ya amsa ya ce, "Marasa bangaskiya da karkataccen zamani, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe zan jure da ku? Ku kawo shi nan a wurina." 18Yesu ya tsauta masa, sai aljanin ya fita daga cikinsa. Yaron ya warke nan take.
19Sai almajiran suka zo wurin Yesu a asirce suka ce, "Me ya sa muka kasa fitar da shi?" 20Yesu ya ce masu, "Saboda karancin bangaskiyarku. Domin hakika, ina gaya maku, in kuna da bangaskiya ko da kamar kwayar mastad, za ku ce wa wannan dutse, 'Matsa daga nan ka koma can,' zai kuwa matsa kuma ba abin da zai gagare ku. 211
22Suna zaune a Galili, Yesu ya ce wa almajiransa, "Za a bada Dan Mutum ga hannun mutane. 23Kuma za su kashe shi, a rana ta uku zai tashi." Sai almajiransa suka yi bakin ciki kwarai.
24Da suka iso Kafarnahum, mutane masu karbar haraji na rabin shekel suka zo wurin Bitrus suka ce, "Malaminku na ba da rabin shekel na haraji?" 25Sai ya ce, "I." Amma da Bitrus ya shiga cikin gida, Yesu ya fara magana da shi yace, "Menene tunaninka Saminu? Sarakunan duniya, daga wurin wa suke karbar haraji ko kudin fito? Daga talakawansu ko daga wurin baki?"
26Sai Bitrus ya ce, "Daga wurin baki," Yesu ya ce masa, "Wato an dauke wa talakawansu biya kenan. 27Amma don kada mu sa masu karbar harajin su yi zunubi, ka je teku, ka jefa kugiya, ka cire kifin da ya fara zuwa. Idan ka bude bakinsa, za ka sami shekel. Ka dauke shi ka ba masu karbar harajin nawa da naka.


1Mafi kyawun kwafin kwafi ba su da. 21, Irin wannan aljanin bashi fita sai tare da addu'a da azumi .

18

1Daidai wannan lokacin, almajiran suka zo wurin Yesu suka ce, "Wanene mafi girma a mulkin sama?" 2Sai Yesu ya kira karamin yaro gunsa, ya sa shi a tsakaninsu, 3ya ce, "Hakika ina gaya maku, idan baku juya kun zama kamar kananan yara ba, babu yadda zaku shiga mulkin sama.

4Saboda haka, duk wanda ya kaskantar da kansa kamar karamin yaron nan, shi ne mafi girma a mulkin sama. 5Duk wanda ya karbi karamin yaro a suna na, ya karbe ni. 6Amma duk wanda ya sa daya daga cikin 'yan yaran nan da suka gaskanta da ni zunubi, gwamma a rataya dutsen nika a wuyansa a jefa shi cikin zurfin teku.
7Kaiton duniya saboda lokacin tuntube! Lallai ne wadannan lokuta su zo, amma kaiton mutumin da ta wurinsa ne wadannan lokutan za su zo! 8Idan hannunka ko kafarka ce za ta sa ka tuntube, ka yanke ta, ka yar daga gare ka. Zai fi maka kyau ka shiga rai da nakasa ko gurguntaka, da a jefa ka cikin madawwamiyar wuta tare da hannayenka ko kafafunka.
9Idan idonka zai sa ka tuntube, ka kwakule shi, ka yar. Zai fi maka kyau ka shiga rai da ido daya, da a jefa ka cikin madawwamiyar wuta da idanu biyu.
10Ku kula fa kada ku rena kananan nan. Domin koyaushe a sama, mala'ikunsu na duban fuskar Ubana da ke sama. 111
12Menene tunaninku? Idan mutum na da tumaki dari, sa'annan daya ta bata, ashe ba zai bar tassa'in da tara a gefen tudu ya tafi neman wadda ta bata ba? 13In ya same ta, hakika ina gaya maku, farin cikinsa na samun dayan nan da ta bace, zai fi na tassa'in da taran nan da basu bata ba. 14Hakanan fa, ba nufin Ubanku dake sama ba ne da ya daga cikin wadannan kananan ya hallaka.
15Idan dan'uwanka yayi maka laifi, fada masa tsakaninku, kai da shi kadai. Idan ya saurare ka, ka maido da dan'uwanka kenan. 16Amma in ya ki ya saurare ka, ka je da 'yan'uwa biyu ko uku su zama shaidu, don ta wurin shaidu biyu ko uku ake tabbatar da kowacce kalma.
17In kuma ya ki ya saurare su, ka kai lamarin ga ikklisiya. Idan ya ki ya saurari ikklisiya, ka maishe shi ba'al'umme da mai karbar haraji.
18Hakika ina gaya maku, duk abin da kuka daure a duniya, a daure yake a sama. Abin da kuka kwance kuma, a kwance yake a sama. 19Kuma ina gaya maku, idan mutum ku biyu zaku yarda akan duk abin da zaku roka, Ubana wanda ke a sama zai yi maku shi. 20Wurin da mutum biyu ko uku suka taru a cikin sunana, zan kasance tare da su."
21Bitrus ya zo ya ce wa Yesu, "Ubangiji, sau nawa ne dan'uwana zai yi mani laifi in gafarta masa? Har sai ya kai sau bakwai?" 22Yesu ya amsa ya ce masa, "Ban gaya maka sau bakwai ba, amma bakwai din ma har sau saba'in.
23Saboda haka, za a kwatanta mulkin sama da wani sarki da yake so ya lisafta dukiyarsa dake a hannun barorinsa. 24Da ya fara yin haka, sai aka kawo masa daya daga cikin barorinsa da yake binsa talanti dubu goma. 25Amma tunda ba shi da abin biya, ubangidansa ya bada umurni a sayar da shi, tare da matarsa da 'ya'yansa da duk mallakarsa, domin a biya.
26Sai baran ya fadi kasa, ya rusuna a gaban ubangidansa ya ce, "Maigida, kayi mani hakuri, zan biya duk abin da na karba." 27Don haka ubangidansa yayi juyayi, sai ya ce, ya yafe bashin, a saki baran.
28Amma bayan an saki wannan baran, ya je ya sami wani baran kamar sa da yake bi bashin dinari dari. Ya cafke shi, ya shake shi a wuya, ya ce, 'Ka biya bashin da nake bin ka.' 29Amma dan'uwansa bara ya roke shi ya ce, kayi mani hakuri, zan biya ka duk abinda na karba.'
30Amma baran nan na farko ya ki. A maimakon haka, ya sa aka jefa dan'uwansa bara a kurkuku sai ya biya bashin nan. 31Da sauran barori suka ga abin da ya faru, suka damu kwarai. Sai suka je suka fada wa ubangidansu yadda abin ya faru duka.
32Sai ubangidansa ya kirawo shi, ya ce masa, "Kai mugun bawa, na gafarta maka bashin nan duka, domin ka roke ni. 33Ashe, bai kamata kaima ka nuna jinkai ga dan'uwanka bara kamar yadda na nuna maka jinkai ba?'
34Ubangidansa yayi fushi, ya danka shi ga masu azabtarwa, har sai ya gama biyan dukan bashin da ake binsa. 35Hakanan Ubana dake a sama zai yi maku, idan kowannenku bai gafarta wa dan'uwansa daga zuciya ba."


1Mafi kyawun kwafin Girkanci ba su da jumlar da wasu fassarori suka haɗa da, Dan Mutum ya zo ya ceci abinda ya bata .

19

1Sai ya zama sa'adda Yesu ya gama wadannan maganganu, sai ya bar Galili ya zo kan iyakokin Yahudiya, ketaren kogin Urdun. 2Taro mai yawa suka bi shi, ya kuma warkar da su a wurin.

3Farisawa suka zo wurinsa, suna gwada shi, suka ce masa, "Ya hallata bisa ga doka mutum ya saki matarsa don kowanne dalili?" 4Yesu ya amsa ya ce, "Baku karanta ba, cewa shi wanda ya yi su tun farko ya yi su miji da mace?
5Shi wanda ya yi su kuma ya ce, "Saboda wannan dalilin, mutum zai rabu da mahaifinsa da mahaifiyarsa ya hade da matarsa, su biyun su zama jiki daya?" 6Su ba biyu ba ne kuma, amma jiki daya. Don haka, duk abin da Allah ya hada, kada wani ya raba."
7Sai suka ce masa, "To me yasa Musa ya umarcemu mu bada takardar saki, mu kuma kore ta?" 8Sai ya ce masu, "Saboda taurin zuciyarku, shi yasa Musa ya yarda maku ku saki matanku, amma da farko ba haka yake ba. 9Ina gaya maku, duk wanda ya saki matarsa in ba saboda zina ba, ya kuma auri wata, yana zina kenan. Wanda kuma ya auri macen da aka saka, yana aikata zina."
10Almajiran suka ce wa Yesu, "Idan haka yake game da mutum da matarsa, ba kyau ayi aure ba." 11Amma Yesu yace masu, "Ba kowa ne zai karbi wannan koyarwa ba, amma sai wadanda an yardar masu su karbe ta. 12Akwai wadanda aka haife su babanni. Akwai wadanda mutane ne suka maida su babanni. Sa'annan akwai wadanda sun mayar da kansu babanni saboda mulkin sama. Duk wanda zai iya karbar wannan koyarwa, ya karba."
13Sai aka kawo masa yara kanana don ya dibiya hannuwansa akansu, yayi masu addu'a, amma almajiran suka kwabe su. 14Amma Yesu ya ce masu, "Ku bar yara kanana, kada ku hana su zuwa wuri na, domin mulkin sama na irinsu ne." 15Ya sa hannuwa akan su, sa'annan ya bar wurin.
16Sai wani mutum ya zo wurin Yesu, ya ce, "Malam, wanne ayyuka nagari ne zan yi domin in sami rai madawwami?" 17Yesu ya ce masa, "Me yasa kake tambaya ta game da abin da ke nagari? Daya ne kawai ke nagari, amma idan kana so ka shiga cikin rai, ka kiyaye dokokin."
18Mutumin ya ce masa, "Wadanne dokokin?" Yesu ya ce masa, "Kada kayi kisa, kada kayi zina, kada kayi sata, kada kayi shaidar zur, 19ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kuma ka kaunaci makwabcinka kamar kanka."
20Saurayin nan ya ce masa, "Ai na kiyaye duk wadannan. Me nake bukata kuma?" 21Yesu ya ce masa, "Idan kana so ka zama cikakke, ka tafi ka sayar da mallakarka, ka kuma ba matalauta, zaka sami dukiya a sama. Sa'annan ka zo ka biyo ni." 22Amma da saurayin nan ya ji abin da Yesu ya fada, ya koma da bakin ciki, domin shi mai arziki ne kwarai.
23Yesu ya ce wa almajiransa, "Hakika ina gaya maku, zai zama da wuya mai arziki ya shiga mulkin sama. 24Ina sake gaya maku, zai fi wa rakumi sauki ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah."
25Da almajiran sun ji haka, suka yi mamaki kwarai da gaske, suka ce, "Wanene zai sami ceto?" 26Yesu ya dube su, ya ce, "A wurin mutane wannan ba zai yiwu ba, amma a wurin Allah, kome mai yiwuwa ne." 27Sai Bitrus ya amsa ya ce masa, "Duba, mun bar kome da kome mun bi ka. To me za mu samu?"
28Yesu ya ce masu, "Hakika ina gaya maku, ku da kuka bi ni, a sabuwar haihuwa, lokacin da Dan Mutum ya zauna a kursiyin daukakarsa, ku ma zaku zauna a kursiyoyi goma sha biyu, kuna shari'anta kabilu goma sha biyu na Isra'ila.
29Duk wanda ya bar gidaje, 'yan'uwa maza, 'yan'uwa mata, mahaifi, mahaifiya, 'ya'ya, ko gonaki, saboda sunana, zai sami ninkin su dari, ya kuma gaji rai madawwami. 30Amma dayawa dake farko yanzu, za su zama na karshe, dayawa dake karshe kuma, su zama na farko.

20

1Gama mulkin sama yana kama da wani mai gona, wanda ya fita da asuba ya nemi 'yan kwadago da za su yi aiki a gonarsa. 2Bayan sun shirya kudin da zai biya ma'aikata kimanin dinari daya a kowanne yini, sai ya aike su gonarsa suyi aiki.

3Misalin sa'a ta uku sai ya sake fita, sai ya ga wasu ma'aikata suna tsaye a bakin kasuwa, babu aiki. 4Sai ya ce masu, 'Kuzo kuyi aiki a gonar, duk abinda ya wajaba, zan ba ku,' Sai suka tafi su yi aikin.
5Sai ya sake fita a sa'a ta shida ya kuma sake fita a sa'a ta tara, ya sake yin hakan din. 6Ya kuma sake yin haka a sa'a ta sha daya, da ya fita sai ya ga wasu a tsaye da ba sa yin kome. Sai ya ce masu, 'Me yasa kuke tsaye ba ku yin kome dukan yini?' 7Sai suka ce masa, 'Ai babu wanda ya dauke mu aiki, shi yasa.' Sai ya ce masu, 'ku ma, kuje cikin gonar.
8Da yamma ta yi, sai mai gonar ya ce wa manajansa, 'Ka kira ma'aikatan nan ka biya su hakkin su, amma ka fara da wadanda suka zo a karshe, zuwa na farkon.' 9Sa'adda wadanda suka fara aiki da yamma suka zo, an biya su daidai yadda ake biya a yini. 10Da wadanda suka fara aiki tun safe suka zo, suna tsammani za a ba su fiye da wadanda sun zo daga baya, amma aka ba kowannensu dinari daya.
11Da suka karbi hakkinsu, suka yi gunaguni game da mai gonar. 12Suka ce, 'Wadannan da suka zo a karshe, sa'a guda ce kadai suka yi aiki, amma ka ba su daidai da mu, mu da muka yi fama da aiki cikin zafin rana.'
13Amma mai gonar ya amsa wa daya daga cikin su, ya ce, 'Aboki na, ban yi maku laifi ba. Ai mun shirya zan biya ku yadda ake biya a yini, ko ba haka ba? 14Ku karbi abin da ke na ku, ku tafi. Ganin dama ta ne, in ba wadannan da suka zo a karshe daidai da ku.
15Ashe, ba daidai bane a gare ni, in yi abin da na ga dama da mallaka ta? Ko kishi ne kuke yi saboda kirki na?' 16Haka yake, na karshe za su zama na farko, na farko kuma su zama na karshe." 1
17Da Yesu zai tafi Urushalima, ya dauki sha-biyun nan a gefe, yayin da suke tafiya, sai ya ce masu, 18"Ku duba fa, zamu tafi Urushalima, kuma za a bada Dan Mutum ga manyan firistoci da marubuta. Za su kuma yanke masa hukuncin kisa, 19za su kuma bada shi ga al'ummai don suyi masa ba'a, su bulale shi, su kuma gicciye shi. Amma a rana ta uku, za a tada shi."
20Sai uwar 'ya'yan Zabadi ta zo wurin Yesu tare da 'ya'yanta. Ta rusuna a gabansa tana neman alfarma a wurinsa. 21Yesu ya ce mata, Me kike so in yi maki?" Sai ta ce masa, "Ina so ka ba 'ya'yana izinin zama a mulkinka, daya a hannun damanka, daya kuma a hannun hagunka.
22Amma Yesu ya amsa, ya ce, "Baku san abin da kuke roko ba. Ko zaku iya sha daga cikin kokon da zan sha bada dadewa ba?" Sai suka ce masa, "Zamu iya." 23Sai ya ce masu, "In dai kokon nan da zan sha ne, lallai zaku sha. Amma, zama a hannun dama na da kuma hannun hagu na, ba ni ne mai bayarwa ba, amma na wadanda Uba na ya shirya domin su ne." 24Sa'anda sauran almajirai goma suka ji haka, sun yi bacin rai da 'yan'uwan nan biyu.
25Amma Yesu ya kira su wurin sa, ya ce, "Kuna sane da cewa, sarakunan al'ummai suna gwada masu mulki, manyan-gari kuma na nuna masu iko. 26Ba zai kasance haka a tsakanin ku ba. A maimakon haka, duk wanda ke da marmari ya zama da girma a tsakanin ku, ya zama baran ku. 27Wanda kuma ke da marmari ya zama na farko a cikin ku, ya zama baran ku. 28Kamar dai yadda Dan mutum bai zo don a bauta masa ba, amma yayi bauta, ya kuma bada ransa fansa domin mutane dayawa."
29Da suka fita daga Yariko, babban taro suka bi shi. 30Suka kuma ga makafi biyu zaune a bakin hanya. Da makafin suka ji cewa Yesu ne ke wucewa, sai suka tada murya suna cewa, "Ya Ubangiji, Dan Dauda, kayi mana jinkai." 31Amma jama'ar suka tsauta masu, suka ce suyi shiru. Duk da haka, makafin suka kara tada murya fiye da na da, suka ce, "Ya Ubangiji, Dan Dauda, kayi mana jinkai."
32Sai Yesu ya tsaya cik, ya sa aka kira su, sai ya ce masu, "Me kuke so in yi maku?" 33Sai suka ce masa, Ya Ubangiji, muna so mu sami ganin gari." 34Sai Yesu yayi juyayi a cikin sa, ya taba idanunsu. Nan da nan, suka sami ganin gari, suka kuma bi shi.


1Mafi kyawun kwafin kwafi ba su da An kira dayawa, amma kadan ne zababbu .

21

1Yayinda Yesu da almajiransa suka kusato Urushalima sai suka zo Betafaji wajen dutsen zaitun, sai Yesu ya aiki almajiransa guda biyu, 2yace masu, "Ku shiga kauyen da yake gaban ku zaku iske wata jaka da aholaki tara da ita. Ku kwance su ku kawo mani su. 3Idan wani ya gaya maku wani abu game da haka, sai ku ce, 'Ubangiji ne yake bukatarsu,' mutumin kuwa zai aiko ku da su nan da nan."

4Anyi wannan kuwa domin a cika annabcin anabin. Yace, 5"Ku cewa diyar Sihiyona, duba, ga sarkinki na zuwa wurin ki, mai tawali'u ne, kuma akan jaki wanda aholaki ne."
6Sai almajiran suka tafi suka yi kamar yadda Yesu ya umarce su. 7Suka kawo jakar da dan aholakin, suka sa tufafinsu akai, Yesu kuwa ya zauna akan tufafin. 8Yawancin jama'a kuwa suka baza tufafinsu akan hanya, wasu kuma suka yanko ganye daga bishiyoyi suka shimfida su a hanya.
9Taron jama'a da suke gabansa da wadanda suke bayansa, suka ta da murya suna cewa, "Hossana ga dan Dauda! mai albarka ne shi wanda ke zuwa cikin sunan Ubangiji. Hossana ga Ubangiji!" 10Sa'adda Yesu ya shiga Urushalima sai doki ya cika birnin ana cewa, "Wanene wannan?" 11Sai jama'a suka amsa, "Wannan shine Yesu annabi, daga Nazaret ta Galili."
12Sai Yesu ya shiga haikalin. Ya kori duk wadanda ke saye da sayarwa a cikin ikiilisiya. Ya birkice teburan masu canjin kudi da kujerun masu sayar da tantabaru. 13Ya ce masu, "A rubuce yake, 'Za a kira gidana gidan addu'a,' amma kun mayar dashi kogon 'yan fashi." 14Sai makafi da guragu suka zo wurin sa a haikalin, ya warkar da su.
15Amma da manyan firistoci da malaman attaura suka ga abubuwan banmamaki da yayi, kuma sa'adda suka ji yara suna tada murya a cikin haikalin suna cewa, "Hossana ga dan Dauda," sai suka ji haushi. 16Suka ce masa, kana jin abinda wadannan mutanen ke fadi?" Yesu ya ce masu, "I! Amma ba ku taba karantawa ba, 'daga bakin jarirai da masu shan mama ka sa yabo'?" 17Sai Yesu ya bar su, ya fice daga birnin zuwa Betaniya ya kwana a wurin.
18Washegari da safe yayin da yake komawa birnin, sai yaji yunwa. 19Da ya ga bishiyar baure a bakin hanya, sai yaje wurin amma bai sami kome ba sai dai ganye. Sai ya ce mata, "Kada ki kara yin 'ya'ya har abada." Sai nan take bishiyar bauren ta bushe.
20Da almajiran suka ga haka, sai suka yi mamaki suka ce, "Kaka bishiyar bauren ta bushe nan da nan?" 21Yesu ya amsa yace masu, "Hakika ina ce maku, in dai kuna da bangaskiya ba ku yi shakka ba, ba abinda aka yi wa bauren nan kadai za kuyi ba har ma za ku cewa tsaunin nan, "Ka ciru ka fada teku,' sai kuwa haka ta kasance. 22Kome kuka roka cikin addu'a, in dai kun gaskanta, za ku samu."
23Sa'adda Yesu ya shiga haikalin, sai manyan fristocin da shugabannin jama'a suka zo suka same shi yayin da yake koyarwa, suka ce, "Da wane iko kake yin wadannan abubuwa?" 24Yesu ya amsa yace masu, "Ni ma zan yi maku tambaya daya. In kun fada mani, ni ma zan fada maku ko da wane iko nake yin wadannan abubuwa.
25Daga ina baftismar Yahaya ta fito, daga sama ko kuma daga mutune?" Sai suka yi shawara a tsakanin su, suka ce, "In munce, 'daga sama,' zai ce mana, 'don me bamu gaskanta dashi ba?' 26Amma in munce, ' daga mutune,' muna tsoron jama'a, saboda sun san Yahaya annabi ne." 27Sai suka amsa ma Yesu suka ce, "Bamu sani ba." Shi ma yace masu, "Nima bazan gaya maku ko da wane iko nake yin abubuwan nan ba.
28Amma me kuke tunani? Wani mutum yana da 'ya'ya biyu. Ya je wurin na farkon yace, 'Da, je ka kayi aiki yau a cikin gona.' 29Yaron ya amsa yace, 'bazan yi ba,' amma daga baya ya canza tunaninsa ya tafi. 30Sai mutumin ya je wurin da na biyun ya fada masa abu guda. Wannan dan ya amsa ya ce, 'zanje, baba,' amma bai je ba.
31Wanene a cikin 'ya'ya biyun nan yayi nufin ubansa?" Suka ce, "na farkon." Yesu ya ce masu, "Hakika ina gaya maku, masu karbar haraji da karuwai za su shiga mulkin Allah kafin ku. 32Gama Yahaya ya zo maku a hanyar adalci, amma ba ku gaskata da shi ba, a yayinda masu karbar haraji da karuwai suka gaskata da shi. Ku kuwa, bayan kun ga abin da ya faru, baku ma tuba daga baya ba don ku gaskata da shi.
33Ku saurari wani misalin. Anyi wani mutum, mai gona. Yayi shuka a gonar, ya shinge ta, ya gina ramin matse inabi a cikin gonar, ya kuma gina wata hasumiyar tsaro, sai ya bada hayar gonar ga wadansu manoma. Sai ya tafi wata kasa. 34Da kakar inabi ta yi, sai ya aiki wadansu bayi su karbo masa amfanin gonar.
35Amma manoman suka kama bayin, suka doddoki dayan, suka kashe dayan, suka jejjefe dayan da duwatsu. 36Sai mai gonar ya sake aika wadansu bayinsa da suka fi na farko, amma manoman suka yi masu kamar yadda suka yi wa sauran. 37Bayan wannnan, sai mai gonar ya aika da dansa wurin su yana cewa, 'za su yi wa dana biyayya.'
38Amma da manoman suka ga dan, sai suka ce a tsakanin su, 'wannan shine magajin. Kuzo, mu kashe shi mu gaji gonar.' 39Sai suka dauke shi, suka jefar da shi daga cikin gonar, suka kashe shi.
40To idan me gonar ya zo, me zai yiwa manoman? 41Suka ce masa, "Zai hallaka mugayen manoman nan ta hanya mai tsanani, zai kuma bada gonar haya ga wadansu manoman, mutanen da za su biya, lokacin da inabin ya nuna."
42Yesu yace masu, "Baku taba karantawa a nassi ba," 'Dutsen da magina suka ki ya zama dutse mafi amfani. Wannan daga Ubangijine, kuma abin mamaki ne a idanunmu?'
43Saboda haka ina gaya maku, za a karbe mulkin Allah daga wurin ku a ba wata al'umma da zata bada amfaninsa. 44Duk wanda ya fadi akan dutsen nan zai ragargaje. Amma duk wanda dutsen ya fadawa, zai nike."
45Da manyan firistocin da farisawan suka ji wannan misalin, sai suka gane da su yake. 46Da suka nemi kama shi, sai suka ji tsoron taron, saboda mutanen sun dauke shi annabi.

22

1Yesu ya sake yi masu magana da misalai, yace, 2"Mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya shirya wa dansa liyafar aure. 3Ya aiki bayinsa su kira wadanda aka gayyata su zo liyafar auren, amma suka ki zuwa.

4Sai sarkin ya sake aiken wasu bayin, yace, "Ku gaya wa wadanda aka gayyata, "Duba, na shirya liyafata. An yanka bajimaina da kosassun 'yanmarukana, an gama shirya komai. Ku zo wurin bikin auren."
5Amma mutanen ba su dauki sakon da mahimmanci ba kuma suka yi tafiyarsu. Wani ga gonarsa, wani ga kasuwancinsa. 6Sauran kuma suka kama bayin sarkin, suka wulakanta su, suka kuma kashe su. 7Amma sarkin ya ji haushi. Ya aika sojojinsa, ku kashe masu kisan kan nan, ku kuma kone birnin su.
8Sai ya ce wa bayinsa, 'An gama shirya bikin, amma wadanda aka gayyata ba su cancanta ba. 9Saboda haka ku je bakin hanya ku gayyaci iyakar yawan mutanen da za ku samu zuwa bukin auren.' 10Bayin suka tafi hanya suka tattaro dukan mutanen da suka samu, da masu kyau da marassa kyau. Zauren auren kuwa ya cika makil da baki.
11Amma da sarkin ya zo don ya ga bakin, sai ya ga wani wanda bai sa kayan aure ba. 12Sai sarkin ya ce masa, 'Aboki, ta yaya ka shigo nan ba tare da kayan aure ba?' Mutumin kuwa ya rasa ta cewa.
13Sai sarkin ya ce wa bayinsa, 'Ku daure mutumin nan hannu da kafa, ku jefa shi cikin duhun, inda za ayi kuka da cizon hakora.' 14Gama mutane dayawa aka kira, amma kadan aka zaba."'
15Sai Farisawan suka tafi suka shirya makirci akan yadda zasu kama shi ta maganarsa. 16Suka tura masa almajiransu, da Hirudiyawa. Suka ce ma Yesu, "Mallam, mun san kai mai gaskiya ne, kuma kana koyar da hanyar Ubangiji da gaskiya. Ba ka damu da ra'ayin kowa ba, kuma ba ka nuna bambanci a tsakanin mutane. 17To gaya mana, menene tunaninka? Ya halarta a biya haraji ga Kaisar ko a'a?"
18Amma Yesu ya gane muguntarsu yace, "Don me kuke gwada ni, ku munafukai? 19Ku nuna mani sulen harajin." Sai suka kawo masa sulen.
20Yesu yace masu, "Hoto da sunan wanene wadannan?" 21Suka ce masa, "Na Kaisar." Sai Yesu ya ce masu, "To ku ba Kaisar abubuwan dake na Kaisar, Allah kuma abubuwan dake na Allah." 22Da suka ji haka, suka yi mamaki. Sai suka bar shi suka tafi.
23A ran nan sai wadansu Sadukiyawa, wadanda suka ce ba tashin matattu, suka zo wurinsa. Suka tambaye shi, 24cewa, "Mallam, Musa yace, 'Idan mutum ya mutu, bashi da 'ya'ya, dole dan'uwansa ya auri matarsa ya kuwa haifawa dan'uwansa 'ya'ya.
25Akwai wasu 'yan'uwa bakwai. Na farkon yayi aure sai ya mutu. Da shike bai bar 'ya'ya ba. Ya bar wa dan'uwansa matarsa. 26Sai dan'uwansa na biyu shi ma yayi haka, haka kuma na ukun, har zuwa dan'uwan na bakwai. 27Bayan dukansu, sai matar ta mutu. 28To a tashin matattu, matar wa zata zama a cikin su bakwai din? Don duk sun aure ta."
29Amma Yesu ya amsa yace masu, "Kun bata, domin ba ku san litattafai ko ikon Allah ba. 30Domin a tashin matattu basu aure, ba kuma a bada su aure. Maimaikon haka, suna kama da mala'ikun sama.
31Amma game da tashin matattu, ba ku karanta abinda Allah ya fada maku ba, cewa, 32'Nine Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da Allah na Yakubu'? Allah ba Allah na matattu bane, amma na rayayyu." 33Da taron suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.
34Amma da Farisawan suka ji cewa Yesu ya kure Sadukiyawa, sai suka tattara kansu. 35Daya daga cikinsu, masanin shari'a, yayi masa tambaya, yana gwada shi- 36"Mallam, wace doka ce mafi girma a cikin shari'a?"
37Yesu yace masa, "Ka kaunaci Ubangiji Allahnka da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka, da dukkan hankalinka.' 38Wannan itace babbar doka ta farko.
39Doka ta biyu kuma kamar ta take- 'Ka kaunaci makwabcinka kamar kanka.' 40Akan wadannan dokoki ne dukkan shari'a da annabawa suka rataya."
41Yayin da Farisawa suke tattare wuri daya, Yesu yayi masu tambaya. 42Yace, "Me kuke tunani game da Almasihu? Shi dan wanene?" Suka ce masa, "Dan Dauda ne."
43Yesu yace masu, "To ta yaya kuma Dauda cikin Ruhu ya kira shi Ubangiji, yana cewa, 44"Ubangiji ya cewa wa Ubangijina, zauna a hannun damana, har sai na mai da makiyanka matakin sawayenka."
45Idan Dauda ya kira Almasihu 'Ubangiji,' ta yaya ya zama dan Dauda?" 46Ba wanda ya iya bashi amsa, ba kuma wanda ya kara yi masa tambayoyi tun daga wannan rana.

23

1Sai Yesu yayi wa taron da alamajiransa magana. 2Ya ce, "Marubuta da Farisawa suna zaune a mazaunin Musa. 3Don haka, duk abinda suka umarceku kuyi, kuyi wadannan abubuwa ku kuma kiyaye su. Amma kada kuyi koyi da ayyukansu, gama suna fadar abubuwa amma kuma ba su aikata su.

4I, sukan daura kaya masu nauyi, masu wuyar dauka, daga nan su dauka su jibga wa mutane a kafada. Amma su kan su baza su mika danyatsa ba su dauka. 5Duk ayyukan su suna yi ne don mutane su gani, suna dinka aljihunan nassinsu da fadi, suna fadada iyakokin rigunansu.
6Su na son mafifitan wuraren zama a gidan biki, da mafifitan wuraren zama a majami'u, 7da kuma gaisuwar musamman a wuraren kasuwanci, a kuma rika ce da su 'mallam.'
8Amma ba sai an kira ku 'mallam, ba' domin malami daya kuke da shi, ku duka kuwa 'yan'uwan juna ne. 9Kada ku kira kowa 'Ubanku' a duniya, domin Uba daya ne ku ke da shi, kuma yana sama. 10Kada kuma a kira ku malamai, saboda malamin ku daya ne, shi ne Almasihu.
11Amma wanda yake babba a cikin ku zaya zama bawanku. 12Duk wanda ya daukaka kansa za a kaskantar dashi. Duk wanda ya kaskantar da kansa kuma za a daukaka shi.
13Amma kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! Kun toshewa mutane kofar mulkin sama. Baku shiga ba, kuma ba ku bar wadanda suke so su sami shiga ba. 14kaiton ku marubuta da Farisawa, domin kuna hallaka gwauraya - 15Kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! Kuna tafiya ketaren tekuna da kasashe domin samun almajiri daya tak, in kwa kun samu kukan mai da shi biyunku danwuta.
16Kaiton ku, makafin jagora, kuda kuke cewa, Kowa ya rantse da Haikali, ba komai. Amma duk wanda ya rantse da zinariyar Haikalin, rantsuwarsa ta daure shi.' 17Ku wawayen makafi! wanene yafi girma, zinariyar ko kuwa Haikalin da yake tsarkake zinariyar?
18Kuma, 'Kowa ya rantse da bagadi, ba komai bane. Amma duk wanda ya rantse da baikon da aka dora a kai, sai rantsuwarsa ta kama shi.' 19Ku makafi! Wanene yafi girma, baikon ko kuwa bagadin da yake kebe baikon ga Allah?
20Saboda haka, duk wanda ya rantse da bagadi, ya rantse da shi da duk abinda ke kansa. 21Kuma duk wanda ya rantse da Haikali ya rantse dashi da kuma wanda yake cikin sa. 22Kuma duk wanda ya rantse da sama, ya rantse da kursiyin Allah da kuma wanda yake zaune akai.
23Kaiton ku Farisawa da marubuta, munafukai! Kukan fitar da zakkar doddoya, da karkashi, da lamsur, amma kun yar da al'amuran attaura mafi nauyi-, wato, hukunci, da jinkai da bangaskiya. Wadannan ne ya kamata kuyi, ba tare da kunyi watsi da sauran ba. 24Makafin jagora, ku kan burtsar da kwaro dan mitsil, amma kukan hadiye rakumi!
25Kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! kuna wanke bayan moda da kwano, amma aciki cike suke da zalunci da keta. 26Kai makahon Bafarise! Sai ka fara tsarkake cikin modar da kwanon domin bayansu ma su tsarkaka.
27Kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! Kamar kaburburan da aka shafa wa farar kasa kuke, masu kyaun gani daga waje, daga ciki kuwa sai kasusuwan matattu da kazanta iri iri. 28Haka nan kuke a idanun mutane ku adalai ne, amma a ciki sai munafunci da mugun aiki.
29Kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! Ku kan gina kaburburan annabawa, kuna kuma kawata kaburburan adalai. 30Kuna cewa, 'Da muna nan a zamanin Ubanninmu, da bamu basu goyon baya ba wajen zubar da jinin annabawa.' 31Domin haka kun shaida kanku ku ne 'ya'yan masu kisan annabawa.
32Sai kuma kuka cika ma'aunin ubanninku! 33macizai, Ku 'ya'yan ganshekai, Yaya zaku tsere wa hukuncin Gidan wuta?
34Saboda haka, duba, ina aiko maku da annabawa, da masu hikima da marubuta. Za ku kashe wadansun su kuma ku gicciye su. Zaku yiwa wasu bulala a majami'un ku, kuna bin su gari gari. 35Sakamakon hakan alhakin jinin dukkan adalai da aka zubar a duniya ya komo a kan ku, tun daga jinin Habila adali har ya zuwa na Zakariya dan Barakiya, wanda kuka kashe a tsakanin Haikali da bagadi. 36Hakika, Ina gaya maku, duk wannan zai auko wa mutanen wannan zamani.
37Urushalima, Urushalima, keda kika kashe annabawa kika kuma jejjefi wadanda aka turo maki da duwatsu! Sau nawa ne naso in tattaro ki kamar yadda kaza take tattara 'yan tsakinta cikin fukafukanta, amma kin ki. 38Ga shi an bar maku gidan ku a yashe! 39Ina dai gaya maku, ba za ku kara gani na ba, sai ran da kuka ce, 'Albarka ta tabbata ga mai zuwa cikin sunan Ubangiji."'

24

1Yesu ya fita daga cikin haikalin ya kama hanyar sa. Almajiran sa suka zo suna nuna masa ginin haikali. 2Amma ya amsa masu yace, "kun ga dukkan wadannan abubuwan? Ina gaya maku gaskiya, ba ko dutse daya da za'a bari akan dan'uwansa wanda ba za'a rushe shi ba."

3Yayin da ya zauna a kan dutsen zaitun, almajiran sa suka zo wurin sa a boye suka ce, "me zai zama alamar zuwanka da kuma na karshen duniya?" 4Yesu ya amsa yace dasu, "Ku kula kada wani yasa ku kauce." 5Gama da yawa za su zo da sunana. Za su ce, "ni ne almasihu," kuma za su sa da yawa su kauce.
6Za ku ji labarin yake-yake da kuma shelar yake-yake. Ku kula kar ku tsorata, domin dole abubuwan nan su faru; amma karshen dai tukunna. 7Gama al'umma zata tayarwa al'umma, kuma mulki zai tayarwa mulki. Za'a yi yunwa da girgizar kasa a wurare dabam dabam. 8Amma dukkan wadannan farkon ciwon haihuwa ne kawai.
9Bayan haka za'a bada ku ga tsanani a kuma kashe ku. Dukkan al'ummai za su tsane ku saboda sunana. 10Daga nan da yawa za su yi tuntube, kuma su ci amanar juna, su kuma tsani juna. 11Annabawan karya da yawa za su taso kuma susa da yawa su kauce.
12Domin mugunta zata ribambanya, kaunar masu yawa zata yi sanyi. 13Amma duk wanda ya jure har karshe, zai sami ceto. 14Za'a yi wa'azin wannan bisharar mulkin a dukkan duniya don ya zama shaida akan dukkan al'ummai. Daganan karshen zai zo.
15Don haka, idan kun ga abin kyama mai lalatarwa, wanda Annabi Daniyel ya yi maganar sa, Ya tsaya a wuri mai tsarki (bari mai karatu ya fahimta), 16bari wadanda ke yahudiya su gudu zuwa kan duwatsu, 17Bari wanda yake kan bene kada ya sauko don daukar wani abu a cikin gidansa, 18kuma wanda yake gona kar ya dawo gida domin daukar babbar rigarsa.
19Amma kaito ga wadanda suke dauke da yaro, ko masu shayarwa a wannan kwanakin! 20Ku yi addu'a kada gudun ku ya zama lokacin hunturu, ko ranan asabaci. 21Domin za'ayi tsanani mai girma, wanda ba'a taba yin irin shi ba, tun farkon duniya har ya zuwa yau, a'a ba za ayi irin shi ba kuma. 22In ba don an rage kwanakin ba, da ba mahalukin da zai tsira. Amma albarkacin zababbun, za a rage kwanakin.
23Sa'annan idan wani yace maku, duba, "ga Almasihu a nan!" ko, "ga Almasihu a can!" kar ku gaskata. 24Gama annabawan karya da almasihan karya za su zo suna nuna alamu da al'ajibai, don su yaudari masu yawa zuwa ga bata, in ya yiwuma har da zababbun. 25Kun gani, na gaya maku kafin lokacin ya zo.
26Saboda haka, idan suka ce maku, "ga shi a jeji," kar ku je jejin. Ko, "ga shi a can cikin kuryar daki," kar ku gaskata. 27Yadda walkiya ke haskakawa daga gabas zuwa yamma, haka nan zuwan Dan mutum zai zama. 28Duk inda mushe yake, nan ungulai suke taruwa.
29Amma nan da nan bayan kwanakin tsananin nan, rana za ta duhunta, wata kuma ba zai ba da haskensa ba, taurari kuma za su fado daga sama, ikokin sammai za su girgiza.
30Sa'annan alamar Dan Mutum za ta bayyana a sararin sama, kuma dukkan kabilun duniya za su yi bakin ciki. Za su ga Dan Mutun na zuwa a gajimarai da iko da daukaka mai girma. 31Zai aiki mala'ikunsa, da karar kaho mai karfi, kuma za su tattara dukkan zababbu daga dukkan kusurwoyi hudu, daga karshen sararin sama har zuwa wani karshen.
32Kuyi koyi da itacen baure. Da zaran reshen sa ya yi toho ya fara bada ganye, za ku sani bazara ta kusa. 33Haka kuma, idan kun ga dukkan wadannan abubuwa, ya kamata ku sani, Ya yi kusa, ya na bakin kofa.
34Ina gaya maku gaskiya, wannan zamanin ba zai wuce ba, sai dukkan wadannan abubuwan sun faru. 35Sama da kasa za su shude, amma kalmomina ba za su shude ba.
36Amma game da ranan nan ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai Uban kadai.
37Kamar yadda kwanakin Nuhu suke, haka zai zama game da zuwan Dan Mutum. 38A wadannan kwankin kafin zuwan ruwan tsufana suna ci suna sha, suna aure suna aurarwa har ranar da Nuhu ya shiga jirgin, 39ba su san kome ba har ruwan ya zo ya cinye su_ haka ma zuwan Dan Mutun zai zama.
40Sa'annan mutane biyu zasu kasance a gona za a dauke daya, a bar daya a baya. 41Mata biyu na nika a manika za a dauke daya, za a bar dayar. 42Don haka sai ku yi zaman tsaro, domin baku san ranar da Ubangijinku zai zo ba.
43Amma ku san wannan, idan maigida ya san lokacin da barawo zai zo, zai zauna a shirye ba zai bar gidan sa har a balle a shiga ba. 44Don haka sai ku shirya, domin Dan Mutum zai zo a sa'ar da ba ku yi zato ba.
45To wanene amintaccen bawannan mai hikima, wanda maigidan sa ya sa ya kula mar da gida, domin ya ba su abinci a kan lokaci? 46Mai albarka ne bawan, da mai gidan zai same shi a kan aikin sa a lokacin da ya dawo. 47Ina gaya maku gaskiya mai gidan zai dora shi a kan dukkan a binda yake da shi.
48Amma idan mugun bawa ya ce a zuciyarsa, "maigida na ya yi jinkiri," 49sai ya fara dukan sauran barorin, ya yi ta ci da sha tare da mashaya, 50uban gidan bawan zai dawo a ranar da bawan bai zata ba, a lokacin da bai sani ba. 51Uban gidansa zai datsa shi biyu, karshen sa zai zama daidai da na munafukai, za a sashi inda a ke kuka da cizon hakora.

25

1Sa'annan mulkin sama zai zama kamar budurwai goma da suka dauki fitilunsu domin su taryi ango. 2Biyar daga cikin su masu hikima ne biyar kuma wawaye. 3Sa'adda wawayen budurwai suka dauki fitilunsu, ba su dauki karin mai ba. 4Amma budurwai masu hikimar suka dauki gorar mai tare da fitilunsu.

5To da angon ya makara, dukkan su sai suka fara gyangyadi sai barci ya dauke su. 6Amma da tsakkar dare sai aka yi shela, 'Ga ango ya iso! Ku fito taryensa.
7Sai dukka budurwan nan suka tashi suka gyaggyara fitilunsu. 8Wawayen su ka ce da masu hikimar, 'Ku sammana kadan daga manku gama fitilunmu su na mutuwa.' 9"Amma masu hikimar suka ce 'Tun da man ba zai ishe mu tare da ku ba, sai ku je gun ma su sayarwa ku sayo wa kanku.
10Sa'adda suka tafi sayan man, sai angon ya shigo, kuma wadanda suke a shirye su ka shiga tare da shi bukin auren, sai aka rufe kofar. 11Bayan dan lokaci kadan sauran budurwan suka dawo suna cewa, 'Mai gida, mai gida, bude mana kofar.' 12Amma ya amsa ya ce, 'A gaskiya ina gaya maku, ni ban san ku ba.' 13Don haka sai ku lura, don baku san rana ko sa'a ba.
14Domin yana kama da wani mutum da zai tafi wata kasa. Ya kira barorinsa ya ba su dukiyar sa. 15Ga wani ya ba shi talanti biyar, ga wani ya ba shi biyu, ga wani kuma ya ba shi talanti daya. kowa an bashi gwargwadon iyawarsa, sai wannan mutum ya yi tafiyar sa 16nan da nan sai wanda ya karbi talanti biyar ya sa nasa a jari, ya sami ribar wasu talanti biyar.
17Haka ma wanda ya karbi talanti biyu ya sami ribar wasu biyu. 18Amma bawan da ya karbi talanti dayan ya yi tafiyar sa, ya haka rami, ya binne kudin mai gidansa.
19To bayan tsawon lokaci sai ubangidan barorin nan ya dawo, domin yayi lissafin kudinsu. 20Bawan da ya karbi talanti biyar, ya kawo nasa da ribar wasu biyar. Yace, 'Maigida, ka bani talanti biyar, gashi na samo ribar karin talanti biyar.' 21Maigidansa yace masa, 'Madalla, bawa na gari mai aminci! Ka yi aminci akan abu kadan. Zan sa ka akan abubuwa masu yawa. Ka shiga cikin farincikin maigidanka.'
22Bawan da ya karbi talanti biyun, ya zo yace, 'Maigida, ka ba ni talanti biyu. Gashi kuwa na sami karin ribar wasu biyun.' 23Ubangidansa yace masa, 'Madalla, kai bawa na gari mai aminci! Ka yi aminci akan abubuwa kadan. Zan saka akan abubuwa masu yawa. Ka shiga cikin farincikin maigidanka.'
24Sai bawan da ya karbi talanti daya ya zo yace, 'Maigida, na san kai mai tsanani ne. Kana girbi inda baka yi shuka ba, kuma kana tattarawa inda ba ka watsa ba. 25Na ji tsoro, don haka sai na je na boye talantinka a rami. Duba, ga abinda yake naka.'
26Amma ubangidansa ya amsa yace, kai mugu malalacin bawa, ka san cewa ni mai girbi ne inda ban shuka ba kuma ina tattarawa inda ban zuba ba. 27To da ba sai ka kai kudina a banki ba, da bayan na dawo da sai in karbi abina da riba.
28Saboda haka ku kwace talantin daga gare shi ku baiwa mai talanti goman nan. 29Gama ga wanda yake da shi za'a kara masa har ma a yalwace za'a kara bashi. Amma ga wanda bashi da komai abinda ke nasa ma za'a kwace. 30Ku jefa wannan mugun bawan marar amfani, cikin duhu mai zurfi, inda ake kuka da cizon hakora.'
31Sa'adda Dan mutum zai zo cikin daukakarsa da dukan Mala'iku tare da shi, sa'annan zai zauna kursiyinsa na daukaka. 32A gabansa za'a tattara dukkan al'ummai, zai rarraba mutanen daya'daya, kamar yadda makiyayi yake rarraba tumaki daga awaki. 33Zai sa tumakin a hannunsa na dama, amma awakin a hannunsa na hagu.
34Sa'annan sarkin zai ce wa na hannun damarsa, 'Ku zo ku da Ubana ya albarkata, ku gaji mulkin da aka shirya maku kafin a kafa duniya. 35Gama na ji yunwa kuka bani abinci; Na ji kishi kuka bani ruwa; Na yi bakunci kun bani masauki; 36Na yi huntanci kuka tufasar dani; Na yi ciwo kuka kula dani; Ina kurkuku kuka ziyarceni.'
37Sa'annan masu adalcin za su amsa su ce, 'Ubangiji, yaushe muka ganka kana jin yunwa muka baka abinci? Ko kana jin kishi muka baka ruwan sha? 38Kuma yaushe muka ganka kana bakunci har muka baka masauki? Ko kuma kana huntanci da muka tufatar da kai? 39Yaushe kuma muka ganka kana ciwo ko a kurkuku har muka ziyarce ka?' 40Sa'annan Sarkin zai amsa masu yace, 'Hakika Ina gaya maku, duk abinda kuka yi wa daya mafi kakanta daga cikin 'yan'uwana a nan ni kuka yi wa.'
41Sa'annan zai cewa wadanda suke hannunsa na hagu, 'Ku rabu da ni, ku la'anannu, ku tafi cikin wutar jahannama da aka shirya wa Shaidan da aljannunsa, 42domin ina jin yunwa baku bani abinci ba; ina jin kishi ba ku bani ruwa ba; 43Ina bakunci amma baku bani masauki ba; ina huntanci, baku tufasar da ni ba; ina ciwo kuma ina kurkuku, baku kula da ni ba.'
44Sa'annan suma zasu amsa su ce, 'Ubangiji, yaushe muka ganka kana jin yunwa, ko kishin ruwa, ko kana bakunci, ko kana huntanci, ko ciwo, kuma a kurkuku, da bamu yi maka hidima ba?' 45Sa'annan zai amsa ya ce masu, 'Ina gaya maku hakika abin da baku iya yiwa mafi karanta daga cikin wadannan ba, ba ku yi mani ba.' 46Wadannan kuwa zasu tafi cikin madawwamiyar azaba amma adalai zuwa rai madawwami."

26

1Yayin da Yesu ya gama fadi masu wadannan maganganu, sai ya cewa almajiransa, 2"Kun sani sauran kwana biyu idin ketarewa ya zo, kuma za'a bada Dan mutum domin a gicciye shi.

3Sa'annan manyan firistoci da dattawan jama'a suka taru a fadar babban firist, mai suna Kayafa. 4Suka shirya yadda zasu kama Yesu a boye su kuma kashe shi. 5Amma suna cewa, "Ba a lokacin idin ba, domin kada tarzoma ta tashi daga cikin mutane."
6Sa'adda Yesu yake Baita'anya a gidan Saminu Kuturu, 7daidai lokacin da ya zauna a gefen teburin cin abinci, sai wata mata ta shigo da kwalbar mai, mai tsada, ta zuba wa Yesu a kansa. 8Amma da almajiransa suka ga haka, sai suka ji haushi suka ce, "Ina dalilin yin irin wannan asara? 9Ai da an sayar da wannan mai da kudi mai yawa a rabawa talakawa."
10Amma da yake Yesu ya san tunaninsu, sai yace masu, "Don me kuke damun matar nan? Ta yi abu mai kyau domina. 11Kuna da talakawa tare da ku koyaushe, amma ni ba zan kasance da ku ba koyaushe.
12Don a sa'adda ta zuba man nan a jikina, ta yi haka ne don jana'iza ta. 13Hakika Ina gaya maku, duk inda za ayi wannan bishara a dukan duniya, abin da matar nan tayi za'a rika ambatar da shi don tunawa da ita."
14Sai daya daga cikin sha biyun, mai suna Yahuza Iskariyoti, ya tafi wurin manyan firistocin, 15yace, "Me kuke da niyyar bani idan na mika maku shi?" Suka auna masa azurfa talatin. 16Daga wannan lokacin yayi ta neman zarafi da zai bada shi a wurinsu.
17To a rana ta fari na idin ketarewa almajiran suka zo wurin Yesu suka ce, "Ina kake so mu shirya maka da zaka ci abincin idin ketarewa?" 18Yace, "Ku shiga cikin birnin zaku sami wani mutum sai kuce masa, 'Mallam yace, "lokaci na ya kusa. Zan ci idin ketarewa a gidanka, da almajiraina."'" 19Almajiran suka yi kamar yadda Yesu ya umarce su, suka shirya abincin idin ketarewar.
20Da yamma ta yi, sai ya zauna domin ya ci tare da almajiransa goma sha biyu. 21Sa'adda suke ci, yace, "Hakika ina gaya maku, daya daga cikin ku zai bada ni." 22Suka yi bakin ciki, suka fara tambayarsa daya bayan daya, "Na tabbata ba ni bane ko, Ubangiji?"
23Sai ya amsa, "Wanda ke sa hannu tare da ni cikin kwano daya shi ne zai bada ni. 24Dan mutum zai tafi, kamar yadda aka rubuta akan sa. Amma kaiton mutumin da ta wurin sa za'a bada Dan mutum! Gwamma da ba'a haifi mutumin nan ba." 25Yahuza da zai bada shi yace, "Mallam ko ni ne?" Yace masa, "Ka fada da kanka."
26Yayin da suke ci, sai Yesu ya dauki gurasa, ya sa albarka, ya karya. Ya ba almajiran yace, "Ku karba, ku ci, wannan jiki nane."
27Sai ya dauki kokon yayi godiya, Ya ba su yace, "Ku sha, dukanku. 28"Gama wannan jinina ne na alkawari wanda aka zubar domin gafarar zunuban mutane da yawa. 29Amma ina gaya maku, ba zan kara shan ruwan inabin nan ba, sai ranar da zan sha shi sabo tare da ku a cikin mulkin Ubana."
30Da suka raira waka, sai suka ka tafi dutsen zaitun. 31Sai Yesu yace masu, "Dukan ku zaku yi tuntube a wannan dare sabili da ni, gama a rubuce yake, "Zan bugi makiyayin, garken tumakin kuma za su watse.' 32Amma bayan an tashe ni, zan riga ku zuwa Galili."
33Amma Bitrus yace masa, "Ko dama duka zasu fadi sabili da kai, ni kam bazan fadi ba." 34Yesu yace masa, "Hakika ina gaya maka, a wannan daren kafin carar zakara, za ka yi musun sani na sau uku." 35Bitrus yace masa, koda zan mutu tare da kai, bazan yi musunka ba." Sai sauran almajiran suma suka fadi haka.
36Sa'anna Yesu ya tafi tare da su, wurin da ake kira Getsaimani sai yace wa almajiransa, "Ku zauna a nan ni kuma zan je gaba in yi addu'a." 37Ya dauki Bitrus da kuma 'ya'ya biyu na Zabadi tare da shi, sai ya fara damuwa da juyayi. 38Sai yace masu, "Raina na cikin damuwa sosai har ga mutuwa. Ku kasance anan kuna tsaro tare da ni."
39Ya dan taka zuwa gaba kadan, sai ya fadi a fuskarsa, yayi addu'a. Yace, "Ya Ubana, in zai yiwu, bari kokon nan ya wuce ni. Duk da haka, ba nufina za'a bi ba, amma naka nufin." 40Ya koma wurin almajiran ya same su suna barci, sai ya cewa Bitrus, "Kai, ba zaku yi tsaro tare da ni ba koda sa'a daya? 41Ku yi tsaro kuma, kuyi addu'a domin kada ku fada cikin jaraba. Ruhu dai ya yarda amma, jiki ba karfi."
42Sai ya koma karo na biyu yayi addu'a, Yace, "Ya Ubana, in wannan kokon ba zai wuce ba sai na sha shi, bari nufinka ya kasance." 43Ya sake dawowa, ya same su suna barci, domin idanunsu sun yi nauyi. 44Sai ya sake barinsu ya tafi. Ya koma karo na uku yana addu'a yana fadin kalmomi iri daya.
45Sai Yesu ya koma wurin almajiran yace masu, "Har yanzu barci kuke kuna hutawa? Duba, lokaci ya kusato, kuma an bada Dan mutum ga hannun masu zunubi. 46Ku tashi mu tafi. Duba, wanda zai badani ya kusato."
47Sa'adda yana cikin magana Yahuza, daya daga cikin sha biyun, ya zo. Babban taro ya zo tare da shi daga wurin manyan firistoci da dattawan jama'a. Suna rike da takubba da kulake. 48To mutumin da zai bada Yesu ya rigaya ya basu alama, cewa, "Duk wanda na sumbata, shine. Ku kama shi."
49Nan da nan ya kaiga Yesu ya ce, "Gaisuwa, Mallam!" sai ya sumbace shi. 50Yesu kuwa yace masa, "Aboki, kayi abin da ya kawo ka." Sai suka iso suka sa hannuwansu kan Yesu suka kama shi.
51Nan take, daya daga cikin wadanda suke tare da Yesu ya mika hannunsa, ya zare takobinsa, ya sare wa bawan babban firist din kunne. 52Sai Yesu yace, masa, "Ka maida takobinka cikin kubensa, domin duk wadanda suka dauki takobi su ma ta wurin takobi za su hallaka. 53Ko kana tunanin ba zan iya kiran Ubana ba, ya kuma aiko da rundunar Mala'iku fiye da goma sha biyu? 54Amma to tayaya za'a cika nassi, cewa dole wannan ya faru?"
55A wannan lokacin Yesu yace wa taron, "Kun zo da takubba da kulake ku kama ni kamar dan fashi? Ina zaune kowace rana a haikali ina koyarwa, amma baku kama ni ba. 56Amma duk wannan ya faru ne don a cika abinda annabawa suka rubuta." Bayan haka sai dukkan almajiran suka bar shi suka gudu.
57Wadanda suka kama Yesu, suka kai shi wurin Kayafa babban firist, inda marubuta da duttawan jama'a suka taru. 58Amma Bitrus ya bi shi daga nesa, har zuwa farfajiyar babban firist din. Ya shiga ya zauna da masu tsaro domin ya ga abinda zai faru.
59A wannan lokaci manyan firistoci da duk 'yan majalisar suka fara neman shaidar karya akan Yesu, domin su samu su kashe shi. 60Amma ba su samu ko daya ba, ko dayake an samu shaidun karya dayawa da suka gabata. Amma daga baya sai wasu su biyu suka fito 61sukace "Wannan mutum yace zan iya rushe haikalin Allah, in kuma gina shi cikin kwana uku.'"
62Babban Firist din ya tashi tsaye yace masa, "Ba zaka ce komai ba? Wace irin shaida ce ake yi akanka?" 63Amma Yesu yayi shiru. Babban Firist ya ce, "Na umarce ka da sunan Allah mai rai, ka gaya mana ko kai Almasihu ne, Dan Allah." 64Yesu ya amsa masa, "Ka fada da bakin ka. Amma ina gaya maka, daga yanzu zaka ga Dan mutun na zaune a hannun dama na iko, ya na zuwa akan gizagizai na sama."
65Sai babban firist din ya yayyaga rigarsa, yana cewa, "Yayi sabo! don me ku ke neman wata shaida kuma? Duba, yanzu kun ji sabon. 66Menene tunaninku?" Suka amsa sukace, "Ya cancanci mutuwa."
67Sai suka tofa masa yawu a fuska, suka kuma yi masa duka, suka kuma mammare shi da tafin hannuwansu, 68sukace, "Ka yi mana anabci, kai Almasihu. Wanene wanda ya dokeka.
69To Bitrus kuwa na zaune a farfajiyar, sai wata yarinya baiwa ta zo wurinsa tana cewa, "Kaima kana tare da Yesu na Galili." 70Amma ya yi musun haka a gaban su duka, yace, "Ban ma san abinda kike magana akai ba."
71Da ya fita zuwa bakin kofa, nan ma wata yarinyar baiwa ta gan shi tace wa wadanda suke wurin, "Wannan mutumin ma yana tare da Yesu Banazare." 72Sai yayi musun haka kuma, har da rantsuwa, yace, "Ban san mutumin nan ba."
73Bayan dan lokaci kadan wadanda suke a tsaye suka zo wurin Bitrus suka ce masa, "Hakika kai daya daga cikin su ne, gama harshen ka ya tonaka." 74Sai ya fara rantsuwa irin ta la'ana, yana cewa, "Ban san wannan mutumin ba," nan da nan zakara yayi cara. 75Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya fada, "Kafin carar zakara zaka yi musun sani na sau uku." Sai ya fita waje yayi kuka mai zafi."

27

1Da gari ya waye, duk manyan firistoci da dattawan jama'a suka shirya yadda zasu kulla makirci domin su kashe shi. 2Suka daure shi, suka mika shi ga gwamna Bilatus.

3Sa'adda Yahuza, wanda ya bashe shi, ya ga an zartarwa Yesu hukuncin kisa, ya nemi tuba ya kuma mayar da azurfar talatin ga manyan firistocin da dattawan, 4yace, "Na yi zunubi ta wurin cin amanar mara laifi." Amma sukace, "Ina ruwan mu? Ka ji da shi da kanka?" 5Sai ya jefar da kwandalolin azurfar a kasa cikin haikalin ya kuma bar su, ya tafi ya rataye kansa.
6Sai babban firist ya dauki kwandalolin azurfar ya ce, "Ba daidai bane bisa ga shari'a musa wannan cikin ma'aji, saboda kudin jini ne." 7Sai suka tattauna al'amarin a tsakanin su, kudin kuma suka sayi filin maginin tukwane domin makabatar baki. 8Dalilin wannan ne ake kiran wurin, "Filin jini" har yau.
9Sai abin da aka fada ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa, "Suka dauki tsabar azurfa talatin na farashin da mutanen Isra'ila suka sa a kansa, 10suka bayar domin sayen filin mai tukwane, kamar yadda Ubangiji ya umarce ni."
11Sai Yesu ya tsaya a gaban gwamna, gwamna ya kuma tambaye shi, "Kai sarkin Yahudawa ne?" Yesu ya amsa, "Haka ka fada." 12Amma da manyan firistocin da dattawan suka zarge shi, bai ce komai ba. 13Sai Bilatus yace masa, "Baka ji dukan zarge-zargen da ake yi maka ba?" 14Amma bai ce masa ko kalma guda ba, sai gwamna yayi matukar mamaki.
15To lokacin bikin idi, al'adar gwamna ne ya saki mutum guda wanda jama'a suka zaba. 16A wannan lokacin suna da wani sanannen dan kurkuku mai suna Barabbas.
17To da suka tattaru, sai Bilatus yace masu, "Wa kuke so a sakar maku? Barabbas, ko Yesu wanda ake kira Almasihu?" 18Saboda ya san sun kawo shi ne domin kishi. 19Da yake zaune a kujerar shari'a, matarsa ta aika masa cewa, "Ka fita sha'anin mutumin nan marar laifi. Saboda na sha wahala sosai a yau cikin mafarki saboda shi."
20A lokacin nan manyan firistoci da dattawa suka rinjayi ra'ayin jama'a suce a sakar masu da Barabbas, a kashe Yesu. 21Sai gwamna ya tambayesu, "Wa kuke so a sakar maku?" Sukace, "Barabbas." 22Bilatus yace masu, "Me zan yi da Yesu wanda ake kira Almasihu?" Sai duka suka amsa, "A gicciye shi."
23Sai yace, "Don me, wane laifi ya aikata?" Amma suka amsa da babbar murya, "A gicciye shi" 24Amma da Bilatus ya ga ba zai iya komai ba don hargitsi zai iya barkewa, ya dauki ruwa ya wanke hannuwansa a gaban jama'a, yace, "Ba ni da laifi ga jinin mutumin nan marar laifi. Ku yi abin da kuka ga dama."
25Duka mutanen sukace, "Bari jininsa ya kasance a kan mu da 'ya'yan mu." 26Sai ya sakar masu da Barabbas amma yayi wa Yesu bulala ya mika shi garesu domin su gicciye shi.
27Sai sojojin gwamna suka dauki Yesu zuwa farfajiya suka kuma tara dukan rundunar sojoji. 28Suka yi masa tumbur sa'annan suka sa masa jar alkyabba. 29Sai suka yi masa rawanin kaya suka sa a kansa, suka kuma bashi sanda a hannunsa na dama. Suka rusuna a gabansa suna masa ba'a, suna cewa, "Ranka ya dade, Sarkin Yahudawa!"
30Suka kuma tofa masa yawu, suka kwace sandar suka buga masa a ka. 31Bayan sun gama masa ba'a, suka cire masa alkyabbar suka sa masa kayansa, suka jagorance shi zuwa wurin da za a gicciye shi.
32Da suka fito waje, sai suka iske wani Bakurame mai suna Saminu, wanda suka tilasta ya tafi tare dasu domin ya dauki gicciyen. 33Suka iso wani wuri da ake kira Golgotta, wanda ke nufin,"Wurin kwalluwa." 34Suka bashi ruwan inabi da aka gauraya da wani abu mai daci. Amma da ya 'dan-'dana shi sai ya ki sha.
35Bayan da suka gicciye shi, suka kada kuri'a a kan rigarsa. 36Suka kuma zauna suna kallonsa. 37A sama da kansa suka sa abinda ake tuhumarsa da ita a rubuce, "Wannan shine sarkin Yahudawa."
38An gicciye shi da 'yanfashi guda biyu, daya ta damansa dayan kuma ta hagunsa. 39Wadanda suke wucewa suna zaginsa, suna girgiza kai, 40suna kuma cewa, "Kai da kace zaka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku, ka ceci kanka mana! In dai kai Dan Allah ne, ka sauko daga gicciyen!"
41Ta haka ma manyan firistocin suka rika yi masa ba'a, tare da marubuta da shugabannin, suna cewa, 42"Ya ceci wasu amma ya kasa ceton kansa. Shi ne sarkin Isra'ila. Ya sauko mana daga kan gicciyen, sai mu ba da gaskiya gareshi.
43Tun da ya yarda da Allah. Bari Allahn ya cece shi mana, saboda yace, "Ni dan Allah ne." 44Hakan nan ma 'yanfashin guda biyu da aka gicciye su tare suka zage shi.
45To tun da tsakar rana sai duhu ya rufe kasar gaba daya har karfe uku na yamma. 46Wajen karfe uku, Yesu ya tada murya mai karfi yace, "Eli, Eli lama sabaktani?" wanda ke nufin, "Allahna, Allahna, don me ka yashe ni?" 47Da wadanda suke tsaye kusa suka ji haka, sai sukace, "Yana kiran Iliya."
48Nan take wani ya ruga da gudu ya dauki soso ya tsoma cikin ruwan inabi mai tsami ya soka kan sandar kara ya mika masa ya sha. 49Sai sauran sukace, "Rabu da shi mu gani ko Iliya zai zo ya cece shi." 50Sai Yesu ya ta da murya mai karfi yayi kuka sai ya saki ruhunsa.
51Sai labullen haikali ya yage gida biyu daga sama zuwa kasa. Kasa kuma ta girgiza, duwatsu suka farfashe. 52Kaburbura suka bude, tsarkaka kuwa wadanda suke barci da yawa suka tashi. 53Suka fito daga kaburbura bayan tashinsa, suka shiga birni mai tsarki suka bayyana ga mutane da yawa.
54Da hafsan sojan da wadanda suke kallon Yesu suka ga girgizar kasar da abinda ya faru, suka ji tsoro kwarai sukace, "Hakika wannan Dan Allah ne" 55Mata dayawa da suka bi Yesu daga Galili domin su lura da shi suka tsaya suna kallo daga nesa. 56A cikin su akwai Maryamu Magadaliya, Maryamu uwar Yesu da Yusufu, da uwar 'ya'yan Zabadi.
57Da yamma sai wani attajiri mutumin Armatiya ya zo, mai suna Yusufu wanda shi ma almajirin Yesu ne. 58Ya je wurin Bilatus ya roka a bashi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a bashi.
59Yusufu ya dauki jikin, ya rufe shi da likafani mai tsabta, 60sai ya sa shi a cikin sabon kabarinsa da ya sassaka cikin dutse. Sai ya mirgina babban dutse a bakin kofar kabarin ya tafi. 61Maryamu Magadaliya da dayan Maryamun suna nan zaune akasin kabarin.
62Washegari, wato bayan ranar Shiri, Sai manyan firistoci da Farisawa suka taru tare da Bilatus. 63Sukace, "Mai gida, mun tuna lokacin da mayaudarin nan yake da rai, yace, "Bayan kwana uku zan tashi." 64Saboda haka, ka bada umarni a tsare kabarin na kwana uku. In ba haka ba almajiransa zasu zo su sace shi, kuma su ce wa mutane, "Ya tashi daga mattatu." Kuma yaudarar karshe zata fi ta farko muni."
65Bilatus yace masu, "Ku dauki masu tsaro. Kuyi tsaro iyakar karfin ku." 66Sai suka tafi suka tsare kabarin, suka hatimce dutsen, suka sa masu tsaro.

28

1Da daddare ranar Asabaci, rana ta fari ga mako ta fara gabatowa, Maryamu Magadaliya da daya Maryamun suka zo don su ziyarci kabarin. 2Sai aka yi girgizar kasa mai karfi, saboda mala'ikan Ubangiji ya sauko daga sama ya kuma murgine dutsen ya zauna a kai.

3Kamanninsa kamar walkiya, tufafinsa kuma fari fat kamar suno. 4Masu tsaron suka razana don tsoro suka zama kamar matattun mutane.
5Mala'ikan ya yi wa matan magana cewa, "Kada ku ji tsoro, nasan kuna neman Yesu wanda aka gicciye. 6Baya nan, amma ya tashi kamar yadda ya fada. Ku zo ku ga wurin da aka kwantar da shi. 7Ku hanzarta ku gaya wa almajiransa, 'Ya tashi daga matattu. Duba, ya tafi Galili, can zaku same shi.' Gashi ni kuwa na fada maku."
8Matan suka yi hanzari suka bar kabarin da tsoro da murna, suka ruga domin su sanar wa almajiransa. 9Sai ga Yesu ya tare su, yace masu, "A gaishe ku." Sai matan suka kama kafar sa, suka kuma yi masa sujada. 10Sai Yesu yace masu, "Kada ku ji tsoro. Ku je ku fada wa 'yan'uwana su je Galili. Can zasu ganni."
11Sa'adda matan suke tafiya, sai wadansu masu tsaro suka shiga gari suka fada wa Shugabanin Firistoci dukan abin da ya faru. 12Firistocin suka hadu da dattawa suka tattauna al'amarin, sai suka bada kudi masu yawa ga sojojin 13Sukace masu, "Ku gaya wa sauran cewa, "Almajiran Yesu sun zo da daddare sun sace gangar jikinsa lokacin da muke barci."
14Idan wannan rahoto ya isa wurin gwamna, za mu lallashe shi mu ja hankalinsa mu raba ku da damuwa." 15Sai sojojin suka karbi kudin suka yi abinda aka umarcesu. Wannan rahoto ya bazu a tsakanin Yahudawa, ya ci gaba har zuwa yau.
16Amma almajiran sha daya suka tafi Galili, kan dutsen da Yesu ya umarcesu. 17Da suka gan shi, suka yi masa sujada, amma wadansu suka yi shakka.
18Yesu ya zo wurin su ya yi masu magana, yace, "Dukan iko dake sama da kasa an ba ni. 19Sai kuje ku almajirantar da dukan al'ummai. Kuna yi masu baftisma cikin sunan Uba da na Da da na Ruhu Mai Tsarki.
20Ku koya masu su kiyaye dukan abin da na umarce ku. Duba, ni kuma kullum ina tare da ku har karshen zamani."

Markus

1

1Wannan itace farkon bisharar Yesu Almasihu, Dan Allah. 2kamar yadda aka rubuta cikin littafin annabi Ishaya. Duba, ina aika manzona, a gabanka, wanda zai shirya maka hanya. 3Akwai murya mai kira a jeji, tana cewa ka shirya hanyar Ubangiji. ka daidaita ta.

4Yahaya ya zo, yana baptisma acikin jeji yana wa'azin tuba, domin gafarar zunubai. 5Dukan kasar Yahudiya da mutanen Urshalima suka zo wurin sa, a ka kuma yi masu baptisma a kogin urdun. suna furta zunubansu. 6Yahaya yana saye da tufa ta gashin rakumi, yana kuma da damara ta fata a kugunsa, abincinsa fara ce da zuma.
7Yana wa'azi, ya ce "akwai mai zuwa a bayana wanda ya ke da iko fiye da ni. wanda ko maballin takalminsa ban isa in kwance ba. 8Ni ina yi maku baptisma da ruwa, amma mai zuwa a bayana zai yi maku baptisma da Ruhu Mai Tsarki".
9Sai ya kasance a kwanakin nan Yesu ya zo daga Nazarat ta Galili, sai Yahaya ya yi masa baptisma a kogin urdun. 10Sa'adda Yesu ya fito daga ruwan, sai sama ta bude, sai Ruhu ya sauko a bisansa da kamanin kurciya. 11Sai wata murya ta zo daga sama, tana cewa, "Kai kaunataccen Dana ne. zuciyata ta na murna da kai kwarai".
12Sai Ruhu ya iza shi zuwa jeji. 13Yana a jeji kwana arba'in, Shaidan yana jarabtar sa. Yana cikin jeji da dabobi, sai malaiku su ka yi masa hidima.
14Bayan da aka kama Yahaya, Yesu ya shiga kasar Galili yana wa'azin bisharar Allah. 15Yana cewa, "Lokaci ya yi, gama mulkin Allah ya kusato. Ku tuba ku bada gaskiya ga bishara".
16Sa'adda ya ke wucewa a gefen takun Galili, sai ya ga Saminu da Andarawus, dan'uwansa suna jefa taru a teku, domin su masunta ne. 17Yesu ya ce masu ku zo, ku biyo ni, ni kuwa sai in maisheku masuntan mutane". 18Nan da nan suka bar tarun su, suka bi shi.
19Sa'adda Yesu ya yi tafiya kadan, sai ya ga Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan'uwansa; suna gyaran tarunsu a jirgin ruwa. 20Sai ya kira su, su kuwa suka bar mahaifinsu Zabadi a jirgin ruwan da ma'aikatansu, sai su ka bi shi.
21Da su ka shigo cikin kafanahum, a ranar asabar, Yesu ya shiga majami'a ya koya masu. 22Su ka yi mamakin koyarwarsa, domin ya na koya masu da iko ba kamar marubuta ba.
23A nan cikin majami'a akwai wani mutum mai kazamin ruhu, sai ya yi ihu da karfi. 24Yana cewa Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo ne domin ka halakar da mu? Na san wanene kai. Kai ne Mai Tsarki na Allah". 25Sai Yesu ya tsauta wa kazamin ruhun ya ce, "Ka yi shiru ka fita daga cikinsa". 26Bayan da kazamin ruhun ya buga shi kasa, sai kazamin ruhun ya yi ihu sa'annan ya fita daga jikinsa.
27Sai dukan mutanen su ka yi mamaki kwarai, suna tambayar junansu menene wannan? wace sabuwar koyarwa ce da iko haka? har yana umartar kazaman ruhohi suna kuwa yi masa biyayya!" 28Nan da nan labarinsa ya bazu ko'ina a dukkan kewayen kasar Galili.
29Bayan da suka bar majami'a, sai su ka shiga gidan Saminu da Andarawus, suna kuma tare da Yakubu da Yahaya. 30Surikar Saminu tana kwance ba lafiya tana fama da zazzabi. Sai suka gaya wa Yesu game da ita. 31Sai ya zo, ya kama hannunta, ya daga ta, sai zazzabin ya sake ta, ta fara yi masu hidima.
32Da yamman nan, bayan da rana ta fadi, sai su ka kawo masa dukan marasa lafiya da masu fama da aljanu. 33Dukan mutanen garin su ka taru a bakin kofa. 34ya warkar da masu ciwo da yawa da masu chututtuka iri-iri, ya kuma fitar da bakaken aljanu, amma bai yarda aljanun su yi magana ba domin sun san shi.
35Ya tashi da sassafe, tun da sauran dare, ya tafi wurin da ba kowa, a can ya yi add'ua. 36Saminu da wandanda suke tare da shi suka neme shi. 37Suka sa me shi, sai su ka ce masa, "kowa yana nemanka".
38Ya ce, bari mu tafi wani wuri, zuwa wadansu garuruwan da ke kewaye, Saboda in yi wa'azi a can kuma. Wannan shi yasa na zo nan". 39Ya tafi dukan kasar Galili, yana wa'azi a majimi'un su yana kuma fitar da aljanu.
40Wani kuturu ya zo wurinsa. Yana rokonsa, ya durkusa. Ya ce masa, "in ka yarda kana iya warkar da ni. 41Sai ya yi juyayi, Yesu ya mi ka hannun sa ya ta ba shi ya na ce masa "Na yarda. Ka sarkaka". 42Nan da nan kuturtar ta barshi, ya kuma sa mu tsarkakewa.
43Yesu ya yi masa gargadi sosai, ya salame shi. 44Ya ce masa "ka tabbata fa kada ka gayawa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, sai ka je ka yi hadaya domin tsarkakewa kamar yadda Musa ya umurta, domin shaida.
45Amma da ya fita sai ya fara gaya wa kowa, ya baza maganar a ko'ina, har Yesu bai iya tafiya a sake a garin ba. Ya tafi ya tsaya a wuraren da ba kowa, mutane kuwa su ka zo wurinsa daga ko'ina.

2

1Da ya dawo Kafarnahum bayan yan kwanaki kadan, aka ji cewa yana gida. 2Da yawa suka taru a can, ba wuri har kofa, sai Yesu ya yi masu magana.

3Sai wadansu mutane su ka zo wurinsa dauke da wuni mutum shanyayye, mutane hudu na dauke da shi. 4Lokacin da ba su iya zuwa kusa da shi ba domin yawan jama'a, sai su ka daye jinkar dakin daidai da inda ya ke. Bayan da suka huda ramin suka saukar da gado wanda shanyayyen ke kwance a kai.
5Da ganin bangaskiyarsu, Yesu ya ce wa shanyayyen mutumin, "Da, an gafarta maka zunuban ka". 6Amma wadansu marubuta da ke zaune a nan, suka yi tunani aransu. 7Yaya wannan mutum zai yi magana haka? Ya yi sabo! wa ke iya gafarta zunubi "sai Allah kadai?"
8Nan da nan Yesu ya sani a ruhunsa, abinda suke tunani a tsakaninsu. Ya ce masu, "Me ya sa kuke tunanin wannan a zuciyarku? 9Me yafi sauki a cewa shanyayyen mutumin, 'An gafarta maka zunuban ka' ko kwa a ce masa, 'tashi, ka dauki shinfidarka, ka yi tafiyarka'?
10Amma domin ku san cewa Dan mutum na da ikon gafarta zunubi a duniya, ya ce wa shanyayyen, 11"Na ce maka, tashi, dauki tabarmanka, ka tafi gidan ka." 12Sai nan da nan ya tashi ya dauki tabarmarsa, ya fita gidan a gabansu, dukansu su ka yi mamaki, su ka girmama Allah, "suka ce ba mu taba ganin abu irin wannan ba."
13Ya sake fita gefen tafki, dukan taron jama'a suka zo wurinsa, sai ya koya masu. 14Sa'adda ya na wucewa, ya ga Levi dan Halfa yana zaune a wurin karbar haraji, sai ya ce masa, "Ka biyo ni." Ya tashi, ya bi shi.
15Sa'adda Yesu ya shiga gidan Levi yana cin abinci, masu karbar haraji da masu zunubi da yawa su ka zo wurinsa da almajiransa, jama'a masu yawan gaske suka ka bi shi. 16Da Marubuta wadanda su ke Farisawa, sun ga cewa Yesu na cin abinci da masu zunubi da masu karbar haraji, sai su ka ce wa almajiransa, "Me ya sa ya ke ci da masu karbar haraji da mutane masu zunubi?"
17Da Yesu ya ji wannan ya ce masu, "Mutane wadanda ke da lafiya a jiki ba su bukatar likita; sai dai ko marasa lafiya ke bukatarsa. Ban zo domin in kira mutane masu a dalci ba, amma mutane masu zunubi."
18Almajiran Yahaya da Farisawa suna azumi, sai wadansu mutane suka zo suka ce, "Don me almajiran Yahaya da almajiran Farisawa na azumi amma na ka almajiran ba su yi?" 19Sai Yesu yace masu, "Abokan ango, za su yi azumi sa'adda ango yake tare da su? muddin suna tare da ango ba za su yi azumi ba.
20Amma kwanaki za su zo da za a dauki angon daga gare su, a wadancan kwanakin ne, za su yi azumi. 21Babu wanda zai dinka sabuwar riga ya hada ta da tsohuwar riga, sai rigar ta yage, kuma ta yi mummunar yagewa.
22Babu wanda zai sa sabon ruwan inabi a cikin tsohuwar salka, ai sai salkar ta fashe kuma ruwan inabin ya zube. duka biyu ruwan inabin da salkar arasa su. A maimakon haka, sai ka sanya sabon ruwan inabi cikin sabuwar salka."
23A ranar asabar Yesu ya tafi cikin gonakin hatsi, sai almajiransa su ka fara zagar hatsi, 24Sai Farisawa su ka ce masa, "Duba, don me suke yin abin da bai dace a yi ranar Asabar ba?"
25Yace masu, Ba ku karanta ba abinda Dauda ya yi sa'adda yake jin yunwa, shi da mutanen da ke tare da shi? 26Yadda ya shiga gidan Ubangiji, sa'adda Abiyata ya ke babban firist, ya ci gurasa da ke ta firist wadda bai dace wani ya ci ba sai Firistoci. Har kuma ya ba wadanda ke tare da shi?"
27Yesu yace, "Asabar an yi ta don mutum ne, ba a yi mutum don Asabar ba. 28Saboda haka, Dan Mutum Ubangiji ne, har da na Asabar."

3

1Sai kuma ya sake tafiya cikin Majami'a sai ga wani Mutum mai shanyayyen hannu. 2Wadansu mutane suna kallonsa sosai, su gani ko zai warkar da shi a ranar Asabar. don su zarge shi.

3Yesu ya ce wa mai shanyayyen hanun " Ka tashi ka tsaya a tsakiyar kowa." 4Sai ya ce wa mutane, "Ya dace a yi abu mai kyau aranar Asabar ko a yi mugunta; a ceci rai, ko a yi kisa? "Amma suka yi shiru.
5Sai ya dube su cikin fushi, yana bakin ciki da taurin zuciyar su, ya ce wa mutumin ka mikar da hanunka, sai ya mikar da hanunsa Yesu kuwa ya warkar da shi. 6Sai Farisiyawa suka fita da sauri zuwa wurin mutanen Hirudus suka shirya yadda za su kashe shi.
7Sai Yesu da almajiransa, suka tafi bakin teku. sai mutane dayawa suka bi shi, daga Galili da Yahudiya 8Daga Urushalima da Edom gaba da Urdun da kewayan Taya da Sidon, da baban taro, ya ji abinda yake yi. suka zo wurinsa.
9Ya tambayi almajiransa su shirya masa karamin jirgin ruwa domin yawan mutane, domin kada su murkushe shi. 10Ya warkar da mutane da yawa, yadda duk wadanda suke da cuttutuka suna kokari su taba shi.
11Duk sa'adda kazaman ruhohin suka ganshi, sai su durkusa a gabansa su yi ihu da karfi su ce, kai Dan Allah ne." 12Ya umarce su da karfi kada su sa a san shi.
13Ya hau saman dutsen, ya kira wadanda yake bukar su, su zo wurinsa. 14Ya zabi guda goma sha biyu (ya kira su manzanni). Wadanda zasu kasance tare da shi, ya kuma aike su, su yi wa, azi, 15Ya kuma basu Ikon fitar da aljanu. 16Ya zabi guda goma sha biyu wato Saminu kuma yaba shi suna Bitrus.
17Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan-uwan Yakubu wanda ya basu sunan Buwanarjis watau 'ya'yan tsawa, 18da Andarawus da Filibus da Bartalamawus da Matta da Toma da Yakubu dan Halfa, da Taddawus da Saminu Ba-kananiye, 19da Yahuza Iskariyoti wanda zai bashe shi.
20Sa'adda ya shiga gida, Taron kuwa ya sake haduwa, har ya hana su cin abinci, 21Da iyalansa suka ji haka, sai suka fito sun kamo shi, saboda sun ce, "Ai, baya cikin hankalinsa " 22Marubutan da suka zo daga Urushalima suka ce "Ai Ba'alzabuba ne ya hau shi, da ikon sarkin aljannu kuma yake fitar da aljannu."
23Yesu ya kirawo su wurinsa ya ce da su cikin misalai, "Yaya shaidan zai iya fitar da shaidan? 24idan mulki ya rabu gida biyu ba zai tsayawa ba. 25Haka in gida ya rabu kashi biyu, gaba da kansa bai zai tsaya ba.
26Shaidan kuma in ya tayar wa kansa ya rabu, ba zai iya tsayawa ba, gama karshen sa ya zo kenan. 27Amma ba mai iya shiga gidan kakkarfan mutum ya kwace kayansa, ba tare da ya fara daure kakkarfan mutumin ba, sa'an nan kuma ya kwashe kayan gidansa.
28Hakika, ina gaya maku, dukan zunuban da mutane suka yi za a gafarta masu, da kowane irin sabon da suka furta, 29amma fa duk wanda yayi sabon Ruhun Mai Tsarki baza a gafarta masa ba ko kadan, ya zama mai zunubi har abada." 30"Yesu ya fadi wadannan abubuwa domin suna cewa yana da ba kazamin ruhu,"
31Sa'an nan uwatasa, da "Yan'uwansa suka zo suna tsaye a waje. sai suka aika masa, suna kuma umurtar sa ya zo. 32Taro kuwa na zaune kewaye da shi, sai suka yi magana da shi da cewa, ga uwarka da yan-uwanka suna nan a waje, suna nemanka."
33Ya amsa masu, "Dacewa su wanene uwa-ta da "yan'uwa na?"34Sai ya waiwayi wadanda suke zaune kewaye da shi, yace, "Ga uwa-ta da yan-uwana anan! 35Gama duk wanda ke yin abin da Allah yake so, shine dan'uwana da yar, uwata, da kuma uwa-ta."

4

1Ya kuma fara koyarwa a bakin teku. Akwai babban taro kewaye da shi, sai ya shiga cikin jirgin ruwa a cikin tekun, ya kuwa zauna. Duk taron kuwa na kan tudu a bakin tekun. 2Ya koya masu abubuwa da yawa da misalai, a cikin koyawarsa ya ce masu,

3"ku saurara! wani mai shuka ya tafi shuka. 4Yana cikin yafa iri, sai wadansu iri suka fadi a kan hanya, tsuntsaye kuma suka zo suka tsince su. 5Wadansu kuma suka fadi a kan dutse inda ba kasa dayawa. Nan da nan kuwa suka tsiro saboda rashin zurfin kasa.
6Da rana fa ta daga, sai suka yankwane da yake ba su da saiwa sosai, sai suka bushe. 7Wadansu kuma suka fadi cikin kayayuwa su ka yi girma sai kayayuwan suka shake su, ba su yi tsaba ba.
8Wadansu kuma suka fadi a kasa mai kyau, suka yi yabanya, suka yi tsaba, suka yi girma, wadansu ribi talattin wadansu sittin, wadansu kuma dari". 9Sai ya ce, Duk mai kunnen ji, ya ji,"
10Sa'adda Yesu yake shi kadai, wadanda suke kusa dashi tare da sha biyun suka tambaye shi ma'anar misalan. 11Sai ya ce masu, "ku an yardar maku, ku san asirin mulkin Allah, amma ga wadanda ba su cikinku, komai sai a cikin Misalai, 12don gani da ido sun gani, amma ba su gane ba. ji kuma, sun ji, amma ba su fahimta ba, don kada su juyo a gafarta masu,"
13Ya ce masu, "Ashe, ba ku fahimci wannan misalin ba? yaushe za ku fahimci sauran? 14Mai shukan nan fa maganar Allah yake shukawa. 15Wadanda suka fadi a hanyar kuwa, su ne kwatancin wadanda. a aka shuka mganar a zuciyarsu, Da suka ji, nan da nan sai shaidan ya zo ya dauke Maganar da aka shuka a zuciyarsu.
16Haka kuma wadanda aka shuka a wuri mai duwatsu, sune wadanda da zarar sun ji Maganar sai su karba da farin ciki. 17Su kuwa basu da tushe, ba su da karfi, idan kunci ko tsanani ya zo saboda kalmar, nan da nan sai su yi tuntube.
18Wadansu kuma su ne kwatacin wadanda suka fadi cikin kayayuwa, sune wadanda suka ji Maganar, 19amma abubuwan duniya, da rudin dukiya da kuma kwadayin wadansu abubuwa, sukan shiga su shake Maganar, har ta zama marar amfani. 20Wadanda aka shuka a kasa mai kyau kuwa, sune kwatancin wadanda suke jin Maganar, su karba, su kuma yin amfani da ita wadansu ribi talatin, wadansu sittin, wadansu dari."
21ya ce masu, "Shin, ana kawo fitila a cikin gida don a rufe ta da kwando ko a ajiye ta a karkashin gado? ku kan kawo ta ne don ku dora ta a kan madorinta. 22Ba abin da yake boye, da baza a sani ba ko kuma ba abinda ke asirce da bazaya bayyana a fili ba. 23Bari mai kunnen ji, ya ji!"
24Sai ya ce masu, ku mai da hankali a kan abin da kuka ji, Mudun da ka auna, da shi za a auna maka, har ma a kara maka. 25Domin mai abu akan karawa, marar abu kuma za a karba daga wurinsa a kuma karawa mai shi."
26Sai ya ce, "Mulkin Allah kamar mutum yake mai yafa iri a kasa. 27A kwana a tashi har irin ya tsiro, ya girma bai kuwa san ta yaya aka yi ba. 28Kasa da kanta, takan ba da amfani, tsiro shine ne na farko, 29Sai kai, sa'anan sai kwaya mai kwari. Sa, adda amfani ya nuna, sai ya sa lauje ya yanke nan da nan, wato kaka ta yi kenan."
30Ya kuma ce, "Da me za mu kwatanta Mulki Allah? ko kuwa da wane misali za mu misalta shi? 31Kamar kwayar zarra yake wadda, in an shuka ta, ko da yake ita ce mafi kankanta cikin kwayoyi a duniya. 32Duk da haka in an shuka ta, sai ta yi girma fiye da duk sauran ita-tuwan da ke a jeji tayi manyan rassa, har tsuntsaye su iya yin sheka arassanta."
33Da misalai da yawa, irin wadannan ya yi masu Magana, dadai gwargwadon ganewarsu, 34ba ya fada masu kome sai da misali, amma a kebe, yakan bayyana wa almajiransa dukan abu.
35A ranan nan da yama ta yi yace masu "Mu haye wancan ketaren." 36Sai suka bar taron, suka tafi tare da shi acikin cikin jirgin. wadansu jirage kuma na tare da shi. 37Sai babban hadari da iska mai karfi ya taso, rakuman ruwa kuma na ta girgizawa cikin jirgin, har jirgin ya cika.
38Yesu kuwa na daga karshen bayan jirgin a kan kujera, yana barci, sai suka tashe shi, suka ce masa "Malam za mu hallaka ba ka kula ba?" 39Sai ya farka, ya tsawata wa Iskar. Ya kuma ce wa ruwan tekun, "Ka natsu! ka yi shiru!" Sai Iskar ta kwanta, wurin duk ya yi shiru.
40Ya ce masu, "Don me kuka firgita haka? Har yanzu baku da bangaskiya ne?" 41Sai suka tsorata kwarai suka ce wa juna, "wanene wannan kuma, wanda har Iska da teku ma suke yi masa biyayya?"

5

1Da su ka zo daya ketaren tekun, wanda ya ke cikin yankin Garasinawa. 2Sa'adda Yesu ya sauko daga cikin jirgin ruwan sai wani mutum mai aljanu ya fito daga cikin kaburbura ya tarbe shi.

3Mutumin yana zama a cikin kaburbura. An daure shi da sarkoki da mari 4An daure shi da sarkoki da mari sau da yawa, amma ya tsuntsunke sarkoki da marin. har ma ba wanda zai iya daure shi kuma.
5Dare da rana a cikin kabarbarun da duwatsu mutumin ya na ihu ya na yaiyage jikinsa da duwatsu masu kaifi. 6Sa'adda ya hango Yesu daga nesa, sai ya tarbi Yesu ya durkusa a gabansa.
7Ya tada muryarsa da karfi ya ce, ina ruwa na da kai? Yesu Dan Allah Madaukaki Ina rokon ka da sunan Allah kada ka bani wahala, 8Gama Yesu ya ce masa kai aljani ka fito daga cikinsa."
9Ya tambaye shi, "Yaya sunanka? Ya ce suna na tari gama muna da yawa. 10Ya yi ta rokonsa kada ya raba su da wannan yankin kasar.
11Akwai babban garken aladu a wurin suna kiwo a gindin tsauni. 12Sai suka roke shi ya bar su su shiga cikin wadannan aladun. 13Shi kuma ya yardar masu. Aljanun suka fita suka shiga cikin aladun su kimanin dubu biyu. Aladun dubu biyu suka gangaro daga gindin tsaunin suka fada cikin ruwa.
14Mutanen da ke kiwon aladun su ka shiga cikin gari da kewaye suka bada labarin abin da ya faru. Mutane da yawa suka je su ga abin da ya faru 15Sai suka zo wurin Yesu suka ga mutumin mai aljanun a zaune, cikin hankalinsa, saye da tufafi, sai suka tsorata.
16Wadanda suka zo su ka ga abin da ya faru da mutumin mai aljanun, suka je suka fada wa mutane abin da suka gani game da aladun. 17Mutanen suka roke shi ya fita daga yankin kasarsu.
18Shi mutumin da aljanu ke iko da shi, sa'adda ya ga Yesu zai shiga cikin jirgin ruwa ya tafi, ya roki Yesu da ya bi shi. 19Amma Yesu bai yarda masa ba. Ya ce masa ka tafi gidanku, wurin mutanenka ka gaya ma su alherin da Ubangiji ya yi maka. 20Mutumin ya shiga cikin Dikafolis yana shaidar babban abin da Yesu ya yi masa, dukansu suka cika da mamaki.
21Sa'adda Yesu ya sake ketaren kogin zuwa daya gefen, acikin jirgin, sai taron jama'a suka keweye shi, a gefen tekun. 22Sai wani daya daga cikin shugabannin Majami'a mai suna Yayirus, ya zo, wurinsa sa'adda ya ganshi ya durkusa a gabansa. 23Ya yi ta rokonsa, yana cewa, "Diya ta ba ta da lafiya har ma ta kusa mutuwa. Ina rokonka mu je gida na ka dora ma ta hannu domin ta warke. ta rayu." 24Sai ya tafi tare da shi, babban taro suka biyo shi har ma suna matse shi.
25Akwai wata mace wadda ta ke zubar jini ta kai tsawon shekara goma sha biyu. 26Ta sha wahala kwarai da gaske ta je wurin likitoci da yawa ta kashe kudi sosai, amma ba ta warke ba abin ma sai karuwa ya ke yi. 27Ta ji labarin Yesu. Sai ta biyo bayansa yana tafiya cikin taro, ta taba habar rigarsa.
28Domin ta ce "Idan dai na taba ko da habar rigarsa zan warke." 29Da dai ta taba shi sai zubar jinin ta ta tsaya, ta ji a jikin ta ta warke, daga damuwarta.
30Nan da nan, Yesu ya ji iko ya fita daga gare shi sai ya ce "wanene ya taba rigata?" 31Almajiransa suka ce, "a cikin wannan taron mutane da yawa ka ce wanene ya taba ni?" 32Amma Yesu ya waiga ya ga ko wanene ya taba shi.
33Matar ta san abin da ya faru sai ta zo cikin tsoro da rawar jiki ta durkusa a gaban Yesu ta fada masa gaskiya. 34Sai ya ce da ita, "Diya bangaskiyarki ta warkar da ke, ki tafi lafiya kin sami warkewa daga cutarki".
35Sa'adda ya ke magana da ita sai ga mutane daga gidan shugaban majami'a suka ce "Diyarka ta mutu me ya sa za ka dami malam?"
36Amma sa'adda Yesu ya ji abin da suka ce, sai ya ce da shugaban majami'ar, "kada ka ji tsoro ka ba da gaskiya kawai." 37Bai bari kowa ya kasance tare da shi ba sai Bitrus da Yakubu da Yahaya dan'uwan Yakubu. 38Suka zo gidan shugaban majami'ar ya ga mutane suna bakin ciki, suna kuka sosai.
39Sa'adda ya shiga gidan ya ce da mutane "Me ya sa kuke damuwa da kuka?" Yarinyar ba ta mutu ba barci ta ke yi. 40Sai su kayi masa dariya. Amma ya fitar da su waje su duka. Ya kira baban yarinyar da mamar ta da wadansu da ke tare da shi su ka shiga wurin da yarinyar ta ke.
41Ya kama hannun yarinyar ya ce da ita "Tilatha koum" wato yarinya na ce ki tashi" 42Nan da nan yarinyar ta tashi ta yi tafiya (gama shekarun ta sun kai goma sha biyu). Nan da nan mutanen suka yi mamaki kwarai da gaske. 43Ya ummurce su da gaske kada kowa ya sani. Ya ce da su su ba ta abinci ta ci.

6

1Ya bar su ya zo garinsu, almajiransa su ka biyo shi. 2Sa'adda ranar Asabar tazo ya shiga cikin masujada ya yi koyarwa. Mutane da yawa da su ka ji koyarwarsa su ka yi mamaki, suka ce daga ina ya sami irin wannan koyarwar? Wacce irin hikima ce Allah ya ba shi haka? Wadanne irin ayyukan al'ajibi ya ke yi da hannuwansa? 3Wannan ba kafintan nan ba ne dan Maryamu, dan'uwan Yakubu da Yosi da Yahuza da Saminu? Ba ga 'yan'uwan sa 'yan mata mu na tare da su ba? Ba su ji dadi ba a ransu saboda Yesu.

4Yesu ya ce, "Annabi ba ya rasa daraja sai a gidansa da garinsa da cikin danginsa." 5Bai iya yin wani aikin al'ajibi a wurin ba sai dai mutane kadan marasa lafiya ya dorawa hannu ya warkar da su. 6Rashin bangaskiyarsu ya ba shi mamaki. Sai ya tafi cikin kauyuka na kewaye da su ya yi ta koyarwa.
7Ya kira almajiransa su goma sha biyu, ya aike su biyu-biyu, ya ba su iko a kan aljanu, 8ya dokace su kada su dauki komai tare da su domin wannan tafiya, sai dai sanda kadai. Kada su dauki abinci ko jaka ko kudi a cikin aljihunsu, 9sai dai su sa takalmi kadai, kada su sa taguwa biyu a jikinsu.
10Ya ce da su, idan ku ka shiga wani gida sai ku zauna a gidan har lokacin da za ku tashi. 11Idan ku ka je wani gari aka ki karbar ku, ku karkabe kurar da ke kafufunku ta zama shaida kan mutanen garin.
12Sai suka tafi suka yi ta shela ga mutane cewa su tuba daga zunubansu. 13Sun fitar da aljanu da yawa, suka shafawa mutane da yawa mai suka warkar da su.
14Sarki Hirudus ya ji wannan, gama sunan Yesu ya zama sananne a wurin kowa da kowa. Wadansu suna cewa Yahaya mai yin baftisma ne ya tashi daga matattu shi ya sa ake yin wadannan ayyukan al'ajibi ta wurinsa. 15Wadansu kuma suna cewa, "Iliya," Har yanzu wadansu suna cewa daya "daga cikin annabawa ne na da can."
16Sa'adda Hirudus ya ji wannan sai ya ce, "Yahaya wanda na fillewa kai shine ya tashi." 17Saboda Hirudus ne ya sa aka kama Yahaya aka kulle shi a kurkuku saboda Hirodiya( matar Filibus dan'uwansa), domin ya aure ta.
18Saboda Yahaya ya gaya wa Hirudus cewa bai halarta ya auri matar dan'uwansa ba. 19Sai ita Hirodiya ta yi kudurin ta kashe Yahaya amma bai yiwu ba. 20Domin Hirudus yana jin tsoron Yahaya, domin ya sani shi mai adalci ce, mai tsarki kuma. Domin haka Hirudus bai so wani abu ya faru da Yahaya ba, amma ya kan fusata idan ya ji wa'azin yahaya. Duk da haka da fari ciki yakan saurare shi.
21Amma sai dama ta samu inda Hirodiya za ta iya yin abin da ta ke so ta yi. A lokacin kewayowar ranar haihuwar sa, sai Hirudus ya shirya liyafa domin manyan da ke aiki tare da shi a cikin gwamnatin sa, da shugabannin da ke cikin Galili. 22Diyar Hirodiya ta zo ta yi masu rawa, rawarta kuwa tagamshi Hirudus da bakinsa. Sarki ya ce da yarinyar, "ki tambayi duk abin da ki ke so ni kuwa zan ba ki shi".
23Ya rantse mata da cewa"Ko menene ki ka ce ki na so, ko da rabin mulkina ne" 24Sai ta fita ta je ta tambayi mamarta, "me zan ce ya bani?" Sai ta ce kan Yahaya Mai Yin Baftisma. 25Sai ta dawo da sauri cikin dakin taro wurin sarki ta ce da shi, "Ina so ka ba ni kan Yahaya Mai Yin Baftisma a cikin tire."
26Sarki ya damu kwarai, amma saboda ya yi alkawari ga kuma ofisoshinsa, ba dama ya ce a'a. 27Sai sarki ya aiki wani soja ya ba shi ummurni ya je ya kawo kan Yahaya. Sojan ya je ya fillo kan sa daga cikin kurkuku. 28Ya kawo kan a cikin tire ya ba yarinyar, yarinyar kuma ta kai wa mamarta. 29Da almajiran su ka ji labari, suka zo suka dauki gawarsa suka rufe a cikin kabari.
30Almajiran suka zo wurin Yesu, suka fada masa dukkan abin da suka yi da abin da suka koyar. 31Sai ya ce da su "ku je cikin kebabben wuri domin ku huta kadan," domin mutane suna ta kaiwa da komowa, ba su sami damar hutawa ba balle su ci abinci 32Sai suka tafi kebabben wuri a cikin jirgin ruwa su kadai.
33Amma mutane da yawa sun gansu suna tafiya sun kuma gane su, sai suka fito daga cikin dukan garuruwa da gudu har su ka kai wurin kafin su zo. 34Sa'adda suka zo bakin gaba Yesu ya ga taron mutane da yawa sai ya ji tausayinsu domin sun yi kamar tumakin da ba da mai kiwo. Sai ya cigaba da koya masu abubuwa da yawa.
35Sa'adda yamma ta yi, almajiran sa suka zo suka ce da shi, "wurinnan kebabben wuri ne kuma ga lokaci ya tafi. 36Ka sallami mutanen nan domin su shiga cikin garuruwa da kauyuka da ke kusa domin su sayi abin da zasu ci.
37Amma sai ya ba su amsa ya ce,"Ku ku basu abinci su ci mana". Sai suka ce da shi, "ma iya zuwa mu sawo gurasa ta sule dari biyu mu basu su ci?" 38Sai ya ce dasu, "Dunkulen gurasa guda nawa kuke dasu? Kuje ku gani." Dasuka gano sai suka ce da shi, dunkule biyar ne da kifi guda biyu."
39Sai ya ba da umarni mutanen su dukka su zauna a kan danyar ciyawa. 40Suka zauna kungiya kungiya wadansu su dari wadansu hamsin. 41Sai ya dauki dunkulen gurasa guda biyar da kifi guda biyu, ya ta da kansa sama, yasa albarka, ya kakkarya dunkulen gurasan, ya ba almajiran domin su rabawa taron jama'a duka.
42Dukansu suka ci suka koshi. 43Suka tattara gutsattsarin gurasar suka cika kwanduna guda goma sha biyu da gutsattsarin da kuma gutsattsarin kifin. 44Mutanen da suka ci gurasar sun kai mutum dubu biyar.
45Nan da nan ya ce almajiran sa su hau jirgin ruwa su yi gaba kafin ya zo, su je Baitsaida. Shi kuma ya tsaya domin ya sallami taron mutanen. 46Bayan da suka tafi shi kuma ya hau kan dutse domin ya yi addu'a. 47Har yamma ta yi jirgin ruwan ya na tsakiyar rafi shi kuma yana kan tudu shi kadai.
48Ya gansu suna wahala gama iska ta hana su tafiya. Wajan karfe hudu na asuba sai ya tawo wurin su yana tafiya a kan ruwa, yana so ya wuce gaban su. 49Sa'adda suka gan shi ya na tafiya a kan ruwa suka yi tsammani fatalwa ce, suka yi ihu, 50gama su duka sun gan shi, tsoro ya kama su. Sai nan da nan ya yi magana dasu ya ce, "Ku karfafa ni ne! kada ku ji tsoro!"
51Ya shiga cikin jirgin ruwan tare dasu, sai iska ta dena bugawa. Sai suka yi mamaki kwarai. 52Gama basu gane batun dunkulen ba. Maimakon haka, sai zukatansu suka taurare.
53Sa'adda suka haye su zo kasar Janisarita suka sa wa jirgin sarka. 54Su na fitowa daga cikin jirgin kenan, mutane suka gane cewa Yesu ne. 55Mutane suka ruga cikin yankin su, suka kawo marasa lafiya a bisa shinfidun su zuwa wurinsa, dukan inda suka ji yana zuwa.
56Ko ina ya shiga birni da kauye, ko a cikin kasar sukan kawo marasa lafiya a kasuwanni suna rokonsa su taba ko da habar rigarsa, dukan wadanda suka taba kuwa suka warke.

7

1Farisawa suka taru wurin Yesu tare da wadansu marubuta wadda suka zo daga Urushalima.

2Sun ga cewa wasu daga cikin almajiransa sun ci gurasa da hannuwa marasa tsabta, wato, basu wanke hannu ba, 3(Domin Farisawa da dukan Yahudawa ba su cin abinci sai dole sun wanke hannu da kyau domin suna kiyaye al'adun dattawa. 4Idan Farisawa suka dawo daga kasuwa, wajibi ne su yi wanka kamin su ci abinci. Akwai sauran al'adun da suke kiyayewa, kamar wanke moda, tukwane, da wasu santula na dalma, har da dakin cin abinci.)
5Farisawa da Marubuta suka tambaye Yesu, "Don me almajiran ka basu kiyaye al'adun dattawa, domin suna cin abinci ba tare da sun wanke hannu ba?"
6Amma ya amsa masu cewa, "Ishaya ya yi anabci akan ku masu bautan ganin ido, da ya rubuta cewa 'wadanan mutane suna girmama ni a baka amma zuciyar su tana nesa da ni. 7Sujadar wofi suke mani suna koyar da ka'idodi na mutane a matsayin rukunansu'".
8Kun watsar da dokar Allah sai kuka rungumi al'adun mutane. 9Sai yace masu, kun yi nasara wurin kau da dokokin Allah domin ku kiyaye al'adun ku na mutane. 10Koda shike Musa ya rubuta cewa, "ka girmama Ubanka da Uwarka", kuma, "duk wanda ya zagi Ubansa ko Uwatasa, ya cancanci mutuwa nan take".
11Amma kun ce, 'idan mutum ya ce wa iyayensa, "duk taimakon da ya cacanci ku samu daga guna ya zama kebabbe (wato, 'na mika wa Allah)"'. 12Sabo da haka, kun ba shi izini kada ya yi wa Ubansa ko Uwatasa wani abu. 13Kuna mayar da dokan Allah abin banza, sabili da al'adun ku da kuka mika masu. Wannan, da wasu abubuwa kamar haka kuke yi."
14Ya kara kiran taron jama'ar yace masu, "ku kasa kunne gareni, kuma ku gane. 15Babu wani abu daga wajen mutum da zai iya gurbatar da shi har idan ya shiga cikinsa. Amma, abinda ya fita daga cikinsa shike gurbatar da shi" 16Bari mai kunnen ji, ya ji.
17Da Yesu ya bar taron jama'ar, ya shiga gida, sai almajiransa suka tambaye shi ma'anar wannan misali. 18Sai Yesu yace, 'ashe baku da ganewa? ko baku sani cewa abin da ya shiga cikin mutum daga waje ba zai iya gurbatar da shi ba, 19domin ba zai iya kai wa cikin zuciyarsa ba, sai dai ya shiga cikin sa ya kuma fita a matsayin bayan gari a salga". Da wannan magana, Yesu ya mayar da dukan abinci ya zama da tsabta.
20Ya ce, abinda ke cikin mutum shike gurbatar da shi 21Domin daga cikin mutum, kuma daga cikin zuciyarsa ne, mugun tunani, lalata, sata, kisa, 22zina, kwadayi, mugunta, hai'inci, mugun guri, kishi, zargi, girmankai, wawanci. 23Duk wadannan miyagun abubuwa suna fitowa ne daga cikin mutum, kuma suke gurbatar da shi."
24Ya tashi daga nan ya tafi shiyyar Sur da Sida. Ya shiga wani gida don baya son wani ya sani cewa yana nan, amma bai iya boyuwa ba. 25Amma nan da nan wata mace, wadda diyarta ke da mugun ruhu-wannan mace kuwa ta ji game da Yesu sai ta zo ta durkusa a gabansa. 26Matar yar kasar Girka ce, kuma asalinta daga Fonishiya take. Ta roke shi da ya fitar da mugun ruhun nan daga diyarta.
27Sai ya ce mata, "Bari a ciyar da 'ya'ya tukuna. Domin bai kamata a dauki abincin yaya a ba karnuka ba". 28Sai ta amsa masa cewa, "I, Ubangiji, Karnukan ma sukan ci abincin da ke fadowa daga teburin 'ya'yan."
29Ya ce mata, "domin kin fadi haka, kina iya ki tafi domin aljani ya fita daga diyarki." 30Ta koma gida sai ta iske diyarta na kwance akan gado, aljanin ya fice daga jikinta.
31Ya sake fita daga shiyar Sur, ya biyo ta Sidon, har zuwa tekun Galili a shiyar Dikafolis. 32Sun kawo masa wani kurma, kuma bebe ne shi, suna rokansa ya dora hanuwansa a bisansa.
33Sai ya jawo shi daga taron jama'ar, zuwa gefe, sai ya sa hanunsa a kunuwan beben bayan ya tufa yawunsa, sannan ya taba harshensa. 34Ya dubi sama, ya ja numfashi ya ce masa, "Ifatha", wato, "bude!" 35Nan da nan ya mayar masa da jinsa. abinda ya daure harshensa ya sake shi, sai ya fara magana da kyau.
36Ya umarce su da kada su gaya wa wani. Amma duk da umarnin da yake basu, suna ta shaida shi ko'ina. 37kuma suna ta mamaki cewa, "Yayi kowanne abu da kyau, har ya sa kurame suna jin magana, da kuma bebaye na magana."

8

1A kwanakin nan, akwai wani gagaruman taron mutane, kuma basu da abincin ci. Yesu ya kirawo almajiransa yace masu, 2"Ina tausayin taron mutanen nan domin kwana uku kenan suna nan tare da ni babu abinci. 3Idan na salame su su koma gidajensu ba tare da sun ci abinci ba, za su galabaita a hanya domin gidajensu na da nisa." 4Almajiransa suka amsa masa cewa, "A ina za mu iya samu gurasa a wannan jeji da zai ishi wadannan mutane haka?"

5Ya tambaye su, "gurasa nawa kuke da su?" Sai suka ce, "Bakwai." 6Ya umarci mutanen da su zauna. Ya dauki gurasar bakwai, bayan da ya yi godiya, ya kakarya gurasar, sa'annan ya umarci almajiransa da su raba wa mutanen. Su kuwa suka raba masu.
7Suna kuma da kananan kifaye kadan. Bayan da ya yi godiya akan su, ya umurci almajiran su rabawa mutanen. 8Sun ci sun koshi. Suka tattara ragowar, har sun cika kwanduna bakwai. 9Akwai maza kimanin dubu hudu a wurin. Yesu ya sallame su. 10Nan take, ya shiga jirgin ruwa da almajiransa zuwa shiyyar Dalmanuta.
11Sai Farisawa suka zo suka fara gardama da shi. Suna nema ya nuna masu alama daga sama, domin su gwada shi. 12Ya ja numfashi a ruhunsa yana cewa, "Don me wannan tsarar tana neman alama. Hakika ina gaya maku, babu wata alama da za a ba wannan tsarar." 13Sai ya bar su ya sake shiga jirgin zuwa hayin tafkin.
14A lokacin nan, almajiransa sun manta su dauki gurasa. Domin gurasa daya ce tak a garesu cikin jirgin ruwan. 15Ya gargade su, "ku yi hattara da yisti na Farisawa da Yisti na Hirudus."
16Almajiran suka fara tattaunawa a tsakaninsu, "Saboda ba mu da gurasa ne." 17Yesu yana sane da wannan, sa'annan ya ce masu, "Don me kuke tattaunawa akan rashin gurasa? Har yanzu baku gane ba? Har yanzu ba ku da sane? Ko zuciyar ku ta duhunta ne?"
18Kuna da idanu, ba ku gani? Kuna da kunnuwa, ba ku ji? Ba ku tuna ba? 19Da na kakkarya gurasar a cikin mutane dubu biyar, kwanduna nawa kuka samu ragowa? Suka ce masa, "Goma sha biyu."
20Kuma da na kakarya gurasa bakwai a cikin mutane dubu hudu, kwanduna nawa kuka dauka cike da ragowar? Suka ce masa, "bakwai." 21Ya ce masu, "har yanzu baku gane ba?"
22Sun zo Baitsaida. Mutanen wurin suka kawo masa wani makaho, sai suka roke shi ya taba shi. 23Yesu ya rike hanun makahon, ya jagorance shi zuwa bayan kauyen. Da ya tofa yawunsa a idon mutumin, kuma ya dora hanunsa akan mutumin, sai ya tambaye shi "kana ganin wani abu kuwa?"
24Ya daga ido sai ya ce, "ina ganin mutane na tafiya kamar itatuwa." 25Ya sake dora masa hannu a idanuwansa, mutumin ya bude idanuwansa, sai ya fara ganin gari da kyau. 26Yesu ya sallame shi zuwa gidansa nan take, ya ce masa, "kada ka shiga cikin garin"
27Yesu da almajiransa sun shiga kauyukan kaisariya ta Filibi. Da suke kan hanya, sai ya tambaye su, "Shin wanene mutane ke ce da ni?" 28Suka amsa masa suka ce, Yahaya mai Baftisma. Wasu suka ce, "Iliya". wadansu kuma, 'Daya daga cikin anabawa".
29Ya tambaye su, "Amma me ku ke ce da ni?" Bitrus ya ce, "Kai ne Almasihu." 30Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa game da shi.
31Sai ya fara koya masu cewa, dole ne Dan Mutum ya sha wahala, dattawa da marubuta da manyan Firistoci zasu ki shi, a kuma kashe shi. Bayan kwana uku, zai tashi daga matattu. 32Ya fadi wannan afili. Sai Birus ya ja shi gefe ya fara tsauta masa.
33Amma Yesu ya juya ya dubi almajiransa sa'annan ya tsautawa Bitrus yana cewa, "Ka koma bayana Shaidan, domin kana kula da abubuwan mutane ne kawai, ba na Allah ba." 34Sai ya kira taron jama'ar da almajiransa a wuri daya, ya ce masu, "Duk wanda yake so ya bini, dole ne ya musunci kansa, ya dauki giciyensa ya biyo ni.
35Domin duk wanda yake so ya ceci ransa zai rasa shi, amma duk wadda ya rasa ransa domina da kuma bishara zai cece shi. 36Me zai amfani mutum idan ya sami dukan duniya sannan ya rasa ransa. 37Me mutum zai bayar amaimakon ransa?
38Duk wanda ke jin kunyata ko maganata a wannan mazinaciyar tsara mai zunubi, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa a lokacin da ya dawo cikin daukakar Ubansa da Malaiku masu tsarki."

9

1Sai ya ce masu, "Hakika, ina gaya maku, akwai wasun ku anan da ba za su mutu ba, sai sun ga mulkin Allah ya bayyana da iko." 2Bayan kwana shida Yesu ya dauki Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, su kadai. Sai kamaninsa ya sake a gabansu.3Sai tufafinsa ya zama fari fat, yadda ba mai rinin da zai iya rininsa haka a duniya.

4Sai Iliya da Musa suka bayyana gare su, suna magana da Yesu. 5Sai Bitrus ya amsa ya ce, malam, bari mu da muke anan mu kafa bukka uku, daya ta ka, daya ta Musa, da ta Iliya, 6Ya rasa abin da zai fada ne, don sun tsorota kwarai.)
7Sai ga wani gajimare ya zo ya rufe su, aka kuma ji wata murya daga gajimaren, "ta ce Wannan shine kaunataccen Dana, Ku saurare shi. 8Nan take da suka duba, ba su ga kowa ba, sai Yesu shi kadai.
9Suna cikin gangarowa daga dutsen, sai ya kwabe su kada su gaya wa kowa abin da suka gani, sai bayan da Dan Mutum ya tashi daga mattatu. 10Sai suka bar zancen a tsakaninsu, amma suka tamabayi junansu "mene ne tashin matattu" ke nufi.
11Suka tambaye shi yaya malaman attaura suka ce Iliya zai fara zuwa?" 12Ya ce masu, laile ne Iliya ya fara zuwa ya raya dukan abubuwan. Don me a ka rubuta cewa Dan Mutum, zai sha wuya iri iri a kuma ki shi? 13Amma ina gaya muku Iliya ya riga, ya zo, amma sun yi masa abin da suke so su yi kamar yadda littatafai suka yi magana a kansa."
14Sa'adda suka dawo wurin sauran almajiran, suka ga taron jama'a masu yawa suna ta muhawara tare da manyan malaman attaura. 15Da ganin sa, sai dukan taron yayi mamaki kwarai da gaske, suka dungumo wurinsa a guje, suna gaishe shi. 16Ya tambayi almajiransa, "Wacce muhawara ce kuke yi da su?"
17Daya daga cikin taron ya amsa masa"malam, ga shi na kawo maka dana don yana da beben aljani. 18Duk lokacin da ya tasar masa yakan buga shi har kasa, na kuma yi wa almajiranka magana su fitar sun kasa. 19Ya amsa masu ya ce ya ku mutanen zamaninnan marasa bangaskiya, har yaushe zan kasance tare da ku ina jimrewa? ku dai kawo mini shi.
20Sai suka kawo masa yaron. Da ruhun ya ga Yesu, nan da nan ya buge yaron jikinsa na rawa. Sai yaron ya fadi yana ta birgima, bakinsa yana kumfa. 21Yesu ya tambayi mahaifin yaron, Tun yaushe wannan abu ya same shi? Mahaifin yaron ya ce tun yana karami. 22Ya kuwa sha jefa shi a ruwa da wuta, don ya halakar da shi. Idan zaka iya yin wani abu, ka ji tausayinmu ka taimakemu.
23Yesu ya ce masa, "In zan iya? Ai dukan abu mai yiwuwa ne, ga duk wanda ya gaskata. 24Nan da nan mahaifin yaron ya daga murya ya ce, Na ba da gaskiya. A kore mini rashin bangaskiyata. 25Da Yesu ya ga taron na dungumowa a guje, sai ya tsawata wa bakin aljanin ya ce masa, "kai, beben aljani na umarce ka, ka fita daga wannan yaron kar ka sake shigar sa.
26Sai wannan aljanin ya daga murya ya fita ya rabu da wannan yaron. Sai yaro ya zama kamar mattacce, sai sauran mutanen suka ce, "Ai, yaron ya mutu. 27Yesu ya kama hannunsa, ya daga shi, sai yaron ya mike tsaye.
28Da Yesu ya shiga gida, sai almajiransa suka tambaye shi a kadaice, me ya sa muka kasa fitar da shi?" 29Ya ce masu, "Ai, irin wannan ba ya fita sai da addu'a."
30Sai suka ratsa cikin Galili, amma ba ya son kowa ya san inda suke. 31Da yake koyar da almajiransa, ya ce masu lokaci na zuwa da za'a ba da Dan mutum a hannun mutane, za su kuwa kashe shi, sa'adda aka kashe shi kuma, bayan kwana uku zai tashi. 32Amma fa ba su fahimci maganar ba, suna kuma jin tsoron tambayarsa.
33Sai suka zo kafarnahum. A lokacin da ya ke cikin gida, ya tambayi Al'majiransa, Menene ku ke magana a kansa a hanya? 34Amma suka yi shiru. don suna gardama da junansu akan hanya, a kan wane ne mafi girma. 35Sai ya zauna, ya kira al'majiransa goma sha biyu, yace masu duk wanda ya ke so ya zama na fari, dole ya kankantar da kansa, sa'annan ya bautawa sauran duka.
36Sai ya dauko karamin yaro a hannunsa ya sa shi a tsakiyarsu. Ya rumgome shi a kafadarsa ya ce masu. 37Dukan wanda ya karbi dan karamin yaron nan a cikin sunana ni ya karba, kuma dukan wanda ya karbi wani, ni ya karba, bai kuma karbeni ni kadai ba, duk da wanda ya aiko ni."
38Sai Yahaya ya ce masa, Malam mun ga wani yana fitar da aljanu da sunanka mun yi kokari mu hana shi domin ba ya tare da mu. 39Sai Yesu ya ce masu ku kyale shi domin babu wanda zai yi irin wannan babban aikin, sa'annan ya fadi wasu maganganu mara sa kyau a kanmu.
40Duk wanda ba ya gaba da mu, na mu ne. 41Duk wanda ya ba ku ruwa ku sha domin kuna na Almasihu, gaskiya nake fada maku ba za ya rasa ladansa ba.
42Amma duk wanda ya sa kananan nan tuntube, ya fi kyau a rataya masa dutsen nika a jefa shi a cikin teku. 43Idan har hannun ka zai sa ka yi tuntube, zai fi kyau ka yanke shi. Domin zai fi kyau ka shiga aljanna da hannu daya da ka shiga jahannama da hannu biyu. 44(Inda tsutsotsi basu mutuwa, wutar kuma bata mutuwa).
45Idan kafarka za ta sa ka yi tuntube, ka yanke ta ka yar. Zai fi kyau ka shiga aljanna da kafa daya da ka shiga jahannama da kafa biyu. 46(Inda tsutsotsi basu mutuwa, wutar kuma bata mutuwa).
47Idan idonka zai sa ka yi tuntube, ka kwakule shi ka yar, domin gwamma ka shiga mulkin Allah da ido daya, da a jefa ka cikin wuta da idanu biyu. 48Inda tsutsotsi basu mutuwa, wutar kuma bata mutuwa.
49Domin da wuta za a tsarkake kowa. 50Gishiri yana da kyau, amma idan ya rasa zakinsa, ta ya ya za ka sa shi yayi zaki kuma? Ku kasance da zaki, kuma ku yi zaman lafiya da kowa.

10

1Yesu ya bar wannan wurin, ya tafi yankin Yahudiya, wajen hayin kogin Urdun. Sai jama'a suka je wurinsa. Ya ci gaba da koya masu, kamar yadda ya zama al'adarsa. 2Sai Farisawa su ka zo wurinsa, su ka ce, "dai dai ne mutum ya saki matarsa?" Wannan tambaya sun yi ta ne domin su gwada shi. 3Ya amsa ya ce, menene Musa ya umarce ku? 4Suka ce, "Musa ya yarda mutum ya rubuta takardar saki ga matarsa, ya sallameta ta fita."

5"Domin taurin zuciyarku ne ya rubuta maku wannan dokar," Yesu ya ce masu. 6Amman tun daga farkon halitta, 'Allah ya halicci namiji da ta mata.'
7Domin wannan dalilin ne mutum zai rabu mahaifinsa da mahaifiyarsa ya mannewa matarsa. 8Su biyu kuwa sun zama jiki daya, ba biyu ba, 9Saboda haka abinda Allah ya hada kada mutum ya raba."
10Lokacin da suke cikin gida, sai almajiransa suka sake tambayarsa akan wannan magana. 11Ya ce da su. Dukan wanda ya saki matarsa ya kuma auro wata matar yayi zina da ita kenan. 12Haka nan duk matar da ta saki mijinta ta auri wani ta yi zina da shi kenan."
13Mutane suka kawo masa 'ya'yansu kanana don ya taba su, sai almajiransa suka kwabe su. 14Da Yesu ya gani, ya ji haushi, ya ce masu. Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su domin mulkin Allah na irinsu ne.
15Gaskiya na ke fada maku duk mutumin da bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, babu shakka ba zai shiga mulkin Allah ba. 16Sai ya rungume su ya sa masu albarka.
17Lokacin da ya fara tafiya, sai wani mutum ya rugo wurinsa, ya durkusa a gabansa. Ya tambaye shi, yace ya "Malam managarci, me zan yi domin in sami rai na har abada?" 18Amma Yesu ya ce masa. Don me ka ke kira na managarci? Babu wani managarci sai dai Allah kadai. 19Kasan dokokin. Kada ka yi kisan kai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar zur, kada ka yi zamba, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka."
20Sai mutumin ya ce masa Malam ai na kiyayye duk wadannan abubuwa tun ina yaro. 21Yesu ya dube shi duban kauna ya ce masa. Abu daya ka rasa. Shi ne ka je ka sayar da duk mallakarka ka ba mabukata, za ka sami wadata a sama. Sa'annan ka zo ka bi ni. 22Da ya ji haka sai ransa ya baci, ya tafi yana bakin ciki, don shi mai arziki ne kwarai.
23Yesu ya dubi almajiransa ya ce. "Yana da wuya masu arziki su shiga mulkin Allah!" 24Almajiransa suka yi mamakin maganarsa. Sai Yesu ce masu, ya ku ya'ya'na yana da wuya kamar me a shiga mulkin Allah. 25Zai zama da sauki ga rakumi yabi ta kafar allura da mai arziki ya shiga mulkin Allah.
26Sai suka cika da mamaki sosai, su kace wa juna, "to idan haka ne wanene zai iya tsira kenan?" 27Yesu ya dube su ya ce masu. Ga mutane a bu ne mai wuyar gaske, amma a wurin Allah komai yiwuwa ne. 28Bitrus ya ce masa, "to gashi mu mun bar kome, mun bika".
29Yesu ya ce. Gaskiya na ke fada maku, babu wanda zai bar gidansa, da yan'uwansa maza da mata, da mahaifiya ko mahaifi, ko 'ya'ya ko gona, saboda da ni da kuma bishara, 30sa'annan ya rasa samun nikinsu dari a zamanin yanzu, na gidaje, da yan'uwa mata da maza' da iyaye mata da 'ya'ya da gonaki, game da tsanani, a duniya mai zuw kuma ya sami rai madawwami. 31Da yawa wadanda suke na farko za su koma na karshe, na karshe kuma za su zama na farko.
32Suna tafiya Urushalima, Yesu kuwa na gabansu. Almajiransa sun yi mamaki, mutane da ke biye da su kuwa sun tsorata. Yesu kuwa ya sake kebe sha biyun nan, ya fara fada masu abin da zai same shi. 33"Kun ga, za mu Urushalima za a bada Dan mutum ga manyan Firistoci da malan Attaura, za su kuma yi masa hukuncin kisa su kuma bada shi ga al'ummai. 34Za su yi masa ba a, su tofa masa yau, su yi masa bulala, su kashe shi, bayan kwana uku kuwa zai tashi."
35Yakubu da Yahaya, 'ya'yan Zabadi, suka zo wurin sa, suka ce, "Malam muna so kayi mana duk abin da mu ka roke ka" 36Ya ce masu. "Me ku ke so in yi maku?" 37Suka ce, "ka yardar mana, a ranar daukakarka, mu zauna daya a damanka, daya kuma a hagunka."
38Yesu ya ce masu. "Ba ku san abinda ku ke roka ba. Kwa iya sha daga kokon da zan sha? Ko kuma za a yi maku baftismar da za a yi mani?" 39Suka fada masa, "Zamu iya." Yesu ya ce masu, "kokon da zan sha, da shi zaku sha, baftismar da za ayi mani kuma da ita za a yi maku." 40Amma zama a damata, ko a haguna, ba na wa ba ne da zan bayar, ai na wadanda a ka shiryawa ne."
41Da sauran almajiran nan goma suka ji, suka fara jin haushin Yakubu da Yahaya. 42Yesu kuma ya kira su wurinsa ya ce masu, "kun sani wadanda aka san su da mulkin al'ummai sukan nuna masu iko, hakimansu kuma sukan gasa masu iko.
43Amma ba haka zai kasance a tsakaninku ba. Duk wanda ya ke son zama babba a cikinku, lalle ne ya zama baranku. 44Duk wanda ya ke so ya shugabance ku lalle ne ya zama bawan kowa. 45Saboda haka ne Dan mutum ya zo ba domin a bauta masa ba, sai dai domin shi yayi bautar, ya kuma ba da ransa fansa saboda da mutane da yawa."
46Sa'adda suka iso Yariko, yana fita daga Yariko kenan, shi da almajiransa, da wani babban taro, sai ga wani makaho mai bara, mai suna Bartimawas dan Timawas yana zaune a gefen hanya. 47Da ya ji Yesu Banazare ne, ya fara daga murya yana cewa, "Ya Yesu, Dan Dauda, kaji tausayina" 48Mutane da yawa suka kwabe shi, cewa yayi shiru. Sai ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, Ya Dan Dauda ka yi mani jinkai, ka ji tausayina!"
49Yesu ya tsaya ya ce, ku kirawo shi. Su kuwa suka kirawo makahon suka ce masa. "Albishrinka, ta so! Yana kiranka." 50Makahon ya yar da mayafinsa, ya zaburo wurin Yesu.
51Yesu ya tambaye shi, ya ce, "me ka ke so in yi maka?" Makahon ya ce, "Malam in sami gani." 52Yesu ya ce masa. "Yi tafiyarka, bangaskiyarka ta warkar da kai." Nan take idanunsa suka bude, ya bi Yesu, suka tafi tare.

11

1Da suka kusa Urushalima, kusa da Betafaji, da Betanya, wajen dutsen zaitun, sai Yesu ya aiki almajiransa biyu 2ya ce masu, "ku shiga kauyen can kusa da mu. Da zarar kun shiga za ku ga aholaki a daure, wanda ba a taba hawa ba. Ku kwance shi, ku kawo mani. 3In wani ya ce maku, "Don me kuke haka? ku ce, 'Ubangiji ne yake bukatarsa, zai kuma komo da shi nan da nan."'

4Sai suka tafi, suka tadda aholakin a daure a kofar gida a bakin hanya, suka kwance shi. 5sai wadanda suke tsaye a gun suka ce masu, "Don me kuke kwance aholakin nan? 6Suka fada masu abinda Yesu yace, sai suka kyale su suka tafi.
7Almajiran nan biyu suka kawo wa Yesu aholakin, suka shimfida mayafansu a kai, sai ya hau. 8Sai mutane da yawa suka shimfida mayafansu a hanya, wadansu kuma suka baza ganyen da suka yanko daga filayen. 9Wadanda suke gaba da shi da wadanda ke bin bayansa suka yi sowa suna cewa, "Hosanna! Albarka ta tabbata ga mai zuwa cikin sunan Ubangiji. 10Albarka ta tabbata ga mulkin nan mai zuwa na Ubanmu Dawuda! Dukaka a cikin sama!"
11San nan Yesu ya shiga Urushalima, ya shiga Haikalin. Sai ya dudduba komai, da magariba ta yi, ya fita ya tafi Betanya tare da goma sha biyu nan. 12Kashe gari, suka tashi daga Betanya, sai ya ji yunwa.
13Da ya hango itacen baure mai ganye daga nesa sai ya je ya ga ko za sami 'ya'ya. Da ya iso wurinsa bai ga komai ba sai ganye, don ba lokacin 'ya'yan baure ba ne.14Sai ya ce wa bauren, "Kada kowa ya kara cin "ya'yanka har abada!" Almajiransa kuwa sun ji maganar.
15Suka iso Urushalima, da shigar su, ya kori masu saye da sayarwa, ya watsar da taburan 'yan canjin kudi, da kujerun masu sayar da tantabaru. 16Ya hana kowa ya dauki wani abu da za a i ya sayarwa a cikin haikalin.
17Sai ya koyar da su cewa, "Ashe ba rubuce yake ba, "Za a kira gidana gidan addu'a na dukan al'ummai? Amma ku kun mayar da shi kogon yan fashi". 18Da mayan Faristoci da marubutan attaura suka ji maganar da ya yi, sai suka nami hanyar da za su kashe shi. Amma suka ji tsoronsa domin dukkan taron na mamakin koyarwarsa. 19Kowace yamma kuma, sukan fita gari.
20Da safe suna wucewa, sai suka ga bauren nan ya bushe. 21Bitrus kuwa ya tuna ya ce "Malam, dubi! Baurenan da ka la'anta ya bushe."
22Yesu ya amsa masu ya ce, "ku gaskata da Allah." 23Hakika, ina gaya maku, duk wanda ya ce wa dutsen nan tashi ka fada cikin tekun', bai kuwa yi shakka a zuciyarsa ba, amma ya gaskata haka kuwa zai faru, haka kuwa Allah zai yi.
24Saboda haka ina dai gaya maku, komai kuka yi addu'a kuka roka, ku gaskata cewa samamme ne, zai kuma zama naku. 25Duk sa'add da kuke addu'a ku gafarta wa wadanda suka yi maku laifi, domin Ubanku shima zai gafarta maku naku laifi." 26(Amma in baku gafartawa mutane laifofinsu ba, Ubanku ma da ke sama ba zai gafarta maku ba.)
27Da suka sake dawowa Urushalima. Yasu na tafiya cikin haikali, sai manyan firistoci, da marubuta, da dattawa suka zo wurinsa, 28suka ce masa, "Da wanne iko kake yin wadanan abubuwa? Ko kuwa wa ya ba ka ikon yinsu?"
29Sai Yesu ya ce masu, "Zan yi maku wata tambaya. ku ba ni amsa, ni kuwa zan gaya maku ko da wanne iko ne nake yin wadannan abubuwan. 30Baftismar da Yahaya yayi, daga sama take ko kuwa daga mutum take? ku bani amsa".
31Sai suka yi mahuwara da juna, suka ce, "in kuwa muka ce, 'daga sama take,' za ya ce, "To, don me ba ku gaskata shi ba? 32In kuwa muka ce, "amma in muka ce ta mutum ce zasu jejjefemu domi suna jin tsoron jama'a, don duk kowa ya tabbata, cewa Yahaya annabi ne. 33Sai suka amsa wa Yesu suka ce, "Ba mu sani ba" Yesu ya ce masu, "Haka ni kuma ba zan fada muku ko da wanne iko nake yin abubuwan nan ba."

12

1Sai Yesu ya fara koyar da su da misalai. "Wani mutum ne ya yi gonar inabi ya shingen ta, ya haka ramin matse inabin, ya kuwa gina hasumayar tsaro. Ya ba wandansu manoma jinginar gonar, sa'an nan ya tafi wata kasa mai nisa. 2Da lokaci ya yi, sai ya aika masu wani bawansa domin ya karbi wadansu daga cikin amfanin gonar. 3Amma manoman suka kama shi, suka yin masa duka, suka kore shi hannu banza.

4Ya sake aikar wani bawan. Shi kuma suka raunata shi aka, suka wulakanta shi. 5Ya sake aiken wani. Shi kam, suka kashe shi. Haka fa aka yi ta yi da wadansu da yawa, sun dodoki wadansu, suka kuma kashe wadansu.
6Yanzu dai yana da sauran daya tak, shine kaunatacen dansa. Daga karshe ya aike shi wurinsu, yana cewa, ai za su bashi girma. 7Amma manoman nan suka ce wa juna, "ai, wannan shine magajinsa, 'ku zo mu kashe shi, gadon ya zama namu."
8Sai suka kamo shi, suka kashe shi, suka jefar da shi bayan shinge. 9To, me mai gonar inabin zai yi? Sai ya zo ya hallaka manoman nan, ya ba wadansu gonar.
10Ashe, ba ku karanta wannan nassi ba? cewa, ' Dutsen da magina suka ki, shi ne ya zama mafi mahmimanci. 11Wannan daga Ubangiji ne, kuma ya yi dai dai a idanunmu."' 12Sai suka nemi su kama shi, don sun lura a kansu ne ya yi masalin, amma suka ji tsoron jama'a. Don haka suka kyele shi, suka tafi.
13Suka aika masa da wadansu farisiyawa da Heridiyawa, don su sa masa tarko da kalamai cikin maganarsa. 14Da suka zo, suka ce masa, "Malam, gaskiya kana koyar da maganar Allah sosai, ba ka nuna bambanci tsakani mutane, sai koyar da tafarkin Allah kake yi sosai. "Shin, mu biya haraji ga Kaisar, ko a a?" 15AmmaYesu ya gane munafuncinsu, ya ce masu, "Don me kuke gwada ni? ku kawo mani dinarin in gani."
16Suka kawowa Yesu daya. Ya ce masu, "Kamar waye da kuma rubutun wanene? suka ce masa, "Na Kaisar ne." 17Yesu ya ce, "to, ku ba Kaisar abinda yake na Kaisar, ku kuma ba Allah abin da yake na Allah. Sai suka yi mamakinsa kwarai.
18Sai Sadukiyawa suka zo wurinsa, su dake cewa babu tashin matattu. Suka tambaya shi suka ce, 19"Malam, Musa dai ya rubuta mana, cewa idan dan'uwan mutum ya mutu, ya bar matarsa ba da, lallai ne dan'uwan mutumin ya auri matar, ya haifa wa dan'uwansa 'ya'ya.'
20To an yi wadansu 'yan'uwa maza guda bakwai, na farko ya yi aure, ya mutu bai bar 'ya'ya ba. 21Na biyu kuma ya aure ta, shi ma ya mutu, ba 'ya'ya. Na ukun ma haka. 22Haka dai duk bakwai din, ba wanda ya bar 'ya'ya. A karshe kuma ita matar ta mutu. 23To, a tashin matattu, matar wa za ta zama a cikinsu? Don duk bakwai din nan sun aure ta".
24Sai Yesu ya ce, "Ba saboda wannan dalili ne kuka yi kuskure ba, wato don ba ku san littafin ba, kuma ba ku san ikon Allah ba? 25Domin in an tashin daga matattu, ba a aure, ba a auraswa, amma sun zama kamar malaiku a sama.
26Amma game da mattattun da suka tashi, ashe, ba ku taba karantawa a littafin Musa ba, yadda Allah ya ce masa? "Ni ne Allah na Ibrahim, da Ishaku, da kuma Yakubu'? 27Ai, shi ba Allahn mattatu bane, amma na rayyayu ne. Hakika kun yi kuskure ".
28Sai wani malamin attuara ya zo ya ji suna muhawara da juna. Da dai ya ga Yesu yana ba su kyakkyawar amsa, sai ya tambaye shi, "Wanne Umarni ne mafi girma dukka?" 29Yesu ya amsa yace, "mafi girma shine, 'ku saurara ya Isra'ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji daya ne. 30Sai ka kaunaci Ubangiji Allah da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka da dukkan tunaninka, da dukkan karfinka. 31ta biyu itace, 'ka kaunaci makwabcinka kamar kanka, Ba wata doka da ta fi wadannan."
32Sai malamin attaura ya ce masa, "Hakika gaskiyarka malam, Allah daya ne, ba kuma wani sai shi. 33A kaunace shi kuma da dukkan zuciya, da dukkan hankali, da dukkan karfi, a kuma kaunaci makwabci kamar kanka, ai ya fi dukkan hadayu na konawa." 34Da Yesu ya ga ya yi masa magana da hikima, sai ya ce masa, "Ba ka nesa da mulkin Allah." Bayan wannan kuma ba wanda ya sake tambayarsa wani abu.
35Yesu ya amsa a lokacin da yake koyarwa a Haikali, ya ce "Yaya malaman attaura suke ce wa Kristi dan Dauda ne? 36Domin Dauda kansa, ta ikon Ruhu Mai Tsarki ya ce, "Ubangiji ya ce wa Ubangijina, zauna a hannun damana, har sai na kaskantar da makiyanka'. 37Dauda da kansa ya kira shi 'Ubangiji; To, ta yaya ya Almasihu zai zama Dan Dauda?" Babban taron jama'ar suka saurare shi da murna.
38A koyarwa sa Yasu ya ce, "ku yi hankali da malaman attaura, masu son yawo da manyan riguna, suna so a gaishesu a kasuwa, 39da kuma son wuraren zama masu daraja a haikali, da wurin bukukuwa. 40Sun kuma kwace gidajen gwauraye, da yin doguwar addu'a, don mutane su gani. Wadanan mutanen zasu sami hukunci mai tsanani."
41Sai ya zauna a gaban akwatin baiko a Haikalin, yana duban yadda jama'a suke zuba kudi a ciki. 42Wadansu masu arziki da yawa suna zuba kudi masu tsoka. Sai gwauruwa mara abin hanu ta saka anini biyu a ciki akwatin baikon.
43Ya kira almajiransa, ya ce masu, "Hakika, ina gaya maku, abinda gwauruwa nan ta saka a akwatin baikon nan ya fi na sauran dukka. 44Su duk sun bayar daga yalwa tasu ne, ita kuwa daga cikin rashinta ta bada duk abinda take da shi."

13

1da Yesu ke fita daga Haikalin, sai daya daga cikin almajirnsa ya ce masa "malam, dubi kyawawan duwatsunnan da kyawawan gine-ginnenan!" 2Ya ce masa, ka ga wadannan kyawawan gine- ginen? babu wani dutsen da za a bar shi akan dan'uwansa, da ba za a rushe shi ba."

3Yana zaune a kan dutsen zaitun wanda yake kusa da Haikali, sai Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, da Andarawus suka tambaye shi a asirce, suka ce. 4Gaya mana yaushe za a yi wadannan abubuwa? mecece zata zama alamar faruwar wadanna abubuwa da zasu faru?"
5Yesu ya ce masu, "ku kula, kada kowa ya rudeku. 6Da yawa za su zo da sunana, suna cewa nine shi, har su bad da mutane da yawa.
7In kuka ji labarin yake- yake, da jita-jitarsu kada ku damu, wannan zai faru, amma karshen duniya bai gabato ba. 8Al'umma za ta tasarwa al'umma, mulki ya tasarwa mulki. Za a yi girgizar kasa awurare dabam-dabam, da kuma yunwa, amma fa dukkan wadanna abubuwan mafarin azaba ne.
9Amma, ku zauna a fadake. Don za su kai ku gaban majalisa. za a yi maku duka a cikin majami'u. Su kuma kai ku gaban masu mulki da sarakuna, saboda sunana, domin ku ba da shaida a gare su. 10Amma lallai sai an fara yi wa dukkan al, ummai bishara.
11Sa'ad da suka kai ku gaban shari'a suka mika ku, kada ku damu a wannan lokacin, za a baku abin da zaku fada, Amma duk abin da aka yi muku a wannn lokacin, shi za ku fada, domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhu mai tsarki ne. 12Dan'uwa zai bada dan'uwarsa akashe shi, uba kuwa dansa. Yara kuma zasu tayar wa iyayensu har su sa akashe su. 13Za a ki ku saboda sunana, amma duk wanda ya jumre har karshe zai cetu.
14Sa'adda kuka ga an kafa mummunan aikin sabo mai ban kyama a wurin da bai kamata ba (bari mai karatu ya fahimta), to, bari wadanda suke kasar Yahudiya, su gudu zuwa dutse. 15Wanda yake tudu kuma kada ya sauko ya shiga gida garin daukar wani abu. 16Wanda yake gona kuma kada ya koma garin daukar mayafinsa.
17Amma, kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokacin. 18Ku yi addu, a kada abin ya faru da damina. 19A lokacin za ayi wata matsanaciyar wahala, wadda bata taba faruwa ba, tun farkon halittar da Allah ya yi har zuwa yau, ba kuwa za a taba yi ba har abada. 20In da ba ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba Dan adam din zai tsira. Amma saboda zabbabunan da ya zaba, ya rage kwanakin.
21To, in wani ya ce maku, kun ga Almasihu nan!' ko, 'kun gan shi can, kada ku gaskata. 22Gama almasihan karya, da annabawan karya zasu bayyana kuma, zasu yi abubuwan al'ajibai masu ban mamaki. 23Amma ku zauna a fadake, Na dai fada maku wadannan abubuwan kafin lokacin.
24Amma, bayan matsanaciyar wahalannan, rana zata duhunta, wata kuma ba zai bada haske ba. 25Taurari za su fado daga sararin sama, za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama. 26Sa' annan zasu ga Dan mutum na zuwa a cikin gajimare, da iko mai girma da daukaka. 27Zai aiko da mala'ikunsa su tattaro zabbabunsa daga kusuwoyi hudu na duniya(watau Gabas da Yamma, kudu da Arewa) har zuwa karshen sama.
28"Ku yi koyi da itacen baure. Da zarar rassansa sun fara taushi yana kuma fitar da toho, kun san damina ta yi kusa ke nan. 29Sa'adda kuka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku dai sani ya kusato, a bakin kofa ma ya ke.
30Hakika ina gaya maku, zamanin nan ba zai shude ba sai dukan abubuwan nan sun faru. 31Sararin sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba. 32Amma wannan rana ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai dai Uban kadai.
33Ku kula, ku zauna a fadake, kuna addu'a don baku san ranar da lokacin zai yi ba. 34Kamar yadda mutum mai tafiya, in ya bar gida ya wakilta bayinsa kan gidansa, kowanne da aikinsa, ya kuma umarci mai gadi ya zauna a fadake.
35To, ku zauna a fadake don ba ku san lokacin da maigidan zai zo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko da carar zakara ne, ko da safe ne. 36Kada ya zo ba zato, ya samu kuna barci. 37Abinda na gaya maku, ina gaya wa kowa, shine ku zauna a fadake!"

14

1Idin Ketarewa da bukin gurasa mara yisti sauran kwana biyu kenan, sai shugabanin firistoci da malaman attaura suka nemi yadda zasu kama Yesu a asirce domin su kashe shi. 2Suna cewa amma "Ba a lokacin idin ba, domin kada su haddasa hargitsi a tsakanin mutane".

3Yesu yana Betanya a gidan Saminu kuturu, yana shirin liyafa kenan sai ga wata mace dauke da kwalbar turare mai tamanin kwarai, ta shafa masa a kansa. 4wasu dake tare da Yesu suka husata, suna kwalbarta da cewa 5"Ai wannan turare ne mai tsada, ina laifin a sayar a raba wa talakawa kudin? ina dalilin wannan almubazaranci?
6Sai Yesu yace masu "Ku kyaleta, don me kuke tsauta mata, 7ai Idan kuna da niyyar taimakon talakawa ko matalauta, suna nan tare da ku ko a yaushe amma ni bazan kasance da ku kullum ba. 8Macen nan tayi aiki nagari domin shirya jikina ga jana'iza. 9hakika, Ina gaya maku, duk inda za'a yi bishara a duniya baza a mance da matan nan da hidimar da ta tayi mini ba."
10Da jin haka sai Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin manzannin ya ruga zuwa wurin baban firist domin ya bashe shi a garesu, 11Da mayan firistoci suka ji haka suka yi murna matuka tare da alkawarin kudi ga Yahuza, shi kuwa sai ya fara neman zarafin da zai mika Yesu a gare su.
12A ranar farko ta bukin gurasa marar yisti da kuma hadayar ragon Idin ketarewa, almajiransa suka ce masa "Ina zamu shirya liyafar domin idin ketarewa? 13Ya aiki biyu daga cikin almajiransa da cewa "Ku shiga cikin birnin, zaku tarar da wani mutum dauke da tullun ruwa. 14Duk gidan da ya shiga ku bishi, sai ku cewa mai gidan, malam yace "ina bukatar masauki domin hidimar idin ketarewa tare da almajiraina?"'
15Zai kuwa nuna maku babban bene gyararre. Sai ku yi mana shiri a can." 16Da shigar almajiran cikin birnin, sai kome ya kasance yadda ya fada, su kuwa suka yi shirye shiryen idin ketarewar.
17Da maraice ta yi, sai ya tare da sha biyun. 18Yayin da suke zazzaune a teburin suna cin abincin, sai Yesu ya ce "Hakika ina gaya maku wani da ke ci tare da ni a nan zai bashe ni". 19Sai suka damu suka tambaye shi daya bayan daya suna cewa "Hakika bani bane ko?"
20Yesu ya amsa masu da cewa "Daya daga cikin sha biyu ne, wanda ke sa hannu tare da ni yanzu cikin tasar". 21Dan Mutum zai tafi ne yadda nassi ya umarta game da shi amma kaiton wanda zai bashe shi! "zai, fiye masa, dama ba a haife shi ba".
22Lokacin da suke cin abincin, Yesu ya dauki gurasa ya sa albarka, ya gutsuttsura ta, sai ya basu yana cewa "Wannan jikinana ne". 23Ya kuma dauki koko, yayi godiya, ya basu, su kuwa suka sha daga kokon. 24Ya ce "Wannan jinina ne na alkawari da an zubar ga yawancin mutane". 25Hakika, bazan kara sha daga wannan ruwan inabi ba sai a ranar da zan sha sabo cikin mulkin Allah."
26Bayan sun raira wakar yabo ga Allah, sai suka tafi wurin dutsen zaitun. 27Yesu ya ce masu dukkan ku zaku yi tuntube harma ku fadi saboda ni gama rubuce take cewa "Zan buge makiyayin, tumakin kuwa za su watse;
28Amma bayan tashina, zai yi gaba in riga ku zuwa Galili. 29Bitrus ya ce masa "ko dukkansu sun fadi, faufau banda ni".
30Yesu yace masa "Hakika ina gaya maka, cikin wannan dare kafin carar zakara ta biyu zaka yi musun sani na sau uku". 31Amma Bitrus ya sake cewa "Koda za'a kasheni tare da kai ba zan yi musun sanin ka ba". Dukkan su kuwa suka yi wannan Alkawari.
32Suka isa wani wuri da ake kira Getsamani, sai Yesu ya ce wa almajiransa "Ku dakata anan domin zan je inyi addu'a". 33Sai ya dauki Bitrus, da Yakubu, da Yahaya. Ya fara jin wahala mutuka tare da damuwa kwarai. 34Sai ya ce masu "Raina na shan wahala harma kamar in mutu. Ku dakata a nan, ku zauna a fadake".
35Da Yesu yayi gaba kadan, sai ya fadi kasa yayi addu'a yana cewa idan mai yiwuwa ne "A dauke masa wannan sa'a daga gare shi. 36Ya ce "Ya Abba Uba, kome mai yuwane gare ka, ka dauke mini kokon wahalan nan, duk da haka ba nufina ba sai dai naka".
37Da komowarsa ya same su suna barci, sai ya ce wa Bitrus, Siman barci kake? Ashe, ba za ka iya zama a fadake ko da sa'a daya ba? 38Ku zauna a fadake, kuyi addu'a kada ku fada cikin jaraba. Lalle ruhu na da niyya amma jiki raunana ne. 39Sai ya sake komawa, yayi addu'a, yana maimaita kalmominsa na farko.
40Har wa yau kuma ya sake dawowa, ya same su suna barci don barci ya cika masu idanu kwarai, sun kuwa kasa ce masa kome. 41Ya sake komowa karo na uku yace masu "har yanzu barci kuke yi kuna hutawa? Ya isa haka! Lokaci yayi, an bada Dan Mutum ga masu zunubi". 42Ku tashi mutafi kun ga, ga mai bashe ni nan ya kusato."
43Nan da nan, kafin ya rufe baki sai ga Yahuza, daya daga cikin sha biyun da taron jama'a rike da takkuba da kulake. Manyan firistoci da malaman attaura da shugabanni suka turo su. 44Mai bashe shi din nan ya riga ya kulla da su cewa "Wanda zan yi wa sumba shine mutumin, ku kama shi ku tafi da shi a tsare. 45Da isowarsa kuwa, sai ya zo wurin Yesu ya ce "Ya malam!". Sai ya sumbace shi. 46Su kuwa suka kama shi, suka tafi da shi.
47Amma daya daga cikin na tsaye ya zaro takobinsa ya kai wa bawan babban firist sara, ya yanke masa kunne. 48Sai Yesu ya ce "kun fito kamar masu kama yan fashi da takkuba da kulake, domin ku kama ni? 49Lokacin da nake koyarwa a Haikali, kowace rana da ku, baku kama ni ba. Amma anyi haka ne domin a cika abinda Nassi ya fada." 50Daga nan duk wadanda suke tare da Yesu suka yashe shi, suka tsere.
51Wani saurayi, daga shi sai mayafi ya bi shi, suka kai masa cafka. 52Shi kuwa ya bar masu mayafin ya gudu tsirara.
53Daga nan suka tafi da Yesu wurin babban firist. a can suka tara dattawa duk da manyan firistoci da shugabanni da marubuta, suka taru a wurinsa. 54Bitrus kuwa ya bi shi daga nesa har cikin gidan babban firist. Ya zauna tare da dogaran Haikalin, yana jin dumin wuta.
55Sai, manyan firistoci da duk 'yan majalisa Yahudawa suka nemi shaidar da za a tabbatar a kan Yesu, don su samu su kashe shi. Amma basu samu ba. 56Da yawa kuma suka yi masa shaidar Zur (Karya), amma bakin su bai zama daya ba.
57Sai wadansu kuma suka taso suka yi masa shaidar zur (karya) suka ce. 58"Mun ji ya ce, wai zai rushe haikalin nan da mutane suka gina, ya sake gina wani cikin kwana uku, ba kuwa ginin mutum ba". 59Duk da haka, sai shaidar tasu bata zo daya ba.
60Sai babban firist ya mike a tsakanin su, ya tambayi Yesu yace "Ba ka da wata amsa game da shaidar da mutanen nan suke yi a kanka? 61Amma yayi shiru abinsa, bai ce kome ba. Sai babban firist din ya sake tambayarsa "To, ashe kai ne Allmasihu Dan Madaukaki? 62Yesu ya ce "Nine. Za ku kuwa ga Dan Mutum zaune dama ga mai iko, yana kuma zuwa cikin gajimare".
63Sai babban firist ya kyakketa tufafinsa yace "Wacce shaida kuma zamu nema? 64Kun dai ji sabon da yayi! Me kuka gani? Duk suka yanke masa hukunci akan ya cancanci kisa. 65Wadansu ma suka fara tottofa masa yau, suka daure masa idanu, suka bubbuge shi suna cewa "Yi annabci" Dogaran kuma suka yi ta marinsa.
66Bitrus kuwa na kasa a filin gida, sai wata baranyar babban firist ta zo. 67Da ta ga Bitrus na jin dumi, ta yi masa kallon gaske ta ce "Kaima ai tare kake da banazaren nan Yesu". 68Amma ya musa ya ce "Ni ban ma san abinda kike fada ba balle in fahimta". Sai ya fito zaure. Sai zakara yayi cara.
69Sai baranyar ta ganshi, ta sake ce wa wadanda ke tsaitsaye a wurin, "Wannan ma daya daga cikinsu ne". 70Amma ya sake musawa, jim kadan sai na tsaitsayen suka ce wa Bitrus "Lalle kai ma dayansu ne don ba Galile ne kai".
71Sai ya fara la'anta kansa yana ta rantsuwa yana ce wa "Ban ma san mutumin nan da kuke fada ba". 72Nan da nan sai zakara ya yi cara ta biyu, Bitrus kuwa ya tuna da maganar Yesu a gare shi cewa "Kafin zakara ya yi cara ta biyu, za ka yi musun sani na sau uku". Da ya tuno haka, sai ya fashe da kuka.

15

1Da sassafe, sai manyan firistoci suka hadu da dattawa da manyan malamai, da majalisa suka daure Yesu, suka sa shi gaba suka mika shi ga Bilatus. 2Bilatus ya tambaye shi, kaine sarkin Yahudawa? ya amsa ya ce "haka ka ce" 3Sai manyan firistochi suka kawo zargi iri iri a kan Yesu.

4Bilatus ya sake tambayarsa, ba ka da abin cewa? ka lura da yawan zargi da ake yi maka. 5Amma Yesu baya sake yi masa magana ba. wannan ya ba shi mamaki.
6A lokacin idi, Bilatus ya kan sakar masu da dan bursuna wanda jama'a suka bukaci a saka, 7A cikin gidan yari, in da aka tsare wadansu yan tawaye, da masu kisan kai, akwai wani mai kisan kai, ana ce da shi Barrabbas. 8Sai Jama'a suka zo wurin Bilatus ya yi masu kamar yadda ya saba yi.
9Bilatus ya amsa masu ya ce, kuna so in sakar maku sarkin Yahudawa? 10Yayi wannan domin ya sani cewa Firistoci sun bada shi ne domin suna kishin sa, 11Sai Firistochi suka zuga jama'a, sai suka yi kuwwa suna cewa, a sakar masu Barrabbas amaimakon Yesu.
12Bilatus ya sake yi masu tambaya "Yaya zan yi da Sarkin Yahudawa?" 13sai suka amsa da kuwwa" a "giciye shi!"
14Bilatus ya ce masu menene laifinsa sai suka kara ihu, "a giciye shi." 15Bilatus don yana son ya farantawa jama'a zuciya sai ya sakar masu da Barrabbas sai ya yi wa Yesu bulala, sannan ya mika shi a giciye shi.
16Sojoji suka kai shi cikin kagara, suka tara rundunan soja, 17Suka sa masa tufafin shulaiya suka nada masa rawanin kaya, 18Suna masa kirari na ba'a suna cewa, "A gaida sarkin Yahudawa!"
19Sai suka buge shi a kai da kulki suka kuma tofa masa yau a fuska, suka kuma durkusa suna yi masa sujadar ba'a. 20Bayan sun gama yi masa ba'a sai suka cire masa tufafin shunnaiya, sai suka maida masa tasa tufafinsa, sai suka fitar dashi don su giciye shi. 21Suna cikin tafiya sai suka hadu da wani, mai suna Saminu Bakairawani (wato uban Alizanda da Rufus); suka tillasta shi ya dauki gijiyen Yesu.
22Sojojin suka kawo Yesu wurin da ake kira Golgota (wato kokon kai) 23Suka bashi ruwan inabi hade da mur, amma ya ki ya sha. 24Sai suka giciye shi, suka kuma raba tufafinsa suka kuma jefa kuri'a domin kowanne soja ya sami rabonsa.
25A sa'a ta uku aka giciye shi. 26Sai aka rubuta alamar zargi da take cewa "Ga Sarkin Yahudawa" 27Suka kuma giciye shi tare da wadansu yan fashi guda biyu. 28Daya a hannun damansa daya a hannun hagunsa. Domin a cika abinda nassi ya fada.
29suke wucewa suna zaginsa suna kada kai suna cewa, "Aha! kai da zaka rushe haikali ka kuma gina shi cikin kwana uku, 30ka ceci kanka mana, ka sauka daga giciye!"
31Haka ma manyan firistoci da malamai, suka yi masa ba'a suna cewa "Ya ceci wadansu amma bai iya ceci kansa ba" 32Bari Almasihu Sarkin Yahudawa ya sauka daga giciye. Domin mu gaskata shi, sai wadanda aka giciye shi tare dasu, suma suka yi masa ba'a.
33sa'a ta shida zuwa sa'a ta tara, duhu ya rufe ko'ina, 34A sa'a ta tara, Yesu ya tada murya da karfi ya ce Eloi, Eloi lamathsabathani?" Ma'ana Ya Allahna Ya Allahna, me ya sa ka yashe ni?" 35Wasu daga cikin na tsaye, da suka ji shi, sai suka ce, "Duba, yana kiran Iliya."
36Sai wani ya hanzarta, ya dauki soso ya tsoma a ruwan inabi mai tsami, ya soka agora ya mika masa don yasha. Mutumin yace bari mu gani ko Iliya zai zo ya saukar da shi. 37Sai Yesu yayi kuka da babban murya da karfi sannan ya rasu. 38Sai labulen haikalin ya rabu kashi biyu daga sama har kasa.
39Sa'adda da jarumin sojan da ke tsaye yana fuskantar Yesu ya ga yadda ya mutum, Sai ya ce "hakika, wannan mutum Dan Allah ne." 40Akwai kuma mata wadanda ke dubawa daga nesa. Daga cikinsu akwai Maryamu Magadala, da Maryamu( Uwar Yakubu da Yusufu) da Salome.41Wadannan matan sune suka bishi sa'adda da yake Galilee suna yi masa hidima. Da wadansu mata da yawa suka zo Urushalima tare da shi.
42Da maraice an shiga shirye shirye domin kashe gari asabbaci ce. 43Sai Yusufu daga garin Arimatiya ya zo, mutumin kirki, mai girma kuma dan majalisar dattawa, mai sauraron mulkin Allah, da gaba gadi ya tafi wurin Bilatus ya bukaci a bashi jikin Yesu. 44Bilatus ya yi mamakin mutuwar Yesu cikin lokaci kadan, sai ya kira jarumin ya tabbattar koYesu ya mutu.
45Bayan ya tabbattar daga wurin jarumin soja cewa Yesu ya mutu, sai ya bada jikin ga Yusufu. 46Yusufu ya sayo likafani. ya saukar da shi daga giciye, ya kawo likafanin nan ya lulube jikin Yesu dashi. Ya kai shi kabarin da aka sassaka da dutse, wadda ya shirya shi domin kansa. Ya kawo dutse ya rufe bakin kabarin da shi. 47Maryamu Magadaliya da Maryamu Uwar Yusufu sun ga wurin da aka yi jana'izar Yesu.

16

1Bayan ranar assabaci, Maryamu Magadaliya da Maryamu uwar Yakubu da Salomi, suka sayo man shafawa mai kamshi domin shafe jikin Yesu saboda jana'iza. 2Da safiyar ranar farko ta mako sai suka tafi kabarin a dai dai fitowar rana.

3Suna magana a tsakaninsu suna cewa, wanene zai gangarar da dutsen da aka rufe bakin kabarin da shi?" 4Da suka daga ido, sai suka ga an riga an gangarar da dutsen, domin yana da girma.
5Da suka shiga cikin kabarin sai ga wani saurayi saye da farar tufa, yana zaune a hannun dama, suna mamaki. 6Sai ya ce masu, "Kada ku ji tsoro. Kuna neman Yesu banazare, wanda aka giciye. Ya tashi! Baya nan. Ku duba wurin da aka kwantar dashi. 7Sai ku je, ku gaya wa almajiransa da Bitrus cewa ya rigaya ya yi gabanku zuwa Galili. A can zaku ganshi, kamar yadda ya fada maku."
8Suka fita daga cikin kabarin da gudu suna rawar jiki da mamaki, ba su cewa kowa komai ba domin suna jin tsoro.
9Da safiyar ranar farko ta mako ya fara bayyana kansa ga Maryamu Magadaliya wadda ya kori aljannu guda bakwai daga cikinta. 10Sai ta tafi ta shaida wadanda suke tare da shi suke makoki da kuka. 11Sai suka ji cewa ya tashi kuma ta ganshi, amma basu gaskata ba.
12Bayan wadannan al'amura ya bayana kansa ta wata siffa ga mutum biyu sa'ilin da suke tafiya akan hanya. 13Sai suka tafi suka gaya wa sauran almajiransa, duk da haka basu gaskata ba.
14Bayan wani lokaci, Yesu ya bayyana kansa ga almajiransa su goma sha daya, ya tsauta masu saboda rashin gaskatawa da taurin zuciya, bayansun ji daga wadanda suka ganshi bayan ya tashi daga matattu. 15Sai ya umarcesu cewa "Ku tafi cikin duniya ku yi bishara ga dukan halitta. 16Wanda ya ba da gaskiya aka kuma yi masa baftisma, zaya sami ceto, wanda baya bada gaskiya ba za ya hallaka.
17Wadannan alamu za su kasance da wadanda suka gaskata; a cikin sunana, za su fidda aljannu, za su yi magana da sabbin harsuna. 18Za su dauki macizai da hannayesu, idan sun sha guba ba ta cutar dasu ba, za su dibiya hannayensu ga marasa lafiya, za su sami warkaswa."
19Bayan Ubangiji ya gama magana da su, sai aka dauke shi zuwa sama in da zai zauna a hannun dama na Allah. 20Almajiransa kuma suka tafi ko'ina suna sheilar bishara. Ubangiji kuma yayi aiki tare da su, yana tabbatar da kalma ta wurin ayukan al'ajiba tare da su.

Luka

1

1Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu, 2kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon. 3Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas. 4Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.

5A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne. 6Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji. 7Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
8Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa. 9Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare. 10Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
11A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren. 12Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi. 13Amma mala'ikan ya ce masa, "Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
14Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa. 15Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
16Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu. 17Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa."
18Zakariya ya ce wa mala'ikan, "Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa." 19Mala'ikan ya amsa ya ce masa, "Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi. 20Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin."
21Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali. 22Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana. 23Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
24Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce, 25"Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a."
26A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat, 27zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu. 28Ya zo wurin ta ya ce, "A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke. 29Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
30Mala'ikan ya ce mata, "Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah. 31Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'. 32Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda. 33Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka."
34Maryamu ta ce wa mala'ikan, "Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?" 35Mala'ikan ya amsa ya ce mata, "Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
36Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya. 37Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah." 38Maryamu ta ce, "To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka." Sai mala'ikan ya bar ta.
39Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya. 40Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu. 41Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
42Ta daga murya, ta ce, "Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki. 43Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni? 44Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna. 45Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
46Maryamu ta ce, "Zuciyata ta yabi Ubangiji, 47kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na."
48Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka. 49Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
50Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi. 51Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
52Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu. 53Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
54Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai 55(kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada."
56Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta. 57Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji. 58Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
59Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa "Zakariya" kamar sunan ubansa, 60amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, "A'a, za a kira shi Yahaya." 61Suka ce mata, "Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna."
62Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna. 63Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, "Sunansa Yahaya." Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
64Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah. 65Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya. 66Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, "To me wannan yaro zai zama ne?" Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
67Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa, 68"Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su."
69Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa, 70kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. 71Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
72Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki, 73rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim. 74Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba, 75a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
76I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa, 77domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
78Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu, 79domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
80Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.

2

1Ananan cikin kwanakin, sai Kaisar Augustas ya yi shela ya umarta a kidaya dukan mutane da ke zaune a cikin duniya. 2Wannan itace kidaya ta farko da aka yi lokacin da Kiriniyus yake mulkin Suriya. 3Sabili da haka, kowa ya koma garinsa domin a yi masa rijista domin kidayan.

4Yusufu kuma ya tashi ya bar birnin Nazarat zuwa garin Baitalami da ke Yahudiya, wanda ake kuma kira birnin Dauda, domin shi daga zuriyar iyalin Dauda ne. 5Ya je can ya yi rijista tare da Maryamu, wadda yake tashi tana kuma da juna biyu.
6Ya zama sa'adda suke can, lokaci ya yi da za ta haifi danta. 7Ta haifi da, dan farinta kuwa, ta nade shi da kyau da 'yan tsummoki. Ta sa shi cikin wani kwami na dabbobi, gama babu daki dominsu a masaukin.
8A cikin wannan yankin, akwai makiyaya wadanda suke zama a sarari suna tsaron garken tumakinsu da dare. 9Nan da nan, sai mala'ikan Ubangiji ya bayyana gare su, daukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, sai suka figita kwarai.
10Sai mala'ikan ya ce masu, "Kada ku ji tsoro, domin na kawo maku labari mai dadi da zai kawo murna da yawa ga dukan mutane. 11Yau an haifi maku mai ceto a cikin birnin Dauda! Shine Almasihu Ubangiji! 12Wannan itace alama da za a ba ku. Za ku ga dan jariri nade cikin 'yan tsummoki kwance cikin kwamin dabbobi."
13Nan take, sai ga babban taro daga sama tare da mala'ikan suna yabon Allah, suna cewa, 14"Daukaka ga Allah daga bisa, bari salama ta kasance a duniya tsakanin mutanen da ya ke jin dadinsu."
15Ya zama sa'adda mala'iku suka bar su zuwa cikin sama, sai makiyayan su ka ce wa junansu, "Bari mu je Baitalami mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya nuna mana." 16Su ka yi hamzari suka tafi can sun iske Maryamu da Yusufu, suka ga jaririn kuwa kwance a cikin kwamin dabbobin.
17Bayan da sun ga wannan, suka gaya wa mutane abinda aka gaya masu game da wannan yaro. 18Dukan wadanda su ka ji, su ka yi mamaki kwarai game da abin da makiyayan su ka gaya masu. 19Amma ita Maryamu ta ci gaba da tunani akan wadanan abubuwa da ta ji, tana tunani mai zurfi a cikin zuciyarta. 20Makiyayan suka koma suna ta daukaka da yabon Allah domin dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, dadai da yadda aka gaya masu.
21Da ya kai kwana takwas, lokacin da za a yi wa jaririn kaciya, sai aka rada masa suna Yesu, sunan da mala'ikan ya bashi kamin a yi cikinsa.
22Da kwanakin tsarkakewar su ya wuce bisa ga shari'ar Musa, Yusufu da Maryamu suka kawo shi cikin haikali a Urushalima dominsu mika shi ga Ubangiji. 23Kamar yadda aka rubuta a dokokin Ubangiji, "Za a kira duk da na fari kebabbe ga Ubangiji." 24Suka kuma zo su mika hadaya bisa ga yadda aka fada a shari'ar Ubangiji, "Kurciyoyi biyu ko 'yan tantabaru biyu."
25Ga shi akwai wani mutum a Ushalima mai suna Siman. Wannan mutum adali ne kuma mai ibada. Yana jiran mai ta'aziyar Isra'ila, kuma Ruhu Mai-sarki na bisansa. 26An kuma bayyana masa ta wurin Ruhu Mai-tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kristi na Ubangiji.
27Wata rana Siman ya zo cikin haikali ta wurin jagorar Ruhu Mai-tsarki. Da iyayen suka kawo yaron ciki, wato Yesu, domin su cika sharudan da shari'ar ke bukata, 28sai Siman ya karbe shi cikin hanuwansa, ya yabi Allah ya ce, 29"Yanzu bari bawanka ya tafi da salama, Ubangiji, bisa ga kalmarka.
30Domin idanuna sun ga cetonka, 31wanda ka shirya a gaban dukan mutane: 32Haske ne na wahayi ga al'ummai, kuma daukakar mutanenka Isra'ila."
33Mahaifin yaron da Mahaifiyarsa, sun yi mamaki kwarai domin abubuwan da aka fada akansa. 34Sai Siman ya albarkace su ya ce wa uwatasa Maryamu, "Ki ji da kyau, wannan yaro zai zama sanadiyar faduwa da tashin mutane dayawa a Isra'ila, kuma alama wadda ake kushen ta. 35Kuma takobi zai tsaga zuciyar ki yadda tunanin mutane za ya bayyana."
36Wata annabiya mai suna Annatu ta na nan wurin. Ita diyar Fanuyila ce daga kabilar Ashiru. Ta riga ta manyanta a shekaru sosai. Ta kasance da maigidanta shekaru bakwai bayan auren ta, 37sannan ta yi zama gwambranci na shekaru tamanin da hudu. Ba ta taba barin haikali ba, tana ci gaba da yi wa Ubangiji sujada, dare da rana. 38A dadai lokacin nan, ta hau zuwa wurinsu ta fara yi wa Allah godiya. Ta gaya wa dukan wadanda ke jiran fansar Urushalima.
39Da su ka gama komai da aka bukace su suyi bisa ga tafarkin shari'ar Ubangiji, sai suka koma Galili, zuwa birninsu, Nazarat. 40Yaron kuma ya yi girma ya zama da karfi, yana karuwa da hikima, alherin Ubangiji kuma yana kansa.
41Iyayensa sukan tafi Urushalima kowacce shekara domin idin ketarewa. 42Da yana shekara goma sha biyu, suka sake haurawa daidai lokacin idin a al'adance. 43Bayan da sun cika dukan kwanakin idin, sun fara dawowa gida. Amma dan yaron Yesu ya jinkirta ya zauna a Urushalima, kuma iyayensa basu sani ba. 44Suna tsammani yana tare da sauran mutane da suke tafiya tare, sai suka yi tafiya na kwana daya. Suka fara neman sa a cikin danginsu da abokansu.
45Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima suna cigiyar sa a can. 46Ya zama bayan kwanaki uku, su ka same shi a cikin haikali, yana zama a tsakiyar malamai, yana sauraron su yana kuma yi masu tambayoyi. 47Dukan wadanda suka ji shi suna ta mamakin fahimtar sa da amsoshin sa.
48Da suka gan shi, suka yi mamaki kwarai. Mahaifiyarsa ta ce masa, "Da na, don me ka yi mana haka? Ka ji, mahaifinka da ni muna ta neman ka rai a bace." 49Ya ce masu, "Don me kuke nema na? Ba ku sani cewa dole in kasance a gidan Ubana ba?" 50Amma ba su gane abin da yake nufi da kalmomin nan ba.
51Sa'annan ya koma gida tare da su zuwa Nazarat yana kuma masu biyayya. Mahaifiayarsa kuma ta ajiye dukan wadannan abubuwa a zuciyarta tana yin tunani akansu. 52Amma Yesu ya ci gaba da hikima da girma, ya kuma karu da tagomashi wurin Allah da mutane.

3

1A cikin shekara ta goma sha biyar da Tibariyus Kaisar ke mulki, Bilatus Babunti kuma ke jagorar Yahudiya, Hirudus yana sarautar Galili, dan'uwansa Filibus yana sarautar yankin Ituriya da Tirakonitis, Lisaniyas kuma na sarautar yankin Abiliya, 2kuma zamanin da Hanana da Kayafa suke manyan firistoci, maganar Allah ta zo wurin Yahaya dan Zakariya, a cikin jeji.

3Ya yi tafiya cikin dukan yankuna da ke kewaye da Kogin Urdun, yana wa'azin baftismar tuba domin gafarar zunubai.
4Kamar yadda aka rubuta a cikin littafin annabi Ishaya, "Ga muryan wani yana kira a cikin jeji, 'Shirya hanyar Ubangiji, ka daidaita tafarkunsa!
5Za a cika kowani kwari, za a fasa kowani dutse a kuma baje kowani tudu, za a mike karkatattun hanyoyi, za a cike hanyoyi masu gargada, 6kuma dukan mutane za su ga ceton Allah."
7Sai Yahaya ya kara fada wa taron jama'ar da ke zuwa domin ya yi masu baftisma, "Ku 'ya'yan macizai masu dafi, wa ya gargadeku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
8Ku ba da 'ya'ya da sun cancanci tuba, kada ku kuma fara cewa a cikinku, 'Muna da Ibrahim a matsayin Ubanmu', domin ina gaya maku, Allah yana iya ta da wa Ibrahim 'ya'ya daga cikin wadannan duwatsu.
9Yanzu kuwa, an rigaya an sa gatari a gindin itatuwa. Sabili da haka, duk itacen da bai ba da 'ya'ya masu kyau ba za a sare shi kasa a kuma jefa shi cikin wuta."
10Sai mutanen da ke cikin taron jama'ar suka tambaye shi cewa, "To me za mu yi?" 11Ya amsa ya ce masu, "Idan wani yana da taguwa biyu, sai ya ba wanda bashi da ita daya, kuma wanda yake da abinci ya yi haka nan."
12Masu karban haraji ma suka zo domin a yi masu baftisma, suka ce masa, "Malam, me za mu yi?" 13Ya ce masu, "Kada ku karba kudi fiye da yadda aka umarce ku."
14Wasu sojoji ma suka tambaye shi cewa, "To, mu fa? Yaya za mu yi?" Ya ce masu, "Kada ku kwace wa wani kudi, kada ku kuma yi wa wani zargin karya. Ku dogara ga albashinku."
15Ana nan da mutane ke sauraron zuwan Almasihu, kowa yana ta tunani a zuciyar sa game da Yahaya, ko shi ne Almasihu. 16Yahaya ya amsa ya ce masu duka, "Game da ni dai, na yi maku baftisma da ruwa, amma akwai wani tafiye wanda ya fi ni iko, ban ma isa in kwance maballin takalmansa ba. Shi zai yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
17Kwaryar shikarsa na hanun sa domin ya share masussukarsa da kyau ya kuma tara alkama a cikin rumbunsa. Amma zai kona buntun da wuta marar mutuwa.
18Da gargadi masu yawa ya yi wa mutanen wa'azin bishara. 19Yahaya kuma ya tsauta wa sarki Hirudus domin ya auri matar dan'uwansa, Hiruduya, da kuma sauran abubuwan da Hirudus ya yi. 20Amma Hirudus ya kara yin wani mugun abu. Ya sa an kulle Yahaya a cikin kurkuku.
21Ana nan, lokacin da ake yiwa dukan mutane baftisma, aka yiwa Yesu mai baftisma. Lokacin da yake yin addu'a, sai sama ta bude, 22kuma Ruhu Mai Tsarki ya sauko masa a kamanin kurciya, sai wata murya ta fito daga sama, "Kai ne kaunataccen Da na. Ina jin dadin ka."
23Ana nan Yesu da kansa, da ya fara, yana kimanin shekara talatin. Shi dan (kamar yadda ake tsammani) Yusufu ne, dan Heli, 24dan Matat, dan Lawi, dan Malki, dan Yanna, dan Yusufu,
25dan Matatiya, dan Amos, dan Nahum, dan Hasli, dan Najjaya, 26dan Ma'ata, dan Matatiya, dan Shimeya, dan Yuseka, dan Yoda,
27dan Yowana, dan Resa, dan Zarubabila, dan Shiyaltiyel, dan Niri, 28dan Malki, dan Addi, dan Kosama, dan Almadama, dan Er, 29dan Yosi, dan Aliyeza, dan Yorima, dan Matat, dan Lawi,
30dan Saminu, dan Yahuda, dan Yusufu, dan Yonana, dan Aliyakima, 31dan Malaya, dan Mainana, dan Matata, dan Natan, dan Dauda, 32dan Yesse, dan Obida, dan Bu'aza, dan Salmon, dan Nashon,
33dan Amminadab, dan Adimi, dan Arama, dan Hezruna, dan Feresa, dan Yahuda, 34dan Yakubu, dan Ishaku, dan Ibrahim, dan Tera, dan Nahor, 35dan Serug, dan Reyu, dan Feleg, dan Abiru, dan Shela,
36dan Kainana, dan Arfakshada, dan Shem, dan Nuhu, dan Lamek, 37dan Metusela, dan Anuhu, dan Yaret, dan Mahalel, dan Kainana, 38dan Enosh, dan Shitu, dan Adamu, dan Allah.

4

1Sai Yesu, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga kogin Urdun, sai Ruhu Mai Tsarki ya bishe shi zuwa cikin jeji 2kwana arba'in, shaidan kuma ya jarabce shi. A kwanakin nan, bai ci abinci ba, kuma yunwa ta kama shi bayan karshen lokacin.

3Shaidan ya ce masa, "Idan kai Dan Allah ne, ka umarci wannan dutse ya zama gurasa." 4Yesu ya amsa masa, "A rubuce yake, 'Ba da gurasa kadai Mutum zai rayu ba.'"
5Sai shaidan ya kai shi zuwa wani tudu mai tsawo, ya kuma nuna masa dukan mulkokin duniyan nan a dan lokaci. 6Shaidan ya ce masa, "Zan ba ka iko ka yi mulkin dukan wadannan, da dukan daukakarsu. Zan yi haka domin an ba ni su duka in yi mulkinsu, kuma ina da yanci in ba dukan wanda na ga dama. 7Saboda da haka, idan ka rusuna ka yi mani sujada, dukansu za su zama naka."
8Amma Yesu ya amsa ya ce masa, "A rubuce yake, 'Dole ne Ubangiji Allahnka za ka yi wa sujada, shi kadai kuma za ka bauta wa."
9Sai shaidan ya kai Yesu Urushalima, ya tsayadda shi a bisan kololuwar haikali, kuma ya ce masa, "Idan kai Dan Allah ne, ka jefas da kanka kasa daga nan. 10Domin a rubuce yake, 'Zai ba mala'ikunsa umarni su kiyaye ka, su kuma tsare ka,' 11kuma, 'Za su daga ka sama a hannunsu, don kada ka yi tuntube a kan dutse."
12Yesu ya amsa masa cewa, "An fadi, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'" 13Da shaidan ya gama yi wa Yesu gwaji, sai ya kyale shi sai wani lokaci.
14Sai Yesu ya koma Galili cike da ikon Ruhu, kuma labarinsa ya bazu cikin dukan wuraren dake wannan yankin. 15Ya yi ta koyarwa a cikin majami'unsu, sai kowa na ta yabon sa.
16Wata rana ya zo Nazarat, birnin da aka rene shi. Kamar yadda ya saba yi, ya shiga cikin majami'a a nan ranar Asabaci, ya kuma tashi tsaye domin ya karanta Nassi. 17An mika masa littafin anabi Ishaya, ya bude littafin ya kuma ga inda an rubuta,
18"Ruhun Ubangiji yana kai na, domin ya shafe ni in yi wa'azin Bishara ga matalauta. Ya aike ni in yi shelar yanci ga daurarru, da kuma budewar idanu ga makafi, in 'yantar da wadanda su ke cikin kunci, 19in kuma yi shelar shekarar tagomashi na Ubangiji."
20Sai ya rufe littafin, ya mai da shi ga ma'aikacin majami'ar, sai ya zauna. Dukan wadanda suke cikin majami'ar suka zura Idanuwansu a kansa. 21Sai ya fara masu magana, "Yau wannan Nassi ya cika a kunuwanku." 22Dukan wadanda ke wurin sun shaida abin da ya fadi kuma dukansu sun yi ta mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suna cewa, "Wannan ai dan Yusufu ne kawai, ko ba haka ba?"
23Yesu ya ce masu, "Lallai za ku fada mani wannan karin magana, 'Likita, ka warkar da kanka. Duk abin da mun ji wai ka yi a Kafarnahum, ka yi shi a nan garinka ma.'" 24Ya sake cewa, "Hakika na fada maku, annabi baya samun karbuwa a garinsa.
25Amma na gaya maku gaskiya akwai gwauraye da yawa cikin Isra'ila a zamanin Iliya, lokacin da an rufe sammai shekaru uku da rabi babu ruwa, lokacin da anyi gagarumar yunwa a duk fadin kasar. 26Amma ba a aiki Iliya zuwa wurin waninsu ba, sai wurin gwauruwa da ke a Zarifat can kusa da Sidon. 27Akwai kutare da yawa kuma a Isa'ila a zamanin anabi Elisha, amma babu wanda aka warkar sai dai Na'aman mutumin Suriya kadai.
28Dukan mutanen da ke cikin majami'a suka fusata kwarai sa'adda suka ji wadannan zantattuka. 29Suka tashi suka tura shi zuwa wajen birnin, suka kai shi bakin dutsen da aka gina garinsu a kai dominsu jefar da shi kasa. 30Amma ya ratsa tsakaninsu ya yi gabansa.
31Sannan ya gangara zuwa Kafarnahum, wani birni a Galili. Wata Asabaci yana koya wa mutane a cikin majami'a. 32Sun yi mamaki kwarai da koyarwan sa, domin maganarsa na da iko.
33A wannan lokacin akwai wani mutum a cikin majami'a mai kazamin ruhu, sai ya yi kara da babbar murya, 34"Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo domin ka hallaka mu ne? Na san ko kai wanene! Kai ne Mai Tsarki na Allah!"
35Yesu ya tsauta wa aljanin yana cewa, "Yi shiru ka fita daga cikinsa!" Da aljanin ya jefar da mutumin kasa a tsakiyarsu, ya fita daga cikinsa ba tare da yi masa rauni ba. 36Dukan mutanen suka yi mamaki, kuma suna ta zancen wannan abu a tsakaninsu. Sun ce, "Wanda irin maganganu kenan? Ya umarce kazaman ruhohin da karfi da iko kuma sun fita." 37Saboda da haka, an fara yada labarinsa zuwa dukan kewayen yankin.
38Sai Yesu ya bar majami'ar ya shiga gidan Siman. A wannan lokacin, surukar Siman tana fama da zazzabi mai zafi, sai suka roke shi dominta. 39Sai ya tsaya a kanta, ya tsautawa zazzabin, kuma ya rabu da ita. Nan take, ta tashi ta fara yi masu hidima.
40Da faduwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan wadanda suke ciwo da cuttuttuka dabam dabam. Ya dora masu hannuwansa ya warkar da su. 41Aljanu kuma sun fita daga wadasunsu da dama, suna kuka cewa, "Kai ne Dan Allah!" Yesu ya tsauta wa aljannun ya kuma hana su magana, domin sun sani cewa shine Almasihu.
42Da safiya ta yi, ya kebe kansa zuwa wani wurin da babu kowa. Jama'a da dama suna neman sa suka zo inda yake. Sun yi kokari su hana shi barin su. 43Amma ya ce masu, "Dole in yi bisharar Allah a wasu birane da dama, domin dalilin da aka aiko ni nan kenan." 44Sai ya ci gaba da wa'azi cikin majami'u dukan fadin Yahudiya.

5

1Ya zama sa'adda mutane sun taru a wurin Yesu suna sauraron maganar Allah, yana kuma yana tsaye a bakin tabkin Janisarata. 2Ya ga jiragen ruwa biyu tsaye a bakin tabkin. Masu kamun kifin kuwa sun fita daga cikin jiragen suna wanke tarunsu. 3Yesu ya shiga daya daga cikn jiragen wanda shike na Bitrus ne, sai ya umarce shi ya dan zakuda da jirgin daga bakin tabkin kadan zuwa cikin ruwa. Sai ya zauna ya kuma koya wa mutane daga cikin jirgin.

4Da ya gama magana, ya ce wa Siman, "Zakuda jirgin zuwa wuri mai zurfi sa'annan ka zuba tarunka domin kamu." 5Siman ya amsa ya ce, "Ubangiji, mun yi aiki dukan dare bamu kama komai ba, amma bisa ga maganarka, zan jefa tarun." 6Da sun yi haka, suka kama kifaye da yawan gaske, har tarunsu suna yagewa. 7Sai suka roki abokan aikinsu da ke a dayan jirgin su zo su taimake su. Suka zo sun cika jiragen biyu da kifaye, har suka fara nutsewa.
8Amma Siman Bitrus, da ya ga haka, ya russuna a gaban Yesu, yana cewa, "Ka rabu da ni Ubangiji, gama ni mai zunubi ne." 9Domin ya yi mamaki, da dukan wadanda suke tare da shi, sabili da yawan kifaye da suka kama. 10Wannan ya hada da Yakubu da Yahaya 'ya'yan Zabadi abokan aikin Siman. Sai Yesu ya ce wa Siman, "Kada ka ji tsoro, domin daga yanzu, za ka kama mutane." 11Da sun kawo jiragensu waje kan kasa, suka bar komai suka kuma bi shi.
12Sa'adda yana daya daga cikin biranen, wani mutum dauke da kuturta yana nan wurin. Da ya ga Yesu, ya fadi bisa fuskarsa kasa yana rokansa, yana cewa, "Ubangji, idan ka yarda, za ka iya tsarkake ni." 13Yesu ya mika hanunsa ya taba shi, yana cewa, "Na yarda. Ka tsarkaka." Sai nan da nan, kuturtar ta rabu da shi.
14Ya umarce shi kada ya gaya wa kowa, amma ya ce ma sa, "Tafi ka nuna kanka ga firist sa'annan ka mika hadaya domin tsarkakewarka, kamar yadda Musa ya umarta, a matsayin shaida a garesu."
15Amma labarinsa ya bazu nesa, taron mutane da yawa kuma suka zo wurinsa domin su ji shi, su kuma samu warkarwa daga cututtukansu. 16Amma ya kan janye zuwa wuraren da babu kowa ya yi addu'a.
17Ya zama daya a cikin kwanakin da yake koyarwa, akwai Farisawa da malaman attaura da ke zaune a wurin wandanda suka zo daga kauyukan da suke kewaye da Galili da Yahudiya da kuma birnin Urushalima. Ikon Ubangiji yana tare da shi domin warkarwa.
18A lokacin nan, wasu mutane suka zo dauke da wani mutum shanyayye a kan tabarma, suka kuma nemi yadda za su shigar da shi ciki, su kwantar da shi a gaban Yesu. 19Ba su iya samun hanyar da za su shigar da shi ba saboda taron, sai suka hau saman gidan, suka saukar da shi daga rufin, a kan tabarman sa, zuwa tsakiyar mutanen, dai dai a gaban Yesu.
20Da ya ga bangaskiyarsu, Yesu ya ce, "Maigida, an gafarta zunubanka." 21Marubuta da Farisawa suka fara sukar wannan, suna cewa, "Wanene wannan da ke sabo? Wa zai iya gafarta zunubi, idan ba Allah kadai ba?"
22Amma da Yesu ya fahimci abin da suke tunani, sai ya amsa ya ce masu, "Don me kuke sukar wannan a zuciyarku? 23Wanne ne ya fi sauki a ce, 'An yafe zunubanka' ko kuwa a ce, 'Tashi ka yi tafiya?" 24Amma domin ku sani cewa Dan Mutum yana da yancin gafarta zunubai a duniya, na ce maka, 'Tashi, dauki tabarmanka, ka tafi gidanka.'"
25Nan take, ya tashi a gabansu ya dauki tabarma da yake kwance; sai ya koma gidansa, yana daukaka Allah. 26Kowa yana ta mamaki kuma suka daukaka Allah. Suna cike da tsoro, suna cewa, "Yau mun ga abubuwan al'ajibi."
27Bayan wadannan abubuwa sun faru, Yesu ya fito daga can sai ya ga wani mai karban haraji mai suna Lawi yana zama a wurin karban haraji. Ya ce masa, "Ka biyo ni." 28Sai Lawi ya bar komai, ya tashi, ya bi shi.
29Lawi kuma ya shirya gagarumar liyafa a gidansa, kuma akwai masu karban haraji da yawa a nan, da wasu mutane da ke zama a gaban teburin liyafar suna cin abinci tare da su. 30Amma Farisawa da Marubuta suka fara korafi ga almajiransa, suna cewa, "Don menene kuna ci da sha tare da masu karban haraji da mutane masu zunubi?" 31Yesu ya amsa masu, "Masu lafiya basu bukatar likita, wadanda ke marasa lafiya kadai ke bukatar likita. 32Ban zo domin kiran masu adalci ba, amma na zo ne domin kiran masu zunubi zuwa ga tuba."
33Sun ce masa, "Almajiran Yahaya sukan yi azumi da addu'a, kuma almajiran Farisawa ma sukan yi haka. Amma almajiranka suna ci suna sha?" 34Yesu ya ce masu, "Akwai wanda zai sa abokan ango su yi azumi, a lokacin da shi ango yana tare da su? 35Amma kwanaki na zuwa wadanda za a dauke ango daga wurinsu, a kwanakin za su yi azumi."
36Sai Yesu ya sake fada masu wani misali. "Babu wanda zai yage kyalle daga sabuwar tufa, ya kuma yi amfani da ita ya dinka tsohuwar tufa. Idan ya yi hakannan, zai yage sabuwar tufar, kuma kyallen daga sabuwar tufar ba zai dace da kyallen tsohuwar tufar ba.
37Kuma, babu mutum da zai sa sabon ruwan inabi a cikin tsofafin salkuna. Idan ya yi haka, sabon ruwan inabin zai fasa salkunan, kuma ruwan inabin din zai zube, salkunan kuma za su lallace. 38Amma dole ne a sa sabon ruwan inabi a sabobin salkuna. 39Babu wanda zai yi marmarin sabon ruwan inabi bayan da ya sha tsohon, gama zai ce, "Tsohon ya fi sabon."

6

1Ana nan wata Asabaci Yesu yana ratsawa cikin gonar hatsi, almajiransa kuma na karyar zangarkun hatsin, suna murtsukawa a hanayensu suna ci. 2Amma wasu daga cikin Farisawa suka ce, "Saboda me kuke yin abin da bai halatta a yi a ranar Asabaci ba?"

3Yesu ya amsa masu, ya ce, "Ba ku karanta abin da Dauda ya yi a lokacin da yake jin yunwa ba, shi da mutanen da ke tare da shi? 4Ya je cikin gidan Allah, ya dauki gurasar alfarwa ya kuma ci daga ciki, ya kuma ba mazajen da ke tare da shi su ci, ko da shike ya halarta ga Firistoci ne kadai su ci." 5Sai ya ce masu, "Dan Mutum shi ne Ubangijin asabaci."
6Ya kasance a wata ranar Asabaci ya shiga cikin majami'a ya kuma koya wa mutane a can. Wani mutum na can wurin wanda hannun damansa ya shanye. 7Marubuta da Farisawa na kallonsa su ga ko zai warkar da wani a ranar Asabaci, domin su samu dalilin zarginsa da yin abin da bai cancanta ba. 8Amma ya san abin da suke tunani, sai ya ce wa mai shanyeyen hannun, "Tashi, ka tsaya a nan tsakiyar jama'a." Sai mutumin ya tashi ya tsaya a nan.
9Yesu ya ce masu, "Ina tambayar ku, ya halatta a ranar Asabaci a yi nagarta ko mugunta, a ceci rai ko a hallaka shi? 10Sai ya dube su duka, ya kuma ce wa mutumin, "Mika hannunka." Ya yi haka, sai hannunsa ya koma lafiyayye. 11Amma suka fusata kwarai, suka yi shawara da junansu game da abin da za su yi da Yesu.
12Ya zama a kwanakin nan, ya hawo bisan dutse domin ya yi addu'a. Ya ci gaba dukan dare yana addua'a ga Allah. 13Da safiya ta yi, ya kira almajiransa zuwa wurinsa, ya kuma zabi goma sha biyu daga cikinsu, wadanda ya kira su "Manzanni."
14Sunayen Manzannin sune Siman (wanda ya kuma kira Bitrus) da dan'uwansa, Andrawus, Yakubu, Yahaya, Filibus, Bartalamawus, 15Matta, Toma, Yakubu dan Halfa, Siman, wanda ake kira Zaloti, Yahuda dan Yakubu, 16da Yahuda dan Iskariyoti, wanda ya zama maci amana.
17Sai Yesu ya gangaro daga dutsen tare da su, suka kuma tsaya a sarari. Almajiransa da yawa na nan a wurin, tare da mutane da yawa daga Yahudiya da Urushalima, da kuma bakin tekun Taya da Sidon. 18Sun zo domin su ji shi, da kuma su sami warkarwa daga dukan cututukansu. Mutane waddan da ke fama da kazaman ruhohi ma sun sami warkarwa. 19Dukan taron jama'ar suna kokarin su taba shi domin ikon warkarwa yana fitowa daga wurinsa, ya kuma warkar da su duka.
20Sai ya dubi almajiransa ya ce, "Masu albarka ne ku matalauta, gama Mulkin Allah naku ne. 21Masu albarka ne ku masu yunwa yanzu, domin za a kosar da ku. Masu albarka ne ku masu kuka a yanzu, domin za ku yi dariya.
22Masu albarka ne ku idan mutane sun ki ku, suka nuna maku wariya suna mai da sunayen ku na mugunta, domin Dan Mutum. 23Za ku yi farin ciki a ranan nan kuna tsalle domin murna, domin hakika za ku samu lada mai girma a sama, domin haka kakannin-kakannin su suka yi wa annabawa.
24Amma kaitonku mawadata! Domin kun rigaya kun samu ta'aziyar ku. 25Kaitonku kosassu a yanzu! Domin za ku ji yunwa nan gaba. Kaitonku masu dariya yanzu! Domin za ku yi makoki kuna kuka nan gaba.
26Kaiton ku idan kowadanne mutane suna yabon ku! Domin haka kakannin-kakanninsu suka yi wa annabawan karya.
27Amma ina ce maku ku masu saurare na, ku kaunaci magabtanku, ku kuma aikata nagarta ga wadanda suke kinku. 28Ku albarkaci masu zaginku, ku kuma yi addu'a ga wadanda suke wulakanta ku.
29Wanda ya mare ku a wannan kunci, ku juya masa dayan. Idan wani ya dauki mayafinka, kada ka hana masa taguwarka. 30Ku bayar ga duk wanda ya roke ku. Idan wani ya dauki wani abu da ke naku, kada ku bidi ya mayar da shi.
31Duk abin da kake so mutane su yi maka, ka yi masu hakan nan. 32Idan ka kaunaci masoyan ka ne kadai, me wannan zai amfane ka? Ko masu zunubi ma na kaunar masoyan su. 33Idan kuna nuna alheri ga wadan da ke maku alheri kadai, menene ladan ku a nan? Ko masu zunubi ma na yin hakan nan. 34Idan kun ba da rancen abubuwa ga mutanen da kuna sa zuciya zasu mayar maku ne kadai, menene ribar ku a nan? Ko masu zunubi suna ba masu zunubi rance, suna kuma sa zuciya a mayar masu dadai gwargwado.
35Amma ku kaunaci magabtan ku, ku kuma nuna masu alheri. Ku basu rance, kada ku sa zuciya a maido maku, kuma sakamakon ku zai zama da girma. Za ku zama yayan Mafifici, domin shi da kansa yana nuna jinkai ga marasa godiya da miyagun mutane. 36Ku zama masu jinkai, domin Ubanku mai jinkai ne.
37Kada ku shari'anta, kuma ba za a shari'anta ku ba. Kada ku kayar, ku ma ba za a kashe ku ba. Ku yafe wa wasu, kuma za a yafe maku.
38Ku bayar ga wasu, ku ma za a ba ku da yawa. Magwaji dankararre, girgizajje har ya cika yana zuba, za su zuba har cinyarku. Domin duk ma'aunin da ku ka yi amfani da shi, da shi za a auna maku.
39Sai ya sake basu wani misali, "Makaho yana iya yi wa makaho jagora? Idan ya yi haka, dukansu biyu za su fada cikin rami, ko ba haka ba? 40Almajiri baya fin Malaminsa, amma duk wanda ya samu horo sosai zai zama kamar malaminsa.
41Don me kake duba dan hakin da ke a idon dan'uwanka, amma ba ka iya ganin gungumen da ke a idonka ba? 42Don me za ka ce wa dan'uwanka, 'Dan'uwa, bari in cire dan hakin da ke a idonka', bayan kai da kanka ba ka iya ganin gungumen da ke a idonka ba? Kai munafuki! Ka fara cire gungumen da ke a idonka, sa'annan za ka gani da kyau yadda zaka cire hakin da ke a idon dan'uwanka.
43Domin babu itace mai kyau da ke haifar rubabbun 'ya'ya, ko rubabben itace da zai haifi kyawawan 'ya'ya. 44Domin ana iya sanin ko wani itace ta wurin 'ya'yan da yake bayarwa. Domin mutane basu kan tsinki 'ya'yan baure a jikin kaya, ko kuwa su dibi inabi daga jikin sarkakkiya.
45Mutumin kirki, daga wadatar zuciyarsa ya kan ba da yaya masu kyau, kuma mugu daga cikin muguwar ajiyar zuciyarsa yake aikata mugunta. Domin daga cikar zuciyarsa ne bakinsa yakan yi magana.
46Don me kuke ce da ni, 'Ubangiji, Ubangiji', amma ba ku yin biyayya da magana ta? 47Duk wanda ya zo wurina ya ji kalmomina ya kuma yi biyayya da su, zan gaya maku yadda yake. 48Yana kama da mutum da ke gina gida, wanda ya haka da zurfi zuwa cikin kasa ya kuma gina harshashin gidan sa a kan dutse. Da rigyawa ta zo, sai ruwa ya buga gidan, amma bai iya girgiza shi ba, domin an gina shi da kyau.
49Amma duk mutumin da ya ji kalmomina ya kuma ki biyayya da su, yana kamar mutum wanda ya gina gidansa a kan kasa, babu harshashi. Amma da ambaliyan ruwa ta buga gidan, nan take ya rushe, ragargajewar gidan kuma da girma take.

7

1Bayan da Yesu ya gama fadar dukan abubuwan da zai fadi a jin kunnen dukan mutanen, sai ya shiga Kafarnahum.

2Bawan wani jarumi, wanda yake kauna, ba shi da lafiya har ma ya kusa mutuwa. 3Amma da ya ji labarin Yesu, jarumin ya aiki wadansu dattawan Yahudawa, ya ce a roki Yesu ya zo ya ceci bawansa daga mutuwa. 4Sa'adda su ka zo kusa da Yesu, su ka roke shi da gaske, cewa, "Wannan ya isa ka yi masa haka, 5saboda shi mai kaunar kasar mu ne, kuma shi ne ya gina mana majami'a.
6Sai Yesu ya tafi tare da su. Amma sa'adda ya zo kusa da gidan mutumin, jarumin ya aiki abokansa su ka ce da shi, "Ubangiji kada ka damu domin ni ban isa ka zo gida na ba. 7Shi ya sa na ga ban isa in zo wurinka ba, ka yi magana kadai bawa na kuwa zai warke. 8Gama ni ma mutum ne mai iko, ina da sojoji karkashina. Ina iya cewa da wannan, 'Ka je' sai ya tafi, in kuma ce da wani 'ka zo' sai ya zo, in kuma ce da bawa na, 'Yi kaza,' sai ya yi."
9Sa'adda Yesu ya ji haka, ya yi mamakin mutumin, ya juya wajen taron da su ke biye da shi, ya ce, "Na gaya maku, ko a cikin Isra'ila ban sami wani mai bangaskiya irin wannan ba" 10Daga nan wadanda a ka aika, suka dawo gida suka tarar da bawan cikin koshin lafiya.
11Wani lokaci bayan wannan, ya zama Yesu yana tafiya wani gari da ake kira Na'im. Almajiransa su na tare da shi, da kuma taron mutane masu yawa. 12Sa'adda ya kusa da kofar garin, sai ga wani matacce ana dauke da shi. Kuma shi kadai ne da a wurin mahaifiyarsa. Ita kuwa gwauruwa ce, mutane da dama daga cikin gari suna tare da ita. 13Da ganin ta, sai Ubangiji ya cika da tausayi a game da ita ya ce da ita, "Kada ki yi kuka." 14Sai ya zo ya taba makarar, sai masu dauke da shi su ka tsaya. Ya ce 'Saurayi na ce ma ka ka tashi." 15Sai mataccen ya tashi ya fara yin magana. Sai Yesu ya ba mahaifiyar danta.
16Sai tsoro ya kama su duka. Su ka kama yabon Allah, su na cewa, "An ta da wani annabi mai girma a cikinmu" kuma "Allah ya dubi mutanensa." 17Wannan labari na Yesu, ya ba zu a cikin dukan Yahudiya da yankuna da su ke kewaye.
18Almajiran Yahaya suka gaya masa dukan wadannan abubuwa. 19Sai Yahaya ya kira biyu daga cikin almajiransa, ya aike su wurin Ubangiji, suka ce da shi, "Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?" 20Sa'adda suka zo kusa da Yesu, sai mutanen suka ce, "Yahaya Mai Baftisma, ya aiko mu, mu tambaya, "Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?"
21A cikin wannan lokaci, ya warkar da mutane da yawa daga cututtuka da matsaloli da miyagun ruhohi. Makafi da yawa sun sami ganin gari. 22Yesu, ya amsa ya ce masu, "Bayan kun tafi, ku ba Yohanna rahoton abin da ku ka ji da abin da ku ka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana kuma tsarkake kutare. Kurame suna ji, ana tayar da matattu, ana gaya wa matalauta labari mai dadi. 23Mai albarka ne mutumin da ya tsaya a kan ba da gaskiya gare ni saboda ayukan da na ke yi."
24Bayan da mutanen da Yahaya ya aiko suka tafi, Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yahaya. "Me ku ka tafi ku gani a cikin hamada, ciyawa wadda iska ta ke girgizawa? 25Amma me ku ka tafi domin ku gani, mutum mai saye da tufafi masu taushi? Duba mutanen da su ke saye da tufafi masu daraja, kuma suna rayuwa cikin jin dadi suna fadar sarakuna. 26Amma me ku ka tafi domin ku gani, annabi ne? I, ina gaya ma ku, ya ma fi annabi.
27Wannan shine wanda aka rubuta a kansa, "Duba, ina aika manzo na a gabanka, wanda za ya shirya maka hanya a gabanka. 28Ina gaya maku, a cikin wadanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yahaya girma. Duk da haka, wanda ya fi kankanta a mulkin Allah, ya fi shi girma.
29Sa'anda dukan mutane suka ji haka, har da ma su karbar haraji, suka shaida Allah mai adalci ne. Su na cikin wadanda Yahaya ya yi wa baftisma. 30Amma Farisawa da wadanda su ke kwararru a cikin shari'ar Yahudawa, wadanda ba shi ne ya yi masu baftisma ba, suka yi watsi da hikimar Allah don kansu.
31Sa'annan Yesu ya ce, "Da me zan kamanta mutanen wannan zamani? Da me suka yi kama? 32Suna kama da yaran da suke wasa a kasuwa, wadanda suke magana da junansu suna cewa, "Mun yi maku busa, ba ku yi rawa ba. Mun yi makoki, ba ku yi kuka ba."
33Haka, Yahaya ya zo, bai ci gurasa ba, bai sha ruwan inabi ba, amma ku ka ce, 'Aljani ne yake mulkinsa. 34Dan Mutum, ya zo, yana ci, yana sha, amma, kuka ki shi, kuna cewa dubi mutum mai hadama, mai shan ruwan inabi da yawa, abokin masu karbar haraji da masu zunubi! 35Amma hikimar Allah tana shaidar dukan 'yayanta."
36Wata rana wani Bafarise, ya roki Yesu ya je ya ci abinci tare da shi. Bayan da Yesu ya shiga gidan Bafarisen, ya zauna a teburi domin ya ci abinci. 37Sai ga wata mace mai zunubi, ta fito daga cikin birni. Sa'anda ta ji labari Yesu yana gidan Bafarisen, domin ya ci abinci. Ta dauki tandun mai na alabastar mai kamshi. 38Ta tsaya kusa da Yesu tana kuka. Ta fara jika kafafunsa da hawayenta, tana shafe kafafunsa da gashin kanta. Tana yi wa kafafunsa sumba, tana shafe su da turare.
39Sa'anda Bafarisen da ya gaiyaci Yesu, ya ga haka, sai ya yi tunani a cikin ransa, da cewa, "In da wannan mutum annabi ne, da ya gane ko wacce irin mace ce, wannan da take taba shi, ita mai zunubi ce." 40Yesu ya amsa ya ce masa, "Siman, ina so in gaya maka wani abu." Ya ce, "malam sai ka fadi!"
41Yesu ya ce, "wani mutum mai ba da bashi yana bin wadansu mutane su biyu kudi, yana bin dayan sule dari, dayan kuma yana bin sa sule hamsin. 42Da yake ba su da kudin da za su iya biyan sa, sai ya yafe masu, su duka biyu. A cikin su biyu, wanne ne zai fi nuna kauna ga wannan mutum?" 43Siman ya amsa ya ce, "Ina tsammani wanda ya yafe wa kudi da yawa." Yesu ya amsa ya ce masa, "Ka shari'anta dai dai."
44Yesu ya juya wajen matar, ya ce da Siman, "Ka ga matan nan. Na shiga gidanka. Ba ka ba ni ruwa domin kafafuna ba, amma ita ta ba ni, da hawayenta ta wanke kafafuna, ta kuma shafe su da gashin kanta. 45Kai ba ka yi ma ni sumba ba, amma ita ta yi, tun sa'adda na shigo nan ba ta dena sumbatar kafafuna ba.
46Kai ba ka shafe kai na da mai ba, amma ita ta shafe kafafuna da turare. 47Saboda haka, ita wadda ta ke da zunubi da yawa ta bayar da mai yawa, ta kuma nuna kauna mai yawa. Amma shi wanda aka gafarta wa kadan, ya kuma nuna kauna kadan."
48Daga nan sai ya ce mata, "An gafarta zunubanki." 49Wadanda su ke a nan zaune tare da shi suka fara magana da junansu, "Wanene wannan wanda har yake gafarta zunubai? 50Sai Yesu ya ce da matar, "Bangaskiyarki ta cece ki. Ki tafi da salama."

8

1Bayan haka, Yesu da almajiransa goma sha biyu, su ka zagaya cikin birane da kauyuka dabam dabam, suna wa'azi da shelar labari mai dadi game da mulkin Allah, 2mata da yawa wadanda Yesu ya warkar daga aljanu da cututtuka iri iri suna tafiya tare da su. A cikinsu akwai Maryamu wadda a ke ce da ita Magadaliya, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta, 3da Yuwana matar Kuza wakilin Hirudus, da Suzanatu da kuma wasu mata da yawa. Daga abin hannunsu suka tanada masu.

4Wata rana aka tara taron mutane da yawa, saboda mutane su na zuwa daga birane da yawa domin su ga Yesu. Ya yi magana dasu cikin misali. 5"Wani mai shuka ya tafi domin ya shuka iri. Sa'adda ya ke yafa iri, wadansu iri suka fada a kan hanya. Sai mutane suka tattake su, tsuntsaye kuma suka tsince wadansu suka cinye. 6Wadansu kuma suka fada a kan duwatsu inda babu kasa da yawa. Da suka tsaro suka fara girma, sai nan da nan suka bushe saboda babu laima a wurin.
7Wadansu irin kuma suka fada inda yake da kayayuwa. Tsiretsiren kayayuwan suka fito tare da irin da aka shuka, suka shake su yadda basu iya yin girma ba. 8Amma wadansu irin suka fada a kan kasa mai kyau, suka yi girma sosai suka ba da anfani da yawa, har rubi dari." Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi kira gare su, "Duk mai kunnen ji, bari ya ji."
9Sai almajiran Yesu suka tambaye shi ya gaya ma su ma'anar labarin. 10ya ce da su, "Ku aka ba dama ku gane boyayyun abubuwa, na mulkin Allah. Amma ga sauran mutane ina yi masu magana cikin misalai, 'Domin ko da sun gani ba za su gane ba, kuma ko da sun ji ba za su fahimta ba."
11To ga ma'anar misalin. Irin shi ne maganar Allah. 12Irin da ya fada a kan hanya sune mutanen da suka ji maganar Allah amma daga baya sai shedan ya zo ya dauke maganar daga cikin hankulansu, domin kada su bada gaskiya su tsira. 13Sa'annan, wadanda suka fada kan duwatsu sune mutanen da, da zarar sun ji maganar, sukan karbe ta da murna, amma ba su da sauyu; su kan bada gaskiya na dan lokaci kadan kawai, da zaran gwaji ya same su sai su ridda.
14Irin da suka fada cikin kayayuwa, sune mutanen da suka ji maganar, amma da suka ci gaba da rayuwa, sai suka bari matsalolin rayuwa kamar dukiya da jin dadin rayuwa suka fi karfinsu, sai ya zama ba su iya bada 'ya'yan da suka yi girma ba. 15Amma irin da suka fada a kan kasa mai kyau, wadannan sune mutanen da suka ji maganar, suka karbe ta da gaskiya da zuciya daya, sun rike ta kam-kam, suna jimrewa wurin ba da 'ya'ya.
16Ba mai kunna fitila, ya rufe ta da kasko, ko su sa ta a karkashin gado. Amma sai a sa ta a wurin zaman ta domin duk wanda ya shigo ya iya ganin hasken ta.17Babu abin da yake a boye wanda ba za a tone shi ba, ko wani asiri da ba za ya fito fili a san shi ba. 18Ku yi hankali da yadda kuke ji, domin duk mai abu, shi za a kara wa, kuma duk mara abu, dan kadan da yake tunani yana da shi ma, za a dauke."
19Sai mahafiyar Yesu da 'yan'uwansa, su ka zo wurinsa, amma ba su iya zuwa ko kusa da shi ba saboda taron jama'a. 20Sai wani ya gaya masa, "Ga mahaifiyarka da 'yan'uwanka, su na tsayuwa a waje, su na son ganin ka." 21Amma Yesu ya amsa ya ce ma su, "Mahaifiyata da 'yan'uwana sune wadanda suke jin maganar Allah, suke yin biyayya da ita."
22Wata rana kuma Yesu ya shiga cikin jirgin ruwa, shi da almajiransa. Ya ce masu, "Ina so mu je dayan ketaren tafkin." Sai su ka fara tafiya domin su ketare tafkin. 23Amma sa'adda su ke tafiya sai Yesu ya yi barci, sai wata iska mai karfi ta taso cikin tafkin, nan da nan sai jirgin ya fara cika da ruwa, kuma su na cikin hatsari.
24Sai almajiran Yesu su ka zo su ka tashe shi daga barci. Suka ce da shi, "Ya Shugaba! Ya Shugaba! Za mu mutu!" Sai ya tashi ya umarci iskar, sai iskar mai hauka da tumbatsar ruwan sun tsaya tsit. 25Daga nan sai ya ce da su, "Ina bangaskiyar ku?" Almajiran suka tsorata suka yi mamakin abin da ya faru nan take. Suka ce wa junansu, "Wanene wannan wanda har zai ba iska da ruwa umarni kuma su yi masa biyayya?"
26Suka zo yankin Garasinawa, wanda ke kusa da Gallili. 27Sa'adda Yesu ya sauka kasa, sai wani mutum daga wannan yankin ya tarbe shi. Wannan mutum kuwa yana da aljanu. Mutumin ya dade ba ya sa tufafi, kuma ba ya zama a gida. Maimakon haka, sai a cikin kabarbura ya ke zama.
28Sa'adda ya ga Yesu, mutumin ya yi ihu da karfi, ya rusuna a gabansa da babban murya ya ce, "Me zan yi da kai, Yesu, Dan Allah Madaukaki? Ina rokonka, kada ka ba ni azaba!" 29Domin Yesu ya umarci aljanun su fita daga cikinsa, domin sau da dama aljanun sukan kama shi. Ko an daure mutumin da sarkoki an kuma tsare shi, yakan tsuttsunke su, kazaman ruhohin sukan kora shi cikin jeji.
30Sa'annan Yesu ya tambaye shi, "Yaya sunanka?" Sai ya ba da amsa, "Suna na dubbai." Ya ce haka ne domin aljanu da yawa sun shiga wannan mutum. 31Aljanun suka yi ta rokon Yesu kada ya ummarce su su shiga cikin rami mai zurfi.
32Akwai babban garken aladu su na kiwo a kan tsauni kusa da wurin. Aljanun suka roki Yesu da ya barsu su shiga cikin aladun, shi kuwa ya yarda masu. 33Aljanun suka bar mutumin suka shiga cikin aladun, sai garken aladun suka gangara kwari suka fada cikin tafkin, suka nutse.
34Lokacin da mutanen da su ke kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka gudu! Suka ba da rahoton abin da ya faru ga mutanen cikin gari da na wannan kewayen. 35Don haka, mutanen da suka ji haka suka tafi domin su ga abin da ya faru, suka zo wurin da Yesu yake, suka ga mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa. Suka ga ya na sanye da tufafi, kuma ya na cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36Mutanen da suka ga abin da ya faru, suka gaya wa wadansu yadda aka warkar da mutumin da aljanu suke iko da shi. 37Sai dukan mutane wadanda suke cikin yankin Garasinawa da wadanda suke kewaye, suka roki Yesu da ya fita daga cikin yankin kasarsu domin sun ji tsoro kwarai da gaske. Daga nan Yesu da almajiransa suka shiga cikin jirgin ruwa suka koma.
38Mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa, ya roki Yesu cewa, "Ka barni in tafi tare da kai!" Amma Yesu ya sallame shi cewa, 39"Ka koma gida ka gaya wa mutanen ka abubuwa masu girma wadanda Allah ya yi maka." Daga nan sai mutumin ya tafi yana ta gayawa dukan mutanen birnin game da abubuwan da Yesu ya yi masa.
40Sa'adda Yesu ya dawo, mutanen suka marabce shi, gama, dukansu suna jiransa. 41Sai ga wani mutum mai suna Yayirus, daya daga cikin shugabannin majami'a, ya zo kusa da Yesu ya rusuna da kansa a kasa. Ya roke shi domin ya zo gidansa, 42saboda diyarsa mai kimanin shekara goma sha biyu ta na bakin mutuwa, kuma ita kadai ce diya a gare shi. Amma sa'adda yake tafiya, taron mutane da yawa suna matsa shi.
43Akwai wata mace a nan wadda take zubar jini har shekara goma sha biyu. Ta kashe kudinta duka a wurin likitoci, domin su warkar da ita amma ba wanda ya iya warkar da ita. 44Sai ta biyo ta bayan Yesu ta taba habar rigarsa. Nan take sai zubar jinin ya tsaya.
45Yesu ya ce, "Wanene ya taba ni?" Wadanda suke kewaye da shi, kowa ya ce bai taba shi ba, Bitrus ya ce, "Shugaba, mutane da yawa suna ta taruwa kewaye da kai suna ta matsowa kusa da kai." 46Amma Yesu ya ce, "Na sani, wani ya taba ni, domin iko ya fita daga wurina."
47Sa'adda matar ta gane cewa ba za ta iya boyewa ba, sai ta zo wurinsa cikin tsoro. Ta durkusa a gaban Yesu, ta fada a gaban dukan jama'a dalilin da ya sa ta taba shi kuma nan da nan ta warke. 48Sai ya ce da ita, "Diya, bangaskiyarki ta warkar da ke. Tafi cikin salama."
49Yana cikin yin magana, wani daga cikin gidan shugaban majami'ar ya zo, ya ce, "Diyarka ta riga ta mutu, kada ka dami malam." 50Amma sa'adda Yesu ya ji haka, sai ya ce da shi, "Kada ka ji tsoro. Ka bada gaskiya za ta rayu."
51Sa'adda ya zo gidan, bai bar kowa ya shiga gidan tare da shi ba sai Bitrus da Yahaya da Yakubu, da mahaifiyar yarinyar da babanta. 52Dukan mutane a wurin, suna ta kuka da karfi saboda sun damu da yarinyar ta mutu. Amma Yesu ya ce da su, "Ku dena kuka! Ba mutuwa ta yi ba! Barci ta ke yi kawai!" 53Mutanen suka yi ma sa dariyan reni, saboda sun sani yarinyar ta mutu.
54Amma ya kama hannun ta yayi kira cewa, "Yarinya, na ce ki tashi!" 55Nan da nan ruhun ta ya dawo jikin ta sai ta tashi. Ya ce masu su ba ta wani abu ta ci. 56Iyayenta suka yi mamaki, amma Yesu ya ce da iyayen kada su gaya wa kowa abin da ya faru.

9

1Ya kira almajiransa goma sha biyu, ya ba su iko su fitar da kowanne irin aljani, su kuma warkar da cututtuka daga mutane. 2Ya aike su, su yi wa'azin mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.

3Ya ce masu, "Kada ku dauki komi tare da ku domin wannan tafiya. Kada ku dauki sanda, ko jakar matafiyi, ko gurasa, ko kudi - Kada ma ku dauki taguwa biyu. 4Dukan gidan da ku ka shiga, ku zauna a gidan har zuwa lokacin da za ku tafi daga wannan yankin.
5Dukan wadanda ba su marabce ku ba, sa'adda ku ke barin wannan gari, ku karkabe kurar kafufunku a matsayin shaida a kansu." 6Daga nan sai almajiran suka tafi zuwa cikin kauyuka, suka yi ta shelar bishara, su na warkar da mutane a ko'ina.
7Ana nan Hirudus, mai mulki, ya ji labarin dukan abubuwan da su ke faruwa. Ya yi mamaki saboda wadansu mutane suna cewa Yahaya mai yin Baftisma ne ya sake dawowa da ransa. 8Wadansu kuma suna cewa, annabi Iliya ne ya sake bayyana, wadansu kuma suna cewa daya daga cikin annabawa na da can ne ya sake bayyana da rai. 9Hirudus ya ce, "Ba zai yiwu Yahaya ne ba, domin na datse masa kai. To, wanene wannan da ni ke jin wadannan abubuwa a kansa?" Daga nan sai ya cigaba da neman hanyar da zai ga Yesu.
10Sa'adda manzannin suka dawo daga tafiyarsu, suka gaya wa Yesu dukan abubuwan da suka yi. Daga nan sai ya dauke su domin su tafi tare da shi zuwa garin Baitsaida. 11Amma sa'adda taron suka ji inda Yesu ya tafi, sai suka bi shi can. Ya marabce su ya yi masu jawabi a kan mulkin Allah, kuma ya warkar da wadanda su ke bukatar warkarwa.
12Da yake yamma ta fara yi, sai almajiransa goma sha biyu suka zo suka ce da shi, "Idan ka yarda ka sallami wannan babban taron mutane dominsu shiga cikin kauyuka, da ke kewaye da gonaki, dominsu sami abinci da wuraren da za su kwana, da yake mu na nan a wurin da ba kowa." 13Amma sai ya ce da su, "Ku ba su abin da za su ci." Suka amsa masa, "Dukan abin da muke da shi shine, 'Yan dunkulen gurasa biyar da 'yan kifaye guda biyu, ba za mu iya zuwa mu sawo abincin da zai ishi mutanen nan su duka ba." 14Mutanen da suke wurin sun kai kimanin mazaje dubu biyar. Sai Yesu ya ce da almajiran, "Ku ce da mutanen su zauna kungiya-kungiya, mutane hamsin a kowacce kungiya."
15Sai almajiran suka yi haka, dukan mutanen suka zauna. 16Ya dauki dunkulen gurasan guda biyar, da kifin guda biyu, yana dubawa zuwa sama ya albakarce su, sa'annan ya gutsuttsura, ya ba almajiran domin su rarraba wa mutane. 17Dukansu suka ci kowa ya koshi. Daga nan almajiran suka tattara sauran abin da ya rage, har kwanduna goma sha biyu suka cika!
18Wata rana Yesu yana yin addu'a shi kadai, sai almajiransa suka zo sai ya tambaye su, "Wa mutane suke cewa da ni?" 19Suka amsa, "Wadansu suna cewa, Yahaya mai yin Baftisma, wadansu suna cewa kai annabi Iliya ne, har yanzu wadansu suna cewa kai wani cikin annabawa na da can ne ya dawo da rai."
20Ya tambaye su, "Ku fa? Wa kuke cewa da ni?" Bitrus ya amsa, "Kai Almasihu ne wanda ya zo daga wurin Allah." 21Sai Yesu ya gargade su da karfi, kada su gayawa kowa haka tukuna. 22Sa'annan ya ce, "Dan Mutum dole ya sha wahalar abubuwa da yawa; dattawa za su ki shi da manyan fristoci da marubuta, sa'annan za a kashe shi. Bayan kwana uku, za a tashe shi da rai."
23Sai ya ce da su duka, "Dukan wanda ya ke so ya biyo ni, dole ne ya yi musun kansa, ya dauki gicciyen sa kulluyomin, ya biyo ni. 24Dukan wanda yake so ya ceci ransa, za ya rasa shi, amma dukan wanda ya ba da ransa domina, za ya cece shi. 25Wacce riba mutum zai samu idan ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa?
26Dukan wanda yake jin kunya ta da magana ta, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa, sa'adda ya dawo cikin darajarsa da darajar Uba da ta mala'iku masu tsarki. 27Amma ina gaya maku wannan tabbas, wadansu cikinku da ke nan tsaye, ba za su mutu ba sai sun ga mulkin Allah."
28Kwana takwas bayan Yesu ya fadi wadannan kalmomi, sai ya dauki Bitrus da Yahaya da Yakubu, ya hau kan dutse domin ya yi addu'a a can. 29Sa'anda ya ke yin addu'a sai yanayin fuskar sa ya canza sosai, tufafinsa kuma suka yi sheki da haske kamar walkiya.
30Nan da nan sai ga mutane biyu suna magana da shi, wato Musa da Iliya. 31Suka bayyana da daraja kewaye da su, suka yi magana da Yesu a kan tafiyarsa wadda za ta zo ba da dadewa ba a cikin Urushalima.
32Bitrus da almajiran da suke tare da shi barci mai nauyi ya dauke su. Sa'adda suka farka sai su suka ga daukakar Yesu; kuma suka ga mutanen su biyu da ke tsaye tare da shi. 33Sa'adda Musa da Iliya suke shirin su bar wurin Yesu, sai Bitrus ya ce, "Ya shugaba, ya yi kyau da muke a nan. Zai yi kyau mu yi runfuna uku, daya dominka, daya domin Musa, daya kuma domin Iliya." Amma hakika bai san abin da ya ke fadi ba.
34Sa'adda yake fadin haka sai wani girgije ya zo ya rufe su. Sai suka ji tsoro sa'adda girgijen ya kewaye su. 35Sai ga wata murya daga cikin girgijen tana cewa, "Wannan Dana ne wanda na zaba, ku ji shi." 36Sa'adda muryar ta gama magana, Yesu yana nan shi kadai. Suka yi shiru ba su iya cewa kome ba a kan abin da suka gani a kwanakin nan.
37Washe gari, da suka sauko daga kan dutsen, sai taron mutane da yawa suka zo wurinsa. 38Nan da nan, wani mutum daga cikin taron mutanen ya yi magana da karfi, "Mallam, kayi wani abu dominka taimaki da na, shi kadai ne gare ni. 39Mugun ruhu ya kan hau kansa, ya sa shi ya yi ta magowa. Ya kan girjiza shi da karfi ya sa bakinsa ya yi ta kumfa. Da kyar ya ke rabuwa da shi, kuma ya kan ji masa ciwo ba kadan ba bayan da ya bar shi. 40Na roki almajiran ka su umurci mugun ruhun ya fita daga cikinsa, amma ba su iya ba!"
41Yesu, ya amsa, ya ce, "Ku karkatattun tsara marasa bangaskiya, har yaushe zan zauna da ku ina jimrewa da ku? "Kawo yaronka anan." 42Sa'adda yaron yake zuwa, sai mugun ruhun ya fyada yaron a kasa, ya jijjiga shi sosai. Amma Yesu ya tsauta wa mugun ruhun, ya warkar da yaron. Sa'annan ya mika yaron wurin mahaifinsa.
43Dukansu suka yi mamaki da girman ikon Allah. Amma sa'anda suke ta yin mamaki a kan dukan al'ajiban da ya yi, ya ce da almajiransa, 44"Ku saurara da kyau a kan abin da zan gaya maku, ba da dadewa ba za a bada Dan Mutum ga mutane." 45Amma almajiran ba su gane abin da yake nufi da haka ba, an hana su fahimta, domin kada su gane abin da ya ke nufi tukuna, kuma suna jin tsoron su tambaye shi.
46Wani lokaci, almajiran suka fara gardama a tsakaninsu game da wanene za ya zama mafi girma a cikinsu. 47Amma Yesu ya san abin da suke tunani a zuciyarsu, sai ya kawo dan karamin yaro ya tsaya a kusa da shi, 48sai ya ce da su, "Idan wani ya karbi dan karamin yaro kamar wannan saboda ni, dai dai yake da ya karbe ni. Idan kuma wani ya karbe ni, ya karbi wanda ya aiko ni kenan. Wanda yake mafi kankanta a cikinku, shi ne mafi mahimmanci."
49Yahaya ya amsa yace, "Ya shugaba, mun ga wani mutum yana ba miyagun ruhohi umarni su fita daga cikin mutane da sunanka. Sai muka ce da shi ya dena yin haka saboda baya tare da mu." 50Amma Yesu ya ce, "Kada ku hana shi yin haka, domin dukan wanda ba ya gaba da ku, yana tare da ku."
51Sa'adda rana ta kusato da zai hawo zuwa sama, ya kudurta sosai zai tafi Urushalima. 52Ya aiki wadansu manzanni su shirya wuri dominsa kafin ya zo. Suka shiga wani kauye a cikin kauyen Samariya domin su shirya masa wuri a can. 53Amma mutanen can ba su karbe shi ba tun da ya ke Urushalima zai tafi.
54Sa'adda biyu daga cikin almajiransa, wato Yakubu da Yahaya suka ga haka, suka ce, "Ubangiji, kana so mu umarci wuta ta sauko daga sama, ta hallaka su?" 55Amma, ya juya ya tsauta masu. 56Sai suka tafi wani kauye dabam.
57Da suna cikin tafiya a kan hanya, sai wani mutum ya ce da shi, "Zan bi ka dukan inda za ka tafi." 58Yesu ya amsa masa, "Dila suna da ramuka a kasa inda za su shiga, tsuntsaye kuma suna da sheka, amma Dan Mutum ba shi da inda zai kwanta."
59Yesu, ya ce da wani mutumin kuma, "Ka biyo ni." Amma mutumin ya ce, "Ubangiji, ka bari in koma gida in bizine mahaifina tukuna." 60Amma Yesu ya ce masa, "Ka bar matattu su bizine matattunsu; amma kai ka tafi ka yi wa mutane shelar mulkin Allah a ko'ina."
61Wani kuma ya ce, "Ubangiji zan tafi tare da kai, amma bari in je gida inyi ban kwana da mutanena tukuna." 62Yesu ya ce da shi, "Dukan wanda ya fara huda a gonarsa idan ya dubi baya, bai isa ya shiga mulkin Allah ba."

10

1Bayan wadannan abubuwa, Ubangiji ya sake nada wadansu saba'in ya aike su biyu biyu, domin su tafi kowanne birni da wurin da yake niyyan zuwa. 2Ya ce da su, "Girbin yana da yawa, amma ma'aikatan sun yi kadan. Saboda haka kuyi addu'a sosai ga Ubangijin girbin, domin ya aiko da ma'aikata cikin gonarsa.

3Ku tafi, duba na aike ku kamar 'yan raguna cikin kyarkyetai. 4Kada ku dauki jakan kudi, ko jakar matafiyi, ko takalma, kada ku gai da kowa a kan hanya.
5Dukan gidan da ku ka shiga, ku fara cewa, 'Bari salama ta kasance a wannan gida.' 6Idan akwai mutum mai salama a gidan, salamar ku za ta kasance a kansa, amma idan babu, salamar ku za ta dawo wurinku. 7Ku zauna a wannan gidan, ku ci ku sha abin da suka tanada maku. Gama ma'aikaci ya wajibci ladansa. Kada ku bi gida gida.
8Dukan birnin da ku ka shiga kuma sun karbe ku, ku ci abin da suka sa a gabanku. 9Ku warkar da marasa lafiyar da ke wurin. Ku ce da su, 'Mulkin Allah ya zo kusa da ku.'
10Amma dukan birnin da ku ka shiga, idan ba su karbe ku ba, ku tafi cikin titunansu, ku ce, 11'Ko kurar birninku da ta like a kafafunmu, mun karkabe maku ita a matsayin shaida a kanku! Amma ku sani mulkin Allah ya zo kusa da ku.' 12Na gaya maku, a ranar shari'a Saduma za ta fi wannan birni samun sauki.
13Kaiton ki, Korasinu! Kaiton ki, Baitsaida! Ayyuka masu girma da aka yi a cikinku, da an yi su a cikin Taya da Sidon, da sun tuba tuntuni a zaune cikin toka da tufafin makoki. 14Amma a ranar shari'a Taya da Sidon za su fi ku samun sauki. 15Ke kuma Kafarnahum, kina tsammani har zuwa sama za a daukaka ki? Babu, za a gangarar dake har zuwa hadas.
16Wanda ya saurare ku ya saurare ni, wanda ya ki ku, ya ki ni, kuma wanda ya ki ni, ya ki wanda ya aiko ni."
17Su saba'in din suka dawo da murna, suna cewa, "Ubangiji, har ma aljanu suna yi mana biyayya, a cikin sunanka." 18Sai Yesu ya ce masu, "Na ga Shaidan yana fadowa daga sama kamar walkiya. 19Duba, na ba ku iko ku taka macizai da kunamai, da kuma kan dukan ikon magabci, kuma ba zai iya yin illa a gareku ba ko kadan. 20Amma duk da haka kada ku yi murna a kan wannan kadai cewa ruhohi suna yi maku biyayya, amma ku yi murna domin an rubuta sunayenku a cikin sama."
21Cikin wannan lokacin, ya yi farin ciki kwarai cikin Ruhu Mai Tsarki, ya ce, "Na ba ka girma, ya Uba, Ubangijin sama da kasa. Domin ka rufe wadannan abubuwa daga masu hikima da ganewa, ka bayyana su ga wadanda ba koyayyu ba ne, kamar kananan yara. I, Uba gama haka ne ya gamshe ka."
22Dukan abu, Ubana ya damka su gare ni, kuma babu wanda ya san Dan, sai Uban, kuma ba wanda ya san Uban, sai Dan. Sai kuma wanda Dan ya yi niyyar ya bayyana Uban a gareshi."
23Ya juya wajen almajiran, ya ce da su a kadaice, "Masu albarka ne su wadanda suka ga abin da kuke gani. 24Na fada maku, annabawa da yawa, da sarakuna da yawa sun so da sun ga abubuwan da kuke gani, amma ba su gani ba. Kuma sun so da sun ji abubuwan da kuke ji, amma ba su ji su ba."
25Sai ga wani malamin shari'ar Yahudawa, ya zo ya gwada shi da cewa, "Malam, me zan yi domin in gaji rai na har abada?" 26Sai Yesu ya ce masa, "Yaya kake karanta abin da aka rubuta cikin shari'a?" 27Ya amsa ya ce,"Dole ne ka kaunaci Ubangiji Allah da dukan zuciyarka, da dukan ranka da dukan karfinka, da dukan lamirinka. Ka kuma kaunaci makwabcinka kamar kanka." 28Yesu ya ce ma sa, "Ka amsa daidai, idan ka yi haka za ka rayu."
29Amma, malamin ya na so ya 'yantar da kansa, sai ya ce da Yesu, "To, wanene makwabcina?" 30Ya amsa ya ce, "Wani mutum yana tafiya daga Urushalima za shi Yariko. Sai ya fada hannun mafasa, suka tube shi, suka kwace dukan abin da ya ke da shi, suka yi masa duka, suka bar shi kamar matacce.
31Ya zama sai ga wani firist ya na bin wannan hanya, da ya gan shi sai ya bi ta gefe daya ya wuce. 32Haka kuma sai ga wani Balawi, sa'adda ya zo wurin, ya gan shi sai ya bi ta wani gefe ya wuce shi.
33Amma wani Basamariye, ya na tafiya sa'adda ya zo wurin da mutumin yake, sa'adda ya ga mutumin sai tausayi ya kama shi. 34Ya zo inda mutumin yake, ya daure masa raunukan da aka ji masa, yana shafa masu mai da ruwan inabi. Ya dora shi a kan dabbarsa ya kawo shi wurin kwana, ya kula da shi 35Washegari ya kawo dinari biyu, ya ba mai wurin kwanan ya ce 'Ka kula da shi, idan ma ka kashe fiye da haka, idan na dawo zan biya ka.'
36A cikinsu ukun nan, wanene kake tsammani makwabcin wannan mutum da ya fada hannun 'yan fashi?" 37Sai malamin ya ce, "Wannan da ya nuna masa jinkai" Sai Yesu yace masa, "Ka je kai ma ka yi haka."
38Sa'adda suke tafiya, sai ya shiga cikin wani kauye, sai wata mata mai suna Marta ta marabce shi a gidanta. 39Tana da 'yar'uwa mai suna Maryamu, wadda ta zauna a kafafun Ubangiji tana jin abin da yake fadi.
40Amma ita Marta ta na ta kokari ta shirya abinci. Sai ta zo wurin Yesu ta ce, "Ubangiji, ba ka damu ba 'yar'uwata ta bar ni ina ta yin aiki ni kadai? Ka ce da ita ta taya ni." 41Amma Ubangiji ya amsa ya ce da ita, "Marta, Marta, kin damu a kan abubuwa da yawa, 42amma abu daya ne ya zama dole. Maryamu ta zabi abu mafi kyau, wanda ba za a iya kwace mata ba."

11

1Wani lokaci, Yesu yana yin addu'a a wani wuri, sai daya daga cikin almajiransa yace da shi, "Ubangiji, ka koya mana yin addu'a kamar yadda Yahaya ya koya wa almajiransa."

2Yesu ya ce ma su, "Sa'anda ku ke yin addu'a ku ce, 'Uba a tsarkake sunanka. Mulkin ka ya zo.
3Ka ba mu abin da za mu ci a kowacce rana. 4Gafarta mana zunubanmu, kamar yadda muke gafarta ma wadanda suke mana laifi. Kada ka kai mu cikin jaraba.'"
5Yesu ya ce masu, "Wanene a cikinku idan yana da aboki, za ya je wurinsa da tsakar dare ya ce masa, "Aboki, ka ba ni rancen dunkulen gurasa guda uku, 6da ya ke wani abokina ya iso yanzu daga tafiya, kuma ba ni da abin da zan ba shi ya ci,' 7Sai wanda yake ciki, ya amsa, ya ce, 'Kada ka dame ni. Na riga na rufe kofa ta, kuma ni da yarana mun riga mun kwanta. Ba zan iya tashi in ba ka gurasa ba.' 8Na fada maku, ko da bai tashi ya ba ka gurasar ba, a matsayin abokinsa, ba ka ji kunya ba, ka nace da rokonsa, za ya tashi ya ba ka dukan yawan gurasar da kake bukata.
9Ni kuma ina ce maku, ku roka za a ba ku; ku nema za ku samu; ku kwankwasa za a bude maku. 10Domin dukan wanda yake roko ya na karba; dukan wanda ya ke nema kuma yana samu; kuma wanda yake kwankwasawa, za a bude masa.
11Wanne uba ne a cikinku, idan dansa ya tambaye shi kifi, zai ba shi maciji a maimakon kifi? 12Ko kuwa idan ya tambaye shi kwai, za ya ba shi kunama? 13To, da yake ku da kuke masu mugunta kun san ku ba 'yanyan ku abu mai kyau. Yaya fa ga Ubanku wanda yake cikin sama, za ya ba da Ruhu Mai Tsarki ga wadanda suka roke shi?"
14Wani lokaci, Yesu yana fitar da wani beben aljani. Sa'adda aljanin ya fita, sai mutumin da yake bebe ya yi magana. Sai taron mutanen suka yi mamaki! 15Amma, wadansu daga cikin mutanen suka ce, "Da ikon Ba'alzabuba sarkin aljanu ne yake fitar da aljanu."
16Wadansu suka gwada shi, suka nemi ya nuna masu wata alama daga sama. 17Amma Yesu da yake ya san tunaninsu, ya ce da su, "Dukan mulkin da ya rabu biyu, gaba da kansa, ya rushe kenan, kuma idan gida ya rabu biyu, gaba da kansa za ya fadi.
18Idan Shaidan ya rabu biyu gaba da kansa, ta yaya mulkinsa zai iya tsayawa? Gama kun ce ina fitar da aljanu ta wurin Ba'alzabuba. 19Idan ni na fitar da aljanu ta wurin Ba'alzabuba, ta wurin wa wadanda suke bin ku suke fitar da aljanu? Saboda haka, su ne zasu zama masu yi maku shari'a. 20Amma idan daga wurin Allah na ke fitar da aljanu, to, ya zama ke nan mulkin Allah ya zo wurinku.
21Idan mutum mai karfi, mai kayan fada ya tsare gidansa, kayansa za su tsira. 22Amma idan wani mutum wanda ya fi shi karfi ya zo ya ci nasara a kansa, zai dauke kayan fadan daga wurin mutumin, kuma ya kwashe kayansa. 23Wanda ba ya tare da ni, gaba da ni ya ke yi, kuma wanda ba ya tattarawa tare da ni, watsarwa yake yi.
24Idan kazamin ruhu ya fita daga cikin mutum, ya kan bi ta wurin busassun wurare yana neman wurin da zai huta. Idan bai samu ba sai ya ce, 'Bari in koma gidana inda na baro. 25Sa'adda ya dawo, ya tarar an share gidan, an kuma gyara shi tsaf. 26Sai ya je ya dauko wadansu aljanu guda bakwai wadanda su ka fi shi mugunta, su zo su zauna a wurin. Sai karshen mutumin nan ya fi farkonsa muni."
27Ya zama, lokacin da ya ke fadin wadannan abubuwa, wata mace ta tada muryarta a cikin taron mutanen ta ce da shi, "Mai albarka ne cikin da ya haife ka, da maman da ka sha." 28Sai shi kuma ya ce, "Masu albarka ne wadanda suke jin maganar Allah suke yin biyayya da ita."
29Lokacin da mutane suke kara taruwa, sai ya fara cewa, "Wannan tsara, muguwar tsara ce. Ta na neman alama, Ko da yake ba wata alamar da za a bata sai irin ta Yunusa. 30Domin kamar yadda Yunusa ya zama alama ga mutanen Neneba, haka kuma Dan Mutum za ya zama alama ga wannan tsara.
31Sarauniyar Kudu, za ta tsaya ta yi shari'a da mutanen wannan tsara, kuma za ta kashe su, gama ta zo daga wuri mai nisa domin ta saurari hikimar Sulaimanu. Kuma ga wani wanda ya fi Sulaimanu a nan.
32Mutanen Neneba, za su tsaya shari'a da matanen wannan tsara, kuma za su kashe su. Gama sun ji wa'azin Yunusa sun tuba. Kuma ga wani wanda ya fi Yunusa a nan.
33Ba wanda zai kunna fitila ya boye ta, ko kuwa ya sa ta a karkashin kasko, amma zai sa ta a mazaunin ta domin dukan wanda ya shiga dakin ya ga haske. 34Idon ku shine fitilar jikinku. Idan idonku yana gani sosai, jikinku zai cika da haske. Amma idan idonku ba ya gani sosai, jikinku zai cika da duhu. 35Ku yi hankali fa, domin kada hasken da ya ke wurinku ya zama duhu. 36Idan dukan jikinku yana cike da haske, babu duhu ko kadan, to sai dukan jikinku ya zama kamar fitilar da take bada haskenta a bisanku."
37Sa'adda ya gama jawabi, sai wani Bafarise ya ce da shi ya zo gidansa ya ci abinci, sai Yesu ya shiga ya zauna. 38Sai Bafarisen ya yi mamaki da ganin bai wanke hannu kafin ya ci abinci ba.
39Amma sai Ubangiji ya ce da shi, "Ku Farisawa kuna tsabtace bayan kofi da bangaji, amma cikin yana cike da kazamta da mugunta. 40Ku mutane marasa tunani, wanda ya yi wajen, ba shine ya yi cikin ba? 41Ku bayar da abin da ke ciki ga matalauta, kuma dukan abu zai zamar maku da tsafta.
42Amma kaitonku Farisawa, gama kuna karbar zakka da daddoya da karkashi da kowanne irin ganye na lambu, amma kun watsar da adalci da kaunar Allah. Dole ne a yi adalci, a kaunaci Allah, a yi sauran abubuwan kuma.
43Kaitonku Farisawa, domin kuna so a ba ku wuraren zama masu kyau a cikin masujadai, a kuma yi maku gaisuwar bangirma a cikin kasuwanni. 44Kaiton ku, gama kuna kama da kabarbarun da ba yi masu shaida ba, mutane kuwa suna tafiya akansu ba tare da saninsu ba."
45Wani malami a cikin shari'ar Yahudawa ya amsa masa ya ce, "Malam, abin da ka ce ya bata mana rai mu ma." 46Sai Yesu ya ce, "Kaitonku malaman shari'a! Gama kun dora wa mutane kaya mai nauyi wanda ya fi karfinsu dauka. Amma ku, ko da dan yatsa ba ku taba kayan ba.
47Kaiton ku, gama kuna gina abubuwan tunawa a kabuburan annabawa, alhali kuwa kakanni-kakanninku ne suka kashe su. 48Ya zama kenan kuna sane da ayyukan kakanni-kakanninku, domin sune suka kashe annabawan da kuke tunawa da su.
49Saboda wannan daliline hikimar Allah ta ce, "Zan aika manzanni da annabawa a wurinsu, kuma za su tsananta masu har ma za su kashe wadansu daga cikinsu.' 50Wannan tsarar, za ta dauki alhakin jinin dukan annabawan da aka kashe tun kafuwar duniya. 51Tun daga jinin Habila, har zuwa jinin Zakariya wanda aka kashe tsakanin bagadi da wuri mai tsarki. I, na gaya ma ku za a nemi hakin su a wurin wannan tsarar
52Kaitonku malaman shari'a na Yahudawa, domin kun dauke mabudin sani, ku da kanku ba ku shiga ba, kuma kun hana masu shiga su shiga."
53Bayan da Yesu ya bar nan wurin, Marubuta da Farisawa suka yi gaba da shi, suka yi jayayya da shi a kan abubuwa da yawa, 54suna kokari su kafa masa tarko domin su kama shi a cikin kalmomin da yake fadi.

12

1Da jimawa kadan, bayan da mutane da yawa suka taru kwarai har suna tattaka junansu. Sai ya fara yin magana da almajiransa. "Ku yi lura da yisti na Farisawa, wanda shine manufunci.

2Amma ba abin da ke rufe wanda ba za a tone ba, ba kuma abin da ke boye wanda ba za a sani ba. 3Saboda haka ba abin da za ku fadi a asirce wanda ba za a ji shi a cikin sarari ba. Abin da ku ka fadi da rada cikin lungu, za a yi shelarsa a ko'ina.
4Ina gaya maku abokaina, kada ku ji tsoron wanda da za su kashe jiki. Bayan haka kuma ba abin da za su iya yi. 5Bari in gargade ku a kan wanda za ku ji tsoronsa. Ku ji tsoron shi wanda bayan ya kashe zai iya jefa ku cikin jahannama. I, ina ce maku ku ji tsoronsa.
6Ba a kan sayar da 'yan tsuntsaye biyar a kan anini biyu ba? Duk da haka, Allah ba zai manta da ko daya daga cikinsu ba. 7Har ma gashin da ke kan ku ya san yawan su. Kada ku ji tsoro, ku kun fi tsuntsaye daraja a wurinsa.
8Ina gaya maku, dukan wanda za ya shaida ni a gaban mutane, Dan Mutum kuma za ya shaida shi a gaban mala'kun Allah. 9Kuma dukan wanda ya ki ni a gaban mutane, za a ki shi a gaban mala'ikun Allah. 10Dukan wanda ya yi magana gaba da Dan Mutum, za a gafarta masa. Amma shi wanda ya yi sabon Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba.
11Idan suka kawo ku gaban majami'a, ko gaban masu shari'a, ko gaban masu iko, kada ku damu da abin da za ku fada domin ku kare kanku. Ko kuwa abin da za ku ce. 12Gama Ruhu Mai Tsarki zai koya maku abin da za ku fadi a wannan lokaci."
13Sai wani a cikin taron ya ce masa, "Malam, ka yi wa dan'uwana magana ya raba gado da ni 14Yesu ya ce masa, "Kai, wanene ya sa ni in zama alkali, ko matsakanci a kanku?" 15Sai kuma ya ce masu, "Ku yi lura kada ku zama masu hadama, gama ba abin da mutum ya mallaka ne ya fi mahimmanci a cikin rayuwar sa ba."
16Sa'annan Yesu ya fada masu wani misali, ya ce, "Gonar wani mutum ta bada amfani sosai, 17ya yi tunani, ya ce, 'Me zan yi, domin ba ni da wurin da zan iya ajjiye amfanin gonata?' 18Sai ya ce, na san abin da zan yi. Zan rushe rumbuna na in gina wadansu manya-manya, a nan zan ajjiye hatsi na da dukan abubuwa. 19Sai in ce da raina, "Ya raina, kana da abu da yawa da aka ajjiye dominka, sai ka huta, ka ci, ka sha, ka yi murna."
20Amma sai Allah ya ce da shi, 'Wawan mutum, a cikin daren nan ana son ranka daga wurinka. Kayan da ka tara ka shirya wa kanka, na wa za su zama?' 21Haka wanda ya tara wa kansa dukiya yake, idan ba shi da dukiya a wurin Allah."
22Yesu, ya ce da almajiransa, "Saboda haka ina cewa da ku, kada ku damu da rayuwarku, wato, abin da za ku ci, ko abin da za ku sa a jikinku. 23Gama rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi.
24Ku dubi hankaki wadanda ba sa yin shuka, ba sa yin girbi. Ba su da rumbuna ko dakunan ajjiya, amma Allah ya na ciyar da su. Ku fa kun fi tsuntsaye daraja! 25Wanene a cikinku ta wurin sha'awarsa za ya iya karawa kansa kwanaki? 26Idan ba ku iya yi wa kanku dan karamin abu ba, me ya sa za ku damu da sauran abubuwa?
27Ku dubi furanni a daji - yadda suke yin girma. Ba su kan yi aiki ba, ba su kan yi kadi ba. Ina gaya maku, ko Sulaimanu, a cikin darajarsa, bai sa tufafin da suka fi nasu kyau ba. 28Idan Allah ya sa wa ciyawa tufafi masu kyau haka, wadda yau tana nan, gobe kuma a sa ta a wuta, ta yaya zai kasa sa maku tufafi, ku masu kankantar bangaskiya!
29Kada ku damu da abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kuma kada ku yi alhini. 30Gama dukan al'umman duniya suna neman wadannan abubuwa, kuma Ubanku ya san kuna bukatar wada nan abubuwan.
31Amma ku bidi mulkinsa, wadannan abubuwa kuma za a kara maku su. 32Kada ku ji tsoro, ku 'yan kanana, domin da murna Ubanku zai ba ku mulkin.
33Ku sayar da abin da ku ke da shi ku ba matalauta. Kuyi wa kanku jakukkuna wadanda ba za su lalace ba, ku yi ajjiya cikin sama inda abin ba ya karewa, inda barayi ba za su iya zuwa ba, kwari kuma ba za su iya lalatawa ba. 34Domin inda dukiyarka take, can zuciyarka za ta kasance kuma.
35Ku rage tsawon tufafinku, ku yi dammara, ya zama fitilarku tana ci koyaushe, 36ku kuma zama kamar wadanda suke jiran mai gidansu ya dawo daga gidan buki, domin duk sa'adda ya zo ya kwankwasa kofa, nan da nan za su bude masa.
37Masu albarka ne wadannan bayi, wadanda ubangijinsu za ya tarar suna jiran dawowar sa. Gaskiya ni ke gaya ma ku, zai yi dammara yasa su zazzauna ya ba su abinci shi da kansa. 38Ko da ubangijinsu ya zo da dare, ko da tsakar dare, ya tarar da su a shirye suna jiransa. Masu albarka ne wadannan bayi.
39Kuma ku san wannan, da mai gida ya san lokacin da barawo zai zo, ba zai bari a fasa masa gida a shiga ba. 40Sai ku zauna da shiri fa domin ba ku san lokacin da Dan Mutum zai dawo ba."
41Sai Bitrus ya ce masa, "Ubangiji, mu ka ke fadawa wannan misali, ko ga kowa da kowa ne?" 42Sai Ubangiji ya ce, "Wanne shugaba ne, mai aminci, mai hikima kuma wanda ubangijinsa za ya damka bayinsa a hannunsa, domin ya kula da su, ya ba su abincinsu a kan lokaci? 43Mai albarka ne wannan bawa, wanda ubangijinsa za ya tarar da shi yana yin abin da aka sa shi ya yi. 44Hakika, ina gaya maku, zai danka dukan malakarsa a gareshi.
45Amma idan wannan bawa, ya ce a cikin zuciyarsa, 'Ubangiji na yayi jinkirin dawowa,' sai ya fara dukan bayin, maza da mata abokan bautarsa, ya ci ya sha, ya bugu, 46ubangijin bawan nan zai dawo a lokacin da bawan bai sa tsammani ba, kuma a cikin lokacin da bai sani ba, ya daddatsa shi gunduwa-gunduwa, ya kuma hada shi da marasa aminci.
47Bawan nan, ya san halin ubagijinsa, amma bai shirya yayi abin da ubangijinsa yake so ba. Zai sha duka da bulala da yawa. 48Amma shi wanda bai sani ba, kuma yayi abin da ba daidai ba, ba zai sha duka da bulala da yawa ba. Dukan wanda aka ba abu da yawa, za a kuma nemi abu da yawa daga wurinsa. Kuma ga wanda aka ba abu da yawa amana, za a nemi abu mafi yawa daga gareshi.
49Na zo domin in sa wuta a duniya, na so da ta riga ta kama. 50Amma ni, ina da baftisma wadda za a yi mani baftisma da ita, kuma na kagara, da an riga an yi ta!
51Kuna zaton na zo duniya domin in kawo salama? Na ce maku a'a, amma tsattsaguwa. 52Daga yanzu za a sami mutane biyar a cikin gida daya, kuma za su rarrabu, mutane uku suna gaba da biyu, biyun kuma suna gaba da ukun. 53Da da mahaifi za su yi gaba da juna, dan zai yi gaba da mahaifinsa. Mahaifiya za ta yi gaba da diyarta, diya kuma gaba da mahafiyarta; uwar miji za ta yi gaba da matar danta, matar da kuma gaba da uwar mijinta."
54Yesu, ya kuma gaya wa taron, "Da kun ga hadari ya taso daga yamma, nan da nan sai ku ce za a yi ruwa, haka kuwa ya kan zama. 55Idan iska tana busowa daga kudu sai ku ce za a yi zafi mai tsanani, haka kuwa ya kan faru. 56Munafukai, kun iya fasarta yanayin kasa da sama, amma baku iya fasarta abin da yake faruwa yanzu ba?
57Me ya sa ba ku iya gane abin da zai tamake ku? 58Idan kuna tafiya wurin shari'a da abokin husumarka, ka yi kokari ku daidaita tun a kan hanya domin kada ya kai ka wurin mai shari'a. Domin kada mai shari'a ya mika ka ga mai tsaron kurkuku, shi kuwa mai tsaron kurkuku ba zai nuna maka sani a cikin kurkuku ba. 59Na gaya maka, ba za ka iya fitowa ba sai ka biya dukan kudin da a ke binka?

13

1A lokacin, wadansu mutane suka gaya masa game da galilawa wadanda Bilatus ya gauraye jininsu da hadayunsu. 2Sai Yesu ya amsa masu yace "Kuna tsammani wadannan Galilawa sun fi duk sauran Galilawan zunubi ne, da suka sha azaba haka? 3A'a, ina gaya maku. In ba ku tuba ba, dukanku za ku halaka kamarsu.

4Ko kuwa mutane goma sha takwas din nan da suna Siluwam wadanda hasumiya ta fado a kansu ta kashe su, kuna tsamani sun fi duk sauran mutanen Urushalima laifi ne? 5Ina gaya maku ba haka bane. Amma duk wanda ya ki tuba, dukanku za su hallaka"
6Yesu ya fada wannan misali, "Wani mutum yana da baure wanda ya shuka a garkar inabinsa sai ya zo neman 'ya'yan itacen amma bai samu ba. 7Sai mutumin ya ce wa mai kula da garkar, "ka ga, shekara uku kenan nake zuwa neman 'ya'yan wannan baure, amma ban samu ba. A sare shi. Yaya za a bar shi ya tsare wurin a banza?
8Sai mai lura da garkar ya amsa yace, 'Ka dan ba shi lokaci kadan in yi masa kaftu in zuba masa taki. 9In yayi 'ya'ya shekara mai zuwa to, amma in bai yi 'ya'ya ba sai a sare shi!"'
10Wata rana Yesu yana koyarwa a wata majami' a ran Asabaci. 11Sai, ga wata mace a wurin shekarunta goma sha takwas tana da mugun ruhu, duk ta tankware, ba ta iya mikewa.
12Da Yesu ya gan ta, sai ya kira ta ya ce mata, an warkar da ke daga wannan cuta." 13Sai Yesu ya dora hannunsa a kanta, nan da nan sai ta mike a tsaye ta fara daukaka Allah. 14Amma shugaban majami'a yayi fushi domin Yesu yayi warkarwa a ranar Asabaci. Sai shugaban ya amsa yace wa jama'a, "Akwai ranaku shida da ya kamata a yi aiki. Ku zo domin a warkar da ku amma ba ranar Asabaci ba."
15Amma Ubangiji ya amsa masa ya ce, "Munafukai! Ashe kowannenku ba ya kwance Jakinsa ko Sa daga turkensa ya kai shi banruwa ran Asabaci? 16Ashe wannan 'yar gidan Ibrahim, wanda shaidan ya daure ta shekara goma sha takwas, wato ba za a iya kwance ta a ranar Asabaci kenan ba?
17Da ya fada wadannan abubuwa, dukansu da suka yi adawa da shi suka kunyata, duk taron kuwa suka yi ta farin ciki da abubuwa masu daraja da yayi.
18Sai Yesu ya ce, "Yaya za a misalta mulkin Allah, kuma da me zan kwatanta shi? 19Yananan kamar kwayar mastad, wanda wani mutum ya dauka ya jefa ta a lambunsa, ta kuma yi girma ta zama gagarumin itace, har tsuntsaye suka yi shekarsu a rassanta."
20Ya sake cewa, "Da me zan kwatanta mulkin Allah? 21Yana kamar yisti wanda wata mace ta dauka ta cuda da mudu uku na garin alkama don ya kumburar da shi."
22Yesu ya ziyarci kowanne birni da kauye, a hanyar sa ta zuwa Urushalima yana koyar da su. 23Sai wani ya ce masa, "Ubangiji, wadanda za su sami ceto kadan ne?" Sai ya ce masu, 24"Ku yi kokari ku shiga ta matsatsiyar kofa, domin na ce maku, mutane dayawa za su nemi shiga amma ba za su iya shiga ba.
25In dai maigida ya riga ya tashi ya rufe kofa, sannan za ku tsaya a waje kuna kwankwasa kofar kuna cewa, 'Ubangiji, Ubangiji, bari mu shiga ciki'. Sai ya amsa yace maku, 'Ni ban san ku ba ko daga ina ku ka fito.' 26Sannan za ku ce, 'Mun ci mun sha a gabanka, ka kuma yi koyarwa a kan titunanmu.' 27Amma zai amsa ya ce, "Ina gaya maku, ban san ko daga ina ku ka fito ba, ku tafi daga wurina, dukanku masu aikata mugunta!'
28Za a yi kuka da cizon hakora a lokacin da kun ga Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu da dukan annabawa a mulkin Allah amma ku-za a jefar da ku waje. 29Za su zo daga gabas, yamma, kudu, da arewa, za su ci a teburin abinci a mulkin Allah. 30Ku san da wannan, na karshe za su zama na farko, na farko kuma za su zama na karshe."
31Nan take, wadansu farisiyawa suka zo suka ce masa, "Ka tafi daga nan domin Hirudus yana so ya kashe ka." 32Yesu ya ce, "Ku tafi ku gaya wa dilan nan cewa, 'Duba, na fitar da aljanu, ina warkarwa yau da gobe, kuma a rana ta uku kuwa zan gama aiki na.' 33Ko da kaka, dole ne in ci gaba da tafiyata yau, da gobe, da kuma jibi, don bai dace a kashe annabi nesa da Urushalima ba.
34Urushalima, Urushalima masu kisan annabawa, masu jifan wadanda aka aiko gare ku. Sau nawa ne ina so in tattara 'ya'yanki kamar yadda kaza take tattara 'ya'yanta a cikin fukafukanta, amma ba ki so wannan ba. 35Duba, an yashe gidanki. Ina kwa gaya maku ba za ku kara ganina ba sai ran da kuka ce, 'Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji.'"

14

1Wata ranar Asabaci, ya shiga gidan wani daya daga cikin shugabanin Farisawa domin cin abinci, mutane kuwa suna sa masa idanu. 2Sai ga wani a gabansa mai ciwon fara. 3Yesu ya tambaye masanan attaura da Farisawa, "Ya halata a wakar a ranan Asabaci, ko a'a?"

4Amma suka yi shiru. Yesu kuwa ya kama shi, ya warkar da shi, ya kuma sallame shi. 5Sai yace masu, "Wanene a cikinku in yana da jaki ko takarkari ya fadi a rijiya ran Asabaci, ba zai fitar da shi nan da nan ba?" 6Sai suka kasa ba da amsar wadannan abubuwa.
7Sa'adda Yesu ya lura da yadda wadanda aka gayyato sun zabi mazaunan alfarma, sai ya ba su misali yana ce masu, 8"Sa'adda wani ya gayyace ka zuwa bikin aure, kada ka zauna a wuri mai daraja, domin yana yiwuwa an gayyaci wani wanda ya fi ka daraja. 9Sa'adda wanda ya gayyace ku duka biyu ya zo, zai ce maka, 'Ka ba mutumin nan wurinka,' sa'annan a kunyace za ka koma mazauni mafi kaskanci.
10Amma idan an gayyace ka biki, sai ka je ka zauna a wuri mafi kaskanci, domin idan wanda ya gayyace ka ya zo, yana iya ce maka, 'Aboki, hawo nan mana'. Sannan za ka sami girma kenan a gaban dukan wadanda kuke zaune tare a kan teburi. 11Duk wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, wanda ya kaskantar da kansa, kuma daukaka shi za a yi".
12Yesu ya ce wa mutumin da ya gayyace shi, "Idan za ka gayyaci mutum cin abinci ko biki, kada ka gayyaci abokanka, ko 'yan'uwanka, ko danginka, ko makwabtanka masu arziki, kamar yadda suna iya gayyatar ka, sai ya zama an maida maka.
13Amma idan za ka kira biki sai ka gayyace matalauta, da nakasassu, da guragu, da makafi, 14za ka kuwa sami albarka da yake ba su da hanyar saka maka. Gama za a saka maka a ranar tashin masu adalci."
15Da daya daga cikin wadanda ke zama akan teburi da Yesu ya ji wadannan abubuwa, sai ya ce masa, "Albarka ta tabbata ga wanda zai ci abinci a mulkin Allah!" 16Amma Yesu ya ce masa, "Wani mutum ne ya shirya babban biki ya gayyaci mutane da yawa. 17Da lokacin biki ya yi, sai ya aiki bawansa ya ce wa wadanda aka gayyata, "Ku zo, duk an shirya kome."
18Sai dukansu, suka fara kawo dalilai. Na farko ya ce masa, 'Na sayi gona, lalle ne in je in gan ta. Ina rokonka ka dauke mani.' 19Sai wani ya ce, 'Na sayi shanu garma biyar, ina so in gwada su. Ina ronkan ka, ka dauke mani.' 20Wani mutum kuma ya ce, 'Na yi aure, don haka ba zan iya zuwa ba.'
21Da bawan ya zo ya fadi wa maigidansa wadannan abubuwa, sai maigidan yayi fushi, ya ce wa bawansa, jeka da sauri ka bi cikin titunan birni da kwararo-kwararo, ka kawo gajiyayyu, da nakasassu, da makafi, da guragu.' 22Sai bawan ya ce, 'Maigida, abin da ka umarta an gama, amma har yanzu da sauran wuri."
23Sai maigidan ya ce wa bawan, 'Jeka, ka bi kwararo-kwararo da hanyoyin karkara, ka rinjayi mutane su shigo, don a cika gidana. 24Gama ina gaya maku, babu ko daya daga cikin mutanen da na gayyata da farko da zai dandana bikina."
25Ana nan, taron suna tafiya tare da shi, sai ya juya ya ce masu, 26"Duk mai zuwa wurina amma bai ki mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa, da 'ya'yansa, da 'yan'uwansa maza da mata ba - I, har da ransa ma, ba zai iya zama almajirina ba. 27Duk wanda bai dauki gijiyensa ya biyo ni ba, ba zai iya zama almajirina ba.
28Wanene a cikinku wanda yake niyyar gina bene, da ba zai zauna ya yi lissafin abin da zai kashe ba tun da farko, ko yana da ishashen kudi da zai iya kare aikin? 29Kada ya zama bayan da ya sa harsashin ginin, ya kasa gamawa, har duk wadanda suka gani su fara yi masa ba'a, 30su rika cewa, ga mutumin nan ya fara gini amma ya kasa gamawa.'
31Ko kuwa wanne sarki ne, in za shi je yaki da wani sarki, da ba zai zauna da farko ya yi shawara ya ga ko shi mai jarumawa dubu goma zai iya karawa da dayan sarkin mai jarumawa dubu ashirin ba? 32In kuwa ba zai iya ba, to tun wancan yana nesa, sai ya aiki wakili ya kuma tambayo sharudan salama. 33Haka ma, ba wani a cikinku wanda bai rabu da duk abin da ya mallaka ba, da zai iya zama almajirina."
34"Gishiri abu ne mai kyau, amma idan gishiri ya sane, da me za a dadada shi? 35Ba shi da wani anfani a kasa, ko ya zama taki. Sai dai a zubar kawai. Duk mai kunnen ji, ya ji."

15

1To sai duk masu karbar haraji da masu zunubi suna ta zuwa wurin Yesu suna sauraronsa. 2Dukan Farisawa da Marubuta suna ta gunaguni da junansu, cewa, "Wannan mutum yana karbar masu zunubi, har ma tare suke cin abinci."

3Yesu ya fadi wannan misali, ya ce, 4"Idan waninku yana da tumaki dari, sai dayarsu ta bace, wato ba zai bar tasa'in da taran nan a makiyaya, ya bi sawun wadda ta bata gudan nan har sai ya same shi ba? 5Idan kuwa ya same ta, sai ya dauke ta a kafadarsa yana farin ciki.
6In ya dawo gida, sai ya kira abokansa da makwabta, yace masu, 'Ku taya ni murna don na samo tunkiyata da ta bata.' 7Ina gaya maku, haka kuma za a yi farin ciki a sama, a kan mai zunubi guda da ya tuba, fiye da kan masu adalci tassa'in da tara wadanda ba su bukatar tuba.
8Ko kuwa wacce mace ce, in tana da kudi azurfa guda goma, in ta batar da daya, ba za ta kunna fitila ta share gidan, ta yi ta neman shi har sai ta same shi ba? 9In kuwa ta same shi sai ta tara kawayenta da makwabtanta, ta ce, 'Ku taya ni farin ciki don na sami kudin nan nawa da ya bace.' 10Haka nake gaya maku, abin farin ciki ne ga mala'ikun Allah idan mai zunubi guda ya tuba."
11Sai Yesu ya ce, "Akwai wani mutum mai 'ya'ya biyu maza, 12sai karamin ya ce wa mahaifinsa, 'Baba, bani rabona daga cikin dukiyarka.' Sai mahaifinsa ya raba masu dukiyarsa tsakaninsu.
13Bayan 'yan kwanaki kadan, sai karamin dan ya tattara duk mallakarsa, ya kama hanya zuwa wata kasa mai nisa. A can ya batas da kudinsa, yana sayan abubuwan da ba ya bukata, ya kuma batas da kudinsa a wajen masha'a. 14Bayan da ya batas da duk abin da ya ke da shi, sai aka yi babbar yunwa a kasar, sai ya shiga fatara.
15Ya je ya mika kansa domin aiki ga wani dan kasar, sai ya aike shi cikin gonakinsa domin ya rika ba aladu abinci. 16Har yayi marmarin ya ci daga cikin barbashin da aladu suke ci, domin babu wanda yake ba shi wani abu ya ci.
17Amma da hankalinsa ya dawo, ya ce, 'Barorin mahaifina su nawa ne da suke da abinci isasshe, amma ina nan a nan, ina mutuwa sabili da yunwa! 18Zan tashi, in tafi gun mahaifina, in ce masa, "Baba, na yi wa sama zunubi, na kuma saba maka. 19Ban cancanci a kara kira na danka ba; ka mai da ni kamar daya daga cikin barorinka.'"
20Sai ya tashi, ya taho wurin mahaifinsa. Amma tun yana daga nesa, sai mahaifinsa ya hango shi tausayi ya kama shi, ya ruga a guje, ya rungume shi, ya yi ta sumbatar sa. 21Dan kuma ya ce masa, 'Baba, na yi wa sama zunubi, na kuma saba maka. Ban isa a kara kira na danka ba.'
22Amma mahaifinsa ya ce wa bayinsa, 'Ku yi hamzari ku kawo riga mafi kyau, ku yafa masa. Ku sa masa zobe a hanunsa da takalma a kafafunsa. 23Sa'annan a kawo kiwataccen marakin nan, a yanka. Mu yi buki! 24Gama da na ya mutu a da, amma yanzu yana a raye. Ya bata a da, amma a yanzu an same shi.' Sai suka fara liyafa.
25A wannan lokacin, babban dansa yana gona. Da ya kai kusa da gida, ya ji ana kade-kade da raye-raye. 26Sai ya kira wani bawan gidan, ya tambayi manufar wadannan abubuwa. 27Bawan ya ce masa, 'Dan'uwanka ne ya dawo gida, mahaifinka kuma ya yanka kiwataccen marakin nan, saboda ya dawo gida lafiya.'
28Amma dan'uwan ya yi fushi, ya ki ya shiga ciki, mahaifinsa kuwa ya fito, ya roke shi. 29Amma babban dan ya amsa wa ubansa ya ce, 'Duba, duk yawan shekarun nan da nake bauta maka, ban taba karya umarnin ka ba, duk da haka ba ka taba bani ko dan taure da zan yi shagali tare da abokaina ba, 30amma da dan nan naka ya zo wanda ya fallasar da dukiyarka a kan karuwai, ka yanka masa kiwataccen marakin nan.
31Sai mahaifin ya ce masa, 'Dana, ai kullum kana tare da ni, duk abin da yake nawa naka ne. 32Amma, daidai ne a yi murna da farinciki, don dan'uwan nan naka da ya mutu, amma yanzu yana da rai, da ya bata, amma yanzu an same shi.'"

16

1Yesu ya kuma ce wa almajiransa, "Akwai wani mai arziki da yake da wakili, sai aka yi karan sa da cewa wannan wakili yana fallasar masa da dukiya. 2Sai mai arziki ya kira shi ya ce masa, 'Labarin me nake ji game da kai? Kawo lissafin wakilcin ka, don ba za ka sake zama wakili na ba.'

3Sai wakilin ya ce a ransa, 'Kaka zan yi, da yake maigida na zai karbe wakilci daga hannuna? Gashi, ba ni da karfin noma ina kuwa jin kunya in yi roko. 4Na san abin da zan yi domin idan an fitar da ni daga wakilcin, mutane su karbe ni a gidajensu.
5Sai wakilin ya kira kowanne daya da maigidansa ke bi bashi, yace wa na farkon, 'Nawa maigida na yake bin ka?' 6Ya ce, 'Garwan mai dari.' Sai ya ce masa, 'Ga takardarka, maza ka zauna, ka rubuta hamsin.' 7Ya kuma ce wa wani, 'Nawa ake binka?' Ya ce, 'Buhu dari na alkama.' Ya ce masa, 'Ga tarkardarka, ka rubuta tamanin.'
8Sai maigida ya yaba wa wakilin nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama 'ya'yan zamanin nan a ma'ammalar su da mutanen zamaninsu sun fi 'ya'yan haske wayo. 9Ina gaya maku ku yi abuta ta dukiya ta rashin gaskiya, saboda idan ya kare, su karbe ku a gidaje masu dauwama.
10Wanda yake da aminci a karamin abu, mai aminci ne a babban abu, wanda yake marar gaskiya a karamin abu, marar gaskiya ne a babban abu. 11Idan fa ba ku yi aminci da dukiya mara adalci ba, wa zai amince maku da dukiya ta gaskiya? 12Idan kuma ba ku yi aminci da kudin wani ba, wa zai ba ku kudin da ke naku?
13Ba bawan da zai iya bauta wa iyayengiji biyu, ko dai ya ki daya, ya so daya ko kuwa ya amince wa dayan, ya raina dayan. Ba za ku iya bauta wa Allah ku kuma bauta wa dukiya ba."
14Da Farisawa da ke da kaunar kudi suka ji dukan wadannan abubuwa, suka yi masa ba'a. 15Sai ya ce masu, "Ku ne masu baratar da kanku a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abin da mutane suke girmamawa kwarai abin kyama ne a gun Allah.
16Attaura da litattafan annabawa suna nan har zuwan Yahaya. Tun daga lokacin nan ake yin bisharar mulkin Allah, kowa kuma yana kokarin kutsawa zuwa cikinta. 17Duk da haka, zai fi sauki sama da kasa su shude, da ko digo daya na attaura ya shude.
18Duk wanda ya saki matansa ya auri wata ya aikata zina, kuma wanda ma ya auri sakakkiya ya aikata zina.
19Akwai wani mai arziki, mai sa tufafi na alfarma masu tsada yana shagalin sa kowace rana. 20Aka ajiye wani gajiyayye a kofarsa, mai suna liazaru wanda duk jikinsa miki ne, 21Shi kuwa yana marmarin ya koshi da barbashin da ke fadowa daga teburin mai arzikin nan har ma karnuka sukan zo suna lasar mikinsa.
22Ana nan sai gajiyayyen nan ya mutu, malaiku kuma suka dauke shi suka kai shi wurin Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi, 23yana cikin hades yana shan azaba, sai ya daga kai ya hangi Ibrahim daga nesa, da Li'azaru a kirjinsa.
24Sai ya yi kira ya ce, 'Baba Ibrahim, ka ji tausayi na, ka aiko Li'azaru ya tsoma dan yatsansa a ruwa ya sanyaya harshena, don azaba nake sha a cikin wannan wuta.'
25Amma Ibrahim ya ce, 'Yaro, ka tuna fa a zamanka na duniya ka sha duniyarka, ka kuma karba abubuwa masu kyau, amma Li'azaru kuma sai wahala. Amma yanzu dadi ake bashi a nan, kai kuwa kana shan azaba. 26Banda haka ma, akwai rami mai zurfi, domin wadanda suke son ketarewa zuwa wurinku kada su iya, kada kuma kowa ya ketaro zuwa wurinmu daga can.'
27Sai mai arziki ya ce, 'To ina rokonka, Baba Ibrahim, ka aike shi zuwa gidan mahaifina - 28domin ina da 'yan'uwa maza biyar, ya je ya yi masu gargadi kada su ma su zo wurin azaban nan.'
29Amma Ibrahim ya ce, 'Suna da Musa da annabawa; bari su saurare su.' 30Sai mai arziki ya amsa, 'A'a, Baba Ibrahim, idan wani daga cikin matattu ya je wurinsu, zasu tuba.' 31Amma Ibrahim ya ce masa, 'In dai har basu saurari Musa da na annabawa ba, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su rinjayu ba.'"

17

1Sai Yesu ya ce wa almajiransa, 'Babu shakka akwai sanadodin tuntube da za su sa mu yin zunubi amma kaiton wanda shine sanadin su! 2Zai gwammaci a rataya masa dutsen nika a wuyansa, a jefar da shi a cikin teku fiye da wanda zai zama sanadiyar tuntube ga wadannan kananan.

3Ku kula da kanku. Idan dan'uwanka ya yi laifi, ka tsauta masa, in kuwa ya tuba ka yafe masa. 4Idan ya yi maka laifi sau bakwai a rana daya sa'annan ya juyo wurinka sau bakwai ya ce, 'Na tuba,' ya wajabta ka yafe masa!"
5Sai Manzannin suka ce wa Ubangiji, 'Ka kara mana bangaskiya.' 6Ubangiji kuwa ya ce, "In kuna da bangaskiya kamar kwayar mastad, za ku ce wa wannan durumin, 'Ka tuge, ka kuma dasu a cikin teku,' zai yi biyayya da ku.
7Amma wanene a cikinku, idan yana da bawa mai yin masa noma ko kiwon tumaki, da zarar ya dawo daga jeji, zai ce masa, 'Maza zo ka zauna ka ci abinci'? 8Ba zai ce masa, 'Ka shirya mani wani abu domin in ci ka kuma yi damara, ka yi mini hidima har in gama ci da sha. Bayan haka sai ka ci ka sha'?
9Ba zai yi wa bawan nan godiya ba domin ya yi biyayya da abubuwan da aka umarce shi ya yi, ko zai yi haka? 10Haka kuma, idan kuka bi duk abin da aka umarce ku, sai ku ce, 'Mu bayi ne marasa amfani. Mun dai yi abin da yake wajibi ne kurum.'"
11Wata rana yana tafiya zuwa Urushalima, sai ya bi iyakar kasar Samariya da Galili. 12Yayin da yana shiga wani kauye kenan, sai wadansu kutare maza guda goma suka tarye shi suna tsaye daga nesa da shi 13sai suka daga murya suka ce, "Yesu, Ubangiji, ka yi mana jinkai."
14Da ya gan su, ya ce masu, "Ku je ku nuna kanku a wurin firistoci." Ya zama sa'adda suke tafiya, sai suka tsarkaka. 15Daya daga cikinsu da ya ga an warkar da shi, ya koma, yana ta daukaka Allah da murya mai karfi. 16Ya fadi a gaban Yesu, yana masa godiya. Shi kuwa Basamariye ne.
17Yesu ya amsa ya ce, "Ba goma ne aka tsarkake ba? Ina sauran taran? 18Babu wani da ya dawo ya girmama Allah sai wannan bakon kadai?" 19Sai ya ce masa, "Tashi, kayi tafiyarka. Bangaskiyarka ta warkar da kai."
20Da Farisawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai bayyana, Yesu ya amsa masu ya ce, "Mulkin Allah ba lura ake yi da shi ba. 21Ba kuwa za a ce, 'Gashi nan!' Ko kuwa, 'Ga shi can ba!' domin mulkin Allah yana tsaknaninku."
22Yesu ya ce wa almajiran, "Kwanaki na zuwa da za ku yi begen ganin rana daya cikin ranakun Dan Mutum, amma ba zaku gani ba. 23Za su ce maku, 'Duba can! 'Duba nan!' Amma kada ku je kuna dubawa, ko kuwa ku bi su. 24Kamar yadda walkiya take haskakawa daga wannan bangaren sararin sama zuwa wancan bangaren, haka ma dan mutum zai zama a ranar bayyanuwarsa.
25Amma lalle sai ya sha wahaloli dabam dabam tukuna, mutanen zamanin nan kuma su ki shi. 26Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka kuma zai faru a lokacin bayyanar Dan Mutum. 27Ana ci, ana sha, ana aure, ana aurarwa, har zuwa ga ranar da Nuhu ya shiga jirgi - ruwan tufana kuma ya zo, ya hallaka su duka.
28Haka ma aka yi a zamanin Lutu, ana ci, ana sha, ana saye, ana sayarwa, ana shuke-shuke da gine-gine. 29Amma a ranar da Lutu, ya fita daga Saduma, aka zubo wuta da kibiritu daga sama, aka hallaka su duka.
30Haka kuma zai zama a ranar bayyanuwar Dan Mutum. 31A ranar nan fa, wanda yake kan soro kada ya sauka domin daukan kayansa daga cikin gida. Haka kuma wanda yake gona kada ya dawo.
32Ku tuna fa da matar Lutu. 33Duk mai son ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai same shi.
34Ina gaya maku, a wannan dare za a sami mutum biyu a gado daya. Za a dauka daya, a kuma bar dayan. 35Za a sami mata biyu suna nika tare. Za a dauka daya a bar daya." 361
37Sai suka tambaye shi, "Ina, Ubangiji?" Sai ya ce masu, "Duk in da gangar jiki yake, a nan ungulai sukan taru."


1Luka 17:36 mafi kyawun tsoffin kwafi ba su da aya 36, Za a ga mutum biyu a gona. Za a dauki daya a bar daya .

18

1Ya kuma ba su wani misali cewa ya kamata kullum su yi addu'a kada kuma su karaya, 2yace, "A wani gari an yi wani alkali mara tsoron Allah, kuma baya ganin darajan mutane.

3Akwai wata mace gwauruwa a wannan garin, wadda ta rika zuwa wurinsa, tana ce masa, 'Ka taimake ni yanda zan sami adalci a kan abokin gaba na.' 4An dade bai so ya taimaka mata, amma daga baya sai ya ce a ransa, 'ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma darajanta mutane, 5duk da haka saboda gwauruwar nan ta dame ni, zan taimake ta domin ta sami adalci, yadda ba za ta gajiyar da ni da zuwanta wurina ba.'"
6Sai Ubangiji ya ce, "Ku ji fa abin da alkalin nan marar gaskiya ya fada. 7A yanzu Allah ba zai biya wa zababbunsa da suke yi masa kuka dare da rana hakkinsu ba? Zai yi jinkiri a wajen taimakonsu ne? 8Ina gaya maku, zai biya masu hakkin su da wuri. Amma sa'adda Dan Mutum ya zo, zai tarar da bangaskiya a duniya?"
9Ya sake ba da misalin nan ga wadansu masu amincewa da kansu, wai su masu adalci ne, har suna raina sauran mutane, 10"Wadansu mutane biyu suka shiga haikali domin yin addu'a - daya Bafarise, dayan kuma mai karbar haraji ne.
11Sai Bafarisen ya mike, ya yi addu'a a kan wadannan abubuwa game da kansa, 'Allah, na gode maka, da cewa ni ba kamar sauran mutane dake mazambata ba, ko marasa adalci, ko mazinata, ko kamar wannan mai karbar harajin. 12Duk mako ina azumi sau biyu. Nakan bayar da zakkar dukan abin da na samu.'
13Amma mai karbar harajin kuwa yana tsaye daga can nesa, bai yarda ya daga kai sama ba, sai dai yana bugun kirjin sa, yana cewa, 'Allah, ka yi mini jinkai, ni mai zunubi.' 14Ina gaya maku, wannan mutum ya koma gidansa baratacce, ba kamar dayan ba, domin dukan wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, amma duk wanda kaskantar da kansa kuwa daukaka shi za a yi."
15Sai mutanen suka kawo masa jariransu, domin ya taba su, da almajiransa suka ga haka, sai suka kwabe su. 16Amma Yesu ya kira su wurinsa, ya ce, "Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai mulkin Allah na irin su ne. 17Gaskiya ina gaya maku, duk wanda bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, lallai ba zai shige shi ba."
18Wani shugaban jama'a ya tambaye shi ya ce "Malam managarci, me zan yi in gaji rai Madawwami?" 19Yesu ya ce masa, "Don me ka kira ni managarci? Babu wani managarci sai Allah kadai. 20Ka dai san dokokin - kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar karya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka." 21Sai shugaban ya ce, "Dukan wadannan abubuwa na kiyaye su tun a kuruciya ta."
22Da Yesu ya ji haka, ya ce masa, "Abu daya ne kadai ya rage maka. Dole ne ka sayar da dukan mallakarka, ka rarraba wa gajiyayyu, za ka kuma sami wadata a sama - sa'annan ka zo ka biyoni." 23Amma da mai arzikin ya ji wadannan abubuwa, sai yayi bakin ciki kwarai, don shi mai arziki ne sosai.
24Yesu kuwa, da ya ga ransa ya baci, sai ya ce, "Yana da wuya masu dukiya su shiga mulkin Allah! 25Zai zama da sauki rakumi ya shiga kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah."
26Wadanda suka ji wannan magana suka ce, "Idan hakane wa zai sami ceto kenan?" 27Yesu ya amsa, "Abin da ya fi karfin mutum, mai yiwuwa ne a gun Allah."
28Sai Bitrus ya ce, "To, ga shi mun bar mallakarmu, mun bi ka." 29Yesu ya ce masu, "Hakika, ina gaya maku, ba wanda zai bar gida, ko matarsa, ko 'yan'uwansa, ko iyayensa, ko kuma 'ya'yansa, saboda mulkin Allah, 30sa'annan ya kasa samun ninkin ba ninkin a duniyan nan, da rai na har abada a duniya mai zuwa."
31Bayan da ya tara su goma sha biyun nan, ya ce masu, "Ga shi, muna tafiya zuwa Urushalima, duk abubuwan da aka rubuta game da Dan Mutum ta hannun annabawa zasu tabbata. 32Gama za a bashe shi ga al'ummai, a yi masa ba'a, a wulakanta shi, a kuma tofa masa miyau. 33Za su yi masa bulala, su kashe shi, a rana ta uku kuma zai tashi."
34Amma ba su fahimci ko daya daga cikin wadannan abubuwa ba, domin zancen nan a boye yake daga garesu, ba su ma gane abin da aka fada ba.
35Da ya kusato Yariko, ga wani makaho zaune a gefen hanya, yana bara, 36da ya ji taro na wucewa, sai ya tambaya ko menene. 37Suka ce masa Yesu Banazarat ne yake wucewa.
38Sai makahon ya ta da murya mai karfi, ya ce, "Yesu, Dan Dauda, ka yi mani jinkai." 39Sai wadanda suke gaba suka kwabe shi, suna gaya masa ya yi shiru. Amma ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, "Dan Dauda, ka yi mani jinkai."
40Sai Yesu ya tsaya, ya umarta a kawo shi wurinsa. Da makahon ya zo kusa, sai Yesu ya tambaye shi, 41"Me kake so in yi maka?" Ya ce, "Ubangiji, ina so in samu gani."
42Yesu ya ce masa, "Karbi ganin gari, bangaskiyarka ta warkar da kai." 43Nan take ya samu gani, ya bi Yesu, yana daukaka Allah. Ganin haka, sai duk jama'a suka yabi Allah.

19

1Yesu ya shiga Yariko ya na wucewa cikinta. 2Sai ga wani mutum a wurin mai suna Zakka. Shugaba ne na masu karban haraji, kuma mai arziki ne.

3Yana kokarin ya ga ko wanene Yesu, amma bai iya gani ba sabo da yawan jama'a, domin shi gajere ne. 4Sai ya ruga gaba ya hau itacen baure domin ya gan shi, saboda Yesu zai wuce ta wannan hanya.
5Sa'adda Yesu ya zo wurin, ya kalli sama sai ya ce masa, "Zakka, ka sauko da sauri, domin yau dole in sauka a gidanka." 6Sai ya sauko da sauri, ya karbe shi da farin ciki. 7Sa'adda dukansu suka ga wannan, sai suka yi gunaguni, cewa, "Ya ziyarci mutum mai zunubi."
8Zakka ya tsaya ya ce wa Ubangiji, "Duba, Ubangiji, zan ba matalauta rabin arzikina, idan kuma na cuci wani a kome, zan mai da adadinsa sau hudu." 9Yesu ya ce masa, "Yau ceto ya shigo wannan gida, domin shi ma dan Ibrahim ne. 10Gama Dan Mutum ya zo ne domin ya nemi, ya kuma ceci batattun mutane."
11Da suka ji wadannan abubuwan, ya cigaba da magana, sannan ya fada masu wani misali, domin yana kusa da Urushalima, sai suka yi tsamani mulkin Allah za ya bayyana nan da nan. 12Sai ya ce, "Akwai wani mutum mai sarauta wanda ya tafi wata kasa mai nisa domin ya karba wa kansa mulki sa'annan ya dawo.
13Sai ya kira bayinsa guda goma, ya ba su fam goma, sai ya ce masu, 'Ku yi kasuwanci da wannan har sai na dawo.' 14Amma mutanensa suka ki shi sai suka aiki jakadu bayansa, cewa, 'Ba za mu yarda wannan mutum ya yi mulki a kanmu ba.' 15Anan nan sa'adda ya koma kuma, bayan da ya sami mulkin, sai ya ba da umarni a kira masa bayin da ya basu kudi, domin ya san ribar da suka samu wajen kasuwancin da suka yi.
16Na farkon ya zo wurinsa, cewa, 'Ubangiji, fam nan na ka ya yi riban fam goma.' 17Masaraucin ya ce masa, 'Madalla, bawan kirki. Domin ka yi aminci a karamin abu, za a baka iko kan birane goma.'
18Na biyun ya zo, yana cewa, 'Fam na ka, Ubangiji, ya yi ribar fam biyar.' 19Sai masarauncin yace masa, 'Ka dauki mulkin birane biyar.'
20Wani kuma ya zo, yana cewa, 'Ubangiji, ga fam naka da na ajjiye shi da kyau cikin kaya, 21gama na ji tsoronka, domin kai mutum mai tsanani ne. Kana daukar abu da baka ajiye ba, kana kuma girbin abin da ba ka shuka ba.'
22Masarauncin ya ce masa, 'Da kalmominka zan shari'antaka, kai mugun bawa. Ka sani cewa ni mutum mai tsanani ne, ina daukan abinda ban ajiye ba, ina kuma girbin abinda ban shuka ba. 23To don me ba ka kai kudi na wurin masu banki ba, saboda bayan da na dawo zan karbe shi da riba?'
24Masaraucin ya ce wa wadanda suke a tsaye a wurin, 'Ku karba fam da ke a wurinsa, ku ba mai fam goman nan.' 25Suka ce masa, 'Ubangiji, yana da fam goma.'
26'Ina ce maku, duk wanda yake da abu za a kara masa, amma wadda bai da shi, za a karba sauran da ke wurinsa. 27Amma wadannan abokan gabana, wadanda ba sa so in yi mulki bisansu, a kawo su nan a kashe su a gaba na.'
28Da ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi gaba, yana tafiya zuwa Urushalima.
29Ananan sa'adda ya zo kusa da Baitfaji da Baitanya, a kan tudu da a ke kira Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, cewa, 30cewa, "Ku tafi cikin kauye da ke gabanku. Sa'adda ku ka shiga, za ku same dan aholaki da ba a taba hawansa ba. Ku kwance sai ku kawo mani shi. 31Idan wani ya tambaye ku, 'Don me ku ke kwance shi?' Ku ce, 'Ubangiji ne ke bukatarsa."
32Wadanda aka aike su suka je sun sami aholakin kamar yadda Yesu ya gaya masu. 33Sa'adda suna kwance aholakin, sai masu shi suka ce masu, "Don me ku ke kwance aholakin?" 34Suka ce, "Ubangiji yana bukatar sa." 35Suka kawo wa Yesu, suka shimfida tufafinsu akan aholakin sai suka dora Yesu akansa. 36Da yana cikin tafiya, suka shimfida tufafinsu akan hanya.
37Da ya yi kusa da gangaren tudun Zaitun, sai dukan taron almajiransa suka fara yin murna suna kuma yabon Allah da murya mai karfi domin dukan ayukan al'ajibi da suka gani, 38cewa, "Albarka ta tabbata ga sarki da ke zuwa cikin sunan Uba! Salama a sama da daraja mafi daukaka kuma!"
39Wadansu Farisawa daga cikin taron jama'a suka ce masa, "Malam, ka tsauta wa almajiranka." 40Yesu ya amsa ya ce, "Ina gaya maku gaskiya, in wadannan sun yi shiru, duwatsu za su yi shewa."
41Sa'adda Yesu yana kusatowa, sai ya yi kuka akan birnin, 42cewa, "Da kun san wannan rana, ko ku ma, abubuwan da ke kawo maku salama! Amma yanzu an boye su daga idanunku.
43Gama rana zata ta zo a gareki, da makiyan ki zasu gina ganuwa a kewaye da ke, su kuma fada maki daga kowace gefe. 44Za su sare ki kasa tare da 'ya'yanki. Ba za su bar wani dutse akan dan'uwansa ba, domin ba ki lura da lokacin da Allah ya na kokarin ceton ki ba."
45Yesu ya shiga Haikalin sai ya fara korar masu sayarwa, 46ya na ce masu, "A rubuce yake, 'Gida na zai zama wurin addu'a,' amma kun mayar da shi kogon mafasa."
47Yesu yana nan yana koyarwa kowace rana a cikin haikali. Amma manyan firistoci da marubuta da shugabanin jama'a suna so su kashe shi, 48amma ba su sami hanyar yin wannan ba, domin mutane suna sauraron sa sosai.

20

1Ana nan wata rana, Yesu yana kan koyarwa a haikali da wa'azin bishara, sai shugaban firistoci da marubuta suka zo wurinsa da dattawa. 2Suka yi magana, su na ce masa, "Gaya mana da wanne iko ne ka ke yin wadannan abubuwan? Ko wanene ya baka wannan ikon?"

3Ya amsa sai ya ce masu, "Ni ma zan yi maku tambaya. Gaya mani game 4da baptisman Yahaya. Daga sama take ko kuwa daga mutane ne?"
5Sai suka yi mahawara da junansu, suna cewa, "In mun ce, 'Daga sama,' zai ce, 'To don me ba ku ba da gaskiya gareshi ba?' 6Amma in mun ce, 'Daga mutane ne,' dukan mutane za su jejjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata a ransu Yahaya annabi ne."
7Sai suka amsa cewa ba su san ko daga ina ne take ba. 8Yesu yace masu, "To haka ni ma ba zan gaya maku ko da wanne iko nake yin wadannan abubuwan ba."
9Ya gaya wa mutane wannan misali, "Wani mutum ya dasa gonar inabi, ya ba wadansu manoma jinginarta, sai ya tafi wata kasa har ya dade. 10Da lokacin girbi ya yi sai ya aiki wani bawansa zuwa wurin manoman, saboda su bashi daga cikin anfanin gonar. Amma manoman suka doke shi, sai suka kore shi hannu wofi.
11Ya aike wani bawa kuma sai suka daddoke shi, suka kunyatar da shi, suka kore shi hannu wofi. 12Ya kuma sake aike na uku suka yi masa rauni, suka jefar da shi a waje.
13Sai mai gonar inabin ya ce, 'Me zan yi? Zan aiki kaunattacen dana. Watakila zasu ba shi daraja.' 14Amma sa'adda manoman suka gan shi, suka yi shawara a tsakaninsu, cewa, 'Wannan ne magajin. Bari mu kashe shi, saboda gadon ya zama namu.'
15Suka jefar da shi waje daga gonar, suka kashe shi. Menene ubangijin gonar inabin zai yi da su? 16Zai zo ya halakar da wadannan manoma, sai ya ba wadansu gonar." Da suka ji wannan, suka ce, "Allah ya sawake!"
17Amma Yesu ya kalle su, sai yace, "Menene ma'anar wannan nassi? 'Dutsen da magina suka ki, an mayar da shi kan kusurwa'? 18Duk wanda ya fadi kan dutsen zai farfashe. Amma duk wanda dutsen ya fadi a kansa, zai rugurguza shi."
19Sai marubutan da manyan firistocin suka so su kama shi a wannan sa'a, domin sun sani ya yi wannan misali a kansu ne. Amma sun ji tsoron mutane. 20Suna fakonsa, suka aiki magewaya, wadanda suke kamar masu adalci, saboda su sami kuskure cikin maganarsa, don su mika shi ga hukumci da kuma ikon gwamna.
21Suka tambaye shi, cewa, "Malam, mun sani da cewa kana fada da koyar da abin ke daidai, kuma ba wanda yake cusa maka ra'ayi, amma kana koyar da gaskiya game da hanyar Allah. 22Wai shin doka ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?"
23Amma Yesu ya gane makircinsu, sai ya ce masu, 24"Nuna mani dinari. Sifar wanene da kuma rubutun wanene akan sa?" Suka ce, "Na Kaisar ne."
25Sai ya ce masu, "To sai ku ba Kaisar abin da ke na Kaisar, ku kuma ba Allah, abin da ke na Allah." 26Marubutan da manyan firistocin ba su sami abin zargi cikin maganarsa, a gaban mutane ba. Suka yi mamakin amsar sa, ba su kuma ce komai ba.
27Sa'adda wadansu Sadukiyawa suka zo wurinsa, wadan da suka ce babu tashin mattatu, 28suka tambaye shi, cewa, "Malam, Musa ya rubuta mana cewa idan dan'uwan mutum ya mutu, mai mace kuma ba shi da yaro, sai dan'uwansa ya auri matar, ya samar wa dan'uwansa yaro.
29Akwai 'yan'uwa guda bakwai kuma na farin ya yi aure, sai ya mutu babu da, 30haka ma na biyun. 31Na ukun ya aure ta, haka nan na bakwai ma bai bar yaya ba, har suka mutu. 32Daga baya sai matar ma ta mutu. 33To a ranar tashin mattatu, matar wa za ta zama? Domin duka bakwai din sun aure ta."
34Yesu ya ce masu, "'Ya'yan duniyan nan suna aure, ana kuma ba da su ga aure. 35Amma wadanda aka ga cancantarsu a waccan tsara, sun isa su sami tashin mattatu, ba za suyi aure ko a aurar da su ba. 36Gama ba za su mutu kuma ba, domin suna daidai da mala'iku kuma su 'ya'yan Allah ne, da shike su 'ya'yan tashin matattu ne.
37Amma batun tashi matattu, ko Musa ma ya nuna wannan, a cikin jeji, inda ya kira Ubangiji, Allah na Ibrahim da kuma Allah na Ishaku da Allah na Yakubu. 38Yanzu shi ba Allahn matattu ba ne, amma na masu rai, saboda duka suna raye a wurinsa."
39Wadansu marubuta suka amsa, "Malam, ka amsa da kyau." 40Gama ba su sake yi masa wadansu tambayoyi ba.
41Yesu ya ce masu, "Yaya suke cewa Almasihu dan Dauda ne? 42Gama Dauda da kansa ya ce a cikin littafin Zabura, Ubangiji ya ce wa Ubangiji na, 'Zauna a hannun dama na, 43sai na maida makiyanka a karkashin tafin sawunka.' 44Dauda ya kira Kristi 'Ubangiji', to ta yaya ya zama dan Dauda?"
45Dukan mutane suna ji ya ce wa almajiransa, 46"Ku yi hankali da marubuta, wadanda suna son tafiya da manyan riguna, suna kuma son a gaishe su a cikin kasuwanni, da mayan wuraren zama a cikin majami'u, da kuma manyan wurare a wurin bukukkuwa. 47Suna kuma kwace wa gwamraye gidaje, suna kuma badda kama ta wurin yin doguwar addu'a. Wadannan za su sha hukumci mai girma."

21

1Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji. 2Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki. 3Sai ya ce, "Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu. 4Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi."

5Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce, 6"Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba."
7Sai suka yi masa tambaya, cewa, "Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?" 8Yesu ya amsa, "Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su. 9Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba."
10Sa'annan ya ce masu, "Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki. 11Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
12Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana. 13Zai zamar maku zarafin shaida.
14Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa, 15gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
16Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku. 17Kowa zai ki ku saboda sunana. 18Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka. 19A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
20Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa. 21Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki. 22Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
23Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan. 24Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
25Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa. 26Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
27Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma. 28Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato."
29Yesu ya bada misali, "Duba itacen baure, da duka itatuwa. 30Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma. 31Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
32Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru. 33Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
34Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri 35kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
36Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum."
37Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun. 38Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.

22

1Anan nan idin gurasa mara yisti ya yi kusa, wanda a ke kira Idin ketarewa. 2Manyan firistoci da marubuta suka yi shawara yadda za su kashe Yesu, gama suna jin tsoron mutane.

3Shaidan ya shiga Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin goma sha biyun. 4Yahuza ya je ya yi shawara da manyan firistoci da Jarumawa yadda zai ba da Yesu a garesu.
5Suka yi farin ciki, suka yarda su ba shi kudi. 6Sai ya yarda, sai ya nimi dama yadda zai ba da shi garesu a lokacin da babu taro.
7Ranar idin gurasa mara yisti ya yi, da dole za a yi hadayan rago na Idin ketarewa. 8Yesu ya aiki Bitrus da Yahaya, ya ce masu, "Ku je ku shirya mana abincin Idin ketarewa, domin mu ci." 9Suka tambaye shi, "A ina ka ke so mu shirya?"
10Ya amsa masu, "Ku ji, sa'adda ku ka shiga birnin, wani mutum mai dauke da tulun ruwa zai same ku. Ku bishi zuwa cikin gidan da za ya shiga. 11Sai ku gaya wa mai gidan, 'Malam ya ce, "Ina dakin baki, inda zan ci abincin Idin ketarewa da almajirai na?'"
12Zai nuna maku babban bene wanda yake a shirye. Ku shirya a can." 13Sai suka tafi, suka sami komai kamar yadda ya gaya masu. Sai suka shirya abincin Idin ketarewan.
14Sa'adda lokacin ya yi, ya zauna da almajiran. 15Sai ya ce masu, "Ina da marmari matuka in ci wannan abincin Idin ketarewa da ku kamin in sha wahala. 16Gama na ce maku, ba zan ci shi kuma ba, sai dai an cika shi a mulkin Allah."
17Sai Yesu ya dauki koko, sa'adda ya yi godiya, sai yace, "Karba wannan, ku rarraba a tsakaninku. 18Gama ina ce maku, ba zan sha wannan ruwan inabi kuma ba, sai dai mulkin Allah ya zo."
19Sai ya dauki gurasa, sa'adda ya yi godiya, ya kakkarya shi, sai ya ba su, cewa, "Wannan jikina ne wanda aka bayar dominku. Ku yi wannan domin tunawa da ni." 20Sai ya dauki kokon kuma bayan jibi, cewa, "Wannan koko sabon alkawari ne cikin jinina, wanda aka zubar dominku.
21Amma ku yi lura. Wanda zai bashe ni yana tare da ni a teburi. 22Gama Dan Mutum zai tafi lallai kamar yadda aka kaddara. Amma kaiton wannan mutum da shine za ya bashe shi!" 23Sai suka fara tambaya a tsakaninsu, wanene a cikinmu da zai yi wannan abu.
24Sai gardama ta tashi a tsakaninsu game da wanene mafi girma. 25Ya ce masu, "Sarakunan al'ummai suna nuna iko akansu, kuma wadanda suke da iko a kansu ana ce da su masu mulki da daraja.
26Amma kada ya zama haka da ku. A maimakon haka, bari wanda ya ke mafi girma a cikinku ya zama mafi kankanta. Bari wanda yafi muhimmanci kuma ya zama kamar mai hidima. 27Gama wanene yafi girma, wanda ya zauna a teburi, ko kuwa wanda yake yin hidima? Ba wanda ya zauna a teburi ba? Duk da haka ina kamar mai hidima a tsakaninku.
28Amma ku ne wadanda ku ke tare da ni a cikin jarabobina. 29Na baku mulki, kamar yadda Ubana ya ba ni mulki, 30domin ku ci ku kuma sha a teburi na mulkina. Za ku zauna a kan kursiyai kuna shari'anta kabilun nan goma sha biyu na Israila.
31Siman, Siman, ka yi hankali, shaidan ya nemi izini a bada kai domin ya tankade ka kamar alkama. 32Amma na yi maka addu'a, saboda kada bangaskiyarka ta fadi. Bayan da ka juyo kuma, ka karfafa 'yan'uwanka."
33Bitrus ya ce masa, "Ubangiji, ina shirye in tafi tare da kai zuwa cikin kurkuku da zuwa mutuwa." 34Yesu ya amsa masa, "Ina gaya maka, Bitrus, kamin caran zakara a yau, za ka yi musu na sau uku cewa ba ka sanni ba."
35Sa'annan Yesu ya ce masu, "Lokacin da na aike ku babu jaka, ko burgami ko takalma, ko kun rasa wani abu? Sai suka amsa, "Babu." 36Ya kuma ce masu, "Amma yanzu, wanda ya ke da jaka, bari ya dauka, da kuma burgami. Wanda ba shi da takobi sai ya sayar da taguwarsa ya sayi guda.
37Gama ina ce maku, abin da aka rubuta game da ni dole sai ya cika, 'An lisafta shi kamar daya daga cikin masu karya doka.' Gama abinda aka fada akaina ya cika." 38Sai suka ce, "Ubangiji, duba! Ga takuba biyu." Sai ya ce masu, "Ya isa."
39Bayan cin abincin yamma, Yesu ya tafi, kamar yadda ya saba yi, zuwa dutsen Zaitun, sai almajiran suka bi shi. 40Sa'adda suka iso, ya ce masu, "Ku yi addu'a domin kada ku shiga cikin jaraba."
41Ya rabu da su misalin nisan jifa, sai ya durkusa kasa ya yi addu'a, 42yana cewa "Uba, in ka yarda, ka dauke wannan kokon daga gareni. Ko da yake ba nufina ba, amma bari naka nufin ya kasance."
43Sai mala'ika daga sama ya bayyana a wurinsa, yana karfafa shi. 44Yana cikin wahala sosai, sai ya dukufa cikin addu'a, har zufarsa kuma tana diga a kasa kamar gudajen jini.
45Sa'adda ya tashi daga addu'arsa, sai ya zo wurin almajiran, ya same su suna barci domin bakin cikinsu, 46sai ya tambaye su, "Don me kuke barci? Tashi ku yi addu'a, saboda kada ku shiga cikin jaraba."
47Sa'adda yana cikin magana, sai, ga taron jama'a suka bayana, tare da Yahuza, daya daga cikin sha biyun, ya na jagabansu. Sai ya zo kusa da Yesu domin ya yi masa sumba, 48amma Yesu ya ce masa, "Yahuza, za ka ba da Dan Mutum da sumba?"
49Sa'adda wadanda suke kewaye da Yesu suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, "Ubangiji, mu yi sara da takobi ne?" 50Sai daya daga cikinsu ya kai wa bawan babban firist sara a kunne, sai ya yanke masa kunnensa na dama. 51Yesu ya ce, "Ya isa haka." Sai ya taba kunnensa, sai ya warkar da shi.
52Yesu yace wa manyan firistoci, da masu tsaron haikali, da dattawa wadanda suke gaba da shi, "Kun fito kamar za ku kama dan fashi, da takuba da sanduna? 53Sa'adda nake tare da ku kowace rana a haikali, ba ku kama ni ba. Amma wannan shine lokacinku, da kuma ikon duhu."
54Suka kama shi, sai suka tafi da shi, suka kawo shi cikin gidan babban firist. Amma Bitrus yana binsa daga nesa. 55Bayan da suka hura wuta a tsakiyar gidan da suka zazzauna tare, Bitrus ya zaune a tsakaninsu.
56Sai wata baranya ta ganshi ya zauna a hasken wuta, sai ta zura masa ido ta ce, "Wannan mutum ma yana tare da shi." 57Amma Bitrus ya yi musu, yana cewa, "Mace, ban san shi ba." 58Bayan dan karamin lokaci sai wani mutum ya gan shi, sai ya ce, "Kaima kana daya daga cikinsu." Amma Bitrus ya ce, "Mutumin, ba ni ba ne."
59Bayan sa'a daya sai wani mutum ya nace da cewa, "Gaskiya wannan mutum yana tare da shi, gama shi dan Galili ne." 60Amma Bitrus ya ce, "Mutumin, ban san abin da kake fada ba." Sai nan da nan, da yana cikin magana, sai zakara ta yi cara.
61Yana juyawa, sai Ubangiji ya dubi Bitrus. Sai Bitrus ya tuna kalmar Ubangiji, sa'adda ya ce masa, "Kafin zakara ya yi cara yau za ka musunce ni sau uku." 62Da fitowarsa waje, Bitrus ya yi kuka mai zafi.
63Sai mutanen da ke tsare da Yesu suka yi masa ba'a da bulala kuma. 64Bayan da suka rufe masa idanu, suka tambaye shi, cewa, "Ka yi annabci! Wa ya buge ka?" 65Suka yi wadansu miyagun maganganu na sabo game da Yesu.
66Da gari ya waye, sai dattawa suka hadu tare, da manyan firistoci da marubuta. Sai suka kai shi cikin majalisa 67suka ce, "Gaya mana, in kai ne Almasihu." Amma yace masu, "Idan na gaya maku, ba za ku gaskanta ba, 68idan na yi maku tambaya, ba za ku amsa ba.
69Amma nan gaba, Dan Mutum zai zauna a hannun dama na ikon Allah." 70Suka ce masa, "Ashe kai Dan Allah ne?" Sai Yesu ya ce masu, "Haka kuka ce, nine." 71Suka ce, "Don me muke neman shaida? Gama mu da kanmu munji daga bakinsa."

23

1Sai duk taron suka tashi, suka kawo Yesu gaban Bilatus. 2Suka fara saransa, cewa "Mun same wannan mutum yana ruda kasarmu, ya haramta a ba Kaisar haraji, yana kuma cewa shi da kansa ne Almasihu, sarki."

3Bilatus ya tambaye shi, cewa "Shin kaine Sarkin Yahudawa?" Sai Yesu ya amsa masa ya ce, "Haka ka ce." 4Sai Bilatus ya ce wa manyan firistocin da taro mai yawa, "Ban samu ko laifi daya game da wannan mutumin ba." 5Amma suka yi ta cewa, "Yana ta da hankalin mutane da koyarwa a dukan Yahudiya, ya fara daga Galili har zuwa ga wannan wuri."
6Sa'adda Bilatus ya ji wannan, sai ya tambaya ko mutumin daga Galiline. 7Sa'adda ya gane cewa yana karkashin mulkin Hirudus, sai ya tura Yesu wurin Hirudus, wanda shi da kansa yana Urushalima a wadannan kwanakin.
8Sa'adda Hirudus ya ga Yesu, sai ya cika da farin ciki sosai, saboda ya so ganinsa tunda dadewa. Tun can ya ji game da shi sai ya yi begen ganin wadansu al'ajibai da zai yi. 9Hirudus ya tambaye Yesu cikin kalmomi masu yawa, amma Yesu bai amsa masa da komai ba. 10Sai manyan firistoci da marubuta suka tsaya, suna ta yi masa zargi mai zafi.
11Hirudus da sojojinsa suka zarge shi, suka kuma yi masa ba'a, suka sa masa tufafi masu kyau, sa'annan ya sake aika Yesu zuwa wurin Bilatus. 12Sai Hirudus da Bilatus suka zama abokai a wannan rana (da ma su abokai gaba ne).
13Bilatus ya kira manyan firistoci tare da masu mulki da kuma taron jama'ar, 14sai ya ce masu, "Kun kawo mani wannan mutum kamar wanda yake jagorar mutane ga munanan ayyuka, ku kuma gani, Ni, na tuhume shi a gabanku, ban sami ko kuskure daya daga mutumin nan game da abinda ku ke zarginsa da shi ba.
15Babu, ko Hirudus ma, ya sake komar mana da shi, kun gani, babu wani abu wanda ya yi da ya cancanci mutuwa, 16saboda haka zan yi masa horo sa'annan in sake shi." 171
18Amma dukansu suka yi ihu tare, cewa, "A tafi da wannan mutumin, sai a sako mana Barabbas!" 19Barabbas mutum ne wanda aka sa a cikin kurkuku saboda wani tada hankali a cikin birni da kuma kisankai.
20Bilatus ya sake yi masu magana, yana so ya saki Yesu. 21Amma suka yi ihu, cewa, "A giciye shi, a giciye shi." 22Sai ya sake ce masu sau na uku, "Don me, wace magunta wannan mutum ya yi? Ban sami wani abu da ya isa sanadin mutuwa game da shi ba. Saboda haka bayan na hore shi, zan sake shi."
23Amma suka nace da murya mai karfi, suna so a giciye shi, sai muryarsu ta rinjayi Bilatus. 24Sai Bilatus ya yarda ya yi masu bisa ga abin da suke so. 25Ya sako masu wanda suka tambaya ya ba su wanda aka sa a kurkuku domin tada hankali da kuma kisankai. Amma ya ba da Yesu bisa nufinsu.
26Da suka tafi da shi, sai suka kama wani mai suna siman Bakurane, yana zuwa daga karkara, sai suka daura masa giciyen ya dauka, yana biye da Yesu.
27Babban taron jama'a, da na mata da suke makoki da kuka dominsa, suna binsa. 28Amma da ya juya wurinsu, Yesu yace, "Yan matan Urushalima, kada ku yi kuka domina, amma ku yi kuka domin kanku da 'ya'yanku.
29Gama ku gani, kwanaki suna zuwa da za su ce, 'Albarka ta tabbata ga bakararru da wadanda basu taba haihuwa ba da kuma wadanda ba a taba shan mamansu ba.' 30Sa'annan za su fara ce wa duwatsu, 'Ku fado bisanmu,' da tuddai ma, 'Ku rufe mu.' 31Gama idan sun yi wadannan abubuwan lokacin da itace yana danye, me zai faru sa'adda ya bushe?"
32Aka kai wadansu mutum biyu masu laifi, domin a kashe shi tare da su.
33Sa'adda suka zo wurin da a ke kira kwalluwa, nan suka giciye shi da barayin, daya daga hannun damansa dayan kuma daga hannun hagu. 34Yesu yace, "Uba, ka yafe masu, gama basu san abin da suke yi ba." Sai suka jefa kuri'a, suka rarraba tufafinsa.
35Mutane sun tsaya suna kallo sa'annan masu mulki suna ta yin masa ba'a, cewa, "Ya ceci wadansu. Bari ya ceci kansa, idan shine Almasihu na Allah, zababben nan."
36Sojojin ma suka yi masa dariya, suna zuwa wurinsa, suna mika masa ruwan tsami, 37suna cewa, "Idan kai Sarkin Yahudawa ne, ceci kanka." 38Akwai wata alama bisansa, "Wannan shine Sarkin Yahudawa."
39Daya daga cikin barayi wanda aka giciye, ya zage shi, cewa, "Ba kai ne Almasihu ba? Ka ceci kanka da mu." 40Amma dayan ya amsa, ya tsauta masa cewa, "Ba ka tsoron Allah, da yake shari'arka daya ne da nasa? 41Mu kam an yi ma na daidai, gama mun samu bisa ga abin da muka yi. Amma wannan mutum bai yi wani abu mara kyau ba."
42Sai ya kara, "Yesu, ka tuna da ni sa'adda ka shiga mulkinka." 43Yesu ya ce masa, "Gaskiya ina ce maka, yau za ka kasance tare da ni a firdausi."
44Anan nan a wajen sa'a na shida, sai duhu ya mamaye kasar duka har zuwa sa'a na tara 45sa'adda rana ya fadi. Sai labulen haikalin ya rabu a tsakiya zuwa kasa.
46Da kuka da murya mai karfi, Yesu yace, "Uba, na mika Ruhu na a hannunka." Bayan da ya fadi wannan, sai ya mutu. 47Sa'adda jarumin ya ga abin da ya faru, ya daukaka Allah, cewa, "Lallai wannan mutumin mai adalci ne."
48Sa'adda dukan taro mai yawa wadanda suka zo tare domin su shaida da idanunsu suka ga abubuwan da suka faru, suka koma suna bugan kirjinsu. 49Amma duk idon sani, da kuma matan da suka bi shi tun daga Galili, suka tsaya daga nesa, suna duban wadannan abubuwa.
50Ga shi kuwa, wani mutum mai suna Yusufu, shi dan majalisa ne, nagari ne kuma mutum mai adalci ne 51(bai yarda da shawarar da kuma abin da suka aikata ba), daga Arimatiya a kasar Yahudiya, wanda yake jiran mulkin Allah.
52Wannan mutum, ya sami Bilatus, ya tambaya a bashi jikin Yesu. 53Ya saukar da shi kasa, sai ya nade shi cikin likafani na linin mai kyau, ya kwantar da shi cikin kabari da aka sassaka shi daga dutse, inda ba a taba binne wani ba.
54Ranar kuwa, ranar shiri ce, Asabaci kuma ta kusato. 55Matan da suka taho da shi tun daga Galili, suka biyo baya, su ga kabarin da inda aka ajiye shi. 56Suka koma, sai suka shirya kayan kamshi da mai. Suka kuma huta a ranar Asabaci bisa ga doka.


1Mafi kyawun kwafin tsoffin ba su da Luka 23:17, Ya zama dole Bilatus ya sakar wa Yahudawa wani daurarre guda daya lokacin idin .

24

1Da sassafe a ranar farko ta mako, suka zo kabarin, suka kawo kayan kamshi wadda suka shirya. 2Sai suka samu dutsen a mirgine shi daga kabarin. 3Suka shiga ciki, amma ba su sami jikin Ubangiji Yesu ba.

4Ya faru kuwa, yayin da suke a rikice game da wannan, ba zato, mutane guda biyu suka tsaya a gabansu da tufafi masu walkiya. 5Sa'adda matan suka sunkuyar da kansu kasa domin tsoro, suka ce wa matan, "Don me kuke neman mai rai ciki matattatu?
6Baya nan, amma ya tashi! Ku tuna fa yadda ya yi maku magana tun sa'adda ya ke Galili, 7cewa za a ba da Dan Mutum ga mutane masu zunubi su kuma giciye shi, a rana ta uku, zai tashi kuma"
8Sai matan suka tuna da kalmominsa, 9suka koma daga kabarin sai suka gaya wa sha dayan wadannan abubuwan da dukan sauran. 10Su Maryamu Magadaliya, Yuwana, Maryamu uwar Yakubu, da sauran matan da ke tare da su suka ba manzanni rohoton wadannan abubuwan.
11Amma manzannin suka dauki maganar kamar ba ta da amfani, kuma ba su bada gaskiya ga matan ba. 12Duk da haka Bitrus ya tashi, sai ya gudu zuwa kabarin, ya sunkuya yana kallon ciki, sai ya gan likaftani linin kadai. Sa'annan Bitrus ya tafi gidansa, yana ta mamakin abinda ya faru.
13A ranan nan, sai ga biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani kauye suna Imawus, wanda nisansa kimanin mil ne daga Urushalima. 14Suna tattaunawa da junansu game da dukan abubuwan da suka faru.
15Sai ya zama da cewa, sa'adda su ke tattaunawa tare da tambayoyi, sai Yesu da kansa ya matsa kusa yana tafiya tare da su. 16Amma idanunsu basu iya ganewa da shi ba.
17Yesu ya ce masu, "Menene ku ke magana akai sa'adda ku ke tafiya?" Suka tsaya a wurin suna bakin ciki. 18Daya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya amsa masa, "Kai ne kadai mutumin da ke Urushalima wanda bai san abubuwan da suka faru a can a wannan kwanakin ba?"
19Yesu ya ce masu, "Wadanne abubuwa?" Suka amsa masa, "Abubuwa game da Yesu ba Nazarat, wanda ya ke annabi ne, mai manyan ayuka da kalmomi daga Allah da kuma mutane. 20Da yadda manyan firistoci da masu mulkinmu suka bada shi domin a hukunta shi ga mutuwa a kuma giciye shi.
21Amma mun yi begen cewa shine wanda za ya yantar da Isra'ila. I, bayan wannan kuma, yanzu kwana uku kenan tunda wadannan abubuwan suka faru.
22Amma har'ila yau, wadansu mata da ke tare da mu sun yi mana abin al'ajabi, da suka kasance a kabarin tunda sassafe. 23Sa'adda ba su sami jikinsa ba, suka zo, da cewa su ma sun ga wahayin mala'iku wadanda suka ce masu ya na da rai. 24Wasu maza wadanda ke tare da mu suka tafi kabarin, suka tarar da shi kamar yadda matan suka fada. Amma ba su ganshi ba."
25Yesu ya ce masu, "Ku mutane masu wauta da marasa ba da gaskiya ga abin da annabawa suka fada! 26Bai zama dole ne Almasihu ya sha wahalan wadannan abubuwan ba, ya kuma shiga cikin daukakarsa?" 27Sa'annan da farko daga Musa da har zuwa dukan annabawa, Yesu ya fasara masu duka abubuwa da ke game da kansa a dukan littattafai.
28Da suka yi kusa da kauyen, inda suke tafiya, ko da yake Yesu ya yi kamar zai wuce su. 29Amma suka tilasta shi, cewa, "Ka zauna da mu, gama yamma ta yi kusa rana kuma ta kusa karewa." Sai Yesu ya tafi ya zauna da su.
30Ya faru cewa, sa'adda ya zauna tare da su domin ya ci abinci, sai ya dauki gurasan, ya albarkace shi, ya kakkarya, sai ya ba su. 31Sa'annan idanunsu suka bude, da suka gane shi, sai ya bace daga garesu, 32Suka ce wa junansu, ashe zuciyarmu ba ta yi kuna a cikinmu ba, sa'adda yake magana da mu a hanya, sa'adda ya bude mana littattafai?"
33Suka tashi a wancan sa'a, sai suka koma Urushalima. Suka sami sha dayan nan tare, da wadanda suke tare da su, 34cewa, "Lalle ne Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman." 35Sai suka fadi abubuwan da suka faru a hanya, da yadda aka bayyana masu Yesu sa'adda ya kakkarya gurasa.
36Sa'adda suke fadin wadannan abubuwan, sai Yesu ya tsaya a sakaninsu, sai ya ce masu, "Salama a gareku." 37Amma suka firgita suna cike da tsoro, suna tsammani sun ga fatalwa.
38Yesu ya ce masu, don me ku ke damuwa? Don me tambayoyi ke tasowa a zuciyarku? 39Duba hannayena da kafafuna, cewa nine da kaina. Taba ni ku gani. Gama ruhu ba shi da jiki da kashi, kamar yadda ku ka ga nake da su." 40Bayan da ya fadi wannan, sai ya nuna masu hannayensa da kafafunsa.
41Sa'adda suke cike da farin ciki, da mamaki, Yesu ya ce masu, "Kuna da wani abinci?" 42Sai suka bashi gasasshen kifi. 43Yesu ya karba, ya ci a gabansu.
44Sai ya ce masu, "Sa'adda nake tare da ku na gaya maku cewa duka abin da aka rubuta a cikin dokokin Musa da na annabawa da Zabura dole su cika."
45Sai ya bude hankalinsu, saboda su gane littattafai. 46Ya ce masu, "A rubuce yake, cewa Almasihu za ya sha wuya, zai tashi kuma daga matattu a rana ta uku. 47Ku yi wa'azin tuba da gafarar zunubai a cikin sunansa ga dukan al'ummai, ku fara daga Urushalima.
48Ku shaidu ne ga wadannan abubuwan. 49Duba, ina aiko da alkawarin Ubana a kanku. Amma ku jira a birni, sai an suturta ku da iko daga sama."
50Sa'annan Yesu ya tafi tare da su har sai da suka kai kusa da Betanya. Sai ya daga hannunsa ya albarkace su. 51Ya zama sa'adda yake sa masu albarka, ya bar su sai aka dauke shi zuwa cikin sama.
52Sai suka yi masa sujada, suka komo Urushalima da murna mai yawa. 53Kullayaumin suna cikin haikali, suna albarkatar Allah.

Yahaya

1

1A cikin farko akwai Kalma, Kalmar kuma tana tare da Allah, wannan Kalma kuwa Allah ne. 2Shi kuwa tare da Allah yake tun farko. 3Dukan abu ta wurinsa aka yi su, babu abin da aka halitta sai ta wurin sa.

4A cikinsa rai ya ke, kuma wannan rai ya zama haske ga dukan mutane. 5Hasken ya haskaka a cikin duhu, kuma duhun bai rinjaye shi ba.
6Akwai wani mutum wanda Allah ya aiko, mai suna Yahaya. 7Ya zo a matsayin mai ba da shaida game da hasken, domin kowa ya ba da gaskiya ta wurinsa. 8Ba Yahaya ne hasken ba, amma ya zo ne domin ya shaida hasken.
9Wannan shine haske na gaskiya mai ba da haske ga dukan mutane, da ke zuwa cikin duniya.
10Yana cikin duniya, kuma an halicci duniya ta wurinsa, amma duniya bata san shi ba. 11Ya zo wurin nasa, amma nasa basu karbe shi ba.
12Amma duk iyakar wadanda suka karbe shi, suka kuma ba da gaskiya ga sunansa, ya ba su 'yanci su zama 'ya'yan Allah. 13Wadanda aka haife su ba ta wurin jini ba, ko ta wurin nufin jiki, ko nufin mutum, amma ta wurin Allah.
14Kalmar kuma ya zama jiki ya zauna cikin mu. Mun ga daukakarsa, daukaka irin ta makadaici shi kadai wanda ya zo daga Uban, cike da alheri da gaskiya. 15Yahaya ya yi shaida akansa yana kira da karfi, cewa, "Wannan shine wanda na yi magana a kansa cewa, 'Shi wanda ke zuwa bayana, ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'"
16Domin daga cikarsa ne muka karbi alheri akan alheri. 17Gama shari'a ta zo daga wurin Musa. Alheri da gaskiya sun zo ta wurin Yesu Almasihu. 18Babu lokacin da wani ya taba ganin Allah, shi wanda shi kadai ne Allah, wanda ke jingine da kirjin Uba, shi ya bayyana shi.
19Wannan ita ce shaidar Yahaya sa'adda Yahudawa suka aika da Firistoci da Lawiyawa zuwa gareshi don su tambaye shi, "Wanene kai?" 20Ya fada dalla dalla, kuma bai musunta ba, yana amsa masu cewa, "ba nine Almasihu ba." 21Sai suka tambaye shi, "To kai wanene? Kai Iliya ne?" Yace, "Ba ni ba ne." Suka ce, "Kai ne anabin?" Ya amsa, "A'a".
22Sai suka ce masa, "Kai wanene, domin mu bada amsa ga wadanda suka aiko mu? Me kake fadi game da kanka?" 23Yace, "Ni murya ne, da ke kira cikin jeji, 'Ku daidaita hanyar Ubangiji,' kamar yadda annabi Ishaya ya fada."
24Su wadanda aka aika daga wurin Farisawa suke. Sai suka tambaye shi cewa, 25"To don me kake baftisma idan kai ba Almasihu bane, ko Iliya, ko annabin?".
26Yahaya ya amsa masu, cewa, "Ina baftisma ne da ruwa. Amma a cikinku akwai wani tsaye wanda ba ku sani ba, 27shi wanda ke zuwa bayana, wanda ko igiyar takalminsa ban isa in kwance ba." 28Wadannan abubuwa sun faru ne a Baitanya, a dayan ketaren Urdun, a wurin da Yahaya ke Baftisma.
29Washegari, Yahaya ya ga Yesu yana zuwa wurinsa ya ce, "Duba, ga Dan Ragon Allah wanda ke dauke zunubin duniya! 30Wannan shine wanda na fada maku cewa, "Shi wanda ke zuwa bayana ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.' 31Ban san shi ba, amma saboda a bayyana shi ga Isra'ila ne nazo ina baftisma da ruwa."
32Yahaya ya shaida, cewa, "Na ga Ruhu yana saukowa kamar kurciya daga sama, ya kuma zauna a kansa. 33Ban gane shi ba, amma shi wanda ya aiko ni in yi baftisma cikin ruwa ya fada mani cewa, 'duk wanda ka ga Ruhun ya sauka kuma ya zauna a kansa, shine wanda ke yin baftisma cikin Ruhu mai tsarki.' 34Na gani, na kuma shaida cewa wannan shine Dan Allah."
35Kuma, washegari, da Yahaya na tsaye da biyu daga cikin almajiransa, 36suka ga Yesu na wucewa, sai Yahaya ya ce, "Duba, ga Dan rago na Allah!"
37Sai almajiransa biyu suka ji ya fadi haka, suka kuwa bi Yesu. 38Da Yesu ya waiwaya ya gan su suna bin sa, sai ya ce masu, "Me kuke so?" Suka amsa, "Rabbi (wato 'Mallam'), ina kake da zama?" 39Yace masu, "Zo ku gani." Sai suka zo suka ga inda yake zama; suka zauna da shi ranan nan, gama wajen sa'a ta goma ne.
40Daya daga cikin wadanda suka ji maganar Yahaya suka kuma bi Yesu shine Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus. 41Ya fara neman dan'uwansa Siman yace masa, "Mun sami Almasihu" (wanda ake kira 'Kristi'). 42Ya kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi yace, "Kai ne Siman dan Yahaya. Za a kira ka Kefas," (ma'ana, 'Bitrus').
43Washegari, da Yesu yana shirin tafiya zuwa Galili, sai ya sami Filibus, ya ce masa, "ka biyo ni." 44Filibus dan asalin Baitsaida ne, garin Andarawus da Bitrus. 45Filibus ya sami Natana'ilu yace masa, "Mun same shi, shi wanda Musa ya rubuta shi a cikin attaura, da annabawa: Yesu Dan Yusufu, Ba-Nazarat."
46Natana'ilu ya ce masa, "za a iya samun wani abu nagari a Nazarat?" Filibus yace masa, "Zo ka gani." 47Yesu ya ga Natana'ilu yana zuwa wurinsa sai yayi magana game da shi, "Duba, Ba-Isra'ile na hakika wanda babu yaudara a cikinsa." 48Natana'ilu yace masa, "Ta yaya ka san ni?" Sai Yesu ya amsa masa yace, "Tun kafin Filibus ya kira ka, sa'adda kake a gindin baure, na gan ka."
49Natana'ilu ya amsa, "Rabbi, Kai Dan Allah ne! Kai Sarkin Isra'ila ne!" 50Yesu ya amsa masa yace, "Don na ce maka, 'Na gan ka a gindin Baure', ka gaskanta? Za ka ga abubuwa da suka fi wannan girma." 51Sai yace, 'Hakika, hakika ina gaya maka, zaka ga sammai a bude, mala'ikun Allah kuma suna hawa suna sauka akan Dan Mutum."

2

1Bayan kwana uku, akwai aure a Kana ta Galili, mahaifiyar Yesu kuma tana wurin. 2An gayyaci Yesu da almajiransa zuwa auren.

3Da ruwan inabin ya kare, maihafiyar Yasu tace masa, "basu da ruwan inabi." 4Yesu yace mata, "Mace, me yasa kika zo wurina? Lokaci na bai yi ba tukuna". 5Maihafiyarsa tace wa ma'aikatan, "Ku yi duk abin da yace maku."
6To akwai randunan ruwa na dutse guda shidda a wurin wadanda Yahudawa ke amfani da su domin al'adansu na tsarkakewa, kowace zata iya daukar durom guda. 7Yesu yace masu, "Cika randunan da ruwa". Sai suka cika randunan makil. 8Sai yace wa ma'aikatan, "Ku diba daga ciki ku kai wa shugaban biki." Sai suka yi hakannan.
9Shugaban bikin ya dandana ruwan da ya zama ruwan inabin, amma bai san inda ya fito ba (amma ma'aikatan wadanda suka jawo ruwan sun sani). Sai ya kira ango 10yace masa, "Kowane mutum yakan raba ruwan inabi mai kyau da farko, kafin mai arhar bayan an shanye mai kyaun. Amma kai ka ajiye mai kyaun sai yanzu."
11Wannan alama ta farko ce da Yesu yayi a Kana ta Galili, ya kuma bayyana daukakarsa, almajiransa kuma suka gaskata da shi.
12Bayan wannan, Yesu, da mahaifiyarsa, da 'yan'uwansa da almajiransa suka tafi Kafarnahum, kuma suka zauna can wasu 'yan kwanaki.
13To idin ketarewa na Yahudawa ya kusato, Yesu kuwa ya wuce zuwa Urushalima. 14Ya iske wadanda suke sayar da shanu da tumaki da tantabaru, masu canjin kudi kuma na zaune a wurin.
15Sai yayi tsumingiya da igiyoyi ya kore su duka daga cikin haikalin, duk da tumakin da shanun. Sai ya watsar da sulallan masu canjin kudin ya birkitar da teburansu. 16Yace wa masu sayar da tantabaru, "Ku fitar da wadannan abubuwa daga nan. Ku daina maida gidan Ubana wurin kasuwanci."
17Almajiransa suka tuna a rubuce yake, "Himma domin gidanka za ta cinye ni." 18Sai shugabannin Yahudawa suka amsa suka ce masa, "Wace alama za ka nuna mana, da shike kana yin wadannan abubuwan?" 19Yesu ya amsa, "Ku rushe wannan haikali, kuma a cikin kwana uku zan gina shi."
20Sai shugabanin Yahudawa suka ce, "An dauki shekaru arba'in da shidda kamin a gama gina wannan haikalin, za ka dau kwanaki uku kadai wajen gina shi?" 21Amma yana nufin haikali na jikinsa ne. 22Bayan da aka tashe shi daga matattu, sai almajiransa suka tuna ya fadi haka, suka kuma ba da gaskiya ga nassi da wannan kalami da Yesu ya fada.
23Kuma, da yana Urushalima a idin ketarewa, a lokacin idin, mutane da yawa suka gaskata ga sunansa, sa'adda suka ga alamun da ya yi. 24Amma Yesu bai yadda da su ba domin ya san su duka, 25saboda baya bukatar wani ya shaida masa game da mutum, domin ya san abinda ke cikin sa.

3

1akwai wani Bafarise da ake kira Nikodimu, shugaba a cikin Yahudawa. 2Wannan mutum ya zo wurin Yesu da dare ya ce masa, "Rabbi, mun sani cewa kai malami ne da kazo daga wurin Allah, gama ba wanda zai iya yin wadannan alamu da kake yi sai idan Allah na tare da shi."

3Yesu ya amsa masa, "Hakika, hakika, idan ba a sake haifuwar mutum ba, ba zai iya ganin mulkin Allah ba." 4Nikodimu ya ce masa, "Yaya za a sake haifuwar mutum bayan ya tsufa? Ba zai iya sake shiga cikin cikin uwarsa kuma a haife shi ba, zai iya?"
5Yesu ya amsa, "Hakika, hakika, idan ba a haifi mutum da ruwa da kuma Ruhu ba, ba zai iya shiga cikin mulkin Allah ba. 6Abin da aka haifa ta wurin jiki, jiki ne, kuma abin da aka haifa ta wurin Ruhu, Ruhu ne.
7Kada ka yi mamaki don na ce maka, 'dole a maya haifuwar ka.' 8Iska takan hura duk inda ta ga dama. Ka kan ji motsin ta, amma ba ka san inda ta fito ko inda za ta tafi ba. Haka duk wanda aka haifa daga Ruhu."
9Nikodimu ya amsa yace masa, "Yaya wannan zai yiwu?" 10Yesu ya amsa yace masa, "Kai malami ne a Israila amma ba ka san wadannan al'amura ba? 11Hakika, hakika, ina gaya maka, muna fadin abubuwan da muka sani, kuma muna shaida abubuwan da muka gani. Duk da haka ba ku karbi shaidar mu ba.
12Idan na gaya maka abubuwan da ke na duniya amma baka gaskata ba, to yaya zaka gaskata idan na gaya maka abubuwa na sama? 13Babu wanda ya taba hawa zuwa sama sai dai shi wanda ya sauko daga sama: wato Dan Mutum.
14Kamar yadda Musa ya ta da maciji a jeji, haka ma dole a ta da Dan Mutum 15domin dukan wadanda suka bada gaskiya gareshi su sami rai na har abada.
16Gama Allah ya kaunaci duniya sosai, har ya ba da makadaicin Dansa, domin duk wanda ya bada gaskiya gareshi, kada ya mutu, amma ya samu rai madawwami. 17Gama Allah bai aiko da Dansa cikin duniya domin ya kayar da duniya ba, amma domin a ceci duniya ta wurin sa. 18Duk wanda ya bada gaskiya gare shi ba a kayar da shi ba, amma duk wanda bai bada gaskiya gare shi ba an riga an kayar da shi, domin bai bada gaskiya ga sunan wannan da shi kadai ne Dan Allah ba.
19Wannan shi ne dalilin shari'ar, domin haske ya zo duniya, amma mutane suka kaunaci duhu fiye da hasken, sabili da ayyukan su na mugunta ne. 20Domin duk wanda ke mugayen ayyuka ya ki haske, kuma baya zuwa wurin hasken domin kada ayyukansa su bayyanu. 21Sai dai duk wanda yake aikata gaskiya kan zo wurin hasken domin ayyukansa, da ake aiwatarwa ga Allah, su bayyanu.
22Bayan wannan, Yesu da almajiransa suka tafi kasar Yahudiya. A can ya dan zauna tare da su ya kuma yi Baftisma. 23Yahaya ma yana Baftisma a Ainon kusa da Salim domin akwai ruwa da yawa a can. Mutane na zuwa wurin sa yana masu Baftisma, 24domin a lokacin ba a jefa Yahaya a kurkuku ba tukuna.
25Sai gardama ta taso tsakanin almajiran Yahaya da wani Bayahude akan al'adun tsarkakewa. 26Suka je wurin Yahaya suka ce, "Rabbi, wanda yake tare da kai a dayan ketaren kogin Urdun, kuma ka shaida shi, duba, yana baftisma, kuma mutane duka suna zuwa wurin sa."
27Yahaya ya amsa, "Mutum ba zai iya samun wani abu ba sai an ba shi daga sama. 28Ku da kanku zaku shaida na ce, 'Ba ni ne Almasihu ba' amma amaimakon haka, 'an aiko ni kafin shi.'
29Amaryar ta angon ce. Yanzu abokin angon, wanda ke tsaye yana saurarensa, yana murna sosai saboda muryan angon. Murnata ta cika domin wannan. 30Dole shi ya karu, ni kuma in ragu.
31Shi wanda ya fito daga sama ya fi kowa. Shi Wanda ya zo daga duniya, na duniya ne, kuma game da duniya yake magana. Shi wanda ya fito daga sama yana saman kowa. 32Ya shaida abubuwan da ya ji ya kuma gani, amma babu wanda ya karbi shaidarsa. 33Duk wanda ya karbi shaidarsa ya tabbatar Allah gaskiya ne.
34Domin duk wanda Allah ya aika kan yi magana da kalmomin Allah. Domin bai bada Ruhun da ma'auni ba. 35Uban ya kaunaci Dan, ya kuma ba da dukan komai a hanunsa. 36Shi wanda ya bada gaskiya ga Dan ya na da rai madawwami, amma wanda ya ki yiwa Dan biyayya ba zai ga rai ba, amma fushin Allah na kansa.

4

1Da Yesu ya sani cewa Farisawa sun ji cewa yana samun almajirai yana kuma yi masu baftisma fiye da Yahaya 2(ko da shike ba Yesu da kansa ke yin baftismar ba, amma almajiransa ne), 3ya bar Yahudiya ya koma Galili.

4Amma ya zamar masa dole ya ratsa ta Samariya. 5Ya zo wani birnin Samariya, mai suna Sika, kusa da filin da Yakubu ya ba dansa Yusufu.
6Rijiyar Yakubu na wurin. Da Yesu ya gaji da tafiyarsa sai ya zauna gefen rijiyar. Kusan karfe goma sha biyu na rana ne. 7Wata mace, Ba-Samariya ta zo domin ta dibi ruwa, sai Yesu ya ce mata, "Ba ni ruwa in sha." 8Gama almajiransa sun tafi cikin gari don sayen abinci.
9Sai ba-Samariyar tace masa, "Yaya kai da kake Bayahude kake tambaya ta ruwan sha, ni da nike 'yar Samariya?" Domin Yahudawa ba su harka da Samariyawa. 10Sai Yesu ya amsa yace mata, "In da kin san kyautar Allah, da shi wanda yake ce da ke, 'Ba ni ruwan sha,' da kin roke shi, sai kuma ya ba ki ruwan rai."
11Matar tace masa, "Mallam, ga shi ba ka da guga, kuma rijiyar tana da zurfi. Ina za ka samu ruwan rai? 12Ai ba ka fi Ubanmu Yakubu ba, ko ka fi shi, shi wanda ya ba mu rijiyar, shi kansa kuma ya sha daga cikin ta, haka kuma 'ya'yansa da shanunsa?"
13Yesu ya amsa yace mata, "duk wanda ya sha daga wannan ruwan zai sake jin kishi, 14amma duk wanda ya sha daga ruwa da zan ba shi ba zai sake jin kishi ba. Maimakon haka, ruwan da zan bashi zai zama mabulbular ruwa a cikinsa wanda ke bulbula zuwa rai madawwami."
15Matar tace masa, "Mallam, ka ba ni wannan ruwa yadda ba zan kara jin kishi ba ba kuma sai na zo nan don in dibi ruwa ba." 16Yesu ya ce mata, "Je, ki kira maigidanki ku zo nan tare."
17Matar ta amsa tace masa, "Ba ni da miji." Yesu yace, "Kin fadi daidai da kika ce, 'ba ni da miji,' 18domin kin auri mazaje har biyar, kuma wanda kike da shi yanzu ba mijin ki bane. Abinda kika fada gaskiya ne."
19Matar tace masa, "Mallam, Na ga kai annabi ne. 20Ubaninmu sun yi sujada a wannan dutse, amma kun ce Urushalima ce wurin da ya kamata mutane su yi sujada."
21Yesu ya ce mata, "Mace, ki gaskata ni, cewa lokaci na zuwa wanda ba za ku yi wa Uban sujada ba ko akan wannan dutse ko a Urushalima. 22Ku kuna bauta wa abinda ba ku sani ba. Mu muna bauta wa abinda muka sani, gama ceto daga Yahudawa yake.
23Sai dai, sa'a tana zuwa, har ma ta yi, wadda masu sujada na gaskiya za su yi wa Uba sujada a cikin ruhu da gaskiya, domin irin wadannan ne Uban ke nema su zama masu yi masa sujada. 24Allah Ruhu ne, kuma mutanen da ke yi masa sujada, dole su yi sujada cikin ruhu da gaskiya."
25Matar ta ce masa, "Na san Almasihu na zuwa (wanda ake kira Kristi). Sa'adda ya zo, zai bayyana mana kowane abu. 26Yesu ya ce mata, "Ni ne shi, wanda ke yi maki magana."
27A daidai wannan lokaci, almajiransa suka dawo. Suna ta mamakin dalilin da yasa yake magana da mace, amma babu wanda yace, "Me kake so?" Ko kuma, "Don me ka ke magana da ita?"
28Sai matar ta bar tulunta, ta koma cikin gari, tace wa mutanen, 29"Ku zo ku ga wani mutum wanda ya gaya mani duk wani abu da na taba yi. Wannan dai ba Almasihun bane, ko kuwa?" 30Suka bar garin suka zo wurinsa.
31A wannan lokacin, almajiransa suna rokansa, cewa, "Mallam, ka ci." 32Amma ya ce masu, "ina da abinci da ba ku san komai akai ba." 33Sai almajiran suka ce da junansu, "Babu wanda ya kawo masa wani abu ya ci, ko akwai ne?"
34Yesu ya ce masu, "Abincina shine in yi nufin wanda ya aiko ni, in kuma cika aikinsa. 35Ba ku kan ce, 'akwai wata hudu tukuna kafin girbi ya zo ba?' Ina gaya maku, daga idanunku ku ga gonakin, sun rigaya sun isa girbi. 36Shi wanda ke girbi yakan karbi sakamako ya kuma tattara amfanin gona zuwa rai na har abada, ta haka shi mai shuka da shi mai girbi za su yi farinciki tare.
37Gama cikin wannan maganar take, 'Wani na shuka, wani kuma na girbi.' 38Na aike ku ku yi girbin abinda ba ku yi aiki a kai ba. Wandansu sun yi aiki, ku kuma kun shiga cikin wahalarsu.
39Yawancin Samariyawan da ke wannan birni suka gaskata da shi sabili da labarin matar data bada shaida, "Ya gaya mani duk abinda na taba yi." 40To sa'adda Samariyawa suka zo wurinsa, sai suka roke shi ya zauna tare da su, ya kuwa zauna wurin kwana biyu.
41Wasu da dama kuma suka gaskata domin maganarsa. 42Suka cewa matar, "Mun bada gaskiya, ba saboda maganar ki kadai ba, amma mu kanmu munji, yanzu kuma mun sani cewa wannan lallai shine mai ceton duniya."
43Bayan wadannan kwana biyu, ya bar wurin zuwa Galili. 44Domin Yesu da kansa yace, ba a girmama annabi a kasarsa. 45Da ya zo Galili, Galiliyawan suka marabce shi. Sun ga dukan abubuwan da ya yi a Urushalima wurin idin, domin su ma sun je idin.
46Kuma ya koma Kana ta Galili inda ya mayar da ruwa zuwa ruwan inabi. Akwai wani ma'aikacin fada wanda dansa na rashin lafiya a Kafarnahum. 47Da ya ji cewa Yesu ya bar Yahudiya ya koma Galili, sai ya tafi wurin Yesu ya roke shi ya sauko ya warka da dansa wanda ke bakin mutuwa.
48Yesu yace masa, "Idan ba ku ga alamu da mu'ujizai ba, ba za ku gaskata ba." 49Ma'aikacin ya ce masa, "Mallam, ka sauko kafin da na ya mutu." 50Yesu yace masa, "Je ka. Dan ka ya rayu." Mutumin ya gaskata maganar da Yesu ya gaya masa, Sai yayi tafiyarsa.
51Yayin da yake sauka kasa, bayinsa suka same shi, suna cewa, danka yana raye. 52Sai ya tambaye su sa'ar da ya fara samun sauki. Suka amsa masa, "Jiya a sa'a ta bakwai zazabin ya bar shi."
53Sai Uban ya gane cewa wannan sa'a ce Yesu ya ce masa, "Jeka, danka na raye." Sabili da haka, shi da dukan gidansa suka bada gaskiya. 54Wannan ce alama ta biyu da Yesu ya yi bayan da ya bar Yahudiya zuwa Galili.

5

1Bayan haka akwai idi na yahudawa, kuma Yesu ya tafi Urashalima. 2To a cikin Urashilima kusa da kofar tumaki akwai tabki, wanda ake kira Baitasda da harshen Ibraniyanci, yana da shirayi biyar. 3Taron mutane dayawa masu ciwo da, makafi da guragu da shanyayyu suna kwance a wurin. 142

5Akwai wani mutum a bakin tabki yana kwance yana da rashin lafiya har shekara talatin da takwas. 6Da Yesu ya gan shi yana kwance a wurin sai ya gane ya dade a wurin, sai ya ce masa, "Ko kana so ka warke?"
7Sai mai rashin lafiyar ya amsa ya ce, "Malam, bani da kowa da zai sa ni a cikin tabkin idan ruwan ya motsa. Yayinda na ke kokari sai wani ya riga ni." 8Yesu ya ce masa," Ka tashi ka dauki shimfidarka ka tafi."
9Nan dan nan Mutumin ya warke, ya dauki shimfidarsa ya tafi. Ranar kuwa Asabar ce.
10Sai Yahudawa suka ce da wanda aka warkar din, "Ai, Asabar ce, bai kuwa halatta ka dauki shimfidarka ba." 11Sai ya amsa ya ce, "Ai wanda ya warkar da ni, shine ya ce mani 'Dauki shimfidarka, ka tafi."
12Suka tambaye shi, "wane mutum ne ya ce maka, 'Dauki shimfidar ka yi tafiya'?" 13Sai dai, shi wanda aka warka din, ba san ko wanene ya warkar da shi ba, domin Yesu ya riga ya tafi aboye, saboda akwai taro a wurin.
14Bayan haka, Yesu ya same shi a Haikalin, ya ce masa, "ka ga fa, ka warke. To, kada ka kara yin zunubi don kada wani abu da ya fi wannan muni ya same ka." 15Sai mutumin ya tafi ya gaya wa Yahuduwa cewa Yesu ne ya warkar da shi.
16To saboda haka Yahudawa suka fara tsanantawa Yesu, don ya yi wadannan abubuwa ran Asabar. 17Yesu kuwa ya amsa masu ya ce, "Ubana yana aiki har yanzu, ni ma ina aiki." 18Saboda haka, Yahudawa suka kara nema su kashe shi ba don ya keta Asabar kadai ba, amma kuma domin ya ce Allah Ubansa ne, wato yana maida kansa dai-dai da Allah.
19Yesu ya amsa masu ya ce, hakika hakika, ina gaya maku, Dan ba ya yin kome shi kadai, sai abin da ya ga Uba yana yi. 20Domin Uban na kaunar Dan, yana kuma nuna masa dukan abinda shi da kansa yake yi, kuma zai nuna masa abubuwan da suka fi wadannan, domin ku yi mamaki.
21Gama kamar yadda Uba yakan tada matattu ya kuma basu rai, haka Dan ma yake bada rai ga duk wanda ya nufa. 22Gama Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya damka dukan hukunci ga Dan, 23domin kowa ya girmama Dan, kamar yadda suke girmama Uban. Shi wanda ba ya girmama Dan, ba ya girmama Uban da ya aiko shi.
24Hakika, hakika, duk mai jin Maganata, yana kuma gaskata wanda ya aiko ni, yana da rai madawwami ba kuma za a kashe shi ba, domin ya ratse daga mutuwa zuwa rai,.
25Hakika hakika, ina gaya maku, lokaci na zuwa, har ma ya yi da matattatu za su ji muryar Dan Allah, wadanda suka ji kuwa za su rayu.
26Kammar yada Uba ya ke da rai a cikinsa, haka ya ba Dan don ya zama da rai cikin kansa. 27Uban ya kuma ba Dan ikon zartar da hukunci, saboda shi ne Dan Mutum.
28Kada ku yi mamakin wannan, domin lokaci na zuwa da duk wadanda suke kaburbura za su ji muryarsa, 29su kuma fito: wadanda suka aikata nagarta zawa tashi na rai, wadanda suka aikata mugunta kuwa zuwa tashi na hukunci.
30Ba na iya yin kome ni da kai na. Yadda na ke ji, haka nake yin hukunci, Hukunci na kuwa na adalci ne, domin ba nufin kaina nake bi ba, sai dai nufin wanda ya aiko ni. 31Idan zan yi shaida game da kaina, shaidata baza ta zama gaskiya ba. 32Akwai wani wanda ya ke bada shaida game da ni, na kuwa sani shaidar da yake bayarwa game da ni gaskiya ce.
33Kun aika zuwa wurin Yahaya, shi kuma ya yi shaidar gaskiya. 34Duk da haka shaidar da na karba bata mutum bace. Na fadi wadanan abubuwa domin ku sami ceto. 35Yahaya fitila ne mai ci, mai haske ne kuma, kun yarda ku yi farinciki da haskensa dan lokaci kadan.
36Amma shaidar da ni ke da ita ta fi ta Yahaya karfi. Domin ayyukan da Uba ya bani ni in yi, wato ainihin ayyukan da nake yi, su ne suke shaida ta cewa, Uba ne ya aiko ni. 37Uba wanda ya aiko ni, shi da kansa ya shaide ni. Ba ku taba jin muryar sa ba, ko ganin kamanninsa. 38Maganarsa kuwa ba ta zaune a zuciyarku, domin baku gaskata da wanda ya aiko ni ba.
39Kuna nazarin littattafai, don a tsammaninku a cikinsu za ku sami rai Madawwami, alhali kuwa su ne suke shaidata. 40kuma baku niyyar zuwa wurina domin ku sami rai.
41Ba na karbar yabo daga wurin mutane, 42amma na sani baku da kaunar Allah a zuciyarku.
43Na zo a cikin sunan Ubana, amma ba ku karbe ni ba. Idan wani ya zo da sunan kansa, za ku karbe shi. 44Ta yaya za ku ba da gaskiya, ku da kuke karban yabo daga junanku, amma ba ku neman yabon dake zuwa daga wurin Allah?
45Kada ku yi tunani zan zarge ku a wurin Uba. Mai zargin ku shine Musa, wanda kuka sa begenku a cikin sa. 46Inda kun gaskata Musa, da kun gaskata da ni domin ya yi rubutu game da ni. 47Idan kuwa ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, ta yaya za ku gaskata maganata?"


1Mafi kyawun kwafin tsoffin ba su da jumlar, suna jira a dama ruwan .
2Mafi kyawun kwafin kwafi ba su da aya 4, Gama mala'ikan Ubangiji kan sabko a cikin tabkin ya dama ruwan, wanda ya fara taba ruwan sai ya warke komai cutar da yake da ita .

6

1Bayan waddannan abubuwa, Yesu ya ketare tekun Galili, wanda a ke kira tekun Tibariya. 2Sai taro mai yawa suka bi shi domin suna ganin alamu da yake yi akan marasa lafiya. 3Sai Yesu ya hau dutse ya zauna a can tare da almajiransa.

4(Kuma da idin Ketarewa, wato idin Yahudawa, ya kusato.) 5Da Yesu ya daga kai sai ya ga babban taro yana zuwa wurinsa, sai ya ce ma Filibus, "Ina za mu sayi gurasar da Mutanen nan za su ci?" 6(Ya fadi haka ne domin ya gwada shi, saboda shi kansa ya san abin da zai yi.)
7Filibus ya amsa masa, "gurasar dinari biyu ma ba zata ishi kowannensu ya samu ko kadan ba." 8Daya daga cikin almajiransa, wato Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus, ya ce masa, 9"Ga wani dan yaro nan da dunkule biyar na sha'ir, da kifi biyu. Amma menene wadannan za su yi wa mutane masu yawa?"
10Yesu ya ce, "ku sa mutane su zauna."( wurin kuwa akwai ciyawa.) Sai mazajen suka zauna, sun kai wajen dubu biyar. 11Sai Yesu ya dauki gurasar, bayan da ya yi godiya, sai ya rarraba wa wadanda suke zaune. Haka kuma ya rarraba kifin gwargwadon abin da zai ishe su. 12Da Mutanen suka ci suka kuma koshi, sai ya ce wa almajiransa, ku tattara gutsattsarin da suka rage, kada ya zama asara."
13Sai suka cika kwanduna goma sha biyu da gutsattsarin gurasar nan biyar da ya rage bayan da kowa ya ci. 14Da jama'a suka ga alamar da ya yi, sai suka ce, "Hakika wannan shi ne annabin nan mai zuwa cikin duniya. 15"Da Yesu ya gane suna shirin zuwa su dauke shi da karfi da yaji su nada shi sarki, sai ya sake komawa kan dutsen da kansa.
16Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara teku. 17Suka shiga cikin jirgi, suka haye teku zuwa kafarnahum. (A lokacin duhu ya yi, Yesu kuwa bai riga ya iso wurinsu ba tukuna.) 18Iska mai karfin gaske tana kadawa, kuma tekun yana hargowa.
19Bayan da almajiran suka yi tuki na wajen kimanin mil ashirin da biyar ko talatin, sai suka hango Yesu yana tafiya a kan teku ya kuma kusa da jirgin, sai suka firgita. 20Amma ya ce masu, "Ni ne! kada ku firgita." 21Sa'an nan suka yarda suka karbe shi a cikin jirgin, kuma nan da nan jirgin ya kai gacci.
22Kashe gari, sauran taron da suke tsaye a dayan hayin tekun suka ga cewa babu wani jirgi a wajen sai dayan, Yesu kuma bai shiga ciki da almajiransa ba, amma almajiransa suka tafi su kadai. 23Sai dai, akwai wadansu jirage da suka zo daga Tibariya kusa da wurin da taron suka ci gurasa bayan da Ubangiji ya yi godiya.
24Sa'anda taron suka gane cewa Yesu da almajiransa ba su wurin, su da kansu su ka shiga cikin jiragen suka tafi Kafarnahum neman Yesu. 25Da suka same shi a hayin tekun, suka ce masa, "Mallam, yaushe ka zo nan?"
26Yesu ya amsa masu, da cewa, "hakika, kuna nema na ne, ba don kun ga alamu ba, amma domin kun ci gurasar nan kun koshi. 27Ku daina yin wahala a kan neman abinci mai lalacewa, sai dai a kan abinci mai dawwama wanda zai kaiku ga rai madawwami wanda Dan Mutum zai ba ku, domin Ubangiji Allah ya sa hatiminsa a kansa."
28Sai suka ce Masa, "Me za mu yi, domin mu aikata ayyukan Allah? 29Yesu ya amsa, "Wannan shi ne aikin Allah: wato ku gaskata da wanda ya aiko."
30Sai suka ce masa, "To wace alama za ka yi, don mu gani mu gaskata ka? 31Me za ka yi? Kakanninmu sun ci manna a jeji, kamar yadda aka rubuta, "Ya ba su gurasa daga sama su ci."
32Sa'an nan Yesu ya ce masu, "hakika, hakika, ina gaya maku ba Musa ne ya ba ku gurasa nan daga sama ba, amma Ubana ne ya baku gurasa ta gaskiya daga sama. 33Gurasar Allah itace mai saukowa daga sama mai kuma bada rai ga duniya," 34Sai suka ce masa, "Mallam, ka rika ba mu irin wannan gurasa kodayaushe."
35Yesu ya ce masu, "Ni ne gurasa mai ba da rai. Wanda ya zo wurina ba zai ji yunwa ba, wanda kuma ya gaskanta da ni ba zai kara jin kishi ba. 36Amma na gaya maku cewa, hakika kun gan ni, duk da haka ba ku ba da gaskiya ba. 37Duk wanda Uba ya bani zai zo gare ni, wanda kuwa ya zo gare ni ba zan kore shi ba ko kadan.
38Gama na sauko daga sama, ba domin in bi nufin kaina ba, sai dai nufin wanda ya aiko ni. 39Wannan shi ne nufin wanda ya aiko ni, kada in rasa ko daya daga cikin wadannan da ya bani, sai dai in tashe su a ranar karshe. 40Gama wannan shi ne nufin Ubana, duk wanda yake ganin Dan ya kuma gaskata da shi zai sami rai madawwami, ni kuma zan tashe shi a ranar karshe.
41Sai Yahudawa suka yi gunaguni akansa, domin ya ce, "Nine Gurasar da ta sauko daga sama." 42Suka ce, "Ba wannan ne Yesu Dan Yusufu, wanda Ubansa da Uwarsa mun san su ba? Ta yaya yanzu zai ce, 'Na ya sauko daga sama'?
43Yesu ya amsa, ya ce masu, "Kada ku yi gunaguni a junanku. 44Ba mai iya zuwa wurina sai dai in Uba wanda ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta karshe. 45A rubuce yake cikin litattafan anabawa cewa, 'Dukkansu Allah zai koya masu'. Duk wanda ya ji ya kuma koya daga wurin Uba, ya kan zo gare ni.
46Ba cewa wani ya taba ganin Uban ba, sai shi wanda yake daga wurin Allah - shine ya ga Uban. 47Hakika, hakika, wanda ya bada gaskiya, yana da rai Madawwami.
48Ni ne Gurasa ta rai. 49Ubanninku sun ci manna cikin jeji, suka kuma mutu.
50Ga gurasa da ta sauko daga sama, domin mutum ya ci daga cikinta ba kuwa zai mutu ba. 51Ni ne gurasa mai rai da ya sauko daga sama. Duk wanda ya ci daga gurasar, zai rayu har abada. Wannan gurasar da zan bayar jiki na ne don ceton duniya."
52Sai Yahudawa suka fusata a tsakanin junansu suka kuma fara gardama, cewa, "Yaya mutumin nan zai iya bamu naman jikinsa mu ci? 53Sai Yesu ya ce masu, "hakika, hakika, in ba ku ci naman jikin Dan mutum ba, ba ku kuma sha jininsa ba, ba za ku sami rai a cikin ku ba.
54Dukan wanda ya ci nama na ya kuma sha jinina yana da rai Madawwami, ni kuwa zan tashe shi a ranar karshe. 55Domin namana abinci ne na gaske, jinina kuma abin sha ne na gaskiya. 56Duk wanda ya ci namana, ya kuma sha jinina yana zamne a ciki na, ni kuma a cikinsa.
57Kamar yadda rayayyen Uba ya aiko ni, nake kuma rayuwa saboda Uban, haka ma wanda ya ci namana, zai rayu sabo da ni. 58Wannan itace gurasar da ta sauko daga sama, ba irin wadda Ubanninku suka ci suka mutu ba. Dukan wanda ya ci gurasar zai rayu har abada." 59Yesu ya fadi wadan nan abubuwa a cikin majami'a sa'ad da yake koyarwa a Kafarnahum.
60Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, "Wannan Magana yana da karfi, wa zai iya jinta?" 61Yesu, kuwa da yake ya sani a ransa da cewa almajiransa suna gunagunin wannan, sai ya ce masu, "Wannan ya zamar maku laifi?
62Yaya Ke nan in kun ga Dan Mutum yana hawa inda yake a da? 63Ruhu shine mai bayar da rai; Jiki ba ya amfana komai. Kalmomin da na fada maku ruhu ne, da kuma rai.
64Amma fa akwai wadansun ku da ba su ba da gaskiya ba. Domin tun farko Yesu ya san wadanda ba su ba da gaskiya ba, da kuma wanda zai bashe shi. 65Ya fada cewa, "shiyasa na gaya maku, ba mai iya zuwa wurina, sai ta wurin Uban."
66Bayan haka, da yawa daga cikin almajiransa suka koma da baya, ba su kara tafiya tare da shi ba. 67Sai Yesu ya ce wa goma sha biyun, "ku ba kwa so ku tafi, ko ba haka ba? 68Bitrus ya amsa masa ya ce, "Ya Ubangiji, gun wa za mu je? kai kake da maganar rai madawwami. 69Mu kwa mun gaskata mun kuma sani kai ne mai tsarkin nan na Allah."
70Yesu ya ce masu, "Ba ni na zabe ku, goma sha biyu ba, amma dayanku Iblis ne?" 71Wato yana magana akan Yahuda dan Siman Iskariyoti, shi kuwa daya daga cikin sha-biyun ne, wanda zai ba da Yesu.

7

1Bayan wadannan abubuwa Yesu ya zagaya cikin Gallili, saboda baya so ya shiga cikin Yahudiya domin Yahudawa suna shirin su kashe shi. 2To Idin Bukkoki na Yahudawa ya kusa.

3Sai 'yan'uwansa suka ce da shi, "ka tashi ka tafi Yahudiya, domin almajiranka su ga ayyukan da kake yi su ma. 4Ba wanda ya ke yin wani abu a boye idan dai yana so kowa da kowa ya san shi. Da yake ka na yin wadannan abubuwa sai ka nuna kan ka a fili ga duniya.
5Domin ko 'yan'uwansa ma basu bada gaskiya gare shi ba. 6Yesu ya ce dasu, "lokaci na bai yi ba tukuna, amma ku koyaushe lokacin ku ne. 7Duniya baza ta iya kin ku ba, amma ta ki ni saboda ina fadin cewa ayyukanta ba su da kyau.
8Ku ku je wurin idin, ni ba zan je wurin idin ba domin lokacina bai yi ba tukuna. 9Bayan da ya gaya masu wadannan abubuwa, ya tsaya a cikin Gallili.
10Amma bayan da 'yan'uwansa su ka tafi wurin idin shi ma ya tafi, amma a asirce ba a fili ba. 11Saboda Yahudawa suna neman sa a wurin idin, su na cewa "Ina yake?"
12Akwai maganganu dayawa a kansa cikin taron. Wadansu suna cewa, "shi mutumin kirki ne." Wadansu kuma suna cewa,"A'a yana karkatar da hankalin jama'a." 13Amma duk da haka ba wanda ya yi magana a fili a kansa saboda suna jin tsoron Yahudawa.
14Sa'anda aka kai rabin idin, sai Yesu ya shiga cikin haikali ya fara koyarwa. 15Yahudawa suna mamaki suna cewa,"Yaya aka yi wannan mutum ya sami ilimi dayawa haka? Shi kuwa bai je makaranta ba." 16Yesu ya ba su amsa ya ce,"Koyarwata ba tawa ba ce, amma ta wanda ya aiko ni ce."
17Idan wani yana so ya yi nufinsa, za ya gane koyarwannan ko daga wurin Allah ta zo, ko ko tawa ce ta kaina. 18Ko wanene yake maganar kansa, yana neman darajar kansa kenan, amma ko wanene ya nemi darajar wanda ya aiko ni, wannan mutum mai gaskiya ne, babu rashin adalci a cikin sa.
19Ba Musa ya baku dokoki ba? Amma duk da haka ba mai aikata dokokin. Me yasa ku ke so ku kashe ni? 20Taron suka ba shi amsa, "Ka na da aljani. Wanene yake so ya kashe ka?"
21Yesu ya amsa ya ce masu, "Nayi aiki daya, dukan ku kuna mamaki da shi. 22Musa ya baku kaciya, {ba kuwa daga Musa take ba, amma daga kakannin kakanni ta ke}, kuma a ranar Asabar kukan yi wa mutum kaciya.
23Idan mutum ya karbi kaciya ranar Asabar, domin kada a karya dokar Musa, don me kuka ji haushi na saboda na mai da mutum lafiyayye sarai ranar Asabar? 24Kada ku yi shari'a ta ganin ido, amma ku yi shari'a mai adalci."
25Wadansun su daga Urushalima suka ce, "wannan ba shine wannan da suke nema su kashe ba?" 26Kuma duba, yana magana a fili, sannan ba wanda ya ce da shi komai. Ba zai yiwu ba mahukunta su sani cewa wannan Kristi ne, ko ba haka ba? 27da haka, mun san inda wannan mutum ya fito. Amma sa'anda Kristi za ya zo, ba wanda zai san inda ya fito."
28Yesu yayi magana da karfi a haikali, yana koyarwa ya na cewa, "Kun san ni kuma kun san inda na fito. Ban zo domin kaina ba, amma wanda ya aiko ni mai gaskiya ne, ku kuwa baku san shi ba. 29Ni na san shi domin daga wurinsa na fito, kuma shine ya aiko ni."
30Suna kokari su kama shi, amma ba wanda ya iya sa masa hannu domin sa'arsa ba ta yi ba tukuna. 31Duk da haka wadansu dayawa a cikin taron suka bada gaskiya gare shi suka ce,"Sa'anda Kristi ya zo, zai yi alamu fiye da wadanda wannan mutum ya yi?" 32Farisawa suka ji tattarmukan suna yin rada a kan wadannan abubuwa game da Yesu, Sai manyan malamai da Farisawa su ka aika jami'ai su kama shi.
33Sa'annan Yesu yace ma su," jimawa kadan ina tare ku, sa'annan in tafi wurin wanda ya aiko ni. 34Za ku neme ni ba za ku same ni ba; inda na tafi, ba za ku iya zuwa ba."
35Yahudawa fa su ka cewa junan su, "Ina wannan mutum zai je inda ba za mu iya samun sa ba? Ko za ya tafi wurin Helinawa na warwatsuwa ya koyawa Helinawa? 36Wace kalma ya ke fadi haka, 'za ku neme ni amma ba za ku same ni ba; inda na tafi, ba za ku iya zuwa ba'?"
37To a rana ta karshe, babbar rana ta idin, Yesu ya mike ya yi magana da karfi cewa, "Idan kowa yana jin kishi, ya zo wuri na ya sha. 38Shi wanda ya bada gaskiya gare ni kamar yadda nassi ya fadi, daga cikin sa rafukan ruwa na rai za su bulbulo."
39Amma ya fadi haka a kan Ruhu, wanda wadanda suka bada gaskiya gare shi za su karba; ba a ba da Ruhun ba tukuna, saboda ba a rigaya an daukaka Yesu ba.
40Wadansu a cikin taron, sa'anda suka ji wadannan kalmomi, suka ce, "Wannan lallai annabi ne." 41Wadansu suka ce, "Wannan Almasihu ne." Amma wadansu suka ce, "Almasihu zai fito daga Gallili ne? 42Ba nassi ya ce Almasihu zai fito daga cikin dangin Dauda daga Baitalami ba, daga kauyen da Dauda ya fito?
43Sai aka sami rabuwa a cikin taron saboda shi. 44Da wadansun su sun kama shi, amma ba wanda ya sa masa hannu.
45Sa'annan jami'an suka dawo wurin manyan Fristoci da Farisawa, wadanda suka ce," me yasa ba ku kawo shi ba?" 46Jami'an su ka amsa, "Ba mutumin da ya taba yin magana kamar haka."
47Farisawa suka amsa masu, "kuma an karkatar da ku? 48Ko wani daga cikin mahukunta ya bada gaskiya gare shi, ko kuwa daga cikin Farisawa? 49Amma wannan taro da basu san shari'a ba, la'anannu ne."
50Nikodimus ya ce masu, (shi wanda ya zo wurin Yesu da, daya daga cikin Farisawa), 51" Ko shari'armu bata hana hukunta mutum ba, sai ta ji daga gare shi ta kuma san abin da ya aikata ba?" 52Suka amsa masa suka ce,"kai ma daga Galili ka fito? Ka yi bincike ka gani ba annanbin da zai fito daga Galili."
53Daga nan sai kowa ya tafi gidansa.

8

1Yesu ya je Dutsen Zaitun. 2Da sassafe ya dawo Haikali, dukan mutane kuma suka zo wurin sa; yazauna koya masu. 3Sai marubuta da Farisawa suka kawo mace wadda aka kama ta tana zina. Su ka sa ta a tsakiya.

4Sai su ka ce da shi, "Malam, wannan mace an kama ta tana cikin yin zina. 5A cikin shari'a, Musa ya bamu umurni mu jejjefe irin wandannan mutume, kai me ka ce game da ita?" 6Sun fadi haka ne domin su gwada shi su sami abinda za su zarge shi da shi, amma Yesu ya sunkuya yayi rubutu da yatsansa a kasa.
7Sa'adda suka cigaba da tambayar sa, ya mike tsaye yace masu, "shi wanda ba shi da zunubi a cikin ku, ya fara jifar ta da dutse." 8Ya sake sunkuyawa, ya yi rubutu da yatsansa a kasa.
9Da suka ji haka, sai suka fita dai-dai da dai-dai, kama daga babbansu. A karshe dai aka bar Yesu shi kadai, tare da matar wadda ta ke a tsakiyar su. 10Yesu ya tashi tsaye ya ce da ita, "mace, ina masu zargin ki? Ba wanda ya kashe ki? 11Ta ce, "Ba kowa, Ubangiji" Yesu ya ce, "Ni ma ban kashe ki ba. Ki yi tafiyar ki, daga yanzu kada ki kara yin zunubi."
12Yesu ya kara yin magana da mutanen cewa, "Ni ne hasken duniya, shi wanda ya biyo ni, ba zai yi tafiya cikin duhu ba, amma za ya sami hasken rai. 13Farisawa suka ce masa, "Kana bada shaida a kan ka, shaidarka ba gaskiya ba ce."
14Yesu ya amsa ya ce masu, "Ko ma na bada shaida a kai na, shaidata gaskiya ce, na san daga inda na fito da inda zan tafi, amma ku baku san daga inda na fito ba, baku kuma san inda zan tafi ba. 15Kuna shari'a ta son kai, ni ko ban yi wa kowa shari'a ba. 16Ko ma da na yi shari'a, shari'ata gaskiya ce domin ba ni kadai ba ne, amma ina tare da Uba wanda ya aiko ni.
17I, a cikin dokarku an rubuta cewa shaidar mutum biyu gaskiya ce. 18Ni ne ni ke shaidar kaina, kuma Uba wanda ya aiko ni ya na shaida ta.
19Su ka ce da shi, "Ina ubanka?" Yesu ya amsa ma su ya ce, "baku san ni ba balle Ubana, in da kun san ni da kun san Uba na kuma."20Ya fadi wadannan kalmomi a kusa da wurin ajiya sa'adda ya ke koyarwa a cikin haikali, kuma ba wanda ya kama shi saboda sa'arsa bata yi ba tukuna.
21Ya kara cewa da su,"Zan tafi, za ku neme ni ba za ku same ni ba, za ku mutu cikin zunubinku. Inda ni ke tafiya, ba za ku iya zuwa ba". 22Yahudawa su ka ce,"Zai kashe kansa ne, da ya ce inda ni ke tafiya ba za ku iya zuwa ba?"
23Yesu ya ce masu ku daga kasa kuke, Ni kuwa daga bisa ni ke. Ku na wannan duniya ne, Ni kuwa ba na wannan duniya ba ne. 24Shiyasa na ce maku za ku mutu cikin zunubanku. In ba kun bada gaskiya NI NE ba, za ku mutu cikin zunubanku.
25Sai kuma suka ce da shi,"Wanene kai?" Yesu ya ce masu, "Abin da na gaya maku tun daga farko. 26Ina da a bubuwa da yawa da zan gaya maku, in kuma hukunta ku a kai. Duk da haka, wanda ya aiko ni, mai gaskiya ne, abubuwan da naji daga wurin sa, wadannan abubuwan su ni ke gaya wa duniya." 27Ba su gane ba yana yi masu magana a kan Uban.
28Yesu ya ce, "Sa'adda kuka tada Dan Mutum sama sa'annan za ku gane NI NE, kuma ban yi komi domin kaina ba. Kamar yadda Uba ya koya mani, haka nike fadin wadannan abubuwa. 29Shi wanda ya aiko ni, yana tare da ni kuma bai bar ni ni kadai ba, domin kullum ina yin abubuwan da suke faranta masa rai." 30Sa'adda Yesu ya ke fadin wadannan abubuwa, dayawa suka bada gaskiya gare shi.
31Yesu ya gayawa wadancan Yahudawa da suka bada gaskiya gare shi, "Idan kun tsaya a cikin magana ta ku almajiraina ne na gaskiya, 32Kuma za ku san gaskiya, gaskiya kuwa zata 'yantar da ku." 33Suka amsa masa, "Mu zuriyar Ibrahim ne kuma bamu taba yin bauta wurin kowa ba, yaya za ka ce, 'Za a 'yantar da ku'?"
34Yesu ya ce masu, "Hakika, hakika, ina ce maku, dukan wanda ya ke aika zunubi bawan zunubi ne. 35Bawa kuwa, ba ya zama a gida dindindin, da yana zama dindindin. 36Saboda haka, idan Dan ya 'yantar da ku zaku zama 'yantattu sosai.
37Na san ku zuriyar Ibrahim ne, kuna so ku kashe ni saboda kalma ta bata da wurin zama a cikin ku. 38Na fadi abubuwan da na gani a wurin Ubana, ku kuma kuna yin abubuwan da kuka ji daga wurin ubanku."
39Suka amsa suka ce masa, "Ibrahim ne ubanmu" Yesu ya ce masu, "Da ku 'yayan Ibrahim ne da kun yi ayukan da Ibrahim ya yi. 40Amma, yanzu kuna so ku kashe ni, mutumin da ya gaya maku gaskiyar da ya ji daga wurin Allah. Ibrahim bai yi haka ba. 41Kuna yin ayyukan ubanku. Suka ce masa, "mu ba a haife mu cikin fasikanci ba, muna da Uba daya: Allah."
42Yesu ya ce masu, "Inda Allah Ubanku ne, da kun kaunace ni, gama na zo daga wurin Allah kuma ga ni anan, gama ba domin kaina nazo ba, shine ya aiko ni. 43Meyasa baku gane magana ta ba? Ai saboda ba za ku iya jin maganata ba ne. 44Ku na ubanku, shaidan ne, kuma kuna so ku yi nufe-nufe na ubanku. Shi mai kisan kai ne tun daga farko kuma ba ya tsayawa gaskiya saboda da babu gaskiya a cikin sa. Sa'anda yake fadin karya, yana maganar halinsa ne domin shi dama makaryaci ne da uban karya kuma.
45Dayake ina fadin gaskiya baku bada gaskiya gare ni ba. 46Wanene a cikin ku ya kama ni da zunubi? Idan na fadi gaskiya don me ba ku gaskanta ni ba? 47Shi wanda yake na Allah ya kan ji maganar Allah, ku ba kwa jin maganar Allah da yake ku ba na Allah bane,"
48Yahudawa suka amsa suka ce masa, "Bamu fadi gaskiya ba da muka ce kai Basamariye ne kuma kana da aljan?" 49Yesu ya amsa, "Ni ba ni da aljan, ina girmama Ubana, ku kuma ba kwa girmama ni."
50Ba na neman daraja domin kaina, akwai wanda ke nema yana kuma hukuntawa. 51Hakika, hakika, iIna ce maku, dukan wanda ya kiyaye maganata, ba za ya ga mutuwa ba."
52Sai Yahudawa su ka ce masa, Yanzu mun sani kana da aljan. Ibrahim da annabawa sun mutu, amma kai ka ce, ' dukan wanda ya yi biyayya da maganata ba zai dandana mutuwa ba'. 53Ai baka fi ubanmu Ibrahim girma ba wanda ya mutu, ko ka fi shi? Annabawa kuma sun mutu. Wa kake daukar kanka ne?."
54Yesu ya amsa, "Idan na daukaka kaina, daukaka ta banza ce, Ubana ne ya daukaka ni. Wanda kuka ce shi ne Allahnku. 55Ku kuwa ba ku san shi ba, amma ni na san shi. Idan na ce ban san shi ba, na zama kamar ku kenan, makaryaci. Sai dai, Ni na san shi ina kiyaye maganarsa. 56Ubanku Ibrahim ya yi farinciki da ganin rana ta; ya gan ta kuma ya yi murna."
57Yahudawa su ka ce masa, "Baka kai shekara hamsin ba tukuna, ka taba ganin Ibrahim?" 58Yesu ya ce masu, "Hakika, hakika, ina ce maku, kafin a haifi Ibrahim, NI NE." 59Suka dauki duwatsu za su jefe shi, amma Yesu ya boye kansa, ya fita daga haikali.

9

1Da Yesu yana wucewa, sai ya ga wani mutum makaho tun daga haihuwa. 2Sai almajiransa suka tambaye shi, "Mallam, wa yayi zunubi, mutumin ne ko iyayensa, har aka haife shi makaho?"

3Yesu ya amsa, Ba mutumin ne ko iyayensa suka yi zunubi ba, amma domin aikin Allah ya bayyana a cikinsa. 4Dole mu yi aikin wanda ya aiko ni tunda rana. Dare na zuwa inda ba mai iya yin aiki. 5Yayinda ina duniya, ni ne hasken duniya."
6Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, ya tofa yawu a kasa, ya kwaba kasar da yawunsa, sai ya shafe idanun mutumin da kasar. 7Ya ce masa, tafi, ka wanke a tafkin Siloam (ma'anarsa: aike)." Sai mutumin ya tafi, ya wanke, ya dawo yana gani.
8Sai makwabtansa da mutanen da da suka gan shi tun can yana roko suka ce, "Ba wannan mutum ne wanda ya ke zaune yana roko ba?" 9Wadansu suka ce, "shi ne." Wadansu suka ce, "A'a, amma yana kama da shi." Amma shi ya ce, "Ni ne wannan mutum."
10Suka ce masa, "To yaya aka bude maka idanu?" 11Sai ya amsa, "Mutumin da ake ce da shi Yesu shi ya kwaba kasa ya shafa mani a idanuna ya ce mani, 'je ka kogin Siluwam ka wanke.' Sai naje na wanke, sannan na samu gani." 12Suka ce masa, "Ina yake?" Ya amsa, "Ban sani ba."
13Suka kawo mutumnin da yake makaho a da wurin farisawa. 14A ranar asabar ne kwa Yesu ya kwaba kasa ya bude masa idanu. 15Har yanzu farisawan suka tambaye shi yadda ya sami ganin gari. Ya ce masu, "Ya sa mani kasa a idanuna, na wanke, kuma yanzu ina gani."
16Wadansu daga cikin farisawa suka ce, "Wannan mutum ba daga Allah yake ba domin ba ya kiyaye ranar Asabar. "Wadansu suka ce, "Yaya mai zunubi zai yi irin wadannan alamu?" Sai rabuwa ta shiga tsakanin su. 17Sai suka tambayi makahon kuma, "Me kake cewa game da shi dashike ya bude maka idanu?" Makahon ya ce, "shi annabi ne." 18Har yanzu kam Yahudawan basu yarda da makantarsa ba da ganin gari da ya samu, sai da suka kirayo iyayen shi wanda ya sami ganin garin.
19Su ka tambayi iyayen, "Wannan shine yaronku da kuka ce an haife shi makaho? Yaya yanzu ya ke iya gani?" 20Sai iyayen suka amsa masu, "Mun san wannan yaronmu ne kuma a makaho aka haife shi. 21Yadda ya ke gani yanzu, bamu sani ba, kuma wanda ya bude masa idanu, bamu sani ba. Ku tambaye shi, ba yaro ba ne. Zai iya magana don kansa."
22Iyayensa sun fadi wadannan abubuwan, domin suna ji tsoron Yahudawan. Gama Yahudiyawan sun rigaya sun yarda duk wanda yace Yesu Almasihu ne, za a fitar dashi daga majami'a. 23Domin wannan ne, iyayensa suka ce, "Ai shi ba yaro ba ne, ku tambaye shi."
24Suka sake kiran mutumin dake makaho karo na biyu, suka ce masa, "Ka girmama Allah. Mu kam mun sani wannan mutum mai zunubi ne." 25Sai wannan mutum ya amsa, "Ban sani ba ko shi mai zunubi ne. Abu guda daya na sani: da Ni makaho ne, amma yanzu ina gani."
26Sai su ka ce masa, "Me ya yi maka? Ta yaya ya bude idanunka?" 27Ya amsa, "Na rigaya na gaya maku, amma ba ku ji ba! Don me kuke so ku sake ji? Ko kuma kuna so ku zama almajiransa, haka ne?
28Sai suka kwabe shi suka ce, "kai ne almajirinsa, amma mu almajiran Musa ne. 29Mun sani Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum, bamu san ko daga ina ne ya zo ba."
30Mutumin ya amsa masu ya ce, "Tirkashi, baku san inda ya fito ba, duk da haka shi ya bude mani idanu. 31Mun san da cewa Allah baya jin masu zunubi, amma idan wani mai ibada ne yana kuma yin nufinsa, to yana jin sa.
32Tunda duniya ta fara ba a taba jin cewa wani ya bude idanun wanda aka haifa makaho ba. 33In mutumin nan ba daga Allah yake ba, ba zai iya yin komai ba." 34Suka amsa suka ce masa, "an haife ka cikin zunubai, yanzu kana so ka yi mana koyarwa?" Sai suka fitar da shi.
35Yesu ya ji cewa sun fitar da shi daga majami'a. Da ya same shi sai ya ce masa, "Kana bada gaskiya ga Dan Allah?" 36Sai ya amsa masa yace, "Wanene shi, Ubangiji, da zan bada gaskiya gare shi?" 37Yesu yace masa, "Ai ka gan shi, shine wanda yake magana da kai." 38Mutumin ya ce, "Ubangiji, Na bada gaskiya." Sai ya yi masa sujada.
39Yesu ya ce, "Don hukunci na zo wannan duniya domin wadanda ba su gani su gani, saboda kuma wadanda suke gani su zama makafi." 40Wadansu Farisawa wadanda suke tare da shi suka ji wadannan abubuwan, suka tambaye shi, "Muma makafi ne?" 41Yesu ya ce masu, "Inda ku makafi ne, da ba ku da zunubi, amma yanzu kun ce, 'Muna gani', don haka zunubinku ya tabbata.

10

1"Hakika, Hakika, ina ce maku, wanda bai shiga ta kofa zuwa garken tumaki ba, amma ya haura ta wata hanya, wannan mutum barawo ne da dan fashi. 2Wanda ya shiga ta kofa shine makiyayin tumakin.

3Mai gadin kofar zai bude masa. Tumakin suna jin muryarsa, ya na kuma kiran tumakinsa da sunayensu, ya kuma kai su waje. 4Bayanda ya kawo su duka a waje, yana tafiya a gabansu, sai tumakin su bi shi, domin sun san muryarsa.
5Ba za su bi bako ba amma sai dai su guje shi, domin basu san muryar baki ba." 6Yesu ya yi masu magana da wannan misali, amma basu gane wadannan abubuwa da yake gaya masu ba.
7Sai Yesu ya ce masu kuma, "Hakika, Hakika, Ina ce maku, Ni ne kofar tumaki. 8Dukan wadanda suka zo kamin ni barayi ne da yan fashi, amma tumakin ba su ji su ba.
9Ni ne kofa, In kowa ya shiga ta wurina, zai sami ceto, zai shiga ya fita ya kuma sami wurin kiwo. 10Barawo ba ya zuwa sai don ya yi sata, ya kashe, ya kuma hallakar. Na zo ne domin su sami rai su kuma same shi a yalwace.
11Ni ne makiyayi mai kyau. Makiyayi mai kyau yana bada ransa domin tumakinsa. 12Wanda yake dan sako kuma, ba makiyayi ba, wanda ba shine mai tumakin ba, in ya ga kyarkeci na zuwa sai ya saki tumakin ya gudu. Sai kyarkecin ya dauke su ya kuma warwatsa su. 13Ya gudu domin shi mai aikin kudi ne kuma bai damu da tumakin ba.
14Nine makiyayi mai kyau, na kuma san nawa, nawa kuma sun san ni. 15Uban ya san ni, ni ma na san Uban, na kuma bada raina domin tumakin. 16Ina da wadansu tumaki wadanda ba na wannan garken ba. Wadannan, kuma, dole in kawo su, su ma za su ji muryata saboda za su zama garke daya da makiyayi daya.
17Domin wannan ne Uban yake kauna ta: Na bada raina domin in same shi kuma. 18Babu wanda zai dauke shi daga wurina, amma ina bayar da shi da kaina. Ina da ikon bada shi, ina da iko in dauke shi kuma. Na karbi wannan umarnin daga wurin Ubana."
19Tsattsaguwa ta sake tashi tsakanin Yahudawa domin wadannan kalmomin. 20Dayawa a cikinsu suka ce, yana da aljani, kuma mahaukaci ne. Don me ku ke sauraronsa?" 21Wadansu suka ce, wadannan ba kalmomin wanda yake da aljani ba ne. Ko mai aljani zai iya bude idanun makaho?"
22Sai lokacin idin Tsarkakewa a Urushalima ya zo. 23A lokacin damuna ne, Yesu kuwa yana tafiya a shirayi cikin haikalin Sulaimanu. 24Sai Yahudawa suka zagaye shi suka ce masa, "Har yaushe ne za ka bar mu cikin shakka? In kai ne Almasihun, ka gaya mana dalla-dalla."
25Yesu ya ce masu, "Na gaya maku, amma baku gaskata ba. Ayyukan da nake yi a cikin sunan Ubana, su ke yin shaida a kaina. 26Duk da haka baku gaskata ba domin ku ba tumakina ba ne.
27Tumakina suna jin murya ta; Na san su, suna kuma bi na. 28Ina ba su rai na har abada; ba za su taba mutuwa ba, babu wanda zai kwace su daga hannu na.
29Ubana, wanda ya bani su, ya fi kowa girma, kuma ba mai iya kwace su daga hannun Uban. 30Ni da Uban daya ne." 31Sai Yahudawa suka dauki duwatsu kuma domin su jajjefe shi.
32Yesu ya amsa masu, "Na nuna maku kyawawan ayyuka masu yawa daga wurin Uban. Saboda wane daga cikin wadannan ayyukan kuke jefe ni?" 33Sai Yahudawa suka amsa masa, "ba don wani aiki mai kyau muke son mu jefe ka ba, amma don sabo, domin kai, mutum ne, amma kana mayar da kanka Allah."
34Yesu ya amsa masu, "Ba a rubuce yake a shari'arku ba, 'Na ce, "ku alloli ne"'?" 35In ya kira su alloli, su wadanda maganar Allah ta zo gare su (kuma ba za a iya karya nassi ba), 36kuna gaya wa wanda Uban ya kebe ya kuma aiko cikin duniya, 'Kana sabo', domin Na ce, 'Ni dan Allah ne'?
37In ba na aikin Ubana, kada ku gaskata ni. 38Amma, idan ina yin su, ko ba ku gaskata da ni ba, ku gaskata da ayyukan saboda ku sani, ku kuma gane cewa Uban yana ciki na, ni kuma ina cikin Uban." 39Suka sake kokarin kama shi, amma ya yi tafiyarsa, ya fita daga hannunsu.
40Ya yi tafiyarsa kuma har gaba da kogin Urdun zuwa inda Yahaya ke yin baftisma ada, ya kuma zauna a wurin. 41Mutane masu yawa suka zo wurinsa, suka ce,"Hakika Yahaya bai yi wasu alamu ba, amma dukan abubuwan da Yahaya ya ce game da wannan mutum gaskiya ne." 42Mutane dayawa suka bada gaskiya gare shi a wurin.

11

1To wani mutum mai suna Li'azaru, yayi rashin lafiya. Shi mutumin Baitanya ne, wato kauyen su Maryamu da 'yar'uwarta Matta. 2Wato wannan Maryamu da ta shafe Ubangiji da mur ta kuma share masa kafafunsa da gashin kanta, wadda dan'uwanta Li'azaru ke rashin lafiya.

3'Yan'uwannan mata suka aika sako wurin yesu, cewa, "Ubangiji, duba, shi wanda kake kauna yana rashin lafiya". 4Da Yesu ya ji, sai ya ce "Wannan ciwo ba zai kai ga mutuwa ba, amma domin daukakar Allah ne, domin Dan Allah ya sami daukaka tawurin ta".
5Yesu yana kaunar Matta, da 'yar'uwarta da Li'azaru. 6Da yaji cewa Li'azaru na rashin lafiya, sai ya tsaya kwana biyu a inda ya ke. 7Bayan haka, sai ya ce wa almajiransa, "Bari mu je Yahudiya kuma."
8Sai almajiransa suka ce masa, "Mallam, harwayau Yahudaya na neman ka domin su jefe ka da duwatsu, kuma kana son komawa can?" 9Yesu ya amsa, "Ba sa'a goma sha biyu ce ta haske a rana guda ba? Idan mutum ya yi tafiya da rana, ba za ya yi tuntube ba, domin yana gani ta wurin hasken wannan duniya.
10Amma idan mutum ya yi tafiya chikin dare, za ya yi tuntube domin haske ba ya tare da shi. 11Ya fadi wadannan al'amura, kuma bayan wadannan abubuwa, sai ya ce masu, "Abokinmu Li'azaru ya yi barci, amma zan je don In tashe shi daga barci".
12Sai almajirai suka ce masa, "Ubangiji, idan barci yake yi, ai za ya farka." 13Yesu kuwa ya yi maganar mutuwar Li'azaru ne, amma su suna tsammani yana magana akan barci ne na hutu. 14Sai Yesu ya yi masu bayani cewa, "Li'azaru ya mutu.
15Ina farinchiki domin ku, da bani a wurin domin ku gaskata. Bari mu je wurinsa." 16Toma wanda ake kira Dan tagwaye, ya ce wa sauran almajirai, "Bari mu tafi domin mu mutu tare da Yesu."
17Da Yesu ya iso, sai ya tarar cewa Li'azaru ya rigaya ya yi kwana hudu a kabari. 18Baitanya kuma tana kusa da Urushalima, 'yar tafiya marar nisa ce a tsakanin su. 19Yahudawa dayawa sun zo wurin Maryamu da Matta domin su yi masu ta'aziyar mutuwar dan'uwansu. 20Da Matta ta ji cewa Yesu na zuwa, sai ta tafi domin ta same shi, amma Maryamu na zamne a cikin gida.
21Matta ta ce wa Yesu, "Ubangiji, da kana nan tare da mu, da dan'uwana baya mutu ba". 22Ko yanzu na san cewa duk abinda ka roka a wurin Allah, za ya ba ka. 23Yesu ya ce mata, "Dan'uwanki za ya rayu kuma.
24Sai Matta ta ce masa, "Na san zaya rayu kuma a tashin mattatu na ranar karshe." 25Yesu ya ce mata, "Ni ne tashin matattu, ni ne kuma rai; wanda ya bada gaskiya gare ni, ko ya mutu, za ya rayu; 26Kuma duk wanda yake raye, ya kuma bada gaskiya gare ni, ba zai mutu ba dadai. Kin gaskata da wannan?"
27Sai ta ce masa, "I, Ubangiji, Na gaskata cewa kaine Almasihu, Dan Allah, wanda ke zuwa duniya. 28Sa'adda ta fadi haka, sai ta koma ta kira yar'uwarta Maryamu gefe guda. Ta ce, "mallam ya iso, kuma yana kiran ki." 29Da ta ji haka, sai ta tashi da sauri ta tafi wurin sa.
30Yesu bai rigaya ya shiga kauyen ba, yana nan inda Matta ta zo ta same shi. 31Da Yahudawan nan dake tare da Maryamu, wato wadannan da suka zo mata ta'aziya, suka ga ta fita daga chikin gida da sauri, sai suka bi ta, suna tsammanin cewa ta tafi ta yi kuka ne a kabari. 32Da Maryamu ta kai inda Yesu ya ke, sai ta fadi gaban sawayensa, ta ce, "Ubangiji, inda kana tare da mu, da dan'uwana bai mutu ba".
33Da Yesu ya gan ta tana kuka, da wadannan Yahudawa da suka bi ta, sai ya yi juyayi a ruhu ya damu kuma; 34sai ya ce, "A ina kuka kwantar da shi?" Sai suka ce masa, "Ubangiji, zo ka gani." 35Yesu ya yi kuka.
36Sai Yahudawa suka ce, "Dubi yadda yake kaunar Li'azaru!" 37Amma wadansun su suka ce, "Shi wannan mutum da ya iya ba makaho ganin gari, da bai iya hana wannan mutum mutuwa ba?
38Yesu yana cikin juyayi kuma a cikin kansa, sai ya tafi kabarin. Kabarin a kogo ne an kuma rufe bakinsa da dutse. 39Sai Yesu ya ce, "A kawar da dutsen." Matta yar'uwar Li'azaru wanda ya mutu, ta ce wa Yesu, "Ubangiji, Yanzu jikin ya ruba domin ya kai kwana hudu da mutuwa". 40Yesu ya ce mata, "Ba na ce maki idan kin gaskata za ki ga daukakar Allah ba?"
41Sai suka kawar da dutsen. Yesu ya daga idanunsa ya ce, "Uba, na gode maka domin kana ji na."42Na san kana ji na a kowane lokaci, amma domin wannan taro da ke tsaye kewaye da ni nike wannan magana, domin su bada gaskiya cewa kaine ka aiko ni."
43Bayan ya yi wannan magana, sai ya daga murya ya ce, "Li'azaru, ka fito!" 44Sai mataccen ya fito; kafafunsa da hannayensa na daure da likkafani, fuskarsa kuma na lullube da tsumma. Yesu ya ce masu, "Ku kwance shi, ya tafi".
45To dayawa daga cikin yahudawan da suka zo wurin Maryamu suka kuma ga abinda Yesu ya yi, suka gaskata da shi; 46amma wadansu suka koma wurin farisawa suka fada masu abubuwan da Yesu ya yi.
47Sai manyan firistoci da farisawa suka tara majalisa wuri guda, suka ce, "menene za mu yi?" Mutumin nan yana alamu masu yawa. 48Idan mun kyale shi haka, duka za su gaskata da shi; Romawa za su zo su kwace wurinmu da al'ummar mu.
49Duk da haka, wani daga cikin su wato, Kayafas wanda shine babban firist a wannan shekara, ya ce da su, "baku san komai ba". 50Ba ku lura cewa ya fi maku kyau mutum daya ya mutu domin mutane, a maimakon dukan al'umma ta hallaka."
51Ya fadi wannan ne ba don kansa ba, amma sabo da shine babban firist, ya yi anabci ne cewa ya kamata Yesu ya mutu domin al'ummar; 52kuma ba don alummar kawai ba, amma domin a tattara 'ya'yan Allah da suke warwatse ko'ina wuri daya. 53Tun daga wannan rana suka fara neman hanyar da za su kashe Yesu.
54Tun daga nan Yesu ya dena tafiya a sarari chikin Yahudawa, amma sai ya koma wani yanki kusa da jeji a wani gari da ake kira Ifraimu. A can kuma ya zamna da almajiransa. 55Idin ketarewa na Yahudawa ya yi kusa, da yawa sun tafi Urushalima daga yankin kasar kamin ranar idi domin su tsarkake kan su.
56Suka shiga neman Yesu, suna magana da junan su yayin da suke tsaitsaye a haikali, cewa "me kuke tunani? Ba za ya zo idin bane?" 57Babban firist da farisawa sun rigaya sun ba da umurni cewa duk inda aka ga Yesu a zo a shaida domin su kama shi.

12

1Kwana shidda kafin idin ketarewa, Yesu ya zo Baitanya inda Li'azaru yake, wato wannan da Yesu ya tada daga matattu. 2Sai suka shirya masa abinci a wurin kuma Matta ce ke hidima, Li'azaru kuwa ya kasance cikin wadanda ke kan tebiri tare da Yesu.3Sai Maryamu ta dauki wani turare da aka yi da man nard, ta shafe kafafun Yesu da shi, ta kuma share kafafun nasa da gashin kanta. Sai gida ya cika da kamshin turaren.

4Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin almajiransa, wanda zai bashe shi, ya ce, "5"Me yasa ba a sayar da wannan turare dinari dari uku a ba gajiyayyu ba?" 6Ya fadi haka ba don ya damu da gajiyayyu ba, amma domin shi barawo ne: shi ne ma'aji, kuma yana sata daga jakkar kudi.
7Yesu ya ce, "Ku kyale ta ta ajiye abinda ta tanada domin jana'iza ta. 8Gajiyayyu suna tare da ku a koyaushe, ni kuwa ba zan kasance da ku koyaushe ba.
9To babban taron Yahudawa sun ji cewa Yesu yana wurin, sai suka zo, ba don Yesu kawai ba amma domin su ga Li'azaru, wanda Yesu ya tada daga matattu. 10Sai manyan firistoci suka kulla makirci akan yadda za su kashe Li'azaru shima; 11domin saboda shi ne yahudawa dayawa suka je suka bada gaskiya ga Yesu.
12Kashegari, babban taro suka zo idin. Da suka ji cewa Yesu na zuwa Urushalima,13Sai suka dauki ganyen dabino suka fita gari suka tare shi da kira mai karfi suna cewa, "Hosanna! Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji, Sarkin Isra'ila.
14Yesu ya sami wani Aholakin jaki, ya hau kansa; kamar yadda aka rubuta,15"Kada ki ji tsoro ke 'yar Sihiyona; duba, ga Sarkinki na zuwa, zaune a kan danJaki".
16Almajiransa basu fahimci wannan al'amari ba da farko, amma bayan da aka daukaka Yesu, sai suka tuna cewa an rubuta wadannan abubuwa game da shi, kuma sun yi masa wadannan abubuwa.
17Sai taron da ke tare da Yesu a ranar da ya kira Li'azaru daga kabari ya kuma tashe shi daga matattu, suka bada shaida. 18Domin wannan ne kuma taron suka zo domin su sadu da shi saboda sun ji cewa ya yi wannan alama. 19Don haka, sai farisawa suka shiga magana a tsakanin su suna cewa "Duba, babu abinda zaku iya yi; kun ga, duniya ta gama bin sa.
20Akwai wadansu Helinawa cikin wadanda suka je sujada a idin. 21Wadannan suka tafi wurin filibus, mutumin Betsaida da ke Galili, suka ce masa, "Mallam, muna so mu ga Yesu.22Filibus ya tafi ya fadawa Andrawus; sai Andrawus ya tafi tare da Filibus, suka kuwa gaya wa Yesu.
23Yesu ya amsa masu ya ce, "sa'a ta zo da za'a daukaka Dan mutum. 24Hakika, hakika, Ina ce maku, in ba kwayar alkama ta fadi kasa ba ta mutu, za ta kasance ita kadai; amma idan ta mutu, za ta bada 'ya'ya masu yawa.
25Duk wanda yake son ransa, zai rasa shi; amma wanda ba ya son ransa a duniyan nan za ya kiyaye shi domin rayuwa ta har abada. 26Idan wani na bauta mani, to bari ya biyo ni; kuma duk inda nike, a can bawana zai kasance kuma. Duk wanda ke bauta mani, Uban zai girmama shi.
27Yanzu raina na cikin damuwa, to me zan ce? 'Uba, ka cece ni daga wannan sa'a? Amma Saboda wannan dalili ne na zo wannan sa'a. 28Uba, ka daukaka sunanka". Sai wata murya daga sama ta ce, "Na daukaka shi, zan kuma sake daukaka shi. 29Daganan sai taron dake tsaye kuma suka ji muryar, suka ce an yi tsawa. Wasu suka ce, "Mala'ika ya yi magana da shi".
30Yesu ya amsa ya ce, "wannnan murya ta zo ba saboda ni ba, amma domin ku." 31Yanzu za'a shar'anta duniya. Yanzu za'a kori mai mulkin duniyan nan.
32Sa, annan ni, idan an daga ni daga duniya, zan jawo dukan mutane zuwa gare ni". 33Ya fadi wannan ne domin ya nuna irin mutuwar da za ya yi.
34Taro suka amsa masa cewa, "Mun ji a cikin shari'a cewa Almasihu za ya kasance har abada. Yaya za ka ce, 'za'a daga dan mutum'? Wanene wannan dan mutum?" 35Yesu ya ce masu, "Nan da lokaci kadan za ku kasance da haske, ku yi tafiya tun haske na tare da ku, kada duhu ya mamaye ku. Wanda ke tafiya cikin duhu, bai san inda za shi ba. 36Ku gaskata ga haske tun yana tare da ku domin ku zama yayan haske". Yesu ya fadi wadannan abubuwa sannan ya tafi ya boye masu.
37Kodashike Yesu ya yi alamu da dama a gabansu, duk da haka ba su gaskata shi ba. 38Saboda maganar annabi Ishaya ta cika, wadda ya ce, "Ubangiji, wa ya gaskata rahoton mu? Ga wa kuma hannun Ubangiji ya bayyana?
39Saboda wannan dalili basu gaskata ba, gama Ishaya ya sake cewa, 40ya makantar da su, ya kuma taurare zuciyarsu, saboda kada su gani da idanunsu, su kuma sami fahimta da zuciyarsu, su juyo wurina in warkar da su.
41Ishaya ya fadi wadannan abubuwa ne domin ya hangi daukakar Yesu ya kuma yi magana game da shi. 42Amma duk da haka, dayawa cikin shugabanni suka gaskata Yesu. Amma saboda farisawa, basu shaida shi a sarari ba, domin kada a kore su daga majami'a. 43Suna son yabo daga mutane fiye da yabon dake zuwa daga Allah.
44Yesu ya yi magana da babbar murya, ya ce, "Wanda ya gaskata ni, ba ni yake gaskatawa kadai ba, amma kuma yana gaskata wanda ya aiko ni, 45kuma wanda ke gani na, yana ganin shi wanda ya aiko ni.
46Na zo ne a matsayin haske a duniya, saboda duk wanda ya gaskata da ni ba za ya yi tafiya cikin duhu ba. 47Duk wanda ya ji maganata baya gaskata ba, ba ni hukunta shi; gama ban zo in yi wa duniya hukunci ba, amma don in ceci duniya.
48Wanda ya ki ni, ya kuma ki ya karbi magana ta, akwai wanda za ya yi masa hukunci. Kalmar da na fada, ita ce za ta yi masa hukunci a rana ta karshe. 49Maganar da ni ke yi, ba ra'ayina ba ne. Amma Uba wanda ya aiko ni shi ke bani umarni game da abin da zan ce da abin da zan fadi. 50Na san umarninsa rai ne madawwami, don haka na ce - kamar yadda Uba ya fada, haka ni ma nake fadi."

13

1Kamin bukin idin ketarewa, sa'adda Yesu ya san lokaci ya yi da zai tashi daga wannan duniya zuwa wurin Uba, da yake ya kaunaci nasa wadanda ke duniya- ya kaunace su har karshe. 2Iblis ya rigaya ya sa a zuciyar Yahuza Iskariyoti dan Saminu, ya bashe da Yesu.

3Ya san cewa Uba ya bada kome a hannunsa, kuma ya zo daga wurin Allah, kuma zai koma wurin Allah. 4Ya tashi daga cin abincin, ya tube tufafinsa, ya dauki tawul ya lullube kansa da shi. 5Sa'an nan ya zuba ruwa a bangaji, ya fara wanke kafafun almajiran, yana shafe su da tawul din da ya lullube jikinsa da shi.
6Ya zo wurin Bitrus Saminu, sai Bitrus ya ce masa,"Ubangiji, za ka wanke mani kafa?" 7Yesu ya amsa ya ce, "Abin da nake yi ba za ka fahimce shi yanzu ba, amma daga baya za ka fahimta." 8Bitrus ya ce masa, "Ba za ka taba wanke mani kafa ba." Yesu ya amsa masa ya ce, "In ban wanke maka ba, ba ka da rabo da ni". 9Bitrus ya ce masa, "Ubangiji, ba kafafuna kadai za ka wanke ba, amma da hannayena da kaina."
10Yesu ya ce masa, "Duk wanda ya yi wanka ba ya da bukata, sai dai a wanke kafafunsa, amma shi tsarkakakke ne baidaya; ku tsarkakakku ne, amma ba dukanku ba." 11(Don Yesu ya san wanda zai bashe shi, shiyasa ya ce, "Ba dukanku ne ke da tsarki ba.")
12Bayan Yesu ya wanke masu kafafu, ya dauki tufafinsa ya zauna kuma, ya ce masu, "Kun san abin da na yi muku? 13kuna kirana, 'Malam, da Ubangiji,' kun fadi daidai, don haka Nake. 14Idan ni Ubangiji da kuma mallam, na wanke maku kafafu, ya kamata kuma ku wanke wa junan ku kafafu. 15Gama na baku misali, saboda ku yi yadda na yi maku.
16Lalle hakika ina gaya muku, bawa ba ya fi mai gidansa girma ba; dan aike kuma ba ya fi wanda ya aiko shi girma ba. 17Idan kun san wadannan abubuwa, ku masu albarka ne idan kun aikata su. 18Ba ina magana akan dukanku ba; Na san wadanda na zaba. Amma domin Nassi ya cika: 'Shi Wanda ya ci gurasata, ya tayar mani'.
19Ina fada maku wannan yanzu tun kafin haka ta faru domin sa'adda ta faru, ku gaskata Ni ne. 20Hakika, hakika, Ina gaya maku, wanda ya karbi wanda na aiko, Ni ya karba, wanda kuma ya karbe ni, ya karbi wanda ya aiko ni.
21Bayan Yesu ya fadi haka, ya damu a ruhu, ya yi shaida ya ce, "Lalle hakika, ina gaya muku cewa daya daga cikinku zai bashe ni." 22Almajiran suka kalli juna, suna juyayin ko akan wa yake magana.
23Daya daga cikin almajiransa, wanda Yesu yake kauna, yana a teburi, jingine a kirjin Yesu. 24Siman Bitrus ya ce wa almajirin, "ka fada mana ko akan wa ya ke magana." 25Sai ya sake jingina a kirjin Yesu, ya ce masa, "Ubangiji, wanene?"
26Sannan Yesu ya amsa, "Shine wanda zan tsoma gutsuren gurasa in ba shi." Sannan bayan ya tsoma gurasar, sai ya ba Yahuza Dan Siman Iskariyoti. 27To bayan gurasar, sai shaidan ya shige shi, sai Yesu ya ce masa, "Abinda kake yi, ka yi shi da sauri."
28Babu wani a teburin da ya san dalilin dayasa ya fada masa wannan. 29Wadansu sun yi tsamanin cewa, tun da Yahuza ne ke rike da jakkar kudi, Yesu ya ce masa, "Ka sayi abinda muke bukata don idin", ko kuma ya bada wani abu domin gajiyayyu. 30Bayan Yahuza ya karbi gurasar, sai ya fita nan da nan. Da daddare ne kuwa.
31Bayan Yahuza ya tafi, Yesu ya ce, "Yanzu an daukaka Dan mutum, kuma an daukaka Allah a cikinsa. 32Allah zai daukaka shi a cikin kansa, kuma zai daukaka shi nan da nan. 33'Ya'ya kanana, ina tare da ku na wani gajeren lokaci. Zaku neme ni, kuma kamar yadda na fadawa Yahudawa, 'in da zan tafi ba za ku iya zuwa ba.' Yanzu kuma na fada maku wannan.
34Ina baku sabuwar doka, ku kaunaci juna; kamar yadda na kaunace ku, haka kuma ku kaunaci juna. 35Ta haka kowa zai san ku almajiraina ne, idan kuna kaunar juna."
36Siman Bitrus ya ce masa, "Ubangiji, ina za ka?" Yesu ya amsa ya ce, "Inda za ni, ba zaka iya bi na ba yanzu, amma zaka bini daga baya." 37Bitrus ya ce masa, "Ubangiji, don me ba zan iya binka a yanzu ba? Zan bada raina domin ka." 38Yesu ya amsa ya ce, "Za ka bada ranka domina? Lalle hakika, ina gaya maka, kafin zakara ya yi cara zaka yi musu na sau uku."

14

1"Kada zuciyarku ta bachi. Kun gaskata da Allah, sai kuma ku gaskata da ni. 2A gidan Ubana akwai wurin zama dayawa. Da ba haka ba, da na fada maku, domin zan tafi in shirya maku wuri. 3In kuwa na je na shirya maku wuri, zan dawo in karbe ku zuwa wurina domin inda nake kuma ku kasance.

4Kun san hanya inda zan tafi." 5Toma ya ce wa Yesu, "Ubangiji, bamu san inda za ka tafi ba, yaya za mu san hanyar?" 6Yesu ya ce masa, "Ni ne hanya, ni ne gaskiya, ni ne rai; Ba mai zuwa wurin Uba sai ta wurina. 7Da kun san ni, da kun san Ubana kuma. Amma daga yanzu kun san shi, kuma kun gan shi."
8Filibus ya ce wa Yesu, "Ubangiji, ka nuna mana Uban, wannan za ya ishe mu." 9Yesu ya ce masa, "Ina tare da ku da dadewa, amma har yanzu baka san ni ba, Filibus? Duk wanda ya gan ni, ya ga Uban. Yaya za ka ce, 'Nuna mana Uban'?
10Baka gaskata cewa Ina cikin Uban, Uban kuma yana ciki na ba? Maganganun da nake fada maku, ba da ikona nake fadi ba, amma Uban ne da yake zaune a ciki na yake yin ayyukansa. 11Ku gaskata ni cewa ina cikin Uban, Uban kuma na ciki na, ko kuwa ku bada gaskiya domin ayyukan kansu.
12"Lalle hakika, ina gaya maku, duk wanda ya gaskata ni zai yi ayyukan da nake yi, kuma zai yi ayyuka fiye da wadannan, domin zan tafi wurin Uba. 13Duk abinda kuka roka da sunana, zan yi shi domin a daukaka Uban cikin Dan. 14Idan kuka roke ni komai cikin sunana, zan yi shi.
15"Idan kuna kaunata, za ku kiyaye dokokina. 16Sa, annan zan yi addu'a ga Uba, zai kuwa baku wani mai ta'aziya domin ya kasance tare daku har abada. 17Ruhun gaskiya. Wanda duniya ba zata iya karba ba, domin bata gan shi ba, ko ta san shi. Amma ku kun san shi, domin yana tare da ku, zai kuma kasance a cikin ku.
18Ba zan barku ku kadai ba; zan dawo wurin ku. 19Sauran dan gajeren lokaci, duniya kuma ba zata ka ra gani na ba, amma ku kuna gani na. Saboda ina raye, kuma zaku rayu. 20A wannan rana zaku sani ina cikin Ubana, ku kuma kuna ciki na, ni ma ina cikin ku.
21Shi wanda yake da dokokina yake kuma bin su, shine ke kauna ta, kuma shi wanda ke kauna ta Ubana zai kaunace shi, Ni ma kuma zan kaunace shi in kuma bayyana kaina gare shi." 22Yahuza (ba Iskariyoti ba) ya ce ma Yesu, "Ubangiji, meyasa za ka bayyana kanka a gare mu, ba ga duniya ba?"
23Yesu ya amsa ya ce masa,"Kowa yake kauna ta, zai kiyaye maganata. Ubana kuwa zai kaunace shi, za mu zo wurinsa mu zauna tare da shi. 24Shi wanda baya kauna ta, ba ya kiyaye maganganuna. Maganar da kuke ji ba daga gareni take ba, amma daga Uba wanda ya aiko ni take.
25Na fada maku wadannan abubuwa, sa'adda nake tare da ku. 26Saidai, mai ta'aziyar- Ruhu Mai Tsarki wanda Uba zai aiko cikin sunana, zai koya maku kome, kuma zai tunashe ku dukan abinda na fada maku. 27Na bar ku da salama; ina ba ku salamata. Ba kamar yadda duniya ke bayarwa Nake bayarwa ba. Kada zuciyarku ta baci, kuma kada ku tsorata.
28Kun ji dai na fada maku, 'zan tafi, kuma Zan dawo gare ku'. Idan kuna kaunata, za ku yi farinciki domin za ni wurin Uban, gama Uban ya fi ni girma. 29Yanzu na fada maku kafin ya faru, domin idan ya faru, ku gaskata.
30Ba zan kara magana mai yawa da ku ba, domin mai mulkin duniyan nan yana zuwa. Bashi da iko a kai na, 31amma domin duniya ta san cewa ina kaunar Uban, Ina yin daidai abinda Uban ya Umarce ni. Mu tashi mu tafi daga nan.

15

1"Nine itacen inabi na hakika, Ubana kuwa shi ne manomin. 2Yakan cire duk wani rashe a cikina da ba ya bada 'ya'ya, mai bada 'ya'ya kuwa ya kan gyara shi domin ya kara bada 'ya'ya.

3Kun rigaya kun tsarkaka saboda maganar da na yi muku. 4Ku zauna ciki na, Ni kuma cikin ku. Kamar yadda reshe ba ya iya bada 'ya'ya shi kadai sai ya zauna cikin itacen, haka kuma ba za ku iya ba, sai kun zauna ciki na.
5Ni ne itacen inabi, ku ne rassan. Wanda ya zauna ciki na, ni kuma cikin sa, yana bada 'ya'ya dayawa, gama in ba tare da ni ba, ba za ku iya yin kome ba. 6Wanda kuma bai zauna a ciki na ba, akan jefar da shi kamar reshe, ya bushe, kuma sukan tattara rassan su jefa a wuta, su kone. 7In kun zauna a ciki na, maganata kuma ta zauna a cikin ku, sai ku roki duk abinda kuke so, za a kuwa yi maku.
8Ta haka ake daukaka Ubana: cewa ku bada 'ya'ya dayawa, kuma cewa ku almajiraina ne. 9Kamar yadda Ubana ya kaunace ni, haka Ni ma na kaunace ku; Ku zauna cikin kaunata.
10Idan kun kiyaye dokokina, za ku zauna cikin kaunata kamar yadda Na kiyaye dokokin Ubana, na kuma zauna cikin kaunarsa. 11Ina gaya maku wadannan al'amura domin farincikina ya kasance a cikin ku, kuma domin farincikinku ya zama cikakke.
12"Wannan shine umarnina, cewa ku kaunaci juna kamar yadda na kaunace ku. 13Babu wanda ke da kaunar da tafi haka, wato ya bada ransa domin abokansa.
14Ku abokaina ne idan kuna yin abubuwan da na umarce ku. 15Nan gaba ba zan kara ce da ku bayi ba, don bawa bai san abinda Ubangijinsa ke yi ba. Na kira ku abokaina, domin na sanar da ku duk abinda na ji daga wurin Ubana.
16Ba ku kuka zabe ni ba, amma Ni ne na zabe ku, na aike ku don ku je ku bada 'ya'ya, 'ya'yanku kuma su tabbata. Wannan ya zama domin duk abinda kuka roki Uba a cikin sunana, zai baku. 17Na baku wannan umarni: domin ku kaunaci juna.
18In duniya ta ki ku, ku sani cewa ta kini kafin ta ki ku. 19Da ku na duniya ne, da duniya ta kaunace ku kamar nata. Amma saboda ku ba na duniya bane, na kuma zabe ku daga duniya, don haka duniya take kin ku.
20Ku tuna da maganar da na yi muku, 'Bawa ba ya fi Ubangijinsa girma ba.' Idan sun tsananta mani, ku ma za su tsananta maku; Idan sun kiyaye maganata, za su kuma kiyaye maganarku. 21Za su yi maku duk wadannan abubuwa saboda sunana, don basu san wanda ya aiko ni ba. 22Da ban zo na yi masu magana ba, da basu da zunubi, amma yanzu, basu da wata hujja don zunubinsu.
23Duk wanda ya ki ni ya ki Ubana. 24Da ban yi ayyukan da babu wanda ya taba yinsu a cikin su ba, da basu da zunubi, amma yanzu sun gani, sun kuma ki ni da Ubana duka. 25An yi wannan kuwa domin a cika maganar da ke rubuce a cikin shari'arsu, ' Sun ki ni ba dalili.'
26Sa'adda Mai Ta'aziya- wanda zan aiko maku daga wurin Uban, wato, Ruhun gaskiya, wanda ke fita daga wurin Uban-ya zo, zai bada shaida a kai na. 27Ku ma kuna bada shaida saboda kuna tare da ni tun daga farko.

16

1"Na fada maku wannan ne domin kada kuyi tuntube. 2Zasu fitar da ku daga majami'u. Amma, sa'a tana zuwa, wadda idan wani ya kasheku, zai yi zaton aikin Allah yake yi.

3Za suyi haka ne kuwa domin ba su san Uban ko ni ba. 4Na fada maku wadannan abubuwa ne domin in lokacin da zasu faru yayi, ku tuna na fada maku." Ban fada maku wadannan abubuwa ba tun da farko, domin ina tare da ku.
5Yanzu kuwa za ni wurin wanda ya aiko ni, duk da haka a cikinku, ba wanda ya tambaye ni, 'Ina za ka?' 6Amma saboda na fada maku wadannan abubuwa, bakin ciki ya cika zuciyarku. 7Amma ina gaya maku gaskiya: zai fi ye maku in na tafi. Domin in ban tafi ba, Mai Ta'aziyya ba zai zo gare ku ba, in kuwa na tafi, zan aiko shi gare ku.
8Idan kuwa ya zo, Mai Ta'aziyyar zai fadarkar da duniya a kan zunubi, da adalci, da kuma hukunci. 9Game da zunubi, domin basu gaskata da ni ba, 10Game da adalci, domin za ni wurin Uba, kuma ba za ku sake ganina ba, 11game da hukunci kuma, domin an yanke wa mai mulki duniyan nan hukunci.
12"Akwai abubuwa da yawa da zan gaya maku, amma ba za ku iya fahimta a yanzu ba. 13Saboda haka, sa'adda Ruhu na gaskiya ya zo, zai bishe ku a cikin dukan gaskiyar, domin ba zai yi magana don kansa ba, sai dai duk abin da ya ji, shi zai fada, zai kuma sanar da ku al'amuran da zasu faru. 14Zai daukaka ni, domin zai dauko abubuwa dake nawa ya sanar da ku.
15Duk abinda Uba yake da shi, nawa ne. Domin wannan ne nace zai dauko abubuwa da yake nawa ya sanar da ku. 16"Bayan dan lokaci kadan, ba zaku kara ganina kuma ba. bayan dan lokaci kadan kuma, zaku gan ni."
17Sai wadansu almajiransa sukace wa juna, "Me nene wannan da yake fadi mana, 'Bayan dan lokaci kadan ba zaku gan ni ba, bayan dan lokaci kadan kuma zaku gan ni?' da kuma, ' zan tafi wurin Uba'?" 18Saboda haka sukace, "Me nene wannan da yake fada, 'Bayan dan lokaci kadan'? Bamu san abinda yake fada mana ba."
19Yesu kuwa ya ga suna so su tambaye shi, sai ya ce masu, "Wato kuna tambayar juna ne abinda nake nufi da cewa, "Bayan dan lokaci kadan ba zaku gan ni ba, bayan dan lokaci kadan kuma zaku gan ni'? 20Hakika, hakika, ina gaya maku, zaku yi kuka da makoki, amma duniya za ta yi farin ciki, zaku cika da bakin ciki, amma bakin cikinku zai koma farin ciki. 21Mace takan ji zafi lokacin da take nakuda don lokacin haihuwa ya zo. Amma da zarar ta haifi jinjirin nan, ba ta kara tunawa da zafin, domin ta na fariciki an haifi mutum a duniya.
22To yanzu dai kuna bakin ciki, amma zan sake ganinku, kuma ba wanda zai iya kwace maku wannan farin ciki. 23A rannan, ba zaku tambaye ni komai ba. Hakika hakika, ina gaya maku, komai kuka roki Uba a cikin sunana zai ba ku shi. 24Harwa yau, ba ku roki komai cikin sunana ba. Ku roka, zaku karba, domin farin cikin ku ya zama cikakke."
25"Na fada maku wadannan abubuwa cikin karin magana. Amma sa'a tana zuwa da ba zan kara fada maku komai ba cikin karin magana, amaimakon haka zan gaya maku komai a sarari game da Uba.
26A ranar nan, zaku yi roko a cikin sunana kuma bance maku zan yi addu'a ga Uba a madadinku ba, 27domin Uba da kansa yana kaunarku, domin kun kaunace ni, kun kuma gaskata daga wurin Uban na fito. 28Daga wurin Uban na fito, kuma na shigo duniya. Har wa yau, kuma zan bar duniya in koma wurin Uba."
29Almajiransa sukace, duba, "Yanzu kake magana a sarari, ba cikin karin magana ba! 30Yanzu mun sani ka san komai, ba sai wani ya tambaye ka ba. Ta haka muka gaskata daga wurin Allah ka fito." 31Yesu ya amsa masu yace, "Ashe, yanzu kun gaskata?
32Duba, sa'a na zuwa, I, sa'ar ta yi, da za a warwatsa ku, kowa ya koma gidansa, kuma ku bar ni ni kadai. Duk da haka kuwa ba ni kadai nake ba, domin Ubana yana tare da ni. 33Na fada maku wannan ne domin a ciki na ku sami salama. A duniya kuna shan tsanani, amma ku karfafa: na yi nasara da duniya,"

17

1Da Yesu ya fadi wandannan abubuwa, sai ya tada idanunsa sama ya ce, ya Uba, sa'a ta zo; ka daukaka Danka, domin Dan shi ya daukaka ka, 2kamar yadda ka ba shi iko akan dukkan 'yan adam, ya ba da rai madawwami ga duk wanda ka ba shi.

3Wannan ne rai madawwami: wato su san ka, Allah makadaici na gaskiya, da shi kuma wanda ka aiko, Yesu Almasihu. 4Na daukaka ka a duniya, na gama aikin da ka ba ni in yi. 5Yanzu, ya Uba, ka daukaka ni tare da kai da daukaka wadda ni ke da ita tare da kai tun kafin duniya ta kasanci.
6Na bayyana sunanka ga mutunen da ka ba ni acikin duniya. Na ka suke, ka ba ni su, sun kuwa kiyaye maganarka. 7Yanzu kuwa sun san duk iyakar abinda ka ba ni daga gare ka yake, 8don kuwa maganganun da ka fada mani. Na fada masu, sun kuma karba, sun sani kuwa hakika na fito daga gareka ne, kuma sun gaskata kai ne ka aiko ni.
9Ina yi masu addu'a. Ba domin duniya ni ke yin addu'a ba, amma domin wadanda ka bani gama na ka ne. 10Gama dukan abinda ke nawa na ka ne, naka kuwa nawa ne, an kuma daukaka ni a cikinsu. 11Ba na cikin duniya kuma, amma wadannan mutane suna cikin duniya, ni kuwa ina zuwa wurin ka. Ya Uba mai Tsarki, ka adanasu cikin sunanka da ka ba ni domin su zama daya, kamar dai yadda muke daya.
12Lokacin da ina tare da su, na adanasu acikin sunanka da ka ba ni. Na kiyaye su, kuma ko daya kuwa daga cikinsu ba ya bace ba, sai dai dan hallakar nan, domin Nassi ya cika. 13Amma yanzu ina zuwa wurinka, Ina fadar wadannan abubuwa tun ina duniya, domin farin cikina ya zama cikakke a zukatansu. 14Na ba su maganarka, kuma duniya ta tsane su domin su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ba na duniya ba ne.
15Ba ina roko ka dauke su daga cikin duniya ba, amma domin ka tsare su daga mugun nan. 16Su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ba na duniya ba ne. 17Ka kebe su domin kanka cikin gaskiya. maganarka gaskiya ce.
18Kamar dai yadda ka aiko ni cikin duniya, haka kuma na aike su cikin duniya. 19Na kebe kaina gareka sabili da su, domin su ma kansu a kebe su gareka cikin gaskiya.
20Ina addu'a ba domin wadannan kadai ba, amma har da wadanda zasu gaskata da ni ta wurin maganarsu, 21Domin su zama daya dukansu, kamar yadda kai, ya Uba, ka ke ciki na, ni kuma na ke cikin ka. Ina roko suma su kasance a cikinmu, domin duniya ta gaskata cewa ka aiko ni
22Daukakar da ka bani, ita nake basu, domin su zama daya, kamar yadda mu ke daya; 23ni a cikinsu, kai kuma a ciki na. Domin su kammalu cikin zama daya, domin duniya ta sani cewa ka aiko ni, kuma ka kaunace su, kamar yadda ka kaunace ni.
24Ya Uba, ina so wadanda ka ba ni, su ma su kasance tare da ni inda nake, domin su dubi daukakata da ka yi mani. Domin ka kaunace ni tun kafin halittar duniya.
25Ya Uba mai adalci, duniya kam, ba ta sanka ba, amma ni na sanka; kuma wadannan sun sani kai ne ka aiko ni. 26Na sanar masu da sunanka, zan kuma sanar da shi domin kaunar da ka yi mani ta kasance a cikinsu, ni kuma in kasance a cikinsu,

18

1Bayan Yesu ya fadi wadannan maganganu, ya fita shi da almajiransa zuwa daya barayin kwarin Kidiron, inda wani lambu ya ke, ya kuma shiga da almajiransa. 2Yahuza ma wanda zai bashe shi ya san wurin, domin Yesu ya saba zuwa wurin da almajiransa. 3Yahuza kuwa, bayan ya dauko kungiyar soja daga manyan firistoci, da Farisawa, da 'yan majalisa, suka zo wurin, rike da fitilu, da cociloli, da makamai.

4Sai Yesu, da ya san duk abinda ke faruwa da shi, yayiwo gaba, yace masu, "Wa kuke nema" 5Suka amsa masa su ka ce, "Yesu Banazare" Yesu yace masu, Ni ne" Yahuza kuma, wanda ya bashe shi, yana tsaye tare da sojojin.
6Sa'adda ya ce masu, "Ni ne", suka koma da baya, suka fadi a kasa. 7Ya sake tambayarsu kuma, "Wa ku ke nema?" su ka ce, "Yesu Banazare."
8Yesu ya amsa, "Ai, na gaya maku cewa, Ni ne. In kuwa ni ku ke nema, ku bar wadannan su tafi abinsu;" 9Wannan kuwa domin maganar daya fada ta cika, "Daga cikin wadanda ka ba ni, ko daya bai bace mani ba."
10Saminu Bitrus kuwa, da ya ke yana da takobi, ya zaro ya kai wa bawan babban firist sara, ya dauke masa kunnensa na dama, sunan bawan Malkus ne. 11Yesu ya ce wa Bitrus, "Mai da takobin ka kubenta. Ba zan sha kokon da Uba ya ba ni ba.'?
12Sai sojojin da hafsan, da 'yan majalisar Yahudawa, suka kama Yesu, suka daure shi. 13Da fari suka tafi da shi wurin Hanana, don shi surukin Kayafa ne, wanda ya ke shi ne babban firist a shekaran nan. 14Kayafa kuma shi ne ya ba Yahudawa shawara, cewa ya fiye masu mutum daya ya mutu domin mutane.
15Saminu bitrus ya bi bayan Yesu, haka kuma wani almajirin yayi. Almajirin nan kuwa sananne ne ga babban firist, sai ya shiga har farfajiyar babban firist din tara da Yesu; 16Amma bitrus kuwa ya tsaya a bakin kofa daga waje. Sai daya almajirin da ya ke sananne ga babban firist ya fita, yayi magana da macen da ta ke tsaron kofar, sa'an nan ya shigo da Bitrus.
17Sai yarinyar mai tsaron kofar ta ce wa Bitrus, "kai ma ba kana cikin almajiran mutumin nan ba?" Yace "bani ba." 18To, barorin da dogaran Haikali suna tsaye a wurin, sun kuwa hura wutar gawayi, suna jin dumi, gama ana sanyi. Bitrus ma yana tsaye tare da su yana jin dumin.
19babban firist ya tambayi Yesu game da almajiransa da koyarwarsa kuma. 20Yesu ya amsa masa, Ai, na yi wa duniya magana a bayyane. Na kuma sha koyarwa a majami'u da Haikali in da Yahudawa duka sukan taru. Ban fadi komai a boye ba. 21Don me kake tambaya ta? Ka tambayi wadanda suka saurare ni a kan abinda na fada, ai, sun san abinda na fada.
22Sa'adda Yesu ya fadi wannan, wani daga cikin 'yan majalisar da ke tsaye a wurin ya nushi Yesu, yace, "Kana amsa wa babban firist haka." 23Yesu ya amsa masa yace, "Idan na fadi mugun abu to, ka bada shaida kan hakan. In kuwa dai dai na fada, to, dan me za ka nushe ni?" 24Sai Hanana ya aika daYesu a daure wurin Kayafa, babban firist.
25To Saminu Bitrus yana tsaye yana jin dumin. Mutanen kuwa suka ce masa, "Anya kai ma ba cikin almajiransa ka ke ba?" Sai yayi musu yace, "A'a, ba na ciki." 26Sai wani daga cikin bayin babban firist, wato dan'uwan wanda Bitrus ya fillewa kunne, yace, "Ashe, ban gan ka tare da shi a lambun ba? 27Bitrus ya sake yin musu, nan da nan kuwa zakara yayi cara.
28Daga wurin Kayafa kuma suka kai Yesu fadar Gwamna. Da asuba ne kuwa, su kansu ba su shiga fadar Gwamnan ba, wai don kada su kazantu su kasa cin jibin Ketarewa. 29Sai bilatus fa ya fita zuwa wurinsu, yace, "Wane zargi ku ke kawowa akan mutumin nan? 30"Sai suka amsa suka ce, "idan da mutumin nan bai yi mugun abu ba, me zai sa mu yi kararsa a wurin ka"
31bilatus yace masu, "Ku tafi da shi da kan ku mana, ku hukunta shi bisa ga shari'arku!" Sai Yahudawa su kace masa, "Ai, ba mu da ikon zartar da hukuncin kisa akan kowa." 32Sun fadi Wannan ne don a cika maganar da Yesu yayi, wadda ta kwatanta irin mutuwar da zai yi.
33Sai bilatus ya sake shiga cikin fadar Gwamnan, ya kira Yesu ya ce masa, "kai sarkin Yahudawa ne?" 34Yesu ya amsa, "wannan fadarka ce, ko kuwa wadansu ne suka ce da ni haka a wurinka?" 35Bilatus ya amsa "Ni ba Bayahude bane, ko kuwa?" Ai, jama'arka ne da manyan firistoci suka bashe ka gareni. "Me ka yi?"
36Yesu ya amsa, "Mulkina ba na duniya nan ba ne. Da mulkina na duniyan nan ne da barorina za su yi yaki kada a bashe ni ga Yahudawa. To, mulkina ba daga nan ya ke ba." 37Sai Bilatus yace masa, "Wato ashe, sarki ne kai?" Yesu ya amsa, "Yadda ka fada, ni sarki ne. Domin wannan dalili aka haife ni, domin kuma wannan dalili na zo cikin duniya, don in bada shaida game da gaskiya. Kowane mai kaunar gaskiya kuma yakan saurari muryata."
38Bilatus yace masa, "Menene gaskiya?" Bayan da ya fadi haka, ya sake fitowa wurin Yahudawa, yace masu, "Ni kam, ban sami mutumin nan da wani laifi ba. 39Amma dai kuna da wata al'ada, in Idin Ketarewa ya yi, na kan sakar maku mutum daya. To, kuna so in sakar maku sarkin Yahudawa?" 40Sai suka sake daukar kururuwa suna cewa, "A; a, ba wannan mutum ba, sai dai Barabbas." Barabbas din nan kuwa dan fashi ne.

19

1Sai Bilatus yayi wa Yesu bulala. 2Sojojin kuwa suka saka rawanin kaya. Suka kuwa dora wa Yesu a kai suka sa mashi kaya irin na saurata. 3Suka zo wurin sa sukace, "Ranka ya dade, sarkin Yahudawa! sai suka nushe shi.

4Sai Bilatus ya sake fita waje yace masu, "Dubi, zan kawo maku mutumin domin ku sani ban same shi da wani laifi ba", 5Yesu kuwa ya fito, da rawanin kaya da kaya irin na sarauta. Sai Bilatus yace "Ga mutumin nan". 6Da manyan firistocin tare da yan majalisar suka ga Yesu, sai suka yi ta ihu suna cewa "A gicciye shi, A gicciye shi" Sai Bilatus yace masu, "ku dauke shi ku gicciye shi, ni kam ban same shi da wani laifi ba".
7Sai Yahudawan sukace mashi, "Ai muna da shari'a, kuma bisa ga shari'ar ya cancanci mutuwa domin ya mai da kansa Dan Allah". 8Da Bilatus ya ji wannan zance sai ya tsorata kwarai. 9Sai ya sake shiga fadar Gwamna, yace wa Yesu, "Daga ina ka fito?" amma Yesu bai amsa mashi ba.
10Sai Bilatus yace masa "Ba zaka yi mani magana ba? Baka san ina da iko in sake ka ba, kuma in gicciye ka? 11Yesu ya amsa masa, "Ai ba ka da iko a kaina sai dai in an baka daga sama, Saboda haka, wanda ya mika ni a gare ka shine mafi zunubi".
12Da jin haka, sai Bilatus yayi kokari a sake shi, amma sai Yahudawa suka tada murya sukace, "In ka saki mutumin nan, kai ba abokin Kaisar bane, duk wanda ya maida kansa sarki, ya sabawa Kaisar". 13Da Bilatus ya ji irin maganganunsu sai ya fito da Yesu waje ya kuma zauna akan kujeransa a inda ake kira "Dakalin shari'a," a Yahudanci kuma, "Gabbata."
14To a ran nan ana shirye shiryen idin ketarewa, da misalin sa'a ta shidda kenan, wato tsakar rana, Bilatus yace wa Yahudawan "Ga sarkin ku!" 15Su kuwa suka yi ihu, a tafi da shi, a tafi da shi, a gicciye shi, Bilatus yace masu "In gicciye sarkin ku? Sai manyan firistocin sukace "Ba mu da wani sarki sai Kaisar". 16Sai Bilatus ya mika Yesu domin su gicciye shi.
17Sai suka tafi da Yesu, ya fito yana dauke da gicciyen zuwa wurin da ake kira "Wurin kwalluwa" da Yahudanci kuma "Golgota". 18Suka gicciye Yesu a wurin, tare da wasu mutum biyu, daya a kowane gefe, Yesu kuwa na tsikiya.
19Bilatus kuwa ya rubuta wata alama a kan gicciyen, "YESU BANAZARE, SARKIN YAHUDAWA". 20Yahudawa da yawa kuwa suka karanta wannan alama domin wurin da aka gicciye Yesu yana kusa da Birnin. Alamar kuwa an rubuta ta da Yahudanci, da Romanci, da Helenanci.
21Sai manyan firistocin yahudawa sukace wa Bilatus, kada ka rubuta sarkin Yahudawa, amma kace, 'wannan yace "Ni ne sarkin Yahudawa"'. 22Bilatus kuwa ya amsa, "Abinda na rubuta na rubuta kenan."
23Bayan da sojojin suka gicciye Yesu, sai suka yayyaga rigarsa kashi hudu, kowane soja da nasa, kashin, sai kuma alkyabbar. Alkyabbar kuwa bata da dinki an saka tane daga sama har kasa. 24Sai sukace wa junansu, "Kada mu yaga alkyabbar, amma kuzo mu jefa kuri'a a kan ta mu gani ko wanene zai dauke ta, anyi haka ne domin a cika nassi cewa "Sun raba rigata a tsakaninsu, sun kuwa jefa kuri'a domin alkyabbata.
25Sojojin suka yi wadannan abubuwa. Uwar Yesu, da 'yar'uwarta, da Maryamu matar Kilofas, da kuma Maryamu Magadaliya. Wadannan mataye suna tsaye kusa da gicciyen Yesu. 26Da Yesu ya ga mahaifiyarsa da almajirin nan da yake kauna tsaye kusa da juna, yace, "Mace, dubi, dan ki!" 27Sai yace wa almajirin, "Dubi, mahaifiyarka!" Daga wannan sa'a almajirin ya dauke ta zuwa gidansa.
28Bayan wannan Yesu, saboda ya san yanzu komai ya kammala, domin a cika nassin, sai yace "Ina jin kishi. 29A gefensu kuma akwai gora cike da ruwan inabi mai tsami, sai suka tsoma soso a cikin ruwan inabin mai tsami suka daura a wata sanda sai suka mika masa a baki. 30Da Yesu ya tsotsi ruwan tsamin, sai yace "An gama" Sai ya sunkuyar da kansa ya kuwa saki ruhunsa.
31Sai Yahudawan, domin ranar shirye shirye ne, domin kada a bar jikunansu akan gicciye har ranar asabacin (domin asabacin rana ce mai muhimmanci), suka roki Bilatus ya kakkarye kafafunsu kuma ya saukar da su. 32Sai sojojin suka zo suka karya kafafun mutum na farko da kuma mutum na biyun wadanda aka gicciye tare da Yesu. 33Da suka iso kan Yesu sai suka tarar ya riga ya mutu, sai basu kuwa karya kafafunsa ba.
34Duk da haka daya daga cikin sojojin ya soki kuibin shi da mashi, nan da nan sai jini da ruwa suka fito. 35Wanda ya ga wannan, shi ya zama shaida, shaidarsa kuwa gaskiya ce. Ya sani cewa abinda ya fada gaskiya ne saboda ku ma ku gaskata.
36Wadannan sun faru ne domin a cika nassi, "Babu ko daya daga cikin kasusuwansa da za'a karya". 37Kuma wani nassin yace, "Zasu dube shi wanda suka soka."
38Bayan wadannan abubuwa, Yusufu mutumin Arimatiya, wanda yake almajirin Yesu ne (amma a boye saboda tsoron Yahudawa) ya roki Bilatus izini domin ya dauke jikin Yesu. Bilatus kuwa ya bashi izini, sai Yusufu yazo ya dauki jikin. 39Nikodimu ma ya zo, wanda da farko ya zo wurin Yesu da daddare, ya kawo hadin man kamshi na mur da al'ul wajen nauyin awo dari.
40Sai suka dauki jikin Yesu suka sa shi a likkafanin lillin tare da kayan kamshin nan, domin jana'iza bisa ga al'adar Yahudawa. 41To a wurin da aka gicciye shi kuwa akwai wani lambu, a cikin lambun kuma akwai sabon kabari wanda ba'a taba sa kowa ba. 42Da yake ranar shirye shirye ce ta Yahudawa, kabarin kuwa na kusa, sai suka sa Yesu a ciki.

20

1To da sassafe ranar farko ta mako, da sauran duhu, Maryamu Magadaliya ta zo kabarin, ta tarar an kawar da dutsen daga kabarin. 2Sai ta ruga da gudu zuwa wurin Saminu Bitrus tare da almajirin nan da Yesu ke kauna, tace masu, "Sun dauke Ubangiji daga kabarin, bamu kuwa san inda aka sa shi ba."

3Sai Bitrus tare da almajirin nan suka fita, kuma suka tafi kabarin, 4dukansu suka ruga da gudu tare, amma daya almajirin ya riga Bitrus isowa kabarin, 5Sai ya sunkuya ya leka ciki, ya ga likkafanin lillin a wurin, amma fa bai shiga ciki ba.
6Sai Saminu Bitrus ya iso daga bayansa sai ya shiga kabarin, ya tarar da likkafanin lillin a ajiye. 7sai fallen kuma da yake kansa. Ba'a ajiye tare da likkafanin ba amma aka linkeshi aka ajiye shi daban.
8Sai almajirin nan da ya riga isa kabarin shi ma ya shiga ya gani, sai ya ba da gaskiya. 9Har ya zuwa wannan lokacin basu san nassin daya ce zai tashi daga matattu ba. 10Sai almajiran suka sake komawa gida kuma.
11Amma Maryamu tana tsaye a bakin kabarin tana kuka. Yayin da take kuka, sai ta sunkuya ta leka cikin kabarin. 12Sai ta ga mala'iku guda biyu cikin fararen kaya zaune, daya ta wurin kai daya kuma ta wurin kafafu inda aka kwantar da Yesu. 13Sukace mata, "Uwargida don me kike kuka? Sai tace masu, "Domin sun dauke Ubangijina, ban kuwa san inda suka ajiye shi ba.
14Bayan ta fadi haka, ta juya sai ta ga Yesu tsaye a wurin. Amma bata san cewa Yesu bane, 15Yesu yace mata, "Uwargida, me yasa kike kuka? Wa kuma kike nema? Domin tana zaton shine mai kula da lambun, sai tace masa, "Maigida in kaine ka dauke shi, gaya mani inda ka sa shi, ni kuwa in dauke shi."
16Yesu yace mata, "Maryamu". Sai ta juya, tace masa da Armaniyanci "Rabboni!" wato mallam. 17Yesu yace mata, kada ki taba ni, domin har yanzu ban hau wurin Uba ba tukuna, amma kije wurin 'yan'uwana kice masu, zan je wurin Ubana da Ubanku, Allahna da kuma Allahnku". 18Maryamu Magadaliya ta je tace wa almajiran, "Na ga Ubangiji" Ta kuma ce ya fada mata wadannan abubuwa.
19Da yamma a wannan rana, a rana ta farko ta mako, almajiran suna kulle a daki saboda tsoron Yahudawa, Yesu yazo ya tsaya a tsakaninsu, yace "Salama Agareku". 20Bayan ya fadi haka, sai ya nuna masu hannuwansa da kuibinsa. Da almajiran suka ga Ubangiji, sai suka yi farin ciki.
21Yesu ya sake ce masu, "salama agareku. "Kamar yadda Uba ya aiko ni, haka Ni ma na aike ku". 22Da Yesu ya fadi haka, sai ya hura masu lumfashinsa, yace masu, "Ku karbi Ruhu Mai Tsarki. 23Duk wanda kuka gafarta wa zunubai, an gafarta masa; kowa kuka rike zunubansa, an rikesu."
24Toma, daya daga cikin sha biyun, wanda ake kira Dan Tagwai, baya tare dasu lokacin da Yesu ya bayyana. 25Sauran almajiran sukace masa "Mun ga Ubangiji". Sai yace masu, "In ban ga gurbin kusoshi a hannuwansa ba, in sa yatsana a gurbin kusoshin ba, in kuma sa hannuna cikin kuibinsa ba, ba zan bada gaskiya ba.
26Bayan kwana takwas har wa yau almajiran na cikin gida, Toma ma na tare dasu, kofofin suna kulle, sai ga Yesu a tsakaninsu yace, "Salama agareku". 27Sa'an nan yace wa Toma, "Iso nan da yatsanka, dubi hannuwana. Miko hannunka kuma kasa a kuibina, kada ka zama marar bada gaskiya, sai dai, mai bada gaskiya".
28Toma ya amsa yace "Ya Ubangijina da Allahna!" 29Yesu yace masa, "Wato saboda ka gan ni, ka bada gaskiya? Albarka ta tabbata ga wadanda basu gani ba, amma kuwa sun bada gaskiya.
30Yesu yayi wadansu alamu da yawa dabam dabam a gaban almajiransa, wadanda ba'a rubuta a littafin nan ba. 31Amma an rubuta wadannan ne, domin ku bada gaskiya Yesu shine Almasihu, Dan Allah, ta wurin gaskatawa kuma ku sami rai cikin sunansa.

21

1Bayan wadannan abubuwa, Yesu ya sake bayyana kansa ga almajiran a bakin tekun Tibariya. Ga yadda ya bayyana kansa: 2Saminu Bitrus na tare da Toma wanda ake kira Dan Tagwai, da Natana'ilu daga Kana ta kasar Galili, da 'ya'yan nan na Zabadi, da kuma wadansu almajiran Yesu biyu. 3Saminu Bitrus yace masu, "Zani su." sukace masa "Mu ma za mu je tare da kai." Sai suka fita suka shiga jirgi, amma a daren nan basu kama komai ba.

4To, gari na wayewa, sai ga Yesu tsaye a bakin gaci, amma almajiran basu gane cewa Yesu bane. 5Sai Yesu yace masu, "Samari, kuna da wani abinda za a ci?" Suka amsa masa sukace "A'a". 6Yace masu, "Ku jefa taru dama da jirgin zaku samu wasu." Suka jefa tarunsu har suka kasa jawo shi don yawan kifin.
7Sai almajirin nan da Yesu yake kauna yace wa Bitrus, "Ubangiji ne fa!" Da Saminu Bitrus yaji, Ashe, Ubangiji ne, yayi damara da taguwarsa, (don a tube yake), ya fada a tekun. 8Sauran almajiran kuwa suka zo a cikin karamin jirgi, (domin basu da nisa da kasa, kamar kamu dari biyu zuwa sama), janye da tarun cike da kifi. 9Da isowarsu gaci, sai suka ga garwashin wuta a wurin da kifi akai, da kuma gurasa.
10Yesu ya ce masu "Ku kawo wandansu daga cikin kifin da kuka kama yanzu". 11Sai Saminu Bitrus ya hau, ya jawo tarun gaci, cike da manyan kifaye dari da hamsin da uku (153). Amma duk da yawansu, tarun bai tsage ba.
12Yesu yace masu, "Ku zo ku karya kumallo". Daga cikin almajiran kuwa babu wanda yayi karfin halin tambayarsa "Ko shi wanene?" Domin sunsani Ubangiji ne. 13Yesu zo ya dauki gurasar ya ba su, haka kuma kifin. 14Wannan shine karo na uku da Yesu ya bayyana ga almajiransa bayan tashinsa daga matattu.
15Da suka karya kumallon, Yesu yace wa Saminu Bitrus, "Bitrus dan Yahaya, kana kaunata fiye da wadannan?" Bitrus yace masa "I ya Ubangiji, ka sani ina kaunarka" Yesu yace masa "Ka ciyar da 'ya'yan tumakina". 16Ya sake fada masa karo na biyu, "Saminu Dan Yahaya, kana kaunata?" Bitrus Yace masa "I ya Ubangiji, ka sani ina kaunarka". Yesu yace masa, "Ka lura da Tumakina".
17Ya sake fada masa, karo na uku, "Bitrus Dan Yahaya, kana kaunata? Sai Bitrus bai ji dadi ba domin Yesu ya fada masa karo na uku, "Kana kaunata" Yace masa, "Ubangiji ka san komai duka, ka sani ina kaunarka." Yesu yace masa "Ka ciyar da tumaki na. 18Hakika, hakika, Ina gaya maka, lokacin da kake kuruciyarka, kakan yi wa kanka damara, ka tafi inda ka ga dama. amma in ka tsufa, zaka mike hannuwanka wani yayi maka damara, ya kai ka inda baka nufa ba."
19To Yesu ya fadi haka ne domin ya nuna irin mutuwar da Bitrus zai yi ga daukakar Allah. Bayan ya fadi haka, sai yace wa Bitrus, ka biyo ni.
20Bitrus ya juya sai ya ga almajirin da Yesu yake kauna yana biye dasu; wanda ya jingina a kirgin Yesu lokacin cin jibin nan da yace "Ya Ubangiji, wanene zai bashe ka?" 21Da Bitrus ya gan shi, yace wa Yesu "Ya Ubangiji, Me mutumin nan zai yi?"
22Yesu yace masa, "Idan ina so ya zauna har in dawo ina ruwanka? Ka biyo ni." 23Wannan zance ya yadu cikin 'yan'uwa cewa, wannan almajirin ba zai mutu ba. Alhali Yesu bai cewa Bitrus, wannan almajirin ba zai mutu ba, Amma "Idan ina so ya zauna har in dawo ina ruwanka?"
24Wannan shine almajirin da yake shaida wadannan abubuwa, wanda ya rubuta su, kuma mun tabbata shaidarsa gaskiya ne. 25Akwai kuma sauran abubuwa da yawa wanda Yesu yayi. Idan da an rubuta kowannensu daya bayan daya, ina gaya maku, ko duniya bazata iya daukar litattafan da za a rubuta ba.

Ayyukan manzanni

1

1Littafin da na rubuta da farko, Tiyofilos, ya fadi abubuwan da Yesu ya fara yi ya kuma koyar, 2har zuwa ranar da aka karbe shi zuwa sama. Wannan kuwa bayan da ya ba da umarni ga zababbun manzanninsa ta wurin Ruhu Mai Tsarki. 3Bayan ya sha wahala, ya bayyana kan sa da rai a garesu, da alamu da dama masu gamsarwa. Kwana arba'in ya baiyana kansa a garesu yana yi masu magana game da mulkin Allah.

4Yayin da yana zaune tare da su ya basu umarni cewa kada su bar Urushalima, amma su jira alkawarin Uban, wanda ya ce, "Kun ji daga gare ni, 5cewa Yahaya babu shakka ya yi baftisma da ruwa, amma ku za a yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki nan da kwanaki kadan."
6Sa'adda suna tare suka tambaye shi, "Ubangiji, a wannan lokaci ne za ka maido da mulki ga Isra'ila?" 7Ya ce masu, "Ba naku bane ku san lokaci ko sa'a wanda Uba ya shirya ta wurin ikonsa. 8Amma za ku karbi iko, idan Ruhu Mai Tsarki ya zo bisanku, sa'annan za ku zama shaidu na cikin Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, har ya zuwa karshen duniya."
9Lokacin da Ubangiji Yesu ya fadi wadannan abubuwa, yayin da suna kallon sama, sai aka dauke shi zuwa sama, kuma girgije ya boye shi daga idanunsu. 10Da suka dinga kallon sama yayin da ya tafi, nan da nan, mazaje biyu suka tsaya a gabansu cikin fararen tufafi. 11Suka ce, "Ku mazajen Galili me yasa ku ke tsaye a nan kuna kallon sama? Wannan Yesu wanda ya hau zuwa sama zai dawo kamar yadda kuka gan shi yana tafiya zuwa sama."
12Da suka dawo Urushalima daga dutsen Zaitun, wanda ke kusa da Urushalima, tafiyar Asabaci daya ne. 13Da suka iso, sai suka haye zuwa cikin bene inda suke da zama. Sune su Bitrus, Yahaya, Yakubu, Andarawus, Filibus, Toma, Bartalamawus, Matiyu, Yakubu dan Alfa, Siman mai tsattsauran ra'ayi, kuma da Yahuza dan Yakubu. 14Dukansu kuwa suka hada kai gaba daya, yayin da suka ci gaba da naciya cikin addu'a. Tare da su kuma akwai mata, Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma 'yan'uwansa.
15A cikin wadannan kwanaki Bitrus ya tashi tsaye a tsakiyar 'yan'uwa, kimanin mutane dari da ashirin, ya ce, 16" 'Yan'uwa, akwai bukatar Nassi ya cika, wanda Ruhu Mai Tsarki ya fada a baya ta bakin Dauda game da Yahuza, wanda ya jagoranci wadanda suka kama Yesu
17Domin yana daya daga cikinmu kuma ya karbi rabonsa na ladan wannan hidima," 18(Wannan mutum fa ya sai wa kansa fili da cinikin da ya yi na muguntarsa, kuma a nan ya fado da ka, cikinsa ya fashe, hanjinsa suka zubo waje. 19Duka mazaunan Urushalima suka ji wannan, saboda haka suka kira wannan fili da harshensu "Akeldama" wato, "Filin Jini.")
20"Domin an rubuta a littafin Zabura, 'Bari filinsa ya zama kufai, kada a bar kowa ya zauna wurin,'kuma, 'Bari wani ya dauki matsayinsa na shugabanci.'
21Saboda haka ya zama dole, daya daga cikin wadanda suke tare da mu tun lokacin da Ubangiji Yesu yana shiga da fita, a tsakaninmu, 22farawa daga baftismar yahaya har zuwa ranar da aka dauke shi daga wurinmu zuwa sama, ya zama daya daga cikin mu wurin shaidar tashinsa." 23Suka gabatar da mutum biyu, Yusufu wanda ake kira Barsabbas, wanda kuma aka yiwa suna Justus, da kuma Matayas.
24Su ka yi addu'a suka ce, "Ubangiji, kai ka san zuciyar dukan mutane, ka bayyana mana wanda ka zaba cikin su biyun nan 25Domin ya dauki gurbin da kuma manzancin daga inda Yahuza ya kauce zuwa nashi waje" 26suka jefa kuri'a a kansu; zabe ya fada kan Matayas kuma suka lissafta shi tare da manzanni sha dayan.

2

1Da ranar Fentikos ta zo, dukansu suna tare wuri daya. 2Nan da nan sai ga wata kara daga sama kamar ta babbar iska, kuma ta sauko ta cika duka gidan inda suke zaune. 3Sai ga wasu harsuna kamar na wuta sun bayyana a garesu aka rarraba su, kuma suka zauna bisa kowannensu. 4Dukansu suka cika da Ruhu Mai Tsarki suka fara magana da wadansu harsuna, yadda Ruhu ya ba su iko su yi magana.

5A lokacin akwai Yahudawa dake zaune a Urushalima, mutanen Allah, daga kowace kasa karkashin sama. 6Da suka ji wannan kara jama'a duk suka taru suka rude saboda kowannensu ya ji suna magana da harshensa. 7Suka yi mamaki matuka; suka ce, "Lallai, wadannan duka ba Galiliyawa ba ne?
8Yaya mu ke jinsu duka, kowannensu na magana a cikin harshen da aka haife mu? 9Fisiyawa da Mediyawa da Elimawa, da Yahudawa da Kafadokiya, cikin Fontus da Asiya, 10cikin Firgia da Bamfiliya, cikin Masar da yankunan Libiya ta wajen Sur, da baki daga Roma, 11Yahudawa da tubabbun cikin Yahudanci, Kiretawa da Larabawa, duk munji su suna fadi a harshenmu game da manyan ayyukan Allah."
12Dukansu suka yi mamaki suka rikice; suka ce da junansu, "Menene ma'anar wannan?" 13Amma wasu suka yi ba'a suka ce, "Sun bugu ne da sabon ruwan inabi."
14Amma Bitrus ya tashi tare da sha dayan, ya daga murya ya ce da su, "Mutanen Yahuda da dukanku dake zaune a Urushalima, bari ku san wannan; ku saurari maganata. 15Domin wadannan mutanen ba buguwa suka yi ba yadda kuke zato, domin yanzu karfe tara ne na safe kawai.
16Amma wannan shine abinda aka fada ta wurin annabi Yowel. 17Allah ya ce, 'Haka zai kasance a kwanakin karshe, zan zubo Ruhuna a kan dukan mutane, 'ya'yanku maza da mata za su yi anabci, kuma samarinku za su ga wahayoyi, kuma tsofaffinku za su yi mafarkai.
18Haka kuma a bisa bayi na maza da mata, a kwanakin nan zan zubo da Ruhuna, kuma za su yi anabci. 19Zan nuna al'ajibai a sararin sama da kuma alamu a bisa duniya, jini da wuta, da girgije.
20Rana zata juya ta koma duhu kuma wata ya koma jini, kafin Babbar ranan nan ta Ubangiji ta zo. 21Zai kuma zama dukan wanda ya kira ga sunan Ubangiji zai sami ceto.
22Mutanen Isra'ila, ku saurari wadannan magana. Yesu Banazare, mutumin da Allah ya tabbatar da shi gareku ta wurin manyan ayyuka da ban mamaki da alamu da Allah ya yi ta wurinsa a tsakiyarku, kamar yadda ku da kanku kuka sani. 23Saboda tabbataccen shiri da riga sani na Allah, aka bayar dashi, ku kuma, ta hannun mutane 'yan tawaye, kuka gicciye shi kuma kuka kashe shi. 24Wanda Allah ya tayar, bayan ya cire zafin mutuwa daga gareshi, saboda ba zai yiwu ba ta rike shi.
25Gama, game da shi, 'Ina ganin Ubangiji a gabana ko yaushe, domin yana gefen hannun damana saboda kada in firgita. 26Saboda haka zuciyata na farin ciki harshena yana yin murna. Kuma, jikina zai zauna gabagadi.
27Gama ba za ka watsar da raina a lahira ba, ba kuwa za ka bar Mai Tsarkinka ya ga ruba ba. 28Ka bayyana mani hanyar rai; da fuskarka zaka cika ni da farin ciki.
29'Yan'uwa, zan yi magana da ku gabagadi game da baba Dauda: ya mutu kuma aka bizne shi, kuma kabarinsa na nan tare da mu har yau. 30Domin haka, don shi annabi ne kuma ya san Allah ya yi masa alkawari da rantsuwa cewa daga cikin zuriyarsa zai sanya wani bisa kursiyinsa. 31Ya hango wannan al'amari kuma ya yi magana game da tashin Almasihu, 'Ba ayi watsi da shi ba a lahira, kuma jikinsa bai ga rubewa ba.'
32Wannan Yesun - Allah ya tashe shi, wanda dukanmu shaidu ne. 33Saboda haka yadda aka tashe shi zuwa hannun dama na Allah kuma ya karbi alkawarin Ruhu Mai Tsarki daga wurin Uba, shine ya zubo mana wannan da kuke gani kuma kuke ji.
34Dauda bai hau zuwa sama ba, amma ya ce, "Ubangiji ya ce wa Ubangijina, "Zauna hannun dama na, 35har sai na maida makiyanka abin takawar sawunka.'" 36Saboda haka, bari gidan Isra'ila su sani tabbas wannan Yesun wanda kuka gicciye, Allah ya maishe shi Ubangiji da kuma Almasihu.
37Da suka ji haka sai suka soku a zukatansu, suka cewa Bitrus da sauran manzanni, '"Yan'uwa me za mu yi?" 38Sai Bitrus ya ce masu, "Ku tuba ayi wa kowannenku baftisma, cikin sunan Yesu Almasihu domin gafarar zunubanku, kuma za ku karbi baiwar Ruhu Mai Tsarki. 39Domin alkawarin a gareku ne da 'ya'yanku da duk wadanda ke nesa, dukan iyakar mutanen da Ubangiji Allahnmu zai kira."
40Da maganganu da yawa ya ba da shaida kuma ya karfafa su; ya ce, "Ku ceci kan ku daga wannan muguwar tsara." 41Sai suka karbi maganar sa kuma aka yi ma su baftisma, a wannan rana kuma aka sami karin rayuka wajen dubu uku. 42Su ka cigaba cikin koyarwar manzanni da zumunta, cikin kakkaryawar gurasa da kuma cikin addu'o'i.
43Tsoro ya sauko bisa kowane rai, kuma aka yi abubuwan ban mamaki da alamu da yawa ta wurin manzannin. 44Duka wadanda suka ba da gaskiya suna tare kuma komai nasu na kowanensu ne, 45kuma suka saida kadarorinsu da mallakarsu kuma suka rarrabawa kowa, bisa ga irin bukatar da kowannensu yake da ita.
46A kowace rana suka cigaba tare da nufi daya a cikin haikali, suna kakkarya gurasa a gidaje, kuma suna raba abinci tsakaninsu cikin farin ciki da tawali'u a zuciya; 47Suna yabon Allah kuma suna da tagomashi a gaban dukan mutane. Ubangiji kuma kullum yana kara masu wadanda suke samun ceto.

3

1Sa'adda Bitrus da Yahaya suna hanya zuwa haikali a lokacin addu'ar karfe uku. 2Wani mutum, gurgu ne tun daga haihuwa, ana daukar sa kulluyomi zuwa kofar haikali da ake kira Kyakkyawa, domin bara gun mutanen da ke shiga haikalin. 3Da ya ga Bitrus da Yahaya suna shiga haikalin, sai ya roke su sadaka.

4Bitrus da Yahaya kuwa suka zuba masa ido, Bitrus ya ce, "Ka dube mu." 5Gurgun nan kuwa ya dube su, yana tsammanin zai sami wani abu a wurin su. 6Amma Bitrus ya ce, "Azurfa da Zinariya ba ni da su, amma abin da nake da shi, zan baka. A cikin sunan Yesu Almasihu Banazare, Yi tafiya"
7Bitrus ya kama hannun damarsa, ya daga shi; nan da nan kafafunsa da kashin idon sawayensa suka samu karfi. 8Da gurgun ya yunkura, ya mike tsaye sai ya fara takawa; ya shiga haikali tare da Bitrus da Yahaya, yana takawa, yana tsalle, yana kuma girmama Allah.
9Dukan mutane suka gan shi yana tafiya yana kuma yabon Allah. 10Sun lura cewa, shine mutumin da ke zama yana bara a Kyakyawar kofar haikali; sai suka cika da mamaki domin abin da ya faru.
11Yayin da yake rike da Bitrus da Yahaya, dukan jama'a suka matso wurinsu, a gefen dakalin Sulaimanu, suna ta mamaki kwarai. 12Da Bitrus ya ga haka ya amsa wa jama'ar, "Ya ku mutanen Isra'ila, don me ku ke mamaki?" Don me ku ka zura mana ido, kamar mu ne muka sa shi ya yi tafiya da ikon kanmu ko adalcin mu?
13Allah na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, Allah na iyayenmu ya girmama bawansa Yesu. Shi kuka ki kun kuma bashe shi a gaban Bilatus da ya so ya sake shi. 14Kuka ki Mai Tsarkin nan, Mai Adalcin, maimakon haka kuka ce a sakkar maku mai kisan kai.
15Kun kashe mai ba da rai, wanda Allah ya tayar daga matattu, mu kuwa shaidu ne ga wannan al'amari. 16Yanzu, ta bangaskiya ga sunansa - wannan mutum da kuke gani kuma kun san shi - ta wurin wannan sunan ne ya sami karfi. Bangaskiya cikin Yesu ta ba shi cikakkiyar lafiya, a gabanku duka.
17Ya ku 'yan'uwa, na san kun yi haka ne cikin rashin sani, yadda shugabaninku suka yi. 18Amma duk abubuwan da Allah ya fada ta bakin dukan anabawansa, cewa Almasihunsa zai sha wahala, yanzu ya cika.
19Saboda haka, Ku tuba, ku juyo, domin a shafe zunubanku, domin lokacin sabuntuwa daga wurin Ubangiji ya zo; 20domin a aiko maku da Almasihu wanda aka kaddara wato, Yesu.
21Shine wanda dole sama ta karbe shi har zuwa lokacin komo da dukan abubuwa, game da abubuwan da Allah ya fada tun da ta bakin annabawansa tsarkaka. 22Musa hakika ya ce, 'Ubangiji Allah zai tayar maku da wani annabi kamar ni daga cikin, 'yan'uwanku. Za ku saurari dukan abin da zai fada maku. 23Zai kasance kowanne mutum da bai saurari annabin nan ba za a kau da shi gabadaya daga cikin mutanensa.'
24I, dukan annabawa tun daga Sama'ila da wadanda suka zo bayansa, sun yi magana sun ambaci wadannan kwanaki. 25Kune 'ya'yan annabawa da na alkawari wanda Allah ya yi da kakanninku, yadda ya ce wa Ibrahim, 'Daga zuriyarka dukan al'uman duniya za su sami albarka.' 26Bayan da Allah ya ta da bawansa, a gareku ne ya fara aiko shi, domin ya albarkace ku tawurin juyadda kowannenku daga muguntarsa."

4

1Yayin da Bitrus da Yahaya suna kan magana da mutanen, sai firistoci da shugaban masu tsaron Haikali da kuma Sadukiyawa suka afko masu. 2Sun damu sosai domin Bitrus da Yahaya suna koyar da mutane game da Yesu kuma suna shelar tashinsa daga matattu. 3Suka kama su suka jefa kurkuku sai washegari, domin yamma ta riga ta yi. 4Amma mutane da yawa da suka ji sakon suka ba da gaskiya; kimanin mazaje dubu biyar ne kuwa suka ba da gaskiya.

5Washegari, da shugabaninsu, da dattawansu, da Marubuta suka taru a Urushalima. 6Anas babban firist, yana nan, da Kayafa, da Yahaya da Iskandari, da dukan dangin babban firist 7Da suka kawo Bitrus da Yahaya a tsakiyarsu sai suka tambaye su, "Da wanne iko, ko cikin wanne suna k ka yi haka?"
8Sai Bitrus, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya ce, "Ku shugabanni da dattawan jama'a, 9idan mu yau ana tuhumarmu saboda aikin kirki da aka yi ga wannan mara lafiya - ta yaya wannan mutum ya sami lafiya? 10Bari ku da dukan mutanen Isra'ila, ku san wannan, cikin sunan Yesu Almasihu Banazare, wanda kuka giciye, wanda Allah ya tayar daga matattu ta dalilinsa ne wannan mutumin yake tsaye a gaban ku lafiyayye.
11Yesu Almasihu ne dutsen da ku magina kuka ki, amma an mai da shi kan gini. 12Babu ceto daga kowanne mutum, domin babu wani suna da aka bayar karkashin sama, a cikin mutane wanda ta wurinsa za a iya samu ceto."
13Sa'adda, suka ga karfin halin Bitrus da Yahaya, suka gane mutane ne talakawa marasa ilimi, sai suka yi mamaki, suka kuma lura suka gane Bitrus da Yahaya sun kasance tare da Yesu. 14Da yake suna ganin mutumin nan da aka warkar tare da su, sai suka rasa abin yi.
15Amma bayan sun fitar da manzannin daga majalisa sai suka tattauna a tsakaninsu. 16Suka ce, "Yaya za mu yi da wadannan mutane? Babu shakka aikin al'ajibi ya faru ta wurinsu, kuma sananne ne ga dukan mazauna Urushalima, kuma ba mu da iko mu musanci haka. 17Amma saboda kada ya cigaba da yaduwa cikin mutane, bari mu yi masu kashedi kada su kara magana da kowa cikin wannan suna." 18Suka kira Bitrus da Yahaya suka dokace su kada su kara magana ko kuma koyarwa ko kadan a cikin sunan Yesu.
19Amma Bitrus da Yahaya suka amsa suka ce, "Ko ya yi daidai a gaban Allah mu yi maku biyayya fiye da shi, ku hukunta. 20Baza mu iya daina magana game da abubuwan da muka ji kuma muka gani ba."
21Bayan sun sake yi wa Bitrus da yahaya kashedi, sai suka sake su, su tafi. Domin ba su iya samu wata hujja da za su hore su a kai ba, domin dukan mutane suna yabon Allah saboda abin da ya faru. 22Mutumin da ya sami wannan al'ajibi na warkarwa yana sama da shekara arba'in.
23Bayan an sake su, Bitrus da Yahaya suka zo cikin mutanensu suka ba da rahoton duk abin da manyan firistoci da dattawa suka fada masu. 24Da suka ji haka, suka daga muryarsu tare ga Allah suka ce, "Ubangiji, kai da ka yi sama da duniya da teku da duk abin da ke cikinsu, 25kai wanda ta wurin Ruhu Mai Tsarki ta bakin ubanmu Dauda bawanka, ya ce, 'Me ya sa al'ummai suka tunzura, kuma mutane suke tunanin abubuwan banza?
26Sarakunan duniya sun hada kansu tare, kuma shugabanninsu sun taru don su yi gaba da Ubangiji, da kuma Almasihunsa.'
27Hakika, Hiridus da Buntus Bilatus, tare da al'ummai da mutanen Isra'ila, sun taru a wannan birni domin su yi jayayya da bawanka mai tsarki Yesu, shafaffe. 28Sun taru domin su aiwatar da dukan abin da hannunka da nufinka ya shirya zai faru.
29Yanzu, Ya Ubangiji ka dubi kashedin su, ka ba bayin ka ikon furta maganar ka gabagadi. 30Sa'adda ka mika hannunka domin warkarwa, alamu da al'ajibai su faru ta wurin sunan bawanka mai tsarki Yesu." 31Bayan sun gama addu'a, wurin da suka taru ya girgiza, suka cika da Ruhu Mai Tsarki, suka furta maganar Allah gabagadi.
32Babban taron da suka ba da gaskiya kansu hade yake; kuma ba wanda ya ce da abinda ya mallaka nasa ne; maimakon haka, komai na su daya ne. 33Da iko mai karfi manzannin suka yi shelar shaidarsu game da tashin Yesu Ubangiji daga matattu, babban alheri kuma na bisansu.
34Babu wani a cikinsu wanda ya rasa komai, domin masu filaye da gidaje suka sayar suka kawo kudin abin da suka sayar 35sai suka kawo kudin gaban manzanni. Aka rarraba wa kowanne mutum bisa ga bukatarsa.
36Yusufu, Balawi, mutumin tsibirin Kubrus, wanda manzannisu ka yi wa lakani da suna Barnaba. (wato, mai karfafa zuciya). 37Yana da fili sai ya sayar da shi ya kawo kudin gaban manzanni.

5

1Sai wani mai suna Hananiya da matarsa Safiratu, suka sayar da filinsu, 2Hananiya kuwa ya boye wasu daga cikin kudin filin, (kuma da sanin matarsa), sa'annan suka kawo ragowar kudin a gaban manzannin.

3Amma Bitrus ya ce, "Hananiya don me shaidan ya cika zuciyarka, har ka yi wa Ruhu Mai Tsarki karya? Har ka boye wasu daga kudin filin? 4Sa'adda ba ka sayar da filin ba, ba mallakarka bane? Bayan da ka sayar ma, ba naka bane? Don me kayi irin wannan tunanin a zuciyarka? To ba mutane ka yi wa karya ba, Allah ka yi wa." 5Nan take da jin haka, Hananiya ya fadi ya ja numfashinsa na karshe. Dukan mutanen da suka ji labarin kuwa tsoro mai girma ya afko masu 6Matasa suka zo suka nannade gawarsa, suka fitar da shi waje suka binne shi.
7Bayan wajen sa'a uku, sai matarsa ta iso, ba tare da sanin abin da ya faru ba. 8Sai Bitrus ya ce mata, "ki gaya mini ko nawa kuka sayar da filin?" Sai ta amsa, "ta ce kaza ne."
9Sa'annan Bitrus ya ce mata, "Don me kuka shirya wannan makidar tare da mijinki don ku gwada Ruhun Ubangiji? Kiji tafiyar wadanda suka bizne mijinki a bakin kofa, kuma za su dauke ki yanzu." 10Nan take sai ta fadi a gabansa, ta ja numfashinta na karshe, matasan kuwa suka zo suka same ta ta mutu; sai suka dauki gawarta suka kai waje suka kuma bizne ta kusa da mijinta. 11Tsoro mai girma kuwa ya afko wa iklisiyar gaba daya da dakan wadanda suka ji wadan nan al'amura.
12Ayyukan alamu da ban mamaki masu yawa kuwa sun faru ga mutane, ta hannun manzannin. Dukansu kuma suna nan tare a dakalin Sulaimanu, 13Sai dai babu mai karfin halin ya hada kai tare dasu; amma suna da kwarjini sosai a gaban jama'a.
14Har wa yau aka rika samun karin masu ba da gaskiya, dinbin jama'a, maza da mata, 15har sukan dauki marasa lafiya su kai su bakin titi, suna kwantar da su a bisa gadaje da shinfidu, domin idan Bitrus ya zo wucewa ko da inuwarsa ma ta taba wasunsu. 16Mutane dayawa kuwa sukan zo daga garuruwan da ke kewaye da Urushalima, suna kuma kawo masu rashin lafiya, da wadanda aljannu ke damunsu, aka kuma warkar da su duka.
17Amma babban firist ya taso tare da duk wadanda ke tare da shi (wato 'yan darikar Sadukiyawa); suka cika da kishi matuka 18suka kama manzannin suka kuma jefasu a kurkuku.
19A cikin dare sai mala'ikan Ubangiji ya bude kofofin kurkukun ya kuma fito da su waje, ya ce, 20"Kuje ku tsaya a gaban haikali ku kuma gaya wa mutane maganar wannan rai." 21Sa'adda suka ji haka, sai suka tafi haikalin da wayewar gari suka yi koyarwa. Amma babban firist da jama'arsa suka zo suka kuma kira taro da kuma dukan yan majalisa, da dattawan jama'ar Isra'ilawa suka fito suka kuma ba da umarni, a fito masu da manzannin.
22Amma ma'aikatan da suka je kurkukun basu sami kowa, a kurkukunba, sai suka dawo suka ba da rahoto, 23Su ka ce kurkukun a rufe gam da masu gadi suna nan a tsaye a bakin kofar amma da muka shiga, bamu sami kowa a ciki ba.
24Yanzu sa'adda shugaban haikalin da manyan firistoci suka ji wadannan kalamai, sai suka rikice sosai game da su, suka ce yanzu me wannan zai haifar. 25Sai wani ya zo ya ce masu, "Wadannan mutanen da kuka jefa a kurkuku suna can a cikin haikali suna koyar da jama'a."
26Sai shugaban haikalin ya je da ma'aikatansa suka kawosu, ba tare da tashin hankali ba, domin gudun kada jama'a su jejjefesu. 27Da suka kawo su, sai suka gabatar da su gaban majalisa, babban firist kuwa ya tuhume su, 28cewa "Ba mun yi maku kashedi da karfi kada ku yi koyarwa cikin wannan sunan ba? Amma ga shi duk kun cika Urushalima da koyarwarku, kuna kuma neman kusa jinin mutumin nan ya sauko kanmu."
29Amma Bitrus da manzannin suka amsa suka ce, "Dole mu yi wa Allah biyayya ba mutane ba. 30Allah na ubanenmu ya ta da Yesu, wanda kuka kashe, ta wurin rateye shi a bisa itace, 31Allah kuwa ya daukaka shi a hannun damarsa, domin ya zama sarki da kuma mai ceto, ya ba Isra'ila tuba da gafarar zunubai. 32Mu kuwa shaidu ne ga wadannan al'amura, haka ma Ruhu Mai Tarki, wanda Allah ya bayar ga dukan wadanda suka yi biyayya a gareshi."
33Da yan majalisa suka ji haka sai suka fusata kwarai da gaske, har suka nemi su kashe manzannin. 34Amma wani Bafarise mai suna Gamaliel, malami ne kuma na attaura wanda dukan jama'a suna martabawa, sai ya mike ya ba da umarni cewa a fid da manzannin waje na dan lokaci.
35Sai ya ce masu "Ya ku mutanen Isra'ila, ku lura sosai da a binda kuke niyyar yi wa mutanen nan, 36A kwanakin baya wani ya zo mai suna Tudas ya dauki kansa wani abu, kimanin mutane dari hudu ne suka bishi, amma da aka kashe shi jama'arsa baki daya sai suka watse, ba wanda ya kara jin labarinsu. 37Bayansa kuma, aka yi wani mai suna Yahuza na Galili wanda a kwanakin kidaya, ya zo ya rinjayi mutane da yawa, shima ya lalace, duk wadanda suka bi shi kuwa suka watse.
38Don haka ina gaya maku ku rabu da mutanen nan, domin idan shirinsu ko kuma ayyukansu na mutane ne za su lalace. 39Amnma idan abin nan daga Allah yake baza ku iya lalata su ba; kada ya zama kuna gaba da Allah." Sai suka rinjayu.
40Da suka kira manzannin ciki suka yi masu duka, sai suka umarce su da cewa kada su sake koyarwa a cikin sunan Yesu, sai suka barsu suka tafi. 41Suka fita daga cikin majalisar, suna murna domin sun cancanta su sha wulakanci saboda sunan. 42Bayan haka kullayomin suna zuwa haikali, suna bi gida gida, suna wa'azi, suna kuma koyarwa ba fasawa cewa Yesu shine Almasihu.

6

1A wadannan kwanaki, yawan almajiran ya ci gaba da ribanbanya, sai Yahudawan da suke zama a kasar Helanawa suka fara gunaguni game da Yahudawan Isra'ila, domin basu damu da gwamrayensu, wajen raba abinci da ake yi kullum.

2Manzannin nan sha biyu suka kira taron almajiran suka ce masu, "Bai kamata mu bar maganar Allah mu shiga hidimar rabon abinci ba. 3Don haka ku zabi 'yan'uwa maza daga cikinku, mutane bakwai wadanda a ke ganin su da daraja, cike da Ruhu da kuma hikima, wadanda za mu zaba suyi wannan hidima. 4Mu kuwa mu ci gaba da da addu'a da kuma hidimar kalmar."
5Maganar su kuwa ta farantawa dukan jama'a rai sosai. Sai suka zabi Istifanus, shi kuwa mutum ne cike da bangaskiya kuma da Ruhu Mai Tsarki da Filibus, da Birokoros, da Nikanar, da Timan, da Barminas, da kuma Nikolas, mutmin Antakiya wanda ya yi tuban Yahudanci. 6Masu bin kuwa suka gabatar da wadannan mutanen a gaban manzannin, su kuwa suka yi masu addu'a suka kuma dora hannuwansu a kansu.
7Sai maganar Allah ta yawaita; yawan almajiran kuwa ya rubanbanya matuka a Urushalima; firistoci da yawa na Yahudawa suka bada gaskiya.
8Sai Istifanus, cike da alheri da iko, ya rika yin ayyukan ban mamaki da alamu a cikin jama'a. 9Amma sai ga wadansu mutane daga wata majami'a da ake kira majami'ar Yantattu, wato su Kuramiyawa da Iskandariyawa, da kuma wasu daga kasar Kilikiya da Asiya. Wadannan mutanen kuwa suna muhawara da Istifanus.
10Amma suka kasa yin tsayayya da Istifanus, saboda irin hikima da Ruhun da Istifanus ya ke magana da shi. 11Sai a asirce suka zuga wasu mutane su je su ce, "Ai munji Istifanus yana maganganun sabo game da Musa da kuma Allah."
12Sai suka zuga mutanen, har da dattawa da marubuta suka tunkari Istifanus, suka kama shi, suka kawo shi gaban majalisa. 13Suka kawo masu shaidar karya suka ce, "Wannan mutumin har yanzu bai dena maganganun gaba akan wannan wuri mai tsarki da kuma shari'a ba. 14Domin kuwa mun ji shi, yana cewa wannan Yesu Banazarat zai rushe wannan wuri zai kuma canza al'adun da muka gada daga wurin Musa." 15Dukan wadanda suke zaune a majalisar suka zuba masa ido, sai suka ga fuskarsa kamar ta mala'ika.

7

1Sai babban firist ya ce, "Wadannan al'amura gaskiya ne?" 2Sai Istifanus ya amsa ya ce, "Ya 'yan'uwa da ubanni, ku saurare ni, Allah Madaukaki ya bayyana ga ubanmu Ibrahim tun yana can kasar Mesofotamiya, kafin ma ya zauna a kasar Haran; 3ya ce masa, 'Ka bar kasarka da danginka, ka tafi kasar da zan nuna maka.'

4Sa'annan ya bar kasar Kaldiyawa ya zo ya zauna a Haran; daga can, bayan rasuwar mahaifinsa, sai Allah ya kira shi zuwa wannan kasa da kuke ciki. 5Amma Allah bai ba shi kasar gado ba tukuna, ko da misalin tafin sawunsa. Amma ya alkawarta - ko da yake bai riga ya haifi da ba tukuna - wanda zai ba shi kasar gado, shi da zuriyarsa, a bayansa.
6Allah ya yi magana da shi kamar haka, cewa zuriyarsa za su yi bakonci a wata kasa wadda ba tasu ba, mutanen wannan kasar kuwa za su gwada masu bakar azaba su kuma bautar da su har shekaru dari hudu. 7'Kuma zan hukunta wannan al'umma da ta bautar da su,' Allah ya ce, 'Bayan haka za su fito daga wannan kasa su bauta mini a wannan wuri.' 8Allah ya ba Ibrahim alkawarin kaciya, sai Ibrahim ya haifi Ishaku ya yi masa kaciya a rana ta takwas; Ishaku ya haifi Yakubu, Yakubu kuma ya haifi ubanni Isra'ila su goma sha biyu.
9Wadannan 'yan'uwa suka yi kyashin danuwansu Yusifu suka sayar da shi bauta zuwa Masar. Amma Allah na tare da shi. 10Ya kuwa cece shi daga dukan sharin da yan uwansa suka kulla masa, Allah kuwa ya ba shi tagomashi da hikima a gaban Fir'auna, sarkin Masar. Fir'auna kuwa ya mai da shi mai mulki a dukan kasar Masar da kuma dukan mallakarsa.
11Sai aka yi babbar yunwa a dukan kasar Masar da ta Kan'ana, iyayenmu suka sha wuya saboda rashin abinci. 12Amma lokacin da Yakubu ya ji akwai hatsi a kasar Masar, sai ya aiki ubannimu a karo na farko. 13Da suka je a karo na biyu, sai Yusifu ya bayyana kansa ga yanuwansa; a wannan lokaci ne Fir'auna ya gane da yanuwan Yusufu.
14Yusufu ya aiki yanuwansa su kawo Yakubu ubansu da dukan mallakarsu da iyalansu zuwa Masar, Dukansu mutane saba'in da biyar ne. 15Yakubu ya tafi ya zauna a Masar; shi da zuriyarsa har mutuwar su. 16Aka dauke su zuwa Shekem aka binne su a kabarin da Ibrahim ya saya da kudin azurfa daga hannun yayan Hamor a Shekem.
17Yayin da alkawarin Allah ya kusato wanda Allah ya fada wa Ibrahim, mutanen suka karu suka hayayyafa kwarai a Masar, 18Sai a ka yi wani sarki a Masar wanda bai san Yusifu ba, 19Wannan sarki ya yaudari kakkaninmu ya yi masu mugunta kwarai da gaske, har ma ya kai ga suna barin jariransu cikin hasari don su ceci rayukansu.
20A wannan lokaci ne aka haifi Musa, kuma kyakkyawan yaro ne sai aka yi renon sa tsawon wata uku a gidan mahaifinsa a asirce. 21Yayin da aka jefar da shi, sai diyar Fir'auna ta dauke shi ta rene shi kamar danta.
22Aka ilimantar da Musa da dukan ilimi irin na Masar; kuma ya shahara cikin fasahar magana da kuma ayyukansa. 23Amma lokacin da yakai shekara arba'in, sai ya yi niyyar ya ziyarci 'yan'uwansa, Isra'ilawa. 24Sai ya ga wani na cin zalin Ba Isra'ile, Musa kuwa ya taimaki wanda ake kwara ta wurin murkushe Bamasaren: 25zaton Musa 'yan'uwansa za su fahimci taimakon Allah ne ya zo masu amma ina! Basu gane ba.
26Washegari ya ga wasu Isra'ilawa na fada da junansu; ya yi kokari ya raba su; sai ya ce masu, 'Malamai, ku 'yan'uwan juna ne; don me kuke fada da junanku?' 27Amma shi wanda ake kwarar makwabcinsa ya ture Musa a gefe guda, ya ce, 'Wa ya nada ka shugaba ko alkali akanmu? 28Kana so ka kashe ni ne, kamar yadda ka kashe Bamasaren nan jiya?'
29Da jin haka sai Musa ya gudu, zuwa kasar Midinawa, a matsayin dan gudun hijira. Anan ya haifi "ya'ya biyu maza. 30Bayan da shekaru arba'in suka wuce, sai mala'ika ya bayyana gare shi a jeji, kusa da dutsen Sinai, a cikin harshen wuta a cikin jeji.
31Sa'adda Musa ya ga wutar, mamaki ya kama shi; sai ya maso kusa don ya kara dubawa, sai ya ji muryar Ubangiji na cewa, 32'Nine Allah na ubanninka, Ibrahim, da na Ishaku, da na Yakubu.' Musa ya razana har ma bai sake daga kai ya duba ba.
33Ubangiji ya ce masa, 'Tube takalminka, domin in da kake tsaye wuri mai tsarki ne. 34Ba shakka na ga wahalar da mutane na ke sha a Masar, kuma na ji nishinsu, don haka na zo in cece su, yanzu fa sai ka zo, in aike ka zuwa Masar.'
35Wannan fa shine Musan da suka ki, harma da cewa, 'Wanene ya nada ka alkali ko shugaba a kanmu?' Shine kuma wanda Allah ya aiko masu a matsayin shugaba da kuma mai ceto. Allah ya aiko shi ta hannun mala'ikan da ya gani a daji. 36Bayan alamu da al'ajibai iri-iri a Masar da kuma Baharmaliya, Musa ya fito da su daga Masar da kuma cikin jeji, a lokacin da suka yi tafiya shekara arbain. 37Wannan shine Musan da ya cewa Isra'ilawa, 'Ubangiji zai tayar maku da wani annabi kamar ni daga cikin Yan'uwan ku.'
38Wannan shine mutumin da ke tare da mutane a jeji. Karkashin jagorancin mala'ikan da ya yi magana da shi a dutsen Sinai. Wannan ne mutumin da ke tare da ubannen mu, wannan shi ne mutumin da ya ba mu maganar Allah mai rai. 39Wannan shine mutumin da ubannenmu suka ki su yi masa biyayya; su ka fitar da shi daga cikinsu, suka kudurta a zuciyarsu za su koma masar. 40A lokacin ne suka cewa Haruna, 'ya yi masu allolin da za su jagorance su zuwa masar. Domin kuwa ga zancen Musan nan da ya fito da mu daga Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba.'
41Sai suka kera dan maraki suka kawo wa gunkin hadaya, suka yi murna da abin da hannayensu suka kera. 42Allah ya bashe su su bauta wa tauraran sama, kamar yadda yake a rubuce cikin littattafafan annabawa, 'Kun mika mani hadayu na yankakkun dabbobi a jeji ne a shekaru arba'in din nan ya ku Isra'ilawa?'
43Kun yarda da haikalin Molek da kuma tauraron allahn nan Rafem, da kuma siffofin nan da kuka kera don ku yi masu sujada; don haka zan kai ku bauta har gaba da Babila.'
44Kakkaninmu suna da alfarwa ta sujada domin shaida a cikin jeji, kamar yadda Allah ya umarta yayin da ya yi magana da Musa, cewa ya yi shi bisa ga salon da aka nuna mashi. 45Wannan shine Alfarwar da kakkaninmu suka zo da shi, a lokacin Joshuwa. Wannan ya faru ne yayin da suka mallaki wannan kasa ta al'ummai da Allah ya kora a gaban kakkaninmu. Haka abin yake har ya zuwa zamanin Dauda, 46wanda ya sami tagomashi a wurin Allah; don ya gina masujada domin Allah na Yakubu.
47Amma Sulaimanu ne ya gina Gidan Allah. 48Sai dai Madaukaki ba yakan zauna a gidan da hannaye suka gina ba, kamar yadda annabin ya ce, 49'Sama kursiyina ce, duniya kuwa wurin ajjiye sawayena ne. To wane irin gida za ku gina mani? inji Ubangiji: ko kuwa ina ne wurin da zan huta? 50Ko ba hannayena ne suka yi dukan wadannan ba?'
51Ku mutane masu taurin kai masu zuciya mara kaciya da kunnuwa marasa ji, kullum kuna gaba da Ruhu Mai Tsarki, kuna aikata abin da kakkaninku suka aikata. 52Wane annabi ne kakkaninku ba su tsanantawa ba? Sun kashe annabawan da suka rigayi zuwan Mai Adalcin nan, kuma kun zama wadanda suka kasance masu bashe shi da masu kashe shi, 53kune mutanen da kuka karbi shari'a wadda mala'iku suka bayar, amma ba ku kiyaye ta ba".
54Yayin da majalisar suka ji wannan, sai ransu ya baci kwarai, har suna cizon hakoransu don gaba da Istifanus. 55Amma shi, cike da Ruhu Mai Tsarki, sai ya daga idonsa sama, ya ga daukakar Allah; ya kuma hango Yesu na tsaye a hannun daman Allah. 56Istifanus ya ce, "Duba, ina ganin sama ta bude, ga Dan Mutum na tsaye a hannun dama na Allah."
57Amma yan majalisar suka daga murya da karfi, suka yi ihu, suka kuma toshe kunnuwansu, gaba dayansu suka afka masa; 58suka fitar da shi bayan gari, suka jejjefe shi da duwatsu, don shaida sai suka tube manyan rigunansu suka ajiye a gaban wani matashi da ake ce da shi Shawulu.
59Lokacin da suke kan jifan Istifanus, ya dinga kira yana cewa, "Ya Ubangiji Yesu, ka karbi ruhu na." 60Ya durkusa ya daga murya da karfi, ya ce, "Ya Ubangiji, kada ka rike wannan zunubi a kansu." Yayin da ya fadi wannan, sai ya yi barci.

8

1Bulus ya amince da mutuwarsa. A wannan rana tsanani mai zafi ya fara tasowa akan Iklisiya da take a Urushalima, sai masu bangaskiya duka suka bazu ko ina a cikin garuruwan Yahudiya da Samariya, sai manzannin kadai aka bari. 2Amintattun mutane suka bizne Istifanus suka yi babban makoki game da shi. 3Amma Shawulu ya yi wa Iklisiya mugunta kwarai, ya dinga shiga gida gida yana jawo mutane maza da mata, kuma yana kulle su cikin kurkuku.

4Duk da haka masu bangaskiyar nan da suka warwatsu suka tafi suka dinga yada wa'azin maganar. 5Filibus ya tafi can Samariya ya yi shelar Almasihu.
6Da taron mutane suka ji kuma suka ga alamun da Filibus yake yi, sai suka mai da hankali dukansu domin su ji abinda yake fadi. 7Domin kazaman ruhohi sun fito daga cikin mutane da yawa da suka saurare shi suna kuka da kururuwa; nakasassun mutane dayawa da guragu suka warke. 8Kuma aka yi farin ciki mai girma a birnin.
9Amma akwai wani mutum a cikin birnin da ake kira Siman, wanda tun farko shi masafi ne da kuma dan dabo, yana yi wa mutanen Samariya abubuwan ban mamaki, yayin da yake kiran kansa wani mai muhimmanci. 10Dukan Samariyawa, manya da yara, suna sauraronsa, su kan ce, "Wannan mutum shine ikon Allahn nan wanda ake kira mai girma." 11Suna sauraron sa, domin ya dade yana yi masu abubuwan mamaki da tsafe-tsafensa.
12Amma da suka yi bangaskiya da wa'azin bisharar da Filibus yake yi game da mulkin Allah da sunan Yesu Almasihu, sai aka yi masu Baftisma dukansu maza da mata. 13Har shima Siman da kansa ya ba da gaskiya. Bayan an yi masa Baftisma ya cigaba da bin Filibus, da ya ga ana nuna alamu da manyan ayyuka, sai ya yi mamaki.
14Da manzannin da ke Urushalima suka ji labarin Samariya ta karbi maganar Allah, sai suka aika masu Bitrus da Yahaya. 15Da suka iso, suka yi masu addu'a, domin su karbi Ruhu Mai Tsarki. 16Domin har wannan lokaci, Ruhu Mai Tsarki bai sauko kan kowannensu ba; an dai yi masu baftisma ne kadai cikin sunan Ubangiji Yesu. 17Sai Bitrus da Yahaya suka dora masu hannuwansu, sai suka karbi Ruhu Mai Tsarki.
18Sa'adda Siman yaga ana bayar da Ruhu Mai Tsarki ta wurin dorawar hannuwan manzanni, ya basu kudi. 19Ya ce, "Ku bani wannan iko, ni ma, don duk wanda na dora wa hannu ya karbi Ruhu Mai Tsarki."
20Amma Bitrus yace masa, "Azurfarka ta lalace tare da kai, saboda kana tunanin za ka malaki baiwar Ubangiji da kudi. 21Baka da wani rabo a wannan al'amari, domin zuciyarka ba daidai take da Allah ba. 22Saboda haka ka tuba daga wannan muguntarka, ka kuma yi addu'a ga Ubangiji, domin mai yiwuwa ya gafarta maka game da manufar zuciyarka. 23Domin na gane kana cikin bacin rai da kuma cikin daurin zunubi."
24Siman ya amsa ya ce, "Kayi addu'a ga Ubangiji domina, kada wani daga cikin abubuwan nan da ka fada ya faru da ni."
25Sa'anda Bitrus da Yahaya suka bada shaida kuma suka fadi maganar Ubangiji, sun koma Urushalima; akan hanya, suka yi wa'azin bishara a kauyukan samariyawa da yawa.
26Yanzu kuwa Mala'ikan Ubangiji ya yi wa Filibus magana cewa, "Tashi ka tafi ta kudu da hanyar da ta yi kasa daga Urushalima zuwa Gaza" (wannan hanyar yana cikin hamada.) 27Ya kuwa tashi ya tafi. Sai ga wani mutum daga Habasha, baba ne mai babban matsayi a karkashin Kandakatu, sarauniyar Habasha. Shine yake mulkin dukan dukiyarta. Ya zo Urushalima domin ya yi ibada. 28Yana komawa zaune cikin karussarsa, kuma yana karanta Littafin annabi Ishaya.
29Ruhun ya ce wa Filibus, "Ka je kusa da karussar nan." 30Sai Filibus ya gudu ya same shi, kuma ya ji shi yana karanta littafin annabi Ishaya, sai ya ce, "Ka fahimci abin da kake karantawa?" 31Bahabashen ya ce. "Yaya zan iya, idan ba wani ya bishe ni ba?" Ya roki Filibus ya shigo cikin karussar ya zauna tare da shi.
32Wannan kuwa shine nassin da Bahabashen yake karantawa, "An kai shi kamar tunkiya zuwa mayanka; shiru kuma, kamar dan rago a hannun masu sosayarsa, bai bude baki ba. 33Cikin kaskancinsa aka yi masa shari'a da rashin adalci: Wa zai bada tarihin tsararsa? Domin an dauke ransa daga duniya."
34Sai baban ya tambayi Filibus, ya ce, "Na roke ka, gaya mani, game da wa annabin yake magana? Da kansa, ko kuwa wani mutum dabam?" 35Filibus ya fara magana; akan littafin Ishaya, ya kuwa yi masa wa'azi akan Yesu.
36Yayin da suke tafiya akan hanya, sai suka iso bakin wani kogi; Baban ya ce, "Duba, ga ruwa anan; me zai hana ayi mani baftisma?" 37Filibus ya ce," Idan ka gaskanta da zuciya daya, ana iya yi maka baftisma." Sai Bahabashen ya ce, "Na gaskata Yesu Almasihu shine Dan Allah." 38Sai Bahabashen ya umarta a tsai da karussar. Sai suka zo wurin ruwa dukan su biyu, Filibus da baban, Filibus kuwa yayi masa baftisma.
39Yayin da suka fito daga cikin ruwan, Ruhun Ubangiji ya dauke Filibus; baban bai sake ganin shi ba, sai ya ci gaba da tafiyar sa yana murna. 40Amma Filibus ya bayyana a Azotus. Ya ratsa wannan yankin yana wa'azin bishara a dukan garuruwan, har sa'anda ya iso Kaisariya.

9

1Amma Shawulu, ya cigaba da maganganun tsoratarwa har ma da na kisa ga almajiran Ubangiji, ya tafi wurin babban firist 2kuma ya roke shi wasiku zuwaga majami'un da ke Dimashku, domin idan ya sami wani da ke na wannan hanya, maza ko mata, ya kawo su Urushalima a daure.

3Yayin da yana tafiya, ya kasance da ya iso kusa da Dimashku, nan da nan sai ga wani haske daga sama ya haskaka kewaye da shi; 4Sai ya fadi a kasa kuma yaji wata murya na ce da shi, "Shawulu, Shawulu, me yasa kake tsananta mani?"
5Shawulu ya amsa, "Wanene kai, Ubangiji?" Ubangiji ya ce, "Nine Yesu wanda kake tsanantawa; 6amma ka tashi, ka shiga cikin birnin, kuma za a gaya maka abinda lallai ne kayi. 7Mutanen da ke tafiya tare da Shawulu suka tsaya shiru sun rasa abin fada, suna sauraron muryar, amma ba su ga kowa ba.
8Shawulu ya tashi daga kasa, kuma daga ya bude idanunsa, baya ganin komai; sai suka kama hannuwansa suka yi masa jagora suka kawo shi cikin birnin Dimashku. 9Har kwana uku ba ya kallo, kuma ba ya ci balle sha.
10Akwai wani almajiri a Dimashku mai suna Hananiya; sai Ubangiji ya yi magana da shi cikin wahayi, ya ce, "Hananiya." Sai ya ce, "Duba, gani nan Ubangiji." 11Ubangiji ya ce masa, "Tashi, ka tafi titin da ake kira Mikakke, kuma a gidan wani mai suna Yahuza ka tambaya mutum daga Tarsus mai suna Shawulu; gama yana addu'a; 12kuma ya gani cikin wahayi mutum mai suna Hananiya na shigowa kuma ya daura masa hannu, domin idanunsa su bude."
13Amma Hananiya ya amsa, "Ubangiji, na ji labari daga wurin mutane da yawa game da mutumin nan, da irin muguntar da ya aikata ga tsarkakan mutanenka da ke Urushalima. 14An bashi izini daga babban firist domin ya kama dukan wanda ke kira bisa sunanka." 15Amma Ubangiji ya ce masa, "Jeka, gama shi zababben kayan aiki na ne, wanda zai yada sunana ga al'ummai da sarakuna da 'ya'yan Isra'ila; 16Domin zan nuna masa irin wahalar da zai sha sabo da sunana."
17Sai Hananiya ya tafi, ya shiga gidan. Ya dora masa hannu a kai, ya ce, "Dan'uwa Shawulu, Ubangiji Yesu, wanda ya bayyana a gareka a hanya sa'adda kake zuwa, ya aiko ni domin ka sami ganin gari ka kuma cika da Ruhu Mai Tsarki." 18Nan take wani abu kamar bawo ya fado daga idanun Shawulu, kuma ya sami ganin gari; ya tashi aka yi masa baftisma; 19kuma ya ci abinci sai aka karfafa shi. Ya zauna tare da almajirai a Dimashku kwanaki da yawa.
20Nan take ya fara shellar Yesu cikin haikali, yana cewa shine dan Allah. 21Dukan wadanda suka saurare shi suka yi mamaki suka ce "Ba wannan mutumin ne yake hallaka mutanen Urushalima da ke kira bisa ga wannan suna ba? Ya kuma zo nan domin ya ba da su a daure ga manyan firistoci." 22Amma Shawulu kuwa ya sami iko sosai, kuma yana haddasa damuwa tare da rinjaya tsakanin Yahudawan dake zama a Dimashku ta wurin tabbatar da Yesu shine Almasihu.
23Bayan kwanaki da yawa, sai Yahudawan suka yi shiri domin su kashe shi. 24Amma shirin su ya zama sananne ga Shawulu. Suna fakkon sa ta wurin tsaron kofar birnin dare da rana domin su kashe shi. 25Amma da tsakar dare almajiransa suka daukeshi a kwando, suka zurara shi ta katanga.
26Sa'adda ya zo Urushalima, Shawulu ya yi niyyar hada kai da almajirai, amma dukansu suna tsoronsa, domin ba su yarda cewa shima ya zama almajiri ba. 27Amma Barnaba ya dauke shi ya kawo shi wurin manzannin. Ya kuwa gaya musu yadda Shawulu ya sadu da Ubangiji a hanya, har Ubangiji ya yi magana da shi, kuma yadda Shawulu ya yi wa'azi cikin sunan Yesu gabagadi a Dimashku.
28Ya sadu da su lokacin shigar su da fitar su a Urushalima. Ya yi wa'azi gabagadi cikin sunan Ubangiji Yesu 29kuma yana muhawara da Yahudawan Helenanci; amma sun ci gaba da kokarin kashe shi. 30Da 'yan'uwa suka gane haka, sai suka kawo shi Kaisariya, suka kuwa tura shi zuwa Tarsus.
31Sa'annan iklisiya dake dukan kasar Yahudiya, Galili da kuma Samariya suka sami salama da kuma ginuwa; suka kuwa ci gaba da tafiya cikin tsoron Ubangiji, da kuma ta'aziyar Ruhu Mai Tsarki, iklisiyar kuwa ta karu da yawan mutane. 32Har ta kai, yayin da Bitrus ya zaga dukan yankin kasar, ya dawo wurin masu bi dake zama a garin Lidda.
33A can kuwa ya sami wani mutum mai suna Iniyasu, wanda yake shanyayye ne, yana kwance har tsawon shekara takwas a kan gado. 34Bitrus ya ce masa, "Iniyasu, Yesu Almasihu ya warkar da kai. Tashi ka nade shimfidarka." Nan take sai ya mike. 35Sai duk mazauna kasar Lidda da kasar Sarona suka ga mutumin, suka kuma juyo ga Ubangiji.
36Yanzu kuwa a Yafa akwai wata almajira, mai suna Tabita, ma'ana "Dokas." Wannan matar kuwa tana chike da ayyukan nagarta da halin tausayi da take yi ga mabukata. 37Ya kai ga cewa a kwanakin can ta yi rashin lafiya har ta mutu; da suka wanke gawar ta suka kwantar da ita a bene.
38Da shike Lidda na kusa da Yafa, almajiran kuma sun ji cewa Bitrus yana can, suka aika mutane biyu wurinsa. Suna rokansa, "Ka zo garemu ba tare da jinkiri ba." 39Bitrus ya tashi ya tafi da su, da isowar sa, suka kai shi benen. Sai dukan gwamrayen suka tsaya kusa da shi suna kuka, sai suka dauko riguna da sutura da Dokas ta dinka lokacin da take tare da su.
40Bitrus ya fitar da su duka daga cikin dakin, ya durkusa, ya yi addu'a; sai, ya juya wurin gawar, ya ce, "Tabita, tashi." Ta bude idanunta, da ta ga Bitrus ta zauna, 41Bitrus kuwa ya mika hannunsa ya tashe ta; sa'annan ya kira masu bi da gwamrayen, ya mika ta a raye garesu. 42Wannan al'amari ya zama sananne cikin dukan Yafa, kuma mutane da yawa suka bada gaskiya ga Ubangiji. 43Ya kasance, cewa, Bitrus ya zauna kwanaki da dama a Yafa tare da wani mutum mai suna Saminu, majemi.

10

1An yi wani Mutum a birnin Kaisariya, mai suna Karniliyas, shugaban sojoji ne na kungiyar da ake kira Italiya. 2Mutum ne mai ibada, wanda ya mika kansa da iyalinsa ga bautar Allah; ya kan bada taimakon kudi mai yawa ga Yahudawa, kuma yana addu'a ko yaushe ga Allah.

3Wajen sa'a ta tara ga yini, an bayyana masa cikin wahayi mala'kan Ubangiji na zuwa gare shi sai mala'ikan ya ce masa, "Karniliyas!" 4Karniliyas ya zuba wa mala'ikan ido a tsorace ya ce "Menene, mai gida?" mala'ikan ya ce masa, "Addu'ar ka da taimakon ka ga talakawa ya kai sama matsayin sadaka abin tunawa a gaban Allah, 5"Yanzu ka aika mutane zuwa birnin Yafa su kawo mutum mai suna Saminu wanda ake kira Bitrus. 6Yana zama tare da Saminu majemi, wanda gidansa ke bakin teku.
7Da mala'ikan da ya yi magana da shi ya tafi, Karniliyas ya kira biyu daga barorin gidansa, da kuma soja guda mai bautar Allah daga cikin sojojin da suke masa hidima. 8Karniliyas ya fada masu dukan abin ya faru sai ya aike su Yafa.
9Washe gari wajen sa'a ta shida (tsakar rana) suna cikin tafiya da suka yi kusa da birni, Bitrus ya hau kan bene don ya yi addu'a. 10Sai ya ji yunwa kuma yana bukatar wani abinda da zai ci, amma a yayin da mutanen na dafa abinci, sai ya ga wahayi. 11Sai ya ga sararin sama ya bude kuma wani tasa na saukowa, wani abu kamar babban mayafi yana saukowa zuwa duniya, ana zuro shi ta kusuryoyinsa hudu. 12A cikinsu kuwa akwai dukan halitun dabbobi masu kafa hudu da kuma masu rarrafe a duniya da tsunstayen sama.
13Sai murya ta yi magana da shi; "Tashi, Bitrus, yanka ka ci " 14Amma Bitrus ya ce "Ba haka ba, Ubangiji, gama ban taba cin abu mara tsarki ko mai kazanta ba." 15Amma muryar ta sake zuwa masa karo na biyu kuma; "Abinda Allah ya tsarkake, kada ka kira shi kazantacce." 16Wannan ya faru sau uku; nan da nan sai aka dauki tasar zuwa sama.
17A yayin da Bitrus na cikin rudani game da ma'anar wahayin da ya gani, sai ga mutanen da Karniliyas ya aika suna tsaye a bakin kofar gidan, bayan sun tambayi hanyar zuwa gidan, 18Kuma suka yi sallama suna tambaya ko Saminu wanda ake kira Bitrus ya sauka a nan.
19A yayin da Bitrus yana kan tunani akan wahayin, Ruhu ya ce masa, "Duba, mutane uku na neman ka." 20Tashi ka sauka ka tafi tare da su. Kada ka yi jinkirin tafiya tare da su, domin Nine na aike su." 21Bitrus kuwa ya sauko wurin mutanen ya ce, "Ni ne wanda kuke nema. Me ya sa kuka zo?"
22Suka ce, "Shugaban soja mai suna Karniliyas, adalin mutum kuma mai bautar Allah, yana da kyakkyawar shaida a dukan al'umman Yahudawa, shi ne wanda mala'ika mai tsarki na Allah ya aika domin ka zo gidansa, ya ji sako daga wurinka." 23Sai Bitrus ya gayyace su su zo ciki kuma su zauna tare da shi. Washegari sai ya tafi tare da su, kuma wadansu 'yan'uwa daga Yafa suka raka shi.
24Kashegari suka shiga Kaisariya, Karniliyas kuwa yana jiran su; har ma ya gayyaci 'yan'uwansa da kuma abokansa na kusa.
25Ya kasance sa'adda Bitrus ya shiga, Karniliyas ya sadu da shi kuma ya durkusa ya yi masa sujada. 26Amma Bitrus ya tashe shi yana cewa, "Tashi tsaye! Ni ma mutum ne."
27A lokacin da Bitrus yake magana da shi, ya shiga ciki sai ya tarar da mutane da yawa sun taru a wuri daya. 28Ya ce masu, "Ku da kanku kun sani bai dace Bayahuden mutum ya yi ma'amulla ko ya ziyarci wani ko wata kabila ba. Amma Allah ya ce da ni kada in ce da kowa mara tsarki ko kazantacce. 29Wannan shine yasa na zo ba tare da musu ba, a lokacin da kuka kira ni. Don haka na tambaye ku me ya sa kuka aika in zo."
30Karniliyas ya ce "Kwanaki hudu da sun wuce a daidai wannan lokaci, ina addu'a da cikin sa'a na tara (karfe uku) a gidana, sai na ga mutum tsaye a gabana da tufafi mai haske. 31Ya ce, "Karniliyas, Allah ya ji addu'ar ka, kuma taimakon ka ga talakawa ya tuna ma Allah da kai. 32Saboda haka ka aika da wani Yafa, ya kira maka mutum mai suna Saminu wanda ake kira Bitrus. Yana zama a gidan Saminu majemi, da ke bakin teku. 133Don haka nan da nan na aika a kira ku. Kuna da kirki da kuka zo. Yanzu haka, duk muna nan a gaban Allah, don jin duk abin da Ubangiji ya umarce ku da ku faɗi.” 2
34Sai Bitrus ya bude bakinsa ya ce, "Gaskiya, na fahimci Allah baya nuna bambanci. 35Maimakon haka, cikin kowace al'umma duk mai ibada kuma mai aikata adalci karbabbe ne a gare shi.
36Ku kun san sakon da ya aika wa mutanen Isra'ila, a lokacin da ya sanar da labarin mai kyau na salama ta wurin Yesu Kristi, wanda shine Ubangiji na duka. 37Ku da kanku kun san al'amuran da suka kasance, wanda ya faru cikin Yahudiya, farawa daga Galili, bayan sanarwar baftismar da Yahaya ya yi. 38Al'amura game da Yesu Banazare, yadda Allah ya kebe shi da Ruhu Mai Tsarki da iko kuma. Ya kuma ci gaba da aikin alheri da warkarwa ga dukan wadanda shaidan ya daure, domin Allah yana tare da shi.
39Mu shaidu ne ga dukan abubuwan da ya yi a kasar Yahudawa da cikn Urushalima, wannan Yesu wanda suka kashe, ta wurin giciye shi a akan itace. 40Wannan mutumin, Allah ya ta da shi rana ta uku ya kuma maishe shi sananne, 41ba ga dukan mutane ba, amma ga shaidun da Allah ya zaba tun da farko - mu kanmu, wadanda muka ci muka sha tare da shi bayan tashin sa daga matattu,
42Ya umarce mu mu yi wa mutane wa'azi mu kuma tabbatar cewa shine wanda Allah ya zaba ya yi shariya bisa masu rai da matattu. 43Gareshi ne dukan annabawa suka yi shaida, domin dukan wanda ya bada gaskiya gareshi ya sami gafarar zunubai ta wurin sunansa.`
44Sa'adda Bitrus yana kan magana game da wadannan abubuwa, Ruhu Mai Tsarki ya sauko a kan dukan wadanda suke sauraron wa'azin sa. 45Mutanen da ke kungiyar masu bi da suka yarda da kaciya, dukan wadanda suka zo tare da Bitrus suka yi mamaki, domin baiwar Ruhu Mai Tsarki ya sauko a kan al'ummai.
46Domin sun ji al'umman nan suna magana da wasu harsuna suna yabon Allah. Sai Bitrus ya amsa, 47"Ko akwai wanda zai hana wa wadannan baftisma ta ruwa, da shike suma sun karbi Ruhu Mai Tsarki kamar mu?" 48Sai ya ba da umarni a yi masu baftisma cikin sunan Yesu Kristi. Sai suka roke shi ya kasance da su na wasu kwanaki.


1Wasu tsoffin kwafi sun ƙara: Idan ya zo, zai yi magana da kai .
2Maimakon Ubangiji ya umarce ya faɗi, wasu tsoffin kwafi sun yi, Allah ya umarce ya faɗi .

11

1Yanzu Manzani da 'yan'uwa wadanda suke cikin Yahudiya suka ji cewa al'ummai ma sun karbi maganar Allah 2Lokacin da Bitrus ya je Urushalima, wadanda suke na kaciya suka zarge shi; 3suka ce, "Ka hada kai tare da mutane marasa kaciya kana ci tare da su!"

4Amma Bitrus ya fara bayyana masu dalla-dalla; ya ce, 5Ina addu'a a cikin birnin Yafa, sai na ga wahayi game da taska yana saukowa, kamar babban mayafi da aka saukar daga sama ta kusurwan nan hudu. Ya sauko gabana. 6Na zura masa ido kuma na yi tunani a kansa, na ga dabbobi masu kafa hudu na duniya, miyagun dabbobi, da masu rarrafe, da tsuntsayen sama.
7Sai na ji murya tana ce da ni, "Tashi, Bitrus, yanka ka ci." 8Na ce, "Ba haka ba, Ubangiji: gama babu abu mara tsarki ko mai kazanta da ya taba shiga bakina." 9Amma murya ta amsa kuma daga sama cewa, "Abin da Allah ya kira mai tsarki, kada ka kira shi mara tsarki." 10Wannan ya faru sau uku, sai dukan komai ya koma sama.
11Nan da nan sai ga mutane uku tsaye a gaban gidan da muke; an aike su daga Kaisariya zuwa gare ni. 12Ruhun ya umurce ni in tafi tare da su, ba tare da nuna banbanci game da su ba. Yan'uwan nan shida sun tafi tare da ni, sai muka shiga gidan mutumin. 13Ya fada mana yadda ya ga mala'ika tsaye a cikin gidansa yana cewa "Aiki mutane zuwa Yafa, su kirawo Saminu wanda ake kira Bitrus. 14Zai gaya maku sakon da za ku sami ceto kai da dukan gidanka."
15Da na fara magana da su, Ruhu Mai Tsarki ya sauko akansu kamar yadda ya sauko mana tun da farko. 16Sai na tuna da maganar Ubangiji, yadda ya ce,"Hakika Yahaya ya yi baptisma da ruwa, amma ku za a yi maku baptisma da Ruhu Mai Tsarki."
17To, idan Allah ya yi masu baiwa kamar yadda ya yi mana yayin da muka bada gaskiya ga Ubangiji Yesu Almasihu, wane ni da zan yi jayayya da Allah? 18Da suka ji wadannan abubuwa, suka rasa ta cewa, amma suka daukaka Allah suka ce "Ga al'ummai ma Allah ya basu tuba zuwa rai."
19Sai wadanda suka warwatsu saboda tsananin da ya bi bayan mutuwan Istifanas, suka yadu har zuwa Finikiya, Kuburus da Antakiya, amma suka yi wa'azin Yesu ga Yahudawa kadai. 20Amma wadan sunsu, mutane daga Kuburus da Kurane, suka zo Antakiya suka yi magana da hellenawa, suna yi masu wa'azin Ubangiji Yesu. 21Kuma ikon Ubangiji yana tare da su, har mutane da yawa suka gaskata kuma suka juyo wurin Ubangiji.
22Labari game da su ya iso kunnen ikilisiya da ke Urushalima: sai suka aika da Barnaba zuwa can Antakiya. 23Da ya iso kuma ya ga kyautar Allah, sai ya yi farinciki; ya karfafa su dukka su kafu cikin Ubangiji da dukan zuciyar su. 24Domin shi mutumin kirki ne, cike kuma da Ruhu Mai Tsarki da bangaskiya, sai mutane da yawa suka karu ga Ubangiji.
25Sai Barnaba ya tafi Tarsus domin ya nemi Shawulu. 26Da ya same shi, ya kawo shi Antakiya. Ya kasance, shekara guda suna taruwa tare da ikilisiya suka koyar da mutane da yawa. A Antakiya ne aka fara kiran almajiran Krista.
27A cikin kwanakin nan wadansu annabawa daga Urushalima suka zo Antakiya. 28Daya daga cikinsu, mai suna Agabas ya mike tsaye yayi magana da ikon Ruhu cewa za a yi tsanani fari ko'ina a duniya. Wannan ya faru ne a zamanin Kalaudiya.
29Sai, almajiran, suka dau niyya kowa gwargwadon karfinsa, su aika wa 'yan'uwa da ke Yahudiya da taimako. 30Suka yi haka; sun aika wa dattawa da kudi ta hanun Barnaba da Shawulu.

12

1A lokacin nan Sarki Hiridus ya sa wa wasu masu bi hannu domin ya musguna masu. 2Ya kashe Yakubu dan'uwan Yahaya da takobi.

3Bayan da ya ga hakan ya gamshi Yahudawa, sai ya kama Bitrus ma. 4Bayan ya kama shi, sai ya tsare shi a kurkuku ya kuwa sa sojoji hudu su dinga tsaron sa; yana niyyar kawo shi gaban mutanen a bayan Idin katarewa.
5To, Bitrus na tsare a kurkuku, amma 'yan'uwa na iklisiya suna yin addu'a ga Allah sosai domin sa. 6Ana kamar gobe Hiridus zai fitar da shi, a wannan daren, Bitrus yana barci a tsakanin sojoji biyu, daure da sarkoki biyu; sojoji kuma na gadi a bakin kurkukun.
7Ba zato, sai ga mala'ikan Ubangiji ya bayyana a gareshi, haske ya haskaka dakin. Ya taba Bitrus a gefe ya tashe shi kuma ya ce, "Tashi da sauri." Sai ga sarkokin suka zube daga hannunsa. 8Mala'ikan ya ce masa, "Yi damara ka sa takalmanka." Bitrus kuwa yayi haka. Mala'ikan ce ma sa, "Yafa mayafinka, ka biyo ni."
9Bitrus kuwa ya bi mala'ikan suka fita waje. Bai gane abin da mala'ikan ke yi zahiri ne ba. Yana zaton ko yana ganin wahayi ne. 10Bayan da suka wuce masu tsaron fari da na biyu, sun kai kofar da aka yi da karfe wadda ta mike zuwa cikin gari; ta bude masu da kanta. Suka fita sun bi titin, kuma nan take kuma sai mala'ikan ya bar shi.
11Da Bitrus ya komo hayyacin sa, ya ce, "Hakika yanzu na gane Ubangiji ya aiko da mala'ikansa don ya kubutar da ni daga hannun Hiridus da abin da Yahudawa suke zato." 12Da ya gane haka, ya zo gidan Maryamu mahaifiyar Yahaya wanda sunan mahaifinsa Markus; masu bi da yawa sun taru a can suna addu'a.
13Da ya kwankwasa kofar gidan, sai baiwar gidan mai suna Roda ta zo don ta bude kofar. 14Da ta gane muryar Bitrus, don farin ciki ta kasa bude kofar; maimakon haka, ta koma daki a guje, don ta basu labari Bitrus na tsaye a bakin kofa. 15Suka ce mata, "Kin haukace." Amma ta nace da cewa haka ne. Suka ce, "Mala'ikansa ne."
16Amma Bitrus ya ci gaba da kwankwasawa, da suka bude kofar, sai suka ga ai shine, suka sha mamaki kwarai. 17Bitrus kuwa ya yi masu hannu yana, masu alama su yi shuru. Sai ya gaya masu labarin yadda Ubangiji ya kubutar da shi daga kurkukun. Ya ce, "Ku gaya wa Yakubu da dukan 'yan'uwa abin da ya faru." Sai ya bar su, ya tafi wani wuri.
18Sa'anda gari ya waye ba karamar hargowa ce ta tashi a cikin sojojin ba, game da abin da ya faru da Bitrus. 19Bayan da Hiridus ya neme shi kuma bai same shi ba, sai ya tambayi masu tsaron kuma ya bada umarni a kashe su. Sai ya gangara daga Yahudiya zuwa Kaisariya ya yi zamansa a can.
20Yanzu kuwa Hiridus ya yi fushi sosai da mutanen Taya da Sidon. Suka tafi wurinsa tare. Suka roki Bilastasa, mataimakin sarkin, ya taimake su. Sai suka nemi sasantawa don suna samun abinci daga kasarsa ne. 21A ranan da aka kayyade, Hirudus ya sha damara da kayan saurata kuma ya zauna akan kursiyi; ya yi masu jawabi.
22Mutanen suka yi ihu, "Wannan muryar allahce, ba ta mutum ba!" 23Nan take mala'ika Ubangiji ya buge shi don bai ba Allah daukaka ba, nan take tsutsotsi suka cinye shi har ya mutu.
24Maganar Allah ta yadu tana ta ribabbanya. 25Bayan Barnaba da Shawulu sun gama aikin su a Urushalima. Suna dawowa, suka zo tare da Yahaya wanda sunan mahaifinsa Markus ne.

13

1A cikin iklisiyar da take Antakiya, akwai annabawa da malamai. Sune su Barnabas, Saminu (wadda ake kira Baki) da Lukiya Bakurame da Manayin (wanda aka yi renon su tare da sarki Hiridus mai mulki) da Shawulu. 2Sa'adda suke bauta wa Allah tare da azumi, sai Ruhu Mai Tsarki ya ce, "Ku kebe mani Barnaba da Shawulu domin aikin da na kiraye su". 3Bayan taron sun yi addu'a da azumi, sai suka sa masu hannu, su suka sallame su.

4Sai Shawulu da Barnabas suka yi biyayya da Ruhu Mai Tsarki suka tafi Sulukiya; daga nan suka ketare zuwa tsibirin Kuburus. 5Sa'adda suke garin Salami, suka koyar da maganar Ubangiji a majami'un Yahudawa, suna kuma tare da Yahaya Markus mai taimakonsu.
6Bayan sun zaga tsibirin duka har Bafusa, nan suka iske wani Bayahude mai suna Bar-yeshua mai tsafi kuma annabin karya. 7Wannan mai tsafin wanda ke tare da Makaddas, shi Sarjus Bulus mutum mai basira ne. Wannan kuwa ya kira Shawulu da Barnaba domin yana so ya ji maganar Allah. 8Amma Elimas "mai tsafi" (fasarar sunansa kenan) ya yi adawa da su; yana so ya baudar da Makaddashin daga bangaskiya.
9Amma Shawulu wanda ake ce da shi Bulus yana cike da Ruhu Mai Tsarki ya kafa masa ido. 10Sai ya ce, "Kai dan iblis, kana cike da kowace irin yaudara da mugunta. Kai abokin gabar kowanne irin adalci ne. Ba za ka daina karkata mikakkakun hanyoyin Ubangiji ba?
11Yanzu ga hannun Ubangiji bisa kanka, zaka zama makaho. Ba za ka ga rana ba nan da dan lokaci." Nan take kuwa sai wani hazo da duhu suka rufe shi ya fara yawo yana neman mutane su yi masa jagora. 12Bayan da Makaddashin ya ga abin da ya faru ya ba da gaskiya saboda ya yi mamakin koyarwa game da Ubangiji.
13Bulus da abokansa suka shirya suka ketare a jirgin ruwa daga Bafusa zuwa Firjiya a Bamfiliya. Amma Yahaya ya bar su ya koma Urushalima. 14Bulus da abokansa suka tafi daga Firjiya zuwa Antakiya na kasar Bisidiya. Nan suka shiga majami'a ran Asabaci suka zauna. 15Bayan karatun dokoki da annabawa, shugabanin iklisiyar suka tura sako cewa, "'Yan'uwa, idan kuna da wani sakon karfafawa ga jama'a ku fadi."
16Bulus kuwa ya tashi ya yi alama da hannunsa ya ce, "Mutanen Isra'ila da ku wadanda kuke girmama Allah, ku ji. 17Allahn Isar'ila ya zabi kakkaninmu ya kuma ribabbanya su sa'adda suke kasar Masar da kuma madaukakin iko ya fito da su daga cikinta. 18Ya yi hakuri da su a jeji har na tsawon shekara arba'in.
19Bayan ya hallaka kasashe bakwai a kasar Kan'ana, ya ba kakkaninmu kasar nan gado. 20Duk wadanan abubuwan sun faru shekaru dari hudu da hamsin da suka wuce. Bayan wadannan, Allah ya ba su alkalai har sai da annabi Sama'ila ya zo.
21Sai jama'a suka roka a ba su sarki, Allah kuwa ya ba su Saul dan Kish, mutumin kabilar Binyamin ya zama sarki har na tsawon shekara arba'in. 22Allah kuwa ya cire shi daga kan kujerar sarauta, ya daga Dauda ya zama sarkinsu. A kan Dauda ne Allah ya ce, 'Na sami Dauda dan Yessi, mutumin da zuciyata ke so; zai yi duk abin da nake so'.
23Daga zuriyar mutumin nan Allah ya fito da mai ceto, Yesu, kamar yadda aka alkawarta zai yi. 24Wannan ya faru kafin Yesu ya zo, Yahaya ya yi shelar baftimar tuba ga jamma'ar Isra'ila. 25Sa'adda Yahaya ya gama aikin sa, sai ya ce, 'Wanene ni a tsamanin ku? Ba nine shi ba. Amma ku saurara, akwai wani mai zuwa bayana wanda maballin takalminsa ban isa in kwance ba.'
26Yan'uwa 'ya'ya daga zuriyar Ibrahim, da wadanda ke bautar Allah a cikinku, saboda mune aka turo sakon ceto. 27Saboda wadanda ke zaune cikin Urushalima, da masu mulkinsu, ba su gane shi ba, kuma sun cika fadin annabawa da a ke karantawa kowace ranar Asabaci ta wurin kashe shi.
28Duk da cewa ba su sami dalilin mutuwa a kansa ba, suka roki Bilatus ya kashe shi. 29Bayan sun gama duk abin da aka rubuta game da shi, sai suka sauke shi daga giciye suka sa shi a cikin kabari.
30Amma Allah ya tashe shi daga matattu. 31Mutanen da suka zo tare da shi daga Galili da Urushalima kuwa suka yi ta ganinsa har kwanaki da yawa. Wadanan mutane kuma sune shaidunsa ga jama'a a yanzu.
32Mun kawo maku labari mai dadi game da alkawaran da aka yi wa kakkaninmu. 33Ubangiji ya bar mana alkawaran. Don haka ya ta da Yesu daga matattu. Kamar yadda ya ke a littafin zabura ta biyu: "Kai da na ne yau na zama mahaifinka." 34Kuma dalilin tayar da shi daga matattu shine saboda kada jikinsa ya rube, ya yi magana kamar haka: "Zan baku albarkun Dauda masu tsarki tabatattu."
35Wannan shine dalilin da ya yi magana kuma a wata Zabura, 'Ba za ka bar Mai Tsarkinka ya rube ba.' 36Bayan Dawuda ya yi wa Allah bauta a cikin zuciyarsa da kuma abin da Allah yake so, ya mutu, aka binne shi tare da kakkaninsa, ya kuma ruba, 37amma wanda Allah ya tayar bai ga ruba ba.
38'Yan'uwa, ku sani cewa ta wurin mutumin nan aka yi maku wa'azin gafarar zunubai. 39Ta wurinsa ne duk wanda ya ba da gaskiya zai kubuta daga dukan abin da dokar Musa bata 'yantar da ku a kai ba.
40Saboda haka ku yi hankali da abubuwan da annabawa suka fada kada su faru a kanku: 41'Ku masu reni, za ku rude don mamaki, ku kuma shude; saboda ina aiki a cikin kwananakinku, aikin da ba za ku yarda ba ko da wani ya gaya maku."
42Da Bulus da Barnaba suna fita kenan, sai jama'a suka rokesu, su sake yin irin wannan magana ranar Assabaci mai zuwa. 43Bayan da sujadar ta kare, Yahudawa da yawa da kuma wadanda suka shiga addinin Yahudanci suka bi Bulus da Barnaba, sai suka gargade su da su cigaba da aikin alherin Allah.
44Da Asabaci ta kewayo, kusan dukan garin suka taru domin su ji maganar Ubangiji. 45Sa'adda Yahudawa suka ga taron jama'a, sai suka cika da kishi suna karyata abubuwan da Bulus ya fada suka kuma aibata shi.
46Amma Bulus da Barnaba sun yi magana gabagadi suka ce, "Dole ne a fara fada maku maganar Allah. Amma da yake kun ture ta, kun nuna baku cancanci rai madawwami ba soboda haka zamu juya ga al'ummai. 47Don haka Ubangiji ya umarce mu, cewa, 'Na sa ku haske ga al'ummai, saboda ku kawo ceto ga iyakar duniya.'"
48Da al'ummai suka ji haka, sai suka yi murna suka kuma yabi kalmar Ubangiji. Dukan wadanda aka kaddarawa samin rai madawwami suka tuba. 49Kalmar Ubangiji kuwa ta bazu a kowanne bangaren yankin.
50Amma Yahudawan suka zuga wadansu mata masu sujada, masu daraja da kuma shugabannin mazan garin. Wannan ya tayar da tsanani ga Bulus da Barnaba har suka fitar da su daga iyakar garinsu. 51Amma Bulus da Barnaba suka kade masu kurar kafarsu. Suka tafi garin Ikoniya. 52Amma almajiran suka cika da farin ciki da kuma Ruhu Mai Tsarki.

14

1A lokacin da Bulus da Barnaba sun shiga garin Ikoniya suka shiga majami'an Yahudawa suka yi wa'azi yadda har mutane da yawa daga cikin Yahudawa da Hellinawa suka ba da gaskiya. 2Amma Yahudawa da basu yi biyayya ba, suka zuga al'umman har suka yi fushi da 'yan'uwan.

3Suka zauna a wurin na tsawon lokaci, suna yni maganarsu gabagadi da ikon Ubangiji, yana kuma shaidar sakon alherinsa. Ya yi wannan ta wurin alamu da al'ajibai ta hannun Bulus da Barnaba. 4Saboda haka mutanen garin sun rabu: wadansun su suka bi ra'ayin Yahudawa, wasu kuwa sun bi manzannin.
5Al'umman garin da Yahudawa sun nemi jan hankali shugabanninsu, don su wulakanta Bulus da Barnaba, su jajjefe su, 6da suka gane haka suka gudu zuwa biranen Likoniya, Listira da Darbe, da garuruwa wadanda ke kewaye da su, 7a can suka yi wa'azin bishara.
8A Listira akwai wani wanda ke zaune bai taba tashi da kafafunsa ba, don shi gurgu ne tun daga haihuwa. 9Wannan mutumin ya ji Bulus yana magana. Bulus ya kafa masa ido, ya gane mutumin na da bangaskiya da za a warkar da shi. Sai ya ce masa da murya mai karfi, "Tashi ka tsaya akan kafafunka" 10Sai mutumin ya yi tsalle ya fara tafiya da kafafunsa, yana yawo.
11Da jama'an garin sun ga abin da Bulus ya yi, suka tada muryarsu suna cewa da Likoniyanci, "Ai alloli sun ziyarce mu daga sama, da kamanin mutane." 12Suna kiran Barnaba da sunan "Zafsa," Bulus kuwa suka kira shi da sunan "Hamisa" domin shine yafi yin magana. 13Sai firist din zafsa wanda dakin yin masa sujada na kofar birni; ya kawo bijimai biyu da furannin da aka saka su kamar gammo; shi da jama'arsa suna so su yi masa hadaya.
14Amma da manzannin, wato Barnaba da Bulus, su ka ji labarin, suka yage rigunansu, suka hanzarta zuwa gun taron mutanen. 15Suna ta cewa, "Kuji! Ku mutane don me kuke wannan abin? Mu fa mutane ne kamarku. Mun kawo maku labari mai dadi ne, da cewa, ku rabu da abubuwa marar amfani, ku koma ga Allah mai rai, wanda ya hallici sama da kasa da teku da dukan abubuwa da ke cikinsu. 16A da dai ya bar mutane su yi abinda suka ga dama.
17Duk da haka, bai bar kansa ba tare da shaida ba, don yana bada abubuwa masu kyau, yana ba ku ruwan sama, lokatai masu albarka, ya cika ranku da abinci da farin ciki." 18Duk da wadannan kalmomin da kyar, Bulus da Barnaba suka iya tsayar da su daga yi masu hadaya.
19Amma wasu Yahudawa daga Antakiya da wasunsu daga Ikoniya suka rinjayi tarun jama'ar. Suka jajjefi Bulus suka ja shi zuwa wajen garin, suna ganin kamar ya mutu. 20Duk da haka da almajirai suka kewaye shi a tsaitsaye, sai ya tashi ya koma cikin garin. Washegari, ya tafi Darba tare Barnaba.
21Bayan sun yi wa'azin bishara a wannan birnin suka kuma sami almajirai da yawa, suka dawo Listira, da Ikoniya da Antikiya. 22Suna karfafa zuciyar almajiran su rike bangaskiyarsu, su ci gaba da ita, suna ce masu, "Ta wurin jimrewa mai yawa zamu shiga mulkin Allah, don haka dole ne mu sha wahala."
23Da suka zabar masu dattawa a kowace iklisiya, sai suka yi addu'oi da azumi, suka mika su ga Ubangiji, ga wanda suka gaskanta a gareshi. 24Sa'annan sun bi ta Bisidiya suka kai Bamfiliya. 25Da suka yi maganarsu a Biriya, sun wuce zuwa har Italiya. 26Ta jirgin ruwa zuwa Antakiya, a nan ne aka mika su ga alherin Allah don aikin da suka gama a yanzu.
27Da isowarsu Antakiya sun tara 'yan iklisiya a wuri daya, sun ba da labarin dukan abin da Allah ya yi ta wurinsu. Da yadda Ya bude kofa a wurin al'ummai ta bangaskiya. 28Sun zauna tare da almajiran na tsawon lokaci.

15

1Wadansu mutane suka zo daga Yahudiya suka koyar da 'yan'uwa, cewa, "Idan ba yi maku kaciya bisa ga al'addar Musa ba, ba za ku sami ceto ba." 2Da Bulus da Barnaba suka tunkare su da mahawara, sai 'yan'uwa suka yanke shawara Bulus da Barnaba da wasu su je Urushalima wurin manzanni da dattawa a kan wannan magana.

3Da shike iklisiya ce ta aike su, sai suka bi ta Finikiya da ta Samariya suka sanar da tuban al'ummai. Ya kawo murna mai yawa a wurin 'yan'uwa. 4Bayan sun zo Urushalima, sai iklisiya da manzanni da dattawa, suka marabce su, sai suka fada masu abin da Allah ya yi ta wurinsu.
5Amma wadansu mutane wadanda suka ba da gaskiya daga cikin Farisawa, suka tashi suka ce, "Dole ne a yi masu kaciya a kuma umarce su su kiyaye dokar Musa." 6Sai manzanin da dattawan suka taru don su duba wannan lamari.
7Bayan mahawara mai tsanani, sai Bitrus ya tashi ya ce masu, "'Yan'uwa, kun san lokacin baya da ya wuce, Allah ya yi zabi a cikinku, cewa ta bakina ne al'ummai za su ji bishara, su kuma ba da gaskiya. 8Allah, wanda ya san zuciya, ya yi masu shaida, ya kuma basu Ruhu Mai Tsarki kamar yadda ya yi mana; 9kuma bai bambanta mu da su ba, ya tsabtace zuciyarsu ta wurin bangaskiya.
10To, saboda haka don me kuke gwada Allah, kuna sa wa almajirai nauyi a wuya wanda ubanninmu duk da mu ba mu iya dauka ba? 11Amma mun gaskanta za mu samu ceto ta wurin alherin Ubangiji Yesu, kamar yadda suke."
12Dukan taron jama'ar suka yi shiru sa'adda suke sauraron sakon shaidar da mamakin abin da Allah ya yi ta wurin Bulus da Barnaba a cikin al'ummai.
13Bayan sun gama magana, Yakubu ya amsa, ya ce, "'Yan'uwa, ku ji ni. 14Saminu ya fada yadda Allah ya fara nuna jinkai ga al'ummai domin ya dauke jama'a daga cikinsu domin sunansa.
15Maganar annabawa ta yarda da wannan, kamar yadda yake a rubuce, 16'Bayan wadannan abubuwa zan dawo, zan gina gidan Dauda wanda ya fadi kasa; in sake gina bangonsa, in tsayar da shi, 17saboda sauran jama'a su nemi fuskar Ubangiji, har da al'ummai da ake kira da sunana. 18Wannan shine abin da Ubangiji ya fadi, shi wanda ya yi wadannan abubuwa da aka sani tun zamanin da.
19Saboda haka, a gani na kada mu matsa wa al'umman da suka juyo gun Allah; 20amma zamu rubuta masu da cewa, su guje wa gumaka da zina da faskanci da maye da cin mushe. 21Tun zamanin da akwai mutane a kowanne birni wadanda suke wa'azi da karatun Musa a majami'u kowanne Asabaci."
22Sai ya yi wa manzanin kyau su da dattawa da dukan iklisiyar su zabi Yahuza da Barnaba da Sila da dattawan iklisiya a tura su Antakiya tare da Bulus da Barnaba. 23Sai suka rubuta wasika, "Manzani da dattawa da 'yan'uwa zuwa ga al'ummai 'yan'uwa a Antakiya da Suriya da Kilikiya, gaisuwa mai yawa.
24Mun ji cewa wasu mutane daga cikinmu wadanda ba mu umarce su ba, sun fita daga cikinmu sun yi maku koyarwar da ta daga maku hankali. 25Ya yi kyau da dukanmu, muka amince mu zabi wadansu mutane mu tura su wurinku tare da Bulus da Barnaba, 26mutane wadanda suka sadaukar da ransu domin sunan Ubangiji Yesu Almasihu.
27Mun aika Yahuza da Sila su gaya maku wadannan abubuwa. 28Saboda haka ya yi kyau Ruhu Mai Tsarki da mu, kada mu sa maku nauyi fiye da wadannan abubuwan: 29ku bar yi wa gumaka hadaya, ku bar cin mushe da shan kayan maye da zina da faskanci, in kun kiyaye wadannan abubuwa za ku zauna lafiya. Ku huta lafiya."
30Da aka sallame su, sai suka je Antakiya. Bayan sun tara jama'a sai suka ba su wasikar. 31Bayan da suka karanta ta, sai suka yi murna sosai saboda karfafawa. 32Yahuza da Sila, da shike su annabawa ne, suka karfafa 'yan'uwa da kalmomi masu yawa.
33Bayan sun yi kwananki a wurin, sai aka sallame su zuwa wurin 'yan'uwa wadanda suka aiko su. 34Amma ya gamshe Sila ya zauna a wurin. 35Amma Bulus da Barnaba suka tsaya a Antakiya da sauran 'yan'uwa, suna koyar da maganar Ubangiji.
36Bayan kwanaki kadan Bulus ya ce ma Barnaba, "Mu koma yanzu mu ziyarci dukan 'yan'uwa da muka yi masu bisharar Ubangiji, mu ga yadda suke. 37Barnaba yana so su dauki Yahaya wanda kuma ake kira Markus. 38Amma Bulus ya yi tunanin bai kamata a tafi da Markus ba, tun da ya bar su a Bamfiliya bai ci gaba da su ba.
39Nan jayayya ta tashi tsakaninsu, har suka rabu da juna sai Barnaba ya tafi tare da Markus suka ketare zuwa Kuburus. 40Amma Bulus ya zabi Sila suka tafi, bayan 'yan'uwa sun yi masu addu'ar alherin Allah ya kiyaye su. 41Bulus ya tafi ya zazzaga Suriya da Kilikiya yana ta karfafa iklisiyoyin.

16

1Bulus ya kuma isa Darbe da Listira, in da akwai wani almajiri mai suna Timoti a wurin, dan wata Bayahudiya wadda ta ba da gaskiya; ubansa kuwa Baheline ne. 2Ana maganar kirki a kansa ta bakin 'yan'uwa da ke Listira da Ikoniyan. 3Bulus ya yi wa Timoti kaciya, domin yana so su yi tafiya tare, domin kuma saboda Yahudawan da ke wurin, sun san cewa ubansa Baheline ne.

4Suna shiga cikin biranen, suna yi wa iklisiyoyi gargadi da su yi biyayya da umurnan da Manzanni da dattawa suka rubuta a Urushalima. 5Bangaskiyar iklisiyoyi kuwa ta karu, ana kuma samun karuwa na wadanda suke ba da gaskiya kowace rana.
6Bulus da abokan aikin sa sun shiga cikin lardin Firigiya da Galatiya, tun da Ruhu Mai Tsarki ya hana su wa'azin kalmar a cikin yankin Asiya. 7Sun zo kusa da Misiya, da nufin shiga cikin Bitiniya, Ruhun Yesu ya hana su. 8Da suka ratse ta cikin Misiya, sai suka shiga birnin Taruwasa.
9Bulus ya ga wahayi cikin dare, wani mutumin Makidoniya na kiransa, yana cewa. "Ka zo Makidoniya ka taimake mu". 10Bulus, da ganin haka, ya kama hanya zuwa Makidoniya, da tunanin Allah ne ya ke so su kai wa mutanen Makidoniya bishara.
11Da barin Taruwasa, Bulus da kungiyarsa sun shiga jirgin ruwa zuwa Samutaraki, da gari ya waye kuma sun tafi Niyafolis; 12Daga nan kuma suka tafi Filibi, birni na Makidoniya, mai muhimmanci ne a yankin Roma, in da mun yi zango kwanaki da dama. 13Ranar Asabaci mun je kofar gari, gefen rafi, da tunanin samun wurin addu'a. Mun zauna mun kuma yi magana da matan da sun taru a wurin.
14Wata mace mai suna Lidiya, 'yar kasuwa ce a birnin Tiyatira, mai bautar Allah ce, ta saurare mu. Ubangiji ya bude zuciyarta, ta mai da hankali ga maganar da Bulus ke fadi. 15Sa'anda da aka yi mata Baftisma tare da mutanen gidanta, ta ce da mu, "Idan kun dauke ni mai bautar Allah, ku zo gidana ku zauna." Sai ta rinjaye mu.
16A daidai wannan lokaci, muna tafiya wurin addu'a, wata yarinya mai ruhun duba ta hadu da mu. Iyayen gijinta na arziki da ita sosai. 17Tana bin Bulus, tare da mu, tana fadi da murya mai karfi cewa, "Wadannan mutanen, bayin Allah mafi daukaka ne, suna sanar maku hanyar ceto ne". 18Ta dauki kwanaki tana haka. Amma Bulus ya yi fushi da ita ainun, ya juya ya umarci ruhun, ya ce, "Na umarce ka, ka rabu da ita a cikin sunan Yesu Almasihu". Ruhun ya yi biyayya ya rabu da ita nan take.
19Da iyayengijinta suka ga cewa hanyar shigar kudinsu ta toshe, sai suka kama Bulus da Sila, suka ja su cikin kasuwa suka kai su gaban mahunkunta. 20Da suka kai su Kotu, suka ce, "Wadannan mutane Yahudawa ne, suna kawo tashin hankali a birninmu. 21Suna koyar da abubuwa da ba su karbuwa a gare mu, balle mu aikata, a matsayinmu na Romawa."
22Sai jama'a gaba daya sun tayar wa Bulus da Sila; alkalan kuma sun yage rigunansu, sun ba da umarni a duki Bulus da Sila da bulala. 23Bayan dukan, an jefa su Bulus a kurkuku, an ba mai tsaron kurkukun umurni ya kulle su da kyau, kada su gudu. 24Shi kuma ya yi hakanan, ya sa masu sarkoki a kafafun su, kamar yadda aka umurce shi.
25Da tsakar dare, Bulus da Sila suna yin adu'a, su na raira wakoki ga Allah, sauran 'yan sarkar su na jin su. 26Nan da nan sai ga wata girgizar kasa, wadda ta sa ginshikan kurkukun sun kadu, nan da nan kofofin kurkukun sun bude, 'yan sarka kuma, sarkokin su sun karkatse.
27Mai tsaron kurkukun ya tashi daga barci ya ga kofofin kurkukun a bude, ya zaro takobi, zai kashe kan sa, a tunanin sa, 'yan sarkar sun gudu. 28Amma Bulus ya ta da murya da karfi, ya ce, "kada kayi wa kanka barna, domin dukan mu muna nan".
29Mai tsaron kurkukun ya aika a kawo fitila, ya shiga ciki a gurguje da rawan jiki, ya fadi a gaban Bulus da Sila, 30ya fitar da su waje ya ce, "Shugabanni, me ya kamata in yi domin in tsira?" 31Sun ce masa, "ka ba da gaskiya ga Yesu Ubangiji, da kai da gidan ka, za ku sami tsira".
32Bulus da Sila suka fada masa maganar Ubangiji, tare da iyalinsa. 33Shi mai tsaron kurkukun ya dauke su cikin daren, ya wanke raunukansu, an kuma yi masa Baftisma nan da nan tare da iyalinsa. 34Ya kai Bulus da Sila gidansa, ya ba su abinci. Murna ta cika gidan mai tsaron kurkukun, domin iyalin sa duka sun ba da gaskiya ga Allah.
35Da gari ya waye, alkalai sun ba da sako a saki Bulus da Sila. 36Mai tsaron kurkukun kuwa ya sanar wa Bulus wannan magana ta alkalan, saboda haka ya ce wa Bulus, "Ku tafi cikin salama".
37Amma Bulus ya ce masu, "Sun yi mana duka a fili a gaban mutane mu da muke Romawa, ba a kashe mu ba, sun kuma sa mu a kurkuku; suna koran mu a asirce? Su zo da kansu su fitar da mu. 38Masu tsaron kurkuku sun mayar da maganar Bulus ga alkalan, wanda ya sa sun firgita, da jin cewa Bulus da Sila Romawa ne. 39Alkalai da kansu sun zo sun roki Bulus da Sila; da suka fitar da su daga kurkukun, sun ce wa Bulus da Sila su bar birnin.
40Da hakanan ne Bulus da Sila suka fita daga kurkuku, sun je gidan Lidiya. Da Bulus da Sila sun ga 'yan'uwa, sun karfafa su, sa'annan suka bar birnin.

17

1Bayan sun wuce biranen Amfibolis da Aboloniya, sun iso birnin Tasalunika, in da akwai wata majami'ar Yahudawa a wurin. 2Bulus, kamar yadda ya saba, ya nufi wurinsu, yana tattaunawa da su har Asabaci uku, daga cikin littattafai.

3Bulus ya bude littattafai yana bayyana masu cewa, dole ne Almasihu ya sha wahala, ya kuma tashi daga matattu. Ya ce, "Wannan Yesu kuwa da nake sanar maku, shine Almasihu". 4Wasu Yahudawa sun yarda, sun bi Bulus da Sila, da wadansu Helenawa, da Shugabannin Mata da jama'a da yawa.
5Yahudawan da basu ba da gaskiya ba suka cika da kishi, suka dauki wadansu 'yan ta'adda daga cikin kasuwa, suka tada tarzoma cikin birnin, mutane da yawa na bin su. Sun kai hari a gidan Yason, da niyyar fitar da Bulus da Sila a gaban jama'a. 6Amma da ba su ga Bulus da Sila ba, suka ja Yason da wasu 'yan'uwa masu bi zuwa gaban mahukuntar birnin, suna cewa, "Wadannan ne fa masu ta da zaune tsaye, gashi sun zo mana. 7Wadannan mutane da Yason ya marabta, sun saba wa dokokin Kaisar; Suna cewa akwai wani sarki mai suna - Yesu."
8Da taron jama'a, da mahukuntan birnin suka ji haka, sun damu. 9Bayan da sun amshi kudi daga wurin Yason da sauran 'yan'uwan, sai suka sake su.
10A wannan daren, 'yan'uwa masu bi suka fitar da Bulus da Sila, suka aike su garin Biriya. Da isar su can, su ka nufa majami'ar Yahudawa. 11Mutanen Biriya daban suke da na Tasalunika, sun yarda da sakon Bulus da zuciya daya, suna kuma binciken littattafai kowace rana domin su tabbatar da sakon Bulus, ko gaskiya ne. 12Saboda haka mutane da yawa cikin su sun ba da gaskiya, tare da wadansu sannanun mata Helenawa da maza da yawa.
13Amma da Yahudawan Tasalunika suka ji cewa Bulus yana wa'azin kalmar Allah a Biriya, sun haura can, sun tada hankulan jama'a. 14Nan da nan, masu bi na Biriya sun dauki Bulus sun aika shi zuwa teku, an bar Sila da Timoti a Biriya tukuna. 15Wadanda sun fitar da Bulus, sun kai shi har zuwa birnin Atina. Bulus ya ba su sako, su fada wa Sila da Timoti suyi hanzari su same shi.
16Sa'anda Bulus yana jiran zuwan Sila da Timoti a Atina, ya yi fushi a ransa, da ya ga birnin cike da gumakai. 17Ya tattauna da Yahudawa a cikin majami'a tare da masu yin sujada ga Allah, da kuma wadanda yake samu a kowace rana, a kasuwa.
18Amma wadan su Abikuriyawa da masana sun yi karo da shi. Wadansun su na cewa, "Menene wannan sakaren ke cewa?" Wadansu kuma sun ce, "Da alama mai wa'azi ne na wasu alloli dabam," domin yana wa'azin Yesu da tashin sa daga matattu.
19Suka dauki Bulus zuwa Tudun Arasa, suna cewa, "Ko za ka sanar mana da wannan sabuwar koyaswar taka? 20Abubbuwan da kake fadi, baki ne a gare mu. Muna so mu san ma'anar su." 21(Atiniyawa da bakin da ke cikinsu, suna ba da lokacin su ga fadin sabobbin abubuwa da sauraron su).
22Bulus ya tsaya a tsakiyar Tudun Arasa ya ce, "Ku mutanen Atiniya na lura masu kwazon addini ne ku. 23Na lura da abubuwan sujadar ku yayin da nake zagawa, amma na ga wani bagadi da rubutu a kansa mai cewa, "Ga Allah wanda ba a sani ba." Abin da kuke bauta wa cikin rashin sani, shi nake sanar maku.
24Allahn da ya yi duniya da kome da ke cikinta, tun da ya ke shine Ubangijin sama da kasa, ba ya zama a haikalin da mutane suka gina da hannu. 25Ba ya neman taimakon kowa, babu kuma wanda ya isa ya ba shi. Shine ke ba da rai, da numfashi da kowanne abu.
26Daga mutum daya ya hallici dukan al'umman duniya, ya rarraba, ya kuma sanya kowa a inda ya shirya masa. 27Domin su nemi Allah ko za su iya kaiwa zuwa gareshi su same shi, ga shi kuwa ba ya nesa da kowannenmu.
28A cikinsa muke rayuwa, muna walwala, kamar yadda wani daga cikin masananku yace, 'Mu 'ya'yansa ne'. 29Idan mu 'ya'yan Allah ne, bai kamata mu danganta Allah da zinariya ko azurfa, ko kuma duwatsu da itatuwa da an sassaka ba.
30Saboda haka ne, Allah ya kawar da kwanakin jahilci, amma ya ba da umarni kowa a ko'ina ya tuba. 31Akwai ranar da ya shirya zai yi wa duniya shari'a cikin adalci, ta wurin mutumin da ya zaba. Allah ya nuna wannan mutumin, ta wurin ta da shi daga matattu".
32Da mutanen Atina sun ji batun tashi daga matattu, wadansu suka yi wa Bulus ba'a; amma wadansu kuma sun ce, "Za mu saurare ka kuma, a kan wannan maganar." 33Bayan haka, Bulus ya bar su. 34Amma wasu maza a cikinsu sun yarda da bisharar, sun ba da gaskiya, hade da Diyonisiyus dan Majalisar Tudun Arasa da wata mace mai suna Damaris, da wadansu tare da su.

18

1Bayan haka sai Bulus ya tafi Antakiya daga nan, ya wuce Korinti. 2A can ya sadu da wani Bayahude mai sunan Akila, dan kasar Buntus ne; bai dade da zuwa garin ba, daga Italiya ya zo da matarsa mai suna Balkisu, saboda Kalaudiyas ya ba da umarni dukan Yahudawa su bar Roma; sai Bulus ya je wurinsu. 3Bulus ya zauna a gidansu don sana'arsu daya ce, wato, masu aikin Tanti ne.

4Saboda haka Bulus na zuwa majami'a, yana yin nazari tare da su a kowace Asabaci. Yana kokari ya rinjayi Yahudawa da Helinawa. 5Amma a lokacin da Sila da Timoti suka iso Makidoniya, Ruhu ya matsa Bulus ya shaida wa Yahudawa cewa Yesu Almasihu ne. 6Lokacin da Yahudawa suka tayar masa suna zarginsa. Bulus ya kakkabe rigansa a gabansu yana cewa, "Alhakin jininku yana kanku; daga yanzu zan koma wurin al'ummai."
7Da ya bar wurinsu, ya tafi gidan Taitus Yustus mai wa Allah sujada. Gidansa na kusa da majami'a. 8Kiristus shine shugaban majami'a, sai shi da dukan iyalin gidansa sun ba da gaskiya ga Ubangiji. Korantiyawa da yawa suka ji jawabin Bulus suka ba da gaskiya, aka yi masu Baftisma.
9Da dare Ubangiji ya ce wa Bulus a cikin wahayi, "Kada ka ji tsoro, amma ka yi magana kada kuma ka yi shuru. 10Gama ina tare da kai, ba wanda zai cutar da kai, gama ina da mutane anan garin." 11Bulus ya zauna a nan tsawon shekara daya da wata shida, yana koyar masu da maganar Allah.
12Amma da Galiyo ya samu zaman gwamnan Akaya, sai Yahudawa suka tayar wa Bulus har suka kai shi gaban dakalin shari'a. 13Suna cewa, "Wannan mutumin yana kokarin rinjayar mutane su yi sujadar da ta saba wa dokarmu."
14Duk da haka kafin Bulus ya yi magana, Galiyo ya ce wa Yahudawa, "Ku Yahudawa in da karar ku ta wani babban laifi ce wanda ya aikata, da sai in hukunta. 15Amma tun da ya ke akan al'amurar, kalmomi ne, da ta sunaye da dokokin ku, ku je ku sasanta al'amuran ku."
16Galiyo ya kore su daga dakalin shari'a. 17Saboda haka sai suka kama Sastanisu, suka yi masa duka sosai a gaban dakalin shari'a. Amma Galiyo bai damu da yadda suka karasa ba.
18Bulus kuwa, bayan ya zauna tare da su na wasu kwanaki masu yawa, ya bar 'yan'uwan zuwa Suriya ta jirgin ruwa, tare da Balkisu da Akila. Kafin ya bar tashar jiragen ruwa da ke a Sankuriya, ya tafi saboda ya aske kansa, domin ya dauki alkawarin Banazare. 19Da suka iso Afisa, Bulus ya bar Balkisu da Akila anan. Shi kuwa ya shiga majami'ar Yahudawa yana nazari tare da su.
20Da suka roki Bulus ya zauna da su na tsawon lokaci, bai yarda ba. 21Ya kama hanyarsa ya bar su ya ce, "In Allah ya yardar mani zan dawo wurinku wata rana." Sai ya shiga jirgin ruwa daga Afisa.
22Daga saukar su a Kaisariya, sai ya haura zuwa Urushalima ya gai da iklisiya daga nan ya tafi Antakiya. 23Bayan ya zauna na dan lokaci a wurin, Bulus ya kama hanyarsa zuwa yakin Galatiya da Firjiya anan ya karfafa almajirai.
24A nan dai akwai wani Bayahude mai suna Afolos, dan asalin Iskandariya ne da haihuwa, ya zo Afisa. Shi masani ne a maganar Allah. 25Afolos dai ya sami horo daga maganar Ubangiji. Shi mai kokari ne a ruhu, yana wa'azi da koyarwa daidai game da Yesu. Amma ya san da Baftismar Yahaya ne kadai. 26Afolos ya fara wa'azinsa da gabagadi a cikin majami'a. Da Balkisu da Akila suka ji shi sai suka yi abokantaka da shi, suka kara bayyana masa game da labarin hanyar Allah mafi daidai.
27Da ya so ya wuce zuwa cikin Akaya 'yan'uwa suka karfafa shi, sun rubuta wa almajiran da ke a Akaya, don su karbe shi da hannu biyu. Da ya iso wurinsu, ya kuwa karfafa 'yan'uwa da sun ba da gaskiya ta wurin alheri. 28Afolos ya ba Yahudawa mamaki da irin ikon da yake da shi da gwanintarsa, yadda yake nunawa daga nassoshi cewa Yesu shine Almasihu.

19

1Sa'adda Afolos yake a Koranti, Bulus ya zagaya kasar tudu ya zo birnin Afisa, a nan kuma ya sami wadansu almajirai. 2Bulus ya ce masu, "Ko kun karbi Ruhu Mai Tsarki sa'anda kuka ba da gaskiya?" Suka amsa, "A'a bamu taba jin labarin Ruhu Mai Tsarki ba.

3Bulus ya ce, "Wacce irin baftisma aka yi maku?" Suka ce, "Baftismar Yahaya" 4Bulus ya amsa ya ce, "Yahaya ya yi wa mutane baftismar tuba, ya ce su ba da gaskiya wanda zai zo bayansa, wato, Yesu kenan."
5Da mutanen suka ji haka, sai aka yi masu baftisma cikin sunan Ubangiji Yesu. 6Sa'adda Bulus ya dibiya hannu a kansu, Ruhu Mai Tsarki kuma ya sauka a kansu suka yi magana da harsuna da kuma annabci. 7Su wajen mutum goma sha biyu ne.
8Bulus ya shiga majami'a ya yi ta koyarwa gabagadi misalin tsawon wata uku. Yana bi da su cikin nazarin maganar yana fahimtar da mutane su gaskanta game da abubuwa da suka shafi mulkin Allah. 9Amma sa'adda wadansu Yahudawa suka taurare, suka ki yin biyayya, sai suka fara bata hanyar Almasihu a gaban taron. Saboda haka sai Bulus ya janye daga wurinsu tare da wadanda suka ba da gaskiya. Ya fara koyarwa a makarantar Tiranus. 10Haka ya cigaba shekaru biyu har duk mazaunan Asiya suka ji maganar Ubangiji, Yahudawa da Helenawa.
11Allah ya yi manyan al'ajibai ta hannun Bulus, 12har marasa lafiya suka warke, mugayen ruhohi suka fito daga cikin mutane, sa'adda suka karbi kyallaye da mayafai daga jikin Bulus.
13Amma akwai Yahudawa masu tsubu da suka biyo ta wajen, suka dauka wa kansu su yi amfani da sunan Yesu. Suka ce, "Mun dokace ku cikin sunan Yesu wanda Bulus yake wa'azinsa, ku fita." 14Wadanda suka yi wannan su bakwai ne 'ya'yan wani babban firist Bayahude mai suna Siba.
15Mugun ruhun ya amsa ya ce, "Na san Yesu, na san Bulus, amma ku, su wanene?" 16Sai mugun ruhun da ke cikin mutumin ya fada a kan matsubatan ya fi karfinsu ya kuma bubuge su. Suka runtuma da gudu suka fice daga dakin tsirara da raunuka. 17Wannan ya zama sanannen abu ga dukan mutane, Yahudawa da Helenawa mazaunan Afisa. Suka ji tsoro kwarai, sunan Ubangiji Yesu ya sami daukaka.
18Masu bi da yawa kuma, suka zo suka furta mugayen ayyukan da suka aikata. 19Masu sihiri suka kawo littattafansu suka kona a gaban mutane. Da aka yi jimilar tamaninsu, aka samu sun kai dubu hamsin na azurfa. 20Sai maganar Ubangiji ta yadu da iko ta hanyoyi da yawa.
21Da Bulus ya kammala aikinsa na bishara a Afisa, Ruhu ya bishe shi sai ya bi ta Makidoniya da Akiya a kan hanyarsa zuwa Urushalima. Ya ce, "Bayan na je can, dole in je Roma." 22Bulus ya aiki almajiransa biyu Timoti da Irastus zuwa Makidoniya, wadanda suka taimake shi. Amma shi da kansa ya jira a Asiya na dan lokaci.
23A wannan lokacin sai aka yi babban tashin hankali a Afisa game da wannan Hanyar. 24Wani Makeri mai suna Damatrayus wanda ke kera sifoffin gunkin azurfa na Dayana, wanda sana'a ce mai kawo wa makera riba sosai. 25Ya tattara makera ya ce da su, "Kun sa ni da wanan sana'a ne muke samun kudi mai yawa.
26Kun gani kun kuma ji cewa, ba a Afisa kadai ba, amma har da fadin kasar Asiya wannan Bulus ya rinjayi mutane da yawa. Yana cewa babu alloli da ake kerawa da hannu. 27Ba sana'ar mu kadai ke cikin hatsari ba, amma har da haikalin allahnmu Dayana babba zai zama mara amfani. Ta haka za ta rasa girmanta, ita da dukan kasar Asiya da duniya ke wa sujada."
28Da suka ji haka sai suka fusata kwarai, suka yi kira mai karfi suna cewa "Mai girma ce Dayana ta Afisa." 29Gari gaba daya ya rude, jama'a kuma sun hanzarta zuwa wurin taron. Kafin wannan lokaci, sun riga sun kama abokan tafiyar Bulus, wato Gayus da Aristakas wadanda suka zo daga Makidoniya.
30Bulus ya yi niyya ya shiga cikin taron jama'ar, amma almajiran suka hana shi. 31Haka nan ma wadansu abokan Bulus da ke shugabanin yankin al'umma Asiya sun aika masa da roko mai karfi kada ya shiga dandalin. 32Wadansu mutane na kirarin wani abu, wadansu kuma na kirarin wani abu dabam, domin jama'a sun rude. Da yawa daga cikinsu ma ba su san dalilin taruwarsu ba.
33Yahudawa suka kawo Iskandari ya tsaya a gaban taruwan jama'a. Iskandari ya mika hannunsa sama domin ya yi bayani ga jama'a. 34Amma da suka gane shi Bayahude ne, sai dukansu suka kwala ihu wajen sa'a biyu, "Mai girma ce Dayana ta Afisa."
35Da magatakardar garin ya sha kan jama'a, sai ya ce, "Ya ku mutanen Afisa, wanene bai san cewa birnin Afisa cibiya ce na allahn nan Dayana mai girma da na sifar da ta fado daga sama ba? 36Tun da ba a karyata wadannan abubuwa ba, ya kamata ku yi shuru don kada ku yi wani abu a gaggauce. 37Gama kun kawo wadannan mutane a wannan dakin sharia ba a kan su mafasa ne na haikali ba ko kuma masu sabo ga allahnmu ba.
38Saboda haka idan Damatrayas da makeran da ke tare da su na da wata tuhuma a kan wani, kotuna suna nan a bude masu shari'a kuma suna nan. Ba ri su kai karar junansu. 39Amma idan akwai maganganu na dubawa, za a daidaita su a taronmu na lokaci lokaci. 40Domin hakika muna cikin hatsarin zargi game da hargitsin yau. Babu dalilin wanan yamutsi domin ba mu da bayani a kansa." 41Da ya fadi haka, sai ya sallami taron.

20

1Bayan da rikici ya kare, Bulus ya aika a kira al'majiran, ya karfafa su. Sa'annan ya yi bankwana da su, ya tashi zai tafi Makidoniya. 2Bayan ya ratsa cikin lardunan yana yi wa masu bi gargadi sosai, sai ya zo kasar Helenawa. 3Sa'adda ya yi wata uku a wurin, Yahudawa suka kulla masa makirci, yayin da yake shirin hawa Jirgi zuwa Suriya, sai ya canza ra'ayi ya koma ta Makidoniya.

4Masu yi wa Bulus rakiyar zuwa yankin Asiya sun hada da Sobatarus dan Burus daga Biriya; Gayus mutumin Derbe; Timoti da Aristakus da Sakundus, dukansu masu bi ne daga Tasalonika; da Tikikus da Trofimus daga Asiya. 5Amma wadansu har suka rigaye mu, suka jira mu a Taruwasa. 6Da muka shiga Jirgi daga Filibi bayan kwanakin Gurasa mara yisti; bayan kwanaki biyar muka iske su a Taruwasa; kwananmu bakwai a wurin.
7A rana ta fari ga mako, da muka taru domin karya gurasa. Bulus ya yi wa masubi jawabi, don ya yi niyyar ya tafi da wayewar gari; jawabinsa ya kai har tsakar dare. 8A benen da suka taru akwai fitilu da yawa.
9Wani matashi mai suna Aftikos yana zaune a kan taga, barci mai nauyi ya dauke shi; da shike Bulus ya tsawaita jawabinsa, saurayin da shike barci mai nauyi ya dauke shi sai ya fado daga kan bene na uku aka dauke shi matacce. 10Sai Bulus ya sauka ya mike a bisansa ya rungume shi, sa'annan ya ce, "Kada kowa ya damu; domin yana darai bai mutu ba."
11Sa'annan ya hawo kan bene domin cin gurasa tare da su, ya yi magana da su har gari ya waye daga nan ya bar su. 12Suka kawo saurayin da rai, sun sami ta'aziya ba kadan ba.
13Amma mu, da muka riga Bulus zuwa gun Jirgin, muka shiga zuwa Asos, mun shirya mu dauki Bulus a jirgi amma shi ya kudurta ya yi tafiya a kasa. 14Da muka sadu a Asos, mun dauke shi a Jirgin ruwa zuwa Mitilitus.
15Bayan tashin mu daga can, washegari muka zo tsibirin Kiyos. Washegari kuma muka zo birnin Militus. 16Amma Bulus ya kudurta wucewa Afisa a Jirgi, don kada ya bata lokaci a Asiya, don yana sauri in ya yiwu ranar Fentekos ta same shi a Urushalima.
17Daga Militus ya aika a kira masa dattawan iklisiyar Afisa. 18Da suka zo wurinsa sai ya ce masu, "Ku da kanku kun san tun daga ranar da na sa kafata a Asiya, irin zaman da muka yi da kasancewar mu tare. 19Na bauta wa Ubangiji da tawaliu har da hawaye, da wahalun da na sha saboda makircin Yahudawa. 20Kun sani ban ji nauyin sanar da ku kowanne abu mai amfani ba, na bi ku gida gida ina koyar da ku abubuwa a sarari. 21Kunsan yadda na gargadi Yahudawa da Hellenawa game da tuba ga Allah da bangaskiya ga Ubangiji Yesu.
22Yanzu fa, gashi, zan tafi Urushalima, Ruhu Mai Tsarki ya nuna mani a fili dole in je, ban san abin da zai faru da ni a can ba. 23Sai dai Ruhu Mai Tsarki ya nuna mani a kowanne gari cewa, sarkoki da wahalu suna jira na. 24Amma ban dauka cewa raina yana da wani amfani gare ni ba, domin in cika tsere da hidimar da na karba daga wurin Ubangiji Yesu, ta shaidar bisharan alherin Allah.
25Yanzu fa, duba, na san dukanku, wadanda na yi wa wa'azin mulkin Allah, ba za ku kara gani na ba. 26Don haka na shaida maku a wannan rana, ba ni da alhakin jinin kowanne mutum. 27Don banji nauyin sanar maku da dukan nufin Allah a gare ku ba.
28Saboda haka ku kula da kanku, da masubi da Ruhu Mai Tsarki ya sanya ku shugabanni. Ku kula ku yi kiwon iklisiyar Allah, wadda ya saya da jininsa. 29Na sani cewa bayan tafiyata, kyarketai masu zafi za su shiga tsakaninku, kuma baza su rangwanta wa masubi ba. 30Na sani har daga cikinku wadansu mazaje za su zo su fadi gurbattatun zantattuka, domin su janye almajirai zuwa gare su.
31Saboda haka ku yi lura. Ku tuna da cewa shekara uku ban fasa yi wa kowannenku gargadi da hawaye dare da rana ba. 32Yanzu ina mika ku ga Allah, da maganar Alherinsa, wadda take da ikon gina ku ta kuma ba ku gado tare da dukan wadanda ke cikin kebabbu na Allah.
33Ban yi kyashin azurfa, ko zinariya, ko tufafin wani ba. 34Ku da kanku kun sani na yi aiki da hannuwana, na biya bukatu na da na wadanda ke tare da ni. 35Na zama maku abin koyi a kowace hanya game da yadda za ku taimaka wa nakasassu ta wurin aiki, da yadda za ku tuna da maganar Ubangiji Yesu, maganar da shi da kansa ya ce: "Bayarwa tafi karba albarka."
36Bayan da ya yi magana haka, ya durkusa ya yi addu'a tare da su duka. 37Dukansu kuwa suka yi kuka mai tsannani, suka rungume shi kuma suka sunbace shi. 38Suka yi bakin ciki musamman domin abin da ya ce masu, ba za su kara ganinsa ba. Sai dukansu suka yi masa rakiya zuwa wurin jirgin ruwa.

21

1Da muka rabu da su, muka shiga jirgin ruwa muka mike hanya zuwa birnin Kos, washegari sai birnin Rodusa, daga nan sai kuma zuwa birnin Batara. 2Da muka sami jirgi mai hayewa zuwa Fonisiya sai muka shiga.

3Da muka hango tsibirin Kubrus muka bar shi a hagun mu muka nufi Suriya, muka sauka a birnin Taya domin a nan ne jirgin ruwan zai sauke kayansa. 4Bayan mun sami almajirai sai muka zauna can kwana bakwai. Al'majiran suka ce ma Bulus, ta wurin Ruhu, kada ma ya je Urushalima.
5Bayan 'yan kwanaki muka cigaba da tafiyarmu. Dukansu da matansu da 'ya'yansu suka raka mu har bayan birnin. Sa'annan muka durkusa a bakin gacci muka yi addu'a muka yi sallama da juna. 6Sai muka shiga jirgin ruwa, su kuma suka koma gida.
7Da muka gama tafiyarmu a Taya muka iso Talamayas. A nan ne muka gaisa da 'yan'uwa, muka zamna kwana daya da su. 8Washegari muka tashi muka tafi Kaisariya. Muka shiga gidan Filibus mai shaida bishara, daya daga cikin bakwai din, muka zauna da shi. 9Wannan mutum yana da 'ya'ya hudu mata, budurwai masu yin annabci.
10Sa'anda muka zauna can 'yan kwanaki, wani annabi ya zo daga Yahudiya mai suna Agabus. 11Ya zo wurinmu ya dauki damarar Bulus ya daure tasa kafar da hannayensa ya ce, "Ruhu Mai Tsarki ya ce, 'Haka Yahudawa za su daure mai wannan damarar, zasu kuma bashe shi ga al'ummai.'"
12Da muka ji wannan sakon, sai dukanmu da mazaunan wurin muka roki Bulus kada ya tafi Urushalima. 13Sai Bulus ya amsa ya ce, "Me kuke yi, kuna kuka kuna karya mani zuciya? Bama a shirye don dauri kadai nake ba har ma da mutuwa a Urushalima, sabili da sunan Ubangiji Yesu." 14Tun da Bulus bashi da niyyar a rinjaye shi, muka daina kuka muka ce, "Bari nufin Ubangiji ya tabbata."
15Bayan wadannan kwanaki, muka dauki jakkunanmu muka haura Urushalima. 16Wadansu almjirai daga Kaisariya suka bi mu. Sun zo ne tare da wani ana ce da shi Manason, mutumin Kuburus mai bi na farko, wanda za mu zauna da shi.
17Da muka isa Urushalima, 'yan'uwa suka marabce mu da farin ciki. 18Washegari Bulus ya tafi tare da mu zuwa wurin Bitrus, dukan dattawa kuma suna nan. 19Bayan ya gaishe su, sai ya shaida masu daya bayan daya abubuwan da Allah ya yi cikin al'ummai ta wurin hidimarsa.
20Da suka ji haka, suka yabi Ubangiji suka ce masa, "Ka gani, dan'uwa, dubban Yahudawa sun bada gaskiya suna kuma da niyyar kiyaye shari'a. 21An kuma gaya masu a kanka cewa, kana koya wa Yahudawan da suke zaune cikin al'ummai su yi watsi da Musa. Kana koya masu kada su yi wa 'ya'yansu kaciya, kada kuma su bi tsofaffin al'adu.
22Me ya kamata mu yi? Hakika za su ji ka zo. 23Sabo da haka ka yi abin da muka fada maka yanzu. Muna da maza hudu da suka dauki wa'adi. 24Tafi da wadannan ka tsarkake kanka tare da su, ka dauki dukan dawainiyar su dana askin kai. Ta haka kowanne mutum zai sani abubuwan da ake fadi a kanka karya ne. Za su sani cewa kai mai kiyaye shari'a ne.
25Game da al'umman da suka bada gaskiya mun yi masu wasika, mun bada umarni su kaurace kansu daga sadakokin da aka mika wa gumaku, da jini, da abin da aka makare da kuma fasikanci. 26Sai Bulus ya dauki mazannan, washegari ya tsarkake kansa tare da su, suka shiga haikali, domin ya sanar da cikar ranakun tsarkakewarsu, wato ranar ba da sadaka domin kowanne dayansu.
27Da kwanakin nan bakwai suka yi gab da cika, wadansu Yahudawa daga Asiya suka ga Bulus a haikali, sai suka zuga taro, suka danke shi. 28Suna ta kururuwa, "Mutanen Isra'ila ku taimaka mana. Wannan shine mutumin da ke koya wa dukan mutane ko'ina abubuwa gaba da mutane, da shari'a da kuma wannan wurin. Banda haka ya kawo Helenawa cikin haikalin nan ya kazantar da wannan wuri tsatsarka." 29Domin dama sun ga Tarofimas mutumin Afisa tare da Bulus cikin birni, suka yi zaton ya kawo shi cikin haikali.
30Sai duk gari ya rude, mutane suka runtuma suka danke Bulus. Suka ja shi waje daga cikin haikalin, nan da nan aka rufe kofofin. 31Suna kokarin kashe shi kenan, sai labari ya kai wurin hafsan sojoji cewa Urushalima duk ta yamutse da tarzoma.
32Nan take ya dauki mayaka da jarumawa, suka sheka da gudu wurin taron. Da mutane suka ga hafsan sojoji da rundunansa sai suka daina dukan Bulus. 33Sai hafsan ya tafi ya danke Bulus ya sa aka daure shi da sarkoki biyu. Ya tambaya ko shi wanene da kuma laifinsa.
34Wadansu cikin taron suna ta kururuwa wadansu su ce wannan, wadansu su ce, wancan. Tunda hafsan bai fahimci abin da suke fadi ba, sabo da ihunsu, ya dokaci a shigar da Bulus farfajiyar sojoji. 35Da suka kai matakala, sojoji suka dauki Bulus sabo da tsananin husatar taron jama'a. 36Domin taron suka biyo baya suna ihu suna cewa, "A kashe shi."
37An kusa shigar da shi farfajiyan kenan sai Bulus ya ce wa babban hafsan, "Ko ka yarda inyi magana da kai?" Hafsan ya ce, "Ka iya Helenanci? 38Ashe ba kai ne Bamasaren nan da kwanakin baya ka haddasa tawaye, ka dauki 'yan ta'adda dubu hudu ka kai su jeji ba?"
39Bulus ya ce, "Ni Ba'ibrane ne daga birnin Tarsus a Kilikiya. Ni dan kasar babban birni ne. Ka amince mani in yi magana da mutanen." 40Da hafsan ya bashi izni, Bulus ya mike a kan matakala ya daga hannayensa sama ya yi nuni su yi shuru. Da wuri ya yi tsit, Bulus ya yi masu magana da Ibraniyanci. Ya ce,

22

1"Yanuwa da Ubanni, ku saurari kariya ta zuwa gare ku yanzu." 2Da taron sun ji Bulus na magana a harshen Ibraniyawa sai sun yi tsit. Ya ce,

3Ni Bayahude ne daga garin Tarwasa na Kilikiya, amma a karkashin Gamaliyal aka ilimantar da ni. An horar da ni sosai bisa ga bin hanyar dokokin kakkaninmu. Ina da himma ga bin Allah kamar yadda ku ma kuna da ita. 4Na tsananta wa wannan Hanyan har ga mutuwa; na daure maza da mata sa'annan na jefa su cikin gidan yari. 5Hakannan ma babban firist da dukan dattawa za su ba da shaida cewa na karbi izini daga wurinsu domin 'yan'uwa da ke a Dimashku, saboda in tafi can. Haki na shine in daure mabiyan Hanyan nan, in kawo su Urushalima domin a hukunta su.
6Sa'anda ina cikin tafiya, ina kuma kusa da Dimashku, da tsakar rana sai farat daya ga babban haske daga sama ya haskaka kewaye dani. 7Na fadi kasa sa'anan na ji murya na ce da ni, 'Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mani?' 8Na amsa, 'Wanene kai, Ubangiji?' Ya ce mani, 'Nine Yesu Banazarat wanda kake tsananta wa.'
9Wadanda ke tare da ni sun ga hasken, amma ba su gane muryar wanda ya yi magana da ni ba. 10Na ce, 'Me zan yi ya Ubangiji?" Ubangiji ya ce mani, 'Tashi ka tafi cikin Dimashku, a can za a fada maka abinda wajibi ne ka yi. 11Ban iya ganin wuri ba domin walkiyar hasken, sai na tafi cikin Dimashku ta wurin jagorancin wadanda ke tare da ni.
12A can na sami wani mai suna Ananiya, mai tsoron Allah bisa ga sharia, da kyakyawan suna kuma a gaban Yahudawa da ke zama a can. 13Ya zo gare ni ya ce, 'Dan'uwa Shawulu, karbi ganin gari.' A daidai wannan sa'a na gan shi.
14Sa'annan ya ce, 'Allah na kakkaninmu ya zabe ka ka san nufinsa, ka ga Mai Adalcin nan, ka kuma ji muryar da ke fitowa daga bakinsa. 15Gama za ka zama mashaidinsa ga dukan mutane game da abinda ka gani da wanda ka ji. 16A yanzu me ka ke jira? 'Tashi a yi maka baftisma a wanke zunubanka, kana kira bisa sunansa.'
17Bayan da na dawo Urushalima, sa'anda ina addu'a a cikin haikali, sai na karbi wahayi. 18Na gan shi ya ce mani, 'Gaggauta ka bar Urushalima yanzu, domin ba za su yarda da shaidarka game da ni ba.'
19Na ce, 'Ubangiji, su da kansu sun san yadda na sa su a kurkuku na kuma doddoke wadanda suka gaskanta da kai a kowacce masujada. 20A sa'anda a ke zubar da jinin mashaidinka Istifanus, ina nan tsaye ina goyon baya, ina kuma lura da rigunan wadanda suka kashe shi.' 21Amma ya ce mani, 'Tafi, domin zan aike ka can wurin Al'ummai.'
22Mutanen sun bar shi yayi magana har zuwa ga wannan lokacin. Amma sai suka ta da murya suna cewa, 'A kawar da wannan dan taliki daga duniya: don bai kamata ya rayu ba.' 23Sa'anda suke tadda muryarsu, suna jefar da tufafinsu da kuma baza kura a iska, 24babban hafsan ya umarta a kawo Bulus a farfajiyan. Ya umarta da cewa a bincike shi da bulala, domin ya san dalilin da suka ta da ihu gaba da shi haka.
25Bayan da suka daure shi da tsirkiya, Bulus ya ce wa Jarumin da ke kusa da shi, "Ko daidai ne bisa ga doka a yi wa Barome wanda ma sharia ba ta kashe shi ba bulala?" 26Da Jarumin ya ji haka, ya tafi wurin babban hafsan, yana cewa, "Me kake so ka yi? Gama wanan mutumin dan asalin Roma ne."
27Babban hafsa ya zo ya ce masa, "Gaya mani, kai dan asalin Roma ne?" Bulus ya ce, "Haka ne." 28Babban hafsan ya amsa masa, "Da kudi masu yawa na sayi yancin zama dan kasa." Amma Bulus ya ce, "An haife ni dan kasar Roma. 29"Sai mutanen da sun zo su tuhume shi sun bar shi nan da nan. Babban hafsa shi ma ya tsorata da ya gane Bulus dan asalin Roma ne, domin ya riga ya daure shi.
30Washegari, babban hafsan ya so ya san gaskiyar tuhuma da Yahudawa suke yi a kan Bulus. Sai ya kwance shi daga sarka, ya kuma umarci babban firist da dukan majalisa su sadu. Sai ya kawo Bulus ya sa shi a tsakiyarsu.

23

1Bulus ya kura wa yan majalisa ido yace, '"Yan'uwa, na yi rayuwa tare da Allah da lamiri mai kyau har wannan ranan." 2Babban firist Hannaniya ya ba wandanda suke tsaye tare da shi urmarni su buge bakinsa. 3Bulus ya ce, "Allah zai buge ka, kai munafiki. Kana zama domin ka shari'anta ni da shari'a, kuma ka umarce a buge ni, gaba da sharia?"

4Wanda suka tsaya a gefe suka ce, "Kada ka zage babban firis na Allah." Bulus yace, "Ban sani ba, 'yan'uwa, cewa shi babban firis ne. 5Domin a rubuce yake, Ba za ku zargi shugaban mutanenku ba."
6Da Bulus ya ga cewa, daya bangaren Sadukiyawa ne dayan kuma Farisawa, ya yi magana da karfi a majalisa, '"Yan'uwa, ni Bafarise ne, dan Farisawa. Don tabbacin tashin matattu ne kuna shari'anta ni." 7Daya fadi haka, mahawara ta fara a tsakanin Farisawa da Sadukiyawa, sai taron ya rabu kashi biyu. 8Don Sadukiyawa suka ce babu tashin matattu, babu mala'iku, babu kuma ruhohi, amma Farisawa suka ce dukan abubuwan nan sun kasance.
9Sai mahawara ta tashi, wadansu marubutan Farisawa suka tashi da mahawara cewa, "Ba mu same mutumin nan da laifi ba sam. Ko mala'iku da ruhohi ne suka yi masa magana?" 10Da jayayya ta tashi, babban hafsa ya ji tsoro kada su yayaga Bulus, sai ya umarce sojoji suje su kwato shi da karfi daga 'yan majalisa, su tafi da shi farfajiya.
11Da dare Ubangiji ya tsaya kusa da shi yace, "Kada ka ji tsoro, kamar yadda ka ba da shaida game da ni a Urushalima, dole zaka sake zama shaida a Roma."
12Da gari ya waye, wadansu Yahudawa sun yi yarjejeniya suka dauka wa kansu la'ana: suka ce ba za su ci ba ba za su sha ba sai sun kashe Bulus. 13Mutane fiye da arba'in suka kulla wannan makirci.
14Suka je wurin manyan firistoci da dattawa suka ce, "Mun sa wa kanmu la'ana, ba za mu ci ba, ba za mu sha ba sai mun kashe Bulus. 15Yanzu, bari majalisa ta ba wa babban hafsa izini a kawo shi a gaba, kamar zai yanke hukunci. Mu kam, a shirye muke mu kashe shi kafin ya iso nan.
16Amma dan yar'uwan Bulus ya ji suna labe, sai ya tafi ya shiga farfajiyar ya fada wa Bulus. 17Bulus ya kira daya daga cikin jarumai yace, "Dauki saurayin nan ka kai shi wurin babban hafsa, don yana da abin da zai fada masa."
18Jarumin ya dauke saurayin ya kai shi wurin babban hafsa yace, "Bulus dan sarka ne yace in kawo saurayin nan a gaban ka. Yana da abin da zai fada maka." 19Babban hafsa ya kai shi wani lungu, sai ya tambaye shi, "Menene kake so ka fada mani?"
20Saurayin yace, "Yahudawa sun yarda su roke ka ka kawo Bulus gobe a majalisa, kamar zasu kara bincike a kan al'amarin. 21Amma kada ka yarda da su, mutane fiye da arba'in suna jiransa. Sun sa wa kansu la'anna, ba za su ci ba ba za su sha ba sai dai sun kashe shi. Yanzu a shirye suke; suna jira ka ba su izini."
22Sai babban hafsa yace wa saurayin ya tafi, da ya gama masa magana, "Kar ka fada wa wani al'amuran." 23Sai ya kira jarumai biyu yace, "Ku shirya sojoji dari biyu, yan dawakai saba'in, masu daukar mashi dari biyu su tafi kaisariya karfe uku na dare." 24Ya umarta a shirya dabbobin da Bulus zai hawo da zasu kai shi lafiya wurin Filikus gwamna.
25Sai ya rubuta wasika a misalin haka: 26Gaisuwa zuwa Kuludiyas Lisiyas zuwa ga mai martaba gwamna Filikus. 27Yahudawa sun kama wannan mutumin suna shirin kashe shi, na abko masu da sojoji na kwace shi, bayan da na ji shi Barome ne.
28Inna son sani dalilin zarginsa, sai na kai shi majalisa. 29Na gane cewa ana zarginsa ne a kan tambayoyi game da shari'ansu, amma ba wani zargi da ya cancanci dauri ko mutuwa. 30Da aka sanar da ni shirin makircin, sai na tura shi wurinka ba da bata lokaci ba, na umarce masu zarginsa su kawo zarginsu wurinka. Huta lafiya."
31Sai sojoji suka yi biyayya da umarni da aka basu: suka dauki Bulus suka kawo shi dadare a wurin Antibatris. 32Da gari ya yawe, yan dawakai suka tafi tare da shi kuma sauran sojoji suka koma farfajiya. 33Bayan da yandawakan suka isa Kaisiririya sun mika wasika ga gwamna, suka kuma danka Bulus a hanunsa.
34Da gwamna ya karanta wasikar, sai ya tambaye su daga wani yanki ne Bulus ya fito; da ya ji daga yankin kilikiya ne, 35Yace zan saurare ka sosai lokacin da masu zargin ka sun zo. Sai ya umarta a tsare shi a fadar Hiridus.

24

1Bayan kwanaki biyar, sai Ananiyas babban firist, Wasu dattawa da wani masanin shari'a mai suna Tartilus, sun tafi can. Suka kai karar Bulus gaban gwamna. 2Lokacin da Bulus ya tsaya gaban gwamna, Tartilus ya fara zarginsa yace wa gwamnan, "Saboda kai mun sami zaman lafiya; sa'annan hangen gabanka ya kawo gyara a kasarmu; 3don haka duk abin da ka yi mun karba da godiya, ya mai girma Filikus.

4Domin kada in wahalsheka, ina roko a yi mani nasiha don in yi magana kadan. 5An iske mutumin nan yana barna irir iri, yana kuma zuga jama'ar Yahudawa a dukan duniya su yi tayarwa. 6Har ma ya yi kokarin kazantar da haikali; saboda haka muka kama shi. 1
7Amma Lisiyas jami'i ya zo ya kwace shi da karfi daga hannunmu. 8Idan ka binciki Bulus game da wadannan al'amura, kai ma, zai tabbatar maka abin da muke zarginsa a kai. 9Dukan Yahudawa suna zargin Bulus cewa wadannan abubuwa gaskiya ne.
10lokacin da gwamnan ya alamta wa Bulus ya yi magana sai yace, "Yanzu na fahimci cewar da dadewa kana mulkin kasarnan, don haka da farin ciki zan yi maka bayani. 11Zaka iya tabbatarwa cewa bai kai kwana sha biyu ba tun da nake zuwa Urushalima don yin sujada. 12Da suka same ni a haikali, ban yi jayayya ko kawo rudami a tsakanin jama'a ba. 13Don haka ba su da tabbas akan abinda suke zargina a kansa yau.
14Amma na sanar da kai, bisa ga abin da suke kira darika, haka ni ma nake bautawa Allah na kakanninmu. Na yi aminci wajen kiyaye dukan abin da ke a rubuce a Attaurat da litattafan annabawa. 15Ina sa bege ga Allah, kamar yadda za a yi tashin matattu, masu adalci da miyagu; 16a kan haka kuma, nake kokarin zama mara abin zargi a gaban Allah da mutane ina yin haka cikin dukan al'amura.
17Bayan wadansu shekaru na zo in kawo wasu sadakoki da baikon yardar rai. 18Cikin kudurin yin haka, sai wasu Yahudawa daga kasar Asiya suka iske ni a cikin ka'idodin tsarkakewa a haikali, ba da taro ko ta da hargitsi ba. 19Yakamata wadannan mutanen su zo gabarka a yau, har idan suna da wani zargi a kai na.
20In kuwa ba haka ba bari mutanennan su fada in sun taba iske ni da wani aibu a duk lokacin da na gurfana a gaban majalisar Yahudawa; 21sai dai ko a kan abu daya da na fada da babbar murya sa'adda na tsaya a gabansu, 'Wato batun tashin matattu wanda ake tuhumata ake neman yi mani hukunci yau.'"
22Filikus yana da cikakken sanin tafarkin Hanyar, shi yasa ya daga shari'ar. Yace da su, "Duk sa'anda Lisiyas mai ba da umarni ya zo daga Urushalima, zan yanke hukunci." 23Sa'annan ya umarci jarumin ya lura da Bulus, amma ya yi sassauci, kada ya hana abokansa su ziyarce shi ko su taimake shi.
24Bayan wadansu kwanaki, Filikus da mai dakinsa Druskila, ita Bayahudiya ce, ya kuma aika a kira Bulus ya saurare shi game da bangaskiya cikin Kristi Yesu. 25Amma sa'adda Bulus yake bayyana zancen adalci, kamunkai, da hukunci mai zuwa, Filikus ya firgita ya ce, "Yanzu ka tafi. Amma idan na sami zarafi an jima, zan sake neman ka."
26A wannan lokacin, yasa zuciya Bulus zai bashi kudi, yayi ta nemansa akai-akai domin yayi magana da shi. 27Bayan shekaru biyu, Borkiyas Festas ya zama gwamna bayan Filikus, domin neman farin jini a wurin Yahudawa, ya ci gaba da tsaron Bulus a gidan yari.


1Wasu tsoffin kwafi suna ƙarawa, Mun so mu shari'anta masa bisa ga dokarmu .

25

1Da Festas ya shiga lardin, kuma bayan kwana uku, ya tashi daga Kaisariya ya tafi Urushalima. 2Sai babban firist da manyan Yahudawa suka kawo wa Festas sara a kan Bulus. 3Suka roki tagomashi wurin Festas ya kira Bulus zuwa Urushalima domin su kashe shi a hanya.

4Amma Festas ya amsa masu cewa, Bulus dan sarka ne a Kaisariya, kuma ba da dadewa ba shi da kansa zai koma can. 5"Saboda haka duk wadanda za su iya, su biyo mu. Idan akwai wani laifi game da mutumin, sai ku zarge shi."
6Bayan kwana takwas ko goma, sai ya gangara zuwa Kaisariya. Washegari ya zauna bisa kursiyin shari'a ya bada umarni a kawo Bulus a gabansa. 7Da Bulus ya iso, Yahudawa daga Urushalima suka tsaya kusa, suka yi ta kawo kararraki, amma basu iya tabbatar da su ba. 8Bulus ya kare kansa ya ce, "Ban yi wa kowa laifi ba, ko Yahudawa, ko haikali, ko kuma Kaisar."
9Amma Festas yana neman farin jini wajen Yahudawa, sabo da haka ya tambayi Bulus ya ce, "Kana so ka je Urushalima in shari'anta ka a can game da wadannan abubuwa?" 10Bulus ya ce, "Ina tsaye a Ddakalin Shari'ar Kaisar inda dole a shari'anta ni. Ban yi wa Yahudawa laifi ba, kamar yadda ka sani sosai.
11Idan lallai na yi laifi kuma na yi abin da ya chanchanci mutuwa, ban ki ba in mutu. Amma idan zarginsu karya ne, kada kowa ya bashe ni gare su. Ina daukaka kara zuwa ga Kaisar." 12Bayan Festas ya tattauna da majalisa ya amsa ya ce, "Kana kira ga Kaisar; za ka tafi wurin Kaisar."
13Bayan wadansu kwanaki, sarki Agaribas da Barniki suka iso Kaisariya domin su ziyarci Festas. 14Da ya kasance kwanaki da yawa, Festas ya fada wa sarki labarin Bulus ya ce, "Akwai wani mutum dan sarka da Filikus ya bari a kurkuku. 15Sa'anda nake a Urushalima, babban firist da dattawan Yahudawa suka kawo kararsa gare ni, suka roka a kashe shi. 16Game da wannan na amsa na ce masu, ba al'adar Romawa ba ce a ba da mutum tagomashi; sai wanda ake kararsa an bashi zarafi ya kare kansa a gaban masu kararsa, ya kuma bada hujjojinsa game da kararakin.
17Saboda haka, da duk suka taru ban bata lokaci ba, washegari na zauna a kujerar shari'a, na ba da umarni a kawo mutumin. 18Da masu karar suka fadi kararsu, sai na fahimci karar ba wani muhimmin abu a cikinta. 19Sai dai na ga cewa jayayya ce tsakanin su ta addini a kan wani Yesu da ya mutu, wanda Bulus ya ce yana da rai. 20Na rasa yadda zan bincike wannan al'amarin, sai na tambaye shi ko zai je Urushalima a shari'anta shi kan wadannan abubuwa.
21Amma da Bulus ya nemi a lura da shi, Kaisar ya shari'anta shi, sai na ba da umarni a ajiye shi har sai na aika shi wurin Kaisar." 22Agaribas yace wa Festas. "Zan so ni ma in saurari mutumin nan." "Gobe za ka ji shi," in ji Fostus.
23Washegari Agaribas da Barniki suka zo tare da kasaitaccen taro suka shiga dakin taro tare da hafsoshi da shugabanin gari. Da Festas ya ba da umarni, aka fito da Bulus wurinsu. 24Festas ya ce, "Sarki Agaribas da dukanku da kuke tare da mu a nan, kun ga mutumin nan, dukan Yahudawa sun gana da ni a Urushalima da nan kuma. Suna mani ihu cewa, bai chanchanta a bar shi da rai ba.
25Na gane bai yi wani abin da ya chanchanci mutuwa ba; amma saboda ya daukaka kara zuwa Kaisar, na yanke shawara in aika shi. 26Amma ba ni da wani dalili na musamman da zan rubuta wasika ga Kaisar. Saboda wannan dalili na kawo shi gabanku, masamman kai ya sarki Agaribas. Domin in sami karin abin da zan rubuta game da shi. 27Gama a ganina wauta ce in aika dan sarka ba tare da na rubuta laifi a kansa ba."

26

1Sai Agaribas ya ce wa Bulus, "Za ka iya kare kan ka." Sai Bulus ya daga hannunsa ya fara kare kansa. 2"Ina farinciki, ya sarki Agaribas, game da saran da Yahudawa ke kawowa a kaina yau; 3musamman ma don kai masani ne game da al'adun Yahudawa da al'amuransu. Don haka, ina rokanka ka yi hakuri ka saurare ni.

4Hakika, dukan Yahudawa sun san yadda na yi rayuwa ta daga kurciyata a kasa ta, da kuma Urushalima. 5Sun san ni tun farko, kuma yakamata su yarda cewa na yi rayuwa kamar Bafarase, darikan nan mai tsatsauran ra'ayi ta addininmu.
6Yanzu ina tsaye a nan dominn a shari'anta ni, saboda alkawalin da Allah ya yi wa ubanninmu. 7Domin wannan shine alkawalin da kabilunmu goma sha biyu suka sa zuciya su karba, yayin da suke yin sujada da himma ga Allah dare da rana. Saboda wanan bege, Sarki Agaribas, Yahudawa ke tuhuma ta. 8Me ya sa wani zai yi tunani cewa abin mamaki ne Allah ya ta da mattatu?
9Da, na yi tunanin yin abubuwa gaba da sunan Yesu Banazarat. 10Na yi wadanan a Urshalima. Na kulle masu bi da yawa a kurkuku, sanadiyar iko da na samu daga wurin manyan firistoci, kuma da ake kashe su ma, ina ba da goyon baya. 11Na wahalshe su sau dayawa a cikin dukan majamiu ina kuma yin kokari in tilasta masu su yi sabo. Na yi gaba mai zafi da su kuma na tsananta masu har zuwa birane na wadansu kasashe.
12A sa'anda nake yin wannan, na tafi Dimashku da izinin manyan firistoci; 13a cikin tafiyata kuma, da tsakar rana, ya sarki, na ga haske daga sama da ya fi rana sheki, ya haskaka kewaye da ni da kuma wadanda ke tafiya tare da ni. 14Da dukanmu muka fadi kasa, na ji wata murya na magana da ni a harshen Ibraniyawa tana cewa, 'Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mani? Yana da wuya ka hauri abin da ke mai tsini.'
15Sai na ce, 'Wanene kai ya Ubangiji?' Ubangiji ya amsa, 'Ni ne Yesu wanda kake tsanantawa. 16Yanzu ka tashi tsaye domin saboda wannan dalili ne na bayyana gare ka in sanya ka, ka zama bawa da mashaidi na game da abubuwan da ka sani a kaina yanzu da wadanda zan bayyana maka daga bisani; 17Zan kubutar da kai daga wurin mutane da kuma al'ummai da zan aike ka wurinsu, 18domin ka bude idanunsu ka juyo su daga duhu zuwa haske da daga ikon Shaidan zuwa ga Allah, domin su karbi gafarar zunubai da gado da zan ba wadanda na kebe wa kaina ta wurin bangaskiya gare ni.'
19Saboda haka, sarki Agaribas, ban yi rashin biyayya da wahayin da na gani daga sama ba; 20amma, da farko ga wadanda ke a Dimashku, sa'annan a Urushalima da kasar Yahudiya gaba daya, da dukan Al'ummai, na yi wa'azi domin su tuba su kuma juyo ga Allah, su yi ayyukan da suka chanchanci tuba. 21Domin wannan dalili ne Yahudawa suka kama ni a cikin haikali kuma suke kokari su kashe ni.
22Allah ya taimake ni har wa yau, domin in iya tsayawa gaban mutane kanana da manya, in bada shaida game da iyakar abin da annabawa da Musa suka fada zai faru; 23wato lallai Almasihu zai sha wahala, ya kuma zama na farko da za'a rayar daga matattu ya kuma yi shelar haske zuwa ga mutanen Yahudawa da Al'ummai."
24Da Bulus ya gama kare kansa, Festas ya yi magana da babban murya, "Bulus, kana hauka; yawan iliminka yasa ka hauka." 25Amma Bulus ya ce, "Ba na hauka, ya mai girma Festas; amma da karfin zuciya nake fadi kalmomin gaskiya da na natsuwa. 26Saboda sarkin ya san wadannan abubuwa duka; shi ya sa nake magana gabagadi, don na hakikance cewa, ba abin da ke a boye gare shi; gama ba a yi wadannan abubuwa a boye ba.
27Ko ka gaskanta da annabawa, Sarki Agaribas? Na sani ka gaskanta." 28Agaribas ya ce wa Bulus, "A cikin karamin lokaci kana so ka rinjaye ni ka mai da ni Krista?" 29Bulus ya ce, "Ina roko ga Allah, domin ko a karamin lokaci ko a dogon lokaci, ba kai kadai ba, amma har da wadanda ke sauraro na yau su zama kamar ni, amma ban da wadannan sarkokin."
30Sai sarki ya tashi tsaye tare da gwamna da Barniki da dukan wadanda ke zaune tare da su; 31da suka bar dakin taron, suka ci gaba da magana da juna suna cewa, "Wannan mutum bai yi wani abin da ya chanchanci mutuwa ko kuma dauri ba." 32Agaribas ya ce wa Fastos, "Da mutumin nan bai daukaka kara zuwa ga Kaisar ba da an sake shi."

27

1Bayan da aka amince zamu tafi Italiya, sun mika Bulus tare da wadansu daurarru a hanun wani jarumi mai suna Yuliyas, daga batalian Agustas. 2Muka shiga Jirgin ruwa daga Adramatiya, wanda ke shirin tashi zuwa kusa da gefen tekun Asiya. Sai muka je teku. Aristakus mutumin Tasalonika a Makidoniya ya tafi tare damu.

3Washegari muka sauka birnin Sidon, inda Yuliyas ya nuna wa Bulus karamci ya kuma yarda abokansa su bi shi don ya kula da su. 4Daga wurin, muka bi teku muka tafi ta Tsibirin Kubrus, domin matsananciyar iska da ke gaba damu. 5Sa'adda muka ketare ruwa zuwa sassan Kilikiya da Bamfiliya, muka zo Mira ta birnin Lisiya. 6Anan, jarumin ya sami jirgin ruwa daga Iskandariya wanda za shi Italiya. Ya samu cikinsa.
7Kwana da kwanaki muna tafiya a hankali a karshe da kyar muka sauka kusa da Sinidus, iska ta hana mu tafiya, sai muka ratsa ta Karita, kusa da Salmina. 8Da wahala muka bi ta makurda har muka zo wani wuri da ake kira Mafaka Mai Kyau wanda ke kusa da birnin Lasiya.
9Yanzu mun dauki dogon lokaci, gashi lokacin azumin Yahudawa ya wuce, tafiyar kuma ta zama da hatsari. Bulus ya gargade su, 10ya ce, "Jama'a, na gane tafiyarmu zata zamar mana da barna da asara mai yawa, ba ga kaya da jirgin kadai ba amma har da rayukan mu." 11Amma jarumin ya fi mai da hankali ga maganar shugabansa da mai jirgin ruwan, fiye da abubuwan da Bulus ya fadi.
12Da shike tashar ba za ta yi dadin zama da hunturu ba, mafi yawa sun ba da shawara a bar wurin, in maiyiwuwa ne muga mun kai birnin Finikiya, don mu yi hunturu a can. Finikiya tashar jirgin ruwa ce a Karita, tana fuskantar arewa maso gabas da kudu maso gabas. 13Sa'adda iska daga kudu ta huro a hankali, sun tsammaci bukatarsu ta biya. Sai suka janye linzamin jirgin ruwan sukabi ta Karita kusa da gaba.
14Amma bayan wani dan lokaci sai iska mai karfi da ake kira Yurokilidon, ta fara bugun mu daga tsibirin. 15Sa'adda Jirgin ruwan ya kasa fuskantar iskar, sai muka bi inda iskar ta nufa. 16Sai muka bi ta inda muka sami kariya kusa da wani dan tsibiri wanda ake kira Kauda; kuma da wahala muka daure karamin jirgin a jikin babban.
17Bayanda suka daga shi, sun yi amfani da igiyoyi don su daure jirgin don gudun fadawa kan yashin Sirtis, suka bar jirgin yana ta korarsu. 18Mun yi ta fama da hadari ba kadan ba, da gari ya waye ma'aikatan jirgin suka fara zubar da kaya daga jirgin.
19A rana ta uku, ma'aikatan jirgi suka jefar da kaya daga cikin jirgin da hannuwansu. 20Kwanaki dayawa ba mu ga hasken rana da taurari a bisan mu ba. Babban hadari kadai ke dukanmu, duk mun fidda zuciya zamu tsira.
21Sa'adda sun dade basu ci abinci ba, sai Bulus ya tashi a gaban ma'aikatan jirgi yace, "Jama'a, da kun saurare ni, da bamu tashi daga Karita ba, balle mu fuskanci wannan barna da asarar. 22Yanzu fa ina karfafa ku kuyi karfin hali, domin ba wanda zai rasa ransa a cikinku, sai dai jirgin kadai za a rasa.
23Domin daren da ya gabata mala'ikan Allah wanda ni nasa ne, wanda kuma nake bautawa -mala'ikansa ya tsaya kusa dani 24ya ce, "Kada ka ji tsoro, Bulus, dole ka tsaya gaban Kaisar, duba kuma, Allah cikin jinkansa ya baka dukan wadannan da ke tafiya tare da kai. 25Domin haka, jama'a, kuyi karfin hali, domin na gaskanta da Allah, kamar yadda aka fada mani haka zai faru. 26Amma lallai dole ne a jefa mu kan wani tsibiri".
27Sa'adda dare na goma sha hudu ya yi, ana ta tura mu nan da can a cikin tekun Adriyat, wajen tsakar dare, ma'aikatan jirgin sun tsammaci sun kusanci wata kasa. 28Da suka gwada sai suka iske kamu ashirin; bayan dan lokaci kadan, sun sake aunawa sai suka iske kamu sha biyar ne. 29Tsoro ya kama su ko watakila a jefar da mu kan duwatsu, sai suka jefa linzami hudu daga karshen jirgin suka yi addu'a don gari ya waye da sauri.
30Ma'aikatan jirgin ruwan suna neman hanyar da za su rabu da jirgin kuma sun jefa karamin jirgin a cikin teku. Suka yi kamar zasu jefa wasu linzamai daga gaban jirgin. 31Amma Bulus ya ce ma jarumi da sojojin, "Idan mutanen nan ba zasu tsaya cikin jirgin ba, ba zaku tsira ba". 32Sai sojojin suka yanke igiyoyin jirgin suka kuma barshi ya fadi.
33Da gari ya fara wayewa, Bulus ya roke su duka su dan ci abinci, ya ce, "Yau kwana goma sha hudu kenan ba ku ci kome ba. 34Saboda haka na roke ku ku ci abinci, domin wannan saboda lafiyarku ne; kuma ko gashin kanku daya baza ku rasa ba". 35Da ya fadi haka sai ya dauki gurasa ya yi godiya ga Allah a idanun kowa. Sai ya gutsutsura gurasa ya fara ci.
36Sai dukansu suka karfafu suka kuma ci abinci. 37Mu mutane 276 (dari biyu da saba'in da shida) ne cikin jirgin. 38Da suka ci suka koshi, suka zubar da alkamar cikin teku domin su rage nauyin jirgin.
39Da gari ya waye, basu fahimci kasar ba, amma suka hangi wani lungu a gacci, sai suka yi shawara tsakaninsu ko su tuka jirgin zuwa cikin lungun. 40Sai suka yanke linzaman suka bar su cikin tekun. Cikin lokaci guda suka kwance igiyoyin da ke juya jirgin, suka saki filafilan goshin jirgi suka nufi gabar tekun. 41Da suka iso inda ruwa biyu suka hadu, sai jirgin ya tsaya kasa. Gaban jirgin ya kafe a nan, ba damar matsawa, sai kuma kurar jirgin ta fara kakkaryewa saboda haukan rakuman ruwa.
42Shirin sojojin ne su kashe 'yan kurkukun domin kada su yi iyo su tsere. 43Amma shi hafsan ya so ya ceci Bulus, sai ya tsai da shirin su, ya ba da umarni, duk masu iya iyo su yi tsalle su fada ruwa su kai gacci. 44Sa'annan sauran mazajen su biyo baya, wadansu a kan karyayyun katakai, wadansu akan abubuwan da ke a jirgin. Ta haka ne dukanmu muka kai gacci lafiya.

28

1Sa'adda muka sauka lafiya, sai muka ji cewa sunan tsibirin Malita. 2Mutanen garin sun nuna mana alheri matuka don sun hura wuta don mu ji dimi, saboda ruwan sama da sanyin da ake yi.

3Amma sa'adda Bulus ya tara kiraruwa don hura wuta, sai maciji saboda zafin wuta, ya fito ya nade hannuwansa. 4Da mazaunan garin suka ga maciji ya nade hannuwansa, sai suka cema junansu, "Ba shakka wannan mutumin mai kisan kai ne, koda shike ya tsira daga Teku, sharia baza ta barshi da rai ba".
5Amma ya karkade macijin cikin wuta ba tare da ya cutar da shi ba. 6Sun saurara su gani ko zai kumbura ko ya fadi matacce. Amma da suka jira dan lokaci basu ga wata matsala ta same shi ba sai suka canza tunaninsu sukace shi wani allah ne.
7A kusa da wannan wurin tsibirin akwai wasu gonakin wani babban mutumin tsibirin, mai suna Babiliyas. Ya karbe mu ya biya bukatun mu har kwana uku. 8Ana nan ashe mahaifin Babiliyas yana fama da zazzabi da atuni. Bulus ya shiga, yayi masa addu'a, ya dibiya masa hannu, ya sami warkarwa. 9Sa'adda wannan ya faru, sauran marasa lafiya da ke tsibirin sun zo sun sami warkarwa. 10Mutanen sun mutunta mu kwarai. Yayin da muke shirin tafiya, sun bamu duk abinda muke bukata.
11Bayan watanni uku, mun shiga jirgin Iskandariya wanda tun da hunturu yake a tsibirin mai zane kamannin Tagwaye Maza. 12Bayan saukar mu a birnin Sirakus, mun yi kwana uku a wurin.
13Daga nan sai muka tafi, har muka zo birnin Rigiyum. Bayan kwana daya iska mai karfi daga kudu ta taso, a cikin kwana biyu muka iso Butiyoli. 14A can muka iske wasu 'yan'uwa suka roke mu mu zauna tare da su har kwana bakwai. Ta wannan hanyar ce muka zo Roma. 15Daga can da 'yan'uwa suka ji labarin mu, suka fito don su tarbe mu tun daga Kasuwar Abiyas da kuma Rumfuna Uku. Da Bulus ya gan su, ya yi wa Allah godiya ya kuma sami karfafawa.
16Sa'adda muka shiga Roma, aka yardar wa Bulus ya zauna shi kadai tare da sojan da ke tsaronsa. 17Ana nan bayan kwana uku, Bulus ya kira shugabannin Yahudawa. Bayan da suka taru, sai ya ce masu, "Yan'uwa, ko da shike ban yi wa kowa laifi ko keta al'adun Ubanninmu ba, duk da haka an bashe ni daurarre tun daga Urushalima zuwa ga hannunwan mutanen Roma. 18Bayan tuhumata, sun yi kudirin saki na, domin ban yi laifin da ya cancanci mutuwa ba.
19Amma da Yahudawa suka tsaya a kan ra'ayin su, ya zama dole in daukaka kara zuwa ga Kaisar, ba domin ina da wani dalilin da zan yi karar al'ummata ba ne. 20Saboda wannan ne na bukaci ganinku in yi magana da ku. Saboda begen da Isra'ila suke da shi ya sa nake daure da wannan sarkar".
21Sai suka ce masa, "Bamu karbi wasiku daga Yahudiya game da kai ba, babu kuma wani daga cikin 'yan'uwa wanda ya kawo mana wani rahoto ko wata magana game da kai. 22Amma muna so mu ji daga gare ka abin da kayi tunani ka kuma gani game da wannan darikar, gama mun sani ana kushenta a ko'ina."
23Sa'adda suka sa masa rana, mutane da dama suka same shi a masaukinsa. Ya gabatarda zantattukan a gare su, yana tabbatar da bayyanuwar mulkin Allah. Har ya nemi ya rinjaye su a kan zancen Yesu, tun daga attaurat ta Musa zuwa litattafan annabawa, ya yi wannan tun daga safiya har yamma. 24Wasu sun kawar da shakkar abin da aka fada, amma wadansu basu gaskanta ba.
25Da shike ba su yarda da junansu ba, sai suka tafi bayan da Bulus ya fadi kalma daya, "Ruhu Mai Tsarki ya yi magana ta bakin annabi Ishaya zuwa ga kakanninku. 26Ya ce, 'Jeka wurin al'umman nan ka ce, cikin ji zaku ji amma ba zaku fahimta ba; zaku gani amma ba zaku gane ba.
27Amma zuciyar mutanen nan ta yi kanta, kunnuwansu sun ji da kyar, sun rufe idanunsu; don kada su gani su gane, su kuma ji da kunuwansu, kuma su fahimta da zuciyarsu, domin su juyo ni kuma in warkar da su."
28Saboda haka, sai ku sani cewa wannan ceto na Allah an aikar da shi zuwa ga Al'ummai, za su kuma saurara." 291
30Bulus ya zauna shekaru biyu a cikin gidan hayarsa, yana marabtar duk wadanda suka zo wurinsa. 31Yana wa'azin mulkin Allah, yana koyarwa da al'amuran Ubangiji Yesu Kristi gaba gadi. Ba wanda ya hana shi.


1Ayyukan Manzanni 28: 29 - Wasu tsoffin kwafi suna da aya ta 29: Sa'adda ya fadi wannan zantattuka, Yahudawa suka tashi, suna gardama da junansu .

Romawa

1

1Bulus, bawan Yesu Almasihu, kirayayye ya zama manzo, kuma kebabbe domin bisharar Allah. 2Wannan itace bisharar da ya alkawarta tuntuni ta wurin annabawansa ta wurin tsarkakakkun littattafan sa. 3Game da Dansa ne, haifaffe daga zuriyar Dauda ga zancen jiki.

4Ta wurin tashinsa daga mattatu aka aiyana shi ya zama Dan Allah ta wurin ikon Ruhu na tsarkakewa. Yesu Almasihu Ubangijimu. 5Ta wurinsa muka karbi alheri da manzanci sabo da biyayyar imani a cikin dukkan al'ummai, domin darajar sunansa. 6cikin wadannan al'ummai kwa, ku ma an kiraku ku zama na Yesu Almasihu.
7Wannan wasika ga dukkanku ne da kuke cikin Roma, kaunatattu na Allah, kirayayyun mutane tsarkakakku. Bari alheri ya kasance tare daku, da salama daga Allah Ubanmu, da kuma Ubangiji Yesu Almasihu.
8Abu na farko dai ina yi wa Allah na godiya ta wurin Yesu Almasihu domin ku duka, domin kuwa ana labarta bangaskiyarku ko ina a cikin dukkan duniya. 9Domin kuwa Allah shi ne shaida ta, wanda nake bautawa a cikin ruhuna a cikin bisharar Dansa, yadda a koyaushe na ke ambaton ku. 10A kullum ina roko cikin addu'o'ina domin ta kowanne hali in yi nasarar zuwa gare ku da izinin Allah.
11Gama ina marmarin ganin ku, domin in baku wata baiwa ta ruhaniya, domin in karfafa ku. 12Wato ina dokin in sami cikakkiyar karfafawa a cikin ku, ta wurin bangaskiyar junanmu, wato tawa da taku.
13Yanzu fa bana so ku rasa sani, yan'uwa, sau da yawa nake yin niyyar zuwa wurinku, amma har yanzu hakan din bata samu ba. Na so yin hakan din ne don in sami 'ya'ya na ruhu a cikinku kamar dai yadda ya ke a sauran Al'ummai. 14Ina dauke da nawayar Hellinawa da ta sauran jama'a, masu hikima da marasa hikima. 15Don a shirye na ke in sanar da bishara a gare ku, ku da kuke cikin Roma.
16Don kuwa ni ba na jin kunyar yin bishara, don ita ce ikon Allah don samun ceto ga duk wanda ya gaskata, da farko dai Yahudawa kana kuma Hellinawa,17Domin a cikin ta adalcin Allah ya bayyana daga bangaskiy zuwa bangaskiya, kamar yadda yake a rubuce, "Mai adalci zai rayu ne tawurin bangaskiya."
18Domin fushin Allah ya bayyana ne daga sama gaba da rashin ibada da rashin adalci na yan'adam, wadanda suke danne gaskiya ta wurin rashin adalcin su. 19Dalili kuwa abinda yakamata a sani game da Allah a bayyane ya ke a gare su. Domin kuwa Allah ya bayyana masu shi a zahiri.
20Domin al'amuransa da ba'a iya gani a bayyane suke tun halittar duniya. A na iya gane su ta wurin halitatattun abubuwa. Wadannan al'amura kuwa sune madawwamin ikonsa da Allahntakarsa. Sakamakon haka, wadannan mutane ba su da hujja. 21Dalili kuwa, koda suna jin sun san Allah, amma basu darajanta shi a matsayin Allah ba, ko kuma su nuna masa godiya. Maimakon haka, suka zama wawaye a cikin tunaninsu, zukatansu marasa tunani sun duhunta.
22Suna daukar kansu akan masu hikima ne su, amma sai ga su sun zama wawaye. 23Sun musanya daukakar Allah madawwami da ta kamannin abubuwan da basa dawwama, kamar mutum, da tsuntsaye, da dabbobi masu kafafu hurhudu, da masu jan ciki.
24Saboda haka Allah ya bashe su ga sha'awoyin kazantar zukatansu, su wulakantar da jukunansu a junansu. 25Sune suka musanya gaskiyar Allah da karya, Kuma suke sujada da bauta ga halittaccen abu, maimakon Mahaliccin, Wanda yake abin yabo har abada. Amin.
26Saboda haka Allah ya bashe su, ga sha'awowin su na lalata da wulakanci, har matansu suka canza ka'idar jima'i da aka saba zuwa madigo mace da mace. 27Mazajensu ma suka sauya ka'idar jima'i tsakanin mace da miji zuwa namiji da namiji suna yin aikin lalata. Maza su na kwana da maza suna aikata aikin ban kyama, suna kuwa girbe sakamakon aiknsu na ban kyama.
28Tunda shike ba su amince da Allah a cikkin al'amuransu ba, Allah ya bashe su ga bataccen hankalinsu, su aikata wadannan munanan abubuwa.
29Suna cike da dukkan rashin adalci, mugunta, kyashi, keta, kuma cike da kishi, kisan kai, tarzoma, makirci, da kuma munanan manufafofi. 30Masu gulma da kage, makiyan Allah. Masu tada zaune tsaye, masu taurin kai, da ruba, masu kaga kowadanne miyagun abubuwa, kuma masu kin yin biyayya ga iyayensu. 31Masu duhun zuciya; masu cin amana, marasa soyayya, da kuma rashin tausayi.
32Suna sane da tsarin Allah cewa masu yin irin wadannan al'amura sun cancanci hukuncin mutuwa. Ba kuwa yin wadannan abubuwan ka dai suke yi ba, harma goyon bayan masu yinsu suke yi.

2

1Saboda da haka baka da hujja, kai mutum, kai mai shara'antawa, domin kuwa abinda kake shara'antawa akan wasu kana kada kanka da kanka. Domin kuwa kai mai shar'antaawa kana aikata wadannan abubuwa. 2Amma mun san cewa shari'ar Allah ta gaskiya ce sa'adda zata fado wa masu aikata wadannan irin abubuwa.

3Amma ka lura da wannan, ya kai mutum, mai shara'anta masu aikata wadannan ababuwa. Duk da shike kaima kana aikatawa. Kana jin zaka kubucewa hukuncin Allah? 4Ko kana raina falalar alheransa da yake yi ta wajen jinkirin hukuncinsa, da hakurinsa? Baka san cewa alheransa musanman domin su kai ka ga tuba bane?
5Amma saboda taurin kanka da zuciyarka marar tuba, kana tanadarwa kanka fushi, a ranar fushi, wato ranar bayyanuwar shari'ar adalci ta Allah. 6Zai baiwa kowanne mutum daidai sakamakon ayyukansa: 7Ga wadanda kuma suka nace da yin ayyukan alheri ba fasawa, sun samarwa kansu, yabo da daraja, da rai na har'abada.
8Amma ga masu son kai, wadanda suka ki yin biyayya ga gaskiya, suka yiwa rashin adalci biyayya, fushi da hasala mai zafi zai afko masu. 9Allah kuma zai sauko da bala'i da bakin ciki ga dukkan rayukan da suka aikata mugunta, ga Yahudawa da fari, sannan kuma Hellinawa.
10Amma yabo daraja da salama zasu kasance ga dukkan wadanda suka aikata ayukan alheri, ga Yahudawa da fari sannan Hellanawa. 11Domin kuwa Allah ba mai tara bane. 12Ga wadanda suka yi zunubi batare da shari'aba, zasu hallaka ba tare da shari'a ba, ga wadanda suka yi zunubi cikin shari'a kuma za'a hukunta su bisa ga shari'a.
13Domin kuwa ba masu jin shari'ar ne masu adalci agaban Allah ba, amma masu aikatawa ne zasu samu barata. 14Gama al'umai da basu san shari'a ba, bisa ga dabi'a sun yi abinda ke na shari'a, sun kuma zame wa kansu shari'a, koda shike basu da shari'ar.
15Dalilin haka kuwa sun nuna cewa ayukan da shari'a take bukata na nan a rubuce a zuciyarsu. lamirinsu kuma na yi masu shaida, tunanainsu kuma, ko dai yana kashe su, ko kuma yana karesu. 16hakanan kuma ga Allah. Wannan zai faru ranar da Allah zai shara'anta asiran boye na dukkan mutane, bisa ga bishara ta cikin Yesu Almasihu.
17Da shike kana kiran kanka Bayahude, kana zaune akan shari'a, kana alfahari cikin Allah, 18ka san nufinsa, ka kuma san abubuwan da suka bambanta da hakan, ka kuma sami koyarwa cikin shari'ar. 19Da shike kana da gabagadi akan cewa kai jagora ne ga makafi, haske ga wadanda suke cikin duhu, 20mai horo ga marasa hikima, mai koyar da jarirai, kuma a cikin shari'ar kana da abin da ya shafi sani da kuma gaskiya.
21ku da kuke koyar da wadansu, ba ku koyar da kanku? ku da kuke wa'azi kada ayi sata, ba ku yin sata? 22Ku da ke wa'azi kada ayi zina, ba ku yin zina? ku da ke hana bautar gumaka, ba ku yin sata a haikali?
23ku masu murna da tinkaho cikin shari'ar, ba kwa wulakanta Allah cikin kurakuranku na rashin bin shari'a? 24"Domin kuwa an wulakanta sunan Allah cikin Al'umai sabili da ku," kamar yadda aka riga aka rubuta.
25Lallai kuwa kaciya tana da riba a gare ku, idan kuka kiyaye doka, amma idan ku marasa bin doka ne kaciyarku ta zama rashin kaciya. 26domin kuwa idan mutum marar kaciya zai kiyaye dukkan bukatun doka, baza'a iya daukan rashin kaciyarsa a matsayin mai kaciya ba? 27Sannan idan mutum marar kaciya ta jini zai kiyaye dukkan dokoki, ba zai iya shara'anta ku masu kaciya ta shari'a ba? Haka kuma ya kasance ne domin kuna da shari'a a rubuce da kuma kaciya amma ba kwa bin doka!
28Domin shi kuwa ba Bayahude bane a waje; ba kuwa mai kaciyar da aka tsaga fata ba. 29Amma Bayahude ne ta ciki, sanna kuma mai kaciyar zuciya da kuma ruhu ba wasika ba, irin wanna mutumin yabonsa ba daga wurin mutane yake zuwa ba, amma daga Allah.

3

1To ina fifikon da bayahude yake dashi? Kuma ina ribar kaciya? 2Akwai muhimmancinsu ta kowacce hanya. Tun farko dai, yahudawa ne aka dankawa wahayi daga Allah.

3Idan wasu yahudawa basu bada gaskiya ba fa? Rashin bangaskiyarsu zai hana amincin Allah aiki? 4Bazai taba zama haka ba. Maimakon haka, bari Allah ya zama mai gaskiya, ko da kowanne mutum makaryaci ne. Kamar yadda aka rubuta, "Domin a nuna kai mai adalci cikin maganganunka, kuma kayi nasara a lokacin da aka kawo ka gaban shari'a."
5Amma idan rashin adalcinmu ya nuna adalcin Allah, to me zamu ce? Allah ba marar adalci ba ne, wanda ke aiwatar da fushinsa, ko kuwa? Ina magana bisa ga tunanin mutuntaka. 6Bazai taba zama haka ba. Domin idan haka ne ta yaya Allah zai shar'anta duniya?
7Amma idan gaskiyar Allah ta wurin karyata ta habaka yabonsa, To me yasa ake shar'anta ni a matsayin mai zunubi? 8To me zai hana ace kamar yadda ake fadin zancen karya a kanmu, wasu kuma sun dauka cewa mun fadi hakan, "Bari muyi mugunta, domin nagarta tazo?" Hukuncin su halal ne.
9To me kenan? Zamu ba kanmu hujja ne? ko kadan. Domin mun riga munyi zargin yahudawa da hellinawa, da cewar dukkansu, suna karkashin zunubi. 10Kamar yadda aka rubuta, babu wani mai adalci, babu ko daya.
11Babu wani mai fahimta. Babu wani mai neman Allah. 12Dukansu sun kauce hanya, dukansu gaba daya sun zama marasa amfani. Babu mai aikin nagarta, a'a, babu ko da guda daya.
13Makogwaronsu a bude yake kamar kabari. Harsunansu na dauke da cuta. Dafin macizai na karkashin lebunansu. 14Bakunansu cike suke da la'ana da daci.
15Sawayensu na saurin zuwa zubar da jini. 16Tafarkinsu wahala ce da lalacewa. 17Wadannan mutane basu san hanyar salama ba. 18Babu tsoron Allah a idanunsu."
19To mun san dai duk abin da shari'a tace, shari'a na magana ne da wadanda ke karkashinta, domin a rufe kowanne baki, domin dukan duniya ta bada amsa a gaban Allah. 20Domin a gabansa babu wanda zai barata ta wurin ayukan shari'a. Domin ta wurin shari'a ne sanin zunubi yazo.
21Amma yanzu ba tare da shari'a ba an bayyana sanin adalcin Allah, wanda shari'a da annabawa suke shaidawa. 22Wato, adalcin Allah ta wurin bangaskiya cikin Yesu Almasihu ga dukkan wadanda ke bada gaskiya. Domin babu bambanci:
23Domin duk sun yi zunubi sun kuma kasa kaiwa ga darajar Allah, 24Da alherinsa an baratar da mu ta wurin fansar dake cikin Yesu Almasihu.
25Amma Allah ya bayar da Yesu Almasihu wanda yake hadayar fansa ta wurin bangaskiya cikin jininsa. Ya mika Almasihu a matsayin tabbacin hukuncinsa, sabo da kuma ketarewar zunubanmu na baya 26cikin hakurinsa. Duk wannan ya faru ne domin a bayyana adalcinsa cikin wannan zamani, domin ya tabbatar da kansa mai hukunci, kuma ya nuna shine mai baratar da kowa saboda bangaskiya cikin Yesu.
27To ina fahariya? An fitar da ita. A kan wane dalilin? Don ayyuka? A'a, amma ta dalilin bangaskiya. 28Domin wannan muka kammala cewar ana baratar da mutum ta wurin bangaskiya ba tare da ayyukan shari'a ba.
29Ko kuwa Allah Allahn yahudawa ne kadai? Shi ba Allahn al'ummai bane? I, na al'ummai ne kuma. 30Idan dai lallai Allah daya ne, zai baratar da mai kaciya ta wurin bangaskiya, da marar kaciya kuma ta wurin bangaskiya.
31Mun kawar da shari'a kenan ta wurin bangaskiya? ba zai taba kasancewa haka ba. Maimako ma, muna inganta shari'a kenan.

4

1Me kenan zamu ce game da Ibrahim, kakanmu a jiki, me ya samu? 2Domin idan Ibrahim ya sami kubutarwa ta wurin ayuka, ai da ya sami dalilin fahariya, amma ba a gaban Allah ba. 3Kuma fa me nassi ke fadi? "Ibrahim ya bada gaskiya ga Allah, sai aka lisafta ta adalci gare shi."

4Yanzu fa shi dake yin ayyuka, ladansa ba a lisafta shi alheri ba ne, amma abun da ke nasa. 5Amma kuma shi da bai da ayyuka kuma maimakon haka ya gaskanta ga wanda ke kubutar da masu zunubai, bangaskiyarsa an lisafta ta a misalin adalci.
6Dauda ya yi furcin albarka bisa mutumin da Allah ya lisafta mai adalci da rashin ayyuka. 7Sai ya ce, "Masu albarka ne wadanda aka yafe laifofinsu, kuma wadanda zunubansu a rufe suke. 8Mai albarka ne mutumin da ko kadan Ubangiji ba zaya lisafta zunubin sa ba."
9To albarkar da aka fadi ko a bisansu wadanda aka yi wa kaciya ne kadai, ko kuwa a bisan su ma marasa kaciya? Domin mun yi furcin, "Bangaskiyar Ibrahim an lisafta ta adalci ce agare shi." 10Yaya aka lisafta ta? Bayan Ibrahim ya yi kaciya, ko kuwa a rashin kaciya? Ba a cikin kaciya ba, amma a rashin kaciya.
11Ibrahim ya amshi alamar kaciya. Wannan shi ne hatimin adalcin bangaskiyar da ya ke da ita tun cikin rashin kaciyarsa. Albarkacin wannan alama ce, ta sa shi ya zama uban dukkan wadanda suka badagaskiya, ko da shike ba su da kaciya. Wato ma'ana, adalci za a lisafta masu. 12Wannan kuma yana da ma'anar cewa Ibrahim ya zama uban kaciya ga wadanda suka fito ba domin masu kaciya kadai ba, amma kuma domin wadanda ke biyo matakin ubanmu Ibrahim. Kuma wannan itace bangaskiyar da ya ke da ita a rashin kaciya.
13Domin ba ta wurin shari'a aka bada alkawarin nan da aka yi wa Ibrahim da zuriyarsa ba, wannan alkawarin da ya ce zasu gaji duniya. Maimako, a ta wurin adalcin bangaskiya ne. 14Domin idan su da ke na shari'a magada ne, bangaskiya bata da komai, kuma alkawarin an wofintar da shi kenan. 15Domin shari'a ta kan jawo fushi, amma ta wurin rashin shari'a, babu karya umarni.
16Saboda wannan dalili haka ta faru ta wurin bangaskiya, domin ya zama bisa ga alheri. Kamar haka, alkawarin ya tabbata ga dukkan zuriya. Kuma wannan zuriya ba zata kunshi wadanda suke da sanin shari'a ba kadai, har ma da wadanda ke daga bangaskiyar Ibrahim. Saboda shi ne uban dukkan kowa, 17kamar yadda aka rubuta, "Na maishe ka uba ga kasashe masu yawa." Ibrahim na gaban aminin sa, wato, Allah, mai bada rai ga mattatu kuma ya kan kira abubuwan da basu da rai su kuma kasance.
18Duk da halin da ke a bayyane, Ibrahim ya gaskata ga Allah kai tsaye game da abubuwan da ke nan gaba. Sai ya zama uba ga kasashe masu yawa, kamar yadda aka ambata, "... Haka zuriyarka zata kasance." 19Ba ya karaya a bangaskiya ba. Ibrahim ya yarda da cewa jikinsa ya rigaya ya tsufa (shekarun sa na misalin dari). Ya kuma yarda da cewa mahaifar Saratu bata iya bada 'ya'ya ba.
20Amma domin alkawarin Allah, Ibrahim bai ji nauyin rashin bangaskiya ba. Maimakon haka, ya sami karfafawa a bangaskiyarsa sai ya daukaka Allah. 21Ya na da cikakkiyar gamsuwa cewa idan Allah ya yi alkawari, shi mai iya kammalawa ne. 22Haka nan ne kuma aka lisafta masa wannan a matsayin adalci.
23To ba'a rubuta kawai damin amfaninsa kadai ba, da aka lisafta dominsa. 24A rubuce yake domin mu, domin wadanda za'a lisafta su, mu da muka bada gaskiya gare shi wanda ya tada Yesu Ubangijinmu daga matattu. 25Wannan shi ne wanda aka bashe shi domin zunubanmu kuma an tada shi saboda fasar mu.

5

1Tun da shike mun sami barata, sabili da bangaskiya, mun sami salama tare da Allah ta wurin Yesu Almasihu. 2. Ta wurin sa kuma mun sami iso zuwa ga alheri inda muke tsayawa albarkacin bangaskiyarmu. Muna murna da gabagadin da Allah ya ba mu game da abin da zai faru, gabagadin da zamu dandana nan gaba cikin daukakar Allah.

3Ba kuwa haka kadai ba, amma muna murna da shan wahalolinmu. Mun san cewa shan wuya na haifar da 4Jimiri, Jimiri kuma na kawo amincewa, amincewa na kawo gabagadi game da abin da zai zo nan gaba. 5Wannan gabagadi wato begen da muke da shi baya kunyatarwa, domin kuwa an kwarara mana kaunar Allah a cikin zuciyarmu ta wurin Ruhu Mai Tsarki, da aka ba mu.
6Domin kuwa ko yayin da muke raunana, Almasihu ya mutu a lokacin da ke dai dai domin marasa ibada.7To ai kuwa yana da wuya kwarai wani mutum ya yarda ya mutu don mutumin kirki ma. Watakila, wani na iyayin kasada ya yarda ya mutu don nagarin mutum.
8Amma Allah ya tabbatar mana da kaunarsa a gare mu, don kuwa tun muna masu zunubi, Almasihu ya mutu domin mu. 9Balle ma yanzu, da muka barata ta wurin jininsa, za mu sami tsira daga fushin Allah.
10Domin kuwa, in tun muna makiya, aka sulhunta mu da Allah ta wurin mutuwar Dansa, balle ma, yanzu da muka sami sulhu, zamu sami tsira ta wurin ransa.11Bama haka kadai ba, amma muna murna a cikin Allah ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu, wanda ta wurinsa ne muka sami wannan sulhu.
12Saboda haka, kamar yadda ta wurin mutum daya zunubi ya shigo cikin duniya, ta haka mutuwa ta shigo ta dalilin zunubi. 13Domin kuwa tun kafin a bada shari'a, zunubi na nan a duniya, amma ba' a lissafin zunubi in da ba shari'a.
14Duk da haka, mutuwa ta mallake tun daga Adamu har Musa, har ma wadanda basu yi zunubin keta umarni irin na Adamu ba, wanda yake misalin mai zuwan nan a gaba. 15Amma kyautar ba kamar keta umarnin take ba. Domin in sabo da laifin mutum dayan nan ne, da yawa suke mutuwa, haka ma alherin sa da baiwarsa ta wurin mutum dayan nan, Yesu Almasihu, sai baiwar ta wadata zuwa ga masu yawa.
16Domin kyautar ba kamar sakamakon wannan da yayi zunubin bace. Ta haka din nan ne, hukuncin nan mai tsanani ya zo sabo da zunubin mutum dayan. Har yanzu dai, wannan baiwa ta yanci ta zo ne bayan laifuffuka masu yawa. 17Domin, idan sabo da laifin mutum dayan nan ne, mutuwa ta mallake, saboda dayan, haka ma wadanda suka karbi alheri mai yawa da kuma baiwar adalci ta wurin ran, Yesu Almasihu.
18Don haka, kamar yadda zunubin dayan ya sa hukunci ya zo kan dukka, haka ma aikin adalci na dayan zai kawo barata da rai ga mutane masu yawa.19Kuma kamar yadda rashin biyayyar dayan ta sa mutane masu yawan gaske su zama masu zunubi, haka ma ta biyayyar dayan mutane da yawan gaske za su sami adalci.
20Amma shari'a ta zo, inda ta sa zunubi ya habaka. Amma inda zunubi ya habaka, alheri ma ya habaka ribin ribi. 21Wannan ya faru ne, don kamar yadda zunubi yai mallaka zuwa mutuwa, haka kuma alheri ya mallaka zuwa adalci da rai na har abada ta wurin Yesu Almasihu Ubangijin mu.

6

1Me kuwa zamu ce yanzu? Sai mu ci gaba da yin zunubi domin Alheri ya yawaita? 2Ba zai taba faruwa ba. 'Yaya za'ace mu da muka mutu cikin zunubi mu ci gaba da rayuwa cikin sa? 3Ba ku san cewa duk wadanda aka yi masu baftisma cikin Almasihu Yesu an yi masu baftisma har ya zuwa mutuwarsa ne ba?

4An kuwa binne mu tare da shi, ta wurin baftisma cikin mutuwarsa. Haka kuma ya kasance ne domin kamar yadda Almasihu ya tashi daga matattu cikin daukakar Uba. Sakamakon haka muma zamu yi tafiya cikin sabuwar rayuwa. 5Domin kuwa idan muna tare dashi cikin kamannin mutuwarsa zamu kuwa zauna tare dashi har ga kamannin tashinsa.
6Mun kuma san cewa, an giciye wannan tsohon mutunmin nan namu tare dashi, domin a hallaka jikin zunubi. wanna kuwa ya kasance ne domin kada mu ci gaba da bautar zunubi. 7Duk kuma wanda ya mutu an ambace shi a matayin adali akan zunubi.
8Amma idan muka mutu tare da Almasihu, mun bada gaskiya zamu yi rayuwa tare dashi. 9Muna da sanen cewa an tada Almasihu daga matattu, don haka kuwa ba matacce yake ba. Mutuwa kuma bata da iko a kansa.
10Game da mutuwar da yayi ga zunubi yayi sau daya kuma domin dukka. Rayuwar da yake yi kuma yana yi wa Allah ne. 11Don haka ku ma sai ku dauki kanku a matsayin matattu ga zunubi amma rayayyu ga Allah cikin Almasihu Yesu.
12Sabili da haka kada ku bar zunubi yayi mulki a cikin jikinku, har ku yi biyayya ga sha'awarsa. 13Kada ku mika gabobin jikinku ga zunubi a matsayin kayan aikin rashin adalci. Amma ku mika kanku ga Allah rayayyu daga mutuwa. Ku kuma mika gabobin jikinku ga Allah a matsayin kayan aiki na adalci. 14kada ku ba zunubi dama yayi mulki a kanku, domin ba karkashin doka kuke ba, amma karkashin alheri kuke.
15To sai me? Sai mu yi zunubi wai don ba a karkashin doka muke ba amma alheri. ba zai taba faruwa ba. 16Ba ku san cewa duk ga wanda kuka mika kanku a matsayin bayi, a gareshi ku bayi ne ba? Wannan fa gaskiya ne, ko dai ku bayi ne ga zunubi wanda kaiwa ga mutuwa ko kuma bayi ga biyayya wanda ke kaiwa ga adalci.
17Amma godiya ta tabbata ga Allah! domin da ku bayin zunubi ne, amma kun yi biyayya daga zuciyarku irin salon koyarwar da aka baku. 18An 'yantar daku daga bautar zunubi, an kuma maishe ku bayin adalci.
19Ina magana da ku kamar mutum, domin kasawarku ta nama da jini. Kamar yadda kuka mika gabobin jikinku ga kazamta da miyagun ayyuka, haka ma yanzu ku mika gabobin jikinku a matsayin bayi na adalci. 20Domin a lokacin da kuke bayin zunubi, ku yantattu ne ga adalci. 21A wannan lokacin wanne amfani kuka samu na ayyukan da yanzu kuke jin kunyarsu? Domin kuwa sakamakon wadannan ayyuka shine mutuwa.
22Amma yanzu da da aka yantar daku daga zunubi aka mai da ku bayin Allah, amfaninsa ku kuwa shine tsarkakewarku. Sakamakon kuwa shine rai na har abada. 23Don kuwa sakamakon zunubi mutuwa ne. Amma kyautar Allah itace rai madauwami cikin Almasihu Yesu Ubangijinmu.

7

1'Yan'uwa, ko baku sani ba (domin ina magana da wadanda suka san shari'a), cewar shari'a na mulkin mutum muddin ransa?

2Domin ta wurin shari'a matar aure a daure take muddin mijinta nada rai, amma idan mijinta ya mutu, ta kubuta daga shari'ar aure. 3To don haka idan, mijinta na da rai, sai ta tafi ta zauna da wani mutumin, za'a kirata mazinaciya. Amma idan mijin ya mutu, "yantarciya ce daga shari'a, domin kada ta kasance mazinaciya idan ta auri wani mutum.
4Domin wannan, 'yan'uwana, ku ma an sa kun mutu ga shari'a ta wurin jikin Almasihu, saboda a hada ku aure da wani, wato, ga wanda aka tashe shi daga matattu, domin mu haifawa Allah 'ya'ya. 5Domin sa'adda muke cikin jiki, ana motsa dabi'armu ta zunubi dake cikin jikunan mu ta wurin shari'a domin mu haifi 'ya'ya zuwa mutuwa.
6Amma yanzu an kubutar damu daga shari'a, mun mutu daga abin da ya daure mu, domin mu yi bauta cikin sabuntuwar Ruhu, ba cikin tsohon rubutun shari'a ba.
7To me zamu ce kenan? ita shari'ar kanta zunubi ce? ba zai taba faruwa ba. Duk da haka. Idan ba ta wurin shari'a ba, ba zan taba sanin zunubi ba, in ba ta wurin shari'a ba. Ba zan taba kyashin abin wani ba, har sai da shari'a tace, "Kada kayi kyashi." 8Amma zunubi, sai ya dauki zarafi ta wurin dokar, ya jawo dukkan sha'awa dake cikina. Domin in da babu shari'a, zunubi matacce ne.
9Ada na rayu sau daya ba tare da shari'a ba, amma da dokar ta zo, sai zunubi ya farfado, ni kuma na mutu. 10Dokar wadda ta kamata ta kawo rai, sai na same ta matacciya.
11Domin zunubin, ya dauki zarafi ta wurin dokar, ya rude ni, kuma ta wurin dokar ya kashe ni. 12Domin haka, shari'ar na da tsarki, dokar na da tsarki, adalci da kuma kyau.
13To abu mai kyau ya zamar mani mutuwa kenan? ba zai taba zama haka ba. Amma zunubi, domin ya nuna shi zunubi ne ta wurin abin da ke mai kyau, sai ya kawo mutuwa a cikina. Wannan ya kasance haka ne domin ta wurin dokar, zunubi ya zama cikakken zunubi. 14Domin mun san shari'a mai Ruhaniya ce, amma ni ina cikin jiki. An sai da ni karkashin bautar zunubi.
15Domin ni ma ban fahimci abin da nake aikatawa ba. Domin abin da nake so in aikata, ba shi nake aikatawa ba, kuma abin da bana so, shi nake aikatawa. 16Amma idan na aikata abin da bana so, na amince da shari'a kenan, cewar shari'a nada kyau.
17Amma yanzu ba ni ke aikata abin ba, amma zunubi da ke zaune a cikina. 18Domin na san a cikina, wato cikin jikina, babu wani abu mai kyau. Domin marmarin aikata abu mai kyau na tare da ni, amma ba ni iya aikatawa.
19Domin abu mai kyau da na ke so in aikata bana iyawa, amma muguntar da ba na so ita na ke aikatawa. 20To idan na yi abin da ba ni so in aikata, wato kenan ba ni bane ke aikatawa, amma zunubin da ke zaune a cikina. 21Don haka, sai na iske, akwai ka'ida a cikina dake son aikata abu mai kyau, amma kuma ainihin mugunta na tare dani.
22Domin a cikina ina murna da shari'ar Allah. 23Amma ina ganin wasu ka'idoji daban a gabobin jikina, su na yaki da wannan sabuwar ka'idar da ke cikin tunanina, suna kuma sanya ni bauta ta wurin ka'idar zunubi wadda ke cikin gabobin jikina.
24Ni wahalallen mutum ne! wa zai kubutar dani daga wannan jiki na mutuwa? 25Amma godiya ga Allah ta wurin Yesu Almasihu Ubangijinmu! Domin haka ni kaina a wannan hannu bisa ga tunani na ina bautawa shari'ar Allah. Duk da haka, ta wani gefen ina bautawa ka'idar zunubi da ke tare da jikina.

8

1Saboda haka babu kayarwa yanzu ga wadanda ke cikin Almasihu Yesu. 2Domin ka'idar ruhun rai a cikin Almasihu Yesu ta maishe mu 'yanttatu daga ka'idar zunubi da mutuwa.

3Saboda abin da shari'a bata iya aikatawa ba domin kasawa ta wurin jiki, Allah ya yi. Ya aiko da dansa a kamanin jiki mai zunubi domin ya zama hadaya domin zunubi, sai ya yi Allah wadai da zunubi a cikin jiki. 4Ya yi haka domin bukatar shari'a ta sami cika a cikinmu, mu da muke tafe ba ta gwargwadon jiki ba, amma ta gwargwadon ruhaniya. 5Wadanda ke rayuwa gwargwadon jiki sukan lura da al'amuran jiki, amma su da ke rayuwa a gwargwadon Ruhu sukan mai da hankali ga al'amuran Ruhu.
6To kwallafa rai ga jiki mutuwa ce, amma kwallafa rai ga Ruhu rai ne da salama. 7Haka yake domin kwallafa rai ga jiki gaba yake da Allah, gama baya biyyaya ga shari'ar Allah, balle ma ya iya. 8Wadanda ke a jiki ba su iya faranta wa Allah zuciya.
9Duk da haka, ba ku cikin jiki amma a cikin Ruhu, idan gaskiya ne, Ruhun Allah na rayuwa cikinku. Amma idan wani ba shi da Ruhun Almasihu, shi ba na sa bane. 10In Almasihu na cikinka, jikin ka fa matacce ne ga zunubi, amma ruhu na rayuwa bisa ga adalci.
11Idan Ruhun wanda ya tada Yesu daga matattu na raye a cikinku, to shi wanda ya tada Almasihu da ga matattu za ya bada rai ga jikinku masu matuwa ta wurin Ruhunsa, da ke rayuwa a cikin ku.
12To, 'yan' uwa, muna da hakki amma ba bisa jiki ba, da za mu yi rayuwa bisa ga dabi'ar jiki. 13Gama idan kun yi rayuwa gwargwadon jiki, za ku mutu kenan, amma idan ta wurin Ruhu ku ka kashe ayyukan jiki, za ku rayu.
14Gama duk wadanda Ruhun Allah ke bishe su, su 'ya 'yan Allah ne. 15Gama ba ku karbi ruhun bauta da ke sa tsoro ba. Maimakon haka, kun karbi ruhun diyanci, ta wurinsa muke tadda murya muna kira, "Abba, Uba!"
16kansa na bada shaida tare da namu ruhun cewa mu 'ya'yan Allah ne. 17Idan mu 'ya'ya ne, ai mu magada ne kenan, magadan Allah. Kuma mu magada ne tare da Almasihu, hakika idan mun sha wahala tare da shi za a kuma daukaka mu tare da shi.
18Gama na yi la'akari cewa wahalonin zamanin nan ba su isa a kwatanta su da daukakar da za'a bayyana mana ba. 19Saboda yadda halitta ke marmarin bayyanuwar 'ya'yan Allah.
20Gama an kaskantar da halitta ga banza, ba da nufin ta ba, amma na shi wanda ya kaskantar da ita. Ta na cikin tabbacin alkawarin. 21Cewa halitta kanta za ta kubuta daga bautar rubewa, kuma za a kawo ta zuwa ga 'yantarwa na yabon daukakar 'ya'yan Allah. 22Gama mun sani dukan halitta na nishi da zafin nakuda tare har ya zuwa yanzu.
23Ba haka kadai ba, amma ko mu kanmu, da ke nunar farko na Ruhu--mu kanmu muna nishi acikin mu, muna jiran diyancinmu, wato ceton jikinmu kenan. 24Gama ta wanan hakikancewa aka cece mu. Amma dai abin da muke da tabbacin zai faru ba mu gan shi ba tukuna, domin wanene wa ke begen tabbatacce abin da yake gani? 25Amma idan muna da tabbacin abin da ba mu gani ba tukuna, to sai mu jjira shi da hakuri.
26Hakanan, Ruhu kuma ke taimako a kasawarmu. Gama ba mu da san yadda zamu yi addu'a ba, amma Ruhu kansa na roko a madadinmu da nishe-nishen da ba'a iya ambatawa. 27Shi da ke bidar zuciya yana sane da tunanin Ruhu, domin yana roko a madadin masu badagaskiya ta wurin nufin Allah.
28Mun san cewa ga wadanda ke kaunar Allah, yakan aikata dukan al'amura domin su zuwa ga alheri, ga duk wadanda aka kira bisa ga nufinsa. Dukan abubuwa sukan zama alheri. 29Saboda wadanda ya sani tuntuni su ne ya kardara su zama da kamanin dansa, domin ya zama dan fari a cikin 'yan'uwa masu yawa. 30Su da ya kaddara, ya kiraye su. Wadanda ya kira, su ya kubutar. Su da ya kubutar, sune kuma ya daukaka.
31Me zamu ce game da wadannan al'amura? Idan Allah na tare da mu, wake gaba da mu? 32Shi da baya hana dansa ba, amma ya bada shi a madadinmu dukka, me zai hana shi bamu dukkan abubuwa a yalwace tare da shi?
33Wa zaya kawo wata tuhuma ga zababbu na Allah? Allah ne ke "yantarwa. 34Wanene ke hukumtawa? Almasihu ne da ya mutu sabili da mu har ma fiye da haka, shi wanda kuma aka tasar. Yana mulki tare da Allah a wuri mai daukaka, shi ne kuma ya ke roko sabili da mu.
35Wa za ya raba mu da kaunar Allah? Kunci, ko bacin rai, ko tsanani, ko yunwa, ko tsiraci, ko hadari, ko takobi? 36Kamar yadda aka rubuta, "Saboda kai ake kisanmu dukkan yini. An mai da mu kamar tumaki yanka."
37A dukan al'amuran nan mun fi karfi a ce da mu masu nasara ta wurin shi da ke kaunar mu. 38Gama na tabata cewa ko mutuwa, ko rai, ko mala'iku, ko mulkoki, ko al'amuran yanzu, ko al'amura masu zuwa, ko iko, 39ko tsawo, ko zurfi, kai ko wace irin halitta, ba su isa su raba mu da kaunar Allah, da ke a cikin Almasihu Yesu Ubangijin mu ba.

9

1Gaskiya ne nake gaskiya nake fada cikin Almasihu. Ba karya nake yi ba. Lamirina, na shaida a cikin Ruhu Mai Tsarki. 2cewa ina da matukar bakin-ciki da takaici marar karewa a zuciyata.

3Dama ace, a la'anta ni, in rabu da Almasihu saboda 'yan'uwana, wato dangina da suke zuriyata bisa ga jiki. 4Sune Isra'ilawa, sun sami karbuwa, da daukaka, da baiwar shari'a, da yi wa Allah sujada, da alkawarai. 5Dukkan ubanni nasu ne daga cikinsu Almasihu ya fito bisa ga jiki- wanda shi ke Allah bisa kowa. Yabo ya tabbata a gare shi har abada. Amin.
6Amma ba wai alkawarin Allah ya kasa ba ne, ba dukkan Isra'ilawa ne suke Isra'ilawa na gaskiya ba. 7Haka nan, ba dukkan zuriyar Ibrahim ne 'ya'yansa ba. Amma "ta wurin Ishiyaku ne za'a kira zuriyarka."
8Yana nuna mana cewa ba 'ya'yan jiki su ne 'ya'yan Allah ba. Amma 'ya'yan alkawari ne ake kirga su, kuma aka kebe su. 9Wanna ce kalmar alkawari, "badi warhaka zan dawo, Saratu kuwa zata sami da."
10Amma ba wannan kadai ba, bayan Rifkatu ta dauki ciki daga gun mijinta, ubammu Ishiyaku. 11Yaran nan kafin ma a haife su, balle ma a ce sun yi wani abu mai kyau ko laifi, saboda zaben da Allah yayi, bai danganta da abin da suka yi ba, ko don aiki ba, amma don shine mai kira-- 12kamar yadda Ya ce, mata, "babban zaya yiwa karamin bauta," haka nassi yace, 13"Kamar yadda aka rubuta: "Yakubu na ke kauna, amma Isuwa na ki shi."
14To me zamu ce kenan? Allah ya yi rashin adalci kenan? Ko kadan. 15Gama ya ce wa Musa, "Ina nuna jinkai ga wanda zan yi wa jinkai, zan ji tausayi ga wanda zan tausaya masa." 16Saboda haka, ba don wanda ke da aniya ba ne, ko kuwa wanda yake kokari ba, amma saboda Allah mai nuna jinkai.
17Gama nassi ya ce da Fir'auna, "Saboda wannan dalilin ne, na tada kai, don in nuna ikona mai karfi a kanka, don sunana ya yadu ga dukkan duniya." 18Ta haka Allah ya nuna jinkansa ga wanda ya so, ya taurarar da zuciyar wanda ya ga dama.
19Za kuce mani, to don me, "Yake kama mu da llaifi? Wa ya taba yin jayayya da nufinsa?" 20In ma mun duba, kai mutum wanene kai da zaka ja da Allah? Ko abin da aka gina zai ce wa magininsa, "Don me yasa ka ginani haka?" 21Ko maginin ba shi da iko akan yimbu daya da zai gina tukunya mai daraja, wata kuma tukunyar don kowanne irin aiki?
22In ace Allah, dake niyyar nuna fushinsa da ikonsa, ya sanu, sai ya jure da matukar hakuri mai yawa da tukwanen fushi da ya shirya don hallakarwar fa? 23To ko ma ya yi haka don ya nuna yalwar daukakarsa da take dauke da alheri, wanda ya shirya don daukakarsa tun farko? 24Zai yiwu ma ya yi haka ne domin mu, mu da ya kira, ba ma daga cikin Yahudawa kadai ba, amma har ma daga cikin al'ummai?
25Kamar yadda ya ce a cikin littafin Yusha'u: "zan kira wadanda ba mutanena ba mutanena, da kuma kaunatattunta wadanda ba kaunatattu ba. 26Zai zama kuma a inda aka ce da su, "ku ba mutanena bane, za a kisa su 'ya'yan Allah mai rai."'
27Ishaya ya yi kira game da Isra'ila, "in a ce yawan 'ya'yan Isra'ila zasu zama kamar yashi a bakin teku, ragowarsu ne kawai za su sami ceto. 28Ubangiji zai tabbatar da cikar kalmarsa a duniya, ba kuwa da dadewa ba. 29Yadda Ishaya ya rubuta ada, "In da ba Ubangiji mai runduna bai bar mana zuriya ba, da zamu zama kamar Saduma, da kuma an maida mu kamar Gomarata.
30To me za mu ce kenan? Ko al'ummai, da ba sa neman adalci, sun samu adalci ta wurin bangaskiya. 31Amma Isra'ila, wadanda suka nemi adalcinsu ta wurin shari'a, ba su kai ga gaci ba.
32To don me? don ba su neme shi da bangaskiya ba, amma ta ayyuka. Sun yi tuntube a kan dutse da zai sa laifi. 33Kamar yadda aka rubuta, "Ga, shi na ajiye dutse a kan Sihiyona dutsen tuntube mai sa laifi. Ga wanda ya bada gaskiya gare shi ba zai ji kunya ba."

10

1'Yan'uwana, muradin zuciyata da dukkan addu'oi na ga Allah dominsu shine don su sami ceton. 2Domin na shaida game da su cewa suna da kwazo game da Allah, amma ba a kan sani ba. 3Don, ba su da sani akan adalcin Allah, suna kokarin tabbatar da adalcin kansu. Ba su bada kan su ga adalcin Allah ba.

4Gama Almasihu shi ne cikar doka zuwa ga adalci ga dukkan wadanda suka gaskata. 5Musa kam ya rubuta game da adalci da zai samu ta shari'a: "mutumin da ya aikata adalcin shari'a, zai rayu ta wurin wannan adalcin."
6Amma adalcin da ya zo ta wurin bangaskiya yace, "Kada ku ce a zuciyarku, wa zai hau zuwa sama?"(don ya sauko da Almasihu kasa). 7Kada ku ce, "Wa zai gangara zuwa kasa?" (Wato wa zai fito da Almasihu daga cikin matattu).
8Amma me yake cewa? "kalmar tana kusa da kai a cikin bakinka da kuma cikin zuciyarka." Wato kalmar bangaskiya, wadda muke shaidawa. 9Don idan da bakinka, ka shaida Yesu Ubangiji ne, kuma ka gaskata a zuciyarka cewa Allah ya tashe shi daga matattu, za ka sami ceto. 10Don da zuciya ne mutum yake gaskatawa zuwa ga adalci, da kuma baki ne yake shaida zuwa ga ceto.
11Don nassi na cewa, "Duk wanda ya gaskata da shi ba zai ji kunya ba," 12Gama ba bambanci tsakanin Bayahude da Ba'al'ume. Gama dukkansu Ubangijinsu daya ne, Shi mayalwaci ne ga dukkan wanda ya kira shi. 13Duk wanda ya kira sunan Ubangiji zai sami ceto.
14To ta yaya zasu kira ga wanda basu gaskata ba? Kuma ta yaya zasu gaskata ga wanda ba su taba jin labarinsa ba? 15Kuma ta yaya zasu ji in ba ayi masu wa'azi ba? Kuma ta yaya zasu yi wa'azin in ba an aike su ba? - Kamar yadda yake a rubuce, "Ina misalin kyau na kafafun wadanda ke shaida labarin farin ciki na abubuwa masu kyau!"
16Amma ba dukkansu ne suka ji bishara ba. Gama Ishaya ya ce, "Ubangiji, wa ya gaskata da sakon? 17Saboda haka bangaskiya na zuwa ta wurin ji, jin kuwa daga maganar Almasihu.
18Amma na ce, "ko basu ji ba ne? I, tabbas" muryarsu ta kai dukkan duniya, kuma kalmominsu sun kai har karshen duniya."
19yau, na ce, "Ko Isra'ila basu sani ba ne?" Da farko Musa ya ce, "Zan sa kuyi fushi da kishi da abin da ba al'umma ba. Abin da nake nufi nan shine al'ummar da basu da fahinta, zan more su, in tayar maku da hankali."
20Amma Ishaya da karfin hali ya ce, "Ga wadanda basu neme ni ba suka same ni. Na bayyana ga wadanda basu nemi ni ba. 21"Amma ga Isra'ila kam ya ce, "na mika hannu na ga masu rashin biyayya dukkan tsawon rana, domin su mutane ne masu taurin kai."

11

1Sai na ce, Allah ya ki mutanensa ne? Ba zai taba yiwuwa ba. Domin ni ma ba-Isra'ile ne, na zuriyar Ibrahim, a kabilar Bilyaminu. 2Allah bai ki mutanen sa da ya ke da rigyasaninsu ba. Ko kun san abin da nassi ya ce game da Iliya, yadda ya kai karar Isra'ila a gaban Allah? 3Ya ce, "Ubangiji, sun kashe annabawanka, sun rushe alfarwanka kuma, Ni kadai ne na rage, ga shi suna neman su kashe ni."

4Amma wacce amsa ce Allah ya ba shi? Ya ce, "Ina da mutane dubu bakwai da na kebe don kaina, da ba su taba rusuna wa Ba'al ba." 5Ban da haka ma, ban da haka ma a wannan lokacin akwai sauran zabe na alheri.
6Amma tun da ta wurin alheri ne, ba ga ayyuka ba. In ba haka ba, alheri ba zai zama alheri ba kenan. 7Sai kuma me? Abin da Isra'ila ke nema, ba su samu ba, amma zababbun sun same shi, saura kuma sun taurare. 8Kamar yadda yake a rubuce, "Allah ya ba su ruhun rashin fahimta, ga idanu amma ba za su gani ba, ga kunnuwa amma ba za su ji ba, har zuwa wannan rana."
9Dauda kuma ya ce, "bari teburinsu ya zama taru, da tarko, ya zama dutsen tuntube da abin ramako a gare su. 10Bari idanunsu ya duhunta domin kada su gani; bayansu kuma a duke kullum."
11Na ce, "sun yi tuntube domin su fadi ne?" Kada abu kamar haka ya faru. A maimakon haka, juyawa baya da suka yi ya sa, ceto ya zo ga Al'ummai, domin ya sa su kishi. 12Idan yanzu juyawa baya da sun yi ya zama arziki ga duniya, rashin su kuma arziki ga Al'ummai, yaya kwatancin girmansa zai kasance in sun zo ga kammala?
13Yanzu ina magana da ku ku da ke Al'ummai. Tunda yake ni ne manzo ga Al'ummai, ina kuma fahariya cikin hidimata. 14Yana yiwuwa in sa "yan'uwa na kishi, domin mu ceci wadansu su.
15Idan kinsu ya kawo sulhuntawa ga duniya, Karbarsu kuma zata zama yaya? Zata zama rai ne daga mutuwa. 16'ya'yan farko sunan haka ma kakkabensu yake, Idan saiwar itace na nan, haka ma rassan za su zama.
17Amma idan an karye wasu daga cikin rassan, idan ku rassan zaitun na ainihi ne, da aka samu daga cinkinsu, kuma idan kuna da gado tare da su, acikin saiwar itacen zaitun din. 18Kada ku yi fahariya a kan rassan. Amma idan kuka yi fahariya to ba ku bane masu karfafa saiwar amma saiwar ce ke karfafa ku.
19Kana iya cewa, "An karye rassan domin a same ni a ciki." 20Wannan gaskiya ne! Saboda rashin bangaskiyarsu ne ya sa aka karye su daga rassan, amma ku tsaya da karfi acikin bangaskiyarku. Kada ku dauki kanku fiye da yadda ya kamata, amma ku ji tsoro. 21Domin idan Allah bai bar ainihin rassan ba, to ba zai bar ku ba.
22Ku duba yadda irin ayyuka masu tsananni na Allah. Ta daya hannun kuma, tsanannin kan zoa kan Yahudawa wadanda suka fadi. Har 'ila yau jinkai Allah ya zo maku, idan kun cigaba cikin alherinsa baza a sare ku ba. Amma in kun ki za a sare ku.
23Hakanan, idan ba su ci gaba cikin rashin bangaskiyarsu ba, za a maida su cikin itacen. Domin Allah zai iya sake maida su. 24Idan an yanke ka daga itacen zaitun da ke na jeji, har ya yiwu an hada ka cikin itacen zaitun na ainihi, yaya kuma wadannan Yahudawa wadanda sune ainihin rassan, da za'a maido cikin zaitun da ke na ainihi?
25Yan'uwa, ba na so ku kasance cikin duhu a game da wannan asirin, domin kada ku zama da hikima cikin tunaninku. Wannan asirin shine cewa wannan taurarewa ta faru a Isra'ila, har sai da Al'ummai suka shigo ciki.
26Ta haka dukan Isra'ila za su tsira, kamar yadda yake a rubuce: "Daga cikin Sihiyona mai Kubutarwa zai fito; Zai kawar da kazanta daga cikin Yakubu. 27Wannan zai zama alkawarina da su, sa'adda na kawar da zunubansu."
28A wani bangaren kuma game da bishara, su makiya ne amamadinku, ta wani fannin kuma bisa ga zabin Allah su kaunattatu ne saboda ubanni. 29Domin baye-baye da kiran Allah basa canzawa.
30Domin ku ma da ba ku yin biyayya ga Allah, amma yanzu kun sami jinkai saboda rashin biyayyarsu. 31Ta wannan hanyar dai, wadannan Yahudawan sun zama marasa biyayya. Sakamakon haka shine ta wurin jinkan da aka nuna maku, suma su samu jikai yanzu. 32Domin Allah ya rufe kowa ga rashin biyayya, domin ya nuna jinkai ga kowa.
33Ina misalin zurfin wadata da kuma hikima da sani na Allah! Hukunce-hukuncensa sun fi gaban a bincika, hanyoyinsa kuma sun fi gaban ganewa! 34Don wanene ya san tunanin Ubangiji? Wanene kuma ya zama mai bashi shawara?
35Ko kuma, wanene ya fara ba Allah wani abu, domin a biya shi?" 36Daga wurinsa ne, ta wurinsa ne kuma, a gare shi ne kuma dukan abu suka fito. A gare shi daukaka ta tabbata har abada. Amin.

12

1Ina rokon ku 'yan'uwa, saboda yawan jinkan nan na Allah, da ku mika jikunanku hadaya mai rai, mai tsarki kuma abar karba ga Allah. wannan itace hidimarku ta zahiri. 2Kada ku kamantu da wannan duniya, amma ku sami canzawa ta wurin sabunta tunaninku, kuyi haka don ku san abin da ke nagari, karbabbe, kuma cikakken nufin Allah.

3Don ina cewa, saboda alherin da aka bani, ka da waninku ya daukaka kansa fiye da inda Allah ya ajiye shi; a maimakon haka ku kasance da hikima, gwargwadon yadda Allah yaba kowa bangaskiya.
4Domin muna da gababuwa da yawa a jiki daya, amma ba dukansu ne ke yin aiki iri daya ba. 5haka yake a garemu, kamar yadda muke da yawa haka cikin jikin Almasihu, dukkanmu gabobin juna ne.
6Muna da baye-baye dabam-dabam bisa ga alherin da aka bayar a gare mu. Idan baiwar wani anabci ne, yayi shi bisa ga iyakar bangaskiyarsa. 7In wani yana da baiwar hidima, sai yayi hidimarsa. Idan baiwar wani koyarwa ce, yayi koyarwa. 8Idan baiwar wani karfafawa ce, yayi ta karfafawa; Idan baiwar wani bayarwa ce, yayi ta da hannu sake; Idan baiwar wani shugabanci ne, yayi shi da kula; Idan baiwar wani nuna jinkai ne, yayi shi da sakakkiyar zuciya.
9Ku nuna kauna ba tare da riya ba. Ku Ki duk abin da ke mugu ku aikata abin da ke nagari. 10Akan kaunar 'yan'uwa kuma, ku kaunaci juna yadda ya kamata; akan ban girma kuma, ku ba juna girma.
11Akan himma kuma, kada ku yi sanyi; akan ruhu kuma, ku sa kwazo; Game da Ubangiji kuma, ku yi masa hidima. 12Akan gabagadi kuma, ku yi shi da farin ciki; akan tashin hankali kuma, ku cika da hakuri; akan adu'a kuma, ku nace. 13Ku zama masu biyan bukatar tsarkaka, ku zama masu karbar baki a gidajenku.
14Ku albarkaci masu tsananta maku, kada ku la'anta kowa. 15Ku yi farinciki tare da masu farinciki; Ku yi hawaye tare da masu hawaye. 16Tunanin ku ya zama daya. Kada tunaninku ya zama na fahariya, amma ku yi abokantaka da matalauta. Kada wani a cikin ku ya kasance da tunanin yafi kowa.
17Kada ku rama mugunta da mugunta. Ku yi ayukan nagarta a gaban kowa. 18Ku yi duk abin da za ku iya yi domin ku yi zaman salama tare da kowa.
19'Yan'uwa, kada ku yi ramako, ku bar Allah ya rama maku. A rubuce yake, "'Ramako nawa ne; zan saka wa kowa,' in ji Ubangiji." 20"Amma idan makiyin ka na jin yunwa, ba shi abinci ya ci. Idan yana jin kishin ruwa, ba shi ruwan sha. Idan kun yi haka, garwashin wuta ne za ku saka akan duk makiyi." 21Kada mugunta ta rinjaye ku, amma ku rinjayi mugunta ta wurin yin aikin nagarta.

13

1Bari kowa yayi biyayya da hukuma, saboda babu wata hukuma sai dai in tazo daga Allah; mahukunta da suke nan kuwa daga Allah ne. 2Saboda da haka duk wanda ya ja hukuma ya ja da dokar Allah; kuma dukan wadanda suka ki hukuma za su sha hukunci.

3Don kuwa mahukunta ba abin tsoro ne ga masu nagarta ba, amma ga masu aikata laifi. Kuna so ku zama marasa tsoron hukuma? Kuyi abu nagari, zaku sami yabo daga yin hakan. 4Saboda shi bawan Allah ne a gare ku don nagarta. Amma in kun yi abu mara kyau, kuyi tsoro, saboda ba ya dauke da takobi ba tare da dalili ba. Don shi bawan Allah ne mai saka wa mugu da fushi. 5Saboda haka dole kuyi biyayya, ba don fushi ba, amma saboda lamiri.
6Saboda wannan ne kuke biyan haraji. Don masu mulki bayin Allah ne, wadanda suke yin haka kullum. 7Ku bawa kowa hakkinsa; haraji ga mai haraji; kudin fito ga mai fito; tsoro ga wanda ya cancanci tsoro; girma ga wanda cancanci girmamawa.
8Kada ku rike bashin kowa, sai dai ku kaunaci juna. Domin duk wanda ya kaunaci dan'uwansa ya cika doka. 9To, "Kada kuyi zina, kada kuyi kisa, kada kuyi sata, kada kuyi kyashi, idan har akwai wata doka kuma, an takaita ta a wannan jimlar: "Ka kaunaci dan'uwanka kamar kanka." 10Kauna bata cutar da makwabci. Domin haka, kauna tace cikar shari'a.
11Saboda wannan, kun san lokaci yayi, ku farka daga barci. Domin cetonmu yana kusa fiye da yadda muke tsammani. 12Dare yayi nisa, gari ya kusan wayewa. Don haka, sai mu rabu da ayyukan duhu, mu yafa makaman haske.
13Sai muyi tafiya yadda ya kamata, kamar da rana, ba a cikin shashanci ko buguwa ba. Kada kuma muyi tafiya cikin fasikanci da muguwar sha'awa, ba kuma cikin husuma ko kishi ba. 14Amma ku yafa Ubangiji Yesu Almasihu, kada kuwa ku tanadi halin mutumtaka, don biye wa muguwar sha'awarsa.

14

1Ku karbi duk wanda yake da rarraunar bangaskiya, ba tare da sukar ra'ayinsa ba. 2Wani yana da bangaskiyar yaci komai, wani wanda yake da rauni yakanci ganye ne kawai.

3Kada wanda yake cin komai ya raina wanda baya cin kowanne abu. Kada kuma wanda baya cin kowanne abu ya shara'anta sauran da suke cin komai. Saboda Allah ya karbe shi. 4Kai wanene, kai wanene da kake ganin laifin bawan wani? Tsayawarsa ko faduwarsa ai hakin maigidansa ne, amma Ubangiji yana da ikon tsai da shi.
5Wani yakan daukaka wata rana fiye da sauran. Wani kuma yana daukan ranakun daidai. Kowa ya zauna a cikin hakakkewa akan ra'ayinsa. 6Shi wanda ya kula da wata rana, ya kula da ita don Ubangiji. Kuma wanda yaci, yaci ne domin Ubangiji, domin yana yi wa Allah godiya. Shi wanda bai ci ba, yaki ci ne domin Ubangiji. Shima yana yi wa Allah godiya.
7Domin babu wanda yake rayuwa don kansa a cikinmu, kuma babu mai mutuwa don kansa. 8Domin in muna raye, muna raye don Ubangiji. Kuma in mun mutu, mun mutu ne don Ubangiji. Ashe, ko muna raye, ko a mace mu na Ubangiji ne. 9Domin wannan dalilin Almasihu ya mutu ya kuma tashi, saboda ya zama Ubangiji ga matattu da rayayyu.
10Amma ku don me kuke shara'anta yan'uwanku? kai kuma don me kake raina dan'uwanka? Dukan mu zamu tsaya gaban kursiyin shari'ar Allah. 11Domin a rubuce yake, "Na rantse, "inji Ubangiji", kowacce gwiwa zata rusuna mani, kowanne harshe kuwa zai yabi Allah."
12Domin kowannenmu zai fadi abin da shi yayi da bakinsa a gaban Allah. 13Saboda da haka kada muyi wa juna shari'a, amma maimakon haka ku dauki wannan kudduri, don kada kowa ya zama sanadin tuntunbe ko faduwa ga dan'uwansa.
14Na sani na kuma tabbata tsakani na da Ubangiji Yesu, ba abin da yake mara tsarki ga asalinsa. Sai dai ga wanda ya dauke shi marar tsarki ne yake zama marar tsarki. 15Idan har abincinka na cutar da dan'uwanka, ba ka tafiya cikin kauna. Kada ka lalata wanda Yesu ya mutu domin sa da abincinka.
16Saboda haka, kada abubuwan da aka dauka kyawawa su zama abin zargi ga wadansu. 17Saboda mulkin Allah ba maganar ci da sha ba ne, amma game da adalci ne, salama, da farin ciki a cikin Ruhu Mai Tsarki.
18Domin wanda yake bautar Almasihu a wannan hanya, karbabbe ne ga Allah, kuma jama'a sun yarda da shi. 19Don haka, mu nemi abubuwa na salama da abubuwan da zasu gina juna.
20Kada ku lalata aikin Allah don abinci. Komai yana da tsarki, amma kaiton mutumin da yake cin abin da zai sa shi ya fadi. 21Bashi da kyau a ci nama ko a sha ruwan inabi, ko duk abin da zai jawo faduwar dan'uwanka.
22Wannan bangaskiyar da kuke da ita, ku adana ta tsakaninku da Allah. Mai albarka ne wanda zuciyarsa bata da laifi akan abin da hankalinsa ya ga daidai ne. 23Duk wanda yayi shakka amma kuma yaci, ya sani yayi laifi kenan, domin ba tare da bangaskiya bane. Duk abin da ba na bangaskya bane zunubi ne.

15

1Yanzu mu da muke da karfi ya kamata mu dau nauyi raunana, kuma bai dace mu nuna son kai ba. 2Bari kowannenmu ya faranta wa makwabcinsa rai, domin wannan yana da kyau, don a gina shi.

3Domin Almasihu bai faranta wa kansa rai ba. Kamar yadda aka rubuta, "zagin da wadansu suka yi masa ya sauka a kaina." 4Don abin da aka rubuta a baya an rubuta ne domin a gargade mu, domin ta hakuri da karfafawar litattafai mu sami karfi.
5Yanzu Allah mai hakuri da karfafawa ya baku zuciya daya ta zaman tare da juna bisa ga halin Yesu Almasihu. 6Domin ya yi haka ne da zuciya daya domin ku yi yabo da bakinku daya. 7Domin ku karbi juna, kamar yadda Yesu ma ya karbe ku domin a daukaka Allah.
8Saboda na ce an mai da Almasihu bawan kaciya a madadin gaskiyar Allah. Ya yi wannan ne don a tabbatar da alkawarai da aka ba kakanin kakaninmu. 9Domin Al'umai su daukaka Allah saboda jinkansa, kamar yadda ya ke a arubuce, "Domin ta haka zan yabe ka cikin Al'umai in yi wakar yabon sunanka."
10Kuma an ce. "Ku yi faranciki, ku Al'ummai tare da mutanensa." 11Kuma." Ku yabi Ubangiji, ku dukan Al'ummai; bari dukan mutane su yabe shi."
12Kuma, Ishaya ya ce "Za a sami tsatson Yessi, wanda zai tashi ya yi mulki a kan Al'umai, Al'umai za su sami karfin hali a cikinsa."
13Yanzu Allah mai karfafawa ya cika ku da dukkan farin ciki salama, saboda da bangaskiyarku, domin ku sami cikkakiyar karafafawa, ta wurin ikon Ruhu Mai Tsarki.
14Ni kaina na amince da ku, yan'uwa. Kuma na amince cewa ku da kanku kuna cike da alheri, cike da dukkan sani. Na amince cewa za ku sami zarafi ku gargadi juna.
15Amma ina rubuta maku da gabagadi kan wadansu abubuwa, domin in tunasheku, saboda baiwar da aka bani daga wurin Allah. 16Cewa baiwar ta sa na zama bawan Almasihu Yesu da aka aika ga Al'ummai, limami na bisharar Allah. Zan yi wannan saboda baikon Al'ummai ya zama karbabbe, kuma kebbabe ga Allah ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
17Don haka ina jin dadi cikin Yesu Almasihu da abubuwa na Allah. 18Domin ba ni da abin da zan ce, sai abin da Yesu ya aikata ta wurina, domin Al'ummai su yi biyayya ta magana da aiki. 19Ta wurin alamu, da al'jibai, da ikon Ruhu Mai Tsarki. Daga Urushalima, da kewaye har zuwa Ilirikum, an kai bisharar Almasihu ko'ina dukka.
20A cikin hanyar nan, burina in sanar da bishara, amma a inda ba a san Yesu ta wurin sunansa ba, don kada in sa gini akan harshashi wani. 21Kamar yadda yake a rubuce."Wadanda ba a taba fada wa labarinsa ba, su gane. Wadanda ba su taba jin labarinsa ba su fahimta."
22Saboda an hana ni zuwa wurin ku a lokatai da dama. 23Amma yanzu bani da sauran wani wuri a lardin nan, kuma cikin shekaru masu yawa ina da marmarin in zo wurin ku.
24Duk lokacin da zan tafi Asbaniya ina begen ganin ku yayin wucewa, don ku raka ni bayan na ji dadin zama da ku na dan lokaci. 25Amma yanzu ina tafiya Urushalima don in yi wa tsarkaka hidima.
26Domin abin farinciki ne ga mutanen Makidoniya da Akaya su yi bayarwa domin gajiyayyu masu bada gaskiya wadanda suke a Urushalima. 27Suna jin dadi domin hakika kamar bashi ne a kansu. Domin Al'ummai sun yi tarayya da su cikin ayyukan ruhaniya, ya zama hakki a kansu su ma su taimake su da abubuwa.
28Domin lokacin da na gama basu kudin, zan zo gareku a hanyata ta zuwa Asbaniya. 29Na san cewa lokacin da na zo gareku, zan zo da cikakkun albarku na Almasihu.
30Yanzu ina rokonku, yan'uwa, ta wurin Ubangiji Yesu Almasihu, da kaunar Ruhu Mai Tsarki, ku yi ta fama tare da ni a cikin yin addu'o, inku ga Allah saboda ni. 31Kuyi haka saboda in tsira daga wadanda suke masu biyayya ga Yahudiya, domin kuma hidimata saboda Urushalima ta zama karbabbiya. 32Ku yi addu'a cewa in zo wurinku da farinciki ta wurin nufin Allah, cewa tare da ni da ku, mu sami hutu.
33Allah na salama ya kasance tare da ku duka. Amin.

16

1Ina gabatar muku da fibi 'yar'uwarmu, wanda take hidima a Ikilisiya dake cikin Kankiriya. 2Domin ku karbe ta cikin Ubangij. A hanyar da ta dace ga masu bada gaskiya, ku tsaya tare da ita cikin kowacce bukata. Domin ita da kanta ta zama da taimako ga masu yawa, har da ni ma.

3Ku gai da Bilkisu da Akila abokan aiki cikin Yesu Almasihu. 4Wadanda sabo da ni suka sadaukar da ransu. Ina godiya garesu, ba ni kadai ba, amma kuma da dukan Ikilisiyoyin Al 'mmai. 5Gaida Ikilisiya da ke gidansu. Ku gai da Abainitas kaunataccena. Wanda shi ya fara bada gaskiya ga Almasihu a Asiya.
6Ku gai da Maryamu, wadda ta yi maku aiki tukuru. 7Ku gai da Andaranikas da Yuniyas, yan'uwana da abokan kurkukuna. Su sanannu ne cikin manzani, wadanda suke cikin Almasihu kafin ni. 8Ku gai da Amfiliyas kaunatace na cikin Ubangiji.
9Ku gai da Urbanas abokin aikinmu cikin Almasihu, da Istakis kaunataccena. 10Ku gai da Abalis amintacce cikin Almasihu. Ku gai da wadanda su ke gidan Aristobulus. 11Ku gai da Hirudiya, dan'uwa na, da wadanda ke gidan Narkissa, wadanda ke cikin Ubangiji.
12Ku gai da Tarafina daTarafusa, masu aikin Ubangiji. 13Ku gai da Barsisa kaunatacciya, wadda ta yi aikin Ubangiji da yawa. Ku gai da Rufas zababbe cikin Ubangiji da mamarsa da ni. 14Ku gai da Asinkiritas da Filiguna da Hamis da Baturobas da Hamisu da kuma yan'uwa da ke tare da su.
15Ku gai da Filolugus daYuliya da Niriyas da yan'uwansa, da Ulumfas da kuma dukan tsarkaka da ke tare su. 16Ku gaggai da juna da tsatsarkar sumba. Dukan Ikilisiyoyin Almasihu na gaishe ku.
17Yanzu ina rokon ku, yan'wa, ku yi tunani fa game da masu kawo rabuwa da tuntube. Sabanin koyarwar da ku ka koya. Ku yi nesa da su. 18Domin irin mutanen nan ba sa bauta wa Ubangiji Yesu, sai dai tumbinsu. Ta dadin bakinsu suke rudin zuciyar marasa laifi.
19Domin rayuwar biyayyarku takai ga kunnen kowa, na yi farin ciki da ku, amma ina so ku zama da hikima game da abin ya ke mai kyau, ku zama marasa laifi ga abin da ke na mugunta. 20Allah na salama zai sa ku tattake Shaidan da sauri kalkashin sawayen ku. Alherin Ubangijin mu Yesu Almasihu ya kasance tare da ku.
21Timoti abokin aikina, yana gaishe ku, haka Lukiyas da Yason da Susibataras da kuma yan'uwana. 22Ni Tartiyas wanda ya rubuta wasikan nan, na gaisheku cikin Ubangiji.
23Gayus mai masaukina da kuma dukan Ikilisiya, suna gaishe ku. Arastas ma'ajin birni na gaishe ku, da Kwartus dan'uwanmu. 24Alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu ya kasance tare da ku dukka. Amin.
25Yanzu ga wanda ke da Ikon karfafa ku bisa ga bisharata da wa'azin Yesu Almasihu, wanda ta gare shi ne aka bayyana asiran nan da suke boye tun da dadewa, 26amma yanzu sanannu ne ta wurin litattafan Annabawa bisa umarnin Allah madauwami, domin biyayyar bangaskiya cikin Al'ummai dukka.
27Ga Allah mai hikima kadai, ta wurin Yesu Almasihu daukaka ta tabbata har abada. Amin.

1 Korintiyawa

1

1Bulus, kirayayye daga Almsihu Yesu don zama manzo ta wurin nufin Allah, da dan'uwanmu Sastanisu, 2zuwa ga Ikilisiyar Allah da ke korinti, zuwa ga wadanda aka kebe su cikin Almasihu Yesu, wadanda aka kira domin su zama al'umma maitsarki. Muna kuma rubuta wa dukan masu kira bisa sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu a ko'ina, wato Ubangijinsu da Ubangijinmu kuma. 3Bari alheri da salama su zo gare ku daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Almasihu.

4Kodayaushe ina gode wa Allahna domin ku, saboda alherin Allah da Almasihu Yesu ya yi maku. 5Ya ba ku arziki ta kowace hanya, cikin dukkan magana da dukkan ilimi. 6Kamar yadda shaida game da Almasihu ta tabbata gaskiya a tsakaninku.
7Saboda haka baku rasa wata baiwa ta ruhaniya ba yayinda kuke marmarin jiran bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Almasihu. 8Zai kuma karfafa ku zuwa karshe, saboda ku zama marasa aibi a ranar Ubangijinmu Yesu Almasihu. 9Allah mai aminci ne shi wanda ya kira ku zuwa zumunta ta Dansa, Yesu Almasihu Ubangijimu.
10Ina rokon ku, yan'uwa, cikin sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu, ku yarda da juna, kada tsattsaguwa ta kasance tsakanin ku. Ina rokon ku ku zama da zuciya daya da kuma nufi daya. 11Gama mutanen gidan Kulowi sun kawo kara cewa akwai tsattsaguwa a cikin ku.
12Ina nufin: kowannen ku na cewa, "Ina bayan Bulus," ko " Ina bayan Afollos," ko "Ina bayan Kefas," ko "Ina bayan Almasihu." 13Almasihu a rarrabe yake? An gicciye Bulus domin ku? Ko an yi maku baftisma a cikin sunan Bulus?
14Na godewa Allah domin ban yi wa wanin ku baftisma ba, sai dai Kirisfus da Gayus. 15Na yi wannan saboda kada wani ya ce an yi maku baftisma a cikin sunana. 16(Na kuma yi wa iyalin gidan Sitifanas baftisma. Banda haka, ban sani ko na yi wa wani baftisma ba.)
17Gama Almasihu bai aiko ni domin yin baftisma ba, amma domin yin wa'azin bishara. Bai aiko ni domin in yi wa'azi da kalmomin hikimar mutum ba, saboda kada giciyen Almasihu ya rasa ikonsa.
18Gama wa'azin gicciye wauta ne ga wadanda su ke mutuwa. Amma cikin wadanda Allah ke ceto, ikon Allah ne. 19Gama a rubuce yake, "Zan watsar da hikimar masu hikima. Zan dode fahimtar masu basira."
20Ina mai hikima? Ina masani? Ina mai muhawara na duniyan nan? Allah bai juya hikimar duniya zuwa wauta ba? 21Tunda duniya cikin hikimarta bata san Allah ba, ya gamshi Allah ta wurin wautar wa'azi ya ceci masu bada gaskiya.
22Gama Yahudawa suna bidar al'ajibai, Helinawa kuma suna neman hikima. 23Amma muna wa'azin Almasihu gicciyayye, dutsen tuntube ga yahudawa da kuma wauta ga Helinawa.
24Amma ga wadanda Allah ya kira, Yahudawa da Helinawa, muna wa'azin Almasihu a matsayin iko da kuma hikimar Allah. 25Gama wautar Allah tafi mutane hikima, kuma rashin karfin Allah yafi mutane karfi.
26Dubi kiranku, yan'uwa. Ba dukkan ku ke da hikima a ma'aunin mutane ba. Ba dukkan ku ke da iko ba. Ba dukkan ku ke da haifuwa ta sarauta ba. 27Amma Allah ya zabi abubuwan da suke wofi na duniya domin ya kunyatar da masu hikima. Allah ya zabi abin da ke marar karfi a duniya domin ya kunyatar da abinda ke mai karfi.
28Allah ya zabi abinda ke marar daraja da kuma renanne a duniya. Ya ma zabi abubuwan da ake dauka ba komai ba, domin ya wofinta abubuwan da ake dauka masu daraja. 29Ya yi wannan ne domin kada wani ya sami dalilin fahariya a gabansa.
30Domin abinda Allah ya yi, yanzu kuna cikin Almasihu Yesu, wanda ya zamar mana hikima daga Allah. Ya zama adalcinmu, da tsarkinmu da fansarmu. 31A sakamakon haka, kamar yadda nassi ya ce, "Bari mai yin fahariya, ya yi fahariya cikin Ubangiji."

2

1Lokacin da na zo wurin ku, yan'uwa, ban zo da gwanintar magana ko hikima ba yayinda na yi shelar boyayyun bayanai game da Allah. 1 2Domin na kudura a zuciyata kada in san komai lokacin da nake tare da ku, sai dai Yesu Almasihu, gicciyayye.

3Ina tare da ku cikin kasawa, da tsoro, da fargaba mai yawa. 4Kuma sakona da shelata basu tare da kalmomin hikima masu daukar hankali. Maimakon haka, sun zo da bayyanuwar Ruhu da iko, 5saboda kada bangaskiyarku ta zama cikin hikimar mutane, amma cikin ikon Allah.
6Yanzu muna maganar hikima ga wadanda suka ginu, amma ba hikima ta duniyan nan ba, ko ta masu mulkin wannan zamani, wadanda suke shudewa. 7Maimakon haka, muna maganar hikimar Allah ta boyayyar gaskiya, boyayyar hikima da Allah ya kaddara kafin zamanin daukakarmu.
8Babu wani mai mulki na zamanin nan da ya san wannan hikimar, domin inda sun gane ta a wancan lokacin, da basu gicciye Ubangijin daukaka ba. 9Amma kamar yadda yake a rubuce, "Abubuwan da babu idon da ya gani, babu kunnen da ya ji, babu zuciyar da ta yi tsammanin sa, abubuwan da Allah ya shirya wa wadanda suke kaunarsa.
10Wadannan ne abubuwan da Allah ya bayyana mana ta wurin Ruhu. Gama Ruhu yana bincika komai, har ma abubuwa masu zurfi na Allah. 11Gama wanene ya san tunanin mutum, sai dai ko ruhun mutumin da ke cikinsa? Haka ma, babu wanda ya san abubuwa masu zurfi na Allah sai dai Ruhun Allah.
12Ba mu karbi ruhu na duniya ba, amma Ruhun da ya zo daga wurin Allah, domin mu san abubuwan da aka bamu a sake daga wurin Allah. 13Muna maganar wadannan abubuwa da kalmomin da hikimar da mutum baza ta iya koyarwa ba, amma wadanda Ruhu ke koyar da mu. Ruhu yana fassara kalmomi na ruhaniya da hikima ta ruhaniya.
14Mutum marar ruhaniya ba ya karbar abubuwan da suke daga Ruhun Allah, gama wauta suke a gareshi. Ba zai iya sanin su ba domin Ruhu ne yake bayyana su. 15Shi wanda yake mai ruhaniya yana shari'anta dukan abubuwa, amma shi baya karkashin shari'ar sauran mutane. 16"Wa zai iya sanin zuciyar Ubangiji, da zai iya ba shi umarni?" Amma mu muna da lamiri irin na Almasihu.


1Wasu 'yan mahimman da tsoffin kwafin Girkanci suna karantawa, a yayinda na bada shaida game da Allah .

3

1Amma ni, yan'uwa, ba zan iya magana da ku kamar mutane masu ruhaniya ba, amma kamar mutane masu jiki, kamar jarirai cikin Almasihu. 2Na shayar da ku da Madara ba da nama ba, don baku isa cin nama ba, kuma ko yanzu ma baku isa ba.

3Gama har yanzu ku masu jiki ne. Muddin akwai kishi da jayayya a tsakaninku, ashe, ku ba masu jiki ba ne, kuma kuna tafiya bisa magwajin mutane? 4Domin in wani ya ce, "Ina bayan Bulus," wani kuma ya ce, "Ina bayan Afollos," ashe, ba zaman mutuntaka kuke yi ba? 5To wanene Afollos? Wanene kuma Bulus? Bayi ne wadanda kuka bada gaskiya ta wurin su, kowannen su kuwa Allah ya bashi ayyuka.
6Ni nayi shuka, Afolos yayi banruwa, amma Allah ne ya sa girma. 7Don haka, da mai shukar da mai banruwan, ba komi bane. Amma Allah ne mai sa girman.
8Da mai shukar, da mai banruwan, duk daya suke, kuma kowannen su zai sami nasa lada, gwargwadon aikinsa. 9Gama mu abokan aiki ne na Allah. Ku gonar Allah ne, ginin Allah kuma.
10Bisa ga alherin Allah da aka bani a matsayin gwanin magini, na kafa harsashi, wani kuma yana dora gini a kai. Sai dai kowane mutum, ya lura da yadda yake dora ginin. 11Gama ba wanda ke iya kafa wani harsashin daban da wanda aka rigaya aka kafa, wato, Yesu Almasihu.
12Yanzu fa in wani ya dora gini a kan harashin da zinariya, ko azurfa, ko duwatsu masu daraja, ko itace, ko ciyawa, ko tattaka, 13aikinsa zai bayyanu, domin ranar nan zata tona shi. Gama za a bayyana shi cikin wuta. Wutar kuwa zata gwada ingancin aikin da kowa ya yi.
14Duk wanda aikinsa ya tsaya, zai karbi lada; 15amma duk wanda aikinsa ya kone, zai sha Asara, amma shi kansa zai tsira, sai dai kamar ta tsakiyar wuta.
16Ashe, baku san ku haikalin Allah ne ba, Ruhun Allah kuma yana zaune a cikin ku? 17Idan wani ya lalata haikalin Allah, Allah zai lalata shi. Gama haikalin Allah mai tsarki ne, kuma haka ku ke.
18Kada kowa ya rudi kansa. Idan wani a cikin ku na ganin shi mai hikima ne a wannan zamani, bari ya zama" wawa" domin ya zama mai hikima. 19Gama hikimar duniyar nan wauta ce a gun Allah. Gama a rubuce yake, "Yakan kama masu hikima a cin makircin su." 20Har wa yau, "Ubangiji ya san tunanin masu hikima banza ne."
21haka ba sauran fariya akan mutane! Domin kuwa kome naku ne, 22Ko Bulus, ko Afollos, ko kefas, ko duniya, ko rai, ko mutuwa, ko abubuwa na yanzu, ko abubuwa masu zuwa. Duka naku ne, 23Ku kuwa na Almasihu ne, Almasihu kuma na Allah ne.

4

1Ga yadda za ku dauke mu, kamar bayin Almasihu da kuma masu rikon asiran Allah. 2Hade da wannan, ana bukatar wakilai su zama amintattu.

3Amma a gare ni, karamin abu ne ku yi mani shari'a, ko a wata kotu irin ta mutane. Gama bani yi wa kaina shari'a. 4Ban sani ko akwai wani zargi a kaina ba, amma wannan bai nuna cewa bani da laifi ba. Ubangiji ne mai yi mani shari'a.
5Sabili da haka, kada ku yanke shari'a kafin lokaci, kafin Ubangiji ya dawo. Zai bayyana dukkan boyayyun ayyuka na duhu, ya kuma tona nufe-nufen zuciya. San nan kowa zai samu yabonsa daga wurin Allah.
6Yan'uwa, ina dora wadannan ka'idoji a kaina da Afollos domin ku, yadda ta wurin mu za ku koyi ma'anar maganar nan cewa, "kada ku zarce abin da aka rubuta." Ya zama haka domin kada waninku ya kumbura yana nuna fifiko ga wani akan wani. 7Gama wa yaga bambanci tsakanin ku da wasu? Me kuke da shi da ba kyauta kuka karba ba? Idan kyauta kuka karba, don me kuke fahariya kamar ba haka ba ne?
8Kun rigaya kun sami dukkan abubuwan da kuke bukata! Kun rigaya kun zama mawadata! Kun rigaya kun fara mulki- kuma ba tare da mu ba! Hakika, marmarina shine ku yi mulki, domin mu yi mulki tare da ku. 9A tunanina, mu manzanni, Allah ya sa mu a jerin karshe kamar mutanen da aka zartar wa hukuncin mutuwa. Mun zama abin kallo ga duniya, ga mala'iku, ga mutane kuma.
10Mun zama marasa wayo sabili da Almasihu, amma ku masu hikima ne a cikin Almasihu. Mu raunana ne, amma ku masu karfi ne. Ana ganin mu marasa daraja, ku kuwa masu daraja. 11Har zuwa wannan sa'a, muna masu yunwa da kishi, marasa tufafi masu kyau, mun sha kazamin duka, kuma mun zama marasa gidaje.
12Mun yi fama sosai, muna aiki da hanuwanmu. Sa'adda an aibata mu, muna sa albarka. Sa'adda an tsananta mana, muna jurewa. 13Sa'adda an zage mu, muna magana da nasiha. Mun zama, kuma har yanzu an dauke mu a matsayin kayan shara na duniya da abubuwa mafi kazamta duka.
14Ban rubuta wadannan abubuwa domin in kunyata ku ba, amma domin in yi maku gyara kamar kaunatattun yayana. 15Ko da kuna da masu riko dubu goma a cikin Almasihu, ba ku da ubanni da yawa. Gama ni na zama ubanku cikin Almasihu Yesu ta wurin bishara. 16Don haka, ina kira gare ku da ku zama masu koyi da ni.
17Shiyasa na aiko Timoti wurin ku, kaunatacce da amintaccen dana cikin Ubangiji. Zai tunashe ku hanyoyina cikin Almasihu, kamar yadda nake koyar da su ko'ina da kowace Ikilisiya.18Amma yanzu, wadansun ku sun zama masu fahariya, suna yin kamar ba zan zo wurinku ba.
19Amma zan zo gare ku ba da dadewa ba, idan Ubangiji ya nufa. Sannan zan san fiye da maganar masu fahariya, amma kuma zan ga ikonsu. 20Gama Mulkin Allah ba magana kadai ya kunsa ba, amma ya kunshi iko. 21Me kuke so? In zo wurin ku da sanda ne ko kuwa da kauna da ruhun nasiha?

5

1Mun ji cewa akwai lalata mai kazanta a cikin ku, irin lalatar ba ba a yarda da ita ba ko a cikin al'ummai. Labarin da na samu shine, wani daga cikin ku yana kwana da matar mahaifinsa. 2Kuma kuna fahariya sosai! Ba bakinciki ya kamata ku yi ba? Shi wanda ya yi haka, dole a fitar da shi daga cikin ku.

3Gama Kodashike ba ni tare da ku cikin jiki, amma ina tare daku a ruhu, na rigaya na hukunta wanda yayi wannan, tamkar ina wurin. 4Lokacin da ku ka taru a cikin sunan Ubangijinmu Yesu, ruhuna yana nan tare da ku cikin ikon Ubangiji Yesu, na rigaya na hukunta wannan mutum. 5Na yi haka ne domin in mika wannan mutum ga Shaidan domin a hallaka jikin, don ruhunsa ya tsira a ranar Ubangiji.
6Fahariyarku bata yi kyau ba. Ko baku sani ba yisti dan kadan ya kan bata dukan dunkule? 7Ku tsarkake kan ku daga tsohon yisti domin ku zama sabon dunkule, wato gurasar da ba ta da yisti. Gama an yi hadayar Almsihu, dan ragonmu na idi. 8Don haka, bari mu yi idinmu ba da tsohon yisti ba, wato yisti irin na rashin tabi'a da mugunta. Maimakon haka, bari muyi bukin idi da gurasa marar yisti ta aminci da gaskiya.
9Na rubuta maku a cikin wasikata cewa kada ku yi hudda da fasikan mutane. 10Ba ina nufin fasikan mutane na wannan duniya ba, ko masu zari, ko 'yan'damfara, ko masu bautar gumaka, tunda kafin ku rabu da su sai kun bar wannan duniya.
11Amma yanzu ina rubuta maku cewa kada ku yi hudda da duk wanda ake kira dan'uwa amma yana zama cikin fasikanci, ko zari, ko bautar gumaka, ko in shi mai ashar ne, ko mashayi, ko dan'damfara. Kada ko abinci ku ci da irin wannan mutum. 12Domin ta yaya zan iya shar'anta wadanda ba 'yan Ikklisiya ba? Maimakon haka, ba ku ne zaku shar'anta wadanda ke cikin ikilisiya ba? 13Amma Allah ke shar'anta wadanda ke waje. "Ku fitar da mugun mutumin daga cikin ku."

6

1Idan wani a cikin ku yana jayayya da wani, to sai ya tafi kotu gaban alkali marar bada gaskiya, a maimakon gaban masu bi? 2Ko ba ku sani ba, masubi ne za su yiwa duniya shari'a? Kuma idan ku za ku yi wa duniya shari'a, sai ku kasa sasanta al'amura marasa mahimmanci? 3Baku sani ba mu za mu yiwa mala'iku shari'a? Balle shari'ar al'amuran wannan rai?

4Idan kuna shar'anta al'amuran yau da kullum, don me ku ke kai irin wadannan matsaloli gaban wadanda ba 'yan ikilisiya ba? 5Na fadi wannan domin ku kunyata. Babu wani mai hikima a cikin ku ko daya da zai iya sasanta gardama a tsakanin 'yan'uwa? 6Amma kamar yadda yake, mai bi ya na kai karar mai bi a kotu, kuma a gaban mai shari'a wanda ba mai bi ba!
7Kasancewar rashin jituwa a tsakanin Kirista na nuna cewa kun rigaya kun gaza. Don me ba za ka shanye laifi ba? Don me ba za ka yarda a kware ka ba? 8Amma kun yi wa wadansu laifi kun kuma cutar su, su kuwa 'yan'uwanku ne!
9Ba ku sani ba marasa adalci ba za su gaji Mulkin Allah ba? Kada ku gaskata karya. Da fasikai, da masu bautar gumaka, da mazinata, da karuwai maza, da masu ludu, 10da barayi, da masu zari, da mashaya, da masu zage-zage, da 'yan damfara - ba waninsu da zai gaji Mulkin Allah. 11Kuma da haka wadansu a cikinku suke, amma an tsarkake ku, an mika ku ga Allah, an maida tsayuwar ku dai-dai a gaban Allah a cikin sunan Ubangji Yesu Almasihu, kuma ta wurin Ruhun Allahnmu.
12Dukkan abu halal ne a gare ni", amma ba kowanne abu ne mai amfani ba. "Dukan abu halal ne a gare ni," amma ba zan yarda wani abu ya mallake ni ba. 13"Abinci don ciki ne, kuma ciki don abinci ne", amma Allah za ya kawar da su duka. Ba a yi jiki saboda fasikanci ba. Maimakon haka, jiki don Ubangiji ne, kuma Ubangiji zai yi wa jiki tanaji.
14Allah ya tada Ubangiji, kuma za ya tashe mu ta wurin ikonsa. 15Ba ku sani ba jikunanku gabobi ne na Almasihu? Na dauki gabobin Almasihu in hada su da karuwa? Allah ya sawwake!
16Ko baku sani ba dukan wanda yake hade da karuwa, ya zama jiki daya da ita kenan? 17Kamar yadda Littafi ya fadi, "Su biyun za su zama nama daya." Amma wanda yake hade da Ubangiji ya zama ruhu daya da shi kenan.
18Ku gujewa fasikanci! Kowane zunubi mutum yake aikatawa a waje da jikinsa yake, amma mutum mai fasikanci yana zunubi gaba da jikinsa.
19Ba ku sani ba jikinku haikali ne na Ruhu Mai-tsarki, wanda yake zaune a cikinku, wanda ku ka samu daga wurin Allah? Ba ku sani ba cewa ku ba na kanku ba ne? 20An saye ku da tsada. Don haka, ku daukaka Allah da jikin ku.

7

1Game da abubuwan da kuka rubuto: "Yayi kyau ga mutum kada ya taba mace." 2Amma Saboda jarabobi na ayyukan fasikanci masu yawa, ya kamata kowane mutum ya kasance da matarsa, kowace mace kuma ta kasance da mijinta.

3Kowanne maigidanci ya ba matarsa hakin ta, kuma kowace mace ta ba maigidan ta hakinsa na saduwa da juna. 4Matan ba ta da iko akan jikin ta amma maigidan ne. Haka ma, maigidan bashi da iko akan jikinsa amma matar ce.
5Kada ku hana wa junanku saduwa, sai dai da yardar junanku domin wani dan lokaci. Kuyi haka domin ku bada kanku ga addu'a. Daganan sai ku sake saduwa, domin kada Shaidan ya jarabce ku saboda rashin kamun kanku. 6Amma ina fada maku wadannan abubuwa ne a matsayin nuni, ba a matsayin umurni ba. 7Na so da kowa da kowa kamar ni yake. Amma kowa na da baiwarsa daga wurin Allah. Wani na da irin wannan baiwar, wani kuma waccan.
8Ga marasa aure da gwamraye, Ina cewa, yana da kyau a garesu su zauna ba aure, kamar yadda nike. 9Amma idan baza su iya kame kansu ba, ya kamata su yi aure. Gama yafi masu kyau su yi aure da su kuna da sha'awa.
10Ga masu aure kwa, ina bada wannan umarni- ba ni ba, amma Ubangiji: "Kada mace ta rabu da mijinta." 11Amma idan har ta rabu da mijinta, sai ta zauna ba aure ko kuma ta shirya da shi. Haka kuma " Kada miji ya saki matarsa."
12Amma ga sauran ina cewa-Ni, ba Ubangiji ba-idan wani dan'uwa yana da mata wadda ba mai bi ba, kuma idan ta yarda ta zauna da shi, to kada ya sake ta. 13Idan kuwa mace tana da miji marar bi, idan ya yarda ya zauna tare da ita, to kada ta kashe aure da shi. 14Gama miji marar bada gaskiya ya zama kebabbe saboda matarsa, sannan mata marar bada gaskiya ta zama kebbiya saboda mijinta mai bi. In ba haka ba 'ya'yanku za su zama marasa tsarki, amma a zahiri su kebabbu ne.
15Amma idan abokin aure marar bi ya fita, a bar shi ya tafi. A irin wannan hali, dan'uwa ko 'yar'uwa ba a daure suke ga alkawarinsu ba. Allah ya kira mu da mu zauna cikin salama. 16Yaya kika sani, ke mace, ko za ki ceci mijinki? ko yaya ka sani, kai miji, ko za ka ceci matarka?
17Bari dai kowa ya yi rayuwar da Ubangiji ya aiyana masa, kamar yadda Allah ya kirawo shi. Wannan ce ka'idata a dukkan ikilisiyu. 18Mutum na da kaciya sa'adda aka kira shi ga bada gaskiya? Kada yayi kokarin bayyana kamar marar kaciya. Mutum ba shi da kaciya sa'adda aka kira ga bangaskiya? To kada ya bidi kaciya. 19Gama kaciya ko rashin kaciya ba shine mahimmin abu ba. Mahimmin abu shine biyayya da dokokin Allah.
20Kowa ya tsaya cikin kiran da yake lokacin da Allah ya kira shi ga bada gaskiya.21Kai bawa ne lokacin da Allah ya kirawo ka? Kada ka damu da haka. Amma idan kana da zarafin samun 'yanci, ka yi haka. 22Domin wanda Ubangiji ya kira shi lokacin da yake bawa, shi 'yantacce ne na Ubangiji. Hakanan kuma, wanda shike 'yantacce lokacin da aka kira shi ga bada gaskiya, Bawan Almasihu ne.23An saye ku da tsada, donhaka kada ku zama bayin mutane. 24Yan'uwa, a kowace irin rayuwa kowannenmu ke ciki lokacin da aka kira mu ga bada gaskiya, bari mu tsaya a haka.
25Game da wadanda basu taba aure ba, ba ni da wani umarni daga wurin Ubangiji. Amma ina bada ra'ayina kamar mutum wanda, ta wurin jinkan Allah, yake yardajje.26Don haka, Ina ganin saboda yamutsin dake tafe ba da jimawa ba, ya yi kyau mutum ya zauna yadda yake.
27Kana daure da mace? Kada ka nemi 'yanci daga gare ta. Baka daure da mace? Kada ka nemi auren mace. 28Amma idan ka yi aure, ba ka yi zunubi ba. Kuma idan mace marar aure ta yi aure, bata yi zunubi ba. Saidai su wadanda suka yi aure za sha wahalhalu iri-iri a yayinda suke raye, kuma ina so in raba ku da su.
29Amma wannan nike fadi ya'nuwa: lokaci ya kure. Daga yanzu, bari wadanda suke da mata suyi rayuwa kamar basu da su. 30Masu kuka su zama kamar marasa kuka, masu farinciki kamar marasa farinciki, masu sayen abubuwa kamar marasa komai. 31Wadanda suke harka da duniya kamar ba su harka da ita, domin ka'idar duniyan nan tana kawowa ga karshe.
32Ina so ku kubuta daga damuwa mai yawa. Mutum marar aure yana tunani akan al'amuran Ubangiji, yadda zai gamshe shi. 33Amma mai aure yana tunani akan al'amuran duniya, yadda za ya gamshi matarsa, 34hankalinsa ya rabu. Mace marar aure ko budurwa tana tunanin al'amuran Ubangiji, yadda za ta kebe kanta a jiki da ruhu. Amma mace mai aure tana tunanin al'amuran duniya, yadda za ta gamshi mijinta.
35Ina fadar wannan domin amfaninku ne, ba domin in takura ku ba. Na fadi wannan domin abinda ke daidai, yadda zaku bi Ubangiji ba tare da hankalinku ya rabu ba.
36Amma idan wani yana tunani da cewa baya yin abinda ya dace ga budurwarsa- idan ta wuce shekarun aure, kuma hakan ya zama dole- sai yayi abinda yake so. Ba zunubi yake yi ba. Sai suyi aure. 37Amma idan ya tsaya da karfi a zuciyarsa, idan baya shan wani matsi kuma yana iya kame kansa, har ya kudurta a zuciyarsa yayi haka, wato ya kiyaye budurwarsa da yake tashi, to hakan ya yi daidai. 38Don haka, shi wanda ya auri budurwarsa yayi daidai, sannan shi wanda ya zabi yaki yin aure yafi yin daidai.
39Mace tana a daure ga mijinta a duk tsawon rayuwarsa. Amma idan mijin ya mutu, tana da 'yanci ta auri duk wanda take so ta aura, amma a cikin Ubangiji. 40Amma a ganina, za ta fi farinciki idan za ta zauna yadda take. Kuma ina tunanin ni ma ina da Ruhun Allah.

8

1Game da abinci da ake yiwa gumakai hadaya: Mun sani cewa, "Dukanmu muna da ilimi." Ilimi ya kan kawo takama, amma kauna tana ginawa. 2Idan wani yana tunanin ya san wani abu, wannan mutumin bai rigaya ya san abinda ya kamata ya sani ba. 3Amma idan wani yana kaunar Allah, to ya san da wannan mutum.

4Game da abincin da aka yiwa gumakai hadaya: Mun san cewa, "Gunki a duniyan nan ba wani abu bane," kuma cewa" Babu wani Allah sai guda daya." 5To wata kila ma a ce wadanda ake kira alloli sun kasance, ko a cikin sama ko duniya, kamar yadda akwai wadanda ake ce dasu "alloli dabam dabam a duniya ko a sama," kamar yadda akwai "alloli da iyayengiji" da yawa. 6"Amma a wurin mu, Allah daya ne, Uban dukan duniya, daga wurinsa aka halita dukan abu, domin sa muke rayuwa, Ubangiji Yesu Almasihu daya, wanda ta wurin sa kome ya kasance, mu kuma daga wurinsa muke."
7Amma ba kowa ke da wannan ilimi ba. Shi ya sa tun da, wadan su na bauta wa gunki, kuma suna cin wannan abincin kamar abin da aka mika wa gunki. Lamirin su ya kazantu sabo da yana da rauni.
8Amma ba abinci ke bamu tagomashi a wurin Allah ba. Ko mun ci, bamu kara karbuwan mu ba, ko ba mu ci ba, ba mu rage karbuwan mu ba. 9Amma, ka yi hatara kada 'yancin ka ya zama sanadiyar tuntuben wani mai rarraunar bangaskiya. 10Anar misali, idan wani mai rarraunar lamiri ya hango ka mai ilimi, kana cin abincin da aka mika wa gunki, ai ba ka bashi kwarin gwiwa kenan yaci abincin da aka mika wa gunki ba?
11Sabili da ganewar ka akan yanayin gumaka, dan'uwa rarrauna wanda Yesu ya mutu domin sa ya hallaka. 12Saboda haka, idan ka saba wa 'yan'uwa masu raunin a lamiri, ka yi zunubi a gaban Almasihu. 13Idan abinci zai sa dan'uwa na yayi tuntube, zan huta cin nama, domin kada in jawo wa 'yan'uwana faduwa.

9

1Ni ba yantacce bane? Ni ba Manzo ba ne? Ban ga Ubangijinmu Yesu ba? ba ku ne aikin hannuna cikin Ubangiji ba? 2Idan ni ba Manzo ba ne ga wadansu, hakika ni Manzo ne a gare ku. Ai kune shedar manzanci na cikin Ubangiji.

3Ga kariya ta zuwa masu zargi na, 4Ba mu da 'yanci mu ci mu sha? 5Ba mu da 'yanci mu dauki mace mai bada gaskiya kamar sauran manzanni da Kefas da 'yan'uwan Ubangiji? 6ko ni da Barnabas ne kawai muka cancanci aiki?
7Wake aikin soja daga aljihunsa? Wake shuka gonar inabi baya ci daga 'ya'yan ta ba? Ko kuwa wake kiwon tumaki ba ya shan madarasu? 8Ina wannan zance da ikon mutum ne? Doka bata fadi haka ba?
9Gama a rubuce yake a attaura ta Musa cewa, Takarkari mai tattake hatsi kada a sa masa takunkumi. Amma shanu ne Ubangiji ke zance a kai? 10Ba don mu yake magana ba? An rubuta domin mu ne. Domin wanda yake noma, yayi cikin bege. mai tattake hatsi kuma yayi da begen samu. 11Idan mun yi shuka ta ruhaniya a rayuwarku, mai wuya ne mu girbi kayan ku na jiki?
12Idan wadansu sun mori wannan 'yanci a gurin ku, ba mu fi su cancanta ba? duk da haka bamu yi amfani da wannan 'yancin ba, maimakon haka, mun yi jimriya da duk abin da zaya hana bisharar Yesu Almasihu. 13Baku sani ba masu bauta a haikali suna samun abincinsu ne daga haikalin? Baku sani ba masu bauta a bagadi, suna da rabo daga abin da ake kawowa kan bagadin? 14Haka kuma Ubangiji ya umarta masu aikin bishara zasu ci abincinsu ta hanyar bishara.
15Amma ban yi amfani da wannan 'yanci ba, ba kuma ina rubuta maku domin ayi mani wani abu bane, na gwanmace in mutu maimakon wani ya hana ni wannan fahariya. 16Ko nayi shelar bishara, ba ni da dalilin fahariya domin ya zama dole in yi. Kaito na idan ban yi shelar bishara ba
17Idan na yi hidimar nan da yardar zuciyata, ina da sakamako, idan kuma ba da yaddar zuciyata ba, harwa yau akwai nauwaya akai na. 18To menene sakamako na? shi ne in yi shelar bishara kyauta, da haka ba zan yi amfani the 'yanci na cikin bishara ba
19Ko da shike ni 'yantacce ne ga duka, amma na mai da kaina bawan kowa domin in ribato masu yawa, 20Ga yahudawa, na zama bayahude, domin in ribato yahudawa, ga wadanda ke karkashin shari'a, na maishe kaina kamarsu, domin in ribato wadanda ke karkashinta. Na aikata wannan ko da shike bana karkashin shari'a
21Ga wadanda basu karkashin shari'a, na maishe kaina kamar su. Ko da shike ban rabu da shari'ar Allah ba. Amma ina karkashin dokar Almasihu. Na yi haka ne domin in ribato wadanda ba sa karkashin shari'a. 22Ga marasa karfi, na maishe kaina kamar marar karfi, domin in ribato raunana. Na mai da kaina dukan abu ga dukan mutane domin in sami zarafin da zan ribato wadansu zuwa ceto. 23Ina dukan abu sabili da bishara, domin kuma in sami albarkar da ke cikinta
24Baku sani ba mutane da dama suna shiga tsere amma daya neke karbar sakamakon, saboda haka ku yi tsere domin ku karbi sakamako. 25Dan wasa yana motsa jiki da kame kansa. Yana yi saboda ya karbi wannan sakamako mai lalacewa, amma muna tsere domin mu karbi sakamako marar lalacewa. 26Saboda haka ba na tsere ko fada haka nan kamar mai bugun iska. 27Amma ina matse jiki na in maishe shi bawa, kada bayan na yi wa wadansu wa'azi ni kuma a karshe a fitar da ni.

10

1Ina son ku sani, 'yan'uwa, cewa ubaninmu duka suna karkashin gajimarai kuma sun bi ta cikin teku. 2Dukansu an yi masu baftisma cikin gajimarai da kuma teku, 3kuma dukansu sun ci abincin ruhaniya iri daya. 4Dukansu sun sha abin sha na ruhaniya iri daya. Gama sun sha daga wani dutsen ruhaniya da ya bisu, kuma wannan dutsen Almasihu ne.

5Amma Ubangiji bai ji dadin yawancinsu ba, saboda haka gawawakin su suka bazu a jeji. 6Wadan nan al'amura, an rubuta mana su domin muyi koyi da su, kada mu yi sha'awar miyagun ayyuka kamar yadda suka yi.
7Kada ku zama masu bautar gumaka kamar yadda wadansun su suka yi. Wannan kamar yadda aka rubuta ne, "Mutanen sukan zauna su ci su sha kuma su tashi suyi wasa." 8Kada mu shiga zina da faskanci kamar yadda yawancin su suka yi, a rana guda mutane dubu ashirin da uku suka mutu.
9Kada mu gwada Almasihu kamar yadda yawancinsu suka yi, macizai suka yi ta kashe su. 10kada kuma ku zama masu gunaguni kamar yadda suka yi, suka yi ta mutuwa a hannun malaikan mutuwa.
11Wadannan abubuwa sun faru dasu ne a matsayin misalai a garemu. An rubuta su domin gargadinmu - mu wadanda karshen zamanai yazo kanmu. 12Saboda haka, bari duk wanda yake tunanin shi tsayyaye ne, to yayi hattara kada ya fadi. 13Babu gwajin da ya same ku wanda ba a saba da shi ba cikin dukan mutane. A maimako, Allah mai aminci ne. Da ba zaya bari ku jarabtu ba fiye da iyawarku. Tare da gwajin zai tanadar da hanyar fita, domin ku iya jurewa.
14Saboda haka ya kaunatattu na, ku guji bautar gumaka. 15Ina magana da ku kamar masu zurfin tunani, domin ku auna abin da ni ke fadi. 16Kokon albarka da muke sa wa albarka, ba tarayya bane cikin jinin Almasihu? Gurasa da muke karyawa ba tarayya bane cikin jikin Almasihu? 17Domin akwai gurasa guda, mu da muke dayawa jiki daya ne. Dukanmu munci daga gurasa daya ne.
18Dubi mutanen Isra'ila: ba wadanda ke cin hadayu ke da rabo a bagadi ba? 19Me nake cewa? gunki wani abu ne? Ko kuma abincin da aka mika wa gunki hadaya wani abu ne?
20Amma ina magana game da abubuwan da al'ummai suke hadaya, suna wa aljannu ne hadaya ba Allah ba. Ba na son kuyi tarayya da al'janu! 21Ba zaku sha daga kokon Ubangiji ku kuma sha na Al'janu ba, ba za kuyi zumunta a teburin Ubangiji ku yi a na Al'janu ba. 22Ko muna so mu sa Ubangiji kishi ne? Mun fi shi karfi ne?
23"Komai dai dai ne," amma ba komai ke da amfani ba, "Komai dai dai ne," amma ba komai ke gina mutane ba. 24Kada wani ya nemi abinda zaya amfane shi. A maimako, kowa ya nemi abinda zaya amfani makwabcinsa.
25Kana iya cin duk abin da ake sayarwa a kasuwa, ba tare da tamboyoyin lamiri ba. 26Gama "duniya da duk abin da ke cikin ta na Ubangiji ne."27Idan marar bangaskiya ya gayyace ka cin abinci, kana kuma da niyyar zuwa, ka je ka ci duk abinda aka kawo maka, ba tare da tamboyoyin lamiri ba.
28Amma idan wani ya ce maka, "Wannan abinci an yi wa gumaka hadaya da shi ne" To kada ka ci. Wannan za ka yi ne saboda wanda ya shaida maka, da kuma lamiri (gama duniya da dukan abinda ke cikin ta na Ubangiji ne). 29Ba ina nufin lamirin ka ba, amma lamirin wanda ya fada maka. Don me za a hukunta 'yanci na domin lamirin wani? 30Idan na ci abincin tare da bada godiya, don mi za a zage ni don abin da na bada godiya a kansa?
31Saboda haka, ko kana ci ko kana shi, ka yi komai domin daukakar Allah. 32Kada ka zama sanadiyyar tuntube, ga Yahudawa, ko Helenawa, ko ikilisiyar Allah. 33Na yi kokari in farantawa dukan mutane rai cikin dukan abubuwa. Ba riba nake nema wa kaina ba, amma domin kowa. Na yi wannan ne domin su sami ceto.

11

1Ku yi koyi da ni, kamar yadda nake koyi da Almasihu. 2Yanzu ina yaba maku ne, don kuna tunawa da ni cikin abu duka. Ina kuma yaba maku wajen bin al'adun da na ba ku daidai yadda na ba ku. 3Amma fa ina son ku fahimta da cewa, shugaban kowane mutum Almasihu ne, shugaban kowace mace mutumin ne, shugaban Almasihu Allah ne. 4Kuma duk mutumin da ya yi addu'a ko annabci kansa a rufe, ya wulakanta shugabansa.

5Amma duk macen da ta yi addu'a ko annabci kanta a bude, ta wulakanta shugabanta. Gama yayi dai dai da idan tayi aski. 6Gama idan mace ba zata rufe kanta ba, to ta yanke gashinta ya zama gajere. Idan abin kunya ne mace ta yanke gashinta ko ta aske kanta, bari ta rufe kanta.
7Bai kamata na miji ya rufe kansa ba, tun da yake shi siffa ne da daukakar Allah. Amma mace daukakar namiji ce. 8Don kuwa namiji ba daga jikin mace yake ba. A maimako, matar daga jikin namiji take.
9Ba a kuma halicci namiji don mace ba. A maimako, an halicci mace don namiji. 10Shi ya sa mace za ta kasance da alamar iko a kanta, saboda mala'iku.
11Duk da haka, a cikin Ubangiji, mace ba a rabe take da namiji ba, haka kuma namiji ba a rabe yake da mace ba. 12Kamar yadda mace take daga namiji, haka ma namiji kuma haihuwar mace ne. Amma dukkan abubuwa daga Allah suke.
13Ku hukunta da kanku: Daidai ne mace ta yi addu'a ga Allah kanta a bude? 14Ashe, ko dabi'a bata nuna maku cewa abin kunya ne namiji, ya kasance da dogon gashi ba? 15Ba dabi'a ta koya maku cewa idan mace tana da dogon gashi, daukakar ta ne ba? Gama domin rufewa aka yi mata baiwar gashin. 16To idan wani yana da niyyaryin gardama game da wannan, mu dai bamu da wata al'adar, ikilisiyoyin Allah kuma haka.
17Amma game da umarnin dake biye, ban yaba maku ba, taruwarku ba ta kirki ba ce, ta rashin gaskiya ce. 18Farko dai sa'adda kuke, taron ikklisiya, na ji har akwai rarrabuwa tsakaninku, har na fara amincewa da maganar. 19Dole ne a sami tsattsaguwa a tsakaninku, don a iya gane wadanda suke amintattu a cikinku.
20Domin, in kun taru a wuri daya, ba jibin Ubangiji kuke ci ba! 21Ya yin da kuke ci, kowa na cin abincinsa ne kamin sauran Wani yana jin yunwa, wani kuma ya zarin ci, har ya bugu. 22Baku da gidajen da zaku ci ku sha, kuna raina ikkilisiyar Allah, kuna kuma wulakanta wa wadanda basu da komai? To, me zan ce maku? Yaba maku zan yi? Ba zan yaba maku ba akan wannan.
23Amma abin da na karba a gun Ubangiji shi nake baku cewa Ubangiji Yesu, a daren da aka bashe shi ya dauki gurasa. 24Bayan ya yi godiya, sai ya kakkarya ya ce, "wanna shi ne jikina wanda yake saboda ku, ku yi domin tunawa da ni."
25Ta wannan hanya kuma, sai ya dauki kokon, ya ce, "kokon nan na sabon alkawari ne, da aka tabbatar da shi da cikin jinina. Ku yi haka kuna sha don tunawa da ni." 26Duk sa'adda kuke cin gurasar nan, kuna kuma sha cikin kokon nan, kuna bayyana mutuwar Ubangiji ke nan, har sai ya dawo.
27Saboda haka duk wanda ya ci gurasar nan, ko ya sha a cikin kokon nan, na Ubangiji da rashin cancanta, ya yi laifin wulakanta jikin Ubangiji da jininsa. 28Sai kowa ya fara auna kansa, kafin ya ci gurasar, ya kuma sha a cikin kokon nan. 29In kowa ya ci, ya sha ba tare da rarrabewa da jikin Ubangiji ba, lalle ya jawowa kansa hukunci, ta wurin ci da sha da ya yi. 30Shi ya sa da yawa a cikin ku suke raunana, kuma suna fama da rashin lafiya, har ma wasun ku da dama suka yi barci.
31Amma, in mun auna kanmu, ba a za a hukunta mu ba. 32In kuwa Ubangiji ne ya ke hukunta mu, To, muna horuwa ke nan, don kada a kayar damu tare da duniya.
33Saboda haka, ya ku 'yan'uwana, idan kuka tattaru don cin abinci, sai ku jira juna. 34Idan kuwa wani yana jin yunwa, ya ci a gida, kada ya zama taronku ya jawo maku hukunci. Batun sauran abubuwan da kuka rubuta kuwa, zan ba da umarni a kai sa'ad da na zo.

12

1Game da baye bayen Ruhu Mai Tsarki 'yan'uwa, bana so ku zama da jahilci.2Kun san cewa lokacin da ku ke al'ummai, an rude ku da alloli marasa magana ta hanyoyi dabam dabam marasa kan gado. 3Saboda haka ina so ku sani babu wanda ya ke magana da Ruhun Allah da zai ce, "Yesu la'ananne ne." Babu kuma wanda zaya ce, "Yesu Ubangili ne," sai dai ta Ruhu Mai Tsarki.

4Akwai bay bye iri iri, amma Ruhu daya ne. 5Akwai hidimomi iri iri, amma Ubangiji daya ne. 6Akwai aikace aikace iri iri, amma Allah daya ke bayyanawa kowane mutum yadda zai aiwatar da su.
7To ga kowanne an bayar da ikon nuna ayyukan Ruhu a fili domin amfanin kowa. 8Ga wani ta wurin Ruhu an bayar da baiwar hikima, kuma ga wani kalmar sani ta wurin Ruhu daya.
9Ga wani an ba shi baiwar bangaskiya ta wurin Ruhun nan, ga wani kuwa an ba shi baiwar warkarwa ta wurin wannan Ruhun. 10Ga wani yin ayyukan iko, ga wani kuwa annabci. Ga wani kuwa an ba shi baiwar bambance ruhohi, ga wani harsuna daban daban, kuma ga wani fassarar harsuna. 11Dukan wadannan Ruhu daya ne ya ke iza su, ya kuma rarraba baye bayen ga kowannen su yadda ya nufa.
12Kamar yadda jiki daya ne amma da gabobi da yawa kuma duk gabobin na jiki daya ne, haka nan Almasihu yake. 13Gama ta Ruhu daya aka yi wa kowa baftisma cikin jiki daya, ko Yahudawa ko al'ummai, ko bayi ko 'ya'ya, dukan mu kuwa an shayar da mu Ruhu daya.
14Gama jiki ba daya ba ne sungun, amma gabobi ne da yawa. 15Idan kafa ta ce, "tun da dai ni ba hannu ba ne to ni ba fannin jikin bane," wannan baya rage masa matsayin sa a jikin ba. 16Kuma da kunne zaya ce, '"Da yake ni ba ido ba ne, ai, ni ba gabar jiki ba ne," fadar haka ba za ta raba shi da zama gabar jikin ba. 17Idan dukan jikin ya kasance ido ne da me za a ji? Da dukan jikin kunne ne, da me za a sunsuna?
18Amma Allah ya shirya gabobin jiki bisa ga tsarin sa. 19Amma da duk jiki gaba daya ce, da ina jikin zai kasance? 20Ga shi akwai gabobi da yawa, kuma jiki daya ne.
21Ba da ma ido ya fadawa hannu, "Bana bukatar ka," ko kuma kai ya fadawa kafafu, "Ba na bukatar ku." 22Amma, sai ma gabobin da ake gani kamar raunannu su ne masu humimmanci, gabobin jiki kuwa da ake gani kamar sun kasa sauran daraja, mu kan fi ba su martaba. 23Ta haka gabobinmu marasa kyan gani, akan kara kyautata ganinsu. Gabobin mu masu kyan kuma ba sai an yi masu ado ba. 24Amma Allah ne da kansa ya hada jiki, yana bada mafificiyar martaba ga kaskantacciyar gaba.
25Yayi haka ne domin kada a sami tsattsaguwa a cikn jikin, amma domin gabobin su kula da juna da matsananciyar lura. 26Kuma idan gaba daya na wahala, dukan gabobin suna wahala tare. ko kuma idan an girmama gaba daya, dukan gabobin na farin ciki tare. 27Yanzu ku jikin Almasihu ne, saboda haka kuma kowannen ku gabarsa ne.
28A cikin ikilisiya, Allah ya sa wasu su zama, na farko manzanni, na biyu annabawa, na uku masu koyarwa, sa'an nan sai masu yin ayyukan iko, sai masu aikin warkarwa, da masu bayar da taimako, da masu aikin tafiyar da al'amura, da masu harsuna daban daban. 29To kowa manzo ne? ko kuwa duka annabawa ne? ko kuma duka masu koyarwa ne? Kowa ne ke yin manyan ayyukan iko?
30Ko kuwa dukan su ne suke da baiwar warkarwa? Dukan su ne ke magana da harsuna? ko kuma dukan su ne ke fassara harsuna? 31Amma bari ku himmantu ga neman baiwa mafi girma. Kuma zan nuna maku wata hanya mafificiya.

13

1Koda ya zamanto ina magana da harsunan mutane, har ma da na mala'iku, amma kuma ba ni da kauna, na zama kamar kararrawa mai yawan kara, ko kuge mai amo. 2Ko da ya zamanto ina da baiwar annabci kuma na fahimci dukkan boyayyar gaskiya, da dukkan ilimi, ko ina da matukar bangaskiya, har ma zan iya kawar da duwatsu. muddin ba ni da kauna, ni ba komai ba ne. 3Ko da ya zamanto na bayar da dukan mallakata domin a ciyar da matalauta, in kuma mika jikina domin a kona. Amma in ba ni da kauna, ban sami ribar komai ba. (Na bayar da jikina ne domin inyi fahariya).

4Kauna na da hakuri da kirki. kauna bata kishi ko fahariya. kauna ba ta girman kai 5ko fitsara. Bata bautar kanta. Bata saurin fushi, kuma bata ajiyar lissafin laifuffuka. 6Bata farin ciki da rashin adalci. A maimako, tana farin ciki da gaskiya. 7Kauna tana jurewa cikin dukan abubuwa, tana gaskata dukan abubuwa, tana da yarda game da dukan abubuwa, tana daurewa dukan abubuwa.
8Kauna ba ta karewa. Idan akwai anabce anabce, zasu wuce. Idan akwai harsuna, zasu bace. Idan akwai ilimi, zaya wuce. 9Domin muna da sani bisa - bisa kuma muna anabci bisa - bisa. 10Sa'adda cikakke ya zo, sai marar kammalar ya wuce.
11Da nake yaro, nakan yi magana irinta kuruciya, nakan yi tunani irin na kuruciya, nakan ba da hujjojina irin na kuruciya. Da na isa mutum na bar halayen kuruciya. 12Gama yanzu muna gani sama - sama kamar ta madubi, amma a ranar fuska da fuska, yanzu na sani bisa - bisa, amma a lokacin zan sami cikakken sani kamar yadda aka yi mani cikakken sani. 13To, a yanzu abubuwan nan uku sun tabbata: bangaskiya, da gabagadi mai zuwa, da kuma kauna, amma duk mafi girma a cikinsu ita ce kauna.

14

1Ku dafkaci kauna kuma ku himmatu domin baye bayen ruhaniya, musamman domin kuyi anabci. 2Domin wanda yake magana da harshe bada mutane yake magana ba amma da Allah. domin babu mai fahimtarsa saboda yana zancen boyayyun abubuwa ciki Ruhu.3Amma wanda yake anabci da mutane yake magana domin ya gina su, ya karfafa su, kuma ya ta'azantar dasu. 4Wanda yake magana da wani harshe, kansa yake ginawa, amma mai yin annabci kuwa, ikilisiya yake ginawa.

5To, fatana ace dukan ku kuna magana da harsuna. Amma fiye da hakama, fatana ace kuyi anabci. Wanda yake anabci yafi wanda yake magana da harsuna (sai dai idan wani ya fassara domin ikilisiya ta ginu). 6Amma yanzu, 'yan'uwa, in na zo wurin ku ina magana da harsuna, ta yaya zaku karu dani? ba zaya yiwu ba, sai idan nayi maku magana da wahayi, ko sani, ko anabci, ko koyarwa.
7Idan kayan kida marasa rai suna fitar da sauti - kamar su sarewa da algaita - kuma basu fitar da amo daban daban, ta yaya wani zaya san irin amon da sarewar da algaitar suke kadawa? 8Domin idan aka busa kaho da sauti marar ma'ana, ta yaya wani zaya san lokacin da ya dace ya shirya zuwa yaki? 9Haka yake game da ku. Idan kuka furta zance marar ma'ana, ta yaya wani zaya fahimci abinda kukace? zaku yita magana, kuma babu wanda zaya fahimce ku.
10Babu shakka akwai harsuna daban daban a duniya, kuma babu wanda baya da ma'ana. 11Amma idan ban san ma'anar wani harshe ba, zan zama bare ga mai maganar, kuma mai maganar zaya zama bare a gareni.
12haka yake gare ku. Tun da kuna da dokin bayyanuwar Ruhu, ku himmatu da habaka cikin gina ikilisiya. 13To wanda yake magana da harshe yayi addu'a domin ya iya fassarawa. 14Domin idan nayi addu'a da harshe, ruhuna yayi addu'a, amma fahimtata bata karu ba.
15To, me zan yi? Zan yi addu'a da ruhuna, in kuma yi addu'a da fahimtata. Zan yi raira waka da ruhuna, kuma in raira waka da fahimtata. 16In ba haka ba, idan ka yi yabon Allah da ruhu kawai, ta yaya wanda yake waje zai ce, "Amin" a kan godiyar da kake yi in bai san abin da kake fada ba?
17Babu shakka kayi godiya sosai, amma wanin baya ginu ba. 18Nagodewa Allah ina magana da harsuna fiye da ku duka. 19Duk da haka dai a taron ikilisiya na gwammace in yi magana da kalmomi biyar cikin fahimta saboda inganta wadansu fiye da dubu goma da harshe.
20'Yan'uwa, kada ku zama yara cikin tunani, sai dai a wajen aikin mugunta, ku yi halin jarirai, amma a tunaninku ku girma. 21A rubuce yake a shari'a cewa, "zan yi magana da mutanen nan ta wurin mutane masu bakin harsuna, da kuma lebunan baki. Duk da haka kuwa ba za su saurare ni ba", in ji Ubangiji.
22Amma harsuna alamu ne, ba ga masu bada gaskiya ba, sai dai ga marasa ba da gaskiya. Annabci kuwa alama ce ga masu ba da gaskiya, amma ba don marasa bangaskiya ba. 23Saboda haka, in dukan ikilisiya ta taru, kowa kuwa yana magana da wasu harsuna, wadansu na waje da kuma marasa ba da gaskiya suka shigo, ashe, ba sai su ce kun haukace ba ba?
24In kuwa kowa yana yin annabci, wani kuma marar ba da gaskiya ko wani daga waje ya shigo, maganar kuwa zata ratsa shi. Za a ma hukanta shi a kan maganar, 25asiran zuciyarsa kuma za su tonu. Sakamokon haka, sai ya fadi ya yi wa Allah sujada, zaya furta cewa lallai Allah yana tare da ku.
26Sai me kuma 'yan'uwa? idan kuka tattaru, wani yana da zabura, koyarwa, wahayi, harshe, ko fassara. Kuyi komai domin gina ikilisiya. 27Idan wani yayi magana da harshe, bari a sami mutum biyu ko uku a yawansu, kuma kowa yayi daya bayan daya. Sai wani ya fassara abinda aka fada. 28Amma idan babu wanda zaya fassara, bari dukansu suyi shiru a ikilisiya. Bari kowa yayi wa kansa maganar a gida shi kadai da kuma Allah.
29Bari annabawa biyu ko uku suyi magana, bari sauran su saurara tare da bambance abinda ake fada. 30Idan kuma anba wani fahimta wanda yana zaune a cikin sujadar, bari wanda yake ta magana kafin yanzu yayi shiru.
31Dukanku kuna iya yin annabci daya bayan daya, domin kowannen ku yayi koyi, a kuma samu karfafawa. 32Gama ruhohin annabawa suna karkashin annabawa, 33domin Allah ba Allahn rudu ba ne, na salama ne. Haka yake kuwa a duk ikllisiyoyin masu bangaskiya.
34Mataye suyi shiru a ikilisiyoyi. Domin ba a basu dama ba suyi magana. A maimako, su zama masu sadaukar da kansu, kamar yadda doka ta ce. 35Idan akwai abinda suke so su koya, bari su tambayi mazajen su a gida. Domin abin kunya ne mace tayi magana a ikilisiya. 36Daga wurinku maganar Allah ta zo ne? ko kuwa a gare ku kadai ta iso?
37In wani yana zaton shi ma annabi ne, ko kuwa mai ruhaniya, to, sai ya fahimta, abin nan da nake rubuta maku umarni ne daga wurin Ubangiji. 38In kuwa wani ya ki kula da wannan, shi ma kada a kula da shi.
39Saboda haka, 'yan'uwa, ku yi marmarin yin annabci sosai, sa'an nan kada ku hana kow yin magana da harsuna. 40Sai dai a yi komai ta hanyar da ta dace bisa ga tsari.

15

1Yanzu ina tunashshe ku 'yan'uwa, game da bisharar nan da nake shelarwa, wadda kuka karba kuke kuma dogara da ita. 2Da wannan bishara aka yi maku ceto, idan kuka rike wa'azi da na yi maku da karfi, sai in dama kun gaskanta a banza.

3Domin na baku muhimmin sako kamar na farko da na karba: cewa Almasihu ya mutu domin zunubanmu, bisa ga nassosi, 4cewa kuma an bizne shi, ya kuwa tashi daga matattu a rana ta uku bisa ga nassosi.
5Cewa kuma ya bayyana ga Kefas, sa'an nan ga sha biyun. 6Daga nan ya bayyana ga 'yan'uwa sama da dari biyar a lokaci guda. Wadanda mafi yawan su na da rai har yau, amma wasun su sun yi barci. 7Daga nan ya bayyana ga Yakubu, da kuma ga manzannin duka.
8A karshe, sai ya bayyana a gare ni, kamar dan da aka haifa bakwaini. 9Gama ni ne mafi kankanta a cikin manzanni. Ban cancanci a kira ni manzo ba, domin na tsanantawa ikklisiyar Allah.
10Amma saboda alherin Ubangiji ina matsayin da nake a yau, kuma alherin sa da ke ciki na ba a banza yake ba. A maimako, nayi aiki tukuru fiye da su duka. Amma duk da haka ba ni bane, amma alherin Allah da ke tare da ni. 11Saboda haka ko nine ko Su, haka mukayi wa'azin, haka kuma kuka gaskata.
12To idan anyi shela a matsayin cewa Yesu ya tashi daga matattu, tayaya wadansunku su ke cewa babu tashin matattu? 13Amma idan babu tashin matattu, Almasihu ma ai ba a tashe shi ba kenan. 14idan kuwa ba a tashi Almasihu ba, wa'azin mu ya zama banza kenan, haka kuma bangaskiyar ku ta zama banza.
15Mun kuma zama shaidun karya game Allah kenan, muna shaida akan Allah cewa ya tashi Almasihu daga matattu alhali ko bai tashe shi ba. 16Domin idan babu tashin matattu, kai, ko Almasihu ma ba a tashe shi ba kenan. 17Idan har ba a tashi Almasihu ba, bangaskiyar ku a banza take, har yanzu kuma, kuna cikin zunuban ku.
18To wadanda suka mutu cikin Almasihu kuma sun hallaka kenan, 19idan a wannan rayuwa ce kadai muke da bege cikin Almasihu, to cikin dukkan mutane munfi kowa zama abin tausayi.
20Amma yanzu, Almasihu ya tashi daga matattu, wanda ya sa shi ya zama nunar fari cikin tashi daga matattu. 21Domin yadda mutuwa ta shigo duniya ta hanyar mutum guda, hakkan nan ma tashi daga matattu.
22Gama kamar yadda a cikin Adamu duka suka mutu, haka kuma a cikin Almasihu za a rayar da duka. 23Amma kowanne da tsarinsa: Almasihu, nunan fari, sannan su wadanda ke na Almasihu za a rayar da su lokacin zuwansa.
24Sa'an nan karshen zai gabato, lokacin da Almasihu zai mika mulkin ga Allah Uba. sa'an nan ne zaya kawar da dukkan mulki, martaba da iko. 25Gama mulkinsa zai habaka har sai ya sa dukkan makiyansa a karkashin sawayen sa. 26Mutuwa kuwa, ita ce makiyi na karshe da za'a hallaka.
27Domin " yasa dukkan komai a karkashin ikonsa," Amma da aka ce" yasa dukkan komai a karkashin ikonsa," a sarari yake cewa wannan baya hada da wanda yasa dukan komai a karkashin ikonsa ba. 28Idan dukan abu na karkashin mulkinsa, to Dan da kansa zaya kasance a karkashin ikon shi wanda yasa komai a karkashin ikonsa. Wannan zaya kasance ne saboda Allah Uba ya zama dukkan komai cikin dukkan komai.
29ko kuma me zai faru da wadanda ake yi wa baftisma domin matattu? Idan kuwa babu tashin matattu sam sam, ina amfanin yi masu baftisma domin su? 30Kuma me yasa muke cikin hadari kowace sa'a?
31Ina mutuwa kullum. Wannan nake furtawa ta wurin fahariya, 'yan'uwa, wadda nake da ita cikin Almasihu Yesu Ubangijinmu. 32Menene ribata, a idanun mutane, idan nayi kokowa da bisashe a Afisa, idan babu tashin matattu? "bari mu ci mu sha, domin gobe zamu mutu."
33Kada fa a yaudare ku, domin " tarayya da mugaye takan bata halayen kirki." 34"Ku natsu! kuyi zaman adalci! kada ku cigaba da zunubi. Domin wasunku basu da sanin Allah. Ina fadar wannan domin in baku kunya.
35Amma wani zaya ce, "Yaya za'a yi tashin matattu? Wane irin jiki kuma zasu tashi da shi? 36Ku jahilai ne sosai! Abinda ka shuka ba zaya fara girma ba sai ya mutu.
37Abinda ka shuka ba jikin da zaya kasance bane, amma kwayar irin ne kawai. Wanda zaya zama alkama ko wani abu daban. 38Amma Allah zaya bashi jiki yadda ya zaba, ga kowane kwayar iri da nashi jikin. 39Ba duka jiki ne yake iri daya ba. A maimako, akwai jiki irin na mutane, akwai kuma wani irin na dabbobi, kuma wani jikin irin na tsuntsaye, kuma da irin na kifi.
40Akwai kuma jikina na samaniya da jikina na duniya. Amma daukakar jikin samaniya wata daban ce kuma daukakar jikin duniya daban ce. 41Akwai daukaka irin ta rana, da kuma wata daukakar irin ta wata, da kuma wata daukakar irin ta taurari. Domin wani tauraron ya bambanta da wani wajen daukaka.
42Haka yake a tashin matattu. Abinda aka shuka mai lalacewa ne, wanda aka tayar marar lalacewa ne. 43An shuka shi cikin rashin daraja; an tayar da shi cikin daukaka. An shuka shi cikin rauni; an tayar da shi cikin iko. 44An shuka shi jiki na zahiri; an tayar da shi jiki na ruhaniya. Idan akwai jiki na zahiri, to akwai jiki na ruhaniya.
45Haka kuma aka rubuta, "Adamu na farko ya zama rayayyen taliki." Adamu na karshe ya zama Ruhu mai bayar da rai. 46Amma na ruhaniyar ba shine ya fara zuwa ba amma na zahirin, daga nan na ruhaniyar.
47Mutumin farkon ai daga turbaya ya fito, wato na duniya. Amma shi na biyun daga sama yake. 48kamar yadda mutumin ya fito daga turbaya haka ma wadanda aka halitta da turbaya. kamar yadda mutumin yake daga sama haka ma wadanda ke na sama. 49Kamar yadda muke dauke da jiki mai kamannin turbaya, haka ma zamu kasance da kamannin mutumin sama.
50To wannan na fada, 'yan'uwa, cewa nama da jini ba za su gaji mulkin Allah ba. Haka kuma mai lalacewa ba za ya gaji marar lalacewa ba. 51Duba! ina gaya maku asirtacciyar gaskiya: Ba dukanmu zamu mutu ba, amma dukanmu za a canza mu.
52Za a canza mu nan da nan, cikin keftawar ido, a kaho na karshe. Domin za a busa kaho, kuma za a tada matattu marasa lalacewa, kuma za a canza mu. 53Domin wannan jiki mai lalacewa dole ya sanya jiki marar lalacewa, kuma wannan jiki mai mutuwa dole ya sanya marar mutuwa.
54Amma idan wannan jiki mai lalacewa ya sanya marar lalacewa, kuma wannan jiki mai mutuwa ya sanya marar mutuwa, sai abinda aka rubuta ya cika, "An hadiye mutuwa cikin nasara." 55"Mutuwa, ina nasararki? Mutuwa, ina dafinki?"
56Gama dafin mutuwa zunubi ne, kuma ikon zunubi shari'a ce. 57Amma godiya ga Allah, wanda ya bamu nasara ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu!
58Saboda haka, ya ku 'yan'uwana kaunatattu, ku dage kuma kada ku jijjigu. Ko yaushe ku habaka da aikin Ubangiji, domin kun san cewa aikinku cikin Ubangiji ba a banza yake ba.

16

1Yanzu game da zancen tattara gudunmuwa ga masu bi, kamar yadda na umurci ikilisiyun Galatiya, haka za ku yi. 2A ranar farko ga mako, kowannen ku ya ajiye wani abu, yana tarawa bisa ga iyawarku. Ku yi haka don in na zo ba sai an tattara ba.

3Sa'adda na zo, zan aiki duk wadanda kuka yarda da su da wasiku don su kai sakonku Urushalima. 4Sannan idan ya dace nima in tafi, sai su tafi tare da ni.
5Zan zo wurinku sa'adda na ratsa Makidoniya. Domin zan ratsa ta makidoniya. 6Meyuwa in jima a wurinku, har ma in yi damuna, domin ku taimaka mani game da tafiyata, duk inda za ni.
7Gama ba na so in yi maku gani na gajeren lokaci. Don ina so in dau lokaci tare da ku, idan Ubangiji ya yarda. 8Amma zan tsaya Afisus har ranar Fentikos. 9Gama an bude mani kofa mai fadi, kuma akwai magabta da yawa.
10Sa'adda Timoti ya zo, ku tabbata ya sami sakewa acikinku, tun da aikin Ubangiji yake yi kamar yadda nake yi. 11Kada fa kowa ya rena shi. Ku tabbata kun sallame shi lafiya, domin ya komo gare ni, don ina duban hanyarsa tare da yan'uwa. 12Game da zancen dan'uwanmu Afollos kuwa, na karfafa shi ya ziyarce ku tare da 'yan'uwa. Sai dai baya sha'awar zuwa yanzu. Amma zai zo sa'adda lokaci ya yi.
13Ku zauna a fadake, ku tsaya daram cikin bangaskiya, kuna nuna halin maza, ku yi karfin hali. 14Bari dukan abinda kuke yi ayi shi cikin kauna.
15Kun dai sani iyalin gidan Sitefanas su suka fara tuba a Akaya, kuma sun bada kansu ga yi wa masu bi hidima. Yanzu ina rokonku, 'yan'uwa, 16kuyi biyayya da irin wadannan mutane da duk wanda ke taimakawa a cikin aikin, yana kuma fama tare da mu.
17Na yi farinciki da zuwan Sitefanas, da Fartunatas, da Akaikas. Sun debe mini kewarku. 18Gama sun wartsakar da ruhuna da naku kuma. Don haka, Sai ku kula da irin wadannan mutane.
19Ikilisiyoyin kasar Asiya suna gaishe ku. Akila da Bilkisu, tare da ikilisiyar da take taruwa a gidansu, suna gaishe ku cikin Ubangiji. 20Dukan 'yan'uwa masu bi na gaishe ku. Ku gaida juna da sumba maitsarki.
21Ni Bulus, nake rubuta wannnan da hannuna. 22Duk wanda ba ya kaunar Ubangiji bari ya zama la'ananne. Ubangijinmu, Ka zo! 23Alherin Ubangiji Yesu ya kasance tare da ku. 24Bari kaunata ta kasance tare da ku duka a cikin Almasihu Yesu. 1


1Copiesan copiesan mahimmanci da tsoffin kwafin Girkanci da wasu tsoffin fassarorin suna da Amin a ƙarshen aya ta 24. Amma da yawa tsoffin kwafin Girkanci, da tsoffin fassarorin da yawa, ba su da Amin a karshen.

2 Korantiyawa

1

1Bulus, manzon Almasihu Yesu ta wurin nufin Allah, da kuma Timoti dan'uwan mu, zuwa ga Ikilisiyar Allah da ke a Korantus, da kuma dukan 'yan'uwa da ke yankin kasar Akaya. 2Bari alheri ya kasance tare da ku da kuma salama ta Allah Ubanmu da kuma Ubangiji Yesu Almasihu.

3Bari yabo ya tabbata ga Allah da kuma Uba na Ubangijinmu Yesu Almasihu. Shine Uba na dukan jiyejiyenkai, da kuma Allah na dukan ta'aziya. 4Allah yana ta'azantar da mu a cikin dukan wahalarmu, domin mu iya ta'azantar da wadanda ke cikin kowace wahala. Muna ta'azantar da wasu da irin ta'aziyar da Allah ke ta'azantar da mu.
5Gama kamar yadda wahalhalun Almasihu suka karu domin mu, haka kuma ta'aziyarmu ta yawaita cikin Almasihu. 6Amma fa idan muna shan wuya, domin ta'aziyarku ne da cetonku. Haka kuma in mun ta'azantu, domin ta'aziyarku ne. Ta'aziyarku tana aiki ne sosai yayinda kuka jure da irin shan wuyar da mu ma muke sha. 7Kuma gabagadinmu game da ku tabbatacce ne. Mun kuwa sani kamar yadda kuke tarayya cikin shan wahalhalun, haka kuma za ku yi tarayya cikin ta'aziyyar.
8Gama ba mu so ku rasa sani, 'yan'uwa, game da tsananin da ya same mu a Asiya. An murkushe mu gaba daya har fiye da karfin mu, har ma mun fidda zuciya za mu rayu. 9Hakika, mun ji hukuncin mutuwa akan mu. Amma wannan ya faru ne domin kada mu dogara ga kanmu, sai dai ga Allah, wanda ke tada matattu. 10Ya kubutar da mu daga wannan mummunan hatsari na mutuwa, kuma zai sake kubutar da mu. Mun kafa begenmu gare shi cewa zai sake kubutar da mu.
11Zai aikata wannan yayinda kuka taimake mu da addu'ar ku. Sa'an nan da dama za su bada godiya a madadin mu don tagomashin alheri da aka yi mana ta wurin addu'o'in mutane masu yawa.
12Muna kuwa alfahari da haka: wato shaidar lamirinmu. Gama da kyakkyawan nufi da aminci da ke zuwa daga Allah muka tafiyar da rayuwarmu a Duniya. Mun yi wannan ne musamman tare da ku-ba kuwa cikin hikimar Duniya ba, amma ta wurin alherin Allah. 13Bamu rubuta maku abinda ba za ku iya karantawa ko fahimta ba. Ina fata za ku fahimce mu baki daya, 14kamar yadda kuka fahimce mu kadan yanzu. Daganan a ranar Ubangijinmu Yesu za mu zama dalilinku na alfahari, kamar yadda za ku zama namu.
15Saboda gabagadin da nake da shi game da haka, naso in zo gare ku da farko, domin ku amfana da ziyara sau biyu. 16Ina da shirin ziyaratar ku a kan hanyata ta zuwa Makidoniya. Daga nan kuma ina da yi niyyar in sake ziyartar ku, a tafiya ta daga Makidoniya, domin ku aike ni a hanyata ta zuwa Yahudiya.
17Yayinda nake irin wannan tunani, ina shakka ne? Ina shirya abubuwa ne bisa ga magwajin mutum, ta yadda har zan ce "I, i" da "A, a, a, a" a lokaci guda? 18Amma kamar yadda Allah yake amintacce, ba ma fadin "I" da "A'a" a lokaci guda.
19Gama Dan Allah, Yesu Almasihu, wanda Silbanus da Sila, da Ni muka shaida maku, ba "I" da "A, a" ba ne. Maimakon haka, Shi "I" ne a kodayaushe. 20Gama dukan alkawaran Allah 'I' ne a cikin sa. Haka kuma ta wurin sa muna cewa "Amin" zuwa ga daukakar Allah.
21Yanzu dai Allah ne ya tabbatar da mu da ku a cikin Almasihu, ya kuma kebe mu. 22Ya sa hatiminsa a kan mu ya kuma ba mu Ruhu a zuciyar mu a matsayin tabbacin abinda zai bamu daga baya.
23Maimakon haka, na yi kira ga Allah ya zama shaida domina, cewa dalilin dayasa banzo Korintis ba domin in kare ku ne. 24Ba muna kokarin mu sarrafa yadda bangaskiyar ku za ta zama ba ne. Maimakon haka, muna aiki tare da ku ne domin farincikinku, yayinda kuke tsaye cikin bangaskiyarku.

2

1Don haka na yanke shawara daga bangarena, ba zan sake zuwa wurin ku cikin yanayi mai tsanani ba. 2Idan na bata maku rai, wa zai karfafa ni, in ba shi wanda na bata wa rai ba?

3Na rubuto maku kamar yadda na yi domin idan na zo gareku kada in sami bacin rai a wurin wadanda ya kamata su faranta mani rai. Ina da gabagadi game da dukan ku, cewa farincikin da nake da shi, shine kuke da shi duka. 4Domin kuwa na rubuto maku cikin kunci da bacin rai da kuma hawaye mai yawa. Ba zan so in sake bata maku rai ba. Maimakon haka, na so ku san zurfin kaunar da nake da ita domin ku.
5Idan wani ya kawo sanadin bacin rai, ba ni kadai ya kawo wa wannan abin ba, amma ta wani fannin- domin kada a tsananta- har a gare ku duka. 6Hukuncin nan da galibinku kuka yi wa mutumin nan ya isa. 7Don haka, yanzu a maimakon hukunci, ku gafarta masa, ku kuma ta'azantar da shi. Ku yi haka domin kada bakinciki mai yawa ya danne shi.
8Don haka ina karfafa ku da ku nuna irin kaunar da kuke yi masa a fili. 9Wannan shine dalilin da ya sa na rubuto maku, domin in gwada ku, ko kuna biyayya cikin komai.
10Duk mutumin da kuka gafarta wa, ni ma na gafarta masa. Abin da na gafarta-idan na gafarta wani abu-an gafarta ne domin ku a gaban Almasihu. 11Wannan ya zama haka ne domin kada shaidan ya yaudare mu. Don ba mu jahilci irin makircinsa ba.
12Na samu budaddiyar kofa daga wurin Ubangiji yayin da nazo birnin Tarwasa, in yi wa'azin bisharar Almasihu a can. 13Duk da haka, raina bai kwanta ba, domin ban ga dan'uwana Titus a can ba. Sai na bar su a can, na dawo Makidoniya.
14Amma godiya ta tabbata ga Allah, wanda cikin Almasihu yake kai mu ga nasara a koyaushe. Ta wurin mu ya baza kamshi mai dadi na saninsa ko'ina. 15Gama mu, kamshi ne mai dadi na Almasihu ga Allah, a tsakanin wadanda ake ceton su, da kuma tsakanin wadanda suke hallaka.
16Ga mutanen da suke hallaka, kamshi ne daga mutuwa zuwa mutuwa. Ga wadanda suke samun ceto kuma kamshi ne daga rai zuwa rai. Wanene ya cancanci wadannan abubuwan? 17Gama mu ba kamar sauran mutane muke ba, masu sayar da maganar Allah domin samun riba. Maimakon haka, da tsarkakkiyar manufa, muke magana cikin Almasihu, kamar yadda Allah ya aiko mu, a gaban Allah.

3

1Muna fara sake yabon kanmu ne? Ba mu bukatar wasikun shaida daga gare ku ko zuwa gare ku, kamar wadansu mutane, ko ba haka ba? 2Ku da kanku kune wasikar shaidarmu, wadda aka rubuta a zukatanmu, wadda Kuma dukan mutane suka sani suke kuma karantawa. 3Kuma kun nuna ku wasika ne daga Almasihu, wadda muka isar. Ba da tawada aka rubuta ta ba amma da Ruhun Allah mai rai. Ba bisa allunan duwatsu aka rubuta ta ba, amma bisa allunan zukatan mutane.

4Gama wannan ne gabagadin da muke da shi cikin Allah ta wurin Almasihu. 5Ba mu da wata gwanintar kanmu da za mu yi takamar wani abu ya zo daga gare mu. Maimakon haka, gwanintar mu daga Allah take. 6Allah ne ya maishe mu kwararrun bayi na sabon alkawari. Wannan alkawari ne ba na rubutu ba amma na Ruhu. Gama rubutu kisa yake yi, amma Ruhu rai yake bayarwa.
7To hidimar da ta haifar da mutuwa- wadda aka rubuta bisa duwatsu- ta zo cikin irin wannan daukaka da har Israila ba su iya kallon fuskar Musa kai tsaye ba. Wannan kuwa saboda daukakar da ke fuskarsa ne, daukaka mai shudewa. 8Ina misalin girman daukakar hidimar da Ruhu ke yi?
9Gama idan hidimar kayarwa tana da daukaka, ina misalin yalwatar daukaka da hidimar adalchi za ta yi! 10Babu shakka, abin da aka maishe shi mai daukaka a da, ba ya da sauran daukaka a wannan fanni, saboda irin daukakar da ta zarce shi. 11To idan har mai shudewar nan ya na da daukaka, ina misalin daukakar da abu na dindindin zai samu!
12Dashike muna da wannan tabbaci, muna da gabagadi sosai. 13Ba kamar Musa muke ba wanda ya sa mayafi ya rufe fuskarsa, ta yadda mutanen Isra'ila basu iya kallon karshen daukaka mai shudewa ba kai tsaye.
14Amma tunaninsu ya zama a rufe. Har yau kuwa mayafin na nan sa'adda ake karanta tsohon alkawari. Ba a bude shi ba, saboda a cikin Almasihu ne kadai ake kawar da shi. 15Amma har yau, duk lokacin da ake karanta littafin Musa, akwai mayafi shimfide a zukatansu. 16Amma sa'adda mutum ya juyo wurin Ubangiji, an kawar da mayafin.
17To Ubangiji shine Ruhun. Inda Ruhun Ubangiji yake, akwai 'yanci. 18Dukan mu yanzu, da fuskoki marasa mayafi, muna ganin daukakar Ubangiji. Muna samun sakewa zuwa cikin irin wannan daukaka, daga wannan mataki na daukaka zuwa wani matakin, kamar dai daga wurin Ubangiji, wanda shine Ruhun.

4

1Don haka, domin muna da wannan hidima, da kuma yadda muka karbi jinkai, ba mu karaya ba. 2Maimakon haka, sai muka rabu da dukan hanyoyin da ke na kunya, kuma na boye. Ba mu rayuwar makirci, kuma bamu yiwa maganar Allah rikon sakaci. Ta wurin gabatar da gaskiya, muna mika kanmu ga lamirin kowa a gaban Allah.

3Amma, idan bishararmu a rufe take, tana rufe ne ga wadanda ke hallaka. 4A al'amarinsu, allahn wannan duniya ya makantar da zukatansu marasa bada gaskiya. A sakamakon haka, ba su iya ganin hasken bisharar daukakar Almasihu ba, wanda shine surar Allah.
5Gama ba mu yin shelar kanmu, amma Almasihu Yesu a matsayin Ubangiji, mu kuma bayinku saboda Yesu. 6Gama Allah shine wanda ya ce, "Haske zai haskaka daga cikin duhu." Ya haskaka cikin zukatanmu don ya bada hasken sanin daukakar Allah a gaban Yesu Almasihu.
7Amma muna da wannan dukiya a randunan yunbu, yadda zai zama a bayyane cewa mafi girman iko na Allah ne ba namu ba. 8Muna shan tsanani ta kowace hanya, ba a ci mu dungum ba. Mun rikice amma ba mu karaya ba, an tsananta mana amma ba a watsar da mu ba. 9Ana tsananta mana amma ba a yashe mu ba. Aka doddoke mu amma ba mu lalace ba. 10Mu dai a kullayaumin muna dauke da mutuwar Yesu a jikkunanmu, saboda a bayyana rayuwar Yesu a jikkunanmu kuma.
11Mu da muke a raye kuwa a kulluyaumin ana mika mu ga mutuwa saboda Yesu, domin rayuwar Yesu ta zama a bayyane a jikunanmu na mutuntaka. 12Saboda haka, mutuwa tana aiki a cikinmu, amma rai na aiki a cikinku.
13Amma dai muna da wannan Ruhu na bangaskiya kammar yadda aka rubuta: "Na gaskata, saboda haka na furta." Mu ma mun gaskata, haka kuwa muke fada. 14Mun sani cewa wanda ya tada Ubangiji Yesu daga matattu za ya sake tada mu tare da Yesu. Mun san cewa zai gabatar da mu tare da ku a gabansa. 15Dukan abubuwa sabili da ku suke domin, yayin da aka baza alheri ga mutane dayawa, bada godiya ta karu ga daukakar Allah.
16Don haka ba mu karaya ba. Kodashike daga waje muna lalacewa, daga ciki ana sabunta mu kulluyaumin. 17Domin wannan 'yar wahala ta dan lokaci tana shirya mu zuwa ga nauyin madauwamiyar daukaka wadda ta wuce gaban aunawa. 18Domin ba muna kallon abubuwan da ake gani bane, amma abubuwan da ba a gani. Abubuwan da muke iya gani ba masu dawwama ba ne, amma abubuwan da ba a gani madawwama ne.

5

1Mun san cewa idan wannan gidan da muke zaune a ciki ya rushe, muna da wani ginin daga wurin Allah. Gida ne wanda ba hannuwan mutane suka gina ba, amma madawwamin gida ne a cikin sama. 2Domin a cikin wannan jiki muna gurnani, muna jira a suturta mu da wurin zaman mu na samaniya. 3Muna jiran wannan ne domin ta wurin suturtar da mu ba za a same mu tsirara ba.

4Gama babu shakka yayinda muke cikin wannan alfarwa, muna gurnani, muna nawaita. Ba mu so muyi zaman hutanci. Maimakon haka, muna so a suturtar da mu, domin rai ya hadiye abu mai mutuwa. 5Wanda kuwa yake shirya mu domin ainihin wannan abu Allah ne, wanda ya ba mu Ruhu a matsayin alkawarin abinda ke zuwa.
6Domin wannan mu zama da gabagadi koyaushe. Mu lura da cewa yayinda muka shagala cikin jiki, muna nesa da Ubangiji. 7Gama bisa ga bangaskiya muke tafiya, ba bisa ga ganin ido ba. 8Don haka muna da gabagadi. Mun gwammace mu rabu da jiki domin mu zauna tare da Ubangiji.
9Sai muka maishe shi burinmu, ko muna cikin jiki ko nesa, mu gamshe shi. 10Domin tilas dukanmu mu hallara a gaban kursiyin shari'a na Almasihu, saboda kowa ya karbi sakamakon abubuwan da yayi cikin jiki, ko masu kyau ne ko marasa kyau.
11Don haka, domin mun san tsoron Ubangiji, muna rinjayar mutane. Allah na ganin yadda muke a fili. Ina fatan hakan a fili take ga lamirinku. 12Ba muna kokarin mu rinjaye ku domin ku kalle mu a matsayin amintattun mutane ba. Maimakon haka, muna ba ku dalilin yin takama da mu, domin ku sami amsar da za ku bada ga wadanda ke fahariya da kasancewarsu amma ba game da abinda ke zuciya ba.
13Gama idan mun fita daga hankulanmu, saboda Allah ne. Kuma idan muna cikin hankalinmu, domin ku ne. 14Domin kaunar Almasihu ta tilas ta mu, domin mun tabbatar da wannan: cewa mutum daya ya mutu domin kowa, kuma domin wannan duka sun mutu. 15Kuma Almasihu ya mutu domin kowa, domin wadanda ke raye kada su sake rayuwa domin kansu. A maimakon haka, su yi rayuwa domin shi wanda ya mutu kuma aka tashe shi.
16Domin wannan dalili, daga yanzu ba za mu kara shar'anta kowa bisa ga ma'aunin 'yan'adam ba, ko da yake a baya mun taba duban Almasihu a haka. Amma yanzu mun daina shar'anta kowa ta haka. 17Saboda haka, duk wanda ke cikin Almasihu, sabon halitta ne. Tsofaffin al'amura sun shude. Duba, sun zama sababbi.
18Dukan wadannan abubuwa daga Allah ne. Ya sulhunta mu da kansa ta wurin Almasihu, ya kuma ba mu hidimar sulhu. 19Wato, cikin Almasihu, Allah na sulhunta duniya zuwa gare shi, ba tare da lissafin zunubansu a kansu ba. Yana damka mana sakon sulhu.
20Don haka an zabe mu a matsayin wakilan Almasihu, kamar dai Allah na kira ga mutane ta wurin mu. Muna rokon ku, saboda Almasihu: "ku sulhuntu ga Allah!" 21Shi ya maida Almasihu ya zama hadaya domin zunubinmu. Shine wanda bai taba zunubi ba. Ya yi haka ne don mu zama adalchin Allah a cikin sa.

6

1haka, tundashike muna aiki tare, na roke ku kar ku yi watsi da alherin Allah. 2Domin ya ce, "A lokacin alheri na saurare ku, kuma a ranar ceto na agaje ku." Yanzu ne fa, lokacin alheri. Duba, yanzu ne ranar ceto.3Ba mu sa sanadin faduwa a gaban kowannen ku, domin ba mu so hidimarmu ta zama marar amfani.

4Maimakon haka, mun tabbatar da kan mu ta wurin dukan ayyukanmu, cewa mu bayin Allah ne. Mu bayinsa ne ta wurin yawan jimiri, azaba, kunci, wahala, 5duka, kurkuku, tarzoma, cikin aiki tukuru, cikin rashin barci yawancin dare, cikin yunwa, 6cikin tsarki, ilimi, hakuri, kirki, cikin Ruhu Mai tsarki, da sahihiyar kauna. 7Mu bayinsa ne cikin kalmar gaskiya, cikin ikon Allah. Muna kuma da makamai na adalci, a hanun dama da hagu.
8Muna aiki cikin daraja da rashin daraja, kushe da yabo. Ana zargin mu a kan mu mayaudara ne, duk da haka mu masu gaskiya ne. 9Muna aiki kamar ba a san mu ba, gashi kuwa mu sanannu ne. Muna aiki kamar masu mutuwa-duba! -har yanzu muna raye. Muna aiki kamar wadanda aka hukunta, amma ba hukuncin kisa ba. 10Muna aiki kamar muna bakinciki, amma a koyaushe muna farinciki. Muna aiki kamar matalauta, amma muna azurta mutane dayawa. Muna aiki kamar ba mu da komai, amma mun mallaki komai.
11Mun fada maku dukan gaskiyar, Korantiyawa, kuma zuciyar mu a bude ta ke. 12Ba mu kange zukatan ku ba, ku ne kuka kange zukatanku a gare mu. 13Yanzu a sabanin haka-Ina magana da ku kamar yara-ku bude mana zukatanku.
14Kada ku yi cudanya da marasa bangaskiya. Wace tarayya ke tsakanin adalci da take shari'a? Ko kuma wace zumunta ce ke tsakanin haske da duhu? 15Wace yarjejeniya ke tsakanin Almasihu da Ibilis? ko kuma me ya hada masu bangaskiya da marasa bangaskiya? 16ko wace yarjejeniya ce a tsakanin haikalin Allah da gumaka? Domin kuwa mu haikali ne na Allah mai rai, kamar yadda Allah ya ce: "Zan zauna a cikin su, in kuma yi tafiya a tsakanin su. Zan zama Allahnsu, su kuma za su zama mutanena."
17Sabili da haka, "Ku fito daga cikin su, kuma ku zama kebabbu," in ji Ubangiji. "Kada ku taba kazamin abu, zan kuma karbe ku. 18Zan zama Uba a gare ku, ku kuma za ku zama 'ya'ya maza da mata a gare ni," in ji Ubangiji Mai iko duka.

7

1Kaunatattu, da shike muna da wadannan alkawura, bari mu tsaftace kanmu, daga dukan abubuwan da ke kazantar da jikinmu da ruhunmu. Bari mu bidi tsarki cikin tsoron Allah.

2Ku ba mu dama! Bamu bata wa kowa rai ba. Ba mu cutar da kowa ko mu zambaci kowa ba. 3Ba domin in kayar da ku na fadi haka ba. Domin kuwa na riga na fada muku, cewa kuna zuciyar mu, domin mu mutu tare mu kuma rayu tare. 4Ina da muhimmin gabagadi a cikin ku, Ina fahariya da ku. Ina cike da ta'aziya. Farincikina ya cika makil duk da wahalhalunmu.
5Yayin da muka zo Makidoniya, jikinmu bai samu hutu ba. A maimakon haka, mun shiga matsaloli ta ko wace hanya ta wurin tashin hankali a waje tsoro kuma a ciki. 6Amma Allah, mai ta'azantar da raunana, ya ta'azantar da mu ta wurin zuwan Titus. 7Ba ta wurin isowar sa kadai Allah ya yi mana ta'aziyya ba. Amma kuma ta wurin ta'aziyyar da Titus ya samu daga wurin ku. Ya gaya mana irin matsananciyar kaunarku, bakincikinku, da zurfin kulawarku a kaina. Na kuwa yi farinciki sosai.
8Kodashike wasikata, ta bata maku rai, ban yi da na sanin haka ba. Amma sa'adda na ga wasika ta ta bata maku rai, na yi da na sani. Sai dai bacin ranku, na dan lokaci ne. 9Yanzu kuwa, ina farinciki, ba domin bacin ranku ba, amma domin bacin ranku ya kawo ku ga tuba, kun fuskanci bakinciki na ibada, donhaka ba ku yi rashi ba sabili da mu. 10Domin bakinciki daga Allah ya kan kai ga tuba da ke kammala ceto ba tare da-da na sani ba. Bakinciki na duniya kuwa ya kan kai ga mutuwa.
11Ku dubi irin kyakkyawar niyya da bakincikin nan daga Allah ya haifar a cikin ku. Ina misalin girman niyyar nan taku ta nuna cewa baku da laifi. Ina misalin girman fushinku, tsoronku, da sa zuciyarku, himmar ku, da marmarin ku na ganin cewa an yi adalci! A cikin komai, kun nuna kanku marasa laifi a cikin wannan al'amari. 12Kodayake na rubuto maku, ban rubuto saboda mai laifin ba, ko kuma saboda wanda aka yi wa laifin. Na rubuto ne domin himmarku gare mu ta sanu gare ku a gaban Allah.
13Dalilin haka ne muka samu karfafawa. Baya ga ta'aziyyar mu, mun kuma yi murna sosai saboda farin cikin Titus, domin ruhunsa ya wartsake ta wurin ku duka. 14Domin kuwa idan na yi fahariya da ku a gaban sa, ban ji kunya ba. A sabanin haka, kamar yadda kowane abu da muka fada maku gaskiya ne, fahariyarmu a kan ku ga Titus ta zama gaskiya.
15Kaunarsa a gare ku tana da girma, kamar yadda ya rika tunawa da biyayyarku duka, yadda kuka karbe shi da tsoro da rawar jiki. 16Ina farinciki matuka domin ina da cikakken gabagadi a cikin ku.

8

1Muna so ku sani, 'yan'uwa, game da alherin Allah da aka bayar ga Ikkilisiyoyin Makidoniya. 2A lokacin babban gwajin wahala, yalwar farincikinsu da tsananin talaucinsu ya haifar da yalwar bayarwa hannu sake.

3Domin ina shaida, sun yi bayarwa iya kokarinsu, fiye da abinda ma suke iyawa. Cikin yaddar ransu 4da roko mai yawa suka nace da a ba su zarafi su yi tarayya a wannan hidima ga masu bi. 5Haka ya auku ba kamar yadda muka yi zato ba. A Maimakon haka, sai da suka fara bada kansu ga Ubangiji. Kuma suka bada kansu gare mu bisa ga nufin Allah.
6Sai muka karfafa Titus, wanda ya rigaya ya fara wannan aiki, domin ya kammala wannan aiki na bayarwa ta fannin ku. 7Amma kun habaka cikin komai-cikin bangaskiya, cikin magana, cikin sani, cikin aiki tukuru, cikin kaunarku dominmu. Don haka, ku tabbata kun habaka a wannan aiki na bayarwa.
8Na fadi haka ne ba kamar ina umurtar ku ba. A maimakon haka, na fadi haka ne in gwada sahihancin kaunarku ta wurin kwatanta ta da himmar sauran mutane. 9Domin kun san alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu. Kodashike shi mai arziki ne, amma ya zama matalauci, domin ta wurin talaucinsa ku yi arziki.
10A wannan al'amari zan ba ku shawarar da za ta taimake ku. Shekarar da ta wuce, ba fara wani abu kawai kuka yi ba, amma kun yi marmarin ku yi shi. 11Yanzu ku kammala shi. Kamar yadda kuke da niyya da marmarin yin haka a lokacin, bari ku yi kokari ku kawo shi ga kammalawa iyakar iyawar ku. 12Idan kuna niyya ku yi wannan aiki, abu mai kyau ne karbabbe kuma. Tabbas ya zama dai-dai da abinda mutum ke da shi, ba abinda ba ya da shi ba.
13Domin wannan aiki ba domin a nawaita maku sannan wadansu su samu sauki ba ne. A maimakon haka, ya kamata a sami daidaituwa. 14Yalwar ku a wannan lokaci za ta zama abin biyan bukatarsu. Haka nan kuma domin yalwar su ta iya biyan bukatarku, domin a sami daidaituwa. 15Yana nan kamar yadda aka rubuta: "Wanda ke da shi dayawa bai samu raguwar komai ba, kuma wanda yake da kadan bai rasa komai ba."
16Amma godiya ga Allah, da yasa a zuciyar Titus marmarin kulawa da ku kamar wadda nake da ita domin ku. 17Gama ba rokon mu kadai ya karba ba, amma ya yi da gaske akan haka. Ya zo gare ku ne da yardar kan sa.
18Mun aiko tare da shi dan'uwa da ake yaba masa a tsakanin dukan Ikkilisiyoyi domin ayyukansa a cikin shelar bishara. 19Ba domin wannan kadai ba, amma Ikkilisiyoyi ne suka zabe shi ya tafi tare da mu a cikin yin wannan hidima ta alheri. Wannan domin girmama Ubangiji ne kansa da kuma domin aniyarmu ta taimakawa.
20Muna gudun kada kowa ya sa mana laifi game da wannan alheri da muke dauke da shi. 21Niyyar mu ce mu yi kyakkyawan abu, ba a gaban Ubangiji kadai ba, amma a gaban mutane ma.
22Mun kuma aiki wani dan'uwan tare da su. Mun sha gwada shi, kuma mun same shi da himma wajen ayyuka da dama. Yanzu kuma ya kara himma, saboda amincewa mai girma da yake da ita gare ku. 23Game da Titus, shi abokin tafiyata ne, kuma abokin aikina domin ku. Game da yan'uwanmu, an aiko su ne daga Ikkilisiyoyi. Su kuwa daraja ne ga Almasihu. 24Don haka, ku nuna masu kaunarku, ku kuma nuna wa Ikilisiyoyi dalilin fahariyarmu game da ku.

9

1Game da hidima domin tsarkaka, ya dace in rubuta maku. 2Na san marmarinku, wanda na yi fahariya da shi a gaban mutanen Makidoniya. Na gaya masu Akaya sun riga sun shirya tun bara. Kwazon ku ya sa yawancin su sun shiga aiki.

3To na aiko maku da 'yan'uwa saboda kada fahariyarmu akanku ta zama a banza, domin kuma ku zauna a shirye, kamar yadda na ce za ku yi. 4Idan kuwa ba haka ba, idan wani cikin makidoniyawa ya biyoni kuma ya tarar da baku shirya ba, za mu ji kunya-ba ni cewa komai game da ku-domin ina da gabagadi a kan ku. 5Sai na ga ya dace in turo 'yan'uwa su zo wurin ku kafin lokaci yayi suyi shirye shirye game da gudummuwar da kuka yi alkawari. Wannan ya zama haka ne domin a shirya shi a matsayin bayarwar albarka, ba wani abin kwace ba.
6Batun shine: wanda ya shuka kadan zai girbi kadan, wanda kuma ya shuka da manufar albarka zai girbi albarka 7Bari kowa ya bayar bisa ga yadda ya yi niyya a zuciyarsa. Kada ya bayar da bacin rai ko kamar dole. Gama Allah yana kaunar mai bayarwa da dadin rai.
8Allah na da ikon ya sa kowace albarka ta ribanbanya domin ku, domin, a koyaushe, a cikin dukan abubuwa, ku sami duk abinda kuke bukata. Hakan zai kasance domin ku ribabbanya kowanne kyakkyawan aiki. 9Kamar yadda aka rubuta, "Ya rarraba arzikinsa, ya bada shi ga matalauta. Adalcinsa ya dawwama har abada."
10Shi wanda ke bayar da iri ga mai shuka da gurasa domin abinci, zai bayar ya kuma ribabbanya maku iri domin shuka. Zai sa girbin adalcinku ya karu. 11Za ku wadata ta kowace hanya domin ku zama masu bayarwa, wannan kuwa zai sa a yi wa Allah godiya ta wurin mu.
12Aiwatar da wannan hidima ba biyan bukatun tsarkaka kawai take yi ba. Tana kuma ribanbanya zuwa ayyuka masu yawa na bada godiya ga Allah. 13Domin an gwada ku an tabbatar da ku akan wannan hidima, za ku kuma daukaka Allah ta wurin biyayyar ku ga shaidar bisharar Almasihu. Za ku kuma daukaka Allah ta wurin yalwar bayarwarku gare su da kowa duka. 14Suna marmarin ganin ku, suna kuma yi maku addu'a. Suna yin haka saboda alherin Allah mai girma da ke bisan ku. 15Godiya ga Allah domin kyautarsa wadda ta fi gaban bayyanawa.

10

1Ni, Bulus, da kaina nake rokon ku, ta wurin tawali'u da nasihar Almasihu. Ina da saukin kai yayinda nake gaban ku, amma ina da gabagadi a gare ku yayinda ba na tare da ku. 2Ina rokon ku, yayinda nake gabanku, ba ni so in zama mai tsaurin hali. Amma ina ganin zan bukaci zama mai gabagadi sa'adda nake tsayayya da su wadanda ke zaton muna zama bisa ga jiki.

3Kodashike dai muna tafiya bisa jiki, ba ma yin yaki bisa jiki. 4Domin makaman da muke yaki da su ba na jiki ba ne. Maimakon haka, makamai ne na Allah da ke da ikon rushe ikokin shaidan. Suna kawar da dukan gardandamin da ke kawo kaucewa.
5Muna kuma rushe duk wani abinda ke gaba da sanin Allah. Muna kuma kama kowanne tunani zuwa biyayya ga Almasihu. 6Muna kuma shirye mu hukunta kowanne irin aiki na rashin biyayya, da zarar biyayyarku ta tabbata.
7Dubi abin da aka sa a bayyane a gaban ku. In har wani ya tabbata shi na Almasihu ne, bari fa ya tunatar da kansa cewa kamar yadda shi na Almasihu ne, hakanan muma muke. 8Ko da zan yi fahariya da ikon da muke dashi, wanda Ubangiji ya ba mu domin mu inganta ku, ba domin mu rushe ku ba, ba zan ji kunya ba.
9Ba na so ya zama kamar ina firgita ku ne da wasikuna. 10Domin wadansu mutane na cewa, "Wasikunsa na da iko da firgitarwa, amma in ka gan shi kumama ne. Kalmominsa ba abin saurare ba ne."
11Bari wadannan mutane su sani cewa abinda muke fadi a kalmomin wasikunmu lokacin da ba mu nan, haka za mu yi in muna nan. 12Mu dai ba mu hada kanmu da kowa, ko kuma mu kwatanta kanmu da wadanda ke yabon kansu. Amma yayin da suke gwada kansu da junansu, suke kuma kwatanta kansu da junansu, ba su da ganewa.
13Saidai, ba za mu yi fahariya fiye da yadda ya kamata ba. Maimakon haka, za mu yi haka ne gwalgwadon iyakar abinda Allah ya sa muyi, iyakar da takai gareku. 14Gama bamu yi zarbabi ba sa'adda muka kai gareku. Mune na farko da muka kai gare ku da bisharar Almasihu.
15Ba mu yi fahariya fiye da kima game da aikin wasu ba. Maimakon haka, muna fatan bangaskiyar ku ta karu domin bangaren aikin mu ya kara fadada kwarai, kuma a daidai iyakarsa. 16Muna fatan haka, domin mu kai bishara zuwa yankunan da ke gaba da naku. Ba za mu yi fahariya akan aikin da aka yi a yankin wani ba.
17"Amma bari duk wanda zai yi fahariya, ya yi ta cikin Ubangiji." 18Domin ba wanda ya ke shaidar kansa shine yardajje ba. Maimakon haka, sai dai wanda Ubangiji ke shaidarsa.

11

1Ina fatan za ku jure da ni cikin wauta kadan. Ko da yake lallai kuna jurewa da ni! 2Domin ina kishi sabili da ku. Kishi na kuwa irin na Allah ne domin ku. Tun da na alkawartar da ku a cikin aure ga miji daya. Na kuma yi alkawarin in gabatar da ku kamar budurwa mai tsarki ga Almasihu.

3Gama ina fargaba a kan ku, ko watakila, kamar yadda macijin ya yaudari Hauwa'u ta wurin kissarsa, Ya zamana tunaninku ya kauce daga sahihiyar sadaukarwa ga Almasihu. 4Anar misali idan wani ya zo ya kawo shelar wani Yesu daban da wanda muka yi maku wa'azinsa. Ko kuma kun karbi wani ruhu daban da wanda muka karba. Ko kuma kun karbi wata bishara daban da wadda muka karba. Amincewar da kuka yi wa wadannan abubuwa ta isa!
5Don kuwa ina tsammanin ba a baya nake ba ga sauran wadanda ake kira manyan manzanni. 6To ko ma ba a ilimantar da ni ba akan yin jawabi, ban rasa horarwar ilimi ba. Ta kowace hanya kuma cikin abubuwa duka mun sanar da ku wannan.
7Na yi zunubi ne da na kaskantar da kai na domin a daukaka ku? Domin na yi maku wa'azin bisharar Allah kyauta. 8Na yi wa sauran Ikilisiyoyi kwace ta wurin karbar gudummuwa daga wurin su domin inyi maku hidima. 9Lokacin da ina tare da ku kuma na sami kai na cikin bukata, ban dora wa kowa nauyi ba. Domin 'yan'uwa da suka zo daga Makidoniya sun biya bukatuna. A cikin komai na kebe kaina daga zama nawaya a gare ku, kuma zan cigaba da yin haka.
10Kamar yadda gaskiyar Almasihu ke ciki na, ba zan yi shiru da wannan fahariya tawa ba a cikin dukan kasar Akaya. 11Don me? Saboda ba na kaunar ku? Allah ya sani.
12Amma abinda na ke yi, zan cigaba da yi. Zan yi haka ne domin in yanke zarafin wadanda ke son samun zarafi kamar mu akan abubuwan da suke fahariya da shi. 13Don irin wadannan mutane manzannin karya ne masu aikin yaudara. Suna badda kama kamar manzannin Almasihu.
14Wannan ba abin mamaki ba ne, domin shaidan ma yakan badda kama ya fito kamar mala'ikan haske. 15Ba wani babban abin mamaki ba ne idan bayin sa sun badda kamanninsu don a dauka bayin adalci ne su. Karshen su zai zama sakamakon abin da suka aikata.
16Ina kara fadi: Kada wani ya yi zaton ni wawa ne. Idan kun yi zaton hakan, to ku dauke ni kamar wawan don inyi fahariya kadan. 17Abinda nake fadi game da wannan gabagadi mai fahariya ba bisa ga amincewar Ubangiji ba ne, amma ina magana a matsayin wawa. 18Tun da mutane dayawa suna fahariya bisa ga jiki, ni ma zan yi fahariya.
19Gama kuna murnar tarayya da wawaye. Ku masu hikima ne! 20Kuma kuna hakuri da wanda zai bautar da ku, idan ya tauye ku, yana amfani da ku don ribar kansa, idan ya dauki kansa fiye da ku, ko ya mammare ku a fuska. 21Ina mai cewa mun kunyata da muka rasa gabagadin yi maku haka. Duk da haka idan wani zai yi fahariya-Ina magana kamar wawa-Ni ma zan yi fahariya.
22Su yahudawa ne? Ni ma haka. Su Isra'ilawa ne? Nima haka. Su zuriyar Ibrahim ne? Nima haka. 23Su bayin Almasihu ne? (Ina magana kamar ba ni cikin hankalina) na fi su ma. Na ma yi aiki tukuru fiye da su duka, shiga kurkuku fiye da kowa, a shan duka babu misali, a fuskantar haduran mutuwa da yawa.
24Daga hannun yahudawa sau biyar na sha bulala "Arba'in ba daya". 25Sau uku na sha dibga da sanduna. Sau daya aka jejjefe ni da duwatsu. Sau uku na yi hadari a jirgin ruwa. Na yi tsawon dare da yini guda a tsakiyar teku. 26Ina shan tafiye tafiye, cikin hadarin koguna, cikin hadarin 'yan fashi, cikin hadari daga mutane na, cikin hadari daga al'ummai, cikin hadarin birni, cikin hadarin jeji, cikin hadarin teku, cikin hadarin 'yan'uwan karya.
27Na sami kaina ina aiki tukuru cikin mawuyacin hali, cikin yin dare dayawa ba barci, cikin yunwa da kishin ruwa, cikin yawan azumi, cikin sanyi da tsiraici. 28Baya ga wadannan duka, akwai nauyi a kaina kullayaumin saboda damuwata akan Ikkilisiyoyi duka. 29Waye kumama, wanda ban zama kumama akan shi ba? Wanene aka sa yayi tuntube, kuma ban kuna ba?
30Idan zan yi fahariya, zan yi fahariya akan abinda ke nuna kasawata. 31Allah kuma Uba na Ubangijinmu Yesu, wanda ya isa yabo har abada, ya san ba karya nake yi ba!
32A Damasku, gwamnan da ke mulki karkashin sarki Aritas yasa aka yi tsaron birnin Damasku domin a kama ni. 33Amma ta taga cikin kwando aka ziraro ni bayan ganuwar birni, na kuwa kucce daga hannunsa.

12

1Dole ne in yi fahariya, ko dashike bata da ribar komai. Amma zan ci gaba da wahayoyi da ruyoyi daga Ubangiji. 2Na san wani mutum cikin Almasihu, wanda shekaru goma sha hudu da suka wuce-ko a cikin jiki ne ko ba a jiki ba, ban sani ba, Allah ya sani-an dauke shi zuwa sama ta uku.

3Kuma na san wannan mutumin-ko cikin jiki ko kuma ba cikin jiki ba, ban sani ba, Allah ya sani- 4an dauke shi zuwa Firdausi ya kuma ji madaukakan al'amura wadanda ba mai iya fadi. 5A madadin irin wannan mutumin zan yi fahariya. Amma a madadin kaina ba zan yi fahariya ba, sai dai game da kumamancina.
6Idan ina so inyi takama, ba zai zama wauta ba, domin gaskiya zan rika fada. Amma zan guje wa fahariya, domin kada wani ya dauke ni fiye da abinda ya gani ko ya ji daga gare ni. 7Zan kuma gujewa fahariya saboda irin wadannan gagaruman ruyoyi. Domin kada in cika da girman kai, an ba ni kaya cikin jikina, manzon shaidan ya wahalshe ni, domin kada in yi girman kai dayawa.
8Na roki Ubangiji har sau uku domin ya kawar mini da wannan. 9Amma ya ce mani, "Alherina isasshe yake a gare ka, domin ta wurin kumamanci karfi yake cika." Don haka zan gwammace takama a akan kasawata, domin ikon Almasihu ya zauna a ciki na. 10Sabili da haka a gamshe nake ta dalilin Almasihu, cikin kumamanci, ko raini, ko matsaloli, ko jarabobi, ko kuma nawaya. Don ko dayaushe na raunana, ina da karfi kuma.
11Na zama wawa! Amma ku ne kuka tilasta mani haka, ya kamata ku yabe ni, domin ban kasa ga wadan da ake kira manyan manzanni ba, ko da shike ni ba komai ba ne. 12Cikakkun alamun mazanni sun faru a tsakanin ku, da cikakken hakuri, alamu da abubuwan ban mamaki da manyan ayyuka. 13Ta yaya kuka zama da rashin muhimmanci akan sauran Ikkilisiyoyin, sai dai don ban zama matsala a gare ku ba? Ku gafarce ni a kan wannan laifin.
14Duba! A shirye nake domin in zo gare ku karo na uku. Ba zan so in zamar maku nawaya ba, domin ba kayanku nake so ba. Amma ku nake so. Domin ba 'ya'ya ne ya kamata su yi wa iyaye tanadi ba. Amma iyaye ne ya kamata su yi wa 'ya'ya tanadi. 15Zan yi murnar biyan bukatunku, ko ya kai ga in bada rai na. Idan ni na kaunace ku, sosai, sai ni za a kaunata kadan?
16Amma kamar yadda yake, ban nawaita maku ba. Amma, da shike ni mai dabara ne, Ni ne na kama ku da yaudara. 17Ko na cutar da ku ta wurin wadanda na turo maku? 18Rokar Titus na yi domin ya zo gare ku, sa'an nan na turo shi da wani dan'uwa. Ko da na turo Titus, ya cutar da ku ne, ba cikin hanya daya muka yi tafiya ba? Ba a sawu daya muka yi tafiya ba?
19Kuna tsammanin a dukan wannan lokaci muna kare kan mu a gaban ku ne? A gaban Allah, a cikin Almasihu muke fadin komai domin ku sami karfi.
20Ina tsoro domin idan na zo ba zan same ku yadda nake zato ba. Ina tsoro kuma ba za ku same ni kamar yadda ku ke zato ba. Ina tsoron cewa za a sami gardandami, kishi, barkewar fushi, buri na son kai, gulma, girman kai da yamutsi. 21Ina tsoron cewa bayan na dawo, Allahna zai iya kaskantar da ni a gaban ku. Ina tsoron cewa zan yi bakinciki domin mutane dayawa da suka yi zunubi kafin yanzu, wadanda kuma ba su tuba daga rashin tsarki da zina da fasikanci da ayyukan sha'awa da suka aikata ba.

13

1Wannan ne karo na uku da nake zuwa gare ku, "Ana tabbatar da kowanne zargi ta bakin shaidu biyu ko uku." 2Na riga na yi magana a baya da wadanda suka yi zunubi da kuma sauran a lokacin da ina tare da ku karo na biyu, kuma ina sake fadi: Idan na sake zuwa, ba zan raga masu ba.

3Ina fadi maku wannan ne domin kuna neman shaida ko Almasihu na magana ta bakina. Shi ba kasashshe bane zuwa gare ku. Maimakon haka, Shi mai iko ne a cikin ku. 4Domin an gicciye shi cikin kasawa, amma yana da rai ta ikon Allah. Don mu ma kasassu ne a cikin shi, amma za mu rayu tare da shi cikin ikon Allah dake cikinku.
5Ku auna kanku ku gani ko kuna cikin bangaskiya. Ku yi wa kanku gwaji. Ba ku lura da cewa Yesu Almasihu yana cikin ku ba? Yana cikin ku, sai dai in ba a amince da ku ba. 6Gama ina da gabagadin cewa za ku iske an amince da mu.
7Ina addu'a ga Allah cewa ba za a same ku da laifi ba. Ba wai ina rokon mu bayyana kamar mun ci gwadawar ba. Maimakon haka, ina addu'a ku yi abinda ke dai dai, ko dayake mun yi kamar mun fadi gwadawar. 8Domin bamu iya yin wani abu na tsayayya da gaskiya ba, sai dai mu yi domin gaskiya.
9Muna farin ciki idan mun kasa ku kuma kun yi karfi. Muna addu'a kuma domin ku kammalu. 10Na rubuta wadannan abubuwa yayinda ba ni tare da ku, saboda yayin da zan kasance da ku ba zan zamar maku mai fada ba. Ba na so inyi amfani da ikon da Ubangiji ya bani in tsattsaga ku, sai dai in gina ku.
11A karshe, 'yan'uwa, ku yi farinciki, ku yi aiki don sabuntuwa, ku karfafa, ku yarda da juna, ku zauna cikin salama. Kuma Allahn kauna da salama zai kasance tare da ku. 12Ku gai da juna da tsattsarkar sumba.
13Masu bi duka suna gaishe ku. 14Bari alherin Ubangiji Yesu Almasihu, da kaunar Allah, da zumuntar Ruhu Mai Tsarki su kasance tare da ku duka.

Galatiyawa

1

1Wannan Bulus manzo ne. Manzancina kuwa, bai zo daga mutane ba ko mutum, amma ta wurin Yesu Almasihu da Allah Uba wanda da ya tashe shi daga matattu. 2Ni da dukan 'yan'uwa da nake tare da su a nan, ina rubuto maku ku iklisiyoyi da ke a Galatiya.

3Alheri zuwa gare ku da salama daga Allah Ubanmu da kuma Ubangjinmu Yesu Almasihu, 4wanda ya ba da kansa domin zunubanmu saboda ya kubutar da mu daga wannan mugun zamani, bisa ga nufin Allah da Ubanmu. 5Daukaka ta tabbata a gare shi har abada abadin.
6Na yi mamaki kwarai yadda kuka juya da sauri zuwa wata bishara daban. Na yi mamakin cewa kuna juyawa daga shi wanda ya kira ku ta wurin alherin Almasihu. 7Ba wata bishara, amma akwai wadansu mutane da suke kawo maku rudani kuma suna so su gurbata bisharar Almasihu.
8Amma, ko da mu ne ko mala'ika daga sama ya yi maku shelar wata bishara ta daban da wadda muka yi shelar ta, la'ananne ne. 9Kamar yadda muka fadi maku a da, yanzu kuma ina sake fada, "Idan wani ya yi maku shelar wata bishara ta daban da wadda kuka karba, la'ananne ne." 10To yanzu ina neman shaidar mutane ne ko Allah? Ina neman in gamshi mutane ne? Idan har yanzu ina kokarin in gamshi mutane ne, ni ba bawan Almasihu ba ne.
11Ina son ku sani fa 'yan'uwa, cewa bisharar da nake shelar ta ba daga mutane take ba. 12Ban karbe ta daga mutum ba, ba ma wanda ya koyar mani A maimakon haka, ta wurin wahayin Yesu Almasihu ne zuwa gare ni.
13Kun riga kun ji game da rayuwa ta a da cikin Yahudanci, yadda da nake da kwazon tsananta wa iklisiyar Allah fiye da misali kuma ina lalatar da ita. 14Ina gaba-gaba cikin Yahudanci fiye da yawancin tsararrakina. A kwazo kuwa fiye da kima game da al'adun ubannina.
15Amma ya gamshi Allah ya zabe ni daga cikin mahaifiyata. Ya kira ni ta wurin alherinsa. 16Ya bayyana dansa a gareni, saboda in yi shelar sa cikin al'ummai. Nan da nan, ban nemi shawarar nama da jini ba 17kuma ban tafi Urushalima ba wurin wadanda suka zama manzanni kafin ni. Maimakon haka sai na tafi Arebiya, daga nan sai na dawo Dimashku.
18Bayan shekara uku na je Urushalima don in san Kefas, na zauna da shi na kwana goma sha biyar. 19Amma ban ga ko daya daga cikin manzannin ba sai Yakubu kadai, dan'uwan Ubangiji. 20Duba, a gaban Allah, ba karya nake yi ba cikin abin da na rubuta maku.
21Daga nan sai na je lardin Suriya da Kilikiya. 22Har a lokacin babu wanda ya san ni a fuska a iklisiyoyin Yahudiya da suke cikin Almasihu, 23amma sai labari kawai suke ji, "Wanda a da yake tsananta mana yanzu yana shelar bangaskiyar da a da yake rusarwa." 24Suna ta daukaka Allah saboda ni.

2

1Daga nan, bayan shekara goma sha hudu na koma Urushalima tare da Barnaba. Na kuma dauki Titus tare da ni. 2Na koma ne domin Allah ya nuna mani in koma. Sai na gabatar masu shelar bisharan da nake yi a cikin al'ummai. (Amma a kebe na yi magana da wadanda aka dauka muhimman shugabanni). Na yi haka ne domin in tabbatar da cewa ba gudun banza nake yi ba, ko kuma na yi gudun banza.

3Amma ko Titus wanda yake tare da ni, Baheline, ba wanda ya tilasta masa ya yi kaciya. 4Wannan maganar ta taso ne daga 'yan'uwan karya da suka zo cikinmu a boye su ga 'yancin mu a cikin Yesu Almsihu. Sun yi marmarin su maishe mu bayi ga doka. 5Ba mu mika kanmu biyayya gare su ba ko da na sa'a daya, domin gaskiyar bishara ta kasance babu canzawa domin ku.
6Amma su wadanda a ke ganin su da muhimmanci ba su taimaka mani da komai ba. Ko su wanene su bai dame ni ba. Allah ba ya karbar wanda mutane suka fi so. 7Maimakon haka, suka ga an danka mani shelar bishara ga wadanda ba su da kaciya. Kamar yadda aka ba Bitrus shelar bishara ga masu kaciya. 8Gama Allah wanda yake yin aiki a cikin Bitrus domin manzanci zuwa ga masu kaciya, haka kuma yake aiki ciki na zuwa ga al'ummai.
9Da Yakubu, Kefas, da Yahaya, wadanda a ke gani masu gina ikilisiya, suka fahimci alherin da aka ba ni, suka bamu hannun dama na zumunci ni da Barnaba, Sun yi haka ne kawai domin mu mu tafi zuwa wurin al'ummai, su kuma su je wurin masu kaciya. 10Suna kuma so mu tuna da matalauta. Ni ma ina da aniyar yin haka.
11Da Kefas ya kai Antakiya, na yi tsayayya da shi a gabansa domin shine ke da kuskure. 12Da ma Kefas yana cin abinci tare da al'ummai kafin zuwan wasu mutane daga wurin Yakubu. Amma da wadannan mutane suka iso, sai ya dena kuma ya ware kansa daga al'umman. Yana jin tsoron wadannan mutanen da ke bukatar kaciya.
13Hakannan ma sauran Yahudawa da suke tare da shi sun bi munafurcin sa. A sakamakon haka Barnaba ma ya bi munafurcin su. 14Da na ga basu bin gaskiyar da take cikin bisharar, na gaya wa Kefas a gaban su duka, "Idan kai Bayahude ne kana rayuwar ka ta al'ummai a maimakon rayuwar Yahudawa, to ta yaya za ka tilasta wa al'ummai su yi zaman Yahudawa?"
15Mu da muke Yahudawa daga haihuwa, ba "Al'ummai masu zunubi ba." 16Ku sani fa, babu wanda za a baratar ta ayyukan shari'a. A maimakon haka an baratar da su ta wurin bangaskiya cikin Yesu Almasihu. Mun zo ga cikin Almasihu Yesu domin mu samu baratarwa ta bangaskiya cikin Almasihu, kuma ba ta ayyukan shari'a ba. Domin ta ayyukan shari'a babu wanda zai samu baratarwa.
17Amma idan mun nemi Allah ya baratar da mu cikin Almasihu, mun samu kanmu masu zunubi kenan, Almasihu ya zama bawan zunubi ne? Ko kadan! 18Idan na sake gina dogara ta a kan shari'a, dogarar da na juya wa baya, na nuna kai na mai karya shari'a kenan. 19Ta wurin shari'a na mutu ga shari'a, domin in yi rayuwa irin ta Allah.
20An giciye ni tare da Almasihu, ba nine ke rayuwa ba kuma, amma Almasihu ke rayuwa a cikina. Rayuwar da nake yi a yanzu a cikin jiki, ina yin ta ne, ta wurin bangaskiya ga dan Allah, wanda ya kaunace ni ya ba da kansa domina. 21Ban yi watsi da alherin Allah ba, domin idan adalci ya wanzu ta wurin shari'a, ashe Almasihu ya mutu a banza kenan.

3

1Ku Galatiyawa marasa wayo! Wanne mugun ido ya cuce ku? Ashe, ba Yesu Almasihu gicciyayye aka nuna a gaban idon ku ba? 2Ina so in gane wannan daga wurin ku ne kawai. Kun karbi Ruhun ta wurin ayyukan doka ne ko ta wurin ba da gaskiya ga abin da kuka ji? 3Rashin wayonku ya yi yawa haka ne? Kun fara da Ruhu, sai kuma yanzu ku karasa a cikin jiki?

4Kun fuskanci abubuwa da yawa a banza ne - har idan a banza ne? 5To, shi wanda ya ba ku Ruhun, da ayyuka masu iko a tsakanin ku, ya yi ne ta wurin ayyukan shari'a ko ta wurin ji tare da bangaskiya?
6Ibrahim "ya ba da gaskiya ga Allah, kuma an lisafta mashi wannan a matsayin adalci." 7Ta wannan hanya ku fahimta su wadanda suka ba da gaskiya, 'ya'yan Ibrahim ne. 8Nassi ya riga ya hangi gaba cewa, ta wurin bangaskiya Allah zai baratar da Al'ummai. An yi wa Ibrahim shelar bishara tuntuni: "A cikinka ne dukan al'ummai za su yi albarka." 9Saboda haka, wadanda suka ba da gaskiya, masu albarka ne tare da Ibrahim wanda ke da bangaskiya.
10La'ana na kan wadanda sun dangana ga ayyukan shari'a. Gama a rubuce yake, "La'ananne ne kowanne mutum da bai tsaya ga duk abin da ke a rubuce cikin littafin shari'a ba, ya kuma aikata shi duka."' 11Yanzu a sarari yake, Allah ba ya baratar da kowa ta wurin shari'a, domin "Mai adalci zai rayu ta bangaskiya." 12Doka ba daga bangaskiya take ba, 'Amma a maimakon haka, "Shi wanda ke yin wadannan abubuwa cikin shari'a, zai yi rayuwa ta wurin shari'a."
13Almasihu ya fanshe mu daga la'anar shari'a da ya zama la'ananne saboda mu. Kamar yadda yake a rubuce, "La'ananne ne duk wanda aka sargafe a bisa itace." 14Dalilin shine, albarkan da ke bisan Ibrahim ta zo ga al'ummai cikin Almasihu Yesu, domin mu samu karban alkawarin Ruhu ta wurin bangaskiya.
15'Yan'uwa, ina magana bisa ga ka'idojin mutane. Idan mutane sun yi yarjejeniya, babu mai kawar da shi ko a kara shi. 16Yanzu fa, an fada alkawaran nan ne ga Ibrahim da zuriyarsa. Bai ce, "ga zuriya ba" da manufar masu yawa; amma a maimakon haka ga daya kadai, "ga zuriyar ka," wanda shine Almasihu.
17Yanzu na fadi wannan. Shari'a, wadda ta zo shekaru 430 daga baya, ba ta kawar da alkawarin da Allah ya tabbatar da shi ba tun a baya. 18Domin idan da gadon ya zo ta dalilin shari'a ne, da ba za ya zo kuma ta dalilin alkawari ba. Amma Allah ya ba da shi ga Ibrahim kyauta ta wurin alkawari.
19Me ya sa kenan aka ba da shari'a? An kara ta ne saboda laifuffuka, har sai zuriyar Ibrahim din nan ta zo ga wadanda aka yi masu alkawarinta. An kaddamar da ikon shari'ar ta wurin mala'iku, ta hannun matsakaici. 20Yanzu dai matsakanci yana nufin mutum fiye da daya, duk da haka Allah daya ne.
21Shari'a tana tsayayya da alkawaran Allah kenan? Ko kadan! Domin idan da an ba da shari'a da ke iya bayar da rai, babu shakka da adalci ya zo ta wurin wannan shari'a. 22A maimakon haka, nassi ya kulle abubuwa duka a karkashin zunubi. Allah ya yi wannan domin alkawarin sa na ceton mu ta wurin bangaskiya cikin Yesu Almasihu ya samu a ba da shi ga wadanda suka gaskanta.
23Amma kafin bangaskiya cikin Almasihu ta zo, an kulle mu kuma aka tsare mu da shari'a har zuwa ga wahayin bangaskiya. 24Daga nan shari'a ta zama mana jagora har sai da Almasihu ya zo, domin mu samu baratarwa ta wurin bangaskiya. 25Yanzu da bangaskiya ta zo, ba mu kuma a karkashin jagora. 26Domin dukanku 'ya'yan Allah ne ta wurin bangaskiya cikin Almasihu Yesu.
27Dukanku da aka yi wa baftisma cikin Almasihu, kun suturce kanku da Almasihu. 28Babu Bayahude ko Baheline, bawa ko 'yantacce, babu na miji ko mace, domin dukanku daya ne cikin Almasihu Yesu. 29Idan ku na Almasihu ne, ku zuriyar Ibrahim ne kenan, magada bisa ga alkawarin.

4

1Ina cewa muddin magaji yaro ne, babu bambancin sa da bawa, ko da yake shine mai mallakan dukan kadarorin. 2A maimakon haka, yana karkashin masu jagora da amintattu har sai lokacin da mahaifinsa ya ajiye.

3Hakannan mu ma, lokaci da muke yara, an rike mu cikin kangi na tushin ka'idojin wannan duniya. 4Amma da lokacin ya yi daidai, Allah ya aiko da dansa, haihuwar mace, haihuwar karkashin shari'a. 5Ya yi haka ne domin ya fanshi wadanda ke a karkashin shari'a, domin mu karbi diyanci a matsayin 'ya'ya.
6Domin ku 'ya'ya ne, Allah ya aiko da Ruhun Dansa cikin zuciyarmu, Ruhun wanda ke kirar, "Abba, Uba." 7Saboda wannan dalilin kai ba kuma bawa ba ne amma da. Idan kai da ne, hakannan kuma kai ma magaji ne ta wurin Allah.
8Duk da haka a da, da ba ku san Allah ba, bayi ne ku ga alloli wadanda ainihi ba alloli ba ne ko kadan. 9Amma yanzu da kuka san Allah, ko kuma, yanzu da Allah ya san ku, me ya sa kuke sake komawa zuwa ga tushen ka'idodin nan mara karfi da amfani? Kuna so ku sake komawa zaman bayi kuma daga farko?
10Kuna kiyaye ranaku na musamman, sabobin watanni, lokatai, da shekaru. 11Ina ji maku tsoro. Ina tsoro cewa kamar na yi aiki cikinku a wofi.
12Ina rokon ku 'yan'uwa, ku zama kamar yadda nake, domin ni ma na zama kamar ku. Ba ku yi mani laifin komai ba. 13Amma kun sani cewa saboda rashin lafiya ne na yi maku shelar bishara da farko. 14Ko da yake halin da nake ciki cikin jiki a zahiri ya sa ku cikin gwaji, ba ku raina ni ba ko kuma kuka watsar da ni. A maimakon haka, kun karbe ni kamar mala'ikan Allah, kamar ni Almasihu Yesu ne da kansa.
15Saboda haka, yanzu ina murnar taku? Domin ina shaidar ku, idan mai yiwuwa ne, da kun kwakulo idanunku, kun ba ni. 16To kenan, na zama makiyin ku ne saboda na gaya maku gaskiya?
17Suna neman ku da himma ba domin wani alheri ba ne. Suna so su raba ni da ku domin ku bi su. 18Yana da kyau ko yaushe a yi himma domin dalilai masu kyau, ba kuma kawai sa'adda ina tare da ku ba.
19'Ya'yana kanana, sabili da ku ina cikin zafin nakuda kuma sai Almasihu ya samu kafuwa cikinku. 20Da ma a ce ina tare da ku yanzu in canza muryata, domin ina damuwa a kanku kwarai.
21Ku gaya mani, ku da kuke marmarin ku zo karkashin shari'a, ba ku ji abin da shari'ar ta ce ba? 22A rubuce yake cewa, Ibrahim yana da 'ya'ya maza biyu, daya dan baiwa ne, dayan kuma dan 'yantaciyar mace ne. 23Abin lura anan, dan baiwar an haife shi ta hanyar mutuntaka ne, amma dan 'yantaciyar macen, an haife shi ta wurin alkawari ne.
24Ana iya bayyana abubuwan nan a hanyar kwatanci kamar haka, wadannan mata na kama da alkawarai ne guda biyu. Dayan alkawarin daga dutsen Sinayi ne. Ta haifi 'ya'ya da ke bayi ne su. Ita ce Hajaratu. 25Yanzu fa, Hajaratu ita ce dutsen Sinayi da ke Arebiya. Misali ce na Urushalima na yanzu, domin tana cikin bauta tare da 'ya'yanta.
26Amma Urushalima da ke bisa 'yantacciya ce, ita ce mahaifiyarmu. 27Kamar yadda yake a rubuce, "Ki yi murna, ke bakarariya, ke da ba ki taba haihuwa ba. Ki yi shewa na farinciki, ke da ba ki dandana haihuwan da ba. Domin 'ya'yan bakarariya da yawa suke, fiye da ta mace mai miji."
28Yanzu fa, 'yan'uwa, kamar yadda Ishaku yake, haka muke, wato 'ya'yan alkawari. 29A lokacin can, shi wanda aka haife shi ta hanyar mutuntaka ya tsananta wa wanda aka haife shi ta hanyar Ruhu. Haka yake har yanzu.
30Amma menene nassi ya ce? "Ka kori baiwar nan tare da danta. Domin dan baiwar nan ba za ya ci gado tare da dan macen nan da ke 'yantacciya ba." 31Saboda haka 'yan'uwa, mu ba 'ya'yan baiwa ba ne, a maimakon haka, mu 'ya'yan macen nan ne da ke 'yantacciya.

5

1Saboda 'yanci ne Almasihu ya yantar da mu. Sai ku dage kada ku sake komawa cikin kangin bauta. 2Duba, ni Bulus, ina gaya maku cewa idan an yi maku kaciya, Almasihu ba zai zama da amfani a gare ku ba a kowace hanya.

3Haka kuma, na shaida ga ko wanda mutum wadda aka yi masa kaciya ya zama dole ya yi biyayya da dukan shari'a. 4Kun rabu da Almasihu, dukanku wadanda aka "baratar" ta wurin shari'a. Kun fadi daga alheri.
5Domin ta wurin Ruhu, cikin bangaskiya, muna jira gabagadi na adalci. 6A cikin Almasihu kaciya ko rashin kaciya ba shi da ma'ana. Bangaskiya kadai mai aiki ta wurin kauna ita ce mafi muhimmanci. 7Da kuna tsere da kyau, wanene ya tsayar da ku daga yin biyayya da gaskiya? 8Rinjayarwa da ke sa yin wannan, ba daga wanda ya kira ku ba ne
9Ai karamin yisti shi yake sa dukan kulli ya kumbura. 10Ina da wannan gabagadin game da ku cikin Ubangiji cewa ba za ku yi tunani a wata hanya daban ba. Shi wanda ya rikita ku zai sha hukunci ko wanene shi.
11'Yan'uwa, idan har yanzu wa'azin kaciya nake yi, don me har yanzu ake tsananta mani? Inda haka ne dutsen sanadin tuntube game da gicciye da ya ragargaje. 12Ina fata wadanda suke badda ku su maida kansu babani.
13'Yan'uwa, domin Allah ya kira ku zuwa ga yanci, kada dai ku mori yancin nan ya zama zarafi domin jiki. A maimakon haka ta wurin kauna ku yi wa juna hidima. 14Saboda dukan shari'a ta cika ne a cikin doka guda daya; "Ka kaunaci makwabcinka kamar kanka." 15Amma idan kuna cizo da hadiye juna, ku lura kada ku hallakar da junanku.
16Na ce, ku yi tafiya cikin Ruhu, ba za ku cika sha'awoyin jiki ba. 17Domin jiki yana gaba mai karfi da Ruhu, Ruhu kuma yana gaba da jiki. Domin wadannan akasin juna suke. Sakamakon shine ba za ku iya yin abin da kuke so ba. 18Amma idan Ruhu ne ke bishe ku, ba ku karkashin shari'a.
19Yanzu ayyukan jiki a bayyane suke. Sune al'amuran lalata, rashin tsarki, sha'awoyi, 20bautar gumaka, sihiri, yawan fada, jayayya, kishi, zafin fushi, gasa, tsattsaguwa, hamayya, 21hassada, buguwa, buguwa da tarzoma, da dai sauran irin wadannan abubuwa. Na gargade ku, kamar yadda a da na gargade ku, cewa wadanda suke aikata wadannan abubuwa ba za su gaji mulkin Allah ba.
22Amma 'ya'yan Ruhu kauna ne, farinciki, salama, hakuri, kirki, nagarta, bangaskiya, 23tawali'u, da kamun kai. Babu wata shari'a da ke gaba da wadannan abubuwa. 24Wadanda suke na Almasihu Yesu sun giciye halin jiki tare da marmarin sa da miyagun sha'awoyi.
25Idan muna zaune cikin Ruhu, mu yi tafiya da Ruhu. 26Kada mu zama masu girman kai, ko muna cakunar juna, ko muna kishin juna.

6

1'Yan'uwa, idan an kama mutum yana yin wani laifi, ku da kuke da ruhaniya sai ku dawo da mutumin a hanya cikin ruhun tawali'u, ka lura da kanka don kada kai ma ka fada a cikin gwaji. 2Ku dauki damuwar juna, ta yin haka za ku cika shari'ar Almasihu.

3Domin idan kowa ya zacci shi wani abu ne alhali shi ba komai ba ne rudin kansa yake yi. 4Sai kowa ya auna aikin sa. Sa'annan zai sami abin da zai yi takama, ba sai ya kwatanta kansa da wani ba. 5Domin kowa zai dauki nauyin kayansa.
6Wanda aka koya masa maganar, wajibi ne ya ci amfanin abubuwansa masu kyau duka tare da malaminsa. 7Kada fa a yaudare ku ba a yi wa Allah ba'a. Dukan abin da mutum ya dasa, shine abin da zai girba. 8Domin shi wanda ya shuka wa kansa dabi'ar zunubi zai girbi hallaka, amma shi wanda ya shuka cikin Ruhu, zai girbi rai madawwami daga Ruhu.
9Kada mu gaji da aikata nagarta, domin a lokacin da ya dace za mu yi girbi idan ba mu gaji ba. 10Saboda haka, lokacin da muke da zarafi, sai mu yi nagarta ga kowa. Mu yi nagarta mussamman ga wadanda suke na iyalin bangaskiya.
11Dubi yawan wasikun da na rubuta maku da hannuna. 12Wadanda suke so su nuna hali mai kyau cikin jiki suke tilasta ku yin kaciya. Suna yin haka ne kadai saboda kada a tsananta masu saboda gicciyen Almasihu. 13Domin ko su wadanda suke masu kaciya ba su kiyaye shari'a. Maimakon haka suna so ne a yi maku kaciya don su yi fahariya game jikinku.
14Bari kada ya zama ina fahariya sai dai ta gicciyen Ubangijinmu Yesu Almasihu. Ta wurinsa ne aka gicciye duniya a gare ni, ni kuma ga duniya. 15Domin kaciya ko rashin kaciya ba komai ba ne. Maimakon haka, sabon halita ne ke da muhimmanci. 16Ga dukan wadanda za su zauna cikin wannan ka'ida, bari salama da jinkai su kasance tare da su da kuma bisa Isra'ila na Allah.
17Daga yanzu zuwa nan gaba kada wani ya dame ni, domin ina dauke da tabbai na Yesu a jikina. 18Alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu ya kasance da ruhun ku, 'yan'uwa. Amin.

Afisawa

1

1Bulus, manzon Yesu Almasihu ta wurin nufin Allah, zuwa ga kebabbu na Allah da ke a Afisa wanda suke aminci cikin Yesu. 2Bari alheri ya kasance da ku, da salama daga wurin Allah Ubanmu da Ubangijinmu Yesu Almasihu.

3Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Almasihu. Shine ya albarkace mu da kowanne albarku na ruhaniya da ke cikin sammai cikin Almasihu. 4Kafin halitar duniya, Allah ya zabe mu da muka ba da gaskiya cikin Yesu. Ya zabe mu domin mu yi zaman tsarki da rayuwar da babu aibu a gabansa.
5Cikin kauna Allah ya kaddara ya dauke mu mu zama yayansa ta wurin Yesu almasihu. Ya yi wannan domin ya gamshe shi ya yi abin da ya ke so. 6Sakamakon shine Allah ya karbi yabo domin daukakan alherinsa. Wannan shine abinda ya ba mu hannu sake ta wurin kaunataccensa.
7Gama cikin kaunataccensa aka fanshe mu ta wurin jininsa, da gafarar zunubai ta wurin wadataccen alherinsa. 8Ya ba da wannan alherin a yalwace cikin dukan hikima da fahimta.
9Allah ya bayyana mana gaskiyar al'amarin da aka boye na shirinsa, ta wurin abin da yake so ya nuna cikin Almasihu. 10Idan lokaci ya yi na kammala shirinsa, Allah zai kawo dukan abubuwan da ke sama da kasa cikin Yesu.
11An zabe mu cikin Almasihu mu zama abin gado na Allah. Ya yi mana wannan shirin tun da cikin shirin sa, shi mai yin dukan abu ta dalilin nufinsa. 12Allah ya yi haka saboda mu rayu domin yabon daukakarsa. Mune na farko da muka sami bege cikin Almasihu.
13A cikin Almasihu ne kuma kuka samu jin maganar gaskiya, bisharan cetonku ta wurin Yesu. A cikinsa ne kuka bada gaskiya aka hatimce ku da Ruhu Mai Tsarki wanda aka alkawarta. 14Ruhun shine tabbacin gadonmu kafin mu kai ga samunsa. Wannan don yabon daukakarsa ne.
15Sabo da haka, tun lokacin da na ji labarin bangaskiyarku cikin Ubangiji Yesu da kaunar ku zuwa dukan wadanda aka kebe dominsa. 16Ban fasa tunawa da ku ba ina addu'a saboda ku cikin addu'o'ina.
17Ina addu'a da cewa Allah Ubangijinmu Yesu Almasihu, Uban daraja, ya ba ku ruhun basira da wahayin saninsa. 18Ina addu'a idanun zuciyarku su bude domin ku san tabacin kiranku. Ina addu'a dominku san arzikin mulkin gadonsa cikin wadanda aka kebe dominsa.
19Ina addu'a ku san ikon nan nasa mai girma mara iyaka da ke cikin mu da muka ba da gaskiya. Wannan girman yana ta wurin aikin karfin ikonsa ne. 20Wannan shine ikon da ya yi aiki cikin Almasihu lokacin da Allah ya tashe shi daga matattu ya sa shi a hannun damansa cikin sammai. 21Ya sanya shi bisa birbishin dukan sarauta, iko, mulki, karfi, da kowanne irin suna. Ya sanya Almasihu ba a wannan zamanin kadai ba, amma da zamani mai zuwa.
22Allah ya saka dukan abubuwa a karkashin kafafun Almasihu. Ya sa shi shugaban dukan abubuwa a cikin ikilisiya. 23Ikilisiya jikinsa ne, cikarsa wanda ya cika dukan abubuwa cikin kowacce hanya.

2

1Amma da ku matattu ne cikin zunubanku da laifofinku. 2A cikinsu kuka yi rayuwa bisa ga al'amuran duniyan nan. Kuka biye wa mai sarautar ikokin sararin sama, wannan ruhun ne da ke aiki cikin kangararrun 'ya'ya. 3Da can dukanmu muna cikin wadannan marasa bada gaskiya. Muka biye wa mugun burin jikinmu. Muna aikata halin mutuntaka da na tunaninmu. Bisa ga dabi'a 'ya'ya ne wadanda sun cancanci fushin Allah, kamar wadansu.

4Amma Allah mai yalwar jinkai ne, sabili da matukar kauna da ya kaunace mu. 5Sa'anda muke matattu cikin zunubai, ya kawo mu cikin sabon rai tare da Almasihu. Ta wurin alheri aka cece mu. 6Allah ya tashe mu tare ya kuma sa muka zauna tare a matsayi guda cikin Almasihu Yesu. 7Ya yi wannan domin a zamanai masu zuwa ya nuna mana matukar yalwar arzikin alherinsa ta wurin Yesu. Yana nuna mana wannan ta wurin alherinsa.
8Domin ta wurin alheri aka cece ku ta wurin bangaskiya, wannan ba daga gare ku ba ne, kyauta ce ta Allah. 9Ba daga ayyuka ba, Saboda wannan dalili kada kowa ya yi fahariya. 10Gama mu aikin hannuwansa ne, halitattu cikin Almasihu Yesu domin mu yi kyawawan ayyuka, wadanda tun da Allah ya tanada, mu yi rayuwa a cikinsu.
11Saboda haka ku tuna da ku al'ummai ne a dabi'ar jiki. Ana kiranku "marasa kaciya", abin da ake kira kaciya cikin jiki wadda hannayen mutane ke yi. 12Gama a lokacin nan a rabe kuke da Almasihu. Ku bare ne ga mutanen Isra'ila. Ku baki ne ga wa'adodi na al'kawarai. Ba ku da tabbaci a kan gobe. Ba ku da Allah a cikin duniya.
13Amma yanzu a cikin Almasihu Yesu ku da da kuke nesa da Allah, an kawo ku kusa da shi ta wurin jinin Almasihu. 14Gama shine salamar mu. Domin ya mai da biyun daya. Cikin jikinsa ne ya rushe katangar gaba da ta raba mu da juna. 15Wato ya kawar da shari'a mai umarnai da sharudda, domin ya halitta sabon mutum daya a cikinsa. Yin haka ya kawo salama. 16Ya yi haka domin ya sulhunta mutum biyu cikin jiki daya ga Allah ta wurin gicciye. Ta wurin gicciye ya kashe gabar da ke tsakaninsu.
17Yesu ya zo ya yi maku shelar salama ku da kuke nesa da ku na kusa. 18Domin ta wurin Yesu dukanmu biyu cikin Ruhu daya muna da hanya zuwa wurin Uba.
19Sabo da haka yanzu ku al'ummai, ko daya, ba bare ba ne. Maimakon haka ku abokai ne tare da kebabbun Allah, abokan aiki. 20Wadanda an gina su bisa tushen manzanni da annabawa. Almasihu Yesu da kansa shine mafificin dutsen ginin. 21A cikinsa dukan ginin ya hade tare, suna kuma girma kamar haikali cikin Ubangiji. 22A cikinsa ne kuma ake gina ku gaba daya kun zama mazaunin Allah a cikin Ruhu.

3

1Saboda haka, ni Bulus, dan sarka sabili da Almasihu dominku al'ummai. 2Ina zaton kun ji a kan aiki mai girma na alherin Allah da ya ba ni dominku.

3Ina rubuto maku bisa ga wahayin da aka sanashe ni. Wannan ita ce boyayyar gaskiya da na rubuta a takaice a cikin wata wasikar. 4Sa'adda kuka karanta a kan wannan, za ku iya fahimtar basira ta cikin boyayyar gaskiya a kan Almasihu. 5Wanda a zamanun da ba a bayyana wa mutane ba. Amma yanzu an bayyana shi ga manzanni da annabawa kebabbu a cikin Ruhu.
6Wannan boyayyar bishara ita ce al'ummai ma abokan gado ne tare da mu, gabobi ne cikin jiki daya. Abokan tarayya ne kuma cikin alkawaran Almasihu Yesu ta wurin bishara. 7Domin wannan na zama bawa ta wurin baiwar alherin Allah da ya bani ta wurin karfin ikonsa.
8Allah ne ya ba ni wannan baiwa. Ko da shike nine mafi kankanta cikin kebabbun Allah, in yi shelar bishara ga al'ummai akan wadatar Almasihu marar matuka. 9In kuma fahimtar da dukan mutane a kan shirin Allah, wannan boyayyar gaskiya wadda tun zamanai da suka wuce Allah ya boye, shi da ke mahallicin dukan abubuwa.
10Saboda haka, ta wurin ikilisiya, masu iko da masu mulkin sararin sama za su san hikimar Allah ta fuskoki daban daban. 11Wannan ya kasance bisa ga dawwamammen nufi da ya zartar cikin Almasihu Yesu Ubangijinmu.
12Gama a cikin Almasihu muna da gabagadi, da dama, da amincewa sabili da gaskiyar mu a cikinsa. 13Saboda haka ina rokon ku kada ku karaya da wahalar da na sha domin ku wadda ta zama daukakar ku.
14Saboda haka nake durkusawa da gwiwa ta a gaban Uba, 15wanda ta wurinsa ake kiran kowanne iyali na sama da na kasa. 16Ina addu'a ya amince maku bisa ga yalwar wadatar daukakarsa, ku karfafa matuka da iko ta wurin Ruhunsa, da yake cikinku.
17Ina addu'a Almasihu ya zauna a cikin zuciyar ku ta wurin bangaskiya. Ina kuma addu'a ku kafu ku kuma ginu da zurfi kwarai cikin kaunarsa. 18Ku kasance cikin kaunarsa domin ku gane, tare da dukan masu bi, menene zurfi, da fadi, da tsawon kaunar Almasihu. 19Ina addu'a domin ku san mafificiyar kaunar Almasihu da ta wuce sani. Ku yi wannan domin a cika ku da dukan cikar Allah.
20Yanzu ga wanda yake da ikon aikata dukan abu fiye da abin da muke roko ko tunani, bisa ga ikonsa da ke aiki a cikinmu, 21daukaka ta tabbata a gare shi a cikin ikilisiya ta wurin Almasihu Yesu har ya zuwa zamanun zamanai har abada abadin. Amin.

4

1Saboda haka a matsayi na na dan sarka saboda Ubangiji; ina rokon ku ku yi zaman rayuwa da ta cancanci kiran da Allah ya kiraye ku. 2Ku zamna da matukar tawali'u da sahihanci da hakuri. Ku karbi juna cikin kauna. 3Ku yi kokarin zaman dayantaka cikin Ruhu kuna hade cikin salama.

4Akwai jiki daya da kuma Ruhu daya, kamar yadda aka kira ku a kan begen nan daya. 5Ubangiji daya, bangaskiya daya, da kuma baftisma daya. 6Allah daya ne da Uban duka. Shine bisa duka, ta wurin duka, da kuma cikin duka.
7Ko wannenmu an ba shi baiwa bisa ga awon baiwar Almasihu. 8Kamar yadda nassi ya ce, "Da ya haye zuwa cikin sama, ya bi da bayi cikin bauta. Ya kuma yi wa mutane baye baye.
9Menene ma'anar, "Ya hau?" Ana cewa kenan ya sauka har cikin zurfin kasa. 10Shi da ya sauka shine kuma wanda ya hau birbishin sammai. Ya yi wannan domin ya cika dukan abubuwa.
11Almasihu ya ba da baye baye kamar haka: manzanni, annabawa, masu shelar bishara, makiyaya, da masu koyarwa. 12Ya yi haka domin ya shiryar da masu bi saboda hidima, domin gina jikin Almasihu. 13Ya yi haka har sai mun kai dayantakar bangaskiya da sanin Dan Allah. Ya yi haka har sai mun kai ga manyanta, kamar wadanda suka kai cikakken matsayin nan na falalar Almasihu.
14Wannan ya zamanto haka domin kada mu kara zama kamar yara. Kada a yi ta juya mu. Wannan haka yake domin kada mu biye wa iskar kowacce koyarwa ta makirci da wayon mutane masu hikimar yin karya. 15Maimakon haka za mu fadi gaskiya cikin kauna domin mu yi girma cikin dukan tafarkun da ke na sa, shi da yake shugaba, Almasihu. 16Almsihu ya hada dukan jikin masu ba da gaskiya. Jikin yana hade ta wurin kowanne gaba, domin jikin ya yi girma ya gina kansa cikin kauna.
17Saboda haka ina yi maku gargadi cikin Ubangiji cewa, kada ku sake yin rayuwa irin ta al'ummai da suke yi cikin azancin wofi marar amfani. 18Sun duhunta cikin tunaninsu. Bare suke da rai irin na Allah, ta wurin jahilcin da ke cikinsu da ta wurin taurare zukatansu. 19Basa jin kunya. Sun mika kansu ga mutumtaka ta yin kazamtattun ayyuka da kowacce zari.
20Amma ba haka kuka koyi al'amuran Almasihu ba. 21Ina zaton kun rigaya kun ji a kansa. Ina zaton an koyar da ku cikinsa, kamar yadda gaskiyar Yesu ta ke. 22Dole ku yarda halin ku na da, wato tsohon mutum. Tsohon mutumin ne ya ke lalacewa ta wurin mugun buri.
23Ku yarda tsohon mutum domin a sabonta ku cikin ruhun lamirinku. 24Ku yi haka domin ku yafa sabon mutum, mai kamanin Allah. An hallitta shi cikin adalci da tsarki da gaskiya.
25Saboda haka ku watsar da karya. "Fadi gaskiya ga makwabcin ka", domin mu gabobin juna ne. 26"Ku yi fushi, amma kada ku yi zunubi." Kada ku bari rana ta fadi kuna kan fushi. 27Kada ku ba shaidan wata kofa.
28Duk mai yin sata, kada ya kara yin sata kuma. Maimakon haka, ya yi aiki. Ya yi aiki da hannuwan sa domin ya sami abin da zai taimaka wa gajiyayyu. 29Kada rubabbun maganganu su fito daga cikin bakinku. Maimakon haka, sai ingantattu da za su ba da alheri ga masu ji. 30Kada ku bata wa Ruhu Mai Tsarki na Allah rai domin ta wurin sa ne aka hatimce ku domin ranar fansa.
31Sai ku watsar da dukan dacin rai, da hasala, da fushi, da tankiya, da reni tare da dukan mugunta. 32Ku yi wa juna kirki, ku zama da taushin zuciya. Ku yafe wa juna, kamar yadda Allah cikin Almasihu ya gafarta maku.

5

1Saboda haka ku zama masu koyi da Allah, kamar kaunatattun 'ya'yansa. 2Ku yi zama cikin kauna kamar yadda Almasihu ya kaunace mu, ya kuma mika kansa sadaka da hadaya ga Allah dominmu, hadaya mai kanshi abin karba ga Allah.

3Fasikanci ko kowacce irin kazamta, ko kazamar lalata kada a ambace su a tsakaninku, don haka ya dace ga masu bi. 4Kada a ambaci batsa, maganar wauta ko alfasha wadanda ba su dace ba. Maimakon haka, mu zama masu godiya.
5Domin wannan kun sani cewa ba fasiki, ko mara tsarki, ko mai hadama wato mai bautar gumaka zai sami gado cikin mulkin Almasihu da Allah. 6Kada kowa ya rude ku da maganganun wofi. Saboda wadannan abubuwa ne fushin Allah ke zuwa kan kangararrun 'ya'ya. 7Kada ku yi tarayya tare da su.
8Domin da ku duhu ne, amma yanzu ku haske ne cikin Ubangiji. Sai ku yi tafiya kamar 'ya'yan haske. 9Saboda amfanin haske shine dukan alheri, adalci da gaskiya. 10Kuna bidar abin da Ubangiji ke murna da shi. 11Kada ku sa hannu ga ayyuka marasa amfani da ayyukan duhu amma gara a tone su. 12Don abubuwan da suke yi a boye abin kunya ne a bayyana su.
13Dukan abu, idan haske ya bayyana su, za a gan su. 14Domin duk abin da aka bayyana ya zama haske. Saboda haka aka ce, "Ka farka, kai mai barci, ka tashi daga cikin matattu; Almasihu kuwa zai haskaka bisanka".
15Saboda haka, ku maida hankali yadda kuke rayuwar ku, ba kamar mutane marasa hikima ba amma kamar masu hikima. 16Ku yi lura yadda kuke amfani da lokaci don kwanakin miyagu ne. 17Kada ku zama wawaye. Maimakon haka, ku fahimci ko menene nufin Ubangiji.
18Kuma Kada ku bugu da ruwan inabi, don yana iya lalata rayuwa. Maimakon haka, ku cika da Ruhu Mai Tsarki. 19Kuna magana da junanku cikin zabura da wakoki da wakokin ruhaniya, kuna rairawa da yabo da zuciyarku ga Ubangiji. 20Kullum kuna ba da gaskiya domin dukan abubuwa cikin sunan Ubangiji Yesu ga Allah Uba. 21Kuna sarayadda kanku ga juna cikin girmama Almasihu.
22Mata, ku yi biyayya ga mazan ku kamar ga Ubangiji. 23Domin miji shine shugaban matarsa kamar yadda Almasihu yake shugaban ikilisiya. Shine kuma mai ceton jiki. 24Amma kamar yadda ikilisiya take biyayya ga Almasihu, haka kuma dole mata suyi ga mazajen su cikin kowanne abu.
25Mazaje, ku kaunaci matanku kamar yadda Almasihu ya kaunaci ikilisiya har ya ba da kansa dominta, 26Ya yi wannan domin ya tsarkake ta. Ya wanke mu da ruwan wanki ta wurin kalma. 27Ya yi wannan domin ya mika ma kansa ikilisiya mai daraja, ba tare da tabo ko cikas ko wani abu kamar wadannan, amma ta zama da tsarki da kuma mara aibi.
28Hakannan kuma, mazaje su kaunaci matansu kamar jikunnansu. Wanda yake kaunar matarsa yana kaunar kansa. 29Ba wanda ya taba kin jikinsa. Amma, yakan ciyadda shi yana kaunarsa, kamar yadda Almasihu ya kaunaci ikilisiya. 30Domin mu gabobin jikinsa ne.
31"Domin wannan mutum zai rabu da ubansa da uwarsa ya manne wa matarsa, su biyu su zama nama daya". 32Wannan asirin gaskiyar, da girma yake, amma ina magana ne game da Almasihu da ikilisiyarsa. 33Duk da haka, kowannenku dole ya kaunaci matarsa kamar kansa, matar kuma dole ta girmama mijinta.

6

1'Ya'ya, ku yi biyayya ga iyayenku chikin Ubangiji, domin wannan daidai ne. 2"Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka" (Doka ta fari kenan da alkawari), 3"ta haka za ku yi albarka, domin kwanakinku su yi tsawo a duniya".

4Hakanan, ku ubanni kada ku cakuni 'ya'yan ku har su yi fushi, amma ku goye su cikin horon Ubangiji da gargadinsa.
5Bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku na duniya tare da girmamawa da tsoro da zuciya mai gaskiya. Ku yi masu biyayya kamar ga Almasihu. 6Ku yi masu biyayya ba don lallai suna kallonku ba domin ku faranta masu rai. Maimakon haka, ku yi biyayya kamar bayi ga Almasihu. Ku yi nufin Allah daga zuciya. 7Ku yi hidima da dukan zuciya, kamar kuna bautar Ubangiji ba mutane ba. 8Sai ku sani cewa duk abinda mutum ya yi zai karbi sakamako daga wurin Ubangiji, ko shi bawa ne ko 'yantacce.
9Ku kuma iyayengiji, ku yi irin wannan ga barorin ku. Kada ku razana su. Kun sani shi wanda ke Ubangijinsu da ku daya ne yana sama. Kun sani tare da shi baya nuna tara.
10A karshe, ku karfafa cikin Ubangiji da cikin karfin ikonsa. 11Ku dauki dukan makamai na Allah, domin ku iya dagewa gaba da dabarun shaidan.
12Gama yakinmu ba da nama da jini bane. Amma, da ikoki da mulkoki da mahukuntan wannan zamani mai duhu da rundunai masu duhu na mugunta cikin sammai. 13Don haka ku dauki dukan makamai na Allah, domin ku iya tsayawa da karfi cikin muguwar rana. Bayan kun yi komai za ku tsaya da karfi.
14Saboda haka ku tsaya da karfi. Ku yi wannan bayan kun yi damara cikin gaskiya kuna yafa sulke na adalci. 15Ku yi wannan bayan kun daure kafafunku da shirin kai bisharar salama. 16Cikin dukan abu ku dauki garkuwar bangaskiya, wadda za ku kashe dukan kibau masu wuta na mugun.
17Ku dauki kwalkwalin ceto da takobin Ruhu, wanda shine maganar Allah. 18Tare da kowacce irin addu'a da roko kuna addu'a kullum cikin Ruhu. Da wannan lamiri, kuna tsare wannan da iyakacin kula da dukan juriya da roko saboda dukan masu bi.
19Ku yi mani addu'a, domin in karbi sako duk sa'adda na bude bakina. Ku yi addu'a in sami gabagadin bayyana boyayyar gaskiyar bishara. 20Saboda bishara nake jakada cikin sarkoki, yadda a cikinta zan yi magana gabagadi yadda takamata.
21Amma domin ku san rayuwa ta, da yadda nake, Tikikus, dan'uwa kaunatacce da amintaccen bawa cikin Ubangiji, zai sanar da ku dukan abu. 22Saboda wannan dalili na aiko shi gare ku, domin ku san al'amuran mu, kuma domin ku sami ta'aziya a zukatan ku.
23Bari salama ta kasance tare da 'yan'uwa, kauna da bangaskiya daga wurin Allah Uba da Ubangiji Yesu Almasihu. 24Alheri ya kasance tare da wadannan da suke kaunar Ubangijinmu Yesu Almasihu tare da kauna mara mutuwa.

Filibiyawa

1

1Bulus da Timoti bayin Almasihu Yesu, zuwa ga dukan wadan da aka kebe cikin Almasihu Yesu da ke a Filibi, tare da masu kula da ikilisiya da dikinoni. 2Bari alheri ya kasance tare da ku da salama daga Allah Ubanmu da Ubagijinmu Yesu Almasihu.

3Ina godiya ga Allahna duk lokacin da na tuna da ku. 4Ko yaushe cikin addu'a ta dominku duka, da farin ciki na ke addu'a. 5Ina godiya domin tarayyar ku a cikin bishara tun daga rana ta fari har ya zuwa yanzu. 6Na tabbata game da wannan abu, shi wanda ya fara aiki mai kyau a cikinku zai ci gaba da shi har ya kai ga kammala zuwa ranar Yesu Almasihu.
7Daidai ne in ji haka game da dukanku domin kuna zuciya ta. Dukanku abokan tarayya ta ne cikin alherin Allah wajen dauri na da kuma kariyar bishara, da tabbatar da bishara. 8Domin Allah mashaidi na ne, a kan yadda ina da marmarin ku duka cikin zurfin kaunar Almasihu Yesu.
9Ina yin wannan addu'a: kaunar ku ta habaka gaba gaba a cikin sani da dukan fahimta. 10Ina addu'a a kan haka domin ku gwada ku zabi mafifitan abubuwa. Ina addu'a domin ku zama sahihai marasa abin zargi a ranar Almasihu. 11Wannan kuma domin a cika ku da 'ya'yan adalci da ake samu ta wurin Yesu Almasihu, zuwa ga daukaka da yabon Allah.
12Yanzu ina so ku sani, 'yan'uwa, cewa al'amuran da suka faru da ni sun zama dalilan cin gaban bishara kwarai da gaske. 13Sakamakon haka, sarkokina cikin Almasihu sun zama sanannu ga dukan sojojin fada da kuma sauran jama'a, 14har galibin 'yan'uwa cikin Ubangiji suka karfafa kwarai sabili da sarkokina, suka fito a fili suka yi shelar maganar Allah gabagadi.
15Lalle wadansu suna shelar Almasihu cikin kishi da husuma, wadansu kuwa domin kyakyawar manufa. 16Masu shelar Almasihu domin kauna sun sani cewa an ajiye ni nan domin in kare bishara. 17Amma wadansu kuwa suna shelar Almasihu saboda sonkai da rashin gaskiya. A zaton su suna wahalar da ni cikin sarkokina.
18Sai kuma me? Ta kowace hanya, ko da gangan ko da gaske, shelar Almasihu ake yi, ina kuma murna da wannan! I, zan yi murna. 19Domin na sani wannan zai kai ga sanadiyar kubuta ta. Wannan zai faru sabili da addu'ar ku, da kuma taimakon Ruhun Yesu Almasihu.
20Bisa ga abin da hakikance nake tsammani da tabbaci cewa ba zan kunyata ba. Maimakon haka, da dukan karfin hali kamar kullum, da yanzu kuma, ina da burin kawo daukaka ga Almasihu a cikin jikina. Ina da begen Almasihu ya sami daukaka a cikin jikina ko cikin rayuwa ko cikin mutuwa. 21Domin ni a gare ni rai Almasihu ne, mutuwa kuwa riba ce.
22Amma idan ya zamanto rayuwata cikin jiki za ta kawo amfanin hidima to, ban san wanda zan zaba ba. 23Amma dukansu biyu suna jan hankali na. Ina da burin in bar nan in kasance tare da Almasihu, wannan ya fiye mani kwarai! 24Duk da haka rayuwata cikin jiki wajibi ne sabili da ku.
25Tunda shike ina da tabbas a kan wannan, na kuma sani zan rayu, in cigaba da kasancewa da ku duka domin cigaban ku, da farincikin ku, cikin bangaskiya. 26Sakamakon haka, takamar ku cikin Almasihu Yesu za ta bunkasa sabili da dawowa ta a gare ku. 27Ku tafiyar da al'amuran ku kamar yadda ya cancanci bisharar Almasihu, ku yi haka domin ko na zo in duba ku, ko bana nan inji yadda kuke tsaye daram cikin ruhu guda. Ina fatan in ji cewa da nufi daya kuke fama tare saboda bangaskiyar nan ta bishara.
28Kada ku tsorata da kome da magabtanku za su yi. Alama ce a gare su ta hallakar su. Amma ku kuwa alama ce ta ceton ku, wannan kuwa daga Allah ne. 29Gama an yi maku alheri, sabo da Almasihu, ba gaskantawa da Almasihu kawai ba, amma har ma shan wuya dominsa. 30Kuna da shan wuya irin tawa wanda kuka gani, wanda kun ji nake sha har yanzu.

2

1Idan akwai wani abin karfafawa cikin Almasihu. Idan da wata ta'aziyya daga kaunarsa. Idan akwai zumunta a Ruhu. Idan da tatausan jinkai da tausayi. 2Ku cika farin cikina don ku zama da tunani irin haka, kuna da kauna daya, kuna tarayya cikin Ruhu daya, ku kasance da manufa iri daya.

3Kada ku yi komai cikin sonkai ko girman kai. A maimakon haka cikin zuciya mai tawali'u kowa na duban wadansu fiye da kansa. 4Kada kowa ya dubi bukatun sa, amma yana lura da bukatun wadansu.
5Ku yi tunani cikin hanya wadda ke cikin Almasihu Yesu. 6Wanda ya yi zama cikin siffar Allah, bai mai da daidaitarsa da Allah wani abin da zai rike ba. 7Maimakon haka, ya wofintar da kansa. Ya dauki siffar bawa. Ya bayyana cikin kamannin mutane. An same shi a bayyane kamar mutum. 8Ya kaskantar da kansa, ya yi biyayya har ga mutuwa, mutuwa ta gicciye.
9Saboda haka Allah ya ba shi mafificiyar daukaka. Ya ba shi suna wanda yafi kowanne suna. 10Domin a cikin sunan Yesu kowace gwiwa za ta durkusa, gwiwoyin wadanda ke cikin sama da kuma duniya da kuma karkashin duniya. 11Kuma kowanne harshe zai furta cewa Yesu Almasihu Ubangiji ne, zuwa daukakar Allah Uba.
12Domin wannan kaunatattuna, kamar yadda kullum kuke biyayya ba sai ina nan kadai ba. Balle yanzu da bananan, ku yi aikin cetonku da tsoro da far gaba. 13Gama Allah ne yake aiki a cikinku ku yi nufi duka da aikata abin da zai gamshe shi.
14Ku yi kowanne abu ba tare da gunaguni da gardama ba. 15Domin ku zama marasa abin zargi kuma masu gaskiya, 'ya'yan Allah marasa aibi. Ku yi haka domin ku haskaka kamar haske a cikin wannan duniya, a tsakiyar karkatacciyar da gurbatacciyar tsara. 16Ku rike kalmar rai da karfi domin in sami dalilin daukaka Almasihu a ranarsa. Sa'annan zan san cewa ban yi tseren banza ba, ban kuma yi wahalar banza ba.
17Ko da ana tsiyaye ni kamar sadaka a kan hadaya da kuma hidimar bangaskiyarku, na yi farin ciki, kuma na yi farin ciki tare da ku duka. 18Kamar haka kuma sai ku yi farin ciki, ku yi farin ciki tare da ni.
19Amma na yi niyya in aiko da Timoti wurin ku ba da dadewa ba, domin ni ma in sami karfafuwa idan na san al'amuran ku. 20Gama bani da wani wanda halinmu yayi daidai da nasa, wanda yake juyayin ku da gaskiya. 21Domin duka ribar kansu suke nema bata Yesu Almasihu ba.
22Amma kun san darajar sa, kamar yadda da ke hidimar mahaifisa, haka ya bauta mani cikin bishara. 23Shi nake sa zuciyar in aiko maku ba da dadewa ba idan naga yadda al'amura nake gudana. 24Amma ina da gabagadi cikin Ubangiji cewa ni da kaina zan zo ba da dadewa ba.
25Amma ina tunanin yakamata in sake aiko maku da Abafaroditus, shi dan'uwana ne, abokin aiki, da abokin yaki, manzon ku da kuma bawa domin bukatu na. 26Da shike yana marmarin ku duka, ya damu kwarai da shike kun ji yayi rashin lafiya. 27Da gaske yayi rashin lafiya har ya kusan mutuwa. Amma Allah ya ji tausayin sa, ba shi kadai ba, amma har da ni, domin kada in yi bakin ciki kan bakin ciki.
28Domin haka na yi niyyar aiko shi, saboda idan kun sake ganinsa za ku yi farin ciki ni kuma in kubuta daga juyayi. 29Ku karbi Abafaroditus da dukan murna cikin Ubangiji. Ku ga darajar mutane irin sa. 30Domin saboda aikin Almasihu ne ya kusan mutuwa. Ya sadakar da ransa domin ya bauta mani domin ya cika hidimar da ya kamata ku yi mani.

3

1A karshe, 'yan'uwana, ku yi farin ciki cikin Ubangiji. In sake rubuta maku wadannan abubuwa ba wani abu mai nauyi ba ne a gare ni. Wadannan abubuwa zasu tsare ku. 2Ku yi hankali da karnuka. Ku yi hankali da miyagun ma'aikata. Ku yi hankali da masu yanke-yanke. 3Gama mune kaciyar. Don mune muke sujada ta wurin Ruhun Allah. Mune masu fahariya chikin Almasihu Yesu, kuma ba mu da gabagadi cikin jiki.

4Ko da shike, ni kaina ina gabagadi ga jiki. Idan wani zai iya tunanin gabagadi ga jiki, ni na fi shi. 5An yi mani kaciya a rana ta takwas, daga mutanen Israila, na kabilar Biliyaminu, Bayahuden Yahudawa; ga zancen shari'a Bafarisiye nake.
6Wajen himma na tsanantawa ikilisiya. Ga zancen adalci cikin sharia, na zama mara abin zargi. 7Amma duk wadannan abubuwan da suka zama riba a gare ni, na dauke su asara ne saboda Almasihu.
8I, lallai ina lisafta dukan wadannan abubuwa asara saboda mafificin sanin Almasihu Yesu Ubangijina. Saboda shine na yi asarar dukan abubuwa. Na maishe su marasa amfani domin in ribato Almasihu, 9a iske ni cikinsa. Ba ni da wani adalcin kaina ta wurin shari'a. Maimakon haka, ina da adalci ta wurin bangaskiya cikin Almasihu, adalcin dake daga wurin Allah ta wurin Bangaskiya. 10Yanzu ina so in san shi da ikon tashinsa, da tarayya cikin shan wuyarsa. In kuma zama kamarsa wajen mutuwarsa, 11domin ta ko kaka in kai ga tashi daga cikin matattu.
12Ba wai na rigaya na sami wadannan abubuwa bane, ko kuma na riga na zama cikakke. Amma ina nace bi domin in cafki wannan da Almasihu Yesu ya cafko ni dominsa. 13'Yan'uwa, ban dauka cewa na riga na cafka ba tukuna. Amma akwai abu daya da nake yi: ina mantawa da abin da ke baya, ina kutsawa zuwa ga abin da ke gaba. 14Ina nacewa zuwa ga manufar nan in kai ga samun ladar nasara na madaukakin kiran Allah cikin Almasihu Yesu.
15Dukan mu wadanda muke kammalallu, sai mu yi tunani ta wannan hanyar, idan kuwa kun yi tunanin wani abu daban, to Allah zai bayyana maku wannan kuma. 16Sai dai, in da muka rigaya muka kai, bari mu rike shi haka.
17Ku zama masu koyi da ni, 'yan'uwa. Ku duba da kyau wadannan da suke tafiya yadda muka zama abin koyi a gare ku. 18Mutane da dama suna tafiya -sune wadanda na ba ku labarin su, yanzu kuma ina fada maku har da hawaye - kamar makiyan gicciyen Almasihu ne. 19Karshen su hallaka ne. Domin allahn su ciki ne, fahariyar su kuma tana cikin kunyar su. Tunanin su na kan al'amuran duniya.
20Amma mu 'yangarincin mu a sama yake, daga inda muke sauraron mai ceto, Ubangiji Yesu Almasihu. 21Za ya sake jikinmu na kaskanci ya siffanta shi kamar jikin darajarsa, siffantacce ta karfin ikonsa inda ya sarayar da dukan abubuwa a gare shi.

4

1Saboda haka, kaunatattu 'yan'uwana da nake marmari, farin ciki na da rawani na, a wannan hanya ku tsaya daram cikin Ubangiji, kaunatattun abokai. 2Ina rokon Afodiya, ina rokon Sintiki, ku zama da ra'ayi daya cikin Ubangiji. 3Babu shakka, ina sake rokon ku, abokan tarayyar takunkumina na gaske: ku taimaka wa matayen nan. Domin mun yi wahala tare a cikin yada bishara tare da Kilimas da sauran abokan aiki na, wanda sunayensu na rubuce cikin littafin rai.

4Yi farin ciki cikin Ubangiji kullayomi. Ina sake cewa, yi farin ciki. 5Bari dukan mutane su ga jimirin ku. Ubangiji ya yi kusa. 6Kada ku damu da kowanne abu, maimakon haka, cikin komai tare da addu'a, da rokeroke, da godiya, bari rokeroken ku su sanu ga Allah. 7Salamar Allah, da ta zarce dukan ganewa za ta tsare zuciyarku da tunaninku cikin Almasihu Yesu.
8A karshe, 'yan'uwa, duk abin da ke mai gaskiya, duk abin da ya isa ban girma, duk abin da ke mai adalci, duk abin da ke mai tsabta, duk abin da ke karbabbe, duk abin da ke kawo kauna, duk abin da ke da kyakkyawan ambato, idan akwai yabo, yi tunani a kan wadannan abubuwan. 9Wadannan abubuwan da kuka koya kuka karba kuka ji kuka gani a rayuwa ta, ku aikata wadannan abubuwan. Allah mai salama zai kasance tare da ku.
10Na yi farin ciki sosai cikin Ubangiji domin yanzu a karshe kun sabunta kulawar ku game da ni. Kun kula da ni da gaske kwanakin baya, amma ba ku samu zarafin taimako ba. 11Ba don bukata ta bane nake fada wannan. Domin na koyi dangana a kowanne irin yanayi. 12Na san yadda zan zauna cikin bukata, na kuma san yadda zan samu a yalwace. A kowace hanya cikin kowanne abu na koyi asirin yadda zan ci da yawa da yadda zan zauna da yunwa, yadda zan zama a yalwace kuma in zama cikin bukata. 13Zan iya yin komai ta wurinsa shi da yake karfafa ni.
14Duk da haka, kun yi zumunta da ni cikin kunci na. 15Kun kuma sani, ku Filibiyawa, cewa da farkon bishara, lokacin da na bar Makidoniya, babu ikilisiya da ta tallafe ni cikin batun bayarwa da karba sai ku kadai. 16Ko lokacin da nake Tassalonika, kun aika da gudumawar biyan bukatu na fiye da sau daya. 17Ba domin ina neman kyauta ba ne. A maimakon haka, ina neman amfani da zai kawo karuwa cikin ajiyar ku.
18Na karbi dukan abubuwan, ina da shi a yalwace. An kosar da ni. Na karba ta hanun Abafroditus abubuwa daga wurinku. Shesheki na dadin kamshi mai dandanno, karbabbiyar hadaya mai gamsarwa ga Allah. 19Allah na zai cika dukan bukatunku bisa ga yalwarsa da ke cikin daukaka cikin Almasihu Yesu. 20Yanzu bari daukaka ta tabbata ga Allah da Ubanmu har abada abadin. Amin.
21Gai da kowanne mai bi cikin Almasihu Yesu. Dukan 'yan'uwa da ke tare da ni suna gaisuwa. 22Dukan masu bi a nan suna gaisuwa, musamman wadanda suke gidan Kaisar. 23Bari alherin Ubangijin Yesu Almasihu ya zauna tare da ruhunku. Amin

Kolosiyawa

1

1Bulus manzon Almasihu Yesu ta wurin nufin Allah da Timoti dan'uwanmu, 2zuwa ga masu bada gaskiya da amintattun 'yan'uwa cikin Almasihu da suke a Kolosi. Bari alheri da salama su kasance tare da ku daga wurin Allah Ubanmu. 3Muna godiya ga Uban Ubangijinmu Yesu Kristi, kuma kullum muna addu'a dominku.

4Mun ji bangaskiyar ku cikin Almasihu Yesu da kaunar da kuke da ita wa dukan kebabbu ga Allah. 5Kuna da kaunar nan domin bege na hakika ga abin da aka tanadar maku a sama. Kun riga kun ji game da begen nan na hakika maganar gaskiya da bishara, 6wanda ta zo maku. Wannan bishara tana ba da yaya tana kuma hayayyafa da kuma girma a cikin dukan duniya. Tana yin haka a cikinku kuma tun ranar da kuka ji ta kun kuma yi koyi game da alherin Allah cikin gaskiya.
7Wannan itace bishara kamar yadda kuka koye ta a wurin Abafaras, kaunataccen abokin bautar mu, wanda ke amintacce mai hidimar Almasihu a madadin mu. 8Abafaras ya bayyana mana kaunarku a Ruhu.
9Saboda da wannan kauna, tun daga ranar da muka ji haka, ba mu fasa yi maku addu'a ba. Muna ta roko domin ku cika da sanin nufinsa cikin dukan hikima da fahimta ta ruhaniya. 10Muna ta addu'a domin ku yi tafiya da ta cancanci Ubangiji a kowace hanya da za ta faranta masa rai. Muna ta addu'a cewa za ku ba da 'ya'ya cikin kowanne aikin nagari kuma za ku yi girma cikin sanin Allah.
11Muna addu'a ku karfafa a cikin kowanne iyawa bisa ga ikon daukakarsa zuwa ga matukar jimrewa da hakuri. 12Muna addu'a za ku yi godiyar farinciki ga Uban, wanda ya sa kuka samu rabo cikin gado na masu bangaskiya cikin haske.
13Ya kwato mu daga mulkin duhu ya kuma maishe mu ga mulkin kaunataccen Dansa. 14Ta wurin Dan ne muka sami fansa, gafarar zunubai.
15Dan shine surar Allah mara ganuwa. Shine farkon dukan hallitta. 16Domin ta wurinsa ne aka halicci dukan abubuwa, wadanda ke sama da wadanda ke duniya, masu ganuwa da marasa ganuwa. Ko kursiyai ko mulkoki ko sarautai ko ikoki, dukan abubuwa shi ya hallice su kuma dominsa. 17Ya kasance kafin dukan abubuwa, a cikinsa ne kuma komai yake hade.
18Kuma shine kan jikin, ikilisiya. Shine farko da kuma dan fari daga cikin matattu, don haka yana da wuri na fari a cikin dukan abubuwa. 19Domin Allah ya yi farinciki cewa dukan cikarsa ta kasance a cikinsa, 20kuma ya sulhunta kowanne abu zuwa gare shi ta wurin Dan. Allah ya kawo salama ta wurin jinin giciyensa. Allah ya sulhunta duka zuwa gare shi, ko abubuwan da ke duniya ko abubuwan da ke sama.
21Domin a da ku baki ne ga Allah, kuma makiyansa ne cikin zuciya da cikin mugun ayyuka. 22Amma yanzu, ya sulhunta ku ta wurin mutuwarsa ta jiki. Ya yi haka domin ya mika ku tsarkakaku, marasa aibu da marasa abin zargi a gabansa, 23idan kuka ci gaba cikin bangaskiya, kafaffu da tsayayyu, marasa kaucewa daga begen ku na hakika na bishara da kuka ji. Wannan itace bishara da aka yi wa kowanne halitaccen taliki a karkashin sama. Wannan itace bishara wadda ni, Bulus, na zama bawa.
24Yanzu ina murna da wahala ta domin ku. A jikina cika abin da ya rage cikin wahalar Almasihu domin jikinsa wadda itace ikilisiya. 25Saboda wannan ikilisiya na zama bawa, bisa ga haki da Allah ya ba ni domin ku, domin cika sakon Allah. 26Wannan shine asirin gaskiya da yake a boye shekara da shekaru da zamanai. Amma a yanzu an bayyana shi ga wadanda suka gaskanta da shi. 27A gare su ne Allah ya so ya bayyana yalwar daukakar asirin gaskiyarsa a tsakanin al'ummai. Ya nuna Almasihu ne ke cikin ku, tabbacin daukaka mai zuwa.
28Wannan shine wanda muke shella. Muna gargadar da kowanne mutum, muna kuma koyar da kowanne mutum tare da dukan hikima, don mu mika kowanne mutum cikakke cikin Almasihu. 29Domin wannan nake aiki da himma bisa ga karfinsa da yake aiki a cikina da iko.

2

1Ina so ku san yadda na sha faman gaske dominku, domin wadanda ke a Lawudikiya, da kuma wadansu da yawa da a jiki basu taba ganin fuska ta ba. 2Na yi aiki saboda zuciyar su ta sami karfafawa ta wurin hada su cikin kauna zuwa dukan arziki na tabbaci da fahimtar asirin gaskiya na Allah, wato Almasihu. 3A cikinsa dukan taskar hikima da sani ke boye.

4Na fadi haka domin kada wani ya yaudare ku da jawabi mai jan hankali. 5Ko da yake ba na tare da ku a jiki, duk da haka ina tare da ku a cikin Ruhu. Ina murnar ganin ku a yanayi mai kyau da kuma karfin bangaskiyar ku cikin Almasihu.
6Kamar yadda kuka karbi Almasihu Ubangiji, ku yi tafiya cikinsa. 7Ku kafu da karfi a cikinsa, ku ginu a kansa, ku kafu cikin bangaskiya kamar yadda aka koya maku, ku yawaita cikin yin godiya.
8Ku lura kada wani ya rinjaye ku ta hanyar ilimi da yaudarar wofi bisa ga al'adun mutane, bisa ga bin abubuwan duniya, ba na Almasihu ba. 9A cikinsa ne dukan Allahntaka ta bayyana ta jiki.
10Ku kuwa kun cika a cikinsa. Shine gaban kowanne iko da sarauta. 11A cikinsa ne aka yi maku kaciya, ba kaciya irin da yan adam suke yi ba, ta cire fatar jiki, amma ta kaciyar Almasihu. 12An binne ku tare da shi ta wurin baftisma. Kuma a cikinsa ne aka ta da ku ta bangaskiya a cikin ikon Allah, wanda ya tashe shi daga mutattu.
13A lokacin da kuke matattu cikin laifofinku, a cikin rashin kaciyar ku ta jiki, ya rayar da ku tare da shi kuma ya yafe maku dukan laifofinku. 14Ya share rubutattun basussukanku da ka'idodin da suke gaba da mu. Ya cire su duka ya kafa su a kan giciye. 15Ya cire ikoki da sarautu. A fili ya falasa su ya shugabance su zuwa ga bukin nasara ta wurin giciyensa.
16Saboda haka, kada kowa ya shari'anta ku ta wurin ci ko sha, ko kuma sabon wata, ko game da ranakun Assabaci. 17Wadannan sune inuwar abubuwan da ke zuwa nan gaba, amma ainihin shi ne Almasihu.
18Kada kowa wanda ke son kaskanci da sujadar mala'iku ya sharantaku ku rasa sakamakonku. Irin wannan mutum yana shiga cikin abubuwan da ya gani ya zama mai girman kai a tunaninsa na jiki. 19Ba ya hade da kai. Daga kan ne dukan jiki da gabobi da jijiyoyi ke amfani suna kuma hade tare; yana girma da girman da Allah yake bayarwa.
20In kun mutu tare da Almasihu ga ala'muran duniya, don me kuke rayuwa kamar kuna karkashin duniya: 21"Kada ku rike, ko ku dandana ko ku taba?" 22Dukan wadannan abubuwa karshen su lalacewa ne in ana amfani da su, bisa ga kaidodi da koyarwar mutane. 23Wadannan dokoki suna da hikima ta jiki irin ta addini da aka kago na kaskanci da kuma wahalar da jiki. Amma ba su da amfanin komai a kan abin da jiki ke so.

3

1Idan dai Allah ya tashe ku tare da Almasihu, ku nemi abubuwan da ke sama, inda Almasihu ke zaune a hannun dama na Allah. 2Yi tunanin a kan abubuwan da ke sama, ba a kan abubuwan da ke kasa ba. 3Gama ku kun mutu, ranku kuma yana boye tare da Almasihu cikin Allah. 4Sa'anda Almasihu ya bayyana, wanda shine ranku, sa'anan ku kuma zaku bayyana tare da shi cikin daukakarsa.

5Ku kashe sha'awacce-sha'awaccen da suke a duniya - zina da fasikanci, rashin tsarki, muguwar sha'awa, mummunar buri, da kuma kwadayi, wadda shine bautar gumaka. 6Saboda wandannan abubuwa ne fushin Allah ke zuwa a kan marasa biyayya. 7A cikin wadannan abubuwa ne kuka yi rayuwa a da da kuke zauna a cikinsu. 8Amma yanzu dole ku kawar da wadannan - zafin rai, fushi, mugayen manufofi, zage-zage, da kazamar magana daga bakinku.
9Kada ku yi wa juna karya, domin kun tube tsohon mutumin da ayyukansa, 10kun kuma yafa sabon mutum, wanda ake sabontawa cikin sani bisa ga surar wannan da ya hallice shi. 11A nan ne inda babu Baheline da Bayahude, mai kaciya da marar kaciya, bare, baubawa, ko Basikitiye, bawa ko yantacce, amma Almasihu shine duka, yana kuma cikin duka.
12A matsayin ku na zababbun Allah, masu tsarki da kaunatattu sai ku yafa jinkai, ayyukan kirki, saukin kai, kamewa da hakuri. 13Yi hakuri da juna. Ku yi wa juna alheri. Idan wani na da damuwa da wani, ku gafarta kamar yadda Ubangiji ya gafarta maku. 14Fiye da wadanan abubuwa duka, ku kasance da kauna, wanda itace cikakkiyar kammalla.
15Bari salamar Almasihu ta mallaki zukatanku. Sabili da wannan salama ce aka kiraye ku cikin jiki daya. Ku yi godiya. 16Ku bar maganar Almasihu ta zauna a cikinku a yalwace. Da dukan hikima, ku koyar, ku kuma gargadi juna da zabura, wakoki, da wakokin yabo na ruhaniya. Kuna rairawa tare da godiya cikin zukatanku ga Allah. 17Kuma duk abin da zaku yi cikin magana ko aiki ku yi duka cikin sunan Ubangiji Yesu. Kuna yin godiya ga Allah Uba ta wurinsa.
18Mata, ku yi biyayya ga mazajenku, yadda yakamata a cikin Ubangiji. 19Mazaje, ku kaunaci matayenku, kada ku muzguna masu. 20Yaya, ku yi wa iyayen ku biyayya cikin dukan komai, domin wannan yana faranta wa Ubangiji rai. 21Ku Ubanni, kada ku cakuni 'ya'yanku domin kada su karaya.
22Bayi, ku yi wa iyayengijinku na jiki biyayya cikin kowane abu, ba tare da bautan ganin ido ba don faranta wa mutane rai, amma da sahihiyar zuciya. Ji tsoron Ubangiji. 23Duk abin da kuke yi, ku yi aiki daga zuci domin Ubangiji ba domin mutane ba. 24Kun san cewa, zaku karbi sakamako na gado daga wurin Ubangiji. Domin Ubangiji Almasihu kuke bauta wa. 25Domin kowa ya yi rashin adalci zai karbi sakamakon rashin adalcin da ya yi, kuma babu son kai.

4

1Ku iyayengiji, ku ba bayinku abin ke daidai ya kuma dace garesu. Kun sani cewa ku ma, kuna da Ubangiji a sama.

2Ku cigaba da himmantuwa ga yin addu'a. Ku zauna a fadake cikin addu'a da godiya. 3Ku yi addu'a tare domin mu kuma, domin Allah ya bude kofa domin kalmar, a fadi asirin gaskiyar Almasihu. Don wannan ne nake cikin sarka. 4Ku yi addu'a domin in iya fadinsa daidai, yadda yakamata in fada.
5Ku yi tafiya da hikima game da wadanda suke a waje, ku yi amfani da lokaci. 6Bari maganarku ko yaushe ta zama ta alheri. Bari ta zama da dadin ji domin ku san yadda za ku amsa wa kowanne mutum.
7Game da abubuwan da nake ciki, Tikikus zai sanar maku da su. Shi kaunataccen dan'uwa, amintaccen bawa, shi abokin barantaka na ne a cikin Ubangiji. 8Na aike shi wurinku don wannan, domin ku iya sanin halin da muke ciki, don kuma ya karfafa zukatanku. 9Na aike shi tare da Onisimus, amintacce da kuma kaunataccen dan'uwa, wanda daya ne daga cikin ku. Za su gaya maku duk abin da ya faru anan.
10Aristarkus, abokin sarka na, yana gaishe ku da Markus, dan'uwan Barnaba (wanda a kansa ne kuka sami umarni; in yazo, ku karbe shi), 11da kuma Yesu wanda ake kira Yustus. Wadannan ne kadai daga cikin masu kaciya abokan aiki na domin mulkin Allah. Sun zama ta'aziya a gare ni.
12Abafaras na gaishe ku. Shi daya daga cikinku ne kuma bawan Almasihu Yesu ne. Kullum yana maku addu'a da himma, don ku tsaya cikakku da hakikancewa a cikin nufin Allah. 13Gama ina shaidarsa a kan ya yi aiki da himma domin ku, domin wadanda ke Lawudikiya, da na Hirafolis. 14Luka kaunataccen likita da Dimas suna gaishe ku.
15Ku gai da 'yan'uwa dake a Lawudikiya, da Nimfa da ikilisiyar da ke cikin gidanta. 16Lokacin da aka karanta wannan wasika a tsakanin ku, sai a karanta ta kuma a cikin ikilisiyar Lawudikiya, ku kuma tabbata kun karanta wasika daga Lawudikiya. 17Ku gaya wa Arkibas, "Mai da hankali ga hidimar da ka karba cikin Ubangiji, don ka cika shi."
18Wannan gaisuwa da hannu na ne - Bulus. Ku tuna da sarka na. Alheri ya tabbata a gare ku.

1 Tassalunikawa

1

1Bulus, Sila, da Timoti zuwa ga Ikilisiyar Tassalonikawa cikin Allah Uba da Ubangiji Yesu Almasihu. Alheri da Salama su kasance a gare ku.

2Kullum muna bada godiya ga Allah domin ku dukka, kamar yadda muke ambaton ku a addu'o'in mu. 3Muna tunawa da ku ba fasawa a gaban Allahn mu da Ubanmu kuma ayyukanku na bangaskiya, da kauna. Da hakurin bege na abinda ke gaba cikin Ubangijinmu Yesu Almasihu.
4'Yan'uwa kaunatattu na Allah, Mun san kiran ku, 5yadda bishararmu ta zo gare ku ba ta magana kadai ba, amma da iko, ta wurin Ruhu Mai Tsarki, haka kuma tawurin tabbatarwa. Ta haka kuma, kun san irin mutanen da muke acikin ku kuma domin ku.
6Kun zama masu koyi da mu da kuma Ubangiji, kamar yadda kuka karbi kalmar cikin tsanani mai yawa da murna tawurin Ruhu Mai Tsaki. 7Sakamakon haka, kuka zama abin misali ga dukkan wadanda ke Makidoniya da na Akaya wadanda suka bada gaskiya.
8Gama daga gare kune maganar Allah ta bazu ko ina, ba kuwa Makidoniya da Akaya kadai ba. A maimako, har ma zuwa ko ina bangaskiyarku cikin Allah ta kai. Don haka, bama bukatar muce maku komai. 9Domin su da kansu suna bada labarin irin zuwan mu gare ku. Suna fadin yadda kuka juyo ga Allah daga bautar gumaka don ku bautawa Allah mai rai. 10Suna bayyana cewa kuna jiran bayyanar Dansa daga sama, wanda ya tasar daga matattu. Wannan shine Yesu, wanda ya 'yantad da mu daga fushi mai zuwa.

2

1Domin ku da kanku kun sani, 'yan'uwa, cewa zuwan mu gareku, ba a banza yake ba. 2Kun kuma san yadda aka wulakantar damu, aka kuma kunyatar damu a Filibi, kamar yadda kuka sani. Muna nan kuwa da karfin zuciya cikin Allahnmu domin yi maku bisharar Allah cikin fama da yawa.

3Domin kuwa gargadinmu zuwa a gare ku ba gurbatacciya bace, ko cikin rashin tsarki, ba kuma ta yaudara bace. 4A maimako, kamar yadda Allah ya amince damu, ya kuma damka mana amanar bishararsa, haka kuma muke yin magana. Muna maganar ba domin mu gamshi mutane ba, amma domin mu gamshi Allah. Domin shi ne yake gwada zuciyarmu.
5Domin bamu taba yi maku dadin baki ba, ko sau daya, kamar yadda kuka sani, ko kwadayi a asirce, kamar yadda Allah shine shaidar mu. 6Bamu kuma nemi daukaka daga mutane ko daga gare ku ko kuma wadansu ba. Da mun so da mun mori ikonmu a matsayin manzannin Almasihu.
7A maimakon haka, mun kaskantar da kanmu a tsakanin ku kamar yadda uwa take ta'azantar da 'ya'yan ta. 8Don haka muna da kauna domin ku, ba bisharar Allahnmu kadai muke jin dadin yi maku ba, amma harda bada rayukan mu domin ku. Domin kun zama kaunatattu ne a garemu, 9Kufa tuna, 'yan'uwa, game da aikinmu da famarmu. Dare da rana muna aiki sosai domin kada mu nawaita wa kowane dayan ku. A lokacin da muke yi maku bisharar Allah.
10Ku shaidu ne, haka ma Allah, yadda muka yi rayuwar tsarki da kuma adalci da rashin abin zargi a wajenku wadanda kuka bada gaskiya. 11Don haka kun kuma sani yadda muka rika yi da kowannenku, kamar uba da 'ya'yansa, yadda muka yi ma ku garadi da kuma karfafa ku, mun kuma shaida. 12Domin ku yi tafiya a hanyar da ta dace ga Allah, wanda ya kira ku zuwa ga mulkinsa da kuma daukakarsa.
13Domin wannan dalili ne yasa muke yi wa Allah godiya a koyaushe. Domin a lokacin da kuka karbi maganar Allah daga wurinmu wadda kuka ji, kun karbeta da gaske ba kamar maganar mutum ba. A maimako, kuka karbeta da gaskiyarta, kamar yadda take, maganar Allah. Wannan kalma kuma ita ce ke aiki a cikin ku wadanda kuka yi bangaskiya.
14Domin ku 'yan'uwa, kun zama masu koyi da ikilisiyoyin Allah da ke Yahudiya cikin Almasihu Yesu. Domim kuma kun sha wahala irin tamu daga wurin mutanen kasarku kamar yadda suma suka sha a hannun Yahadawa. 15Yahudawane suka kashe Ubangiji Yesu da sauran Annabawa, kuma Yahudawane suka koro mu, Basu gamshi Allah ba. A maimako, suna hamayya da dukkan mutane. 16Sun kuma haramta mana yin magana da Al'ummai domin su sami ceto. Sakamakon haka kuwa kullum suna cika zunubansu. Fushi kuma ya afko kansu daga karshe.
17Mu kuma, 'yan'uwa, mun rabu daku na karamin lokaci, a zahiri, ba a zuciya ba, mun kuma yi iyakar kokarinmu da marmarin ganin fuskarku. 18Domin mun yi maramarin zuwa gareku. Ni, Bulus, ba sau daya ba, amma Shaidan ya hanamu. 19To menene begenmu a gaba, ko murnarmu ko rawanin alfahari, a gaban Ubangijinmu Yesu a ranar zuwansa? Ko ba ku bane, da kuma sauran jama'a? 20Don kuwa kune daukakarmu da kuma farin cikinmu.

3

1Saboda haka, da bamu iya jimrewa ba, sai mukayi tunanin cewa ya dace mu dakata a Atina tukunna. 2Sai muka aikaTimoti, dan'uwanmu dakuma bawan Allah a bisharar Almasihu, domin karfafaku ya kuma ta'azantar daku a fannin bangaskiya. 3Mun yi haka ne saboda kada waninku ya raunana domin wadannan wahaloli. Domin ku da kanku kun sani cewa don haka aka kiraye mu.

4Hakika, a lokacin da muke tare daku, mun gaya maku cewa muna daf da shan wahala, haka ya kuma kasance, kamar yadda kuka sani. 5Domin haka, da ban iya jimrewa ba, sai na aiko domin in san yadda bangaskiyar ku take. Watakila ko magafci a wata hanya ya rinjaye ku, sai ya kasance wahalarmu ta zama a banza.
6Amma Timoti da ya dawo daga gareku sai ya kawo mamu labari mai dadi akan bangaskiyarku da kuma kaunarku. Yako gaya mana cewa kuna kyakkyawan tunani a kanmu, kuma kuna marmarin ganinmu yadda muke marmarin ganinku. 7Sabili da haka, 'yan'uwana, mun sami ta'aziyya tawurinku domin bangaskiyarku, a cikin dukkan bakin cikinmu da shan wuyamu.
8Yanzu a raye muke, idan kun tsaya da karfi a cikin Ubangiji. 9Gama wace irin godiya zamu ba Allah sabili da ku, domin dukan farin cikin da muke dashi a gaban Allah domin ku? 10Dare da rana muke yi maku addu'a sosai domin muga fuskokinku kuma mu cika abin da kuka rasa cikin bangaskiyarku.
11Bari Allah da kuma Ubanmu da kansa, da Ubangijinmu Yesu, ya bida sawayen mu zuwa gareku. 12Bari Ubangiji yasa ku karu ku kuma ribambamya a kaunar 'yan'uwanku da dukan mutane, kamar yadda muke maku. 13Bari yayi haka domin ya karfafa zukatanku marassa abin zargi a cikin tsarki a gaban Allah da Ubanmu a lokacin zuwan Ubangijinmu Yesu da dukan tsarkakansa.

4

1A karshe, 'yan'uwa, muna karfafa ku kuma muna yi maku gargadi cikin Ubangiji Yesu. Yadda kuka karbi umarni a garemu game da yadda dole za kuyi tafiya kuma ku gamshi Allah, kuma a cikin wannan hanya ku tafi, ku kuma wuce haka. 2Domin kun san umarnin da muka baku cikin Ubangiji Yesu.

3Gama wannan ne nufin Allah: kebewar ku - cewa ku kauce wa zina da fasikanci, 4Cewa kowannenku ya san yadda zai rike mata tasa cikin tsarki da girmamawa. 5Kada kayi mata cikin zautuwar sha'awa (kamar al'ummai wadanda basu san Allah ba). 6Kada wani ya kuskura yaci amanar dan'uwansa akan wannan al'amari. Gama Ubangiji mai ramuwa ne akan dukkan wadannan al'amura, Kamar yadda a baya muka yi maku kashedi kuma muka shaida.
7Gama Allah bai kira mu ga rashin tsarki ba, amma ga rayuwar tsarki. 8Domin haka, duk wanda yaki wannan ba mutane yaki ba, amma Allah, wanda ya bada Ruhunsa Mai Tsarki a gareku.
9Game da kaunar 'yan'uwa, baku bukatar wani ya sake rubuta maku, gama ku da kanku Allah ya koyar da ku kaunar 'yan'uwa. 10Ba shakka, kunayin haka ga dukkan 'yan'uwa wadanda ke cikin dukkan Makidoniya. Amma muna gargadin ku 'yan'uwa, kuyi haka bugu da kari. 11Kuma muna gargadin ku 'yan'uwa kuyi kokari ku zauna a natse, ku kula da al'amuranku, kuyi aiki da hannuwanku, Yadda muka umarceku a baya. 12Kuyi haka domin tafiyar ku ta zama dai dai a gaban wadanda basu bada gaskiya ba, kuma ya zama baku cikin bukatar komai.
13Bamu so ku zama da rashin fahimta ba, 'yan'uwa, game da wadanda sukayi barci, domin kada kuyi bacin rai kamar sauran wadanda basu da tabbacin abinda ke gaba. 14Domin idan mun bada gaskiya Yesu ya mutu kuma ya tashi, haka kuma tare da Yesu Allah zai maido da duk wadanda suka yi barci a cikinsa. 15Gama muna fada maku wannan daga maganar Ubangiji, cewa mu da muke a raye, da aka bari har zuwan Ubangiji, babu shakka ba za mu riga wadanda suka yi barci ba.
16Gama Ubangiji da kan sa zai sauko daga sama. Zai zo da muryar babban mala'ika, da karar kahon Allah, sai matattu cikin Almasihu su fara tashi. 17Sai mu da muke a raye, wadanda aka bari, tare dasu za'a fyauce mu zuwa cikin gizagizai, mu hadu da Ubangiji cikin sararin sama. Haka zamu cigaba da kasancewa da Ubangiji. 18Domin haka ku ta'azantar da juna da wadannan maganganu.

5

1Yanzu fa game da zancen lokatai da zamanai 'yan'uwa, ba ku da bukatar a rubuta maku wani abu. 2Domin ku da kanku kun sani kwarai cewa ranar zuwan Ubangiji kamar barawo take da dare. 3Da suna zancen "zaman lafiya da kwanciyar rai," sai hallaka ta zo masu ba zato ba tsammani. Zai zama kamar nakudar haihuwa ce da ke kama mace mai ciki. Ba su kwa da wata hanyar kubuta.

4Amma ku, 'yan'uwa, ai ba cikin duhu kuke ba har da wannan rana zata mamaye ku kamar barawo. 5Domin dukkan ku 'ya'yan haske ne 'ya'yan rana kuwa. Mu ba 'ya'yan dare ba ne ko na duhu, 6Don haka, kada muyi barci kamar yadda sauran ke yi. Maimakon haka, bari mu kasance muna zaman tsaro kuma muna a fadake. 7Don masu yin barci da dare suke yin barci, haka kuma masu sha su bugu ma da dare suke yi.
8Tunda shike mu 'ya'yan rana ne, bari mu zauna a natse. Bari musa sulke na bangaskiya da kauna, mu kuma sa kwalkwali don ceton mu dake gaba. 9Domin Allah bai kaddara mu ga fushinsa ba, sai dai ga samun ceto ta wurin Ubangijin mu Yesu Almasihu. 10Shi ne wanda ya mutu domin mu, don ko da muna raye ko muna mace, mu iya rayuwa tare da shi, 11Domin haka ku ta'azantar da juna ku kuma inganta juna, kamar yadda kuke yi.
12Muna rokon ku, 'yan'uwa, ku bada daraja ga wadanda suke aiki a tsakaninku wadanda kuma suke shugabanci a kan ku cikin Ubangiji, wadanda kuma suke horonku. 13Muna kuma rokon ku, da ku kula dasu ku kuma kaunacesu sabili da irin ayyukansu. Ku kuma yi zaman lafiya da junan ku. 14Muna yi maku gargadi 'yan'uwa; ku jawa marassa ji kunne, ku karfafa marassa karfin zuciya, ku taimaki gajiyayyu, kuyi zaman hakuri da kowa.
15Ku lura kada wani ya rama mugunta da mugunta, Maimakon haka ma, Ku cigaba da abinda ke mai kyau ga juna da kowa duka. 16Kuyi farin ciki koyaushe. 17Kuyi addu'a ba fasawa. 18A cikin kome kuyi godiya. Domin wannan ne nufin Allah a cikin Yesu Almasihu game daku.
19Kada ku hana Ruhun Allah aiki a cikin ku. 20Kada ku raina anabce anabce. 21Ku gwada komai. Ku rike abinda ke mai kyau. 22Ku kaucewa duk wani abinda yayi kama da mugunta.
23Bari Allah na salama ya mai da ku cikakun tsarkaka. Bari dukkan ruhun ku, da zuciyar ku, da jikin ku su zama adanannu marassa zargi domin zuwan Ubangijin mu Yesu Almasihu. 24Wanda ya kira ku mai aminci ne, wanda kuma zai aikata.
25Yan'uwa, kuyi addu'a domin mu. 26Ku gaida dukkan yan'uwa da tsattsarkar sumba. 27Ina rokon ku saboda Ubangiji ku karanta wasikar nan ga dukkan 'yan'uwa. 28Bari alherin Ubangijin mu Yesu Almasihu shi kasance tareda ku.

2 Tasalonikawa

1

1Bulus da Silbanus da Timoti, zuwa ga ikilisiyar Tasolonika cikin Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Almasihu. 2Bari alheri ya kasance tare da ku da salama daga Allah Ubanmu da Ubangijinmu Yesu Almasihu.

3Lallai ne mu godewa Allah kulluyaumin domin ku, yan'uwa. Domin hakan dai dai ne, saboda bangaskiyarku ta karu sosai, kuma kaunar junanku tana karuwa. 4Mu da kanmu muna fahariya da ku a ikilisiyoyin Allah. Muna maganar hakurinku da bangaskiyarku a cikin dukkan tsananin da kuke fuskanta. Muna maganar kuncin da kuke jimrewa. 5Wannan itace alamar shari'ar Allah ta adalci. Sakamakon haka shine za a dauke ku cancantattu na mulkin Allah wanda kuke wahala dominsa.
6Adalci ne ga Allah ya mayar da kunci ga wadanda suke kuntata maku, 7ya kuma baku hutu ku dake shan wuya tare da mu. Zai yi haka ne a bayyanar Ubangiji Yesu daga sama da Mala'ikun ikonsa. 8A cikin wuta mai huruwa zai dau fansa bisa wadanda basu san Allah ba da wadanda basu karbi bisharar Ubangijinmu Yesu almasihu ba.
9Za su sha azaba ta hallaka har abada daga fuskar Ubangiji da kuma daukakar ikonsa. 10Zai yi wannan lokacin da yazo a wannan rana don jama'arsa su daukaka shi, kuma ya zama abin mamaki ga dukkan wadanda suka bada gaskiya. Domin kun gaskata shaidarmu a gare ku.
11Saboda wannan muke addu'a kullum domin ku. Muna addu'a domin Allahnmu ya sa ku cancanci kiran ku. Muna addu'a ya biya ku muradin ku na yin nagarta da dukkan wani aikin bangaskiya da kuma iko. 12Muna addu'a haka domin sunan Ubangijinmu Yesu ya sami daukaka daga gare ku. Addu'armu itace ya daukaka ku, saboda alherin Allahnmu da Ubangijinmu Yesu Almasihu.

2

1Yanzu game da zuwan Ubangijinmu Yesu Almasihu da taruwarmu domin kasancewa tare da shi; muna rokonku yan'uwa, 2kada kuyi saurin damuwa ko ku gigice saboda wani ruhu ko kuma sako ko kuma wasika da ta yi kamar daga wurin mu, da ke cewa ranar zuwan Ubangiji ta rigaya ta zo.

3Kada wani ya yaudare ku ta kowace hanya. Domin wannan rana baza ta zo ba sai fandarewar nan ta zo kuma an bayyana mutumin tawayen nan wato dan hallaka. 4Wannan shi ne wanda ya ke gaba, yana kuma daukaka kansa fiye da duk abin da ake kira Allah ko kuma ake bautawa. Sakamakon haka yana zama a kursiyin Allah har ma yana cewa shine Allah.
5Baku tuna ba lokacin da nake tare daku na gaya maku wadannan abubuwa? 6Yanzu kun san abinda ke tsaida shi, domin a bayyana shi a lokacin da ya dace. 7Ko yanzu asirin take shari'a ya na aiki, sai dai a kwai wanda ke tsaida shi yanzu har sai an dauke shi.
8Sa'anan za'a bayyana dan tawayen, wanda Ubangiji Yesu zai hallaka shi da numfashin bakinsa. Ubangiji zai mayar da shi ba kome ba ta wurin bayyanuwar zuwansa. 9Mai tawayen nan kuwa, zai zo ne bisa ga aikin shaidan da dukan iko, alamu, da al'ajiban karya, 10da kuma dukan yaudara ta rashin adalci. Wadannan abubuwa za su zama ga wadanda suke hallaka, saboda ba su karbi kaunar gaskiya ba domin su sami ceto.
11Saboda wannan dalilin Allah ya aiko masu da sabani, saboda su yarda da karya. 12Sakamakon shine dukkan su za'a yi masu shari'a, wato wadanda ba su yarda da gaskiya ba suna kuma jin dadin rashin adalci.
13Amma muna masu godiya kulluyaumin ga Allah domin ku, yan'uwa wadanda Ubangiji yake kauna. Ubangiji ya zabe ku a matsayin yayan fari don ceto cikin tsarkakewar Ruhu da gaskatawa da gaskiya. 14Wannan shine abinda ya kira ku gare shi ta wurin bishararmu domin ku sami daukakar Ubangijinmu Yesu Almasihu. 15Saboda haka yan'uwa, ku tsaya da gaske. Ku rike al'adun da aka koya maku, ko ta kalma ko kuma ta wasikarmu.
16Yanzu bari Ubangiji Yesu Almasihu da kansa, da Allah Ubanmu wanda ya kaunace mu ya ba mu madawwamiyar ta'aziya da gabagadi mai kyau domin gaba ta wurin alheri, 17ya ta'azantar da ku ya kuma gina zuciyarku cikin kowane aiki mai kyau da kalma.

3

1Yanzu yan'uwa, ku yi mana addu'a saboda maganar Ubangiji tayi sauri ta sami daukaka, kamar yadda take tare da ku. 2Ku yi addu'a domin mu kubuta daga mutane masu mugunta da keta, gama ba kowa ke da bangaskiya ba. 3Amma Ubangiji mai aminci ne, shi wanda zai kafa ku ya tsare ku daga mugun.

4Muna da gabagadi cikin Ubangiji a kan ku, cewa kuna yi, kuma za ku ci gaba da yin abubuwan da muka umurta. 5Ubangiji ya bi da zuciyarku zuwa kaunar Allah da kuma jimrewar almasihu.
6Yanzu muna umurtar ku, yan'uwa, a cikin sunan Ubangiji Yesu Almasihu, ku guji duk dan'uwa wanda yake zaman banza ba kuma akan al'adun da kuka karba daga wurin mu ba. 7Saboda ku da kan ku kun sani yana da kyau kuyi koyi da mu. Ba mu yi zama a cikin ku kamar wadanda ba su da tarbiya ba. 8Ba mu kuma ci abincin kowa ba tare da mun biya ba. Maimakon haka, mun yi aiki dare da rana cikin wahala da kunci domin kada mu dora wa kowa nauyi. 9Mun yi haka ba don ba mu da iko ba. Maimakon haka, mun yi wannan ne saboda mu zama abin koyi a wurin ku, domin ku yi koyi da mu.
10Lokacin da muke tare da ku, mun umurce ku, "Duk wanda ba ya son yin aiki, kada yaci abinci." 11Saboda mun ji cewa wasun ku sun ki yin aiki. Ba su aiki sai dai shiga shirgin wasu. 12Irin wadannan, muke umurta da kuma karfafa wa cikin Ubangiji Yesu Almasihu, da su yi aiki da natsuwa, suna cin abincin kan su.
13Amma ku yan'uwa, kada ku rabu da yin abinda ke daidai. 14In wani yaki biyayya da kalmominmu cikin wannan wasika, ku kula da shi kuma kada kuyi ma'amalar komai dashi, saboda ya ji kunya. 15Kada ku dauke shi a matsayin makiyi, amma ku gargade shi a matsayin dan'uwa.
16Bari Ubangijin salama da kansa ya ba ku salama kulluyaumin ta kowace hanya. Ubangiji ya kasance tare da ku duka. 17Wannan ita ce gaisuwa ta, ni Bulus, da hannuna, wanda shine alama a kowace wasika ta. Haka nake rubutu. 18Bari alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu ya kasance tare da ku duka.

Wasikar bulus manzo ta fari zuwa ga timoti

1

1Bulus, manzon Almasihu Yesu bisa ga umarnin Allah Mai cetonmu, da Almasihu Yesu begenmu, 2zuwa ga Timoti, dana na gaske cikin bangaskiya: Alheri, jinkai da salama daga wurin Allah da Almasihu Yesu Ubangijinmu.

3Kamar yadda na nanata maka ka yi, da zan tafi Makidoniya cewa, ka dakata a Afisa domin ka umarci wadansu mutane kada su koyar da wata koyarwa dabam. 4Kada su bata lokacinsu wajen sauraron tatsunniyoyi da kididdiga marar iyaka. Wannan yana haddasa gardandami, maimakon taimakawa shirin Allah, da ke ta wurin bangaskiya.
5Manufar shari'a kuwa kauna ce daga tsabtacciyar zuciya, da tsatstsakan lamiri, da kuma sahihiyar bangaskiya. 6Wadansu sun kauce daga tafarkin sun juya zuwa ga maganganun banza. 7Suna so su zama malaman sha'ria, amma basu fahimci abin da suke fada ba ko abin da suka tsaya akai. 8Amma mun sani shari'a tana da kyau idan an yi amfani da ita bisa ga ka'ida.
9Gama mun san wannan, shari'a ba domin mai adalci take ba, amma domin marasa bin doka, mutane masu tawaye, da marasa bin Allah, da masu zunubi, da marasa Allah, da masu sabo. An bada shari'a domin masu kisan iyaye maza da iyaye mata, da masu kisan kai, 10Domin fasikai da 'yan ludu, domin masu satar mutane su kai su bauta, domin makaryata, da masu shaidar zur, da kuma dukan abin da ke gaba da amintaccen umarni. 11Wannan umarni bisa ga daukakkiyar bisharar Allah ne mai albarka, wadda aka bani amana.
12Ina gode wa Almasihu Yesu Ubangijimu. wanda ya karfafa ni, gama ya karbe ni amintacce, ya sani cikin hidimarsa. 13Dama can ni mai sabo ne, mai tsanantawa kuma dan ta'adda. Amma duk da haka aka yi mani jinkai domin na yi su cikin jahilci da rashin bangaskiya. 14Amma alherin Ubangijinmu ya kwararo mani tare da bangaskiya, da kauna da ke cikin Almasihu Yesu.
15Wannan bishara amintacciya ce, ta isa kowa ya karba, cewa Almasihu Yesu ya zo cikin duniya domin ceton masu zunubi, a cikinsu kuwa ni ne mafi lalacewa. 16Saboda haka ne na sami jinkai, domin ta wurina ni na farko, a nuna hakurin Yesu Almasihu. Ya yi wannan domin in zama misali ga wadanda za su bada gaskiya zuwa rai madawwami. 17Yanzu, ga Sarkin zamanai, marar mutuwa, boyayye, Allah makadaici girma, da daukaka su tabbata a gare shi har abada abadin. Amin.
18Ina danka wannan umarni gareka, dana, Timoti. Ina haka ne bisa ga anabcin da aka yi a baya game da kai, domin ka shiga yaki mai kyau. 19Ka yi wannan domin ka zama da bangaskiya da kyakkyawan lamiri. Wadansu mutane sun ki sauraron wannan suka yi barin bangaskiyarsu. 20Kamar su Himinayus da Iskandari, wadanda na bada su ga shaidan domin su horu su koyi kin yi sabo.

2

1Don haka da farko dai, Ina roko a yi roke-roke da addu'o'i, da yin roko domin jama, a dukka, da ba da godiya, a yi haka domin dukkan mutane, 2domin sarakuna da dukkan masu mulki, domin mu yi zaman salama da rayuwa a natse cikin Allahntaka da daraja. 3Wannan yana da kyau da karbuwa a gaban Allah mai cetonmu. 4Yana so dukkan mutane su sami ceto, su kai ga sanin gaskiya.

5Domin Allah daya ne, Matsakanci kuma daya ne, tsakanin Allah da mutum, wannan mutum Almasihu Yesu ne. 6Ya bada kansa fansa domin kowa, domin shaida a daidaitaccen lokaci. 7Sabo da wannan dalilin, aka sa ni kaina, na zama mai shelar bishara da manzo. Gaskiya nake fada. Ba karya nake yi ba. Ni mai koyarwa ne na al'ummai cikin gaskiya da kuma imani.
8Saboda haka, ina so maza da ke a kowanne wuri suyi addu'a, kuma suna daga hannuwa masu tsarki a sama ba tare da fushi da gardama ba. 9Kazalika, ina so mata su sa kayan da ya cancanta, da adon da ya dace da kamun kai. Kada su zama masu kitson gashi da zinariya da azurfa da tufafi masu tsada. 10Ina so su sa tufafin da ya cancanci matan da ke rayuwar Allahntaka ta wurin kyawawan ayyuka.
11Mace ta koya cikin natsuwa da saukin kai a cikin komai. 12Ban ba da izini mace ta koyar ko ta nuna iko a kan namiji ba, amma ta zauna da natsuwa.
13Adamu ne aka fara halitta, kafin Hauwa'u. 14Ba Adamu ne aka yaudara ba, amma macen ce aka yaudara cikin laifi. 15Duk da haka, zata sami ceto ta wurin haifuwar 'ya'ya, idan suka ci gaba cikin bangaskiya, da kauna da tsarki da sahihiyar zuciya.

3

1Wannan magana tabattaciya ce: Idan wani na da marmari ya zama shugaban Ikilisiya, ya na marmarin aiki mai kyau. 2Don haka, wajibi ne shugaban Ikilisiya ya zama mara abin zargi. Ya zama mai mace daya. Wajibi ne ya zama mai kamewa, mai hankali, mai natsuwa mai karbar baki. Wajibi ne ya iya koyarwa. 3Kada ya zama mashayin giya, da mai tankiya. A maimakon haka ya zama da natsuwa, mai salama. Ba mai son kudi ba.

4Wajibi ne ya iya lura da gidansa da kyau, 'ya'yansa su zama masu yi masa biyayya da dukkan bangirma. 5Gama idan mutum bai iya sarrafa gidansa ba, ta yaya zai iya lura da Ikkilisiyar Allah?
6Bai kamata ya zama sabon tuba ba, domin kada ya kumbura da girman kai, kada ya fadi cikin irin hukunci da aka yi wa Ibilis. 7Wajibi ne kuma ya kasance mai kyakyawar shaida a cikin wadanda ba masubi ba, domin kada ya fadi cikin kunya da kuma tarkon Ibilis.
8Hakanan kuma Dikinoni su kasance da halin mutunci, ba masu magana biyu ba. Bai kamata su zama mashayan giya ko masu hadama ba. 9Su zama masu rikon bayyananniyar gaskiyar bangaskiya da lamiri mai tsabta. 10Daidai ne kuma a fara tabbatar da su, daga nan su fara hidima domin basu da abin zargi.
11Hakanan ma mata su zama masu mutunci. Bai kamata su zama magulmanta ba, amma masu kamewa da aminci cikin komai. 12Tilas Dikinoni su zama masu mata daya daya. Su iya kulawa da 'ya'yansu da gidajensu. 13Gama wadanda suka yi hidima da kyau sun sami tsayawa mai kyau da gabagadi cikin bangaskiyar da ke cikin Almasihu Yesu.
14Ina rubuta maka wadannan abubuwa, da sa zuciya zan zo wurin ka ba da jimawa ba. 15Amma idan na yi jinkiri, ina rubuta maka ne domin ka san yadda za ka gudanar da al'amuranka a cikin gidan Allah, wato Ikklisiyar Allah rayyayiya, ginshiki da kuma mai tallafar gaskiya.
16Babu musu an bayyana cewa ibadarmu ta gaskiya da girma take: "Ya bayyana kansa cikin jiki, Ruhu ya baratar da shi, mala'iku suka gan shi, aka yi shelarsa a cikin al'ummai, aka gaskanta shi a duniya, sa'an nan aka dauke shi sama cikin daukaka.

4

1To Ruhu ya fada a fili cewa, a zamanin karshe wadansu mutane za su kauce daga bangaskiya, su mai da hankalin su ga ruhohi masu rudi, da koyarwar aljannu, 2cikin karya da munafunci. Lamirinsu zai yi kanta.

3Za su haramta aure da karbar abincin da Allah ya halitta, domin su raba da godiya a cikin wadanda suka bada gaskiya suka kuma san gaskiyar. 4Gama duk abin da Allah ya halitta yana da kyau. Domin duk abin da muka karba da godiya, bai kamata mu ki shi ba. 5Gama an tsarkake shi ta wurin maganar Allah da addu'a.
6Idan ka tuna wa 'yan'uwa wadannan abubuwa za ka zama bawan kirki na Almasihu. Domin ana gina ka ne ta wurin maganar bangaskiya da kuma kyakkyawar koyarwa wadda ka bi. 7Amma ka guji labaran almara wadanda tsofaffin mata ke so. Maimakon haka sai ka hori kanka cikin bin Allah. 8Domin horon jiki ya na da amfani kadan. Amma horon kai cikin bin Allah yana da amfani ga dukkan abubuwa. Gama a cikinsa akwai alkawari domin wannan rayuwar da kuma rayuwa mai zuwa.
9Maganan nan amintacciyace ta isa a karbe ta dungum. 10Dalilin da ya sa kenan mu ke aiki tukuru. Domin muna sa bege ga Allah mai rai, mai ceton dukkan mutane, musamman masu ba da gaskiya.
11Ka yi shela ka kuma koyar da wadannan abubuwa. 12Kada ka yarda kowa ya rena kuruciyarka. Maimakon haka, ka zama abin koyi ga dukkan masubi: a furci, hali, kauna, aminci da kuma tsarki. 13Har sai na zo, ka himmatu da yin karatu, da wa'azi, da kuma koyarwa.
14Kada ka yi sakaci da baiwar da ka ke da ita wadda aka baka ta wurin anabci sa'ad da dattawa suka dibiya maka hannayensu. 15Ka kula da wadannan abubuwa. Ka himmatu a cikinsu. Domin ci gabanka ya zama sananne a idanun kowa. 16Ka kula da kanka da kuma koyawarka. Ci gaba a cikinsu. Domin ta yin haka ne za ka ceci kanka da masu sauraronka.

5

1Kada ka tsauta wa dattijo. Sai dai ka gargade shi kamar mahaifi. Ka gargadi samari kamar 'yan'uwa. 2Gargadi dattawa mata kamar iyaye mata, 'yan mata kamar 'yan'uwa mata cikin dukkan tsarki.

3Ka girmama gwamraye, gwamraye na gaske. 4Amma gwamruwar da take da 'ya'ya ko jikoki, bari su fara nuna bangirma cikin danginsu. Bari su sakawa iya-yensu, domin Allah yana jin dadin haka.
5Amma gwamruwa ta gaske da ke ita kadai, ta kafa begenta ga Allah. Kullum tana tsananta yin roke-roke da addu'o'i dare da rana. 6Amma, mace mai son zaman annashuwa ta riga ta mutu, ko da shike tana raye.
7Kuma ka yi wa'azin wadannan al'amura donsu zama marasa abin zargi. 8Amma idan mutum bai iya biyan bukatun 'yan'uwansa ba, musamman iyalin gidansa, ya musunci bangaskiya, kuma gara marar bi da shi.
9Bari a lisafta mace gwamruwa idan ba ta kasa shekara sittin ba, matar miji daya. 10A san ta da kyawawan ayyuka, ko ta kula da 'ya'yanta, ko tana mai karbar baki, ko mai wanke kafafun masubi, ko mai taimakon wadanda ake tsanantawa, mai naciya ga kowanne kyakkyawan aiki.
11Amma game da gwamraye masu kuruciya, kada a sa su cikin lissafi. Domin idan suka fada cikin sha'awoyin jiki da ke gaba da Almasihu, sukan so su yi aure. 12Ta wannan hanya ce sun tara wa kansu tsarguwa saboda sun tada alkawarinsu na fari. 13Sun saba da halin ragwanci, suna yawo gida gida. Ba zama raggwaye kawai su ka yi ba. Amma sun zama magulmata, masu shishshigi, masu karambani. Suna fadin abin da bai dace ba.
14Saboda haka ina so gwamraye masu kuruciya su yi aure, su haifi 'ya'ya, su kula da gida, domin kada a ba magabci zarafin zargin mu ga aikata mugunta. 15Domin wadansu sun rigaya sun kauce zuwa ga bin shaidan. 16Idan wata mace mai bada gaskiya tana da gwamraye, bari ta taimakesu, don kada a nawaita wa Ikilisiya, domin Ikilisiya ta iya taimakon gwamraye na gaske.
17Dattawa wadanda suke mulki da kyau sun cancanci girmamawa ninki biyu, musamman wadanda suke aiki da kalma da kuma koyarwa. 18Gama nassi ya ce, "Kada a sa takunkumi a bakin takarkari lokacin da yake sussukar hatsi," kuma "Ma'aikaci ya cancanci a biya shi hakinsa."
19Kada ka karbi zargi game da dattijo sai shaidu sun kai biyu ko uku. 20Ka tsauta wa masu zunubi gaban kowa domin sauran su ji tsoro.
21Na umarce ka a gaban Allah, da Almasihu Yesu, da zababbun mala'iku ka kiyaye ka'idodin nan ban da hassada kuma kada ka yi komai da nuna bambanci. 22Kada ka yi garajen dibiya wa kowa hannuwa. Kada ka yi tarayya cikin zunuban wani. Ka tsare kanka da tsabta.
23Kada ka ci gaba da shan ruwa. Amma, maimakon haka ka sha ruwan inabi kadan saboda cikinka da yawan rashin lafiyarka. 24Zunuban wadansu mutane a bayyane suke, sun yi gaba da su cikin hukunci. Amma wadansu zunubansu na bin baya. 25Haka kuma, wadansu kyawawan ayyukansu a bayyane suke, amma wadan sun ma ba su boyuwa.

6

1Bari duk wadanda ke bayi a karkashin karkiya su ga iyayengijinsu sun cancanci dukan daraja. Su yi haka domin kada a sabawa sunan Allah da koyarwarsa. 2Bayin da suke da iyayengiji da ke masu ba da gaskiya kada su rena su saboda su 'yan'uwa ne. A maimakon haka, su yi masu hidima da kwazo. Gama iyayengijin da suke cin ribar aikinsu masu bi ne, kaunattatu kuma. Ka koyar ka kuma bayyana wadannan abubuwa.

3Idan ya kasance wani na koyar da wani abu dabam bai kuma yarda da amintaciyar koyarwa ba, wato maganar Ubangijinmu Yesu Almasihu. Alal misali ba su amince da koyarwa da ke kai ga Allahntaka ba. 4Wannan mutum mai girman kai ne, kuma bai san komai ba. A maimakon haka, yana da matukar jayayya da gardama game da kalmomi. Wadannan kalmomi na kawo kishi, da husuma, da zage-zage, da miyagun zace-zace, da 5yawan rashin jituwa tsakanin mutane masu rubabbun hankula. Sun bijire wa gaskiya. Suna tunani cewa ibada hanya ce ta yin arziki." Ka zame daga wadannan abubuwa.
6Yanzu bin Allah tare da dangana babbar riba ce. 7Gama ba mu kawo komai a duniya ba, ba zamu iya fita cikinta da komai ba. 8A maimakon haka, mu dangana da abinci da kuma sutura.
9To wadanda ke son zama mawadata su kan fada cikin jaraba, cikin tarko. Suna fadawa cikin abubuwan wauta da sha'awoyi masu illa da kowanne abu da ke sa mutane su dulmaya cikin lallacewa da hallaka. 10Gama son kudi shine tushen kowacce irin mugunta. Wadansu mutane garin neman kudi sun kauce daga bangaskiya, sun kuma jawowa kansu bakin ciki mai yawa.
11Amma kai, mutumin Allah, ka guji wadannan abubuwa, ka bi adalci, ibada, aminci, kauna, jimiri, da tawali'u. 12Ka yi fama, fama mai kyau na bangaskiya. Ka kama rai madawami da aka kira ka gare shi. A kan wannan ne ka ba da shaida a gaban shaidu masu yawa game da abin da ke da kyau.
13Ina ba ka wannan umarni a gaban Allah wanda ke rayar da dukan abubuwa, da gaban Almasihu Yesu, wanda ya fadi abin da ke gaskiya ga Bilatus Babunti. 14Ka bi doka daidai, babu abin zargi har bayanuwar Ubangijinmu Yesu Almasihu.
15Allah zai nuna bayyanuwarsa a daidai lokaci- Allah, mai albarka, Makadaicin iko, Sarkin da ke sarauta, Ubangiji mai mulki. 16Shine kadai marar mutuwa, mai zama cikin hasken da ba ya kusantuwa. Ba wanda ke ganinsa, ko ya iya hango shi. Girma ya tabbata a gare shi da kuma madawwamin iko. Amin.
17Ka gaya wa masu dukiya a cikin wannan duniya kada su daga kai, kada su sa bege ga arziki mara dawwama. Maimamakon haka, su sa begensu ga Allah wanda ke ba mu wadatar gaske domin jin dadin mu. 18Gaya masu su yi nagarta su arzurta a ayyuka nagari, su zama masu bayarwa hannu sake. 19Ta haka za su ajiye wa kansu harsashi mai kyau kan abin da ke zuwa domin su amshi rayuwa ta kwarai.
20Timoti, ka kare abin da aka ba ka. Ka nisanci maganar wauta da gardamomin da ke sabawa juna wanda ake kira ilimi a karyace. 21Wadansu mutane suna shelar wadannan abubuwa, don haka sun kauce wa bangaskiyar. Bari alheri ya kasance tare da kai.

Wasikar bulus manzo ta biyu zuwa ga timoti

1

1Bulus, manzon Almasihu Yesu ta wurin nufin Allah, bisa ga alkawarin rai da ke cikin Almasihu Yesu, 2zuwa ga Timoti, kaunataccen da: Alheri, jinkai, da salama daga Allah Uba da Almasihu Yesu Ubangijinmu.

3Na gode wa Allah, wanda na ke bautawa tun daga kakannina, da lamiri mai tsabta, sa'adda na ke tuna wa da kai cikin addu'o'ina koyaushe (dare da rana). 4Sa'adda na tuna da hawayenka, na yi marmarin ganinka, saboda in cika da farin ciki. 5An tunashshe ni game da sahihiyar bangaskiyarka, wadda ta samo asali daga kakarka Loyis da mahaifiyarka Afiniki. Na kuma tabbata ta na zaune a cikinka.
6Wannan shine dalilin da ni ke tunashshe ka cewa ka sake rura baiwar Allah da ke cikinka wadda ka samu sa'adda na dibiya maka hannuwana. 7Domin Allah bai ba mu ruhun tsoro ba, amma na iko da kauna da kamun kai.
8Saboda haka kada ka ji kunyar shaida ga me da Ubangijinmu, ko ni, Bulus, daurarrensa. Maimakon haka, ka zama a shirye ka sha wahala domin bishara bisa ga ikon Allah. 9Allah ne ya cecemu kuma ya kira mu da kira mai tsarki. Ya yi wannan, ba ta wurin ayyukanmu ba, amma ta wurin shirinsa da alherinsa. Ya ba mu wadannan abubuwan a cikin Almasihu Yesu kafin farkon zamanai. 10Amma yanzu an bayyana ceton Allah ta wurin bayyanuwar mai cetonmu Almasihu Yesu. Almasihu ne ya kawo karshen mutuwa ya kuma kawo rai marar karshe da ya bayyana ta wurin bishara. 11Domin wannan, an zabe ni mai wa'azi, manzo da mallami zuwa ga al'ummai.
12Domin wannan dalili na ke shan wahalar wadannan abubuwa. Amma ban ji kunya ba, domin na san shi, wanda na gaskanta. Na sakankance zai iya adana abinda na mika masa har zuwa ranan nan. 13Ka adana misalin amintattun sakwanni da ka ji daga gare ni, ta wurin bangaskiya da kauna da ke cikin Almasihu Yesu. 14Abu mai kyau da Allah ya danka maka, ka tsare shi ta wurin Ruhu Mai Tsarki, da ke zaune a cikinmu.
15Ka dai sani, dukkan wadanda su ke zama a Asiya sun juya mani baya. A cikin kungiyar akwai Fijalas da Harmajanas. 16Bari Ubangiji ya yi wa iyalin Onisifaras jinkai, domin ya na yawan yi mani hidima, kuma ba ya jin kunyar sarkata. 17Maimakon haka, sa'adda ya ke a Roma, ya neme ni da kokarin gaske, ya kuma same ni. 18Bari Ubangiji ya sa, ya sami jinkai daga gare shi a wannan rana. Dukkan hanyoyin da ya taimake ni a kasar Afisa, kun sani sarai.

2

1Domin wannan kai, dana, ka karfafa cikin alherin da ke cikin Almasihu Yesu. 2Abubuwan da ka ji daga gare ni a bainar jama'a masu yawa, ka danka su ga mutane masu aminci da za su iya koya wa wadansu kuma.

3Ka daure shan tsanani tare da ni, kamar amintaccen sojan Almasihu Yesu. 4Ba bu sojan da zai yi bauta yayin da ya nannade kansa da al'amuran wannan rayuwar, domin ya gamshi shugabansa. 5Hakanan, idan wani yana gasa a matsayin dan wasa, ba zai sami rawani ba tukuna har sai in ya karasa tseren bisa ga ka'idodin gasar.
6Wajibi ne manomi mai kwazon aiki ya fara karbar amfanin gonarsa. 7Ka yi tunani game da abin da na ke gaya maka, gama Ubangiji zai ba ka ganewa a cikin komai.
8Ka tuna da Yesu Almasihu, daga zuriyar Dauda, wanda a ka tayar daga matattu. Bisa ga wa'azin bisharata, 9wanda na ke shan wahala har ya kai ga dauri kamar mai laifi. Amma maganar Allah ba a daure ta ba. 10Saboda haka na jure wa dukkan abubuwa domin wadanda aka zaba, saboda su ma su sami ceton da ke cikin Almasihu Yesu, da daukaka madawwamiya.
11Wannan magana tabbatacciya ce: "Idan mun mutu tare da shi, za mu kuma rayu tare da shi. 12Idan mun jure, zamu kuma yi mulki tare da shi. Idan mun yi musun sa, shi ma zai yi musun mu. 13Idan mun zama marasa aminci, shi mai aminci ne koyaushe, domin shi ba zai yiwu ya musunta kansa ba."
14Ka yi ta tuna masu da wadannan abubuwan. Ka yi masu kashedi a gaban Allah kada su yi ta dauki ba dadi game da kalmomi. Saboda wannan bai da wani amfani. Domin wannan zai halakar da ma su sauraro. 15Ka yi iyakacin kokarika domin ka mika kanka ma'aikacin Allah wanda aka tabbatar, wanda babu dalilin kunya a gareshi. Wanda ya ke koyar da kalmar gaskiya daidai.
16Ka guje wa masu maganar sabo, wanda ya kan kara kaiwa ga rashin bin Allah. 17Maganarsu za ta yadu kamar ciwon daji. Daga cikinsu akwai Himinayus da Filitus. 18Wadannan mutanen sun kauce wa gaskiya. Sun fadi cewa an rigaya an yi tashin matattu. Suka birkitar da bangaskiyar wadansu.
19Duk da haka, ginshikin Allah ya tabbata. Ya na da wannan hatimi: "Ubangiji ya san wadanda ke nasa," Kuma "Duk mai kira bisa ga sunan Ubangiji dole ya rabu da rashin adalci." 20A gida mai wadata, ba kayayyaki na zinariya da azurfa ba ne kawai. Haka kuma akwai kayayyaki na itace da yunbu. Wadansu domin aikin mai daraja, wadansu kuma ga aiki mara daraja. 21Idan wani ya tsarkake kansa daga rashin daraja, shi kayan aiki ne mai daraja. An kebe shi, abin aiki domin mai gidan, kuma a shirye domin kowanne aiki mai kyau.
22Ka guje wa sha'awoyi na kuruciya, ka nemi adalci, bangaskiya, kauna da salama da wadanda suke kira ga sunan Ubangiji daga zuciya mai tsabta. 23Amma ka ki tambayoyi na wauta da jahilci. Ka sani sukan haifar da gardandami.
24Tilas bawan Ubangiji ya guje wa jayayya. A maimakon haka dole ya zama mai tawali'u ga kowa, mai iya koyarwa, kuma mai hakuri. 25Dole ne ya koyarwa mutane da su ke jayayya da shi a cikin tawali'u. Watakila Allah ya ba su ikon tuba domin sanin gaskiyar. 26Suna iya sake dawowa cikin hankalinsu kuma su bar tarkon Ibilis, bayan da ya cafke su domin nufinsa.

3

1Amma ka san da wannan: a cikin kwanakin karshe za a yi lokuta masu matsananciyar wahala. 2Gama mutane za su zama masu son kansu, masu son kudi, masu Kumburi, da girman kai, masu sabo, marasa biyayya ga iyaye, marasa godiya, da kuma marasa tsarki. 3Za su kasance marasa dabi'a, wadanda basu son jituwa da kowa, masu tsegumi, marasa kamun kai, 'yan tawaye, marasa kaunar nagarta. 4Za su zama masu zagon kasa, taurin kai, masu takama, da masu kaunar anishuwa fiye da kaunar Allah.

5Za su kasance da siffar ibada amma za su musunci ikonta. Ka juya daga wadannan mutanen. 6A cikinsu akwai wadanda suke shiga gidaje suna yaudarar mataye marasa hikima. Wadannan ne mataye wadanda suke cike da zunubi, kuma sun kauce hanya sabili da sha'awoyi dabam daban. 7Wadannan matayen suna ta koyo, amma ba za su taba kai wa ga sanin gaskiya ba.
8Kamar yadda Yannisu da Yambrisu suka yi jayayya da Musa. Haka nan wadannan malaman karya kuma suke yin tsayayya da gaskiya. Mutane ne lalatattu a zuciya, marasa sahihiyar bangaskiya. 9Amma ba za su yi nisa ba. Domin wautarsu za ta bayyana a fili ga kowa, kamar wadannan mutane.
10Amma kai, ka bi koyarwata, da dabi'ata, nufe nufena, da bangaskiyata, da jimriyata, da kaunata, da hakurina, 11da yawan kuncina, da wahalolina, da duk abubuwan da suka faru da ni a Antakiya, da Ikoniya da kuma Listra. Na jure a cikin kuncina. Amma a cikinsu dukka, Ubangiji ya cece ni. 12Duk wadanda su ke so su yi rayuwa ta ibada a cikin Almasihu Yesu za su sha tsanani. 13Miyagun mutane da masu hila za su yi ta kara lalacewa. Za su badda wasu. Su da kansu ma sun bijire.
14Amma kai, ka ci gaba da abubuwan da ka koya kuma ka gaskata da zuciya daya. Ka san daga wurin wanda ka koya. 15Ka san da cewa, tun kana dan karamin yaro ka san wadannan littattafai masu tsarki. Wadannan suna iya mai da kai mai hikima domin ceto ta wurin bangaskiya a cikin Almasihu Yesu.
16Dukkan Nassi hurarre ne daga Allah. Yana da amfani domin koyarwa, domin tsautawa, domin gyara, kuma domin horarwa cikin adalci. 17Wannan domin mutumin Allah ya zama cikakke ne, shiryayye domin dukkan ayyukan nagarta.

4

1Ina bada wannan umarni a gaban Allah da Yesu Almasihu, wanda zai yi wa rayayyu da matattu shari'a, kuma saboda bayyanuwarsa da mulkinsa: 2Ka yi wa'azin Kalma. Ka himmantu a kai ko da zarafi ko ba zarafi. Ka tsautar, ka kwabar, ka gargadar, da dukan hakuri da koyarwa.

3Gama lokaci na zuwa wanda mutane ba za su jure wa koyarwar kirki ba. Maimakon haka, zasu tattara wa kansu malamai bisa ga sha'awowin zuciyarsu. Za su rika fada masu abin da kunnuwansu ke so. 4Za su juya kunnuwansu daga koyarwar gaskiya, za su koma wa tatsunniyoyi na banza. 5Amma kai, sai ka natsu a cikin dukan abubuwa. Ka jure wa wahala; ka yi aikin mai bishara, ka cika hidimarka.
6Gama ana-tsiyaye ni. Lokacin yin kaurata yayi. 7Na yi tsere na gaskiya; na kuma kammala tseren; na rike bangaskiya. 8An adana mani rawani na adalci, wanda Ubangiji, alkali mai adalci, zai ba ni a ranan nan. Ba ni kadai ba, amma kuma ga dukkan wadanda suke kaunar zuwansa.
9Ka yi iyakacin kokarinka ka zo wurina da sauri. 10Domin Dimas ya yashe ni. Ya kaunaci wannan duniyar, ya tafi Tassalonika, Kariskis ya tafi Galatiya, Titus kuma ya tafi Dalmatiya.
11Luka ne kadai yake tare da ni. Ka nemo Markus ka zo tare da shi domin yana da amfani a gareni a cikin aikin. 12Na aiki Tikikus zuwa Afisus. 13Ka kawo mani mayafin da na bari a Taruwasa wurin Karbus, idan za ka zo ka taho da shi, duk da littatafan nan, musanman takardun nan.
14Iskandari makerin dalma ya kulla mani makirci ba kadan ba. Ubangiji zai biya shi gwargwadon ayyukansa. 15Kai ma ka yi hankali da shi, domin yana tsayyaya da maganganunmu sosai. 16Da farkon kariyar kaina, babu wanda ya goyi bayana. Maimakon haka kowa ya guje ni. Bana so dai a lissafta wannan a kansu.
17Amma Ubangiji ya kasance tare da ni, ya kuma karfafa ni, yadda ta wurina, shelar ta sami cika da kyau, domin dukan al'ummai su ji. An kwato ni daga bakin zaki. 18Allah zai kubutar ni daga dukan ayyukan mugunta, ya kuma cece ni domin mulkinsa na sama. Daukaka ta tabatta a gareshi har abada abadin. Amin.
19Ka gayar da Briskilla, da Akila, da gidan Onisifurus. 20Arastus ya nan zaune a Korinti, amma na bar Turufimus ya na zazzabi a Militus. 21Ka yi iyakar kokarinka, ka zo kamin hunturu. Yubulus yana gayar da kai, haka ma Budis da Linus da Kalafidiya da dukan 'yan'uwa. 22Bari Ubangiji ya kasance tare da ruhunka. Bari Alheri ya kasance da kai.

Titus

1

1Bulus, bawan Allah, kuma manzon Yesu Almasihu, ta wurin bangaskiyar zababbun mutanen Allah da sanin gaskiya da ta yadda da allahntaka. 2Wadannan na cikin begen rai marar matuka wanda Allah, wanda babu karya a cikinsa, ya alkawarta kafin dukkan lokatan zamanai. 3A daidai lokaci, ya bayyana maganarsa ta wurin sakonsa da ya damka mani in shelar. Zan yi wannan ta wurin umarnin Allah mai ceton mu.

4Zuwa ga Titus, da' na gaske a cikin bangaskiyarmu. Alheri, jinkai da salama daga wurin Allah Uba da Almasihu Yesu mai ceton mu. 5Sabili da wannan ne na bar ka a Karita domin ka daidaita abubuwan da basu cika ba, ka kuma nada dattibai a dukan birane kamar yadda na umarceka.
6Dole ne dattijo ya zama marar abin zargi, mijin mace daya, da amintattun 'ya'ya wadanda babu wani zargi na mugunta ko rashin kamun kai a kansu. 7Wajibi ne shugaban Ikklisiya, a matsayin sa na mai kulla da haikalin Allah, ya zama marar aibi. Kada ya zama mai surutu ko rashin hakuri. Kada ya zama mai saurin fushi, ko mashayi, ko mai hayaniya, ko mai handama.
8Maimakon haka, ya zama mai karbar baki, abokin abinda ke mai kyau. Dole ne ya zama mai hankali, adali, cike da allahntaka, da kuma kamun kai. 9Ya zama mai rike amintaccen sakon da aka koyar da karfi, yadda zai iya karfafa wasu da koyarwa mai kyau ya kuma yi wa wadanda suke hamayya da shi gyara.
10Domin akwai kangararrun mutane dayawa, musamman masu kaciya. Maganganunsu na banza ne. Suna yaudara kuma suna badda mutane. 11Wajibi ne mu hana su. Suna koyar da abinda bai kamata su koyar ba saboda makunyaciyar riba suna kuma rusar da iyalai dungum.
12Daya daga cikinsu, kuma mai hikima ne daga cikinsu, yace, "Kirawa manyan makaryata ne, lalatattu kuma miyagun dabbobi, masu kyiuya da zarin cin abinci." 13Wannan magana gaskiya ne, ka yi masu gyara da tsanani yadda zasu kafu a cikin bangaskiya.
14Kada ka mai da hankalin ka ga tatsunniyoyi na Yahudawa ko dokokin mutane wadanda sun sauya gaskiya.
15Ga wadanda suke da tsarki, komai mai tsarki ne. Amma wadanda suke marasa tsarki da rashin bangaskiya, komai marar tsarki ne. Domin zuciyarsu da lamirinsu sun gurbata. 16Suna cewa sun san Allah, amma sun musanta shi ta wurin ayyukansu. Sun zama abin kyama da marasa biyayya. Ba za a iya tabbaatar dasu ba akan wani aiki maikyau.

2

1Amma kai, ka fadi abinda yayi daidai da amintaccen umarni. 2Dole tsofaffin mazaje su zama masu kamun kai, masu daraja kansu, masu-hankali, masu aminci cikin bangaskiya, cikin kauna da jurewa.

3Haka ma tsofaffin mataye su kame kansu da girma, ba magulmata ba. Kada su zama bayi wajen yawan shan ruwan inabi. Su koyar da abubuwa masu kyau 4domin su koyar da kananan mataye da hikima su kaunaci mazajensu da 'ya'yansu. 5Su horar dasu su zama masu hikima da tsabtar zuci, masu tsaron gidajensu, kuma masu biyayya da mazajensu. Suyi wadannan abubuwa saboda kada maganar Allah ta sami zargi.
6Ta haka kuma, ka karfafa samari, su zama masu hankali. 7A kowanne fanni, ka mayar da kan ka abin koyi a cikin kyawawan ayyuka; idan kayi koyarwa, ka nuna mutunci da martaba. 8Ka bada sako lafiyayye marar abin zargi, yadda masu hamayya da maganar Allah zasu ji kunya, domin rashin samun mugun abin fadi akan mu.
9Bayi suyi biyayya ga iyayengijin su a cikin komai. Su faranta masu rai, ba suyi gardama dasu ba. 10Kada suyi sata. Maimakon haka, sai su nuna dukan bangaskiya mai kyau, domin suyi wa koyarwarmu game da Allah mai cetonmu kwalliya a cikin dukan komai.
11Domin alherin Allah ya bayyana ga dukan mutane. 12Yana koya mana mu musanci miyagun ayyuka, da sha'awoyin duniya. Yana horar damu muyi zama cikin hankali, da adalci a cikin hanyar allahntaka a wannan zamani 13yayin da muke cigaba da jiran karba albarkataccen begenmu, wato bayyanuwar daukakar Ubangiji Allah da kuma mai cetonmu Yesu Almasihu.
14Yesu ya bada kansa domin mu, domin ya cece mu daga rashin kiyaye doka ya mai damu masu tsarki, domin sa, mutane na musamman wadanda suke da marmarin aikata kyawawan ayyuka.
15Ka yi magana da karfi ka karfafawa wadannan abubuwa. Ka yi gyara da dukan iko. Kada ka bar wani ya raina ka.

3

1Ka tuna masu su zama masu sadaukar da kai ga masu mulki da masu iko, suyi masu biyayya, su zama a shirye domin kowane kyakkyawan aiki. 2Ka tuna masu kada su zagi kowa, su gujiwa gardama, su bar mutane su bi hanyarsu, su kuma nuna tawali'u ga dukan mutane.

3Domin a da, mu da kan mu marasa tunani ne kuma masu rashin biyayya. Mun kauce hanya muka zama bayi ga sha'awoyin duniya da annashuwa. Mun yi zama a cikin mugunta da kishi. Mu lalatattu ne kuma muna kiyyaya da junanmu.
4Amma da jinkan Allah mai ceton mu da kaunarsa ga 'yan Adam ta bayyana, 5ba saboda wani aikin adalci da muka yi ba, amma sabili da jinkan sa ne ya cece mu. Ya cece mu ta wurin wankewar sabuwar haihuwa da sabuntuwar Ruhu Mai Tsarki.
6Allah ya zubo mana Ruhu Mai Tsarki a wadace ta wurin Yesu Almasihu mai cetonmu. 7Ya yi wannan saboda, bayan mun samu 'yantarwa ta wurin alherinsa, za mu zama magada a cikin begen rai na har abada.
8Wannan amintaccen sako ne. Ina son kayi magana gabagadi game da wadannan abubuwa, yadda dukan wadanda suka bada gaskiya ga Allah za suyi kudirin yin kyawawan ayyuka da Allah ya mika masu. Waddannan abubuwa masu kyau ne da kuma riba ga dukan mutane.
9Amma ka guji gardandami na wofi, da lissafin asali, da husuma da jayayya game da dokoki. Wadannan abubuwa basu da amfani kuma marasa riba. 10Ka ki duk wani dake kawo tsattsaguwa a tsakaninku, bayan ka tsauta masa sau daya ko biyu, 11ka kuma sani cewa wannan mutumin ya kauce daga hanyar gaskiya, yana zunubi kuma ya kayar da kansa.
12Sa'adda na aiki Artimas da Tikikus zuwa wurin ka, kayi hanzari ka same ni a Nikobolis, a can na yi shirin kasancewa a lokacin hunturu. 13Kayi hanzari ka aiko Zinas wanda shi gwani ne a harkar shari'a, da Afolos ta yadda ba zasu rasa komai ba.
14Ya kamata Jama'armu su koyi yadda zasu yi ayyuka masu kyau da zasu biya bukatu na gaggawa yadda ba za suyi zaman banza ba.
15Dukan wadanda suke tare da ni suna gaishe ka. Ka gai da masu kaunar mu a cikin bangaskiya. Alheri ya kasance tare da dukan ku.

Filimon

1

1Bulus, daurarren Yesu Almasihu, da kuma dan'uwa Timotawus zuwa ga Filimon, kaunataccen abokinmu da kuma abokin aikin mu, 2da Afiya yar'uwanmu da Arkifus abokin aikin mu a filin daga, da kuma Ikilisiyar da take taruwa a gidan ka: 3Alheri da salama su kasance gare ka daga wurin Allah Ubanmu, da Ubangiji Yesu Almasihu.

4Kowane lokaci ina gode wa Allah. Ina ambaton ku cikin addu'oi na. 5Na ji labarin kauna da bangaskiya da ka ke da ita a cikin Ubangiji Yesu da dukkan yan'uwa masu bi. 6Ina addu'a zumuntar bangaskiyarka ta inganta ga kawo sanin kowane kyakkyawan abu dake cikin mu a cikin Almasihu. 7Na yi farinciki kwarai, na kuma ta'azantu saboda kaunarka, saboda zukatan masu bi sun kwanta ta wurin ka, dan'uwa.
8Saboda haka, ko da ya ke ina da gabagadi a cikin Almasihu domin in ba ka umarni ka yi abinda ya kamata ka yi, 9duk da haka sabo da kauna, na fi so in roke ka- Ni, Bulus, dattijo, a yanzu kuma ga ni dan kurkuku domin Almasihu Yesu.
10Ina rokon ka saboda da na Onisimus, wanda na zama uba a gare shi sa'adda nake cikin sarkokina. 11Domin a da kam, ba shi da amfani a wurin ka, amma yanzu yana da amfani a gare ka da kuma a gare ni. 12Na kuma aike shi wurinka, shi wanda ya ke a cikin zuciyata kwarai. 13Na so da na rike shi a wuri na, domin ya rika yi mini hidima a madadin ka, a lokacin da ni ke cikin sarkoki saboda bishara.
14Amma ba na so in yi wani abu ba tare da sanin ka ba. Ba ni so nagarin aikinka ya zama na dole amma daga kyakkyawar nufi. 15Watakila dalilin da yasa ya rabu da kai na dan lokaci ke nan, domin ka karbe shi kuma har abada. 16Daga yanzu ba za ya zama bawa ba kuma, amma fiye da bawa, wato kaunataccen dan'uwa. Shi kaunatacce ne musamman a gare ni, har fiye da haka ma a gare ka, a cikin jiki da kuma cikin Ubangiji.
17Idan ka maishe ni abokin hidima, ka karbe shi kamar yadda za ka karbe ni. 18Idan kuwa ya yi maka abinda ba daidai ba ko kuwa kana bin sa wani abu, ka dauka yana wurina. 19Ni, Bulus, na rubuta wannan da hannuna: zan biya ka. Ba kuwa cewa sai na gaya maka cewa ina bin ka bashin kanka ba. 20I, dan'uwa, ka yi mani alheri cikin Ubangiji; ka ba zuciyata hutu a cikin Almasihu.
21Saboda Ina da tabbaci game da biyayyarka, na rubuta maka. Na san za ka yi fiye da abinda na roka. 22Harwayau, ka shirya mani masauki. Domin ina fata ta wurin adu'oinku, nan ba da dadewa ba za a maida ni wurin ku.
23Efafaras, abokina cikin Almasihu Yesu a kurkuku yana gaishe ka, 24haka ma Markus da Aristarkus, da Dimas, da Luka abokan aikina. 25Bari Alherin Ubangiji Yesu Almasihu ya kasance da Ruhunka. Amin.

Ibraniyawa

1

1A zamanin da, Allah ya yi wa kakanin kakanninmu magana ta hanyoyi ma su yawa iri iri, ta bakin annabawa. 2Amma a zamanin nan na karshe, ya yi mana magana ta wurin Dansa, wanda ya sa magajin kome, wanda ta wurinsa ya halicci duniya. 3Shi ne hasken daukakar Allah, ainihin kamanin zatinsa. Ya na rike da dukkan abubuwa ta ikon kalmarsa. Bayan da ya tsarkake zunubanmu, sai ya zauna a hannun dama na madaukaki a can sama.

4Ta haka ya ke da fifiko a kan mala'iku, kamar yadda sunansa da ya gada yake da fifiko nesa a kan nasu. 5Domin kuwa wanene a cikin mala'iku Allah ya taba cewa, "Kai Da na ne, yau na zama Uba a gare ka?" kuma, "Zan kasance Uba a gareshi, shi kuma, zai kasance Da a gare ni?"
6Kuma, da Allah ya kawo magaji a duniya, sai ya ce, "Dukan mala'ikun Allah su yi masa sujada." 7A game da mala'iku kuma sai ya ce, "yakan mai da mala'ikunsa ruhohi, masu hidimarsa kuma harsunan wuta.
8A game da Dan, ya ce "kursiyinka, ya Allah, na har abada abadin ne. Sandar sarautarka sanda ce ta tsantsar gaskiya. 9Ka kaunaci aikin adalci, ka ki aikin sabo. Saboda haka Allah, wato Allahnka, ya shafe ka da man farin ciki fiye da tsararrakinka."
10"Tun farko, Ubangiji, kai ne ka hallici duniya. Sammai kuma aikin hannayenka ne. 11Za su hallaka, amma kai madawwami ne. Duk za su tsufa kamar tufafi. 12Za ka nade su kamar mayafi, za su kuma sauya, amma kai kana nan ba sakewa, Har abada shekarunka ba za su kare ba."
13Amma wanene a cikin mala'ikun Allah ya taba cewa, "Zauna a hannun dama na, sai na sa makiyanka a karkashin kafafunka?" 14Ashe, ba dukkan mala'iku bane ruhohi, wadanda Allah yakan aika, don su yi wa wadanda za su gaji ceto hidima?

2

1Saboda haka, lalle ne mu kara mai da hankali musamman da abubuwan da mu ka ji, don kada mu yi sakaci, su sullube mana.

2Idan kuwa maganar nan da aka fada ta bakin mala'iku ta zama tabbatacciya, har kowanne keta umarni da rashin biyayya, suka gamu da sakamakonsu wanda ya kamace su, 3ta kaka za mu tsira, in mun ki kula da ceto mai girma haka? Domin Ubangiji da kansa, shi ne ya fara sanar da shi, wadanda suka saurare shi kuma suka tabbatar mana da shi. 4San'nan kuma Allah da kansa ya shaida ta wasu alamu, da abubuwan al'ajabai, da mu'ajizai iri iri, da kuma baiwar Ruhu Mai Tsarki dabam dabam da ya rarraba kamar yadda ya nufa.
5Ai ba ga mala'iku ba ne Allah ya sa mulkin duniyar nan da za a yi, wanda muke zance. 6Amma wani ya shaida a wani wuri cewa, "Mutum ma menene, har da za ka tuna da shi? Ko dan mutum ma, har da za ka kula da shi?
7Ka sa mutum ya gaza mala'iku; Ka nada shi da daukaka da girma. Bisa dukkan hallitta. 8Ka dora shi a kan dukkan halittarka, ka kuma mallakar da kome a karkashin sawayensa. Domin Allah ya mallakar da dukkan abubuwa a karkashinsa. Bai bar kome a kebe ba. Amma kuwa har a yanzu ba mu ga yana sarrafa dukkan abubuwa ba tukuna.
9Amma mun ga wani wanda dan lokaci aka sa shi ya gaza mala'iku, shine Yesu, an nada shi da daukaka da girma, saboda shan wuyarsa ta mutuwa, wanan kuwa duk ta wurin alherin Allah ne Yesu ya mutu saboda kowa. 10Saboda haka, ya dace ga Allah, shi da dukkan abubuwa suka kasance domin sa, ta gare shi, domin ya kawo 'ya'ya masu yawa ga samun daukaka. Domin a kammala cetonsu ta wurin shan wuyarsa.
11Domin da shi mai tsarkakewar da kuma wadanda aka tsarkaken, duk tushensu daya ne. Saboda wanan dalili ne shi ya sa ba ya jin kunyar kiran su 'ya'uwansa. 12Da yace, "zan sanar da sunanka ga ya'uwana, a tsakiyar taronsu zan yabe ka da waka."
13Har wa yau, yace, "Zan dogara a gare shi." Da kuma "Ga ni nan, ni da 'ya'yan da Allah ya ba ni." 14Wato tun da yake 'ya'yan Allah duk suna da nama da jini, Yesu ma ya dauki kamannin haka, ta wurin mutuwa ya hallakar da mai ikon mutuwa, wato Iblis. 15Ya kuma 'yanta duk wadanda tun haihuwarsu suke zaman bauta sabo da tsoron mutuwa.
16Don hakika ba mala'iku yake taimako ba, a'a, zuriyar Ibrahim ne yake taimako. 17Saboda haka, lalle ne ya zama kamar yan'uwansa ta kowacce hanya, domin ya zama babban Firist, mai jinkai, mai aminci kuma na al'amarin Allah, ya kuma mika hadayar sulhu ta gafarta zunuban jama'a. 18Tun da yake Yesu ma da kansa ya sha wahala, sa'adda aka gwada shi, don haka, zai taimaki wadanda ake yi wa gwaji.

3

1Don haka yanuwana tsarkaka, a bokan kira a samaniya. Yi la'akari da Yesu. wato Manzo da babban firist na shaidar bangaskiyarmu. 2Shi amintacce ne na Allah, wanda ya bashi hidima, kamar yadda Musa ya kasance amintacce a gidan Allah. 3Gama Yesu ya cancanci daukaka mafi girma fiye da ta Musa. Domin wanda ya gina gida, ya fi gidan nan daukaka. 4Gama kowane gida, akwai wanda ya gina shi, amma mai ginin komai shine Allah.

5Musa hakika amintaccen bawa ne a gidan Allah, yana ba da shaidar abubuwan da za su faru a nan gaba. 6Amma Almasihu shi Da ne mai mulki a gidan Allah. Mu ne gidansa idan mun rike begenmu da dukkan zuciyarmu.
7Saboda haka, kamar yadda Ruhu Mai Tsarki ya fadi: "Yau, Idan kun ji muryarsa, 8kada ku taurare zuciyarku kamar yadda 'ya'yan isra'ila suka yi cikin tawaye a lokacin gwaji a jeji.
9A lokacin nan ne kakanninku suka yi mani tawaye, ta wurin gwada ni, bayan shekara arba'in suna ganin ayyukana. 10Saboda haka na yi bakin ciki da wannan tsarar, sai na ce,' Kullum suna yawan bijirewa a zukatansu. Basu san tafarkuna ba.' 11Don haka na yi rantsuwa a cikin fushina, ba za su shiga cikin hutuna ba."
12Ku yi hankali 'yan'uwa kada a tarar da mummunar zuciya marar bangaskiya a tsakaninku, zuciya wadda ke juyawa daga Allah mai rai. 13Maimakon haka, ku karfafa juna a kowacce rana, muddun muna cikin wannan rana kada wani cikinku ya taurare zuciyarsa saboda yaudarar zunubi.
14Gama mun zama abokan aiki da Almasihu, idan mun rike begenmu cikinsa da karfi, daga farko zuwa karshe. 15Game da wannan, an fadi "Yau idan kun saurari muryarsa, kada ku taurare zuciyarku, kamar a kwanakin tawaye nan."
16Su wanene suka ji muryar Allah suka yi tawaye? Ba wadanda Musa ya yi masu jagora daga Masar ba ne? 17Kuma da su wa Allah ya yi fushi shekara arba'in? Ba da wadanda suka yi zunubi ba ne, wadanda gawawwakinsu suka warwatsu a jeji? 18Da su wa Allah ya rantse ba za su shiga hutunsa ba? In ba wadanda suka yi masa rashin biyayya ba? 19Mun kuma gani cewa basu iya shiga hutunsa ba saboda rashin bangaskiyarsu.

4

1Saboda haka, sai muyi lura kwarai don kada wani ya kasa kai ga shiga hutun da aka alkawarta maku na Allah. 2Don mun ji albishir game da hutun Allah kamar yadda aka fada masu. Amma wancan sakon bai anfana ga wadanda suka ji ba tare da sun bada gaskiya ga sakon ba.

3Ai mu, wadanda muka gaskata-mune zamu shiga wannan hutun, kamar yadda ya ce, "Yadda na yi rantsuwa cikin fushina, baza su shiga hutu na ba." Ya fadi hakan, ko da yake ya gama aikin hallittarsa tun daga farkon duniya. 4Domin yayi fadi a wani wuri game da rana ta bakwai, "Allah ya huta a rana ta bakwai daga dukkan ayyukansa." 5Ya sake cewa, "Baza su taba shiga hutu na ba."
6Saboda haka, tun da hutun Allah na kebe domin masu su shiga, kuma tun da Isra'ilawa da yawa wadanda suka ji sakon nan mai kyau game da hutunsa ba su shiga ba saboda rashin biyayya, 7Allah ya sake shirya wata rana da ake kira, "Yau." Ya sa wannan rana sa'adda yayi magana ta wurin Dauda, wanda ya ce tun da dadewa da aka fara fada, "Yau idan kun ji muryarsa, kada ku taurare zukatanku."
8Don idan Joshua ya ba su hutu, da Allah ba zai sake magana a kan wata rana ba. 9Saboda haka, akwai hutun asabar kebabbe ga mutanen Allah. 10Don shi wanda ya shiga hutun Allah shi kansa ma ya huta daga ayyukansa, kamar yadda Allah yayi da nasa. 11Saboda haka muyi marmarin shiga wancan hutun, don kada kowa ya fadi ga irin rashin biyayyar da suka yi.
12Maganar Allah kuwa rayayyiyace, kuma mai ci, fiye da takobi mai kaifi-biyu. Takan ratsa har tsakanin rai da ruhu, kuma tana kaiwa bargo. Takan iya bincika tunanin zuciya da manufarta. 13Babu halittaccen abu da ke boye a idon Allah. Sai dai, kome a sarari yake, kuma a bayyane yake a idonsa wanda lallai ne zamu bada lissafin kanmu a gare shi.
14Da yake muna da babban firist wanda ya ratsa sammai, Yesu Dan Allah, sai mu riki bangaskiyarmu da karfi. 15Domin babban firist namu ba marar tausayi ga kasawarmu bane, amma wanda aka jarraba ne ta ko wanne hali irin yadda aka yi mana, sai dai ba'a same shi da zunubi ba. 16Sai mu zo wurin kursiyin alheri gabagadi, domin a yi mana jinkai mu kuwa sami alherin da zai taimake mu a lokacin bukata.

5

1Kowanne babban firist, da yake an zabe shi ne daga cikin mutane, a kansa shi ya wakilci mutane ga al'amarin Allah, don ya mika sadakoki da kuma hadayu domin kawar da zunubai. 2Yana kuma iya tafiyar da jahilai da sangartattu a cikin salihanci, tun da shi ke rarrauna ne shi ta ko'ina. 3Saboda haka, wajibi ne ya mika hadayu, ba saboda kawar da zunuban jama'a kadai ba, har ma da na kansa.

4Ba wanda zai kai kansa wannan matsayi mai girma, sai dai Allah ya yi kiransa ga haka, kamar yadda aka kirayi Haruna. 5Haka kuma, Almasihu, ba shi ya daukaka kansa ya zama Babban firist ba, sai dai wannan ne ya sa shi, wanda ya ce da shi, "Kai Dana ne; Yau na zama Uba a gare ka."
6Kamar dai yadda a wani wuri kuma ya ce, "Kai firist ne na har abada, bisa ga kwatancin Malkisadak."
7Almasihu, a lokacin zamansa a duniya, ya yi addu'o'i da roke-roke, tare da kuka mai tsanani, har da hawaye, ga wannan da yake da ikon cetonsa daga mutuwa, aka kuwa saurare shi saboda tsannin mika kansa. 8Ko da yake shi Da ne, ya koyi biyayya ta wurin wuyar da ya sha.
9Har ya kai ga kammala, sai ya zama tushe madawwami, ceto ga dukkan wadanda suke masa biyayya. 10Gama Allah yana kiransa Babban firist, bisa ga kwatancin Malkisadak. 11Muna da abu da yawa da za mu fada a game da Yesu, amma zai yi wuyar bayani, da yake basirarku ta dushe.
12Ko da yake yanzu kam, ya kamata ku zama masu koyarwa, duk da haka, ashe, ba ku wuce wani ya sake koya muku jigajigan farko na Maganar Allah ba? har ya zamana sai an ba ku madara ba abinci mai tauri ba? 13To, duk wanda yake madara ce abincinsa, bai kware da maganar adalci ba, kamar jariri yake. 14Amma abinci mai tauri, ai, na manya ne, wato wadanda hankalinsu ya horu yau da kullum, don su rarrabe nagarta da mugunta.

6

1Saboda haka, sai mu ci gaba a kan ka'idodin farko na al'amarin Almasihu, har ya zuwa kammala, ba wai mu sake koyar da jigajigan nan na tuba da ibada marar tasiri ba, da na gaskatawa da Allah, 2da kuma na koyarwa a kan wanke-wanke, da dora hannu, da tashin matattu, da dawwamammen hukuci. 3Za mu kuwa ci gaba in Allah ya yarda.

4Domin wadanda aka haskaka zukatansu sarai, har suka dandana baiwar nan Basamaniya, suka kuma sami rabo na Ruhu Mai Tsarki, 5har su ka dandana dadin Maganar Allah, da ikon zamani mai zuwa, 6sa'an nan kuma suka ridda--ba mai yiwuwa ba ne a sake jawo su ga tuba, tun da yake sake gicciye Dan Allah suke yi su da kansu, suka kuma wulakanta shi a sarari.
7Kasa ma da take shanye ruwan da ake yi a kai a kai, take kuma fid da tsire-tsire masu amfani ga wadanda ake nomanta dominsu, Allah yakan sa mata albarka. 8Amma idan tsire-tsirenta kaya ne da kashin yawo, ba ta da amfani ke nan, tana kuma gab da la'antarwa, karshenta dai konewa ne.
9Ko da yake mun fadi haka, a game da ku kam, ya kaunatattu mun tabbata kuna abubuwa mafiya kyau na zancen ceto. 10Gama Allah ba marar adalci ba ne, har da zai ki kula da aikinku, da kuma kaunar sunansa da kuke yi, wajen yi wa tsarkaka hidima, har yanzu ma kuna yi.
11Muna dai bukata kwarai kowannanku ya nuna irin wannan himma ga yin cikkaken bege, tabbatacce, har ya zuwa karshe. 12Don kada ku yi ragwanci, sai dai ku yi koyi da wadanda suka karbi cikar alkawaran nan, ta wurin bangaskiyarsu da hakurinsu.
13Sa'adda Allah ya yi wa Ibrahim alkawari, da yake ba wani wanda ya fi shi girma da zai rantse da shi, sai ya rantse da kansa, 14Ya ce, "Hakika zan yi maka albarka, in kuma ribambamya zuriyarka." 15Ta haka, Ibrahim bayan da ya jure da hakuri, ya karbi cikar alkawarin.
16Hakika mutane sukan rantse da abin da ya fi su. Rantsuwa kuma ita ce abar da take tabbatarwa da kowacce magana. 17Don haka, sa'adda Allah yake son kara tabbatar wa magadan alkawarin nan dahir, cewa nufinsa ba mai sakewa ba ne sam, sai ya hada da rantsuwa, 18Domin albarkacin abubuwa guda biyun nan marasa sakewa, masu nuna, cewa ba shi yiwuwa Allah ya yi karya, mu da muka gudu muka sami mafaka, mu karfafa kwarai mu riski abin da muka kafa bege a kai.
19Muna da bege, kamar yadda yake ga rai, kafaffe, tabbatacce, shi ne kuma yake shiga har can ciki bayan labulen. 20Inda saboda mu ne Yasu ya riga mu shiga, da yake ya zama Babban Firist na har abada, kwatancin Malkisadak.

7

1Wannan ne Malkisadak, sarkin Salem, firist na Allah Madaukaki, wanda ya gamu da Ibrahim na dawowa daga yaki da wasu sarakuna ya kuma albarkace shi. 2Ibrahim ya ba shi ushirin dukkan ganimar da ya samu. Sunansa," Malkisadak," ma'anar itace, "Sarkin adalci," haka ma, "sarkin salem," ma'anar iitace," Sarkin salama," 3Bashi da uwa bashi da uba, ba shi da lissafin asalin zuriya, ba shi da farkon rayuwa ba shi da karshen rai. Shi firist ne na har abada, kamar Dan Allah.

4Yanzu fa dubi irin girman wannan mutum. Kakan kakanninmu Ibrahim ya bada ushira ta abubuwan da ya samo na ganimar yaki gare shi. 5Kuma hakika, zuriyar Lawi da suka karbi aikin nan na firistanci suna da umarni daga shari'ar Allah cewa su karbi zakka a gun jama'a, wato, daga yan'uwan su Isra'ilawa, koda shike suma zuriyar Ibrahim ne. 6Amma Malkisadak, shi da ba zuriyar Lawi ba ne, ya karbi zakka daga Ibrahim, ya kuma albarkace shi, shi wanda ya ke da alkawarai.
7Ba jayayya, karami shi ke karban albarka daga babba wanda ya girme shi. 8A wannan tsarin mutanen da ke karban zakka wata rana sai ka ga sun mutu, amma a wani kauli mutumin da ya karbi zakka a wurin Ibrahim, ance, wanzaje ne har yau. 9Kuma bisa ka'ida Lawi, wanda ke karban zakka, shi ma ya bada zakka ga Ibrahim, 10Saboda kuwa Lawi na cikin tsatson Ibrahim lokacin da Malkisadak ya gamu da Ibrahim.
11Yanzu in da mai yiwuwa ne a sami kammala cikin aikin firistanci na Lawiyawa (domin ta wurin ta ne aka bada shari'a), to ina amfanin wani firist ya zo bisa ga ka'ida irin ta Malkisadak, ba'a kuma ambaci ka'idar Haruna ba? 12Don kuwa lokacin da aka canza firistanci, shari'a kuma dole ne a sauya ta.
13Domin mutumin da aka fadi wadannan abubuwa a kansa na wata kabila ne, wadda ba wani mutumin da ya taba yin aiki a kan bagadi. 14Wannan a bayyane yake Ubangijinmu ya zo ne daga zuriyar Yahuza, kabilar da Musa bai taba anbatonsu game da zancen firistanci ba.
15Abinda muke fadi a bayyane yake cewa, idan wani firist ya taso da kamanin Malkisadak. 16Wannan sabon firist, ba firist ne da ya taso bisa ga ka'idar zuriya ta yan'adam ba, amma ya zama firist ne ta rayuwa mai iko marar shudewa. 17Domin a rubuce yake cikin littafi ga me da shi; "Kai firist ne na har'abada bisa ga tsari irin na Malkisadak."
18Domin doka ta fari an ajiye ta a gefe guda saboda rarrauna ce kuma marar amfani. 19Don kuwa shari'a ba ta iya kamalta kome. Amma fa a kwai bege mai kyau a nan gaba wanda ta gare shi ne zamu sami iso a gun Allah.
20Kuma wannan kyakkyawan bege baya faruwa ba tare da rantsuwa ba, don kuwa su wadancan firistocin ba su dauki wata rantsuwa ba. 21Amma Allah yayi rantsuwa game da Yesu cewa, "Ubangiji ya rantse ba kuwa zai fasa tunaninsa ba; 'Kai firist ne har'abada.'"
22Ta wurin haka Yesu ya bada tabbatacce da kuma ingataccen alkwari. 23Hakika, mutuwa ta hana firistoci su yi aiki har'abada. Wannan shi ya sa akwai firistoci da yawa daya bayan daya. 24Amma da shi ke Yesu na rayuwa ne har'abada, aikinsa na firist ba a musanya shi sam sam.
25Domin haka kuma yana da cikakken ikon ceton wadanda ke gusowa ga Allah ta wurinsa, domin kullum a raye ya ke yana kuma roko dominsu 26. Domin irin wannan babban firist shi ne ya dace da mu. Ba shi da zunubi, marar abin zargi, tsarkakakke, kebabbe daga masu zunubi, ya na sama da sammai dukka.
27Ba shi da bukata, kamar manyan firistoci, da ke mika hadayu kullum, da farko don zunubin kansu, sa'annan don zunubin jama'a dukka. Amma Yesu yayi wannan sau daya tak ba kari don kowa da kowa, yayin da ya mika kansa. 28Domin shari'a na nada mutane da ke da gazawa a matsayin firistoci, amma maganar rantsuwa, wadda ta zo a bayan shari'a, ta nada Dan, wanda ya ke cikakke har'abada.

8

1Yanzu abin da muke kokarin cewa shine: Muna da babban firist wanda ke zaune a hannun dama na kursiyi mai martaba dake sammai. 2Shi kuwa bawa ne a wannan wuri mai tsarki, haikali na gaskiya wanda Allah ya shirya ba wani bil'adama ba.

3Kowanne babban firist kuwa yana mika bayebaye da hadayu. Don haka ya kamata a sami abin hadaya. 4Da a ce Almasihu yana duniya ba zai zama firist ba ko kadan. 5Domin a kwai masu mika hadaya bisa ga shari'a. Suna hidimar misalin abubuwan da suke inuwar sama. Kamar yadda Allah ya yi wa Musa gargadi yayin da ya ke shirin gina Alfarwa: "Duba" Allah ya ce, "kayi komai bisa ga salon da aka koya maka a bisa dutse."
6Amma yanzu hidimar da Almasihu ya karba ta dara tasu dukka, domin kuwa shine matsakancin muhimmin alkawari, wanda aka kammala a kan muhimman alkawura. 7Domin kuwa idan alkawarin fari ba shi da laifi babu anfanin neman alkawari na biyu.
8Da Allah ya sami laifi akan mutane, sai ya ce "Zan sake sabon alkawari da gidan Isra'ila da kuma gidan Yahuza. 9kuma ba zai zama kamar yadda nayi da kakanninku ba, kamar yadda na rike su a hannu har Na fidda su daga kasar Masar. Basu kuma ci gaba da Alkawarina ba, ni kuwa na yi watsi da su," inji Ubangiji.
10Gama wanna shine alkawarin da zan yi da gidan Isra'ila bayan wadannan kwanaki, Inji Ubangiji. Zan sa shari'a ta a bakinsu in kuma rubuta ta a zuciyarsu, Zan kuma zama Allah a garesu, su kuma su zama jama'ata.
11Ba za su kuma koyar da makwabta ko yan'uwansu cewa, "ku san Ubangiji" gama dukkanin su za su san ni, daga karami har zuwa babba. 12Zan kuma nuna tausayi ga ayyukan su na rashin adalci, ba kuma zan kara tunawa da zunubansu ba.
13A kan fadin "sabo" ya mayar da alkawarin fari tsoho. Wannan kuma da aka ambata tsoho na shirin bacewa.

9

1To ko da alkawarin farko ma ya na da wurin sujada da kuma ka'idojin sujada a nan duniya. 2Domin a cikin alfarwar akwai daki da aka shirya, daki na waje wanda ake kira wuri mai tsarki. A wannan wuri akwai kebabbun fitilu, akwai teburi da kuma gurasa.

3Kuma bayan labule na biyun akwai wani daki, wanda ake kira wuri mafi tsarki. 4Yana da bagadin zinariya domin turare. Yana kuma da akwatin alkawarin, wanda aka lailaye shi gaba daya da zinariya. A cikinsa a kwai kaskon zinariya dake dauke da manna, da sandar Haruna wadda tayi toho, da kuma allunan duwatsu na alkawarin. 5A sama da akwatin alkawarin akwai siffofin kerubobi masu daukaka da suke wa marfin jinkai inuwa, wadanda yanzu ba zamu iya yin bayani akansu ba daki daki.
6Bayan an shirya wadannan abubuwa, firistocin alfarwar sukan shiga daki na wajen alfarwar akai akai suna aikin hidimominsu. 7Amma babban firist din ne kadai yake shiga daki na biyun, sau daya tak a shekara, kuma tilas sai tare da jinin hadaya domin kansa, da kuma domin laifuffukan mutane da a kayi ba dagangan ba.
8Ruhu Mai Tsarki yana nuna cewar ba'a riga an bayyana hanyar zuwa wuri mafi Tsarki ba muddin alfarwar nan ta farko na a tsaye. 9Wannan ya zama bayani ne game da lokacin yanzu. Da kyaututtuka da hadayu dukka da ake mikawa basu iya sun kammala lamirin mai yin sujadar ba. 10Abinci ne da abin sha kawai wadanda aka hada da bukukuwan wanke wanke dabam dabam. Wadannan duka tsare tsare ne da aka shirya a dinga yi a zahiri har sai an shirya sabuwar ka'ida.
11Almasihu yazo a matsayin babban firist na abubuwa masu kyau da suka zo, ta wurin alfarwa babba, kammalalla kuma mafi tsarki wadda ba hannuwan mutane suka gina ba, wadda ba ta wannan duniyar aka halicce ta ba. Amma almasihu ya zo a matsayin babban firist na abubuwa masu kyau da ke zuwa. 12Ba ta jinin awaki da 'yan, maruka bane, amma Almasihu da jininsa ya shiga wuri mafi tsarki sau daya tak domin kowa dukka ya karbo mana fansa ta har abada.
13To idan jinin awaki da na bajimai da yayyafa tokar karsana bisa wadanda suka bata tsarkinsu yana tsarkake su ya wanke jikkunansu. 14To balle kuma jinin Almasihu, wanda ta wurin Ruhu madawwami ya mika kansa hadaya marar aibi ga Allah, wanda yake wanke lamirinmu daga matattun ayyuka domin muyi bautar Allah mai rai? 15Domin wannan dalili, Almasihu shine magamin sabon alkawari. Wannan kuwa ya kasance ne domin anyi mutuwar da ta 'yantar da wadanda ke karkashin tsohon alkawari daga sakamakon zunubansu, saboda wadanda Allah ya kira su karbi alkawarin gadonsu madawwami.
16Gama duk inda wani ya rubuta wasiyya ya bari, dole ne a tabbatar da mutuwar wanda yayi wasiyyar nan. 17Gama sai inda akayi mutuwa ake amfani da wasiyya, amma ba ta da amfani idan wanda ya rubuta ta yana nan da rai.
18Ko alkawari na farko bai tabbata ba sai tare da jini. 19Gama bayan Musa ya bada dukkan dokoki da ke cikin shari'ar ga dukkan mutanen, sai ya dauki jinin 'yan marukan da awakin, tare da ruwa, da jan yadi, da reshen itacen doddoya mai soso, ya yayyafa bisa mutanen da kuma littafin dokokin. 20Daga nan yace, "Wannan ne jinin alkawarin da Allah ya bayar da dokoki gareku."
21Ta haka kuma, ya yayyafa jinin bisa alfarwar da dukkan kayayyakin da ke cikinta wanda ake hidimar firistanci da su. 22Kuma bisa ga shari'a, kusan komai da jini ake tsarkake shi. Idan babu zubar da jini to babu gafarar zunubi.
23Saboda haka ya zama tilas wadannan kayayyaki na kwaikwayon abubuwan dake cikin sama a tsarkake su da hadayar dabbobi. Duk da haka abubuwa na sama dole a tsarkake su da hadaya mafi kyau. 24Domin Almasihu bai shiga cikin wuri mafi tsarki da aka yi da hannuwa ba, wanda kwaikwayo ne kawai na abin da ke na gaske. Maimakon hakan, ya shiga cikin samaniya da kanta, sa'an nan yaje gaban Allah domin mu.
25Bai je wurin don ya mika kansa sau da yawa, kamar yadda firist din alfarwa yake yi ba, wanda yake shiga wuri mafi tsarki kowacce shekara da jinin wata dabba. 26Idan haka ne, to dole ke nan ya sha wahala akai akai tun farkon duniya. Amma yanzu sau daya ne tak aka bayyana shi a karshen zamanai domin ya kauda zunubi ta wurin mika hadayar kansa.
27Kamar yadda aka kaddara wa kowa ya mutu sau daya tak, kuma bayan haka sai shari'a. 28Haka kuma Almasihu, wanda aka mika shi sau daya tak domin ya dauke zunuban mutane da yawa, zai kuma bayyana karo na biyu, ba domin yin aikin kawar da zunubi ba, amma domin ceton wadanda suke jiran zuwansa da hakuri.

10

1Domin shari'a hoto ce na kyawawan abubuwan da ke zuwa, ba ainihin siffar wadannan abubuwa ba. Wadanda ke gusowa kusa da Allah ba za su taba ingantuwa ta wurin hadayu da firistoci ke mikawa shekara da shekaru ba. 2In ba haka ba, ba sai a dena mika hadayun ba? Bisa ga wannan al'amari, inda sun tsarkaka sau daya tak da masu sujada ba su san menene zunubi ba. 3Amma wadannan hadayun sun zama matuni ne na zunubi shekara biye da shekara. 4Domin ba shi yiwuwa jinin bijimai da awakai su kawar da zunubai.

5Yayin da Almasihu ya zo duniya, ya ce, "Ba hadayu da sadakoki kake marmari ba. Maimakon haka, ka shirya mini jiki domin hadaya. 6Baka murna domin sadakoki da hadayu na konawa domin zunubi. 7Sai na ce, 'Duba, gani na zo in yi nufinka, kamar yadda aka rubuta akaina.'"
8Da fari Yace "ba hadayu, ko sadakoki, ko kuma hadaya ta konawa domin zunubi kake bukata ba. Ba ka kuwa jin dadinsu." Wadannan sune hadayun da ake bayarwa bisa ga shari'a. 9Sa'annan sai ya ce "gani na zo domin in aikata nufinka." Ya kawar da hidimar farko domin ya kafa hidima ta biyu. 10A hidima ta biyu, an kebe mu ga Allah ta wurin nufinsa ta wurin hadayar jikin Yesu Almasihu bugu daya ba kari.
11Haka, kowanne firist ya ke tsayawa kulliyomi domin ya yi hidima ga Allah. A kullum yana mika hadayu, iri daya, koda shike ba za su taba kawar da zunubai ba. 12A ta wata hanya kuma, Almasihu ya mika hadaya sau daya tak domin zunubai har abada, ya zauna a hannun dama na Allah. 13Yana jiran har a maida makiyansa matashin sawayensa. 14Domin ta wurin hadaya guda dayan nan ya kammala har abada ga wadanda suka sadaukar da kansu ga Allah.
15Kuma Ruhu mai Tsarki ya shaida mana. Abu na farko yace, 16"Wannan shi ne alkawarin da zan yi da su a bayan kwanakin nan,' inji Ubangiji Zan sa dokokina a cikin zukatansu, kuma zan rubuta su a lamirinsu.
17Ba zan sake tunawa da zunubansu da kurakuransu ba." 18Yanzu fa duk in da aka sami gafara domin wadannan abubuwa, babu wata hadaya domin zunubi.
19Saboda haka, yan'uwa, ba mu da shakkar shigowa wurin nan mafi tsarki ta wurin jinin Yesu. 20Wannan ita ce sabuwar rayayyar hanya da ya bude mana ta wurin labulen, wato ta wurin jikinsa. 21Saboda muna da babban firist a gidan Allah. 22Bari mu matso kusa da sahihiyar zuciya, da kuma cikakken gabagadi cikin bangaskiya, da zuciyarmu wadda aka tsarkake daga mummunan tunani, da kuma jikunanmu wankakku da ruwa mai tsabta.
23Bari mu rike da karfi shaidar bangaskiyar begenmu, ba tare da raurawa ba, domin Allahn, da ya yi alkawari, mai aminci ne. 24Bari mu kuma yi lura yadda za mu iza juna ga kauna da ayyuka masu dacewa. 25Kada mu fasa zumunci da juna, kamar yadda wadansu sukan yi. A maimakon haka, bari mu karfafa juna a kulluyomin, kamar yada kuke ganin kusantowar ranan nan.
26Saboda idan mun ci gaba da zunubin ganganci bayan mun rigaya mun sami wannan sanin gaskiyar, hadayar irin wannan zunubi bata samuwa. 27Maimakon haka, sai fargabar babban tsoron hukunci, da kuma wuta mai zafi, da zata cinye makiyan Allah.
28Dukkan wanda ya ki bin dokar Musa zai mutu ba tausayi ta wurin shaidu biyu ko uku. 29Wanne irin hukunci kuke tsammani ya dace ga wadanda suka raina Dan Allah, duk wadanda suka maida jinin alkawarin nan kamar ba tsarkakakke ba, wanda ta wurin jinin nan ne aka kebe shi ga Allah- wadanda suka wulakantar da Ruhun alheri?
30Domin mun san wanda yace, "Ramako nawa ne; Zan yi sakayya." Sa'annan kuma, "Ubangiji zai hukumta jama'arsa." 31Abin tsoro ne a fada cikin hannuwan Allah mai rai!
32Amma ku tuna da kwanakin baya, bayan da ku ka sami haske, yadda kuka jure babban fama cikin wahala. 33Aka kunyatar da ku a gaban jama'a, ta wurin ba'a da cin mutunci, kuna kuma dandana irin azabar da wadansu suka shiga ciki. 34Domin kuna da tausayi ga wadanda suke kurkuku, da farin ciki, kun amince da kwace na dukiyarku da aka yi, kun mallaki madauwamiyar mallaka mafi kyau. Dominn kun ji tausayina sa'adda na ke a kurkuku.
35Don haka kada ku yarda gabagadinku, wanda ke da babban sakamako. 36Domin kuna bukatar hakuri don ku sami abin da Allah ya alkawarta, bayan kun aikata nufinsa. 37"Domin a dan karamin lokaci, mai zuwan nan zai zo ba zai yi jinkiri ba.
38Adalina kuwa zai rayu ta wurin bangaskiya. In kuwa ya ja da baya, ba zan yi farin ciki dashi ba." 39Amma mu bama cikin wadanda suka ja da baya zuwa hallaka. Maimakon haka, muna cikin wadanda suke da bangaskiya domin kula da rayukanmu.

11

1Bangaskiya ita ce tabbatawar al'muran da muke begensu. Ita ce tabbatawar al'amuran da idanu basu gani. 2Domin ta wurin ta ne kakanninmu suka sami yardar Allah. 3Ta wurin ta ne aka hallicci duniya da umarnin Allah, har ma abubuwan da ake gani ba'a yi su daga abubuwan da suka kasance ba.

4Ta dalilin bangaskiya ne Habila ya mikawa Allah hadaya da ta fi dacewa fiye da ta Kayinu. Don haka ne kuma aka yaba masa akan cewa shi adali ne. Ya sami yardar Allah sabili da sadakarsa da ya bayar. Don haka kuma, harwayau Habila yana magana, ko da shike ya rigaya ya mutu.
5Ta dalilin bangaskiya aka dauki Anuhu zuwa sama domin kar ya ga mutuwa. "Ba a same shi ba kuwa, domin Allah ya dauke shi." Kamin a dauke shi an shaida da cewa ya faranta wa Allah zuciya. 6Zai yi wuya matuka a faranta wa Allah zuciya in ba tare da bangaskiya ba. Domin ya kamata dukkan wanda zai zo ga Allah, tilas ne ya bada gaskiya da kasancewar sa, kuma shi mai sakamako ne ga dukkan masu nemansa.
7Ta dalilin bangaskiya Nuhu, ya karbi sako daga Allah akan al'amuran da ba'a gani ba, ta wurin girmamawa da rawar jiki. ya gina jirgin ruwa domin ya ceci iyalan sa. Dalilin haka kwa, Allah ya hallakar da duniya, Nuhu kwa ya gaji adalci wadda ke bisa ga bangaskiya.
8Ta dalilin bangaskiya ne Ibrahim, sa'an da aka kira shi, ya yi biyayya sai ya tafi wurin da zai karba a matsayin gado. Ya kwa fita bai ma san inda za shi ba. 9Ta dalilin bangaskiya kuma ya zauna bare a kasar alkawari. Ya yi zama cikin Alfarwa tare da Ishaku da Yakubu, magadan alkawari guda tare da shi. 10Domin yana hangar birnin da ke da tushi, Birnin da mai zaiyanar sa da ginin sa shine Allah.
11Ta dalilin bangaskiya, Ibrahim ya sami haihuwa ko da shike shi da matarsa Saratu sun yi nisa a cikin shekaru, kuma Saratu bakarariya ce, ta kuma wuce lokacin haihuwa. Tun da shike sun amince da wanda ya yi musu alkawari mai aminci ne. 12Sabo da haka, ta wurin mutumin nan daya, wanda ya ke kamar matacce ne, aka haifi zuriya mai dimbin yawa, su ka yawaita kamar taurari a sama kamar yashi a bakin teku, wanda ba shi kidayuwa.
13Dukkan su kuwa suka mutu a cikin bangaskiya ba tare da sun karbi alkawarin ba. Maimakon haka, sun hango, kuma sun marabcesu daga nesa, sai suka amince su baki ne kuma matafiya ne a duniya. 14Gama wadanda suka yi furci haka sun nuna a fili cewa suna bidar kasa ta kansu.
15Da kamar suna tunanin kasar da suka fita daga ciki, da sun sa mi damar komawa. 16Amma kamar yadda yake, sun bukaci kasa mafi dacewa, wato, wadda take a sama. Saboda haka ne Allah bai ji kunyar a kira shi Allahnsu ba, da shike ya shirya birni dominsu.
17Ta dalilin bangaskiya ne Ibrahim, sa'adda aka yi masa gwaji, akan ya mika Ishaku dansa hadaya. 18Shi ne kuwa makadaicin dansa, wanda aka yi alkawari da cewa, "Ta wurinsa ne za a kira zuriyarka." 19Ibrahim ya yi tunani da cewa Allah na da ikon tada Ishaku ko daga cikin matattu ma, haka kuwa yake a misalce, daga matattun ne ya sake karbarsa.
20Ta dalilin bangaskiya ne kuma Ishaku ya albarkaci Yakubu da Isuwa game da abubuwan da ke zuwa a gaba. 21Dalilin bangaskiya ne Yakubu, sa'adda yake bakin mutuwa, ya albarkaci 'ya'yan Yusufu dukkansu biyu. Yakubu ya yi ibada, yana tokare a kan sandarsa. 22Ta dalilin bangaskiya Yusufu, sa'adda karshensa ya kusa, ya yi magana game da fitar 'ya'yan Isra'ila daga Masar har ya umarce su game da kasussuwansa.
23Ta dalilin bangaskiya Musa, sa'adda aka haife shi, iyayensa suka 'boye shi kimanin watanni uku domin kyakkyawan yaro ne shi, kuma basu ji tsoron dokar sarki ba. 24Ta dalilin bangaskiya ne kuma Musa, sa'adda ya girma, yaki a kira shi 'dan diyar Fir'auna. 25A maimakon haka, ya amince ya sha azaba tare da jama'ar Allah, a kan shagali da annashuwar zunubi na karamin lokaci. 26Ya fahimci cewa wulakanci domin bin Almasihu babbar wadata ce fiye da dukiyar Masar. Gama ya kafa idanunsa a kan sakamakon da ke gaba.
27Ta dalilin bangaskiya Musa ya bar Masar. Bai ji tsoron fushin sarki ba, ya jure kamar yana ganin wannan da ba a iya ganinsa 28Ta dalilin bangaskiya ya yi idin ketarewa da kuma yayyafa jini, domin kada mai hallaka 'ya'yan fari ya taba 'ya'yan fari na Isra'ila.`
29Ta dalilin bangaskiya suka haye baharmaliya kamar bushashiyar kasa. Sa'adda Masarawa su ka yi kokarin hayewa, bahar din ta hadiye su. 30Ta dalilin bangaskiya ganuwar Yeriko ta fadi, bayan sun kewaya ta har kwana bakwai. 31Ta dalilin bangaskiya Rahab karuwan nan bata hallaka tare da marasa biyayya ba, don ta saukar da masu leken asirin kasa a gidanta, ta kuma sallame su lafiya.
32Me kuma za mu ce? Gama lokaci zai kasa mini idan zan yi magana game da Gidiyon, Barak, Samson, Yefta, Dauda, Sama'ila, da annabawa. 33Ta dalilin bangaskiya suka ci nasara kan kasashe, suka yi aikin adalci, sa'annan suka karbi alkawura. Suka rufe bakin zakuna, 34suka kashe karfin wuta, suka tsira daga bakin takobi, suka sami warkaswa daga cutattuka, suka zama jarumawan yaki, sa'annan suka ci nasara akan rundunar sojojin al'ummai.
35Mata kuwa suka karbi matattunsu da aka tayar daga mutuwa. Aka azabtar da wadansu, ba su nemi yancin kansu ba, domin suna begen tashi daga mattatu. 36Wadansu kuwa suka sha ba'a da duka da bulala, har ma da sarka da kurkuku. 37A ka jejjefe su. Aka tsaga su kashi biyu da zarto. A ka karkashe su da takobi. Su na yawo sanye da buzun tumakai da na awaki, suka yi hijira, suka takura, suka wulakantu. 38Duniya ma ba ta dauke su a matsayin komai ba. Suka yi ta yawo a jazza, da duwatsu, da kogwanni, da kuma ramummuka.
39Ko da yake mutanen nan amintattun Allah ne domin bangaskiyarsu, basu karbi cikar alkawarin ba tukunna. 40Domin Allah ya shirya mana wani abu mafi kyau ba kuwa za su kammala ba sai tare da mu.

12

1Da shike muna kewaye da wannan irin kasaitaccen taro na shaidu, sai mu watsar da dukkan abubuwan dake nawaita mana da kuma zunubin da zai saurin makale ma na. Bari a cikin hakuri mu yi tseren da ke gabanmu. 2Bari mu kafa idonmu ga Yesu, wanda shine mafarin bangaskiyarmu da cikarta. Wanda sabili da murnar da a ka sa a gabansa ya jimre giciye, ya kuma yi watsi da kunyarsa, wanda kuma ya zauna a hannun dama na kursiyin Allah. 3Ku dube shi wanda ya jimre irin wannan adawa daga masu zunubi, domin kada ku gaji ko ku karai.

4Ba ku yi tsayayya ko jayayya da zunubi har ta kai ga zub da jininku ba tukunna. Kun kuma manta da gargadin da a ka yi maku a matsayin 'ya'ya: 5"Dana, kada ka dauki horon Ubangiji da wasa, kadda kuma ka yi suwu lokacin da ka sami horonsa," 6Domin kuwa Ubangiji yana horon dukkan wadanda yake kauna, yana kuma hukunta duk wadanda ya karba.
7Ku daure wahala a matsayin horo. Allah yana yi da ku kamar 'ya'yansa, domin kuwa wanne da ne wanda ubansa bazai yi masa horo ba? 8Amma idan baku da horo kamar yadda sauran mutane ke da shi, kun zama shegu kenan ba 'ya'ya ba.
9Hakannan kuma kamar yadda muke da iyaye a duniya wadanda suke yi mana horo, kuma muna basu daraja. To ba sai mu yiwa Ubanmu na Ruhaniya biyayya don mu rayu ba? 10Ta wani fanni kuwa iyayenmu suna yi mana horo na kwanaki kadan bisa ga yadda suka ga ya dace, Amma Allah kuwa yana yi mana horo domin anfanin kanmu, domin kuma mu sami rabo daga cikin tsarkinsa. 11Ba horon da ke da dadi a lokacin yinsa, amma sai zafi. Sai dai kuma bayan haka yakan haifar da 'ya'ya na ruhaniya da kuma adalci ga dukkan wadanda aka yi rainonsu a ciki.
12Don haka sai ku karfafa hannayenku da ke reto, da kuma guwawunku da ke kaduwa. 13Ku bi hanyoyi mikakku domin abin da ya gurgunce kada ya karye amma ya warke.
14Ku bidi salama da kowa, da kuma rayuwar tsarki wanda in ba tare da shi, babu wanda zai ga Allah. 15Ku mai da hankali domin kada waninku ya rasa, alherin Allah, kuma kada wani tushe mai daci ya tsiro a cikinku har ya haifar da fitina, domin kada da dama daga cikinku su gurbata ta wurinsa. 16Ku yi hankali kuma kada a sami mazinanci ko marar ibada a cikinku, kamar Isuwa, wanda sabili da abinci ya sayar da 'yancinsa na dan fari. 17Kun kuwa san cewa sa'adda ya yi marmarin ya gaji albarka a gaba, an kishi, domin kuwa bai sami damar tuba ba, ko da shike ya nema har da hawaye.
18Domin kuwa baku zo ga dusen da ake tabawa da hannu ba, dutse ne mai ci da wuta, da tukuki da bakin hayaki da hadari. 19Ba Ku zo ga karar kaho mai ban razana da murya mai firgitarwa ba, da masu sauraro suka yi roko kar su sake jinta. 20Don basu iya jimre abin da aka yi doka a kan saba: "koma dabba ce ta taba dutsen, sai a jejjefe ta." 21Abin tsoro ne kuwa kwarai, har Musa yace, "A tsoroce nake kwarai har na firgita."
22Maimakon haka kun zone ga Dutsen Sihiyona da kuma birni na Allah mai Rai, kuma na Urushalima ta Samniya, da kuma dubun dubban mala'iku cikin murna da farin ciki. 23Kun zo taro na dukkan 'ya'yan fari, rubuttatu a sama, kuma kun zo ga Allah wanda shine alkalin dukka, hakannan kuma zuwa ga ruhu na adalai wanda a ka rigaya aka tsarkake. 24Kun zo ga Yesu, wanda shine matsakancin sabon alkawari, kuma ga jinin yayyafawa da ke magana fiye da na jinin Habila.
25Ku yi lura kada ku ki wannan da ke yi mu ku magana. Gama in har basu kubuta yayin da su ka yi jayayya da wanda ya yi mu su gargadi a duniya ba, balle ma mu ba za mu kubuta ba in mun ki wanda ke mana gargadi daga sama. 26A wani karo, muryar sa ta girgiza duniya. Amma yanzu yayi alkawari da cewa, "Har'ila yau ba duniyar kadai zan girgiza ba, amma har da sammai."
27Wannan kalma, "Harl'ila yau," ta bayyana cirewar abubuwan nan da za su girgizu, wato abubuwan da a ka halitta, domin abubuwan da ba zasu girgizu ba su kasance. 28Don haka, samun mulkin da ba za ya girgizu ba, sai mu zama masu godiya, kuma a cikin wannan yanayi mu yi wa Allah sujada cikin daraja da tsaninin gimamawa. 29Domin kuwa Allahnmu wuta ne mai konewa.

13

1Bari kaunar 'yan'uwa ta cigaba. 2Kada ku manta da karrama baki, domin ta wurin yin haka, wasu suka marabci mala'iku ba tare da saninsu ba.

3Ku tuna da wadanda ke cikin kurkuku, kamar dai kuna tare da su cikin wannan hali. Kuma ku tuna da masu shan azaba kamar tare kuke cikin wannan hali 4Bari kowa ya girmama aure, bari kuma a tsarkake gadon aure, gama Allah zai shar'anta fasikai da mazinata.
5Bari halinku ya kubuta daga kaunar kudi. Ku dangana da abubuwan da kuke dasu, domin Allah da kansa yace, "Bazan barku ba, ba kuma zan yashe ku ba." 6Bari mu zama da dangana domin mu sami gabagadin cewa, "Ubangiji ne mai taimakona, ba zan ji tsoro ba. To me mutum zai iya yi mani?"
7Ku fa lura da wadanda ke shugabanninku, wadanda suka horar da ku cikin maganar Allah, kuma ku lura da sakamakon rayuwarsu, ku yi koyi da bangaskiyarsu. 8Yesu Almasihu daya ne a jiya, da yau, da har abada.
9Kada ku kauce zuwa ga bakin koyarwa daban daban, domin yana da kyau zuciya ta ginu ta wurin alheri, amma ba da dokoki game da abinci ba, wadanda basu taimaki wadanda suka kiyayesu ba. 10Muna da bagadin da wadanda ke hidima a cikin alfarwa basu da ikon su ci daga bisansa. 11Babban firist na shiga wuri mai tsarki da jinin dabbobin da aka yanka, hadayar zunubai, amma namansu a kan kai bayan sansani a kone shi.
12Domin haka Yesu shima ya sha wahala a bayan kofar birnin, domin ya tsarkake mutane ta wurin jininsa. 13Domin haka bari mu tafi gare shi a bayan sansani dauke da kunyarsa. 14Domin bamu da wani birni dawwamamme a nan. Maimako haka muna bidar birni dake zuwa.
15Ta wurin sa kuma, bari kullum mu mika hadayu na yabo ga Allah, yabon kuwa shine kalmomin bakinmu da ke daukaka sunansa. 16Kada kuma mu manta da yin nagarta da kuma taimakon juna, domin Allah na farin ciki sosai da irin wadannan hadayun. 17Ku yi biyayya da sadaukarwa ga shugabanninku, domin suna aikin tsaro a kanku saboda rayukanku, kamar wadanda zasu bada lissafi. Kuyi biyayya gare su saboda su yi aikin lura daku cikin farin ciki, ba da bakin ciki ba, don in su yi da bakin ciki ba zai amfane ku ba.
18Kuyi mana addu'a, domin mun tabbata muna da lamiri mai tsabta, kuma muna burin muyi rayuwar dake daidai cikin dukkan al'amura. 19Kuma ina karfafa ku dukka kuyi haka, domin in sami dawowa gareku da sauri.
20To bari Allahn salama, wanda ya tada babban makiyayin tumakin nan daga matattu, Ubangijinmu Yesu, ta wurin jinin madawwamin alkawari, 21ya kammala ku da dukan abu mai kyau domin ku aikata nufinsa. Bari yayi aiki a cikinmu wanda zai gamshe shi sosai. Ta wurin Yesu Almasihu, bari daukaka ta tabbata gare shi har abada. Amin.
22'Yan'uwa, yanzu dai ina karfafa ku, da ku jurewa takaitacciyar maganar karfafawar da na rubuto maku. 23Ina so ku sani an saki dan'uwan mu Timoti, tare da shi zan zo in gan ku idan ya iso da sauri.
24Ku gaida shugabanninku dukka da kuma dukkan masu bada gaskiya. 'Yan'uwa daga can Italiya suna gaishe ku. 25Bari alheri ya kasance tare daku dukka.

Yakubu

1

1Yakubu, bawan Allah, da kuma Ubangiji Yesu Almasihu, zuwa ga kabilun nan goma sha biyu da suke warwatse: ina gaishe ku. 2Ku dauke su duka da farin ciki, 'yan'uwana, duk sa'adda kuke fuskantar jarabobi. 3Ku sani cewa gwajin banskiyar ku ta kan haifi jimiri.

4Bari jimiri ya cika aikin sa, domin ku kai ga cikakken girma kuma ku kammalu, domin kada ku rasa komai. 5Amma idan waninku yana bukatar hikima, sai ya roki Allah, wanda yake bayarwa a yalwace, ba tare da gori ba ga duk wanda ya roke shi, zai kuwa ba shi.
6Amma fa sai ya roka da banskiya ba tare da shakka ba, don mai shakka kamar rakumin ruwan teku yake, wanda iska take korarwa tana tunkudawa. 7Tilas ne wannan mutum kada ya yi tunanin zai karbi wani abu a wurin Ubangiji. 8Irin wannan mutumin mai zuciya biyu ne, mara tsai da hankali a dukan hanyoyin sa.
9Bari dan'uwa matalauci ya yi takama da matsayin sa babba, 10amma mutum mai arziki kuma a kaskantaccen matsayin sa, gama zai shude kamar furen ciyawa na jeji. 11Domin rana na bullowa da zafi mai konarwa kuma ya busar da ciyawa. Furen ya fadi, kuma kyaun sa ya lalace. Haka ma, mai arziki zai bushe yana cikin tsakiyar tafiyarsa.
12Albarka ta tabbata ga mutum mai jurewa da gwaji. Domin in ya jure gwajin, zai sami rawanin rai, wanda aka yi alkawarin sa ga wadanda ke kaunar Allah. 13Kada wani ya ce idan aka gwada shi, "Wannan gwaji daga wurin Allah ne," domin ba a gwada Allah da mugunta, shi kan sa kuwa ba ya gwada kowa.
14Amma kowanne mutum yakan sami gwaji daga muguwar sha'awar sa, wadda take janye shi kuma ta rinjaye shi. 15Bayan da muguwar sha'awar ta dauki ciki, sai ta haifi zunubi. Kuma bayan da zunubi ya yi girma, yakan haifi mutuwa. 16Kada fa ku yaudaru, 'yan'uwana kaunatattu.
17Kowace kyakkyawar baiwa, da kowace cikakkiyar baiwa daga sama take. Ta sauko ne daga wurin Uban haskoki. Wanda babu sauyawa ko wata alamar sakewa kamar yadda inuwa ke yi. 18Allah ya zabi ya haife mu ta wurin maganar gaskiya, domin mu zama kamar nunar fari na dukan halittar sa.
19Kun san wannan, 'yan'uwana kaunatattu: bari kowanne mutum ya yi hanzarin kasa kunne, da jinkirin yin magana, da kuma jinkirin yin fushi. 20Domin fushin mutum ba ya aikata adalcin Allah. 21Saboda haka, sai ku yar da kowanne irin aikin kazanta da yalwar mugunta. A cikin tawali'u ku karbi dassashiyar maganar, wadda ke iya ceton rayukan ku.
22Ku zama masu aikata maganar, kada ku zama masu jin ta kawai, kuna yaudarar kanku. 23Domin duk wanda ya ke mai jin maganar ne kawai, ba mai aikatawa ba, kamar mutum yake mai duba fuskarsa a madubi. 24Yakan dubi kansa sai ya tafi, nan da nan kuwa sai ya manta da kamannin sa. 25Amma duk mai duba shari'ar da bin ka'idar nan ta 'yanci, ya kuma nace biyayya da ita, ba zai zama kamar wanda zai ji ya manta ba, wannan mutum zai zama da albarka a cikin abin da yake yi.
26Idan wani yana zaton shi mai addini ne, amma bai kame bakinsa ba, yana yaudarar zuciyarsa ne, addinin mutumin nan na banza ne. 27Addini sahihi kuma marar aibi a gaban Allahnmu da Ubanmu, shine a kula da gwauraye da marayu a cikin kuntatar su, kuma mutum ya kebe kansa ya zama marar aibi daga duniya.

2

1Ya ku 'yan'uwana, muddin kuna rike da bangaskiyar ku ga Ubangijinmu Yesu Almasihu, Ubangijin daukaka, kada ku nuna bambanci ga wadansu mutane. 2Idan wani mutum ya halarci taron ku da zobban zinariya da tufafi masu kyau, wani matalauci kuma ya shigo da tufafi marasa tsabta. 3Sa'adda kuka kula da mai tufafi masu kyau nan, har kuka ce masa, "Idan ka yarda ka zauna a nan wuri mai kyau," mataulacin nan kuwa kuka ce masa, "Kai ka tsaya daga can," ko kuwa, "Zauna a nan kasa a gaba na," 4Ashe ba kuna zartar da hukunci a tsakanin ku ba ke nan? Ba kun zama alkalai na mungayen tunani kenan ba?

5Ku saurara, ya 'yan'uwana kaunatattu, ashe, Allah bai zabi matalautan duniyar nan su zama mawadata cikin bangaskiya ba, su kuma zama magada a cikin mulkin nan da ya yi wa masu kaunar sa alkawari ba? 6Amma, kun wulakanta matalauta! Ashe, ba masu arzikin ne suke matsa maku ba? Ba su ne kuwa suke jan ku zuwa gaban shari'a ba? 7Ba kuma sune ke sabon sunan nan mai girma da ake kiran ku da shi ba?
8Duk da haka, idan kuka cika muhimmiyar shari'ar da nassi ya ce, "Ka kaunaci makwabcin ka kamar kanka," to, madalla. 9Amma in kun nuna bambanci, kun yi zunubi kenan, shari'a ta same ku da laifin keta umarni.
10Duk wanda yake kiyaye dukan shari'a, amma ya yi tuntube a hanya daya kadai, ya sabi shari'a gaba daya ke nan. 11Domin wanda ya ce, "Kada ka yi zina," shi ne kuma ya ce, "Kada ka yi kisan kai." Idan ba ka yi zina ba amma ka yi kisan kai, ai, ka zama mai taka shari'a kenan.
12Saboda haka, ku yi magana ku kuma yi aiki kamar wadanda za a hukunta ta wurin 'yantacciyar shari'a. 13Gama hukunci yana zuwa ba tare da jinkai ba ga wadanda ba su nuna jinkai. Jinkai ya yi nasara a kan hukunci.
14Ina amfanin haka, 'yan'uwana, idan wani ya ce yana da bangaskiya, kuma ba shi da ayyuka? Wannan bangaskiyar ba za ta cece shi ba, ko za ta iya? 15Misali, idan wani dan'uwa ko 'yar'uwa ba su da tufa mai kyau ko suna rashin abincin yini. 16Misali, idan waninku kuma ya ce masu, "Ku tafi cikin salama, ku kasance da dumi ku koshi." Idan baku ba su abubuwan da jiki ke bukata ba, ina amfanin wannnan? 17Haka ma, bangaskiya ita kadai, ba tare da aikin da ya nuna ta ba, matacciya ce.
18To, wani zai ce, "Ai, kai kana da bangaskiya, ni kuwa ina da ayyuka." Nuna mani bangaskiyar ka ba tare da ayyuka ba, ni kuma in nuna maka bangaskiya ta ta wurin ayyuka na. 19Ka gaskanta cewa Allah daya ne; ka yi daidai. Amma ko aljannu ma sun gaskata, kuma suna rawar jiki. 20Kana so ka sani, kai marar azanci, cewa bangaskiya ba tare da ayyuka ba banza ce?
21Ba an baratar da Ibrahim mahaifinmu ta wurin ayyuka ba, sa'adda ya mika Ishaku dansa a bisa bagadi? 22Ka gani, ashe, bangaskiyar sa ta yi aiki da ayyukan sa, kuma da cewa ta wurin ayyuka bangaskiyar sa ta ginu sosai. 23Nassi kuma ya cika da ya ce, "Ibrahim ya gaskata Allah, aka kuma lisafta masa ita a matsayin adalci." Aka kuma kira shi abokin Allah. 24Kun ga, ta wurin ayyuka ne mutum yake samu baratarwa ba ta wurin bangaskiya kadai ba.
25Ta wannan hanyar kuma, ba Rahab karuwar nan ta samu baratarwa ta wurin ayyuka, da ta marabci masu leken asirin nan ta fitar da su ta wata hanya dabam ba? 26Kamar yadda jiki idan ba tare da ruhu ba matacce ne, haka kuma, bangaskiya ba tare da ayyuka ba matacciya ce.

3

1Ba mutane dayawa za su zama masu koyarwa ba, 'yan'uwana. Mun san cewa za mu karbi hukunci mafi tsanani. 2Domin mukan yi tuntube ta hanyoyi dayawa. Duk wanda bai yi tuntube ta hanyar kalmomi ba, shi mutum ne ginanne sosai, wanda ke iya kame dukan jikinsa.

3Idan muka sa linzami a bakunan dawakai, domin su yi mana biyayya, za mu iya sarrafa jikunan su gaba daya. 4Ku lura kuma da jiragen ruwa, ko da yake suna da girma sosai kuma iska mai karfi tana kora su, da karamin karfe ne matukin yake juya su inda ya so.
5Haka kuma harshe dan karamin gaba ne a jiki, sai fahariyan manyan abubuwa. Ku lura yadda dan karamin wuta yake cinna wa babban jeji wuta. 6Harshe ma wuta ne, a cikin dukan gabobin mu, duniyar zunubai da aka sa cikin fannonin jikunan mu. Yana gurbata dukan jiki, ya kuma sa al'amurar rayuwa su kama da wuta. Shi kuwa gidan wuta ne yake zuga shi.
7Domin kowace irin dabbar jeji, tsunsu, da masu jan ciki, da hallittar teku, ana sarrafa su kuma dan Adam har ya sarrafa su ma. 8Amma game da harshe, babu wani a cikin 'yan Adam da ya iya sarrafa shi. Mugunta ne mara hanuwa, cike da dafi mai kisa.
9Da wannan harshe muke yabon Ubangiji da kuma Uba, da shi kuma muke la'antar mutane wandanda aka hallitta cikin kamanin Allah. 10Bakin da ake sa albarka, da shi kuma ake la'antarwa. 'Yan'uwana, ai, wannan bai kamata ba.
11Mabulbulan ruwa ba zai iya bubbugowa da ruwan dadi da na zartsi tare ba, ko zai iya? 12"Yan'uwana, itacen baure ba zai iya yin zaitun ba, zai iya? Ko kuwa gonar inabi ya yi baure? Haka kuma, ruwan zartsi ba zai iya bayar da ruwan dadi ba.
13Ina mai hikima da fahimta a cikin ku? Bari wannan mutumin, ta kyakkyawan zaman sa ya nuna aikin da halin tawali'u da hikima ke sawa. 14Amma in kuna da matsanancin kishi da kazamin buri a cikin zuciyar ku, kada ku yi fahariya da karya game da gaskiya.
15Wannan hikima ba irin wadda take saukowa daga sama ba ce, a maimakon haka, ta duniya ce, mara ruhaniya, ta aljanu. 16Domin duk inda kishi da kazamin buri suke, a nan ake samun hargitsi da kowanne irin aikin mugunta. 17Amma hikiman nan ta sama, da farko dai tsattsarka ce, mai lumana ce, kamila ce, mai saukin kai, mai tsananin jinkai, mai yawan alheri, mara gajiya, sahihiya kuma. 18Kuma 'ya'yan adalci wanda ake shukawa a cikin salama a tsakanin wadanda ke kulla zumunci.

4

1Me ke kawo gaba da rashin jituwa a tsakanin ku? Ba yana tasowa ne daga muguwar sha'awa da ke yaki a cikin ku ba? 2Kuna sha'awa, kuma ba ku da shi. Kuna kisa da kyashi, kuma ba za ku iya samu ba. Kuna danbe da fada. Har wa yau baku samu ba domin baku tambaya ba. 3Kun roka kuma ba a baku ba saboda kuna roko ta hanya mara kyau, kuna so ku yi amfani da shi domin miyagun sha'awoyin ku.

4Ku mazinata! Baku sani ba, abokantaka da duniya, tawaye ne ga Allah? Don haka duk wanda ya shiga abokantaka da duniya ya zama magabcin Allah.5Ko kuna zaton nassi ya fadi haka a banza ne, "Ruhun nan da ke a cikinmu yana da kishi matuka?"
6Amma Allah ya bayar da karin alheri, shi ya sa nassi ya ce, "Allah yana gaba da mai girman kai, Amma yana ba da alheri ga mai tawaliu." 7Saboda haka ku mika kan ku ga Allah. Ku yi tsayayya da shaidan, zai kuma guje maku.
8Ku matso kusa da Allah, shi kuma za ya matsa kusa da ku. Wanke hannayen ku, ku masu zunubi, ku tsabtace zukatan ku, ku masu zuciya biyu. 9Ku yi bakin ciki, makoki, da kuka! Ku mayar da dariyar ku ta koma bakin ciki, farin cikinku kuma zuwa ga bakin ciki. 10Ku kaskantar da kanku a gaban Ubangiji, shi kuma za ya daukaka ku.
11Kada ku rika zargin juna, 'yan'uwa. Wanda ya ke zargin dan'uwa ko shari'anta dan'uwansa, yana zargin shari'a kuma yana hukunta shari'a. Idan ka hukunta shari'a, ya nuna ba ka biyayya da shari'ar, amma mai hukunci. 12Mai ba da shari'a da yin hukunci daya ne. Shine mai iya ceto kuma ya hallakar. Kai wanene, da ke hukunta makwafcin ka?
13Saurara, ku da kuke cewa, "Yau ko gobe za mu tafi wancan birnin mu yi shekara guda a wurin, muna kasuwanci, mu kuma yi riba." 14Wa ya san abin da zai faru gobe, kuma yaya rayuwan ka zai kasance? Kai kamar hazo ne mai bayyana bayan dan lokaci kadan ya bace.
15Maimakon haka, sai ka ce, "Idan Ubangiji ya nufa, za mu rayu kuma mu yi wannan ko wancan." 16Amma yanzu kana fahariya da shirye shiryen ka na takama. Irin wannan fahariya, mugunta ce. 17Saboda haka ga wanda ya san abin da ya kamata ya aikata amma bai yi ba, ya zama zunubi a gare shi.

5

1Ku zo yanzu, ku da kuke masu arziki, ku yi ta kuka da kururuwa domin bakin ciki iri-iri da ke zuwa gare ku. 2Arzikin ku ya rube, tufafinku kuma duk cin asu ne. 3Zinariya da azurfarku sun yi tsatsa. Tsatsar su kuwa zai zama shaida a kanku. Zai cinye naman ku kamar wuta. Kun yi ajiyar dukiyarku domin ranakun karshe.

4Duba, hakin ma'aikata yana kuka - hakin da kuka hana wa wadanda suka girbe maku gonaki. Kuma kukan masu girbin ya tafi ya kai ga kunnuwan Ubangiji mai Runduna. 5Kun yi zama cikin annashuwa a duniya kuma kun tsunduma kanku. Kun sa zukatan ku sun yi kiba domin ranar yanka. 6Kun hukunta kuma kun kashe adalin mutum. Bai kuwa yi tsayayya da ku ba.
7Saboda haka ku yi hakuri, 'yan'uwa, har sai zuwan Ubangiji. Duba, yadda manomi ya kan jira kaka mai amfani daga gona. Da hakuri yake jiran ta har sai ta karbi ruwa na fari da na karshe. 8Ku, ma, ku yi hakuri. Ku karfafa zukatan ku, domin zuwan Ubangiji ya yi kusa.
9Kada ku yi gunaguni, 'Yan'uwana, game da juna, don kada a hukunta ku. Duba, mai shari'a na tsaye a bakin kofa. 10Dauki misali, 'yan'uwa, daga shan wuya da hakurin annabawa, wadanda suka yi magana a cikin sunan Ubangiji. 11Duba, mukan kira wadanda suka jimre masu albarka. Kun dai ji irin jimiri da Ayuba ya yi, kun kuma san nufin Ubangiji, yadda yake mai yawan tausayi da jinkai.
12Fiye da komai duka, 'yan'uwana, kada ku yi rantsuwa, ko da sama, ko da kasa, ko da kowace irin rantsuwa ma. A maimakon haka bari "I" ya zama "I", in kuwa kun ce "A'a", ya zama "A'a", don kada ku fada a cikin hukunci.
13Akwai wanda ke fama a tsakanin ku? Sai ya yi addu'a, akwai wanda yake murna? Sai ya raira wakar yabo. 14Akwai mara lafiya a tsakanin ku? Sai ya kira dattawan ikilisiya, sai su yi masa addu'a. Suna shafa masa mai a cikin sunan Ubangiji. 15Addu'ar bangaskiya zai warkar da mara lafiyan, Ubangiji zai tashe shi. Idan ma ya yi zunubi, Allah zai gafarta masa.
16Soboda haka, ku furta zunuban ku ga juna, kuna yi wa juna addu'a, don a warkar da ku. Addu'ar mai adalci tana da karfin aiki kwarai da gaske. 17Iliya dan Adam ne kamar mu. Amma da ya nace da addu'a kada a yi ruwa, ba kuma yi ruwa a kasar ba har shekara uku da wata shida. 18Sai Iliya ya sake yin addu'a. Sammai suka ba da ruwa, kasa kuma ta ba da amfanin ta.
19Ya ku 'yan'uwana, idan wanin ku ya baude wa gaskiya, wani kuma ya dawo da shi, 20wannan mutum ya sani cewa, duk wanda ya dawo da mai zunubi a hanya daga baudewar sa, zai cece shi daga mutuwa, kuma zai rufe dunbin zunubai.

Bitrus ta fari

1

1Bitrus, manzon Yesu Almasihu, zuwa ga zababbu wadanda suke baki, a warwatse cikin Buntus, Galatiya, kappadokiya, Asiya, da Bitiniya. 2Bisa ga rigasanin Allah Uba, Ta wurin tsarkakewar Ruhu, zuwa biyayya da yayyafar jinin Yesu Almasihu. Alheri da salama su yawaita a gareku.

3Albarka ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Almasihu. Ta wurin jinkansa mai girma, ya maya haihuwarmu zuwa bege mai rai ta wurin tashin Yesu Almasihu daga matattu. 4Zuwa gado marar lalacewa, marar baci, ba kuma zai kode ba. Wanda aka kebe a sama dominku. 5Ku da ikon Allah ya kiyaye ta wurin bangaskiya domin ceto wanda za'a bayyana a karshen zamanai.
6Cikin wannan kuna murna da yawa, duk da ya ke ya zama wajibi gare ku yanzu ku yi bakin ciki, a cikin jarabobi iri iri. 7Wannan kuwa da nufin a iske aunawar bangaskiyarku ne, bangaskiyar da tafi zinariya daraja, wadda takan lalace ko da an gwada ta da wuta. Wannan ya faru domin bangaskiyan nan taku ta jawo maku yabo da girma da daukaka a bayyanuwar Yesu Almasihu.
8Wanda kuke kauna, ko da yake baku ganshi ba. Ko da yake baku ganinsa yanzu, duk da haka kun bada gaskiya gare shi murnar da ku ke yi kwarai da farin ciki wanda tafi gaban a fadi cike da daukaka. 9Kuna karbar sakamakon bangaskiyarku, ceton rayukanku. 10Annabawan da su ka yi annabcin ceton da ya zama naku su ka yi bidassa suka bincike kuma da himma.
11Sun nemi su san ko wanene da kuma kowanne lokaci ne Ruhun Almasihu da ke cikinsu yake bayyana ma su. Wannan ya faru ne sa'adda yake gaya ma su tun da wuri game da shan wahalar Almasihu da kuma daukakar da zata biyo baya. 12An kuwa bayyana wa annabawan cewa ba kansu suke hidimtawa ba, amma ku suke yi wa hidima. Wannan shine abin da suke yi game da abin da aka rigaya aka gaya maku, ta wurin wadanda da Ruhu mai Tsarki ya bishe su. Wanda aka aiko daga sama. Wadannan sune abubuwan da mala'iku ma suka yi marmarin a bayyana masu.
13Domin wannan fa ku natsu. Ku yi dammara a hankalinku. Ku kafa begenku sarai akan alherin da za'a kawo maku a lokacin bayyanuwar Yesu Almasihu. 14Kamar 'ya'ya masu biyyaya, kada ku biyewa sha'awoyinku na da a zamanin jahilcinku.
15Amma yadda shi wanda ya kira ku mai tsarki ne, kuma ku zama da tsarki cikin dukkan al'amuranku. 16Domin a rubuce yake, "Ku zama da tsarki, gama ni mai tsarki ne." 17Idan ku na kira bisa gare shi "Uba" shi wanda yake hukuntawa ba da tara ba, amma gwar-gwadon aikin kowane mutum, sai kuyi zaman bakuncinku da tsoro da bangirma.
18Kun san cewa ba da azurfa ko zinariya mai lalacewa aka fanshe ku ba, daga halinn wauta da kuka gada daga wurin iyayenku. 19Maimakon haka an fanshe ku da jinin Almasihu mai daraja, marar aibu kamar na dan rago.
20An zabi Almasihu tun kafin kafawar duniya, amma a karshen zamanu ya bayyanu a gare ku. 21Ku da kuka bada gaskiya ga Allah ta wurinsa, wanda ya tashe shi daga matattu ya kuma bashi daukaka domin bangaskiyarku da begenku su kasance cikin Allah.
22Da shike kun tsarkake rayukanku cikin biyayyar ku ga gaskiya zuwa ga sahihiyar kauna ta 'yan'uwa, sai ku kaunaci junanku da zuciya mai gaskiya. 23da shike an sake hai'huwarku ba daga iri mai lalacewa ba amma daga iri marar rubewa, ta wurin maganar Allah wadda take rayuwa ta kuma dawwama.
24Gama "dukkan jiki kamar ciyawa yake, dukkan darajarsa kuwa kamar furen ciyawa take. Ciyawa takan yi yaushi, furenta ya kan yankwane ya fadi, 25amma maganar Ubangiji tabbatacciya ce har abada. "Wannan ita ce maganar bishara wadda akayi maku wa'azinta."

2

1Saboda haka sai ku tube dukkan keta, rikici, da riya, kishi, da dukkan mugun zance. 2Kammar jarirai, sababbin haihuwa, ku yi marmarin madara mai ruhaniya wadda take sahihiya, domin ta wurinta kuyi girma zuwa ceto, 3idan kun dandana Ubangiji mai-alheri ne.

4Kuzo gareshi rayayyen dutse wanda mutane suka ki, amma zababbe ne mai-daraja wurin Allah. 5Ku kuma kamar rayayyun duwatsu ana gina ku gida mai ruhaniya, domin ku zama tsarka-kan fristoci, domin ku mika hadayu masu ruhaniya abin karba ga Allah ta wurin Yesu Almasihu.
6Gama nassi ya ce, "Ga shi na sanya dutse na kan kusurwa, zababe, mai daraja a cikin Sihiyona. Duk wanda ya bada gaskiya gareshi ba zaya kunyata ba."
7Daraja a gareku take ku da kun bada gaskiya. Amma, ga wadanda suka ki bada gaskiya, "Dutsen da magina suka ki shine aka mai she shi kan kusurwa". 8kuma, "Dutsen sa tuntube da fa na sa tuntube. "Sun yi tuntube, da shike sun ki biyayya da maganar, an kuwa kaddara su ga wannan.
9Amma ku zababben jinsi ne, kungiyar fristoci ba-sarauci, al'umma mai-tsarki, jama'ar mallakar Allah, domin ku sanar da mafifitan al'amuran wanda ya kiraye ku daga chikin duhu zuwa cikin haskensa mai'ban al'ajibi. 10Ku da ba jama'a ba ne a da, amma yanzu jama'ar Allah ne. Da baku sami jinkai ba, amma yanzu kun sami jinkai.
11Kaunatattu, ina rokon ku misalin baki da masu-tafiya kuma, ku guje wa sha'awoyin jiki wadanda ke yaki da rai. 12Ku kasance da kyakkyawan hali a cikin al'ummai, domin, sa'adda suke kushen ku kamar masu aikata mugunta, sai su lura da nagargarun ayyukanku su kuma daukaka Allah a ranar zuwansa.
13Kuyi biyayya ga kowacce hukuma ta mutane sabili da Ubangiji, ko ga sarki domin shi ne shugaba. 14Ko kuwa ga masu mulki aikakkunsa ne domin su hori masu aikata mugunta da yabawa masu aikata nagarta. 15Gama wannan nufin Allah ne, ta wurin aikin kirki ku, kwabi jahilcin mutane marassa hikima. 16Kamar 'yan'tattu kada ku mori 'yan'cinku kamar mayafin mugunta, amma ku zama kamar bayin Allah. 17Ku girmama dukkan mutane. Ku kaunaci 'yan'uwa, kuji tsoron Allah. Ku girmama sarki.
18Ku barori, kuyi biyayya ga iyayen gidanku da dukkan bangirma, ba ga nagargaru da masu saukin kai ba, amma har ga miskilai. 19Gama abin yaba wa ne idan sabili da lamiri zuwa ga Allah in wani ya jimre da shan zalunci. 20Gama wacce riba ke nan idan kun yi zunubi ana horonku kuna jimrewa da hukuncin? amma idan kunyi aikin kirki kuka sha wuya a kansa kuka yi hakuri, wannan abin karba ne wurin Allah.
21Gama akan haka aka kiraye ku, gama Almasihu ma yasha azaba saboda ku, ya bar maku gurbi kubi sawunsa. 22Bai taba yin zunubi ba, ba'a taba jin yaudara a bakinsa ba. 23Da'a ka zage shi bai mai da zagi ba. Da ya sha azaba, bai yi kashedi ba, amma ya mika kansa ga wanda yake yin shari'ar adalci.
24Shi da kansa ya dauki zunubanmu a cikin jiki nasa ya kai su bisa itace, domin kada a iske mu cikin zunubi, amma muyi rayuwa ga adalci. Ta wurin raunukansa ne kuka warke. 25Dukkanku da kun bata kuna yawo kamar batattun tumaki, amma yanzu kun dawo wurin makiyayi da mai tsaron rayukanku.

3

1Haka ku kuma da kuke matan aure, kuyi biyayya da na ku mazajen, domin in har wadansunsu basa biyayya da maganar Allah, halin matansu ya shawo kansu ba tare da magana ba, 2Domin sun ga tsattsakan halinku da ladabinku.

3Haka ma adonku kar ya zama na kwalliyar waje kitson kai, kayan zinariya ko tufafi masu kawa. 4Amma bari adon ya zama na mutum na cikin zuciya, kuma adon ya zama kyan nan marar dushewa, na kamun kai da natsatsen ruhu, wanda yake da daraja a gaban Allah.
5Haka tsarkakan mata su ka yi ado kamar haka. Suka dogara ga Allah suka yi biyayya ga mazajensu. 6Ta haka Saratu ta yi biyayya ga Ibrahim ta kira shi "ubangiji". Yanzu ku 'ya'yantane in dai kun yi aiki nagari, idan kuma ba ku ji tsoron wahala ba.
7Kamar yadda na fada wa matan aure haka ma mazaje, ku zauna da mata da sanin su raunana ne abokan tarayya ne na karbar baiwar rayuwa. Ku dinga yin haka domin a rika jin addu'oinku.
8Daga karshe, dukanku ku hada hankulanku, ku zama masu juyayi, masu kauna kamar 'yan'uwa, masu taushin zuciya, masu tawali'u. 9Kada ku rama mugunta da mugunta ko zagi da zagi. A maimakon haka ku cigaba da sa albarka, gama sabili da haka ne musamman aka kiraye ku, domin ku gaji albarka.
10"Wanda duk yake so ya more a rayuwarsa ya kuma ga kwanaki masu alheri, to fa, ya kame harshen sa daga mugunta da lebensa daga maganganun yaudara. 11Ya rabu da mugunta ya aikata abin da ke nagari. Bari ya nemi zaman salama ya kuma dimanceta. 12Idanun Ubangiji suna duban adalai, kunnuwansa kuma suna sauraron roke rokensu. Amma fuskar Ubangiji tana gaba da masu aikata mugunta."
13Wanene ya isa ya cuce ku idan kun himmatu ga yin abin da ke nagari? 14Amma idan kuna shan wuya saboda adalci, ku masu albarka ne. Kada ku ji tsoron abin da su ke tsoro. Kada ku damu.
15Maimakon haka, ku kebe Ubangiji a cikin zukatanku cewa shi mai tsarki ne. Kullum ku zauna da shiri domin ku amsa wa mai tambayar ku dalilin sa begenku ga Allah. Amma fa kuyi haka tare da tawali'u da bangirma. 16Ku zama da tsatsakan lamiri domin mutanen da ke zargin rayuwarku mai kyau cikin Almasihu, su ji kunya domin suna maganar gaba da ku kamar ku mugaye ne. 17Ya fi kyau, a sha wuya akan aiki nagari, idan nufin Allah ne, da a sha wuya sabili da mugun aiki.
18Almasihu ya sha wahala sau daya tak sabili da zunubai. Shi da ya ke mai adalci ya sha wahala domin mu marasa adalci, domin ya kawo mu ga Allah. Aka kashe shi cikin jiki, amma aka rayar da shi cikin Ruhu. 19A Ruhu ne, ya je ya yi wa'azi ga ruhohin da ke a yanzu cikin kurkuku. 20Sun yi rashin biyayya ne sa'adda hakurin Allah yake jiransu a lokacin Nuhu a zamanin sassaka jirgin ruwa, sai Allah ya tsirar da mutane kalilan wato rayuka takwas daga cikin ruwa.
21Wannan kwatancin baftismar da take cetonmu yanzu ne, ba kamar ta wanke Dauda daga jiki ba, sai dai ta rokon Allah da lamiri mai kyau ta wurin tashin Yesu Almasihu daga matattu. 22Ya hau sama. Yana dama ga Allah. Mala'iku, da mulkoki da masu iko dole su yi masa biyayya.

4

1Saboda haka, tunda yake Almasihu ya sha wuya a jiki, muma mu sha damara da wannan ra'ayi. Duk wanda ya sha wuya a jiki ya daina aikata zunubi. 2Wannan mutum kuma baya kara zaman biye wa muguwar sha'awar mutumtaka, amma sai dai nufin Allah dukkan sauran kwanakinsa a duniya.

3Gama lokaci ya wuce da zamu yi abin da al'ummai suke son yi, wato fajirci, mugayen sha'awace-sha'awace, da buguwa da shashanci da shaye-shaye da bautar gumaku da abubuwan kyama. 4Suna tunanin bakon abu ku ke yi da ba kwa hada kai tare da su yanzu a yin wadannan abubuwa, sai suna zarginku. 5Za su bada lissafi ga wanda yake a shirye ya shari'anta masu rai da matattu. 6Shi yasa aka yi wa matattu wa'azin bishara, cewa ko da shike anyi masu shari'a cikin jikunan mutane, su rayu bisa ga Allah a ruhu.
7Karshen dukkan abubuwa yana gabatowa. Saboda haka, ku zama natsatsu, ku natsu cikin tunaninku domin yin addu'oi. 8Gaba da kome, ku himmatu wajen kaunar juna, domin kauna bata neman tona zunuban wadansu. 9Ku yi wa juna bakunta da abubuwa nagari ba tare da gunaguni ba.
10Yadda kowanne dayanku ya sami baiwa, kuyi amfani da su domin ku kyautata wa juna, kamar masu rikon amanar bayebaye na Allah, wanda ya ba mu hannu sake. 11Idan wani yana yin wa'azi, ya zamana fadar Allah ya ke fadi, idan wani yana hidima, ya yi da karfin da Allah ya ba shi, domin cikin dukkan abubuwa a daukaka Allah ta wurin Yesu Almasihu. Daukaka da iko nasa ne har abada abadin. Amin.
12Ya kaunatattu, kada ku zaci cewa matsananciyar wahalar da ta zo ta gwada ku bakon abu ne, ko kuma wani bakon abu ne yake faruwa a gareku. 13Amma muddin kuna tarayya da Almasihu cikin wahalarsa, ku yi murna, domin kuyi farin ciki da murna sa'adda za a bayyana daukakarsa. 14Idan ana zargin ku sabili da sunan Almasihu, ku masu albarka ne, domin Ruhun daukaka da Ruhun Allah ya tabbata a kanku.
15Amma kada kowannen ku ya sha wahala sabo da horon shi mai kisan kai ne, ko barawo, ko mamugunci, ko mai shisshigi. 16Amma in wani yana shan wahala sabili da shi na Almasihu ne, kada ya ji kunya, amma ya daukaka Allah a wannan sunan.
17Domin lokaci ya yi da shari'a za ta fara daga gidan iyalin Allah. Idan kuwa za a fara da mu, menene karshen wadanda suka ki biyayya da bisharar Allah? 18Idan mutum, "mai adalci ya tsira da kyar, to, me zai faru da marar bin Allah da mai zunubi kuma?" 19Sabo da haka bari wadanda suke shan wuya bisa ga nufin Allah, su mika rayukansu ga amintaccen Mahalicci suna kuma yin ayyuka nagari.

5

1Ina yiwa dattawan da ke cikinku gargadi, ni da nike dan'uwanku dattijo, mashaidin shan wuyar Almasihu, ni kuma mai samun rabo ne daga cikin daukakar daza a bayyana. 2Saboda haka na gargade ku dattawa, kuyi kiwon garken Allah dake tare da ku. Ku kula da su, ba a kan dole ba, amma domin kuna son yin haka, bisa ga yin Allah. Ku kula da su, ba don cin ribar banza ba amma sabo da yardar rai. 3Kada ku zama kamar masu iko akan mutanen dake hannunku, amma ku zama abin koyi ga garken. 4Sa'adda za a bayyana Sarkin Makiyaya zaku karbi rawanin da darajarsa bata dushewa.

5Hakannan, ku kuma samari kuyi biyayya ga dattawa. Dukanku kuyi damara da tawali'u, kuna bauta wa juna, domin Allah ya na tsayayya da mai girman kai, amma yana yiwa masu tawali'u alheri. 6Saboda haka ku kaskantar da kanku karkashin hannuwan Allah mai iko duka domin ya daukaka ku a madaidecin lokaci. 7Ku jibga masa duk taraddadin zuciyarku, domin yana kula da ku.
8Ku natsu, ku zauna a fadake. Magabcinku, ibilis, kamar zaki mai ruri yana zazzagawa, yana neman wanda zai cinye. 9Ku yi tsayayyiyar gaba da shi. Ku yi karfi cikin bangaskiyarku. Ku sani fa abokan tarayyarku da suke cikin duniya suna jimrewa da shan wuyan nan irin taku.
10Bayan shan wuyarku na dan lokaci kadan, Allah mai alheri mara iyaka, wanda ya kiraye ku zuwa ga madawwamiyar daukakarsa cikin Almasihu, zai kammalaku, ya kafa ku, ya kuma karfafa ku. 11Mulki ya tabbata a gare shi har abada abadin. Amin.
12Na amince da Sila amintaccen dan'uwa ne, kuma na rubuto maku a takaice ta hannunsa. Ina yi maku gargadi ina kuma shaida maku cewa abin da na rubuto alherin Allah ne na hakika. Ku kafu a cikinsa. 13Ita matar da ta ke a Babila zababbiya tare da ku, ta na gaisheku, da Markus, dana, yana gaisheku. 14Ku gai da juna da sumbar kauna. Salama ta tabbata a gare ku dukanku da ke cikin Almasihu.

Wasikar bitrus ta biyu

1

1Siman Bitrus, bawa da manzon Almasihu Yesu, zuwa ga wadanda suka karbi bangaskiya mai daraja kamar yadda muka karba, bangaskiya cikin adalcin Allahnmu da Yesu Almasihu. 2Bari alheri ya kasance tare da ku; bari salama ta karu ta wurin sanin Allah da na Yesu Ubangijinmu.

3Dukkan abubuwan ikon Allah na rayuwa da Allahntaka an bamu su ta wurin sanin Allah, wanda ya kira mu ta wurin daukakarsa da nagarta. 4Ta wurin wanan, ya bamu babban alkawari mai daraja. Yayi wanan ne saboda ku zama masu rabo cikin Allahntaka, yayin da ku ka kubuta daga lalacewa da ke cikin duniya saboda mugayen sha'awace sha, awace.
5Saboda wanan dalilin kuyi iyakacin kokarinku ku kara nagarta ta wurin bangaskiyarku, kuma ta wurin adalci, sani. 6Ta wurin sani ku kara da kamun kai, kuma ta wurin kamun kanku, ku kara da jimrewa, ta wurin jimrewarku, ku kara da bin Allah. 7Ta wurin bin Allah, ku kara da kauna irin ta 'yan'uwa, ta wurin kauna irin ta 'yan'uwa, ku kara kauna.
8Idan wadannan abubuwan suna cikinku, kuma suka yi girma a cikinku, baza a sami bakarare ko rashin 'ya'ya cikin sanin Ubangijinmu Yesu Almasihu ba. 9Amma duk wanda ya rasa wadannan abubuwan yana kallon abin da ke kusa ne kawai; ya makance. Ya manta da cewa an wake shi daga tsofaffin zunubansa.
10Saboda haka, 'yan'uwa, kuyi iyakacin kokari ku tabbatar da kiranku da zabenku. Idan kun yi wadannan abubuwan, baza ku yi tuntube ba. 11Ta haka zaku sami shiga cikin mulki na har'abada na Ubangijinmu da Maicetonmu Yesu Almasihu.
12Saboda haka a shirye nake kulayomi in tunashe ku game da wadannan abubuwan, ko da yake kun san su, kuma kun yi karfi cikin gaskiya yanzu. 13Ina tunani daidai ne in zuga ku da tuni game da wadannan abubuwan, tun ina cikin wannan jiki. 14Domin na sani jim kadan zan bar wannan jiki, kamar yadda Yesu Almasihu ya nuna mani. 15Zan yi iyakancin kokarina kulayomi domin ku rika tunawa da abubuwan, bayan kaurata.
16Domin bamu bi labaru da aka kago na nuna wayo cikinsu ba, da muka fada maku game da iko da bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Almasihu, amma mu shaidu ne na ikonsa. 17Gama ya karbi daukaka da daraja daga wurin Allah Uba lokacin da murya ta zo daga ikon mai daukaka cewa, "Wannan shine dana, kaunataccena, wanda nake jin dadinsa kwarai." 18Mun ji muryar nan da ta zo daga sama, lokacin da mu ke tare da shi a dutse mai tsarki.
19Muna da wannan kalmar annabci wanda akwai tabbaci sosai, kun yi daidai idan kun mayar da hankali a kansu. Yana nan kamar fitillar da take walkiya a wuri mai duhu kafin asubahi ya zo, kuma tauraron asubahi ya tashi cikin zukatanku. 20Ku san da wannan tun da farko, cewa babu annabci da ke bisa ga fasarar mutum. 21Domin babu annabcin da ya taba zuwa ta wurin nufin mutum. Maimakon haka, Ruhu Mai Tsarki ne ke iza su, su fadi maganar Allah.

2

1Annabawan karya sun zo ga mutane, hakannan kuma malaman karya suma sun zo. A asirce za su zo maku da karkatacciyar koyarwa mai hallakarwa, su kuma yi musun sanin Ubangiji da ya fanshe su. Su na jawowa kansu hallaka da sauri. 2Da yawa za su bi gurbinsu, kuma ta wurinsu za a sabawa sahihiyar gaskiya. 3Ta wurin hadama za su ribace ku ta wurin maganganunsu na yaudara. Hallakarsu ba za ta yi jinkiri ba; hukuncinsu na nan tafe.

4Allah bai kebe mala'ikkun da suka yi zunubi ba. Maimakon haka ya tura su a cikin bakin duhun jahannama daure da sarkoki, har ya zuwa ranar shari'a. 5Hakan nan kuma bai kebe duniya ta zamanin da ba. Maimakon haka, ya kebe Nuhu, wanda yake wa'azin adalci, tare da mutane bakwai, lokacin da ya kawo ambaliyar ruwan Tsufana a fuskar duniyar marasa bin Allah. 6Sa'annan Allah ya kone biranen Sadoma da Gomrata da wuta ya maishe su toka, wannan ya zama misalin abin da zai faru da marasa ibada.
7Amma ga adalinnan Lutu, wanda ya zaku a ransa ta wurin miyagun halayen mutanen, Ubangiji kuwa ya cece shi. 8Ga wannan mutum mai adalci, wanda yayi zama a cikinsu kowace rana ransa na baci, domin abin da yake gani yake kuma ji. 9Saboda haka Allah ya san yadda zai ceci masu adalci daga gwaji, da yadda kuma zai kama masu rashin adalci da hukunci a ranar shari'a.
10Wannan kuwa musamman gaskiya ce ga wadanda suka ci gaba da ayyuka na jiki suka kuma raina masu mulki. Suna da taurin kai da kuma yin ganin dama. Ba sa tsoron sabo ga wadanda aka daukaka. 11Ko da shike mala'iku suna da karfi da iko fiye da su, amma basu kawo karar batanci a kansu a gaban Ubangiji ba.
12Amma wadannan dabbobi marassa tunani an yi su ne musamman domin a kama a yanka. Suna sabawa abin da ba su sani ba. Zasu halaka. 13Za su sami sakamakon mugun aikinsu. Suna tunanin yin nishadi da rana abin annashuwa ne. Su kan su tababbu ne. Suna jin dadin ayyukansu na yaudara yayin da suke liyafa tare da ku. 14Suna da idanun sha'awace sha'awacen mata mazinata; ba sa koshi da aikata zunubi. Suna rinjayar wandanda ba su da tsayayyan hankali zuwa ga munanan ayyuka, kuma sun kafa zukatansu ga hadama, su 'ya'yan la'ana ne!
15Sun bar bin hanyar gaskiya. Sun bijire kuma sun bi hanyar Bal'amu dan Be'or wanda yake kaunar ribar rashin adalci. 16Amma ya karbi tsautawa domin zunubinsa. Jaki ma da baya magana ya tsauta wa haukan annabin da muryar dan adam.
17Wadannan mutane suna kamar mabulbullai da babu ruwa. suna nan kamar gizagizai da iska ke korawa. Duhu mai tsanani yana jiransu. 18Su masu babatu ne da girman kai. suna yadaurar mutane ta wurin sha'awowin jiki. Suna yaudarar mutane da suke kokarin su tsere daga wadanda suke rayuwa cikin kuskure. 19Suna masu alkawarin yanci, amma su da kan su bayi ne ga zunubi. Domin mutum bawa ne ga duk abinda ya rinjaye shi.
20Duk wanda ya kubuta daga shashanci na duniya ta wurin sanin Ubangiji da mai Ceto Yesu Almasihu, sa'annan ya koma cikin shashaci, yanayinsu na karshe ya zama da muni fiye da na farkon. 21Da ma zai fi masu kada su san hanyar adalci da su san ta amma sa'annan su juya daga ka'ida mai tsarki wanda aka damka masu. 22Wannan karin magana ya zama gaskiya a kan su: "Kare ya dawo yana lashe amansa. Aladen da akayi masa wanka ya koma cikin tabo."

3

1Yanzu, ina rubata maku, kaunatattu, wannan wasika ta biyu domin in tunashe ku, in kuma zuga tunaninku na gaskiya, 2don ku tuna da kalmomin da annabawa tsarkaka suka fada a da, kuma da umurnin Ubangijinmu da mai ceto da aka bayar ta wurin manzaninku.

3Ku san wannan da farko, cewa masu ba'a za su zo a kwanakin karshe. Za su yi ba'a kuma su ci gaba bisa ga sha'awowinsu. 4Za su ce, "Ina alkawarin dawowarsa? Tun lokacin da kakaninmu suka mutu, dukkan abubuwa sun kasance yadda suke, tun farkon halitta."
5Da gangan suka manta cewa sama da kasa sun kasance daga ruwa, kuma ta wurin ruwa, da dadewa ta wurin umarnin Allah, 6kuma cewa ta wurin wadannan abubuwa duniyar wancan zamani ta halaka, da ambaliyar ruwan tsufana. 7Amma sama da kasa na yanzu, an tanada su domin wuta ta wurin wannan umarnin. An tanada su domin ranar shari'a da halakar marassa ibada.
8Kada ku manta da wanan, kaunatattu, cewa rana daya a gun Allah kamar shekaru dubu ne, kuma shekaru dubu kamar rana daya suke. 9Ubangiji baya jinkiri game da alkawaransa kamar yadda wadansu ke ganin jinkiri. Maimakon haka, yana hakuri da ku. Ba ya so ko dayanku ya hallaka, amma kowanenku ya kai ga tuba.
10Duk da haka, ranar Ubangiji za ta zo kamar barawo. Sammai za su shude da kara mai karfi. Wuta zata kone komai da komai, kuma duniya da dukkan ayyukan da ke cikinta zasu bayyanu.
11Da shike dukkan wadanan abubuwa za a hallaka su haka, wadanne irin mutane yakamata ku zama? Ya kamata kuyi rayuwar tsarki da ta ibada. 12Ku zauna cikin bege da kuma hanzarta zuwan ranar Allah. A ranan nan, za a hallaka sammai da wuta, kuma dukkan komai da komai zai narke cikin zafi mai tsanani. 13Amma bisa ga alkawarinsa, muna jiran sabuwar sama da sabuwar duniya, inda adalci zai kasance.
14Saboda haka, kaunatattu, tun da kuna da begen wadannan abubuwa, ku yi iyakacin kokarinku a same ku marassa tabo da marasa aibu a gabansa, cikin salama. 15Kuma, ku dauki hakurin Ubangiji domin ceto ne, kamar yadda kaunataccen danuwanmu Bulus ya rubuta maku bisa ga hikima da aka ba shi. 16Bulus yayi magana akan wadanan abubuwa cikin dukkan wasikunsa, a ciki akwai abubuwa da suke da wuyar ganewa. Jahilai da mutane marassa natsuwa sukan juya ma'anarsu, kamar yadda suke yi wa sauran nassoshi, don hallakar kansu.
17Saboda haka, kaunatattu, tun da kun san wadannan abubuwa, ku kula da kanku kada a badda ku ta wurin rudun mutanen da ba su bin doka, har ku rasa amincinku. 18Amma ku yi girma a cikin alheri da sanin Ubangijinmu da mai ceto Yesu Almasihu. Bari daukaka ta tabbata a gare shi yanzu da har abada. Amin.

Wasikar yahaya ta fari

1

1Abin nan da yake tun daga farko, wanda muka ji, wanda muka gani da idanunmu, wanda muka gani hannuwanmu suka kama, a wajen maganar rai. 2Ran kuwa aka baiyyana shi, muka gani, muka bada shaida, muka gaya maku labarin rai na har abada, wanda da yake a wurin Uba, aka kuma sanar da mu.

3Wannan da muka gani muka ji muka baku labari, domin kuyi zumunci da mu, zumuncinmu kuwa tare da Uba yake da Dansa Yesu Almasihu. 4Haka nan, muna rubuta maku wadannan abubuwa domin farin cikinmu ya cika.
5Wannan shi ne sakon da muka ji daga wurinsa mu kuwa muka sanar da ku: Allah haske ne a wurinsa kuwa babu duhu ko kadan. 6Idan mun ce muna zumunci da shi kuma muna tafiya cikin duhu, muna yin karya kuma bama aikata gaskiya. 7Amma idan muna tafiya cikin haske kamar yadda yake cikin haske, muna zumunci da juna, jinin Yesu Dansa ya wankemu daga dukka zunubi.
8Idan mun ce bamu da zunubi, muna rudin kanmu kenan, ba kuma gaskiya a cikinmu. 9Amma idan mun fadi zunubanmu, shi mai aminci ne, mai adalci da zai gafarta mana zunubanmu, ya kuma wankemu daga dukkan rashin adalci. 10Idan mun ce bamu yi zunubi ba, mun mai da shi makaryaci kenan, maganarsa kuma bata cikinmu.

2

1'Ya'yana, na rubuta ma ku wadannan abubuwa domin kada kuyi zunubi. Amma idan wani yayi zunubi muna da matsakanci a wurin Uba, Yesu Almasihu, mai adalci. 2Shine fansar zunubanmu, ba ma namu kadai ba amma na duniya dukka. 3Ta haka muka san cewa mun san shi, idan mun kiyaye dokokinsa.

4Duk wanda yace, "Na san Allah" amma bai kiyaye dokokinsa ba, makaryaci ne gaskiya kuwa ba ta cikinsa. 5Amma duk wanda ya kiyaye maganarsa, hakika kaunar Allah ta kammala a cikin wannan mutum. Ta wurin haka muka sani muna cikinsa. 6Duk wanda yace yana cikin Allah dole ne shi da kansa yayi tafiya kamar yadda Yesu Almasihu yayi.
7Kaunatattu, ba sabuwar doka nike rubuta maku ba, amma tsohuwar doka ce wadda kuka ji tun farko. Tsohuwar dokar kuwa itace maganar da kuka ji tun farko. 8Amma yanzu ina rubuta maku sabuwar doka wadda gaskiya ce a cikin Almasihu da cikinku, saboda duhu yana wucewa, haske na gaskiya yana haskakawa.
9Duk wanda yace yana cikin haske amma yana kin dan'uwansa, yana cikin duhu har yanzu. 10kuma wanda yake kaunar dan'uwansa yana cikin haske babu dalilin tuntube a wurinsa. 11Amma duk wanda yake kin dan'uwansa yana cikin duhu, yana kuma tafiya cikin duhu, bai san ma inda ya nufa ba, domin duhu ya makantar da shi.
12Na rubuta maku, ya ku kaunatun 'ya'yana, saboda an gafarta zunubanku domin sunansa. 13Na rubuta maku, ubanni, saboda kun san shi wanda yake tun daga farko. Na rubuta maku matasa saboda kun yi nasara da mugun. Na rubuta maku, yara kanana, saboda kun san Uban. 14Na rubuta maku, Ubanni, saboda kun san shi wanda yake tun daga farko. Na rubuta maku, matasa, saboda kuna da karfi, kuma maganar Allah tana zaune cikinku. Kuma kun yi nasara da mugun.
15Kada kuyi kaunar duniya ko abubuwan da suke cikin duniya. Idan wani yayi kaunar duniya, kaunar Uban bata cikinsa. 16Domin dukkan abubuwan da suke a cikin duniya, kwadayi na jiki, abin da idanu suke sha'wa, da rayuwar girman kai ta wofi, ba na Uban bane amma na duniya ne. 17Duniya tana wucewa tare da sha'awarta. Amma dukkan wanda ya aikata nufin Allah zaya kasance har abada.
18Yara kanana, sa'a ta karshe ce. Kamar dai yadda kuka ji magafcin Almasihu yana zuwa, ko yanzu ma magaftan Almasihu da yawa sun rigaya sun zo, ta haka muka san sa'a ta karshe ce. 19Sun fita daga cikinmu, dama su bana cikinmu bane. Gama idan da su namu ne da sun ci gaba tare damu. Amma da yake sun fita, ya nuna su ba na cikinmu bane.
20Amma ku kun karbi shafewa daga wurin Mai Tsarki, kuma dukkanku kun san gaskiya. 21Bana rubuta maku bane domin baku san gaskiya ba, amma saboda kun santa, kuma ba wata karya da ta fito daga gaskiya.
22Wanene makaryaci shine wanda yayi musu cewa Yesu ba Almasihu bane? Wannan mutumin shi ne magafcin Almasihu, tun da yayi musun Uba yayi musun Dan. 23Ba wanda yayi musun Dan kuma yake da Uban. Dukkan wanda ya amince da Dan yana da Uban ma.
24A game daku kuma, sai ku bari abinda kuka ji daga farko ya zauna a cikinku. Idan abin da kuka ji daga farko ya zauna a cikinku, kuma zaku kasance a cikin Dan da kuma Uban. 25Alkawarin da ya bamu kenan, rai na har abada. 26Na rubuta maku wadannan abubuwa ne game da wadanda zasu baudar daku.
27Game daku, shafewar daku ka samu daga wurinsa tana nan a cikinku, baku bukatar wani ya koyar daku. Amma kamar yadda shafewar da kuka karba a wurinsa ta koya maku dukkan abu, kuma gaskiya ne ba karya bane, tana nan a cikinku kamar yadda a ka koya maku, ku kasance a cikinsa. 28Yanzu fa, 'ya'ya na kaunatattu, ku kasance a cikinsa domin sa'adda zai baiyyana mu zama da gabagadi ba tare da kunya ba a gabansa sa'adda zai zo. 29Idan kun sani shi mai adalci ne, kun sani dukkan wanda ke aikata adalci haifaffe ne daga wurinsa.

3

1Dubi irin kaunar da Allah ya bamu, har da za a kira mu 'ya'yan Allah, haka muke kuwa. Saboda wannan dalili ne duniya bata san muba, saboda bata san shi ba. 2Kaunatattu, yanzu mu 'ya'yan Allahne, kuma ba a bayyana mana yadda zamu zama ba tukuna, mun sani sa'adda Almasihu zai bayyana, zamu zama kamarsa, domin zamu ganshi kamar yadda yake. 3Dukkan wanda yake da wannan bege game da gidan gobe ya kan tsarkake kansa, kamar yadda shima yake da tsarki.

4Dukkan wanda yaci gaba da yin zunubi yana ketare shari'a kenan. Gama zunubi ketare shari'a ne. 5Kun sani Almasihu ya bayyana domin ya dauke zunubai ne. Kuma a cikinsa babu zunubi. 6Ba wanda zai kasance a cikinsa da zai cigaba da yin zunubi. Ba wanda zai ci gaba da aikata zunubi da zai ce ya sanshi, ko kuma ya ganshi.
7'Ya'yana kaunatattu, kada ku bari kowa ya baudar da ku, wanda yake aikata adalci shi adali ne, kamar yadda Almasihu yake adali. 8Wanda yake aikata zunubi na ibilis ne, gama ibilis yayi zunubi tun daga farko. Dalilin haka ne Dan Allah ya bayyana, domin ya rushe ayyukan ibilis.
9Duk wanda aka haife shi daga Allah ba ya yin zunubi, saboda irin Allah na cikinsa. Ba zaya iya ci gaba da yin zunubi ba domin an haife shi daga wurin Allah. 10Ta haka ne ake bambanta 'ya'yan Allah da 'ya'yan ibilis. Dukkan wanda baya aikata adalci ba na Allah bane; haka kuma wanda ba ya kaunar dan'uwansa.
11Domin wannan shine sakon da kuka ji tun daga farko: cewa mu kaunaci junanmu, 12ba kamar Kayinu ba wanda yake na shaidan kuma ya kashe dan'uwansa. Me yasa ya kashe shi? Saboda ayyukansa miyagu ne, na dan'uwansa kuma masu adalci ne.
13Kada kuyi mamaki 'yan'uwana, idan duniya ta ki ku. 14Mun sani mun ratsa mutuwa zuwa cikin rai, saboda muna kaunar 'yan'uwa. Dukkan wanda ba ya yin kauna, shi matacce ne. 15Dukkan wanda yake kin dan'uwansa, mai kisan kai ne. Kun kuma sani babu rai na har abada a cikin mai kisankai.
16Ta wurin haka muka san kauna, da ya ke Almasihu ya bayar da ransa saboda mu. Mu ma ya kamata mu bada ranmu saboda 'yan'uwamu. 17Amma duk wanda yake da kayan duniya, ya ga dan'uwansa cikin bukata, kuma bai ji tausayinsa ba, ta yaya kaunar Allah ke cikinsa? 18'Ya'yana kaunatattu, kada muyi kauna ta fatar baki kawai, amma muyi aikin kauna da gaskiya.
19Ta wurin haka mun sani mu masu gaskiya ne kuma mun tabbatar da zuciyarmu a gabansa. 20Gama idan zuciyarmu bata kayar damu ba, Allah ya fi zuciyarmu girma, kuma yana sane da kome. 21Kaunatattu, idan zuciyarmu bata kashe mu ba, muna da gabagadi a gaban Allah. 22Kuma duk abin da muka nema zamu samu a wurinsa, saboda muna kiyaye dokokinsa, muna yin abubuwan da suka gamshe shi.
23Kuma ummurninsa kenan: mu bada gaskiya ga sunan Dansa Yesu Almasihu, mu yi kaunar juna kuma kamar yanda ya bamu wannan doka. 24Duk wanda yake kiyaye umarnin Allah, yana cikinsa, Allah kuma yana cikin mutumin. Ta haka muka gane cewa yana cikinmu, Ta wurin Ruhu, wanda ya bamu.

4

1Kaunatattu, kada ku amince da kowanne ruhu. Amma ku gwada ruhohi ku gani ko na Allah ne, gama annabawan karya masu yawa sun fito zuwa cikin duniya. 2Ta haka zaku gane Ruhun Allah, dukkan ruhun da ya amince Yesu Almasihu ya zo cikin jiki na Allah ne, 3kuma dukkan ruhun da bai amince da Yesu ba, ba na Allah bane. Wannan ruhun magafcin Almasihu ne, wanda kuka ji cewa yana zuwa, ya kuwa rigaya yazo cikin duniya.

4'Ya'yana kaunatattu, daga Allah ke, kuma kun rigaya kun yi nasara da su da yake wanda ke cikinku ya fi wanda ke cikin duniya girma. 5Su na duniya ne, saboda haka abin da suke fadi na duniya ne, duniya kuma tana sauraronsu. 6Mu na Allah ne, duk wanda ya san Allah yana saurarenmu. Wanda ba na Allah bane, ba ya sauraronmu. Ta haka muka gane ruhun gaskiya da ruhun karya.
7Kaunatattu, mu yi kaunar juna, gama kauna ta Allah ce, wanda yake kauna an haife shi daga wurin Allah, kuma ya san Allah. 8Mutumin da baya kauna ba na Allah ba ne, kuma bai san Allah ba, gama Allah kauna ne.
9A cikn haka aka bayyana kaunar Allah a garemu, Allah ya aiko tilon Dansa cikin duniya domin mu rayu ta wurinsa. 10A cikin wannan akwai kauna, ba mune muka kaunaci Allah ba, amma shi ya kaunace mu ya aiko da Dansa ya zama mai gafarta zunubanmu.
11Kaunatattu, da yake Allah ya kaunace mu haka, ya kamata mu kaunaci junanmu. 12Ba wanda ya taba ganin Allah. Idan muna kaunar juna, Allah yana zaune cikinmu, kuma kaunarsa tana zaune a cikinmu. 13Ta haka mun sani muna zaune a cikinsa shi kuma a cikinmu, saboda ya bamu Ruhunsa. 14Mun gani mun shaida, cewa Allah ya aiko Dan, domin ya zama mai ceton duniya.
15Duk wanda ya amince Yesu Dan Allah ne, Allah na zaune cikinsa, shi kuma a cikin Allah. 16Mun sani kuma mun gaskata da kaunar da Allah yake da ita dominmu, Allah kauna ne wanda yake zama cikin kauna yana zaune cikin Allah, Allah kuma a cikinsa.
17Dalilin wannan kauna ta kammala a cikinmu, domin mu kasance da gabagadi a ranar shari'a, domin kamar yanda ya ke haka muma muke a cikin duniyan nan. 18Babu tsoro a cikin kauna. Amma cikkakiyar kauna takan kawar da tsoro, domin kuwa tsoro na tafi tare da hukunci. Amma wanda yake da tsoro ba shi da cikkakiyar kauna.
19Muna kauna domin Allah ne ya fara kaunarmu. 20Idan wani ya ce,"Ina kaunar Allah", amma yana kin dan'uwansa, makaryaci ne. Domin wanda baya kaunar dan'uwansa da yake gani, ba zai iya kaunar Allah da bai taba gani ba. 21Wannan ne umarnin da muke da shi daga wurinsa: Duk wanda yake kaunar Allah dole ne ya kaunaci dan'uwansa.

5

1Duk Wanda ya gaskata Yesu shine Almasihu haifaffe na Allah ne. Kuma duk wanda ya kaunaci uba ya kaunaci dan da uban ya haifa. 2Haka muka sani muna kaunar 'ya'yan Allah: yayin da muka kaunaci Allah, kuma muka aikata umarninsa. 3Wannan itace kaunar Allah, cewa mu kiyaye umarninsa. Domin umarninsa ba masu nawaitawa bane.

4Duk wanda yake haifaffe na Allah yakan yi nasara da duniya. Wannan itace nasarar da ta rinjayi duniya, wato bangaskiyarmu. 5Wanene wannan mai nasara da duniya? Sai dai wanda ya gaskata Yesu Dan Allah ne.
6Wannan shine wanda yazo ta wurin ruwa da jini: Yesu Almasihu. Ya zo ba ta wurin ruwa kadai ba, amma ta wurin ruwa da jini. 7Domin akwai uku wadanda suke bada shaida: 8Ruhu, da ruwa, da kuma jini. Wadannan ukun kuwa manufarsu daya ce.
9Idan mun karbi shaidar mutane, shaidar Allah ta fi girma. Wannan ita ce shaidar Allah, wato ya bada shaida akan Dansa. 10Wanda ya gaskata da Dan Allah shaidar tana nan tare da shi. Duk wanda bai bada gaskiya ga Allah ba, ya mai da shi makaryaci kenan, domin bai gaskata da shaidar da Allah ya bayar game da Dansa ba.
11Wannan ita ce shaida: Allah ya bamu rai madawwami, wannan rai kuwa yana cikin Dansa. 12Duk wanda yake da Dan, yana da rai. Duk wanda ba shida Dan Allah kuwa bashi da rai.
13Na rubuto maku wannan ne don ku tabbata kuna da rai madawwami--a gare ku wadanda suka gaskata da sunan Dan Allah. 14Wannan shine gabagadin da muke da shi a gabansa, wato, in mun roki kome bisa ga nufinsa, zai ji mu. 15Haka kuma, in mun san yana jinmu--Duk abin da mu ka rokeshi--mun sani muna da duk abin da muka roka daga gare shi.
16Idan wani ya ga dan'uwansa ya yi zunubin da bai kai ga mutuwa ba, sai yayi masa addu'a, Allah kuwa zai ba shi rai. Ina nufin wadanda suka yi zunubin da bai kai ga mutuwa ba. Akwai zunubin da yake kai wa ga mutuwa: Ban ce a yi addu'a domin wannan ba. 17Dukkan rashin adalci, zunubi ne, amma akwai zunubin da bai kai ga mutuwa ba.
18Mun sani kowanne haiffafe daga wurin Allah ba ya yin zunubi. Amma wanda ke haifaffe daga wurin Allah, ya kan kare shi, mugun nan kuwa ba zai iya yi masa illa ba. 19Mun sani mu na Allah ne, mun kuma sani dukkan duniya tana hannun mugun nan.
20Amma mun sani Dan Allah yazo, kuma ya bamu fahimta, domin mu san wanda yake shi ne mai gaskiya. Haka kuma muna cikin wannan wanda shine gaiskiya, kuma cikin Dansa Yesu Almasihu. Shine Allah na gaskiya, da kuma rai na har abada. 21'Ya'ya, ku tsare kanku daga bautar gumaka.

2 Yahaya

1

1Daga dattijon zuwa ga uwar gida zababbiya da yayanta, wadanda nake kauna da gaskiya, ba ni kadai ba, amma da dukan wadanda sun san gaskiya - 2domin gaskiya da take cikinmu za ta kuma kasance tare da mu har abada. 3Alheri da jinkai da salama za su kasance tare da mu, daga Allah Uba da kuma daga Yesu Almasihu Dan Uba, a cikin gaskiya da kauna.

4Na yi murna sosai sa'anda na sami wadansu yayanki suna tafiya cikin gaskiya, kamar yadda muka karbi wannan umarni daga Uba. 5Yanzu ina rokon ki, uwar gida, ba kamar ina rubuta maki sabon umarni ba, amma wannan da muka samu tun da can, cewa mu kaunaci junanmu. 6Wannan kuma itace kauna, cewa mu yi tafiya bisa ga umarnin sa. Wannan shine umarnin, daidai kamar yadda kuka ji da fari, da cewa ku yi tafiya a cikinsa.
7Gama masu yaudara sun fito a duniya, wadanda ba su yarda cewa Yesu ya zo cikin jiki ba. Wannan ne mayaudari da kuma magabcin Almasihu. 8Ku dubi kanku, domin kada ku rasa abubuwan da mu duka muka yi aiki a kansu, amma domin ku karba dukan sakamon ku.
9Duk wanda ya ci gaba da tafiya ba cikin koyarwa Almasihu ba, ba shi da Allah. Wanda ya zauna cikin koyarwar kwa yana tare da Uban da kuma Dan. 10Duk wanda ya zo wurinku, ba tare da wannan koyarwar ba, kar ku karbe shi cikin gidanku, kada ma ku gaishe shi. 11Domin duk wanda ya gaishe shi ya yi tarayya da shi kenan cikin miyagun ayyukan sa.
12Ina da abubuwa dayawa da nake so in rubuta maki amma al'kalami tawada da takarda baza su iya daukar su duka ba. Amma duk da haka ina begen zuwa gare ki domin mu yi magana fuska da fuska, domin farin cikn mu ya zama cikakke. 13Yayan yar'uwarki zababbiya suna gaishe ki.

3 Yahaya

1

1Daga dattijon zuwa ga Gayus, wanda nake kauna da gaske. 2Ya kaunatace na, ina addu'a domin ka samu albarka cikin kowanne al'amari, da kuma koshin lafiya, kamar yadda ruhun ka yake lafiya. 3Na yi farin ciki kwarai sa'adda wadansu 'yan'uwa suka zo suka ba da shaida a kan bangaskiyar ka, kamar yadda ka ke bin gaskiya. 4Ba abin da ya fi faranta mani rai kamar in ji yayana suna tafiya cikin gaskiya.

5Ya kaunatace na, kana aiki da aminci zuwa ga 'yan'uwa da baki, 6wadanda suka shaida kaunar ka a gaban ikilisiya. Zai yi kyau ka yi masu taimako da kyakkyawar salama, ta hanyar da ta dace da masu ibada, 7domin sabili da sunan nan ne suka fito, ba su kuma karbar kome a hannun al'ummai. 8Don haka ya kamata mu karbi irin wadannan mutane, domin mu zama abokan aiki tare da su a kan gaskiya.
9Na rubuta wasika zuwa ga ikilisiya, amma Diyotariffis, wanda ya fi kowa son girma a cikinsu, bai karbe mu ba. 10Saboda haka, idan na zo, zan tuna masa da irin ayukkan sa, da kuma yadda yake babbata sunayen mu a wurin jama'a da miyagun kalmomi. Wannan ma bai ishe shi ba, har ma yana kin karbar 'yan'uwa. Ya kuma hana wadanda suke son su yin hakan, harma ya kan kore su daga ikilisiya.
11Ya kaunatace na, kada ka yi koyi da mugun abu, sai dai abu mai kyau. Dukan wanda yake yin abu mai kyau na Allah ne; mai aikata mugunta kuma bai san Allah ba. 12Dimitiriyas yana da kyakkyawar shaida a gun kowa har a wurin gaskiyar da kanta. Mu ma mun shaida shi, ka kuma san shaidar mu gaskiya ce.
13Ina da abubuwa dayawa da zan rubuta maka, amma ban so in rubuta maka su da alkalami da tawada ba. 14Ina sa zuciya mu sadu ba da dadewa ba, sa'annan mu yi magana ido da ido. 15Bari salama ta kasance tare da kai. Abokanmu suna gaishe ka, kuma ka isadda sakon gaisuwar mu ga sauran abokai da sunayen su.

Yahuda

1

1Yahuza, bawan Yesu Almasihu kuma dan'uwan Yakubu, zuwa ga kirayayyu, kaunatattu a cikin Allah Uba, kebabbu domin Yesu Kristi: 2bari jinkai da salama da kauna su ribabanya a gare ku.

3Kaunatattu, ina iyakar kokari in rubuta maku game da ceton mu duka, ya zama dole in gargade ku sosai game da bangaskiya wadda aka mika wa masu bi sau daya tak ba kari. 4Don wasu mutane sun sadado sun shigo da sanda a asirce wadanda an rubuta game da hukuncin su tun da dadewa-mutane marasa imani, wanda suka canza alherin Allah zuwa lalata, kuma sun karyata makadaicin Shugaba da Ubangijinmu, Yesu Almasihu.
5Ina so in tunashe ku-ko da shike kun rigaya kun san abin, da cewa Allah ya ceci wasu mutane daga kasar masar, amma daga baya ya hallaka wadanda basu ba da gaskiya ba. 6Kuma mala'iku wadanda ba su rike matsayin ikon su ba, amma suka bar wurin zaman su na ainihi-Allah ya tsare su a sarka na har'abada a cikin bakin duhu domin babban ranar shari'a.
7Suna nan kamar Saduma da Gwamrata da kuma biranen da ke kewaye da su, wadanda suka ba da kansu ga fasikanci suna bin sha'awoyi wanda ba na dabi'a ba. Aka mai da su abin misalin wadanda suka sha wuta mara matuka. 8Haka kuma, wadannan masu mafarkan suna lalatar da jikinsu. Suna raina masu mulki, kuma suna fadar miyagun abubuwa a kan masu daukaka.
9Amma ko Mika'ilu babban mala'ika, a lokacin da yake jayyaya da muhawara da shaidan a kan gawar Musa, bai kuskura ya fadi wata kalmar hukunci a kansa ba. Maimakon haka ya ce, "Bari Ubangiji ya tsauta maka!" 10Amma waddannan mutane suna kawo batanci game da dukan abin da ba su gane ba. Wadannan mutane masu halin dabbobi ne, suna kwa jawo wa kansu hallaka kenan. 11Kaiton su! Domin sun bi hanyar Kayinu, kuma sun tsunduma cikin kuskuren Bal'amu domin samun riba. Suka hallaka cikin husuma irin ta Kora.
12Wadannan hatsari ne a boye cikin bukukuwan ku na kauna. Suna shagali ba kunya ba tsoro, suna ciyar da kansu kadai. Su holokon hadari ne marar ruwa, wanda iska ke korar sa. Su itatuwa ne shirim ba yaya, mattatu ribi biyu, tumbukakku tun daga saiwa. 13Su rakuman teku ne masu hauka, suna fahariya cikin kumfar kunyar su. Su kamar taurari ne masu tartsatsi. Wadanda aka tanada wa duhu baki kirin na har abada.
14Ahnuhu, mutum na bakwai daga Adamu, ya yi anabci game da su cewa, "Duba, Ubangiji zai zo da tsarkakan sa dubun dubbai. 15Domin ya zartar da hukunci a kan dukan kowa, ya kuma cakune dukan marasa da'a a cikin dukan ayyukan su na rashin da'a wanda suka aikata a hanyar da bata cancanta ba, da kuma kalmomi masu kaifi da masu zunubi suka fada game da shi." 16Wadannan masu cecekuce ne, masu gunaguni, wadanda ke bin sha'awar su ta mugunta, masu tinkaho da fahariya, masu bambadanci domin ribar kansu.
17Amma ku, kaunatattu, ku tuna da kalmomin da manzannin Yesu Almasihunmu suka gaya maku tun da. 18Sun ce maku, "A cikin kwanaki na karshe, za a samu masu ba'a, wadanda ke bin sha'awoyin su na rashin ibada," 19Wadannan mutane masu haddasa tsatsaguwa ne, kuma su yan duniya ne, ba su kuma da Ruhu.
20Amma ku, kaunatattu, ku gina kanku a cikin mafificiyar bangaskiyar ku mai daraja, kuma kuna addu'a a cikin Ruhu Mai Tsarki. 21Ku rike kanku a cikin kaunar Allah, kuna kuma jiran jinkan Ubangijinmu Yesu Almasihu wanda ke kawo rai na har abada.
22Ku nuna jinkai ga masu shakku. Ceci wadansu ta wurin fizge su daga wuta. 23Ga wadansu kuma ku nuna jinkai da rawar jiki, kuyi kyamar koda tufafin jikinsu ma.
24Yanzu, zuwa ga wanda yake da iko ya hana ku tuntube, ya kuma sa ku tsaya a gaban madaukakiyar kasancewarsa, marasa abin zargi da kuma murna mai yawa, 25zuwa ga Allah makadaici mai ceton mu ta wurin Yesu Almasihu Ubangijinmu, daukaka, da girma, da mulki, da iko su kasance, kamin dukan lokuta, yanzu, da har abada. Amin.

Wahayin yahaya

1

1Wannan shine wahayin Yesu Almasihu da Allah ya bashi ya nuna wa bayinsa abinda zai faru ba da dadewa ba. Ya bayyana wannan ta wurin aiko da mala'ikansa ga bawansa Yahaya. 2Yahaya yayi shaida akan abinda ya gani game da maganar Allah da kuma shaidar da aka bayar game da Yesu Almasihu. 3Mai albarka ne wanda ke karanta littafin nan da murya mai karfi, da kuma wadanda ke sauraron kalmomin wannan annabci kuma suke biyayya da abinda aka rubuta a ciki, domin kuwa lokaci ya kusato.

4Ni Yahaya, zuwa ga ikilisiyoyi bakwai na kasar Asiya: alheri zuwa gare ku da salama daga wanda ke yanzu, wanda ya kuma kasance a da, shi ne kuma mai zuwa nan gaba, kuma daga ruhohin nan bakwai da ke gaban kursiyinsa, 5kuma daga Yesu Almasihu, wanda ke amintaccen mashaidi, dan fari na tashi daga cikin matattu, kuma mai mulkin sarakunan duniya. Ga wanda ya ke kaunar mu ya kuma kwance mu daga daurin zunubanmu ta wurin jininsa, 6ya maishe mu masu mulki, firistoci na Allahnsa da Ubansa - daukaka da iko su tabbata gare shi har abada abadin, Amin.
7Duba yana zuwa tare da gizagizai, kowane ido zai gan shi, har ma da wadanda suka soke shi. Haka kuma dukkan kabilun duniya za su yi makoki saboda da shi. I, Amin. 8"Nine na farko da na karshe", in ji Ubangiji Allah, "Wanda yake shine a yanzu, shine wanda ya kasance a da, kuma shi ne mai zuwa nan gaba, Mai iko duka."
9Ni, Yahaya- dan'uwan ku da wanda ke tarayya daku cikin shan wahala, da mulki da tsawon jimrewa wadanda ke cikin Yesu - ina tsibirin da ake kira Batmusa saboda maganar Allah da kuma shaida game da Yesu. 10Ina cikin Ruhu a ranar Ubangiji. Sai naji wata murya mai karfi a baya na kamar ta kaho. 11Ta ce, "Rubuta abinda ka gani a cikin littafi, ka kuma aika wa ikilisiyoyin nan bakwai - ga Afisus, ga Simirna, ga Birgamas, ga Tayatira, ga Sardisu, ga Filadalfiya, da kuma ga Laudikiya."
12Na juya don in ga wanda muryarsa ke magana da ni, da na juya sai na ga fitilu bakwai akan madorin su 13A tsakiyar fitilun akwai wani mai kama da dan mutum, yana sanye da doguwar tufa har tafin sawunsa, da damara ta zinariya kewaye a kirjinsa.
14Kansa da gashinsa fari fat kamar auduga - kamar dusar kankara, kuma idanun sa kamar harshen wuta. 15Kafaffunsa kamar gogaggiyar tagulla, kamar tagullar da aka tace da wutar makera, muryar sa kuma kamar kugin ambaliyar ruwan teku ne. 16A hannunsa na dama yana rike da taurari bakwai, daga bakinsa kuma kakkaifan takobi mai kaifi biyu ke fitowa. Fuskarsa tana haskakawa kamar sa'adda rana ke haskakawa kwarai.
17Lokacin da na gan shi, na fadi kamar mataccen mutum a kafaffunsa. Ya dora hannunsa na dama a kaina ya ce, "Kada ka ji tsoro. Nine na farko da na karshe, 18da kuma wanda ke raye. Na mutu, amma duba ina raye har abada! Kuma ina da mabudin mutuwa da na hades.
19Domin haka ka rubuta abinda ka gani, abin da ke yanzu, da abin da zai faru bayan wanan. 20Akan boyayyar ma'ana game da taurari bakwai da ka gani a hannun dama na, da madorin fitilu bakwai na zinariya: Taurarin nan bakwai mala'iku ne na ikilisiyoyi bakwai, kuma madorin fitilun nan bakwai ikilisiyoyi ne bakwai.

2

1"Zuwa ga mala'ikan dake ikilisiyar Afisus, ka rubuta: 'Wadannan sune kalmomin wanda ke rike da taurari bakwai a cikin hannun damarsa. wanda yake tafiya a tsakanin zankayen fitilun zinari bakwai, 2"Na san abubuwan da ka yi, da famar ka, da hakurinka da jimirinka. Na sani ba ka jimrewa miyagun mutane, na sani ka gwada wadanda suka ce da kansu, su manzanni ne, amma ba haka ba, ka tarar da su makaryata.

3Na san kana da tsawon jimrewa, kuma ka sha wahala sosai sabili da sunana, kuma baka gaji ba. 4Amma ga rashin jin dadi na da kai, ka bar kaunar ka ta fari. 5Domin haka ka tuna daga inda ka fadi. Ka tuba ka yi abubuwan da ka yi da fari. Sai fa ka tuba, zan zo maka in kuma cire fitilar ka daga mazauninta.
6Amma kana da wannan: Ka tsani abubuwan da Nikolatawa suka yi, wanda nima na tsana. 7wanda yake da kunnen ji ya saurari abinda Ruhu yake fada wa ikilisiyoyi. Ga wanda yayi nasara zan bashi dama ya ci daga itacen rai, wanda ke cikin firdausin Allah.""
8Zuwa ga mala'ikan da ke Ikilisiliyar Samirna rubuta: 'Wadannan su ne kalmomin wanda yake shine farko shine karshe, wanda ya mutu ya sake rayuwa kuma. 9"Na san wahalun ka da talaucin ka amma kana da arziki. Nasan masu bata suna wadanda suke cewa su Yahudawa ne, amma ba haka suke ba. Su majami'ar Shaidan ne.
10Kada ka ji tsoron wahalar da zaka fuskanta nan gaba. Duba! Shaidan yana gab da jefa wadansun ku cikin kurkuku, domin a gwada ku, kuma zaku sha wahala ta kwana goma. Kuyi aminci har ga mutuwa zan baku rawanin rai. 11wanda yake da kunne ya saurari abinda Ruhu yake fada wa ikilisiyoyi. Shi wanda yayi nasara ba zai cutu a mutuwa ta biyu ba.""
12"Zuwa ga mala'ikan dake ikilisiyar Burgamas rubuta: 'Wadannan ne kalmomin wanda ya ke da takobi mai kaifi biyu; 13"Na san inda kake zama can inda kursiyin shaidan yake. Duk da haka ka rike sunana da karfi, na sani baka yi musun bangaskiyar ka da ni ba, ko a lokacin Antifas mashaidina, amintaccena, wanda aka kashe a tsakaninku, can inda shaidan yake zama.
14Amma ga rashin jin dadi na kadan da kai: Kana da wadansu da suke rike da koyarwar Bil'amu kamkam, wanda ya koya wa Balak ya sa abin tuntubi gaban 'ya'yan Isra'ila, domin su ci abincin da aka mika wa gumaka kuma suyi fasikanci. 15Hakannan kuma wasunku sun rike koyarwar Nikolatawa kamkam.
16Sabili da haka ka tuba! Idan ka ki zan zo gare ka da sauri, kuma in yi yaki gaba da su da takobi dake cikin bakina. 17Bari wanda yake da kunne ya sauriri abin da Ruhu yake fadawa ikilisiyoyi. Ga wanda yayi nasara zan bada wata boyayyar manna, kuma zan bashi farin dutse da sabon suna a rubuce a kan dutsen, suna wanda ba wanda ya sani, sai shi wanda ya karbe shi.""
18Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar Tiyatira rubuta: 'Wadannan sune kalamomin Dan Allah, wanda yake da idanu kamar harshen wuta; sawayen kamar gogaggiyar tagulla: 19"Na san abin da ka yi, kaunar ka, da bangaskiya da hidima da tsawon jimrewar ka. Na san abinda ka yi bada dadewa ba ya fi abinda ka yi da fari.
20Amma ga rashin jin dadi na da kai: Kana hakurce wa matar nan Yezebel, wadda take kiran kanta annabiya. Ta wurin koyarwarta, ta rudi bayina suyi fasikanci kuma su ci abincin da aka mika wa gumaka sadaka. 21Na bata lokaci domin ta tuba amma bata so ta tuba da fasikancin ta.
22Duba! zan jefa ta a kan gadon jinya, wadanda kuma suka yi zina da ita za su shiga babbar wahala, sai dai in sun tuba daga ayukan ta. 23Zan buga 'ya'yanta da mutuwa, kuma dukan ikilisiyoyi zasu san cewa nine wanda nake bincike tunani da zukata. Zan ba kowanen ku bisa ga ayyukansa.
24Amma ga sauran ku dake cikin Tayatira, ga kowanen ku wanda bai rike wannan koyarwar ba, kuma bai san abinda wadansu suke kira zurfafan abubuwan Shaidan ba--ga ku na ce ban sa muku wata nawaya ba.' 25Duk da haka dole ku tsaya da karfi har in zo.
26Wanda yayi nasara da wanda ya yi abin da na yi har karshe, a gareshi zan bada iko akan al'ummai 27Zai yi mulkin su da sandar karfe, zai farfasa su kamar randunan yumbu." 28Kamar yadda na karba daga wurin Ubana, ni kuma zan bashi tauraron asubahi. 29Bari wanda yake da kunne ya saurari abinda Ruhu yake fadawa ikilisiyioyi.""

3

1"Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar Sardisu rubuta: 'Wadannan ne kalmomin wanda yake rike da ruhohi bakwai na Allah da taurari bakwai. "Na san abin da ka aikata. Ka yi suna cewa kana raye amma kai mattacce ne. 2Ka farka ka karfafa abin da ya rage amma ya kusan mutuwa, domin ban sami ayyukanka cikakku a gaban Allahna ba.

3Domin haka sai ka tuna, da abubuwan da ka karba kuma kaji. Ka yi biyayya da su, ka kuma tuba. Amma idan baka farka ba, zan zo maka kamar barawo, kuma ba zaka farga da sa'ar da zan zo gaba da kai ba. 4Amma akwai sunayen mutane kadan a Sardisu wadanda basu kazantar da tufafinsu ba. Za su yi tafiya tare da ni sanye da fararen tufafi domin sun cancanta.
5Wanda ya yi nasara za a sanya mashi fararen tufafi, kuma ba zan taba share sunansa ba daga Littafin Rai, kuma zan fadi sunansa a gaban Ubana, da kuma gaban mala'ikunsa. 6Bari wanda yake da kunne ya saurari abin da Ruhu ke fadawa ikilisiyoyi."'"
7Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar cikin Filadelfiya rubuta: kalmomin wanda yake maitsarki ne kuma mai gaskiya - yana rike da mabudin Dauda, yana budewa babu mai rufewa, kuma inda ya rufe ba mai budewa. 8Na san abin da ka aikata. Duba, na sa budaddiyar kofa a gabanka wanda ba mai iya rufewa. Na san kana da karamin karfi, duk da haka ka yi biyayya da maganata kuma baka yi musun sunana ba.
9Duba! Wadanda ke na majami'ar Shaidan, wadanda suke cewa su Yahudawa ne; amma maimakon haka karya suke yi. Zan sa su zo su rusuna a kafafunka, kuma za su san cewa ina kaunarka. 10Tun da ka jure cikin hakuri ka kiyaye dokoki na, ni ma zan kiyaye ka daga sa'a ta gwaji da zata sauko kan dukan duniya, domin a gwada mazauna duniya. 11Ina zuwa da sauri. Ka rike abin da kake da shi kamkam domin kada wani ya dauke maka rawani.
12Zan sa wanda ya yi nasara ya zama ginshiki a haikalin Allahna, kuma ba zai taba fita daga cikin sa ba. Zan rubuta sunan Allahna a kansa, sunan birnin Allahna (sabuwar Urushalima, mai saukowa daga sama daga wurin Allahna), da kuma sabon sunana. 13Bari wanda yake da kunne ya ji abin da Ruhu ke gayawa ikilisiyoyi."
14"Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar da ke Lawudikiya rubuta: 'Wadannan sune kalmomin Amin, madogara da mai shaidar gaskiya, mai mulki bisa hallittar Allah. 15Na san abin da ka aikata, ba ka sanyi ko zafi. Naso ko da kana sanyi ko zafi! 16Amma saboda kai tsaka-tsaka ne - ba zafi ba sanyi - na kusa tofar da kai daga bakina.
17Domin ka ce, "Ni mai arziki ne, na mallaki kadarori da yawa, ba na bukatar komai." Amma ba ka sani ba kana cike da takaici ne, abin tausayi, matalauci, makaho kuma tsirara kake. 18Saurari shawara ta: Ka sayi zinariya a wuri na wadda aka goge da wuta domin ka zama mai arziki, domin ka suturta kanka da fararen tufafi masu kyalli domin kada ka nuna kunyar tsiraicin ka, da mai domin ka shafa wa idanunka ka sami gani.
19Ina horar da duk wanda nake kauna, ina kuma koya masu yadda za su yi rayuwa. Saboda haka, ka himmatu ka tuba. 20Duba, ina tsaye a bakin kofa ina kwankwasawa. Idan wani ya ji muryata ya bude kofar, zan shigo cikin gidansa, in ci tare da shi, shi kuma tare da ni.
21Wanda ya ci nasara, zan bashi dama ya zauna tare da ni bisa kursiyina, kamar yadda nima na ci nasara kuma na zauna da Ubana a kan kursiyinsa. 22Bari wanda yake da kunne ya saurari abin da Ruhu yake fadawa wa ikilisiyoyi."

4

1Bayan wadannan abubuwa na duba, sai ga budaddiyar kofa a sama. Muryar fari da na ji kamar kakaki, na cewa hauro in nuna maka abubuwan da dole za su faru bayan wadannan al'amura." 2Nan da nan ina cikin Ruhu, sai na ga wani kursiyin da aka ajiye shi a sama, da wani zaune bisansa. 3Shi da ke zaune a kan tana da kamanin yasfa da yakutu. Akwai Bakangizo kewaye da kursiyin kamanin bakangizon kuwa zumurudu.

4A kewaye da kursiyin kuwa akwai kursiyoyi ashirin da hudu, masu zama bisa kursiyoyin nan kuwa dattawa ne ashirin da hudu, sanye da fararen tufafi, da kambunan zinariya bisa kawunansu. 5Daga kursiyin walkiya na ta fitowa, cida, da karar aradu. Fitilu bakwai na ci a gaban kursiyin, fitilun sune ruhohin Allah guda bakwai.
6Gaban kursiyin akwai tekun gilashi, mai haske kamar karau. A tsakiyar kursiyin da kewayen kursiyin akwai rayayyun hallitu guda hudu cike da idanu gaba da baya.
7Rayayyen hallitta na farko na da kamanin zaki, rayayyen hallitta na biyun kamanin dan maraki ne, rayayyen hailitta na uku fuskar sa kamar dan adam, kuma rayayyen hallitta ta hudu na da kamanin gaggafa mai tashi. 8Dukan rayayyun hallittan nan hudu na da fukafukai shida shida, cike da idanu a bisa da karkashin fukafukan. Dare da rana ba sa daina cewa, Mai Tsarki, Mai Tsarki, Mai Tsarki ne Ubangiji Allah, mai iko duka, shine da shine yanzu shine mai zuwa."
9A dukan lokacin da rayayyun hallittun nan suke ba da girma, daukaka, da godiya ga shi da ke zaune bisa kursiyin, wanda ke raye har abada abadin, 10sai dattawan nan ashirin da hudu suka fadi da fuskokinsu a kasa gaban shi da ke zaune bisa kursiyin. Suka yi sujada ga shi da ke rayuwa har abada abadin, suna jefar da kambinsu a gaban kursiyin, suna cewa, 11"Ka cancanta, ya Ubangijinmu da Allahnmu, ka karbi yabo da daukaka da iko. Domin kai ka hallicci dukan komai, da kuma nufinka ne, suka kasance aka kuma hallicce su.

5

1Sa'annan na ga a cikin hannun daman wanda ke zaune a kan kursiyin, na ga littafi wanda ke da rubutu ciki da waje, an kuma hatimce shi da hatimai bakwai. 2Na kuma ga wani kakkarfan mala'ika na shela da murya mai karfi, "Wa ya isa ya bude littafin ya kuma bambare hatimin?"

3Ba wani a sama ko a kasa ko karkashin kasa da ya iya ya bude littafin ko ya karanta abin da ke cikinsa. 4Na yi kuka mai zafi saboda ba wani da ya cancanta da zai bude littafin ko ya karanta abin da ke cikinsa. 5Amma daya daga cikin dattawan nan ya ce mani, "Kada ka yi kuka. Duba! Zaki na kabilar Yahuza, Tushen Dauda, ya yi nasara. Ya cancanci bude littafin da kuma hatimansa bakwai."
6Na ga Dan Rago yana tsaye tsakanin kursiyin da rayayyun halittun nan guda hudu a cikin dattawa. Yana kama da wanda aka kashe. Yana da kafonni bakwai da idanuwa bakwai; wadannan sune ruhohin Allah bakwai da aka aiko zuwa dukan duniya. 7Ya tafi ya karbi littafin daga hannun daman wanda ke zaune bisa kursiyin.
8Lokacin da Dan Ragon ya dauki littafin, rayayyun halittun nan hudu da dattawan nan ashirin da hudu suka fadi har kasa a gaban Dan ragon. Kowannen su na dauke da molo da tasar zinariya cike da kayan kamshi, wadanda kuwa sune addu'o'in masu ba da gaskiya.
9Suka raira sabuwar waka: "Ka cancanta ka dauki littafinka kuma bude hatimansa. Domin an yanka ka, da jininka ka saya wa Allah mutane daga kowacce kabila, harshe, jama'a da al'umma. 10Ka maishe su mulki da firistoci su bauta wa Allanmu, kuma za su yi mulki a duniya."
11Da na duba sai na ji karar mala'iku masu yawa kewaye da kursiyin da rayayyun halitu da kuma dattawa. Jimillarsu ya kai dubbai goma, sau dubbai goma, da dubun dubbai. 12Suka tada murya da karfi suka ce, "Macancanci ne Dan Ragon da aka yanka ya karbi iko, wadata, hikima, karfi, girma, daukaka da yabo."
13Na ji kowanne halittaccen abu da ke cikin sama da kasa da karkashin kasa da cikin teku - dukan abubuwan da ke cikinsu - na cewa, "Ga shi wanda ke zaune a kan kursiyin da kuma Dan Ragon, yabo, girma, daraja, da kuma ikon yin mulki, har abada abadin. 14Sai rayayyun halittun nan hudu suka ce, "Amin!" dattawan nan kuma suka fadi da fuskokinsu suka yi sujada.

6

1Na duba lokacin da Dan Ragon ya bude daya daga cikin hatiman bakwai, sai na ji daya daga cikin rayayyun halittattun hudu ya fada da murya kamar tsawa, "Zo!" 2Sai Na duba sai ga wani farin doki, mahayinsa na rike da baka, kuma an bashi rawani. Ya fito a matsayin mai nasara domin ya yi nasara.

3Sa'anda Dan Ragon ya bude hatimi na biyu, sai na ji rayayyen halitta na biyu ya ce, "Zo!" 4Sai wani doki ya fito waje - jawur. Ga mahayin aka bashi dama ya dauke salama daga duniya, domin mutanen ta su karkashe juna. Wannan mahayin an bashi babbar takobi.
5Sa'anda Dan Ragon ya bude hatimi na uku, sai na ji rayayyen halita na uku ya ce, "Zo!" Na ga bakin doki, mai hawanta na rike da ma'auni a cikin hannunsa. 6Sai na ji kamar wata murya daga cikin rayayyun halittattun nan hudu ta ce, "Mudun alkama guda a kan albashin yini, kuma mudun sha'ir uku. Amma kar ka bata mai da kuma ruwan inabi."
7Da Dan Ragon ya bude hatimi na hudu, na ji muryar rayayyen halitta na hudu ya ce, "Zo!" 8Sai na ga wani doki ruwan toka. Mai hawansa an bashi suna mutuwa, hades kuma tana biye da shi. An basu iko bisa kashi hudu na duniya su kashe da takobi, yunwa, cututtuka, da kuma namomin jeji na duniya.
9Da Dan Ragon ya bude hatimi na biyar, a karkashin bagadi sai na ga rayukan wadanda aka kashe saboda maganar Allah, da kuma shaidar da suka rike. 10Suka yi kuka da babban murya, "Sai yaushe ya mai iko duka, Mai Tsarki da gaskiya, zaka shari'anta mazaunan duniya, ka kuma dauki fansar jininmu? 11Sai kowanne dayan su aka bashi farar tufa aka kuma fada masu su kara jira na lokaci kadan har sai adadin abokan bautar su da kuma 'yan'uwansu maza da mata wadanda aka kashe ya cika, kamar yadda aka kashe su.
12Da Dan Ragon ya bude hatimi na shidan, ina kallo sai ga babbar girgizar kasa. Rana ta zama baki kirin kamar bakar tufa, wata kuma ya zama kamar jini. 13Taurarin sama suka fado kasa, kamar yadda itacen baure ke karkade 'ya'yansa da basu nuna ba, yayin da babbar iska ta kada. 14Sama kuma ta bace kamar takardar da aka nannade. Kowanne dutse da tsibiri aka kau da shi daga wurinsa.
15Sai sarakan duniya da muhimman mutane da sarakunan yaki, attajirai, da masu iko, tare da kowanne mutum, bawa da 'yantacce suka boye cikin duwatsu da tsaunuka. 16Suka ce wa tsaunuka da duwatsu, "Ku fado bisan mu! Ku boye mu daga fuskar wanda yake zaune bisa kursiyin da kuma fushin Dan Ragon. 17Domin babban ranar fushin sa ta zo. Wa zai iya tsayawa?"

7

1Bayan wannan sai na ga mala'iku hudu suna tsaye bisa kusurwoyi hudu na duniya, suka rike iskoki hudu na duniya kamkam domin kada iska ta hura a kan duniya, a kan teku, ko wani itace. 2Sai na ga wani mala'ika na zuwa daga gabas, wanda yake da hatimin Allah mai rai. Ya yi kira da babbar murya da mala'ikun nan hudu da aka basu dama su azabtar da duniya da teku: 3"Kada ku azabtar da duniya, da teku, da itatuwa har sai mun sa hatimi bisa goshin bayin Allahnmu."

4Sai naji yawan wadanda aka hatimce: 144, 000, wadanda aka hatimce daga kowacce kabilar mutanen Isra'ila: 5dubu goma sha biyu aka hatimce daga kabilar Yahuza, dubu goma sha biyu daga kabilar Ra'ubainu, dubu goma sha biyu daga kabilar Gad, 6dubu goma sha biyu daga kabilar Ashiru, dubu goma sha biyu daga kabilar Naftali, dubu goma sha biyu daga kabilar Manassa.
7Dubu goma sha biyu daga kabilar Saminu, dubu goma sha biyu daga kabilar Lawi, dubu goma sha biyu daga kabilar Issaka, 8dubu goma sha biyu daga kabilar zabaluna, dubu goma sha biyu daga kabilar Yusufu, sai kuma dubu goma sha biyu daga kabilar Bilyaminu aka hatimce.
9Bayan wadannan abubuwa na duba, sai ga wani babban taro wanda ba mai iya kirgawa daga kowacce al'umma, kabila, mutane da harsuna tsaye a gaban kursiyin da gaban Dan Ragon. Suna sanye da fararen tufafi da ganyen dabino a hannuwansu, 10kuma suna kira da murya mai karfi: "Ceto ya tabbata ga Allahnmu wanda ke zaune bisa kursiyi, da kuma Dan Ragon!"
11Dukan mala'iku suna tsaitsaye kewaye da kursiyin kuma kewaye da dattawan nan da kuma rayayyun halittun nan hudu, suka kwanta rib da ciki da fuskokinsu a gaban kursiyin. Suka yi sujada ga Allah, 12suna cewa, "Amin! yabo, daukaka, hikima, godiya, girma, iko, da karfi su zama na Allahnmu har abada abadin! Amin!"
13Sai daya daga cikin dattawan ya tambaye ni, "Su wanene wadannan, da suke sanye da fararen tufafi, kuma daga ina suka fito?" 14Sai nace masa, "Ya shugaba, "Ka sani," sai ya ce mani, "Wadannan sune suka fito daga babban tsanani. Sun wanke tufafin su sun maida su farare cikin jinin Dan Ragon.
15Domin wannan dalili, suke gaban kursiyin Allah, kuma suna masa sujada dare da rana cikin haikalinsa. Shi wanda ke zaune bisa kursiyin zai zama runfa a bisan su. 16Ba za su kara jin yunwa ba, ko kishin ruwa ba. Rana ba zata buge su ba, ko kowanne zafi mai kuna. 17Domin Dan Ragon dake tsakiyar kursiyin zai zama makiyayin su, kuma zai bishe su zuwa mabulbulan ruwan rai, kuma Allah zai share dukan hawaye daga idanuwansu."

8

1Lokacin da Dan Ragon nan ya bude hatimi na bakwai, sai aka yi shiru a sama na kimanin rabin sa'a. 2Sa'anan na ga mala'iku bakwai wadanda ke tsaye a gaban Allah, aka kuma basu kahonni bakwai

3Wani mala'ika ya zo, rike da tasar turaren konawa na zinariya, a tsaye gaban bagadi. Turaren konawa mai yawa aka bashi saboda ya mika su tare da adu'o'in dukan masu bada gaskiya akan bagadin kona turare na zinariya a gaban kursiyin. 4Hayakin turaren konawa, da adu'o'in masu bada gaskiya, suka tashi sama a gaban Allah daga hanun mala'ikar. 5Mala'ikan ya dauki tasar turaren konawa ya cika ta da wuta daga bagadin. Sa'annan ya wurgo ta kasa zuwa duniya, sai ga tsawar aradu, da cida, da walkiya mai haske, da kuma girgizar kasa.
6Mala'ikun nan bakwai wadanda suke da kahonni bakwai suka yi shirin busa su. 7Mala'ika na fari ya hura kahonsa, sai ga kankara da wuta a garwaye da jini. Aka jeho shi kasa zuwa duniya sai kashi daya cikin uku na duniya ya kone, daya cikin uku na itatuwa suka kone, da duk danyar ciyawa suka kone kaf.
8Mala'ika na biyu ya busa kahonsa, sai wani abu mai kama da babban dutse mai cin wuta aka jefo shi cikin teku. Kashi daya cikin uku na tekun ya zama jini, 9daya cikin uku na rayayyun halittu da ke cikin ruwa suka mutu, sai daya bisa uku na jiragen ruwa aka hallaka.
10Mala'ika na uku ya busa kahonsa, sai gagarumin tauraro ya fado daga sama, yana ci kamar cocila, bisa kashi daya cikin uku na koguna da mabulbulan ruwa. 11Sunan tauraron Daci. Kashi daya cikin uku na ruwaye suka yi daci, sai jama'a da yawa suka mutu domin ruwayen sun yi daci.
12Mala'ika na hudu ya busa kahonsa, sai daya cikin kashi uku na rana ya harbu, da daya cikin kashi uku na wata da kuma daya cikin kashi uku na taurari. Sai daya cikin kashi uku nasu duka suka duhunce; daya cikin kashi uku na yini da daya cikin uku na dare suka rasa hasken su.
13Da na duba sai na ji gaggafa da take shawagi a tsakiyar sararin sama tana kira da babban murya, "Kaito, kaito, kaito, ga mazaunan duniya sabili da sauran karar kahonni na mala'ikun nan uku da za su busa."

9

1Sa'annan mala'ika na biyar ya busa kahonsa. Na ga tauraro daga sama da ya fado zuwa duniya. An ba tauraron nan mabudin hanyar rami marar iyaka. 2Ya bude hanyar rami marar iyaka, sai hayaki ya fito daga kofar kamar hayaki daga babban ramin wuta. Rana da iska suka juya duhu, sabili da hayakin da ke fitowa daga kofar ramin.

3Daga cikin hayakin kuwa sai ga fari sun fito zuwa duniya, aka ba su iko kamar na kunamai cikin duniya. 4Aka gaya masu kada su yi wa ciyayi da kowanne koren ganye ko itace illa, sai dai mutanen da basu da hatimin Allah a goshinsu.
5Ba a basu izini su kashe wadannan mutane ba, sai dai su azabtar da su na watani biyar. Zafinsu kuwa zai zama kamar na cizon kunama idan ta harbi mutum. 6A kwanakin nan mutane za su nemi mutuwa, amma ba za su same ta ba. Za su yi marmarin mutuwa, amma mutuwa za ta guje su.
7Farin kuwa suna kama da dawakai da aka shirya domin yaki. A bisa kansu akwai wani abu kamar rawanan zinariya, fuskokinsu kuma kamar na 'yan adam. 8Gashinsu kuma kamar na mata yake, hakoransu kamar hakoran zaki. 9Sulkunansu kuma kamar na karfe, karar fikafikansu kuma kamar karar kekunan dawakin yaki masu yawa da dawakai da aka shirya domin zuwa yaki.
10Suna da wutsiya da kari kamar kunamai; A wutsiyar su kuma suna da ikon da zai azabtar da mutane na tsawon wata biyar. 11Suna da wani kamar sarki a kansu, mala'ikan rami marar iyaka. Sunansa da Ibraniyanci Abadon, da Helenanci kuma Afoliyon. 12Bala'i na fari ya wuce. Duba! Bayan wannan akwai masifu guda biyu masu zuwa.
13Mala'ika na shida ya busa kahonsa, sai na ji murya daga kahonin bagadin zinariya da ke gaban Allah. 14Muryar ta ce wa mala'ika na shida da ke rike da kahon, "Kwance mala'ikun nan hudu da ke daure a babban kogin Yufiretis," 15Mala'iku hudun da aka shirya domin wannan sa'a, da wannan rana, da wannan wata, da kuma wannan shekara, aka sake su su kashe daya bisa uku na 'yan adam.
16Yawan sojoji da ke kan dawakai shine 200, 000, 000. Na ji adadin su. 17Haka na ga dawakan a cikin wahayina da mahayansu: Sulkunansu jawur kamar wuta, bakin shudi, da kuma ruwan doruwa. Kawunan dawakan suna kama da na zakuna, daga bakunansu kuma wuta, da hayaki da farar wuta suka fito.
18Aka kashe daya bisa uku na mutane ta annoban nan uku: wuta, hayaki da farar wuta da suka fito daka bakunansu. 19Domin iko na dawakan na bakunansu da wutsiyoyinsu - domin wutsiyoyinsu suna kama da macizai, kuma suna da kawuna wadanda dasu suke ji wa mutane rauni.
20Sauran 'yan adam, da ba a kashe su ta wannan annoba ba, basu tuba daga ayyukan da suka yi ba. Basu kuma daina bautar aljanu da gumakan zinariya, da azurfa, da tagulla, da dutse, da itace ba - abubuwan da ba su gani, ji, ko tafiya. 21Basu kuma tuba ba daga kisan kai, sihiri, fasikanci, ko kuma ayyukansu na sata ba.

10

1Sa'anan na ga wani babban mala'ika yana zuwa daga sama. Yana lullube cikin girgije, a bisa kansa akwai bakangizo. Fuskarsa kamar rana, kafafunsa kamar ginshikan wuta. 2Yana rike da karamin littafi a hannunsa, da aka bude, sai ya sa kafarsa ta dama a bisa teku, kafarsa ta hagu kuma a kan kasa.

3Sai yayi ihu da babbar murya kamar zaki mai ruri. Lokacin da ya yi ihu, tsawan nan bakwai suka yi magana da karar su. 4Da tsawan nan bakwai suka yi magana, ina dab da rubutu, amma na ji wata murya daga sama cewa, "Ka rike asirin abin da tsawan nan bakwai suka fada. Kada ka rubuta shi."
5Sai mala'ikan da na gani tsaye bisa teku da kasa, ya daga hannun damarsa sama. 6Sai ya rantse da wannan da ke raye har abada abadin - wanda ya halicci sama da duk abinda ke cikinsa, da duniya da duk abin da ke a kanta, da teku da dukan abin da ke cikinsa, sai mala'ikan ya ce, "Babu sauran jinkiri. 7Amma a ranar da mala'ika na bakwai yana dab da busa kahonsa, a lokacin ne asirin Allah zai cika, daidai da yadda ya sanar wa bayinsa annabawa."
8Muryar da na ji daga sama ta sake magana da ni: "Tafi, ka dauki budadden littafin da ke hannun mala'ikan da ke tsaye bisa teku da kan kasa." 9Sai na tafi wurin mala'ikan na ce da shi ka bani karamin littafin. Yace dani, "Dauki littafin ka ci. Zai sa cikinka ya yi daci, amma a bakinka zai yi zaki kamar zuma."
10Na dauki karamin littafin daga hannun mala'ikan na ci. Ya yi zaki sosai a bakina kamar zuma, amma da na ci, sai cikina ya zama da daci. 11Wani yace mani, "Dole ka sake yin annabci kuma game da mutane masu yawa, da al'ummai, da harsuna da sarakuna."

11

1Aka bani sanda in yi amfani da ita kamar sandar awo. Aka ce mani, "Tashi ka auna haikalin Allah da bagadi, da wadanda ke sujada a cikinsa. 2Amma kada ka auna harabar haikalin, domin an ba da shi ga Al'ummai. Za su tattake birnin mai tsarki har wata arba'in da biyu.

3Zan ba shaidu na biyu iko su yi anabci na kwanaki dubu daya da dari biyu da sittin, sanye da tsummoki. 4Wadannan shaidu sune itatuwan zaitun biyu da kuma fitilu biyu da suke tsaye a gaban Ubangijin duniya. 5Idan wani ya yi niyyar cutar da su, wuta na fitowa daga bakinsu ta lashe makiyansu. Duk mai son cutar da su, dole a kashe shi ta wannan hanya.
6Wadannan shaidu suna da iko su kulle sama domin kada a yi ruwa a lokacin da suke anabci. Suna da iko su juya ruwaye su zama jini, su kuma bugi duniya da kowacce irin annoba duk lokacin da suka ga dama. 7Sa'adda suka gama shaidarsu, dabban da ke fitowa daga rami marar iyaka zai yi yaki da su. Zai ci nasara da su ya kashe su.
8Gawawwakinsu zasu kwanta kan hanyar babban birnin nan (wanda ma'anar sa ake kira Saduma da Masar) inda aka gicciye Ubangijinsu. 9Wajen kwana uku da rabi wadansu daga dukan mutane, da kabila, da harshe, da al'umma za su yi kallon gawawwakinsu. Za su ki yarda a sa su cikin kabari.
10Mazaunan duniya zasu yi murna da biki a kansu. Har za su aika wa juna kyautai saboda annabawan nan biyu da suka azabtar da mazaunan duniya. 11Amma bayan kwana uku da rabi, numfanshin rai daga wurin Allah zai shiga cikinsu sa'annan za su tsaya a kan kafafunsu. Matsanancin tsoro zata fado kan wadanda za su gansu. 12Sa'annan zasu ji murya mai kara daga sama tana ce masu, "Ku hauro nan!" Sa'annan za su tafi sama cikin gajimarai, makiyansu suna kallo.
13A waccan sa'a za a yi babbar girgizar kasa, sai kashi daya cikin goma na garin ya fadi. Mutane dubu bakwai za su mutu a girgizar kasar, wadanda suka tsira kuwa za su tsorata su ba da daukaka ga Allah na sama. 14Annoba ta biyu ta wuce. Duba! Annoba ta uku tana zuwa nan da nan.
15Sa'annan mala'ika na bakwai ya busa kahonsa, sai muryoyi masu kara suka yi magana cikin sama cewa, "Mulkin duniya ya zama mulkin Ubangijinmu da na Almasihunsa. Zai yi mulki har abada abadin."
16Sa'annan dattawan nan ashirin da hudu da ke zaune a kursiyoyinsu a gaban Allah, suka fadi fuskokinsu na kasa. Suka yi wa Allah sujada. 17Suka ce, "Mun yi maka godiya, Ubangiji Allah, Madaukaki, wanda yake yanzu da wanda yake a da, saboda ka dauki ikonka mai girma ka fara mulki.
18Al'ummai suka fusata, amma hasalar ka ta zo. Lokaci ya zo da za a yi wa mattatu sharia, da zaka ba da sakamako ga bayinka annabawa, da masu ba da gaskiya, da wadanda suka ji tsoron sunanka, karami da babba. Lokaci kuma ya yi da za ka hallaka wadanda ke hallakar da duniya."
19Sa'annan aka bude haikalin Allah da ke sama, sai aka ga akwatin alkawarinsa a cikin haikalinsa. Sai ga hasken walkiya, da rugugi, da aradu, da girgizar kasa, da manyan duwatsun kankara.

12

1Aka ga wata babbar alama a sama: wata mace ta yi lullubi da rana, kuma wata na karkashin kafafunta; rawanin taurari goma sha biyu na bisa kanta. 2Tana da ciki, tana kuma kuka don zafin nakuda - a cikin azabar haihuwa.

3Sai aka ga wata alama cikin sama: Duba! Akwai wani katon jan maciji mai kawuna bakwai da kahonni goma, sai kuma ga kambi guda bakwai bisa kawunansa. 4Wutsiyarsa ta share daya bisa uku na taurari a sama ta zubo su kasa. Diragon nan ya tsaya a gaban matar da ta kusan haihuwa, domin lokacin da ta haihu ya lankwame yaronta.
5Sai ta haifi da, namiji, wanda zai yi mulkin dukan al'ummai da sandar karfe. Aka fizge yaron ta zuwa ga Allah da kursiyinsa, 6matar kuwa ta gudu zuwa jeji inda Allah ya shirya mata domin a iya lura da ita kwanaki 1, 260.
7A lokacin sai yaki ya tashi a sama. Mika'ilu da mala'ikunsa suka yi yaki da diragon, sai diragon da nasa mala'iku suka yake su su ma. 8Amma diragon ba shi da isashen karfin da zai ci nasara. Don haka, shi da mala'ikunsa ba su kara samun wuri a sama ba. 9Sai aka jefa katon diragon nan tare da mala'ikunsa kasa, wato tsohon macijin nan da ake kira Iblis ko Shaidan wanda ke yaudarar dukan duniya.
10Sai na ji wata murya mai kara a sama: "Yanzu ceto ya zo, karfi, da mulkin Allahnmu, da iko na Almasihunsa. Gama an jefar da mai sarar 'yan'uwanmu a kasa - shi da yake sarar su a gaban Allah dare da rana.
11Suka ci nasara da shi ta wurin jinin Dan Ragon da kuma shaidar maganarsu, gama ba su kaunaci ransu ba, har ga mutuwa. 12Don haka, yi farinciki, ya ku sammai da duk mazauna da ke cikinsu. Amma kaito ga duniya da teku saboda iblis ya sauko gare ku. Yana cike da mummunan fushi, domin ya san lokacin sa ya rage kadan.
13Da diragon ya ga an jefar da shi kasa, sai ya fafari matar nan da ta haifi da namiji. 14Amma aka ba matar nan fukafukai biyu na babbar gaggafa domin ta gudu zuwa inda aka shirya mata a jeji. A wannan wuri ne za a lura da ita na dan lokaci, da lokatai, da rabin lokaci - a lokacin da babu macijin.
15Macijin ya kwararo ruwa daga bakin sa kamar kogi, don ya kawo ambaliyar da zai kwashe ta. 16Amma kasa ta taimaki matar. Kasa ta bude bakinta ta hadiye kogin da diragon ya kwararo daga bakinsa. 17Sai diragon ya fusata da matar, sai ya tafi ya yi yaki da sauran zuriyarta, wadanda suka yi biyayya da umarnan Allah suna kuma rike da shaida game da Yesu. 18Sai diragon ya tsaya a kan yashi, a gaban teku.

13

1Sai na ga wani dabba yana fitowa daga teku. Yana da kahonni goma da kawuna bakwai. A kan kahonninsa akwai kambi goma, a kan kowanne kansa akwai suna na sabo. 2Wannan dabban da na gani yana kama da damisa, kafafunsa kuma kamar na beyar, bakinsa kuma kamar na zaki. Wannan diragon ya ba shi karfinsa, da kursiyinsa da ikonsa mai girma na sarauta.

3Daya daga cikin kawunan dabban ya yi kamar an kashe shi, amma rauninsa mai tsanani ya warke. Sai dukan duniya ta yi mamaki a yayin da suke bin dabban. 4Su ma suka yi wa diragon sujada, domin ya ba dabban ikonsa. Suka yi wa dabban sujada suna ta cewa, "Wanene kamar dabban? Wa kuma zai iya yin fada da shi?"
5Aka ba dabban baki da zai iya fadin kalmomin fahariya da sabo. Ya sami izini na zartar da iko har wata arba'in da biyu. 6Sai dabban ya bude bakinsa yana maganganun sabo ga Allah: yana sabon sunansa, da mazauninsa, da kuma wadanda ke zaune a sama.
7Aka yarje wa dabbar ya yi yaki da masu bi ya kuma yi nasara da su. An kuma ba shi iko bisa kowacce kabila, da jama'a, da harshe, da al'umma. 8Dukan wadanda ke zaune a duniya za su yi masa sujada, dukan wadanda tun hallitar duniya ba a rubuta sunayensu a littafin rai na Dan Rago ba, wanda aka yanka.
9Idan wani yana da kunne, bari ya ji. Duk wanda za a dauke shi zuwa bauta, ga bauta zai tafi. 10Duk wanda za a kashe da takobi, da takobi za a kashe shi. Wannan kira ne na dauriya, hakuri da bangaskiya ga wadanda suke da tsarki.
11Sai na ga wani dabban na fitowa daga cikin kasa. Yana da kahonni biyu kamar na dan rago, ya kuma yi magana kamar maciji. 12Ya zartar da dukan ikon dabban na farko a gabansa, ya kuma sa duniya da duk mazaunanta su yi wa dabban nan na farko sujada, wanda aka warkar masa da rauni mai kamar na ajali.
13Ya yi manyan al'ajibai. Har ya sa wuta ta sauko kasa daga sama a gaban mutane. 14Ta wurin alamu da aka yarje masa ya yi, ya yaudari mazaunan duniya. Ya ce masu su yi wata siffa don girmama dabban da yake da raunin takobi, amma duk da haka ya rayu.
15Aka yarje masa ya ba da numfashi ga siffar dabban domin siffar ta yi magana, ta kuma sa a kashe duk wadanda suka ki yin sujada ga dabban. 16Ya kuma tilasta kowa, kanana da manya, mawadata da matalauta, masu yanci da bayi, su karbi alama a hannun dama ko kuma a goshi. 17Ba shi yiwuwa wani ya saya ko ya sayar sai dai yana da alamar dabban, wato lambar nan da ke wakiltar sunansa.
18Wannan na bukatar hikima. Idan wani yana da hikima, sai ya kididdige lambar dabban nan. Gama lambar ta mutum ce. Lambarta itace 666.

14

1Sai na duba na ga Dan Ragon yana tsaye a kan Dutsen Sihiyona. Tare da shi akwai mutum dubu dari da arba'in da hudu wadanda aka rubuta sunansa da sunan Ubansa a goshinsu. 2Na ji wata murya daga sama mai kara kamar kogin ruwa mai gudu da kuma aradu mai kara. Muryar da na ji ta yi kama da masu molo suna kada molonsu.

3Suka raira sabuwar waka a gaban kursiyin da kuma gaban rayayyun halittun nan hudu, da kuma dattawan. Ba mai iya koyon wakar nan sai dai mutum 144, 000 nan wadanda aka fanso daga duniya. 4Wadannan sune wadanda basu kazantar da kansu da mata ba, gama sun kebe kansu da tsarki daga halin jima'i. Wadannan ne ke bin Dan Ragon duk inda ya tafi. Aka fanso su daga cikin mutane domin su zama nunan fari domin Allah da Dan Ragon. 5Ba a iske karya a bakinsu ba; ba su da aibi.
6Na ga wani mala'ika na firiya a tsakiyar sararin sama, wanda yake da madawwamin sako na labari mai dadi domin a sanar da ita ga mazaunan duniya - ga kowacce al'umma, da kabila, da harshe, da kuma jama'a. 7Yayi kira da babbar murya, "Ku ji tsoron Allah, ku daukaka shi. Gama sa'arsa ta hukunci ta yi. Yi masa sujada, shi wanda ya yi sama da kasa, da teku, da kuma mabulbular ruwa."
8Sai wani malai'ka, malaika na biyu, ya biyo yana cewa, "Ta fadi, Babila mai girma ta fadi, wadda ta rinjayi dukan al'ummai su sha ruwan inabin fasikancinta."
9Wani mala'ika - na uku - ya biyo su da murya mai karfi yana cewa, "Duk wanda ya yi sujada ga dabban da kuma siffarsa, ya karbi alama a goshinsa ko a hannunsa, 10shi ma zai sha daga ruwan inabin fushin Allah, ruwan inabi da aka zuba tsantsa cikin kokon fushinsa. Wanda ya sha shi za a azabtar da shi da wuta, da farar wuta, a gaban tsarkakan mala'ikun Allah da kuma Dan Ragon.
11Hayaki daga azabarsu yana tashi sama har abada abadin, kuma ba su da hutu dare ko rana - wadannan masu sujada ga dabban da siffarsa da kuma dukan wadanda suka karbi alamar sunansa. 12Wannan shine kira domin hakurin jimrewa na wadanda ke da tsarki, wadanda suke biyayya ga dokokin Allah da bangaskiya cikin Yesu."
13Na ji murya daga sama cewa, "Rubuta wannan: Masu albarka ne matattu da suka mutu cikin Ubangiji." Ruhu yace, 'I' domin sun huta daga wahalarsu, gama ayyukansu na biye da su."
14Na duba sai ga farin gajimare. Zaune a kan gajimaren akwai wani kamar Dan Mutum. Yana da kambin zinariya a kansa da lauje mai kaifi a hannunsa. 15Sai wani malaika ya fito daga haikalin, ya yi kira da murya mai karfi ga wanda ke zaune kan gajimare: "Dauki laujenka ka fara girbi, domin lokacin girbin duniya ya yi." 16Sai wanda ke zaune a kan gajimaren ya wurga laujensa bisa kan duniya, aka kuma girbe duniya.
17Wani mala'ika ya fito daga haikali a sama, shi ma yana da kakkaifan lauje. 18Sai wani mala'ika ya fito daga bagadin kona turare, wanda yake da iko kan wutar. Ya yi kira da murya mai karfi ga wanda yake rike da kakkaifan lauje, "Ka dauki kakkaifan laujenka ka tattara nonnan innabi daga itacen inabin na duniya, gama inabin ya nuna."
19Mala'ikan ya jefa laujensa duniya ya tattara girbin inabin duniya. Ya zuba shi a cikin babbar taskar wurin matsar ruwan inabi na fushin Allah. 20Aka tattake wurin matsar inabin a bayan birni, jini ya yi ta gudu daga wurin matsar inabin, ya kai kamar tsawon linzami a bakin doki, har mil dari biyu.

15

1Sai na ga wata alama cikin sama, babba mai ban mamaki: Akwai mala'iku bakwai rike da annobai bakwai, wadanda sune annobai na karshe domin da su ne fushin Allah zai cika.

2Na ga wani abin da da ya bayyana mai kama da tekun gilashi mai haske garwaye da wuta. Tsaye a gefen tekun sune wadanda suka ci nasara a kan dabban da siffarsa, da kuma lambar da ke wakiltar sunansa. Suna rike da molayen da Allah ya ba su.
3Suna rera wakar Musa, bawan Allah, da wakar Dan Rago: "Ayyukan ka manya ne da ban mamaki, Ubangiji Allah, Mai iko duka. Adalci da gaskiya hanyoyinka ne, Sarkin al'ummai. 4Wanene ba zai ji tsoron ka ba, Ubangiji, ya kuma daukaka sunanka? Domin kai kadai ne mai tsarki. Dukan al'ummai za su zo su yi sujada a gabanka domin an bayyana ayyukan ka na adalci."
5Bayan wadannan abubuwa na duba, kuma aka bude haikalin alfarwar shaida a cikin sama. 6Daga wuri mafi tsarki mala'iku bakwai masu rike da annobai bakwai suka zo. Suna sanye da tufafi masu tsabta, da lallausar linin mai haske, suna kuma da damarar zinariya a kirjinsu.
7Daya daga cikin rayyayun halitu hudu ya ba mala'iku bakwai tasoshin zinariya bakwai cike da fushin Allah wanda yake raye har abada abadin. 8Haikalin ya cika da hayaki daga daukakar Allah da kuma ikonsa. Ba wanda ya iya shigarsa har sai da annoban nan bakwai na mala'ikun nan bakwai suka cika.

16

1Na ji babban murya na kira daga cikin haikali tana ce wa malai'iku bakwai, "Ku je ku zuba tasoshi bakwai na fushin Allah a kan duniya."

2Mala'ika na fari ya je ya zuba tasarsa a kan duniya; munanan gyambuna masu zafi suka fito wa mutane wadanda suke da alamar dabbar, wadanda suka bauta wa siffarsa.
3Mala'ika na biyu ya zuba tasarsa cikin teku. Ya zama jini, kamar jinin wanda ya mutu, kuma kowane abu mai rai da ke cikin tekun ya mutu.'
4Malaika na uku ya zuba tasarsa a cikin rafuffuka da mabulbulan ruwa, sai suka zama jini. 5Na ji mala'ikan ruwaye ya ce, "Kai mai adalci ne - wanda ya ke yanzu wanda yake kuma a da, Mai Tsarkin nan, domin ka shari'anta wadannan abubuwa. 6Domin sun zubar da jinin masu ba da gaskiya da annabawa, ka basu jini su sha; shine abinda da ya dace da su. 7Na ji bagadi ya amsa, "I, Ubangiji Allah Mai iko duka, shari'un ka gaskiya ne da adalci."
8Mala'ika na hudu ya zuba tasarsa a kan rana, kuma aka ba shi izini ya kone jama'a da wuta. 9Suka kone da zafi mai tsanani, kuma suka sabi sunan Allah, wanda ke da iko akan annobai. Ba su tuba ba ko su daukaka shi.
10Sai malaika na biyar ya zuba tasarsa a kan kursiyin dabban, sai duhu ya rufe mulkinsa. Suka cicciji harsunansu saboda zafi. 11Suka yi sabon Allah na sama domin zafi da gyambunansu, suka kuma ki su tuba daga abin da suka yi.
12Mala'ika na shida ya zuba tasarsa cikin babban rafi, Yufiretis. Ruwansa ya bushe domin a shirya hanya da sarakuna za su zo daga gabas. 13Na ga kazamun ruhohi uku suna kama da kwadin da ke fitowa daga bakin diragon, da makaryacin annabi. 14Gama su ruhohin aljanu ne masu aikata alamun ban mamaki. Sun fita za su wurin sarakunan dukan duniya domin su tattaro su wuri daya saboda yaki a babbar ranar Allah Mai iko duka.
15("Duba! Ina zuwa kamar barawo! Mai albarka ne wanda ke zaune a fadake, wanda ke sanye da tufafinsa domin ba zai fita tsirara a ga tsiraicin sa ba.") 16Aka kawo su tare a wurin da ake kira Armagiddon da Ibraniyanci.
17Mala'ika na bakwai ya zuba tasarsa cikin iska. Sa'annan babbar murya ta fito daga cikin haikali da kuma kursiyin, cewa, "An gama!" 18Aka yi walkiya, da kararraki masu tsanani, da aradu da babbar girgizar kasa - girgizar da ta fi kowacce da aka taba yi tun da 'yan adam suke a duniya, girgizar da girma ta ke. 19Babban birnin ya rabu kashi uku, kuma biranen al'ummai suka fadi. Sai Allah ya tuna da Babila mai girma, sai ya ba wancan birnin koko cike da ruwan innabi wanda aka yi daga fushinsa mai tsanani.
20Kowanne tsibiri ya bace, sai ba a kara ganin duwatsun ba. 21Manyan duwatsun kankara, masu nauyin talanti, suka fado daga sama kan mutane. Suka zagi Allah domin annobar kankarar saboda annobar ta yi tsanani.

17

1Daya daga cikin mala'ikun nan bakwai wanda ke rike da tasoshi bakwai ya zo ya ce mani, "Zo, zan nuna maka hukuncin babbar karuwarnan da ke zaune a kan ruwaye masu yawa. 2Da ita ce sarakunan duniya suka yi fasikanci. Da ruwan inabinta na fasikanci marar dacewa ta sa mazaunan duniya suka bugu."

3Sai mala'ikan ya dauke ni cikin Ruhu ya tafi da ni jeji, sai na ga mace zaune bisa jan dabba cike da sunayen sabo. Dabbar tana da kawuna bakwai da kahonni goma. 4Matar kuwa tana sanye da tufafi na shunayya da kuma jar garura, ta kuma ci ado da kayan zinariya da duwatsu masu tamani da lu'u-lu'ai. Tana rike da kokon zinariya a hannunta cike da abubuwan kyama da na kazantar fasikancinta marar dacewa. 5Bisa goshinta an rubuta wani suna mai boyayyar ma'ana: "Babila mai girma, uwar karuwai da na kazamtattun abubuwan duniya."
6Sai na ga matar a buge da jinin masu ba da gaskiya da kuma jinin wadanda aka kashe su domin Yesu. Da na gan ta, na yi mamaki kwarai da gaske. 7Amma mala'ikan ya ce mani, "Don me kake mamaki? Zan bayyana maka ma'anar matar da kuma na dabbar da ke dauke da ita, dabban nan da ke da kawuna bakwai da kahonni goma.
8Dabban da ka gani da, yanzu ba ta, amma ta na kusan hawowa daga rami marar iyaka. Sa'annan za ta je hallaka. Wadanda ke zaune a duniya, wadanda ba a rubuta sunayensu cikin littafin rai ba tun kafuwar duniya - za su yi mamaki idan suka ga dabbar da da ta kasance, ba ta nan yanzu, amma ta kusa zuwa.
9Wannan al'amari na bukatar hikima. Kawunnan bakwai, tuddai ne bakwai da macen ke zaune a kai. 10Su kuma sarakuna ne bakwai. Sarakuna biyar sun fadi, daya na nan, amma dayan bai zo ba tukuna; sa'anda ya zo zai kasance na dan lokaci kadan.
11Dabban da ya kasance a da, amma yanzu ba shi, shi ma sarki ne na takwas; amma shi daya ne cikin sarakunan nan bakwai, kuma zai tafi hallaka.
12Kahonnin nan goma da ka gani sarakuna goma ne wadanda ba a nada su ba tukuna, amma za su karbi iko kamar na sarakai na sa'a daya tare da dabban. 13Ra'ayinsu daya ne, za su ba da sarautarsu da ikon su ga dabban. 14Za su yi yaki da Dan Rago. Dan Ragon zai ci nasara a kansu domin shi Ubangijin iyayengiji ne da Sarkin sarakuna - kuma tare da shi sune kirayayyun, zababbun, amintattun."
15Mala'ikan ya ce mani, "Ruwayen da ka gani, inda karuwar ke zaune, jama'a ce, da taro masu dumbin yawa, da al'ummai da harsuna.
16Kahonnin nan goma da ka gani - su da dabban za su ki karuwar. Za su washe ta su tsiranceta, za su lankwame namanta, za su kone ta gaba daya da wuta. 17Gama Allah ya sa a zukantansu su yi nufinsa ta wurin amincewarsa, su sadaukar da ikonsu na yin mulki ga dabban har sai maganar Allah ta cika.
18Matar da ka gani ita ce babban birnin nan da ke mulki bisa sarakunan duniya."

18

1Bayan wadannan abubuwa sai na ga wani mala'ika yana saukowa daga sama. Yana da babban iko sosai, duniya kuwa ta haskaka da daukakarsa. 2Ya yi kira da kakkarfar murya cewa, "Ta fadi, Babila mai girma ta fadi! Ta zama mazaunin aljannu, da matattarar kowanne kazamin ruhu da kuma mazaunin kowanne kazami da kyamataccen tsuntsu. 3Gama dukan al'ummai sun sha ruwan innabin fasikancinta. Sarakunan duniya sun aikata fasikanci da ita. Attajiran duniya sun arzuta da ikon rayuwar annashuwarta."

4Sai na ji wata murya daga sama ta ce, "Ku fito daga cikinta, mutanena, domin kada kuyi zunubi irin na ta, domin kuma kada bala'inta ya auko maku. 5Zunubanta sun taru sun yi tsayi har sama. Allah kuma ya tuna da miyagun ayyukanta. 6Ku saka mata gwargwadon yadda ta saka wa wadansu, ku biya ta ninki biyu na abin da ta yi; a cikin kokon da ta dama, ku dama mata ninki biyu.
7Kamar yadda ta daukaka kanta ta yi ta annashuwa, ku wahalsheta da azaba da bakin ciki haka. Domin ta ce a zuciyarta, 'Ina zaune kamar sarauniya; ni ba gwauruwa ba ce, kuma ba zan taba yin makoki ba,' 8Saboda haka a rana daya bala'inta zai auko mata; mutuwa, makoki da kuma yunwa. Wuta za ta kona ta kurmus, domin Ubangiji Allah mai iko ne, kuma shine mai hukuntata."
9Sarakunan duniya da suka yi fasikanci, har suka baude tare da ita, za su yi kuka da kururuwa domin ta sa'adda suka ga hayakin kunarta. 10Za su tsaya can nesa suna tsoron azabarta, suna cewa, "Kaito, kaiton babban birni, Babila, birni mai iko! Domin cikin sa'a guda hukuncinta ya zo."
11Manyan 'yan kasuwan duniya za su yi kuka da bakin ciki dominta, da shike ba wanda ke sayan kayanta kuma - 12kayan zinariya, azurfa, da duwatsun alfarma, da lu'u-lu'u, da lilin mai laushi, da hajja mai ruwan jar garura, da siliki, da jar alharini da itacen kamshi iri iri, da kayan da aka sassaka da itace mai tsada, da na tagulla, da na bakin karfe, da na dutse mai sheki, 13da kirfa, da kayan yaji, da turaren wuta, da mur da lubban, da ruwan innabi, da mai, da garin alkama, da alkama, da shanu, da tumaki, da dawakai, da kekunan doki, da bayi, da rayukan 'yan adam.
14Amfanin da kika kwallafa rai da duk karfinki sun fice daga gareki. Duk annashuwarki da darajarki sun bace, ba za a kara samunsu ba kuma.
15Manyan 'yan kasuwa na wadannan kaya da suka azurta ta wurinta, za su tsaya can nesa da ita, sabili da tsoron azabarta, kuka da kururuwar bakin ciki. 16Za su ce, "Kaito, kaito ga babban birni da take sanye da lilin mai laushi da tufafi masu jar garura da kuma jan alharini, da ta ci ado da kayan zinariya, da duwatsu masu daraja da lu'u-lu'u! 17A cikin sa'a guda duk dukiyan nan ta lallace. Kowanne matukin jirgin ruwa, da fasinjoji, da masu tuki da duk wadanda suke samun biyan bukatun rayuwarsu daga ruwa, suka tsaya can nesa.
18Suka yi kuka sa'anda suka ga hayakin kunarta. Suka ce, "Wanne birni ne ya yi kama da babban birnin?" 19Suka watsa kura a kawunansu, suka yi kuka da karfi, da kururuwa da bakin ciki, "Kaito, kaiton babban birnin nan inda duk masu jiragen ruwa suka azurta daga dukiyarta. Domin a sa'a guda an hallakar da ita." 20"Ku yi murna a kanta, sama, ku masu ba da gaskiya, manzanni, da annabawa, domin Allah ya kawo hukuncinku a kanta!"
21Wani kakkarfan mala'ika ya dauki wani dutse mai kama da dutsen nika, ya jefa shi cikin teku yana cewa, "Ta wannan hanya, Babila, babban birnin, za a jefar da ita kasa da karfi, ba za a kara ganinsa ba. 22Muryar masu kidar molaye, mawaka, masu busa sarewa, da na masu busa algaita, ba za a kara ji a cikinta ba. Babu wani mai kowanne irin sana'a da za a samu a cikinta. Ba za a kara jin karar nika a cikinta ba.
23Hasken fitila ba za ya kara haskakawa a cikin ki ba. Ba za a kara jin muryoyin ango da na amarya a cikinki ba, domin attajiranki sune 'ya'yan masu mulki a duniya, kuma ta wurin sihirinki kika yaudari al'ummai. 24A cikinta aka sami jinin annabawa da na masu ba da gaskiya, da jinin duk wadanda aka kashe a duniya."

19

1Bayan wadannan abubuwa na ji wata karar da ta yi kamar muryar mutane masu yawa a sama suna cewa, "Halleluya. Ceto, daukaka da iko sun tabbata ga Allahnmu. 2Hukunce - hukuncensa gaskiya ne da adalci, domin ya hukunta babbar karuwan nan wadda ta kazamtar da duniya da fasikancinta. Ya dauki fansar jinin bayinsa, wadda ita da kanta ta zubar."

3Suka yi magana a karo na biyu: "Halleluya! Hayaki na tasowa daga wurinta har abada abadin." 4Dattawan nan ashirin da hudu da rayayyun halittun nan hudu, suka fadi suka yi wa Allah sujada shi da yake zaune a kan kursiyin. Suna cewa, "Amin. Halleluya!"
5Sai wata murya ta fito daga kursiyin tana cewa, "Ku yabi Allahnmu, dukanku bayinsa, ku da kuke tsoronsa, da duk marasa iko da masu iko."
6Sai na ji murya kamar na kasaitaccen taron mutane, kamar rurin kogi na ruwaye masu yawa, kuma kamar tsawar aradu, cewa, "Halleluya! Gama Ubangiji yana mulki, Allah mai iko duka.
7Bari mu yi murna, mu yi farinciki matuka mu kuma ba shi daukaka domin bikin auren Dan Ragon ya zo, amaryarsa kuma ta shirya kanta. 8An yardar mata ta sa kaya masu haske da tsabta na lilin mai laushi" (domin lilin mai laushi shine ayyukan adalci na tsarkaka).
9Mala'ika ya ce mani, "Rubuta wannan: Masu albarka ne wadanda aka gayyace su zuwa bikin auren Dan Ragon." Ya kuma ce mani, "Wadannan kalmomin Allah na gaskiya ne." 10Na fadi a gaban kafafunsa domin in yi masa sujada, amma ya ce mani, "Kada ka yi haka! Ni ma abokin bauta ne tare da kai da 'yan'uwanka wadanda ke rike da shaida game da Yesu. Yi wa Allah sujada, domin shaida game da Yesu shine ruhun annabci."
11Sai na ga sama a bude, na kuma duba sai ga wani farin doki. Mahayinsa ana kiransa amintacce da gaskiya. Yana shari'a da adalci yana yaki. 12Idanunsa kamar harshen wuta suke, a kansa akwai kambuna da yawa. Yana da suna a rubuce a jikinsa wanda ba wani da ya sani sai dai shi da kansa. 13Yana sanye da riga da aka tsoma a cikin jini, kuma ana kiran sunansa Kalmar Allah.
14Rundunonin sama suna biye da shi a kan fararen dawakai, suna sanye da lilin mai laushi, fari mai tsabta. 15Daga cikin bakinsa takobi mai kaifi na fitowa, da ita yake sarar al'ummai, zai kuma mulke su da sandar karfe. Yana tattake wurin matsar ruwan inabi da matsananciyar fushin Allah Mai iko duka. 16Yana da suna a rubuce a rigarsa da cinyarsa: "Sarkin sarakuna da Ubangijin iyayengiji."
17Na ga mala'ika tsaye a rana. Yayi kira da murya mai karfi ga dukan tsuntsaye da ke firiya a sama. 18"Ku zo, ku tattaru saboda babban bukin Allah. Ku zo ku ci naman sarakuna, da naman sarakunan yaki, da naman manyan mutane, da naman dawakai, da na mahayansu, da naman dukan mutane, yantattu da bayi, marasa iko da masu iko."
19Na ga dabban da sarakunan duniya da rundunoninsu. Suna tattaruwa domin su yi yaki da wanda ke bisa doki da rundunarsa. 20Aka kama dabban tare da makaryatan annabawa da suka yi ayyukan al'ajibai a gabansa. Da wadannan alamu ya yaudari wadanda suka karbi alamar dabbar da wadanda suka yi wa siffarta sujada. Aka jefa dukansu biyu da rai cikin tafkin farar wuta mai ci.
21Sauran aka karkashe su da takobin da ke fitowa daga bakin mahayin dokin. Dukan tsuntsaye suka ci gawarwakinsu.

20

1Sai na ga mala'ika na saukowa daga sama. Yana da makullin rami marar iyaka, yana kuma da babar sarka a hannunsa. 2Sai ya dauki tsohon macijin, wanda shine iblis, ko shaidan, ya daure shi shekaru dubu. 3Ya jefa shi cikin rami marar iyaka, ya rufe shi ya kuma sa hatimi a bisansa. Hakan ya faru ne domin kada ya kara yaudarar al'ummai har sai bayan shekaru dubu. Bayan wannan, dole a sake shi na dan lokaci.

4Sa'annan na ga kursiyoyi. Wadanda ke zaune a bisansu sune wadanda aka ba ikon hukunci. Na kuma ga rayukan wadanda aka fille wa kai saboda shaidar Yesu da maganar Allah. Ba su yi wa dabban sujada ba ko siffarsa, suka ki su karbi alamar a goshinsu ko a hannu. Sun sake rayuwa, suka yi mulki tare da Kristi shekaru dubu.
5Sauran matattun basu sake dawowa da rai ba har sai da shekaru dubu din suka cika. Wannan shine tashin matattu na fari. 6Mai albarka ne mai tsarki ne kuma wanda yake da rabo cikin tashin matattu na fari! Mutuwa ta biyu ba ta da iko akan wadannan. Za su zama firistocin Allah da na Almasihu za su kuma yi mulki tare da shi shekaru dubu.
7Sa'adda shekaru dubu suka zo ga karshe, za a saki shaidan daga kurkukunsa. 8Za ya fito domin ya yaudari al'ummai da ke kursuyoyi hudu na duniya, Gog da Magog ya tattara su domin yaki. Yawan su zai zama kamar yashin teku.
9Suka bazu a fuskar duniya suka kuma kewaye sansanin masu ba da gaskiya, kaunataccen birni. Amma wuta ta sauko daga sama ta lankwame su. 10Shaidan, wanda ya yaudare su, aka jefa shi cikin korama ta farin wuta mai ci, inda aka jefa dabban da makaryacin annabin. Za su sha azaba dare da rana har abada abadin.
11Sai na ga babban kursiyi da wanda ke zaune a kansa. Duniya da sama suka guje wa fuskarsa, amma babu wurin da za su tafi. 12Na ga matattu manya da kanana- suna tsaye gaban kursiyin, aka bude litattafai. Sai aka bude wani littafi - Littafin rai. Aka yi wa matattu shari'a bisa ga abinda aka rubuta cikin litattafan, gwargwadon ayyukansu.
13Teku ta ba da matattun dake cikinta. Mutuwa da hades suka ba da matattun da ke cikinsu, aka yi masu shari'a gwargwadon abin da suka yi. 14Aka jefa mutuwa da hades cikin tafkin wuta. Wannan shine mutuwa ta biyu - tafkin wuta. 15Duk wanda ba a sami sunansa a rubuce cikin littafin rai ba, aka jefar da shi cikin tafkin wuta.

21

1Sai na ga sabuwar sama da sabuwar duniya, domin sama ta fari da duniya ta fari sun shude, ba kuma teku. 2Na ga birni mai tsarki, sabuwar Urushalima, wadda ta sauko kasa daga sama wurin Allah, shiryayya kamar amaryar da aka yi wa ado domin mijinta.

3Na ji babbar murya daga kursiyinta na cewa, "Duba! Mazaunin Allah yana tare da 'yan adam, zai zauna tare da su. Za su zama mutanensa, Allah kuma da kansa zai kasance tare da su ya kuma zama Allahnsu. 4Zai share dukan hawaye daga idanunsu, kuma babu sauran mutuwa, ko bakinciki, ko kuka, ko azaba. Abubuwan da sun shude.
5Shi wanda yake zaune a kan kursiyin ya ce, "Duba! Na maida kome ya zama sabo." Ya ce, "Ka rubuta wannan domin wadannan kalmomi amintattu ne da gaskiya". 6Ya ce mani, "Wadannan abubuwan an gama! Ni ne Alpha da Omega, farko da karshe. Ga mai jin kishi, zan bashi kyauta daga mabulbular ruwan rai.
7Wanda ya ci nasara, zai gaji wadannan abubuwa, ni kuma zan zama Allahnsa, shi kuma ya zama da na. 8Amma ga matsorata, da marasa bangaskiya, da masu kazanta, da masu kisan kai, da fasikai, da masu sihiri, da masu bautar gumaka, da dukan makaryata, mazaunin su zai kasance cikin tafki mai ci da farar wuta. Mutuwa ta biyu kenan."
9Daya daga cikin mala'ikun bakwai ya zo wurina, wanda yake dauke da tasoshi bakwai cike da annobai bakwai na karshe, yace, "Zo nan. Zan nuna maka amarya, matar Dan Rago". 10Sai ya dauke ni cikin Ruhu zuwa wani babban dutse mai tsawo ya nuna mani birni mai-tsarki, Urushalima, tana saukowa daga cikin sama daga wurin Allah.
11Urushalima tana da daukakar Allah, shekinta yana kama da dutse mai tamani, sai kace dutsen yasfa, garau kamar karau. 12Tana da babban garu mai tsawo, da kofofi goma sha biyu, da mala'iku goma sha biyu a kofofin. Akan kofofin an rubuta sunayen kabilu sha biyu na 'ya'yan Isra'ila. 13A gabas akwai kofofi uku, a arewa kofofi uku, a kudu kofofi uku, da kuma yamma kofofi uku.
14Garun birnin yana da harsashin gini goma sha biyu, a bisansu akwai sunaye goma sha biyu na manzanni goma sha biyu na Dan Rago. 15Shi wanda yayi magana dani yana da sandan awo na zinariya domin ya auna birnin, da kofofinsa, da garunsa.
16Birnin; da tsawonsa da fadinsa iri daya ne. Ya gwada birnin da sandar awo, mil dubu sha biyu a tsaye (fadinsa, da tsawonsa, da tsayinsa duka daya ne) 17Ya kuma gwada garunsa, kamu 144, bisa ga gwajin 'yan adam (wanda shine ma'aunin mala'ika).
18An gina garun da Yasfa birnin kuma da sahihiyar zinariya, mai kama da madubi mai kyalli. 19An kawata harsashin garun da kowanne irin dutse mai tamani. Na fari yasfa, na biyu saffir, na uku agat, na hudu emerald, 20na biyar Onis, na shida sardiyus, na bakwai kirisolat, na takwas beril, na tara tofaz, na goma kirisofaras, na sha daya yakinta, na sha biyu kuma ametis.
21Kofofi goma sha biyu lu'u-lu'ai ne goma sha biyu; kowacce daya a cikin kofofin daga lu'u-lu'u daya aka yi shi. Titunan birnin kuwa zinariya ce sahihiya, sai kace madubi garau. 22Ban ga haikali a cikin birnin ba, gama Ubangiji Allah Mai iko duka da Dan Ragon su ne haikalinsa.
23Birnin ba ya bukatar rana ko wata su haskaka shi gama daukakar Allah ta haskaka shi, kuma fitilarsa Dan Rago ne. 24Al'ummai za su yi tafiya cikin hasken birnin. Sarakunan duniya kuma za su kawo daukakarsu cikinsa. 25Kofofinsu kuma ba za a rufe su da rana ba, babu dare kuma a can.
26Za su kawo daukaka da darajar al'ummai a cikinsa, 27babu wani abu mai kazanta da zai taba shiga cikinsa. Ko wanda yake aikata abin kunya da karya, sai wadanda an rubuta sunayensu a cikin littafin rai na Dan Rago kadai.

22

1Sai mala'ika ya nuna mani kogin ruwan rai, ruwa mai tsabta. Yana fitowa daga cikin kursiyin Allah da na Dan-Rago 2ta tsakiyar titin birnin. A kowanne gefen kogin akwai itacen rai, mai ba da 'ya'ya iri goma sha biyu, kowanne wata. Ganyayen itacen kuma domin warkar da al'ummai ne.

3Babu sauran la'ana nan gaba. Kursiyin Allah da na Dan Rago za su kasance a cikin birnin, bayinsa kuma za su yi masa bauta. 4Za su ga fuskarsa, sunansa kuma zai kasance a goshinsu. 5Babu sauran dare; ba za su bukaci hasken fitila ko hasken rana ba gama Ubangiji Allah zai haskaka su. Za su yi mulki har abada abadin.
6Mala'ika ya ce mani, "Wadannan kalmomi amintattu ne da gaskiya. Ubangiji, Allah na ruhohin annabawa, ya aiki mala'ikansa ya nuna wa bayinsa abin da lallai zai faru ba da dadewa ba". 7"Duba! Ina zuwa ba da dadewa ba! Mai albarka ne wanda ya yi biyayya da kalmomin littafin nan."
8Ni, Yahaya, nine na ji na kuma ga wadannan abubuwa. Sa'adda na ji na gan su, sai na fadi gaban kafaffun mala'ikan da ya nuna mani wadannan abubuwa domin in yi masa sujada. 9Ya ce mani, "Kada ka yi haka! Ni abokin bauta ne tare da kai, tare da 'yan'uwanka annabawa, da wadanda ke biyayya da kalmomin littafin nan. Yi sujada ga Allah!"
10Ya ce mani, "Kada ka rufe kalmomin anabcin littafin nan, gama lokaci ya kusa. 11Wanda yake mara adalci, bari ya cigaba da yin rashin adalci. Wanda yake mai kazanta bari ya cigaba da kazantar da kansa. Wanda yake mai adalci bari ya cigaba da yin adalci. Wanda yake mai-tsarki, bari yaci gaba da tsarki."
12"Duba! Ina zuwa ba da dadewa ba. Sakamakona na tare da ni, zan saka wa kowa gwargwadon aikin da ya yi. 13Nine Alpha da Omega, farko da karshe, mafarin abu da karshensa.
14Masu albarka ne wadanda suka wanke rigunansu domin su sami izini su ci daga itacen rai su kuma shiga birnin ta kofofinsa. 15A waje akwai karnuka, masu sihiri, masu bautar gumaka, fasikai, masu kisan kai, da duk wanda yake kaunar aikata rashin gaskiya.
16Ni, Yesu na aiko mala'ikana ya shaida maku wadannan abubuwa saboda ikilisiyoyi. Nine tushe da zuriyar Dauda, tauraron asubahi mai-haske."
17Ruhu da Amarya suka ce, "Zo!" Bari wanda ya ji ya ce, "Zo!" Kowanne mai jin kishi, da kowanne mai bukatar ta, bari ya sami ruwan rai kyauta.
18Ina shaida wa duk mai jin kalmomin anabcin wannan littafi: Idan wani ya kara a kansu, Allah zai kara masa annoban da ke rubuce a cikin littafin. 19Idan wani ya rage daga kalmomin wannan littafin anabci, Allah zai rage rabonsa daga cikin itacen rai daga cikin birni mai-tsarki, wadanda aka rubuta cikin wannan littafi.
20Shi wanda ya shaida wadannan abubuwa ya ce, "I! Ina zuwa ba da dadewa ba." Amin! Zo, Ubangiji Yesu! 21Alherin Ubangiji Yesu ya kasance tare da kowanne dayanku. Amin.